Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Friday, December 7, 2018

BAZAN BARSHIBA COMPLETE STORIES IN HAUSA LANGUAGE

adsense here
Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
        (admin
   Arewa hausa novels
       Novels villa
     Duniyan novels
   Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
          And
Cool novel, makeup and cooking)

      WHATSAPP NO:
    +2347039625239
```🔮BAZAN BAR SHI BA!🔮```



_[9/25/2016]_







*Na Billy giro😊*



               🔮🔮🔮🔮񛠊
      _*page  1*_
 

Rayyanat! Rayyanat!! Rayyanat!!!
  Er 16 yrs ce ta fito da gudu tana fad'in "Na'am Baffanah"
  Shiru baffan nata yayi yana mai kallon Rayyanat wacce ta kasance chocolate ba qiba ba rama tana da kyau daidai gwargwado tana sanye da riga da zane bara da bana sae dankwalin kanta da shima ba kalarkayan jikin ta bane ga zanen jikinta duk gabad'ayan sa dashi ne ba masoka tsintsinya gashi ta riqe wani gurin da ya yage bata son aga jikin ta yace"Rayyanat baki sami allura da zare bane wannan karon? Abba ban samu ba naje suka ce baza su ara min ba sun gaji da siya ina qare musu zaren"cikin muryar kuka ta qarasa maganar ,Baffan ta yace"kar kiyi kuka Rayyant inshaAllah yau idan mai gari ya biyani kud'in noman da nake masa zan saya miki allura da zare domin ki huta da aro maqota kinji"to Baffanah na gode  Allah yasa ayi nasara fiye da kullum"
yace "Amin Rayyant, zan tafi ki kula da kanki banda yawon maqota"inshaAllah amma Abba yau baka so na raka ne?Rayyanat ta yaya zaki fita bayan zanin ki ya yage ga samarin da ke dandali a tsakiyar gari"Haka ne Baffa Allah kiyaye hanya"Amin Amin.
   Daga haka ya fita  rataye da fartanya kan kafad'ar shi inda Rayyant tabi mahaifin nata da kallo wanda shima tufafin jikin sa  duk sun tsufa sun tamure.
   sae da ta daina hango shi sannan ta koma d'aki tayi zaune
tana qarewa d'an akurkin d'akin ta kallo   wanda ba wasu kayan kirki a ciki face d'an kunshin tufafin ta da baza su wuce kala biyu zuwa uku ba sae tsofuwar tabamar da take kwanciya da wani  pillow akai mai kama latsatstsen biredi sae gidan sauro da aka dunqule shi aka soka jikin taga sae wasu kwallaye guda biyu da ke cikin d'akin da bansan meye a cikin su ba.
  Tana cikin qarewa d'akin kallo cikin ta ya shiga qugi sbd yunwar da ke addabar ta wacce tun safiyar jiya da suka ci abinci  ita da Baffan ta   har yau washe gari basu sake samun abinda suka ci ba.

 Kwanciya tayi ko zata samu bacci ya d'auke ta kafin Baffan ta ya dawo amma yunwa ta hana ta bacci kamar yanda tayi fama a daren jiya wanda sae da ta cika cikin ta da ruwa ta samu tayi bacci haka ko yanxu tashi tayi taje waje gurin randar ruwa ta cika cikin ta tap ta koma ta kwanta .
   Har bacci ya soma d'aukar ta ne taji sallamar wata qawar ta mai suna "Sarat"

Sae da Rayyanat ta amsa mata sallama sannan ta shigo .
  Yarinya ce doguwa er sililiya baka wacce ita ma tana da kyaun ta dai dai gwargwado zama tayi tace"Rayyanat kiyi haquri fa tun jiya naso ace nazo amma shiryen shiryen tafiyar da muke yi na komawa Birni bai barni ba "
  D'an guntun murmushi Rayyanat tayi taji kamar ita ce zasu je Birni ita da Baffan ta sbd ta kasance tana mugun son zuwa Birni amma ko sau d'aya bata ta6a samun zuwa ba.

Sarat ta miqa mata wata er baqar leda wacce ake kira cefanen mutum d'aya tace"dan Allah kar ki ce baza ki kar6a ba  sbd nasan halin ki kuma ban saya miki don wata manufa ba sae don nasan kina bala'in son rogo inda har ka kasuwa naje na saya miki  amma kiyi haquri nasan ba kya son haka "
  ba komai Sarat a yau zan kar6i kyautar ki sbd zaki tafi ki barni ban kuma san yaushe zamu sake had'uwa ba nagode amma yaushe ne zakuyi tafiyar ?a yau d'in nan kuma a yanzu shiyasa na baki haquri kan rashin zuwa na tun jiya nima ban so haka ba wlh...kar ki damu domin nafi kowa sanin yanda kika damu dani shiyasa a kullum bani da wata qawar da ta fiki...Uhm na gode Rayyanat ni zan tafi su Abba na a bakin qofar gida da mota suna jiran fitowa ta .
  Nan Rayyanat ta tashi suka fito inda Rayyanat ta russuna  cikin ladabi ta gaida iyayen Sarat kafin wani  d'an matashin saurayi ya fito a cikin motar wanda sak Sarat ce da alama yayanta ne.
  Da sauri Rayyanat ta duqar da kanta qasa cikin jin kunya tana d'an kame kame gayen yayi murmushi yace"ako yaushe ina sonki Rayyanat ba kuma zan daina ba duk rintsi duk wuya ina tare da sonki a cikin zuciya ta koda kuwa bana raye.

 Ga wannan na roqe ki ki kar6i kyauta ta ta farko da na ta6a baki wanda a duk lokacin da ki ka sanya abinda ke ciki zaki kasance cikin farin ciki sbd tamkar kina tare da nine,
 ina fatar masoyiya ta zata kar6i kyautar da na mata ko don tsalkakekken son da take min,,,cikin tausassar muryar ta mai sa shi natsuwa tace "yaya Anwar ban ta6a kar6ar kyautar ko wane d'a namiji ba face ta mahaifina amma yau zan fara a kanka kuma nayi maka alqawari kai kad'ai ne d'a namijin da zan ci gaba da kar6ar kyautar sa har abada kuwa bazan ta6a sa6a alqawarin da na maka ba, ka riqa tuna hakan ako yaushe domin nima na riqa kiyaye wa"
A hankali ya lumshe kyawawan idanun sa yace"InshaAllah Rayyanat bye mu zamu tafi dan Allah ki kula min da kanki "
   Daga haka ya shiga mota ya zauna seat d'in driver ya tashi mota yana danne hawayen da ke qoqarin zubo mishi yayinda yake kallon fuskar Rayyanat ta jikin mirror.
   Sarat kuwa bye bye take yiwa Rayyanat yayinda kowannen su ke fitar da hawaye a idon shi .
 Tsaye take har suka 6ace ma ganin ta nan ta kalli Viva ledar da ke hanun ta ta rungume ta tsam a qirjin ta wasu zafafan hawaye suka gangaro kan kumatun ta inda a hankali ta furta cewa"ina sonka yaya Anwar ba kuma zan daina sonka ba har abada duk rintsi duk wuya ina tare da kai koda kuwa bana raye to kuwa ruhi na zai kasance tare da kai"

    🔮🔮🔮🔮🔮

_*Page  2*_

Komawa tayi daga ciki cike da kewar Anwar da Sarat .
   Bata yarda ta bud'e ledar ba ta ajiye kusa da ledar rogon da Sarat ta kawo mata a cewar sae Mahaifin ta ya dawo ko za a bud'e komai.

Har guraren la'asar mahaifin ta bai dawo ba haka taci zama duk yunwar da take fama da ita bata ci rogon ba iya karta ta qara sakawa cikin ta ruwa .

  Sae guraren qarfe biyar mahaifin ta ya dawo yayinda fuskar shi take cike da damuwa.
Rayyanat taje a natse cikin murna tana tarbon mahaifin ta inda ta kai hannu ta d'auke fartanyar da ke kan kafad'ar sa ta kuma d'obo ruwa ta bashi,
 bai sha ruwan ba sae hannun sa ya tara ya wanke ya zauna a sukwane tare da dafe kan shi.
   Rayyanat da ko kad'an bata son ganin mahaifin ta cikin damuwa nan take idanun ta suka ciko da qwallah ta durqusa a gaban shi tare da jaye hannayen sa da ya dafe kansa.
  Muryar ta na rawar kuka tace "me yake faruwa ne Baffa dan Allah ka sanar da ni"
   A hankali mahaifin ta ya d'ago idanuwan sa da sukayi jajir ya goge en guntayen hawayen da ke gefen su yace"Rayyanat na kasance bani da wani  buri a rayuwa sae don ganin na faranta miki hakan yasa tun lokacin da mahaifiyar ki ta rasu ta barki kina jinjira naqi nayi aure don kawai kar ki shiga quncin rayuwa domin bansan matar da zan auro wace iri bace shiyasa na haqura da aure gavad'aya sbd zan iya zamowa auri sake idan har na had'u da matan da ke quntata miki ni kuma bana son kasance wa haka kuma gashi bani da wasu en uwa da zan kaiki a gurin su shiyasa na za6i na raine ki da hannu na,yayinda na zame miki tamkar uwa na kuma so na kasance uban da ba wani  abu da zaki nema ki rasa amma talauci bai bar na miki haka ba  kiyi haquri Rayyanat da na kasance uban da kullum sae kin nema kin rasa ba yin kaina bane wannan jarabtar ubangiji ce wacce a kullum nake roqon Allah ya kawo muna qarshen ta muna masu lashe jarabawar ba tare da mun sa6a masa ba.
   Rayyanat nasan ke 'yace ta gari zaki fahimci abinda nake nufi da kuma abinda zan fad'a a yanzu.
   Rayyanat a yau zamu kwashe komatsan mu mu koma daji da zama can gurin gonar mai gari da nake masa noma....Baffa me yasa zamu koma inda ba kowa ?dole ne Rayyanat sanin kan ki ne wannan gidan ba nawa bane kuma bani da wani  gida na kaina haya muke kuma sanin kanki ne duk wata na kanyi qoqarin ganin na biya kud'in haya koda kuwa su kad'ai ne suka rage mana na abinci amma a yau Bala yaje har gurin mai gari yakai  qara ta kan cewa bana biyan shi kud'in haya wai har ma yana bina na wata biyu naqi na biya shi, duk da cewa nayi ma mai gari bayanin cewa ba gaskiya ya fad'a ba amma mai gari ya zare kud'in noman da nake binsa na wata d'aya ya bawa Bala na zamo bani da ko sisi kuma Bala ya nemi na bar masa gida wai yana so zai saka wad'an da ke biyan sa duk wata.
 Ba irin haqurin da ban bashi ba amma yaqi shiyasa mai gari yace idan har zan iya ya bani dama naje can kusa da gonar shi na haqa bukka mu riqa zaman mu a can tunda ba wasu namun dajin da ke cutarwa a gurin.
   Cikin kuka Rayyanat tace"Allah yasa haka shi yafi Alhairi Baffa"Amin Rayyanat bari naje cikin gari naga ko zan sami wani  aikin da zanyi a biyani mu samu abinda muka ci kafin mu kwanta"
   Kallon mahaifin ta tayi kafin take share hawayen da ke kan fuskar ta tace"Baffa akwai rogo da Sarat ta kawo min ka bari kaci tukun ko zaka fita"
    Aa Rayyanat ki dai ci in yaso idan Allah yasa nayi nasara sae mu qara cin abinda ya samu,, Baffa rogon fa mai yawa ne kuma tun safe na ajiye shi sae kazo muci tare,,,girgiza kansa yayi yayinda yake qara jin son er shi sbd yasan halin Rayyanat komai qanqantar abu bata yarda taci ita kad'ai sae tare da shi.
  Nan ya dafa kanta yace"Allah yayi miki albarka Rayyanat ya kuma sanya nasara da albarka a cikin al'amurranki ya kuma sauya miki wannan rayuwa da muke ciki ma'ana nan gaba kad'an ki kasance cikin wadata da walwala had'e jin dad'i mai d'orewa har izuwa qarshen rayuwar ki"Amin Baffa na gode.
   Nan ta d'auko musu rogo suka ci bayan sun kammala ta d'auko  ledar da Anwar ya bata ta bawa Baffan ta ba tare da tace da shi komai ba yace"Rayyanat daga ina wannan ledar ta fito? Cikin jin kunya ta duqar da kanta ta kasa cewa komai wanda hakan yasa nan take ya fahimci inda ledar ta fito yace"Anwar ko sun tafi kenan? Eh sun tafi tun d'azu ,,to Allah ya kiyaye hanya ,,Amin Baffa,,tace"Baffa kayi haquri ban kar6a ba sae don ya had'a ni da Allah"ba komai kuma ai ba a maida hannun kyauta baya.
   Nan Abban ta yace ta bud'e kayan koda ta bud'e kala biyu ne masu kyau less da atamfa kuma da hijab kala biyu wato kalar kayan sae takalmi taki d'aya da kuma tokar wanka mai had'e da set d'in turare sae wata envelope da aka d'ora akai wacce ta bawa Baffan ta tace shi zai bud'e sbd tana ganin kamar kud'i ne a ciki koda mafahaifin ta ya bud'e en dubu dubu ne sabbi dal har dubu biyar sae wani  tsadadden zoben azurfa black an white da wata er guntuwar takarda soke a cikin zoben.
  kasa had'a ido tayi da Baffan ta yayinda yake miqa mata kayan bata kar6i kud'i ba sae zobe ta kar6a had'e da takarda tace"Baffa ai a gurin ka kud'in ya kamata su kasance da kuma wad'anan tufafin"Rayyanat ki ajiye komai a gurin ki sbd kinga fita zanyi naje naga gurin da ya kamata mu haqa bukka na fara aikin kafin gobe sbd tun da safe yake so mu bar gidan"
  Baffa muje na taya ka ba musu yace "to adana kayan muje"
 kwalla taje ta bud'e ta saka kayan suka fita.



Da suka fita basu suka dawo ba sae yamma liqis.

Da dare Rayyanat bata iya bacci ba sae da ta d'auko wannan takardar ta fara karantawa kamar haka
*_"Rayyanat ina so ki saka wannan zoben a yanzu kuma kimin alqawari baza ki ta6a cire shi ba har abada domin cire wannan zoben tamkar kin cire ni a cikin zuciyar ki ne_*

Murmushi ne ya bayyana a fuskar ta yayinda take sanya zoben inda ta rufe idon ta a hankali tace"
*_yaya Anwar nayi maka alqawari wannan zoben ba zai ta6a fita a yatsa ta ba sae dai idan mutuwa nayi aka cire shi_*

Daga haka ta kwanta sae kallon yanda zoben yayi matuqar kyau a yatsan ta take har ta shiga magana a ranta cewa
_"Da ace ko mutuwa nayi baza a raba ni da zoben nan ba da nafi kowa farin ciki"_
  Yaya Anwar ina ma ace zoben nan mai 6acewa ne da na bashi umarnin ya 6ace a lokacin da na mutu har akaini makwanci na don dai kawai ya kasance ina tare da kai a duk inda nake ko da yake ko ba zoben nan kana tare da ni sbd kana cikin zuciya ta ba kuma zan ta6a iya fitar da kai ba kamar yanda hanta bata iya rabo da jini.
  Tana maganar ne a fili cikin natsuwa tamkar anwar na kusa da ita.


Washe gari tun da asuba ta had'u da mummunan labari su Anwar sunyi had'arin mota kuma ba wanda ya rayu a cikin su kuka taci tamkar ranta zai fita Baffan ta kuwa sae bata baki yake yana aikin rarrashi.
  Suna cikin haka ne Bala yazo cike da masifa yasa aka yi ta fitar da kayan su ana watsi da su wanda hakan ya qara sa Rayyanat cikin wani  yanayi ganin yanda ake wulaqanta mahaifin ta da ke ta ba Bala haquri kan su daina watsar musu da kaya bai saurare shi ba sae da suka fitar da kayan kaf tare da jan hannun Rayyanat suka ingiza ta waje wacce ta kasa yin komai sae kuka .
  Mahaifin ta ne ya kama ta ta tashi sbd fad'uwar da tayi garin ingiza ta da akayi har ma suka fasa mata baki.


Nan suka fara kwasar kayan su suna zubawa a cikin wani  tsofon baro da mahaifin ta yayi yayin tallar ruwa a ciki wanda maya biyu sukayi suka gama kwasar kayan na su hakan yasa basu koma cikin gari ba sae qoqarin ganin sun qarasa bukkar da suke su samu su zuba kayan su.

Bayan sun kamalla ne mahaifin ta ya zauna yana qara bata baki kan tayi haquri da komai na duniya sae haquri kuma mai wuce wa ne amma Rayyanat tamkar mahaifin ta na qara mata qarfin kuka ne domin da zarar ta kalli zoben da ke kan yatsar ta sae ta sake fashewa da wani  sabon kuka .

Haka Rayyanat  tayi sati tana kukan rashin Anwar da Sarat duk tabi ta rame ta zamo tamkar ba ita ba,sae dai yanzu suna samun d'an abinda suka ci ta hanyar amfani da kud'in da anwar ya bawa Rayyanat.


Yau kusan wata biyu kenan da komawar su jeji tun Rayyanat na tsoron zaman jejin har ta saba sae dai har yañzu mutuwar anwar bata sake ta ba bcs duk lokaçin da ta kàlli zoben da ke kan yatsar ta sae ta zubar da qwallah.


Tafe suke ita da mahaifin ta sun fito daga cikin gari  suna qoqarin tsallake titi nan wata mota tazo a gurguje ba qaqqautawa  inda Rayyanat tayi saurin jawo hannun mahafinta don ganin sun kaucewa motar amma tuni motar tayi awon gaba da mahaifinta,a rikice ta d'ora hannu aka ta kurma wani  irin ihu mai cike da tsànàñin firgici ganin yanda motar ta sake dawowa kan mahaifin ta tare da jefo bunch d'in 1k  kan fuskar mahaifin nata aka kuma ja motar a tsiyace inda duk tashin hankalin da take ciki bai hana ta qure lambar motar da kallo ba wanda bata kauda idon ta ba sae da ta hadda ce numbar.
   Sannan ta koma kan mahaifin ta da ko shurawa bai yi ba ta shiga girgiza shi cikin kuka tana kiran"kai kad'ai ka rage min Baffa dan Allah ka tashi wlh nayi ma alqawari ko shi waye *BA ZAN BAR SHI BA!*sae na rama abinda ya maka dan Allah Baffa ka tashi kar kace zaka tafi ka bar ni,kasan bani da wani  a duniyar nan bayan kai,ka tashi Baffa! Baffah!! Baffah!!!
 Kuka ta shiga yi sosai har da majina ganin Baffan nata yaqi ya motsa nan ta rungume shi qam a qirjinta tana ci gaba da kuka mai mugun ban tausayi .




*_Billy giro😊_*
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BAR SHI BA!```🔮





```Na Billy giro😊```




09/12/2016




🔮```3```🔮
Haka Rayyanat taci gaba da kuka har ta gode Allah dmn ta fahimci tuni Allah ya kar6i ran mahaifinta.
   Sati  d'aya da rasuwar mahaifinta ta baro qauyen su ba tare da kowa ya sani ba.
   Kuka takeyi sosai a cikin mota har suka iso garin kano ta shiga qarewa garin kallo ba tare da tasan inda zata je ba wani  kuka ta shiga yi sosai shike nn yanzu bata da kowa a duniya sae wanda yaga Allah ya taimaka mata,yanzu bata san wace irin rayuwa zata shiga ba kawai dai tasan duk rnr da Allah ya had'a ta da wanda ya kashe mahaifinta Baza ta bar shi ba! koda kuwa itama zata bar duniya ta dalilin hakan.
  Zaune take kusa da wani  gidan mai sae rusar kuka take kamar yanzu ne mahaifin nata ya rasu.
  Mabaratan da take zaune kusa da su sae kallonta suke abin tausayi dmn ganin suke har sunfi ta dama a yanayin da suka ganta ciki.
  Ta jima sosai a gurin ga yunwa ga qishi ta tashi tsaye da qyar sbd jirin da ke d'ibar ta, kallon mabaratan da ke kusa da ita take ta hango er gorar ruwa aje kusa dasu ta fara tako cike da son taje tace su en mata ruwan tasha ba tare da ta damu da ganin su mabarata bane ita dai ta samu ta kawadda qishin da take ji.
    Gab take da isa gurin su wata irin tsaleliyar mota ta tsaya a gurin wanda ke ciki ya sauke glass d'in motar a hankali yana kallon mabaratan cikin wani yanayi na qyama kamar wanda zai yi amai.
 Hannu yasa ya zaro kud'i a aljihun sa 1k bunch ya jefa musu kud'in dai dai Rayyanat ta juyo kan ganin yanda taga mabaratan sun qure guri d'aya da kallo, yanayin yanda ya jefa musu kud'in yasa gabanta yayi mugun fad'uwa kuma tabbas kalar motar da ta kad'e mahaifinta ce take gani tsaye a gabanta

 Mabaratan sukayi ruu! dmn d'aukar kud'in da aka jefo musu sae qoqarin kada Rayyanat suke da kud'in ke tsakiyar qafafunta ita kuwa ko qwaqqwaran motsi ta kasa sae qarewa motar kallo take ba tare da ta iya hango wanda ke ciki ba dmn tuni ya mayarda glass d'in motar sa ya rufe.
 Tako ta fara a hnkli dmn ta kai idonta ga numbar motar,taga ba ko shakka ita ce numbar motar da ta kad'e mahaifinta wani  irin yanayi Rayyanat ta tsinci kanta a ciki marar misaltuwa idanuwanta suka ciko tap da qwalla ta samu da qyar ta d'aga yatsarta tana nuna  numbar motar, cikin rasa iya motsa koina na ga66an jikinta take ci gaba da kallon numbar.
 firgigit tayi ganin motar ta  fara tafiya sauri sauri  ta shiga bin motar wacce still yatsarta na kan numbar motar tana nunawa........"ke! ke!! ke!!!" shine abinda mutanen gurin keta fad'a amma sam hanklin Rayyanat na tare da motar hakan yasa taji an kwashe ta kai tsaye  kanta ya daki wani  guri tun daga lokacin bata qara sanin inda take ba.

Matar da ta kad'e Rayyanat ce keta faman zarya a asibiti cike da takaici se faman duba wristwatch d'inda ke hannunta take....wayar ta ce ta shiga ringing ta d'aga cikin sauri tace"yauwa honey pls kazo *MAN HOSPITAL* na kad'e wata yarinya ne"
daga haka ta katse wayar ba jimawa ya iso sae ga doctor ya fito yace taje yanzun zata iya ganin yarinyar.

Sosai Rayyanat ta samu rauni har dai saman goshinta sae dai bata farfad'o ba sae bacci take ana mata qarin jini.
   "Garin yaya haka ta faru?cewa da mijinta
Tace
"Honey kasan matsalar talaka da baqin hassada duk inda motar mai kud'i ta wuce sun fara binta da ido kenan shine fa  ita bata tsaya a kallo ba har bin motar take kamar motar ubanta! sae wani qoqarin kamo motar take ana faman kiranta amma a banza! gashi yanzu duk ta 6ata min tsari har yaya ya tafi ya barni may be ma har jirgin su umma ya sauka ya kai su gida,eyya sorry yanzu ki tafi kawai in yaso ni na tsaya.

Tunda Rayyanat ta farfad'o bata da aiki sae na kuka duk yanda yaso tayi mai magana taqi har kusan kwana biyu snn aka sallameta .


Gidan shi yaje da ita suna shiga falo yaji qarar fashewar glass da sauri ya kalli inda yaji sautin yaga matar sa ce ta saki glass cup tana masa wani  mugun kallo cikin tsananin kishi .
  Da mamaki yace"lafiya pretty"har ka tambaya! wnn wace er iskar ce ka shigo min da ita a gida!
 Yace"ikon Allah yarinyar da ki kad'e ce fa aka sallame ta yau......to dan ita ce sae ka wani  kwasota ka kawo min ita a gida har da wani  riqo mata qunshin ledar ta,to pretty ina kike son taje  bata qarasa jin sauqi ba kuma kinsan har yanzu ko magana batayi ba bare asan daga inda ta fito....fuuu! tazo ta fizge qunshin Rayyanat dake hannun shi tace"Ai tunda ba gidan ubanta bane wlh sae ta fita!da gani ma irin shegun yaran nn ne da iyayen su ke jefarwa suna gantali a hanya shine tayi shiru taqi fad'in inda ta fito ita ala dole taga ta samu mafaka,nn ta jefa ma Rayyanat qunshinta tace"oya! fitar mana daga gida shegiya! kije can ki qarata da baqin gantalin ki da uwar ki taja miki!
   A hnkli Rayyanat ta duqa ta tsince en kayanta da suka fito cikin ledarta snn ta tashi tana mai share qwallah a idonta ta fita.


```Billy giro😊```
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BAR SHI BA!```🔮









```Na Billy giro😊```





11/12/2016





🔮```4```🔮
Cikin hanzari mijin pretty yabi Rayyanat yana fad'in ta dakata.
   Kamar kar ta tsaya sae kuma ta tsaya ba tare da ta juyo ba sbd kuka take yi sosai har yana so yaci qarfinta.     Kafin ya qarasa gurinta pretty tayi sauri tasha gabanshi tace"wlh bafa zata zauna a gidan nn ba!bai kula ta ba sae qoqarin wucewa yake tana tare mai hanya ya tsaya tare da nuna  ta da yatsa snn yace"kinga pretty kar ki kaini qul fa!
daga haka ya ra6a ta gefenta ya wuce yace da Rayyanat "muje"ta sake shan gabanshi
tace"ban gane kuje ba ina zaka tafi da ita? Koma ina ne ba ruwanki yanzu,tunda ke baki san ki tasauya ma bayin Allah ba!ta wani le6ace baki tace"meye abin tausayi wa talaka ko talaka mabaraciya wad'anda basu da burin da ya wuce ganin bayan dukiyar mutum kullum cikin roqo da fad'in a basu,basa nema sae dai a nema a basu sbd baqin lalaci irin nasu.
   Ki iya bakin ki pretty kullum cikin aibata talaka kike talaka ba abin gori bane dmn kema baki wuce Allah ya jarrabace ki da talauci ba........ Tuf!bakin ka ya sari d'anyen kashi wlh ni Allah tsare ni da baqin bakin ka!
  Ganin abin na son zama musu fad'a Rayyanat tace"ka bar shi kawai nagode ni zan tafi koma ina ne"
Yace"Kwantar da hnklin ki ba nn gidan zaki zauna ba gidan kakata zan tafi dake har ki qarasa jin sauqi tukun....cabd'i!lallai ma Nasir kai baka ji me tace bane "wai zata tafi koma ina ne" hakan fa na nuna ba tada asali amma shine har kake qoqarin kaita gidan kaka!
 Wai pretty me yake damunki ne ya zaki kama fad'ar magana akan abinda baki da tabbacin sa! Murgud'a mai baki tayi tace"wane tabbacin kuma zan nema bayan sanin kanka ne duk er asali bazata kama gantali kan hanya ba har ma tana fad'in koma ina ne zata tafi ai duk d'an asali ba zai ce haka ba sae dai yace zai koma gurin en uwansa!
   Guntun tsaki yayi snn ya kalli Rayyanat yace"baiwar Allah gaya min sunanki"
  Sae da ta share hawayen da keta faman sintiri a kan fuskarta snn tace"sunana Rayyanat..... Mtsw kaji wani kilinbibi d'an qauye ne yasan ya qawata suna haka ai sae dai Rayyanatu hm!wai Rayyanat....yi mana shiru a nn pretty meye ruwanki da sunanta kuma!
yace"Rayyanat yi haquri sanar dani abinda ya kawo ki garin nn dmn na fahmici kamar ke ba er garin nn bace ko"kuka kawai Rayyanat ta fashe dashi ,Nasir yayi shiru yana nazari inda ya fahimci tabbas akwai abinda ya faru da Rayynat wanda bata son a tambaye ta inda ta fito tunda ko asibiti haka take ajiye mai kuka idan ya tambayeta nn ya tsara a ransa bazai qara mata tambayar ba har se taji sauqi tukun.
  Yace"daina kuka zo muje"
pretty tayi saurin riqo hannun shi tace"honey bafa inda zaka je da ita"wani  mugun kallo ya watsa mata ya kuma fizge hannun shi,cikin tsiwa tace"ai ko wlh sae dai ka za6a ni ko ita! don duk ka fita da ita nima sae nasa qafa na bar gidan nn na tafi gidan mu"yace"in kin iya kivar duniya gabad'aya ba ma gidan ba!
   Daga haka yasa qafa ya fita shida Rayyanat.


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BAR SHI BA```🔮








```Na Billy giro😊```





11/12/2016





🔮```5```🔮
 Suna shiga gidan kakar  ta tarbe su da murna kamar har
Rayyanat d'in ta sani dmn akwai ta da son mutane sosai.
    Bayan sun zauna ta kawo musu ruwa snn ita ma ta zauna suka qara gaisawa tace"daga ina haka muka samo baquwa nasir?, Nasir yace "wlh kaka pretty ce ta kad'e ta a bisa qaddara shine bayan ta kaita asibiti da kwana biyu aka sallamota to har yanzu dai bata fad'i ita wace ce ba dmn duk na tambayeta sae tayi  tamin kuka ,
kawai dai ta sanar dani sunanta Rayyanat ,naso ta zauna can gidana har ta qarasa jin sauqi amma kinsan halin pretty shine naga kawai na kawota gurinki dmn zata ma fi jin dad'in zama a nn.
    Kakar da ta bude baki tun fara mgnr sa tace "ikon Allah, wani irin tuki take har xata buge yar mutane snn kuma ta ki Bari ta xauna gidanta har ta warke, ni dae yaran Kabiru suna bn mmki da irin halinsu" Nasir dae yyi shiru bae ce komae ba, ganin sae fada kaka ke tayi kmr xata ari baki yasa yace "ynxu dae kaka kiyi hkuri hka, sae ta xauna gun ki har Allah ya sa a samo yan uwanta" kaka tace "yo in bata xauna nn ba ina xata xauna da" Nasir yyi murmushi yace "gskya ne kaka" Rayyanat kam sae kallon tsohuwar take nn da nn taji ta kwanta mata taji kuma xata iya xama da ita.

   Kakar ta tashi ta shiga kitchen ta d'ebo abinci ta kawo mata tace "ki saki jinkinki fa ki d'auka nan tamkar gidan ku ne kinji, ita kuma xata xo ta sameni har gida, tukin ma daga ynxu sa xanyi Khabiru ya hanata tunda abun nata har da buge mutum, kwanaki ma hka ta buge dan mutane" Nasir dae bae ce komae ba,
  Rayyant ta sunkuyar da kanta tana mai share qwallah had'e da ajiye d'an ledar da ke hannunta.
Kakar tace "kawo ledar na shigar miki da ita idan kin kammala sae ki watsa ruwa ko kyaji d'an damar jikin ki, ki kwanta ki huta"
   Bayan takai ledar ta dawo tana mai duban Nasir tace"ina ce ka siya mata magungunan da zata ci gaba da sha? Nasir yace Eh akwai magunguna a cikin ledar ta idan ta gama cin abinci sae tasha kafin tayi wanka dmn lokacin shan magunan ma yayi.
  Yana gama fad'ar haka ya tashi yace"inna ni zan tafi  sae anjima idan na dawo " inna ta washe baki tace "To Allah yyi maka albarka" ya amsa da Ameen yana murmushi ya nufi kofa xae fita, juyowa yyi yace "am yau man bai shigo bane inna? Inna tace " waye kuma hka?" Nasir yyi dariya yace "Mai gidan ki mana" ta tabe baki tace "Tun da safe ya shigo da dan rashin mutun cin sa, amma na taka masa burki, to har ynxu dae bn gansa ba"  Nasir yyi dariya yace "to shknn" inna tace"ko da wani  abu ne?" Aa ba komae naga ko yaushe na xo yana nane da ke ne,"

Har gurin motar sa ta rakashi ta dube shi da kulawa tace"Nasir gaskiya yarinyar nn da akwai alamomi ban tausayi a tare da ita jifa tunda kuka shigo bata da aiki sae na share qwallah,ai ma inna kad'an kika gani baran idan aka tambayeta inda ta fito, shiyasa yanzu nafi son sae taji sauqi tukun ko zan sake tuntu6ar ta.
    To Allah yasa ta kirki ce kamar yanda nake ji a raina ni dae ta kwanta min wllh, Nasir yace Amin inna.
   Daga haka ya shiga motorsa ya wuce, inna kuwa ta koma daga ciki.

Nasir kuwa yana zuwa gida ya samu gidan a hargitse duk pretty ta farfashe abubuwa ta kuma tafiyarta gidan su kamar yanda tace.


6angaren pretty sae kuka take sosai a jikin wata mata da nake sa ran ummanta ce ita kuwa sae masifa take inda take fita ba nn take shiga ba na ganin har dare Nasir yaqi zuwa ya sasanta shida pretty.
    Wani  gaye ne ya shigo d'akin Alhmdlh ya had'u ta koina baya da makusa tamkar balarabe fari tas dashi,yana d'auke da d'an siririn saje kan fuskarsa .
   D'ayan hannunsa yana riqe da suit baqa kalar wandon da ke jikin sa,yayinda rgr  jikinsa ta kasance fara mai ratsin layi layi.
  D'ayan hannunsa kuma yana sanye a cikin aljhun wandonsa.
   tsaye kawai yayi yana kallon su ba shi da niyyar cewa komai .
  Mamar ce ta fara ganin shi ,ya gaishe ta ta amsa inda cikin nuna damuwa sosai tace"man kaji abinda Nasir yayi wa qanwar ka pretty.

Nan mamar ta zayyana mai abinda pretty ta fad'a mata.
   Bai ce da mamar komai ba ya kalli kanwar tasa fuskar sa ba yabo ba fallasa yace "garin ya akayi kika kad'e ta? Kmr xata yi kuka tace yaya ina lokacinda zamu tarbo su umma har ka tsaya wani  gidan mai ka bada sadaka? Yyi shiru yana kallonta, hkn yasa ta turo baki tace yaya ni fa ba laifi na bne yarinyar ce Jaka, ina ga daga kauye ta fito, wani mugun kallo ya shiga yi mata, ta dauke kai tana murguda baki, ya gyada kai yace "daga yau kar ki kuskura ki kara jan mota" ta xaro ido tana kallonsa tace "sbda me, ko mijina fa bae hanani va yaya" tsawa ya daka mata yace "nace kar ki kuma jan mota"
   Daga haka ya fita ba tare da ya tsaya jin me zata ce ba .


Tafiya yake a hnkli har ya isa 6anfarensa.
    D'akin sa wani  irin d'aki ne mai masifar kyau da tsari komai fari tas sae qawar da akayi da golden ga tsarin d'akin ba wani  tarkace kamar tsarin d'akin turawa.
   Frigde ya bud'e ya ciro gorar ruwa ya bud'e ya tsiyaya ruwan a glass cup yasha snn yaje ya cire kayan jikin sa ya sanya white bathrobe ya nufi bathroom.

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA```🔮





```Na Billy giro😊```



11/12/2016




🔮```6```🔮
Ya jima sosai kafin yake fitowa yana gama shiri yaji ana masa knocking yaje ya bud'e qofa idanunsà suka sauka kan qanwar sa pretty dake tsaye  riqe da trayn abinci  fuskar ta fam kamar zata fashe don fushi tace"amma dai yaya zancen na daina tuqi da wasa kake min ko?mugun kallo ya watsa mata ya juyarwarsa ya koma daga ciki,ta shiga ta ajiye trayn sea qunquni take ita ba wanda ya isa ya hanata tuqin mota kan wata jaka can er qauye marar asali ma,
 Bai kulata ba har ta qaraci surutunta ta fita.


Washe gari sallah kawai tayi tace da ummarta"ni xan koma"
Umma ta saki baki tana kallonta snn tace"amma pretty ni  nasara ke wace irin mace ce wlh kowace mace na ganin ta samarwa kanta enci amma banda ke ,wane irin abu ne da baza ki bari sae nasir yazo da kansa ba ko zaki koma ,wlh kwata kwata kin 6ata kanki da sonda  kike yiwa nasir kmr ba nice na haife ki ba....nifa umma ba haka bane naji kina waya da Abba yana kan hanya shiyasa zan tafi kar yazo ya sameni ya min fad'a kuma kinsan jiya da dare nasir  yazo har yayi ta kiran wayata naqi na d'aga,to shi baqon gidan nn ne da bazai shigo ba sae ke zaki fita ki same shi ai inace yaje 6angaren uwar sa amma yaqi zowa nn,ai umma barshi don ni bama gidan sa nayi ba  wlh gidan inna zan tafi,to idan inna ta tambayeki lafiya fa? Ai inna ce zan kwashe da ita dai dai ba kamar Abba ba ,to ai sae ki tashi kiyi niyya dmn gab yake da isowa garin nn.
  Sauri sauri taje tayi wanka ta shirya  sae neman makullin motar ta take duk ta jigata kamar zata yi kuka ta kalli ummarta da ta shigo tace"umma ina makullin mota ta? Yayanki yazo ya kar6a....haba umma meyasa  kika bashi, kije ki roqe sa mana ai zai baki ,Allah umma kinsan da kamar wuya kidai roqa min shi ya bani, Aa ba ruwana can tsakanin ku ne kije ki gwada sa'ar ki idan ya baki to.
     Wani  abu yace miki da zai kar6i makullin motar ne?ba abinda yace min kawai dai ya kar6a ya tafi.
    Cikin 6acin rai ta fito tayi kici6is da yayanta da kuma mijinta Nasir a nn harabar gidan kallo d'aya tayiwa Nasir ta kauda kai ta kalli yayanta tare da marairiace fuska tana roqon ya bata makullin motar ta,kallon nasir yayi yace"sae kaja matar taka ku tafi"
  Ya sa qafa zai wuce tayi saurin shan gabanshi tace"pls yaya kayi haquri ka bani"
 tsawa ya daka mata yace"wai ina wasa dake ne da kike tunanin zan kar6e abu na baki!
   Le6ace baki tayi zuwa kuka tace"yaya ba fa laifi na bane na gaya ma"
  Wayar sa da tayi ringing ya d'aga ya bar gurin ,kuka ta fashe dashi nasir yazo yaja hannunta ta fizge hannun taje ta shiga mota shima ya zagaya ya shiga yaja motar tana ganin ya hau titin zuwa gidan su ta dalla mai harara tace"nifa ba gidan ka zan tafi ba don ka sani gidan inna zanje gara tun wuri ka sauya hanya don ko munje gida ba shiga zanyi ba wlh ,kuma sae naci uban wnn er iskar yarinyar da ka kaiwa inna wacce a dalilinta aka hana ni jan mota sae naga ta yanda ma zata zauna gidan inna d'in dole ta barshi tunda ba gidan kakarta bane ko wani  nata.
 Nasir yayi shiru yana kallon pretty shidai ko kad'an baya son  masifar nn tata gashi aikin kenan idan aka ta6o ta.
       Hannun ta ya riqo tare da kai mata sumba snn yace"da kika yi shiru sae kika min kyau  kamar ace ko yaushe haka kike ba ruwanki da fad'a"
   Hm ba wani  dad'in baki da zaka min nifa sae ka kaini gidan inna ,kallon ta yayi yana tunanin wayon da zai mata dmn yasan duk taje gidan inna ba qaramar rigima za'ayi ba,yace"gidan inna kwantar da hankalinki zan kaiki amma  sae kin raka ni gida nayi wanka tukun,ta6e baki tayi tana kallonshi snn tace"wankan me zakayi da baza ka kaini gidan inna ba har sae na raka ka,banyi wanka ba da safen nn ina gama sallar asuba naje gida dmn nazo dake, kuma yunwa nake ji sosai kinsan kin tafi kin bar ni ba abinci kuma yau da safe ma haka,shine nake son ki had'a min breakfast kafin na fito wanka kinji,
 ya fad'i haka ne cikin marairaicewa had'e da tsare ta da ido dmn yasan da ya mata haka bata iya masa gardama,
  ta kauda fuskarta gefe kamar baza ta amince ba sae kuma tace "naji"

  Karfe takwas da minti goma na dare Rayyanat na kitchen tana yi ma inna goge goge bayan ta gama wanke kwanukan da suka ci abincin ta ji an bude katon gate din gidan alamar mota xae shigo knn, duk lkcn da taji karan bude gate din sae gabanta ya fadi don ba sabawa tayi ba, bayan kusan minti bakwae inna ta shigo kitchen din ta gwalo ido tace "lahh bar maki aikin Hurera tayi" Rayyanat tace "A'a ni na karba inna" inna ta washe baki tace "ayyo!sannu da aiki jikata, ynxu duk ke kika gyara kitchen din nn hka" Rayyanat tayi murmushi ta sunkuyar da kanta bata dae ce komae ba, inna tace "to miko min wancan kulan abincin in kai ma mai gidana ya xo" Rayyanat ta dauko ta mika mata da ladabi inna ta fita tana cewa "yau ko dan kankanan da lemo bae siyo min ba ya kwaso kafafuwa ya xo xae cinye min abinci uwa shi ke siyo min"  bayan minti goma da fitan inna Rayyanat ta gama abinda take a kitchen din baka taba cewa daga kauye take komae nata tsaf tsaf take yi, da kyar ta iya fitowa daga kitchen din a sanyaye tuno babanta da ta yi, hkn yasa kwalla ya cika idonta, tayi saurin sharewa bata tarda kowa falon ba sae hurera yar dattijuwar matar da ke goge tiles din falon ta kalleta tana murmushi tace "sannu Rayyanah, ki tafi can daya falon inna na can, amma ga furar ta nn da na dama mata ki dauka ki tafi mata da shi, Rayyanat ta gyada mata kai kawae ta dauki furan da ke rufe kan centre table ta nufi falon da Baaba Hurera ke nuna mata, inna na xaune kan tabarma ta tankwashe kafa ta kapa ma tv ido tana kallo uwa tasan abinda ake yi, shi kam yana xaune kan three seater rike da remote waya na kare kunnansa alamar waya yake, kallonsa kawae Rayyanat take a sace kuma a tsorace sae dae har lkcn bae juyo ba, inna ta juya da sauri ganinta a tsaye tace " A'a karaso mana Rayyanah" Sae a snn ya juya yana kallon da warce kakar tasa ke mgna, Rayyanat ta sake kwanon furar hannunta ba tare da ta shirya ba, inna ta mike da sauri tana salati, ya katse kiran da yake shi ma ya mike yana yatsine fuska yace "ina kika samo mai aikin nn kuma Inna, idan xa ku dauki masu aiki ku dinga bincike da kyau don Allah ku dena dauko yara irin hka masu kananan kwakwalwa, bnda hka meye xata shigo falon mutane ta sake masu kwanon fura a kasa kmr wata me tabin hnkli" juyawa Rayyanat tayi da gudu ta fice daga falon a rude.

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮






```Na Billy giro😊```



16/12/2016



🔮```7```🔮
  Oh Allah yoni hajara!kai muhammadu ai wnn yarinyar iyakar hnkli da natsuwa tsautsayi ne kawai da in yazo ba mai tare shi.
     Inna ina hnkli a nn da shigowarta ta 6arar da fura kmr wacce bata saba ganin mutane ba,kudai 'ya'yan kabiru haka kuke abu kad'an ya isheku masifa,
inna yau maigidan naki kike gaya ma haka, yo ai ko waye kai tunda ka ta6a er albarkar nn dole na maka magana yarinya tsakanin jiya iyau lafiya muke zaune sae gashi kazo zama d'aya ka rikita ta har ta tafi da kuka,nidai inna da wnn mitar kira hurera tazo ta goge gurin nn ,kuma dan Allah kidaina kwaso iren iren yaran nn sam ba abin yarda bane da har kike saurin bama yarda zama d'aya,wai er had'uwar jiya zuwa yau ce kike kora min bayani kamar kun shekara, masifa inna ta shiga yi dashi,Man ya bita da kallo yana murmushi har ta fita.

Taje ta samu Rayyanat a d'aki sae kuka take rusawa,
 tayi zaune tana rarrashinta har ta samu tayi shiru.
 Rayyanat ta tashi tana share hawaye tace"inna bari naje na kwashe furar"a'a ai nasa hurera ta kwashe, kika sata inna nifa na 6arar,kar ki damu indai hurera ce bata da wnn,bari na tashi naje nabar maigidana shi kad'ai ,tace"to inna"inna na fita Rayyanat ta kifa kai taci gaba da kukanta.


 Da dare Nasir yazo ya samu sun kammala cin abinci sunyi zaune suna kallo ya gaida inna snn ya samu guri ya zauna ,Rayyanat ta sadda kanta qasa tana miqa gaisuwa ya amsa gaisuwar snn yace"ya jiki ?tace"Alhmdlh yace"kina dai shan maganin ki akan lokaci ko? Gyd'a masa kai kawai tayi tana wasa da en yatsunta.
   Ya maida dubansa gun inna da ta miqe qafafu tana kallon Indian film kamar wacce kejin wani  abu dmn duk ta tattara natsuwarta a can.

Sae da  abin ya bashi dariya sae dai bai yarda yayi ba dmn yasan masifa zata aje mai in tasan dalili dryr dmn kallo d'an gidan ta ne ba mai shiga tsakanin su.
   Yace"inna hln mai gidan naki ya koya miki indiyan ci ne naga kin maida hankali sae sauraren su kike?yo ina fa na iya Rayyanah na saka ma shine nayi zaune nima ina kallon abin tausayi naga sae wulaqanci yarinyar kesha a gun mijinta,dariya yayi yace"to ke inna ya akayi kika san mijinta ne? Yo kai Nasir banda idanu ne ko ko banda fahimta,gashi har gado d'aya naga suna kwanciya ai wnn sae miji da mata,dariya kawai yayi ya ajiye zancen dmn ya kalli film d'in ba miji da mata bane budurwa ce da saurayi ya mata ciki shine yake wulaqanta ta.

 Hannu yakai ya shafi sumar kanshi yace"inna zan tafi "ah ah kaiko da wuri haka ,inna aski zanje sae dai gobe idan na sake shigowa ,to Allah kiyaye ,
sae da yace"Amin snn ya fita.


Ko minti ashirin bai yi da fita ba sae ga Man ya shigo gidan sae dai shi ba kallo ya samu suna yi ba tausa ya samu Rayyanat tana yima inna.
   Rayyanat na ganin shi sae duk ta nemi natsuwar ta ta rasa, haka ta dake ta gaida shi ta kuma yi saurin tashi tabar gurin.
 Bai ma amsa gaisuwar ba sae inna ya gaida  ya ajiye ledar da ya shigo da ita kusa da inna snn ya zauna,inna ta tashi zaune tana washe haqora tace"me kuma kazo min dashi yau? Sae da ya jingina bayansa kan 2 seater d'inda yake zaune snn yace"gasasshiyar hantar rago ce na siyo miki kan hanya"
  Kai Allah dai shi yi maka albarka kamar kasan nayi kewarta wlh,ai inna har fruit naso siya miki se na manta,,ayyo ai d'azun da rana Nasir ya shigo min dasu munsha har mun gode Allah har ga saura a fridge  ko na d'auko ma zaka sha?Aa inna, to abinci kam zaka ci dai ko? shima haka dmn a qoshe nake, yau tawaye kamin kenan ,Aa naci abinci ne a gidan wani  abokin mu da yayi sabon aure muka je, oh ni kakata talatu kai yanzu ka gwammace kayi ta zuwa gidan abokanai ba a zuwa naka ,
wai nikam yaushe zaka fara ra'ayin aure ne muhamnadu,hm inna ai aure lokaci
ne dashi kin sani in lokaci yayi zanyi har ma a wayi gari watarana kina zaune zagaye da en jikokin ki, nn inna ta washe baki tace"Allah nuna mana lokaci muna masu rai da lafiya"Amin inna.


Washe gari Rayyanat ta gama taya hurera duk ayukkan da take tazo tayi kwance  qasan tiles tana jiran fitowar inna daga gurin wanka nn bacci yayi awon gaba da ita.

Pretty ce ta shigo gidan tayi tsaye tana kallon Rayyanat dake bacci tace"yau zaki ci ubanki yarinya"
   Nan taje ta bud'e fridge har ta d'auko gorar ruwan sanyi sae kuma ta girgiza kai ta mayar ta nufi kici tana murmushin mugunta ta d'auko flask d'in ruwan zafi tazo kai tsaye ta bud'e tana kwara ma Rayyanat su a jiki ,
ihu Rayyanat ta saki ta tashi a firgice tana lalubar bayanta inda taji saukar ruwan zafi.
   Mari pretty takai mata tace"er iska ai yau sae kin bar gidan nn wlh tunda bana ubanki bane!
Taja Rayyanat kamar wata kayan banza ta ingizata waje da qarfi sae kawai Rayyanat taji ta fad'a jikin mutum hkn yasa taji saukar wani  irin gigitaccen marinda ya soma fitar da ita hayyacinta.

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮





```Na Billy giro😊```



17/12/2016



🔮```8```🔮
La'ilaha ilallahu Muhammadu rasulillahi sallallahu Alaihi wa sallam!
   Cewar inna wacce ta fito daga gurin wanka tace"Muhammad me rayyanah ta muku ne da zaku mata taron dangi tun ina bayi naji ihunta Fatima na faman sirfa mata masifa yanzu gashi na samu ka tafka mata uban mari haka!inna ta qarasa magana cikin muryar kuka irin na tsafi d'in nan.
  Nan take man damuwar sa ta bayyana ya shiga bawa inna haquri bata kula shi ba sae kuka take taja Rayyanat suka koma cikin d'aki.
   Pretty ta kalli man dake qoqarin bin su inna tace"to wai meye abun damuwa kabar su mana tunda kasan halin inna dama saurin kuka ne da ita in ba don shi ba meye abin kuka wa wannan er qauyen,harara ya dalla mata yace ai duk ta dalilin kine banga uban me ya kawo ki gidan nn ba....kamar ya yaya...zan mare ki wlh idan baki 6ace min da gani ba!
  Turo baki tayi tana faman gunguni har ta fita gidan.
 Man kuwa shiga d'akin yayi amma a iya falo ya tsaya inna ta fito tana shar6ar hawaye zata d'auki wayarta dake kan TV stand yace"inna yi haquri Allah sam na d'auka rashin hnklinta ne yasa ta fad'o min a jiki ban san cewa pretty ce ta ingixo ta ba,amma Muhammadu ai ka saurara mata ko! yanzu gashi bayan fasa mata baki da kayi duk bayanta ya kwaye... Kamar ya inna nifa marinta kawai nayi... Yo kai ba kasan ruwan zafi pretty ta watsa mata a baya ba,shiga ka duba ta kaga ai nasan dole sae an yanke wnn ftr ,ta qarasa maganar cikin kuka snn tace"ka shiga mana ka duba min yarinyar mutane kazo kayi tsaye se kallona kake!
    Ba musu ya shiga ya sami Rayyanat ruf da ciki se kuka take abin tausayi zip d'in rigar ta a bud'e fatar bayanta har yyi ja, kauda fuskar sa yayi tare da sauke ajiyar zuciya snn ya kalli inna dake tsaye kusa dashi tana matsar kwalla yace "inna ina ganin ta sosa bayanta ne a lokacin da aka watsa mata ruwan, kuma wnn da gani ma ba wani ruwa me xafi bne, Rayyanat da bata ji shigowarsa dakin ba sae maganar sa taji tayi saurin tashi xata rufe zip d'in rgrta, inna ta karaso da sauri
tace "A'a Rayyanah kar ki rufe ai shi likita ne zai duba miki bayanki in kuma baxae iya ba sae ya kira mana ubansa ya xo ya kai mu asibiti," Rayyanat ta girgiza kai ba tare da ta kallesu ba alamar bata so, inna tace "A'a ki yi haquri ya duba ki kinji jikata"
Man da takaici ya ishe shi yace "inna bari kawai zan turo a duba ta" yana kai wa nn ya fice daga dakin kmr xae tashi sama.

Sae da ya kira wani abokinsa likita snn ya bar gidan ya nufi gidan kanwarsa pretty.
   Yana isa gidan Nasir ya samu kan dining sama sama suka gaisa yace masa "ina pretty" kafin ya basa amsa sae ga prettyn ta sauko, bata damu da ganin fuskar yayanta ba annuri ba ta daure fuska ssae tace "gani yaya lafiya dai ko"
  Yyi mata wani mugun kallo yace "me wnn yarinyar ta miki da zaki xuba mata ruwan xafi a jiki," shiru pretty tayi tana kallon shi kamar bata san me ya faru ba har lkcn fuskarta a tamke, ya daka mata tsawa yace "ya kika min shiru kina kallona ina maki mgna?" Ta tabe baki tace
"To nifa yaya ban gane zancen da kake ba bare na iya ce maka wani  abu," nn ya fahimci ta fita ne bada ixinin nasir ba shine take wani nuna kamar bata san da zancen ba.
 mari ya kai mata don bata da nisa daga inda yake yace "yanzu kin fahimci zancen nawa!ko kuma sae na qara miki wani," da sauri taja baya tana kuka don ganin da gaske yake, tace "to shine zaka wani mareni wlh sae na gaya ma umma!
 daga haka ta tafi da gudu tana kuka ta haura sama.
  Duk da Man ya fahimci Nasir yana buqatar jin bayani bai tsaya yi masa ba ya tafiyar sa hakan yasa nasir ya tafi ya haura sama gun matarsa da shima ya fahimci gidan inna taje bai sani ba.

Da shigarsa ta taso ta rungume shi tana kuka tace "ka gani dai ko honey ban masa komai ba yazo ya mareni," mugun kallo yyi mata yace "bana son qarya pretty nasan halin Man ba zai zo haka kawai ya mareki ba ,ba makawa gidan inna kika je gun Rayyanat kika aiwatar da nufinki ko?" shiru tayi alamar can taje d'in, nn ya shiga yi mata fad'a sosai daga qarshe yace duk ta qara fita bada izinin sa ba sae ya sanar da Abbanta, fushi ta shiga yi dashi bai kula ta ba ya tafiyarsa yaci abinci ya fice daga gidan.


Gidan  inna ya nufa yaje yaga aikin da pretty tayiwa Rayyanat lokacin ma har likita ya xo ya dubata, bata wani kone ba sae dae fatar jikinta da yyi ja ssae.
   Sosai ya bata haquri daga ita har inna da abun yabi ya dama har tana cewa a kira mata kabiru, Nasir dae ya dinga bata haquri yace shi zai yi maganin abun amma fafau inna tace ita fa sae taje shima zai kaita gidan da kanshi.


Haka ko akayi dmn tare suka fita shida inna suka bar Rayyanat ita da hurera.

Wani  makeken gida suka nufa kyace gidan shugaban qasa ne kan tsari da kyawo irin nashi, kuma ba wani  gida bane face gidan su Nasir d'in da kuma su pretty wato qanwar man sbd gabad'ayan su family's ne en wa da qani ne,
Baban su Man shine babba snn mahaifin Nasir bayan shi kuma akwai wani Alhj sa'eed wato qanin mahaifin Nasir inda shi kuma yana da qanwa mai aure a garin kd dukkan su 'yayan inna ne shine maxan suka had'e kansu suna zama gida d'aya sae dai kowa da nasa 6angare.
   Suna shiga gidan
 inna ta nufi 6angaren su pretty sae ga wata yarinya tazo da murna ta tarbe ta tana fad'in "he inna nida nake batun zuwa gurinki shine kika zo, inna ta washe baki tace "tukuna saukar yaushe Ameera? Yau yau d'in nan aka bamu hutu inna ,to ina er uwar taki saliha? "Tana 6angaren su tare ma ne zamu tafi gurin ki nasan yanzu haka ta shirya tana can tana jirana wlh, inna tace "ayyo to ai yanzu komawa zanyi sae mu tafi tare je kira min Abbanku kabiru yazo ina da magana dashi, tace "to inna zauna na kira miki shi"inna ta zauna ita kuma ta haura sama.

Nasir kuwa wani  6angaren ya nufa da alama shine na iyayensa dmn matar da ya samu zaune a falo sak suke kama dashi, cike da ladabi yaje ya durqusa ya gaisheta yana qoqarin tashi yaji an rungume shi ana fad'in "oyoyo yaya" cike da murmushi yake kallon wacce ta rungume shi yace "A'a saliha shin yau ne hutun ku ko to wa ya d'auko ku?
turo baki tayi snn tace "Abba ne  yaje da kanshi tunda kai kaqi zuwa "oh no saliha yi haquri sam na manta da yau ne hutunku amma umma ya akayi ba a sanar dani ba sae Abba ne yaje da kanshi? Mamar tace "Abban ne yace akwai aikinda yasa ka shine ya tafi dakanshi ya d'auko su, Nasir yace "eh gaskiya ya bani aiki tun jiya ban samu na qarasa ba amma inshaAllah yanzu zanje office na kammala kafin ya tambaye ni, nn ya kalli saliha yace "ina zuwa haka naga kinci kwalliya? Tace "Gidan inna zamuje nida Ameera," eyyah ai tare muka zo nida inna tana ma 6angaren su Ameera, Saliha ta 6ata fuska tace "ita ko dai inna...ai ba jimawa zatayi ba dn inaga sae na maida ita gida ne ko zan tafi office ,yauwa bara naje na ganta, cewar saliha wacce ta tashi cikin murna ta fita.
  Nasir ya kalli mahaifiyar sa da kulawa yace"umma ina yarinyar da na gaya miki cewa nakaita gidan inna? Hajiyar tace "eh na ji" "wlh pretty yau taje ta mata lahani a baya ta xuba mata ruwan zafi, inda Allah ya taimaka ma ba wani xafi ga ruwan ba" Hajiya ta gwalo ido tace "ni kuwa yaushe pretty zata yi hankali ne tukuna me ma ta mata da tayi mata wnn d'anyen aikin? Nasir yace "Kawai don tana jin haushin an hanata tuqin mota a dalilinta kuma kinsan halin pretty ta tsani talaka ba kad'an ba, cikin damuwa mamar tace "to kai nasir baza ka sallami yarinyar mutane bane ka huta, shawarar da nazo yi dake kenan umma don gsky bana son wani  abu ya sake faruwa da ita duk da nayi ma pretty kashedi amma hankalina zai fi kwanciya idan ta koma ga en uwanta sae dai inna ce matsala don yanda Rayyanat ta kwanta mata a rai ba lalle bane ta yarda da hakan zata iya cewa a kaita gun en uwan Rayyanat d'in in yaso ta nemi alfarmar su bar mata ita ta riqa yi mata en wasu aikace aikace in yaso duk wata ta riqa biyanta kinga kuwa duk dai ba'a rabu ba dmn gsky nafi son Rayyanat ta komawarta  gun en uwanta.
  umma ta nisa tace"to ya kake ganin za'ayi haka? Ya dan yi shiru snn yace "Eh to ina ganin kawai zan maida Rayyanat ba tare da sanin inna ba sae bayan na dawo na snr da ita kinga dole zata haqura.

 Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮





```Na Billy giro😊```



19/12/2016



🔮```9```🔮
To shikenan Nasir amma ina son kafin Ku tafi kazo min da yarinyar na samu abinda na bata don yarinyar ta bani tausayi wlh har dai in na tuna ko wane hali en uwanta suke ciki na rashinta oho Allah kad'ai ya sani.
   Wlh umma nima tunanina kenan kullum gashi taqi fad'a bare naji ko akwai lambar wayar su  a kira a snr dasu halin da take ciki amma yanzu Alhmdlh tunda taji sauqi zan lalla6ata ta gaya min sae na maida ta.
 Nasir Yayi mgnr ne yayinda ya tashi yace "to umma ni zan tafi "
  Umma tace "To ka gaida innar" yace "to" snn ya fita.

 Nasir na fita ya nufi 6angaren su pretty ya d'auki inna dasu saliha suka wuce.

Hajiyarsu pretty na fitowa daga bathroom sae ga mai gidanta ya shigo ransa a 6ace ta kalle sa da kulawa tace "lafiya Alhj me yake faruwa ne?" da taikaci ya kalle ta snn yace" ni nasara wace irin tarbiya ce kika bawa 'ya'yanki? kaf dangin nn ba wanda yakai  su rashin mutunci idan suka tashi, musamman ma Fatima" nn cikin fad'an duk ya kwashe abinda inna tazo ta gaya mai har da yaron da pretty ta kad'e kwanaki don duk shi bai sani ba.
  A fusace ya d'ora da cewa "kiramin ita yanzun nn tazo ina son ganinta, kwata kwata  daga yau ma ta daina jan mota na hanata"
  Umma ta dan tabe baki tace "ni dae kayi haquri Alhj, ai ba laifinta bane tsautsayi ne da kuma qaddara...." Rae bace Alhj yace "idan wnn tsautsayi ne me yakaita gidan inna har taje ta watsa ma er mutane ruwan zafi a jiki ko shima tsauyayin ne! Ku fa kiyaye ni ke da 'ya yan ki" ganin ynda ransa ya bace yasa tace "Ayi haquri Alhj bata kyauta ba dae, amma zancen tuqa mota tuni yayanta ma ya kar6e motar," Alhj yace "yayi dai dai don in kece baza Ki kar6e ba duk kinbi 'ya'ya kin lalata da baqin so sae kace kanki aka fara haifuwa.

 Nasir na sauke su inna gida ya wuce office bayan sun shiga gidan, saliha da Ameera suka shiga kallon Rayyanat da ke zaune ta lanqwashe qafafu tana shan fura a falon, kallo d'aya Ameera tayi mata ta kauda kai sbd ta gano ita ce yarinyar da inna taje tana faman masifa akai don a gabanta akayi komai ita da saliha.
  Saliha kuwa kallon Rayyanat take da d'an murmushi a fuskarta ta kalli inna tace "inna wnn itace Rayyanah?" Inna ta washe baki tace "eh ita ce er albarka babu ruwanta wlh" Saliha tace "eyyah sannu Rayyanat ya jiki?" D'an guntun murmushi tayi snn tace "Alhmdlh" a takaice.
   Ameera ta ta6e baki taja hannun saliha tace "ke ni tashi mu tafi gidan inna hajjo mu gaidata" (wata makociyar inna dake nn kusa bbu nisa)
  Inna ta washe baki tace "to in kunje ku kar6o min nono na samu na dama furar anjima" nn ta kwance  ha6ar zanen ta ta basu nera d'ari tace "ku siyo na duka," Ameera ce ta kar6i kud'in tana walwale su tana dariya ganin yanda suka tamure tace "kai inna wai har yanzu baki daina dunqule kud'i a ha6ar zani ba" bata jira cewar Inna ba ta ja Saliha suka fice daga falon, sae a snn Rayyanat ta gaida inna da ladabi, inna ta amsa da fara'a tace "sae ynxu kike shan hurar, ya bayan in ga ni?" Rayyanat ta dan xuge zip din rigar jikinta inna ta duka da sauri tana kallon bayan, kmr xata yi kuka tace "Allah ya Isar maki, da bayan nn ya tashi yau da anga xube xuben ruwan xafi a jiki don duk sae na tafasa ruwa na bi ta har gidan mijinta na kona ta ni ma" Hurera dake kitchen ta fito tana dariya tace "A'a ba ayi hka ba Inna, Allah dae ya tsare" inna tace "ae ynxu ma daga gidan ubansu nake, kuma yace anjima da daddare xae xo ya gane ma idonsa" Bude kofar falon aka yi, duk suka juya don ganin wnda xae shigo, inna na ganinsa ta tsuke fuska, ya karaso falon fuskarsa a tamke, Rayyanat tayi saurin gyara rigarta, a fusace yana kallon inna ya soma magana "don me xa ki je ki hada ni da Baffana kan wata bnxa can yar kauye Hajiya," inna ta tabe baki tace "sae dae kae ne bakauye ko uwar ka amma ba yar nn ba," xaro ido yyi yana kallonta, ita ma ta yo waje da ido tace "kwarae kuwa!" Rayyanat da tun shigowarsa falon ta sunkuyar da kanta hawaye ya shiga bin kuncinta, ya huzar da iska ya cije lebe lkci daya idonsa ya kada, ya juya fuuu ya fice daga falon, inna tace "Wawa kawae." Baaba hurera ta sauke ajiyar xuciya tace "Ayi hkuri dae inna" mikewa Rayyanat tayi har lkcn hawaye na bin kuncinta, Inna na ganin hka ta rude ta shiga tambayarta lfya, Rayyanat ta kasa bata amsa, hkn yasa inna ta fashe da kuka tace "yo baki ji nace shine dan kauyen ko uwarsa ba, ni dae na shiga uku da 'ya yan kabiru" lkci daya Rayyanat ta hadiye kukan da take tace "kiyi hkuri inna, ni ba shi yasa nake kuka ba, naga ina ta hada ki da jikokin ki ne" cikin kuka ta karashe mgnr, inna ta hade rae tace "suke dae hadani da ke, kuma Allah ya fi su" Baaba hurera tayi murmushi, Rayyanat ta duka ta dauki sauran furan da take sha ta nufi kitchen.
  Da rana nasir ya shigo gidansa, ya nufi dakin pretty ganin bbu kowa falon ga ko ina kaca kaca,  xaune ya sameta sae fushi take, yaje kusa da ita ya zauna ya shafi gefen fuskarta yace "nasha gaya miki ki daina fushi baya miki kyau," hararar sa tayi snn taja tsaki tace baka son nayi fushi shine zaka kaini qara gun daddy," Nasir ya xaro ido yace "au kin dauka nine, to inna ce taje da kanta ta gaya mai aikin da kikayi don haka ko yanzu kika sake gigin aikata wani  abu akan Rayyanat zata je ta snr dashi ne," cike da bacin rae ta tashi tana masa mugun kallo tace"ni yanzu banda lokacin wnn er qauyen bare na qara kulata" ta ja dogon tsaki daga haka ta wuce fuuu! ta barshi nn zaune" girgiza kansa kawai yayi ya tashi yaje ya bud'e fridge ya tsiyaya ruwa a cup yasha.

Washe gari ya gama shirin sa tsaf yaje d'akin pretty wacce yanzu ne tashinta zata shiga Bathroom dmn yin wanka.
  Bai qarasa inda take ba a iya gun dressing mirror ya tsaya ya ajiye mata kud'i yace "zanyi tafiya ne ban kuma san yau ko gobe zan dawo ba" ta hade rae tace "ina zaka tafi?" Ya daga kafada yace "Kina da sako ne?" daga haka yyi ficewarsa, ta6e baki tayi gami da jan tsaki tace "aikin banxa, kadda Allah yasa ka dawo ma"

Nasir bai zarce ko ina ba sae gidan inna cike da niyyar ya d'auki Rayyanat ya maida ta gun en uwanta. Bbu kowa falon Inna, hkn yasa ya nemi gu ya xauna yana tunanin ynda xae fita da Rayyanat ba tare da sanin Inna ba, Baaba hurera ce ta shigo falon daga kitchen, da mamaki tace "A'a Nasiru yaushe kuma ka shigo" yyi murmushi ya gaisheta ta amsa da fara'a tana tambayarsa ya kwanan pretty, ya amsa da Alhmdllh snn yace "Baaba Rayyanat xa ki kira min amma fa kar ki bari inna tasan da ina gidan nn" tace "to bari in kirata" ba a dau lkci ba ta dawo falon Rayyanat na biye da ita a baya, hijab ne har kasa jikinta yasan inna ce ta sa aka dinko mata, ya kafa mata ido har ta karaso ta xauna kasa kanta a sunkuye ta gaishesa, ya amsa yana murmushi ya tambayeta ta tashi lfya, kai kawae ta gyada masa, bae kuma cewa komae ba har na kusan minti biyar hkn yasa ta dago kai tana kallonsa da manyan idanuwanta, murmushi ya sakar mata ta dukar da kanta da sauri, ya kira sunanta a nutse ta amsa ba tare da ta kallesa ba, yace "nasan yan uwanki na cikin tashin hnkli Rayyanat, kiyi hkuri ki gaya min ina ne garin ku" Rayyanat tayi kkrin ganin hawaye bae sakko idonta ba a karo na farko ta gaya masa sunan garin a hnkli, ya gyada kai da gamsuwa yace "to ina xa ki pretty ta kade ki da mota?" Ta girgixa masa kae da kyar tace "garinmu xan ko ma" yyi shiru snn yace "to da me ya shigo da ke kano? Shiru tayi taki cewa komae hkn yasa yace"kin shirya komawa garin naku gun yan uwanki ynxu?" Gyada masa kai tayi kawae, yyi shiru na wani lkci snn yace "to tashi ki dauko ledan kayan ki, amma kar ki Bari Inna ta ganki" tace "to" snn ta nufi dakin da Inna ta bata tana murmushi a ranta tace "don xan tafi ba yana nufin na bar shi bane, har abada baxan bar shi ba, nemo sa baxae min wahala ba tun da na ga gari."






Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZANBAR SHI BA!```🔮





```Na Billy giro😊```



22/12/2016



🔮```10```🔮

 A sanyaye Rayyanat ta dawo falon rike da ledan kayanta ta samu har nasir ya fita xuwa gun motarsa, ita kad'ai yake jira taje ta bud'e gambun motar a hnkli xata shiga ta tsaya cak jin murya inna a bayanta tana fad'in "Rayyanah me zan gani hka ina kuma zakije har da leda a hannunki?"
  Sake gambun motar tayi ta juya tare da sadda kanta qasa ta ki barin su had'a ido da inna, ba shiri Nasir ya fito daga cikin mota ya tsaya yana d'an kame kame sbd yanda inna ta tsare shi da ido baki bude.
 Kmr xata yi kuka tace " kaddai mayadda rayyanah zaka yi baka ko snr dani ba Nasiru"
 Ya dan sosa keya yace  "Aa inna, dama wae da.." sae kuma yayi shiru. inna ta fashe da kuka tace "dama me nasiru! mayadda ita zakayi d'in knn, na rasa dalilin da yasa aka rainani hka, ynxu da bn fito ba sae dae in nemi yar nn in rasa" ta fashe da wani matsanancin kuka har da dukawa, Nasir yyi murmushi yace "kiyi hkuri Inna, kuskure ne" inna ta dago ta tsuke fuska tana kallonsa tace "rufe min baki munafuki kawae" dariya yyi yana shafa kansa yace "na yarda, amma inna baki tunanin halin da yan uwanta da iyayenta ke ciki ynxu? Ynxu misali lkci daya a nemi pretty a rasa wani hali kike tunanin xa mu shiga gaba daya" lkci daya inba ta marairaice tace "ni fa ban ce kadda a mayar da ita gun iyayenta ba, kawae rashin sanar dani da ba ayi bne ya bata min rae" Nasir yace "to ayi haquri inna,"  ta galla masa harara tace "yo da ban hkura ba da ban tara maka mutan anguwar nn ynxu ba," dariya yyi yana kallonta, tace "ynxu dae dani ya kamata muje gun en uwan nata su ganni nima na gansu na samu ko zasu bar min Rayyanah in rike, ni dae yarinyar ta kwanta min in sonta" ta karashe mgnr cikin kuka, tana matsar kwalla tace "ka ga idan Allah ya kawo mata miji na gari sae tayi auranta,"

  Ba yanda nasir ya iya yace "to shiknn inna jeki d'auko mayafinki mu tafi"
 Inna ta washe baki ta  ja hannun Rayyanah  tace "zo ki rakani er albarka bazan barki a nn ba don tunda yayi niyya zan iya dawowa na samu ya tafi dake ne kawae,
 ko meye dalilin hkn da yyi ne oho," nn dai inna ta jata suka tafi ciki don dauko mayafinta.
  Har yaja mota inna bata bar mitan da take ba, hkn yasa nasir sam ya manta da zancen kaiwa umman shi Rayyanat kamar yanda ta buqata.
   Tafiya sukayi ba mai wani  nisa sosai ba dmn da kano zuwa qauyensu awa biyu ne sae dai tun lokacin da suka kama hanya Rayyanat keta zubda qwalla a boye har suka isa.
  A bakin shiga garin tace da Nasir ya tsaya a nn, ya juya ya kalleta yace "garin naku ba'a shiga da mota ne?" Rayyanat ta daure tace "Ana shiga da ita amma ku sauke ni kawai nagode, zan iya qarasawa da kaina," inna ta yo waje da ido tace "yo Rayyanah ai ni en uwan naki nake son gani ko zan samu sumin alfarmar bar min ke"
  Shiru Rayyanat tayi hawaye suka shiga silalowa a hnkli kan kumatunta ta, inna ta saki baki tana kallonta, can tace "Rayyanah ko ba kya son komawa gu nane?" da sauri ta girgixa kanta muryarta na rawa tace "inna ni bani da kowa duk sun rasu"
   Inna ta rafka salati da karfi ta fashe da kuka tana cewa "wayyo ni Hajara, wayyo ni" Nasir dae yyi shiru yana kallon Rayyanat amma ya kasa yrda da abinda tace, inna ta ci kukanta ta koshi Rayyanat na taya ta kmr a lkcn aka yi mutuwar, daga karshe tana fyace majina cikin kuka tace "Allah ya rahama masu, wayyo ni rayuwa" Da kyar Nasir ya iya bude baki yace "Allah ya ji Kansu" ba don ya yrda ba gani yake kmr karya tayi masu.
   Cikin muryar kuka Inna yace "to nasiru muje muga mai garin nasu dmn haqqi ne akansa yasan Rayyanat zata zauna gun mu ko?" Nasir ya gyada mata kai kawae ya tada motar ya shiga tafiya a hnkli Rayyanah na nuna mai hanya har suka isa qofar mai gari.
  Cikin girmawa aka tarbe su mai garin yyi mamakin ganin Rayyanah ya shiga tambayarta daga ina take, nn Nasir ya dan ji dama dama gnin mai garin ya santa, bayan an gama gaggaisawa Nasir ya zayyano abinda ke tafe dasu yana kallon Rayyanah, mai gari bai musa musu ba ya amince da abinda suka buqata ya Dora da cewa suyi kkrin ganin sun riketa amana don marainiya ce sun samu lbrin rasuwan mahaifinta, Inna tace "ka ji ka da wata mgna, kasan wacece ni kuwa," mikewa tayi tana washe baki tana kallon Rayyanat tace "tashi mu je jikata, Allah xae taya ni riko"

Bayan sun koma gida da kwana biyu inna ta fito cikin shirinta Rayyanat ma dake shirye cikin wani atamfa da aka dinko mata da hijab jiya tace "to Rayyanah jeki snr da hurera mu zamu fita."
  Rayyanat ta nufi dakin hurera, dae dae nn Man ya shigo falon yana waya murmushi dauke a lebbansa, inna ta washe haqora tace "Allahu Akbar, sannu da xuwa d'an albarka dama kmr kasan neman wanda zai kaimu anguwar nake, sae gashi Allah ya jefo min kai"
  Ya katse wayar da yake yana kallonta yace "kai Inna, ina xa ki cikin ranan nn" inna tace "yo ni rana da yana gasa mutum da bae gashe ni ba, kasan irin wahalar da na sha gidan mijina kuwa" ya tabe baki ya juya ya fita yace ina jiran ki a waje, tace "to to ynxu xa mu fito" tare inna suka fito da Rayyanah, yana jingine jikin motar yana jiranta don duk a tunaninsa ita da baaba hurera xa su fita, suna karaso gun motarsa ya zaro ido yana kallon innar yace "wae ke da wa xa ku fita?" Inna tace "yo Rayyanah mana" ya kuma xaro ido kmr wanda yaji abin tsoro cikin shan toka yace "nifa gasky baza ta shigar min mota ba, mgnr gskya knn, idan dai ke kad'ai ce to muje," inna ta tsuke fuska tana huci tace "yo naga ja'irin yaro, kai baka san tafiyar tata bace ma gaba daya, xuwa fa zanyi da it cikin dangi tasan kowa, kowa ya santa."

Girgixa kai yyi yana masu wani irin kallo yace "to ba da motata ba, ki kira Nasir da yyi maki hanyar ta ya kai ku" inna ta fashe da kuka tana girgixa kai tace "Ni ban san meyasa bn dace da jikoki ba a rayuwa duk sun rainani uwa ba ni na haifi ubansu ba" Muhammad ya girgixa kai yana kallon innar yace "bari to in kira wani ya kai ku inna kin ga fa sauri nake" inna ta hade rae tace "A'a sae dae ka kira ubanka Kabiru ya kai mu, idan ba shi ba kam al-quran bbu motar shegen da xan shiga" Muhd ya fuxa isa ya juya yana kallon Rayyanah yace "ke shiga muje" inna tayi murmushi tace "shiga Rayyanah" kasa shiga motar Rayyanah tayi fuskarta a daure, har sae da inna tace "ki shiga nace mana" snn ta shiga inna ma ta shiga motar tana goge dan kwallar idonta tana murmushi " sae da suka hau babban titi snn Muhd ya dake yace "ina muka nufa?" Inna tace "A'a wae da gidansu Murja xaka fara kai mu, daga can sae gidansu Fatee, daga gidansu fatee sae ka kai mu gidan bari'a,  daga can sae mu garxaya gidan kawata hjya Laure, in mun fito sae mu shiga gidansu Audi, to ba wani ddewa xa muyi a can ba, muna fitowa sae ka garxayo da mu gidansu Alhaji bukar, to daga gidan Alhaji bukar sae ka kai ni gidan tanko ina son gninsa, idan mun fito sae ka kai mu gidanku, daga gidanku kuma sae ka dawo da mu gida kawae don ni ban fiye son yawan gidajen mutane ba" murmushi kawae yyi yana shafa sajen fuskarsa bae ce mata komae ba.

Billy Giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZANBAR SHI BA!```🔮





```Na Billy giro😊```



26/12/2016



🔮```11```🔮
Sae da ya kaisu duk gidajen da inna ta lissafa snn ya kaisu gidan su wato family house.
   6angaren hajiyar pretty suka fara zuwa snn 6angaren su hajiyar nasir wacce ta tarbe su cikin fara'a da murna ba kamar hajiyar pretty da ta kama kallon Rayyanat a yatsine ba.
     Haka  d'ayan 6angaren da girmamawa suka tarbi inna yayinda suke kallon Rayyanat ba yabo ba fallasa .


 Nan inna tabar Rayyanat amma a 6angaren su hajiyar Nasir a cewar ta musu yini.
 Saliha sai janta take a jiki sbd yarinyar tana da son mutane sosai ba kamar sauran yaran gidan ba hkn yasa Rayyanat ta d'an saki jikinta da saliha har ma tana jan Rayyanat da fira.
inda cikin firar take ta bata labarin rayuwar  su ta school , ita dai Rayyanat saurarenta kawai take ba um ba um um sae dai idan taji abin dariya tayi d'an guntun murmushinta,saliha tace "wai nikam Rayyanat kin barni ni kad'ai keta zuba kamar parrot ba kuwa zan yarda ba don kema sae kin bani naki labarin makaranta,d'an guntun murmushi Rayyanat tayi snn tace"aini banyi secondary school ba ma bare zancen boarding school,xaro ido saliha tayi tace "hm kedai ba kya son bani labari ne,a sanyaye Rayyanat tace"da gaske nake wlh"
Saliha ta kalleta tace"meyasa gashi da alama zaki kai s .s 2 ko 3 inda kinci gaba?Baffana ne baya iya d'aukar nauyin karatuna"
 tayi maganar cike da qwallah a idonta kan tuna baffanta da tayi"
  Saliha tayi shiru tana kallonta sae duk taji ba dad'i tace"to ynx idan kika sami dama kina so kici gaba da karatun?girgiza kanta tayi tare da share hawayenta snn tace"ai lokaci ya qure min"
 lokaci bai qure miki ba Rayyanat kina da lokaci har yanzu"
um um ynz ba wnn ne burina ba sae nn gaba kad'an tukun"er dariya saliha tayi tace"hm Rayyanat har wani  buri kike da shi yanzu da ya wuce karatu sae dai idan karatun ne ba kya so"kallonta kawai Rayyanat tayi yayinda idanunta suka sake cikowa da qwallah ta kauda kanta gefe ba tare da tace da ita komai ba.
  Qofa suka ga an turo saliha ta tashi taje ta kar6i trayn abinci da ke hannun ummnta ,hjy ta bata tare da kama kunnenta ta murd'e tace"kina nn kin cika ta da baqin surutun nn naki ko kiyi tunanin d'ebo muku  abinci ma bakiyi ba, dariya saliha keyi  mai had'e da jin ciwo tace"wash umma Allah inada niyyar tashi na d'ebo mana abinci sae gashi kin shigo mana dashi "ta sake mata kunnen tare da fad'in"oya yi ki zuba muku abincin kuci ina so zamu d'an fita ne zuwa anjima,to  umma,nn Hajiya ta fita saliha ta zuba musu abinci a plate d'aya suka fara ci sae dai basu wani  ci sosai ba Rayyanat tace ya isheta sbd dama kafin su fito taci abinci.

Sea bayan sllr la'asar suka fita wani  qatoton mall suka je Hajiya tace da Rayyanat ta d'auki duk abinda take so, Rayyanat bata iya d'aukar komai ba sae saliha ce  ta shiga d'aukar mata kayan sawa kmr su Arabian gown da turarukku designers da kuma kayan kwalliya bayan sun gama siye siyen su ne suka maida Rayyanat gida da kayanta niqi niqi wad'anda saliha ta kwasar mata,
 inna sae washe haqora take tana sama Hajiya albarka.

7 days later
Rayyanat ce a kitchen ta gama wanke kwanika tana goge kitchen bayan ta gama ta koma d'aki.
  Saliha ce ta shigo gidan ta sami Mohd  shida inna sae fira suke sae da ta gaishe su snn ta zauna har inna na tambayar ta ya mutanen gida tace duk suna lafiya tace"to ya na ganki yau ke kad'ai ba abokiyar yawonki Ameera? Tana gida wai yau bata jin fita tace"ayyo to ya hajiyarki tana lfy dai ko?lfiya qalau wlh ta ma ce a gaida ke,ina amsawa ai yau tama kirani a waya mun gaisa kmr kullum,eh inna Rayyanah fa? Shiga daga ciki yanzun nn ma ta shiga.
Rayyanat na zaune tana duba litattanfanta na islamiya sae ga saliha ta shigo da sallamarta ,da sakin fuska Rayyanat ta tarbe ta  ta nemi guri ta zauna tare da jawo littafan Rayyanat na Islamiya tace"ke yau fa Alhamis ko kin manta" Rayyanat tace"ai ba shirin zuwa makaranta nake yiba ina muraji'a ne sae gashi na sami kaina da mantuwa da wani  gun a cikin littafin ishmawee babun sallati janazatee gun da ake cewa....cab ai ke ban kai babin ba wlh kad'an dai ya rage,nn taja hannunta tare da fad'in "amma muje gun yaya Man ya tuna miki kafin ya fita "cikin rashin fahimta Rayyanat tace "waye kuma haka?oops baza ki san sunan ba sbd da Muhammadu inna ke kiran shi, Man kuma complete name d'inshi ne frnds d'insa suka had'e wato Muhammad Aminullah Nasir shine har mu qannansa ke kiransa dashi sbd koda muka taso mun samu ana kiransa da sunan.
  Ta6e baki tayi ba tare da tace komai ba Saliha tace "muje ya tuna maki ko"um um nafi son na tuna da kaina sbd zanfi riqe abun da kyau"to amma dai zaki ajiye muraji'an nn har zuwa dare tukun sbd ina son muje ki rakani familyn mamana,a natse Rayyanat ta ware kyawawan idanuwanta tana kallon saliha snn tace"ni d'in nn? Eh man ai anguwar ba nisa da nn kuma wa ke kad'ai na biyo gidan nn wlh ,don hk ki tashi ki shirya mu tafi,nifa ban son shiga inda ban sani bane saliha ki tafi kawai abunki kinji,
,kinji Ki sae kace wacce za'a cinye dan Allah nidai tashi ki shirya mu tafi ai da sannu ake yin sabo ba wai zama zakiyi tayi kice ba kya shiga mutane ba.
  Turo qofar da akayi ne ya katse Rayyanat da abinda tayi niyyar fad'a,Saliha tace"yauwa inna dan Allah ina son Rayyanat xata rakani gidan  Baaba.
  Ba musu inna ta amince da su tafi.
  Duk da Rayyanat bata so ba amma haka ta haqura Saliha ta tasa ta gaba tana mata kwalliya yayinda tace ta rufe idonta har sae an gama kwalliyar ko zata bud'e,
byn an gama kwalliyar Rayyanat na bud'e idanuwanta ta wani  ware su kan tsananin kyawon da taga tayi har ma ta fara shakkun anya ita ce kuwa tace"saliha wnn kwalliyar na tafi ina dashi nikam rage min ita don wlh ni ko kwalliya ma banayi bare na iya fita da wnn kwalliyar haka,,,um um gsky ba abinda zan rage maki ,
kawai don baki saba kwalliya bane kika ga kmr tayi yawa amma dai dai take, da qyar Rayyanat ta iya yarda aka bar kwalliyar saliha ta bata Arabian gown ta saka ta jawo qatoton hijabinta zata zuba saliha ta dalla mata harara da wasa tace"meye haka zan gani ki wani zuba hijabi har qasa sae kace zaki tafi islamiyya ?ban gane ba saliha to dame kike son na fita?saliha bata ce mata komai ba sae hijabin ta cire mata ta d'auko top d'in gown ta roller mata, duk da cewa Rayyanat ba wata fara bace amma shirin ya matuqar d'aukar ta sae dai faffau tace bata iya fita da shirin sae tasa hijab Saliha ta buga qasa da sama a cewar ta duba ita ma fa irin shirin ne da ita amma ina sam Rayyanat bata yarda ba, bbu ynda Saliha ta iya da ita hka ta kyaleta da hijab din suka sallami inna da ke kitchen suna wainar flower da baaba hurera, inna na ganinsu ta washe baki tace "Ma'sha Allahu" saliha tace "ku fa ajiye mana namu inna, don nasan kina iya kwashewa gaba daya ki ba ma yaya" saliha na kai wa nn ta ja hannun Rayyanat suka fice daga kitchen din, kwance suka tar da shi a falo idonsa lumshe kmr mai bacci, lkci daya ya bude ido yana kallonsu, Saliha ta dan hade rae tace "sae mun dawo yaya" Rayyanat kam kauda kai tayi ita ma fuskarta a daure, mikewa yyi xaune da sauri yace "ina xa ki?" Dauke kai tayi tace "gidan fa kaka xa mu, kuma Hajiya ta sani" kallon Rayyanat ya tsaya yi da mmki ganin ynda ta wani hade rae, can ya mike ya nufi kitchen sae ga shi ya fito inna na biye da shi a baya tana cewa "lfya me ya faru?" Sae da suka karaso cikin falon snn ya juya yana kallon innar da kyau yace "dama tambaya ce xan maki, wae wnn yarinyar me aiki ce ko ko a ina kika jajubo ta" ya fadi yana nuna Rayyanat, inna ta ja dogon tsaki ta balla masa harara tace "uwar ka ce ba me aiki ba, wnn tayi maka kama da mai aiki, hka kawae kasa ma yarinya ido a gida, uwar me ta tsare maka, to in kai maye ne sae dae ka ci kanka wllh" a fusace ya karasa gaban Rayyanah yana mata wani mugun kallo fuskarsa a daure ya dago fuskarta da kyau yana kallo, ta kuma hade rae ita ma tana kallonsa da manyan idanuwanta, a nutse ya fara mgna, "daga yau, I mean daga this vry moment kika kuma min wani irin kallo a gidan nn, ko kuma kika gan ni kika ki gaida ni sae na....." Kukan da inna ta fashe da yasa ya tura ta da karfi, ya juya yana kallon innar, kwashe wayoyinsa yyi da ke kan kujera ya juya ya fice daga falon kmr xae tashi sama, inna ta bi sa da ja'irin yaro kawai, ta karaso gun Rayyanat tana matsar kwalla tace "kiyi hkuri kin ji 'yar nn, tambada yake ji yau shi yasa yyi maki hka, amma ki kyaleni da shi, da ubansa ma xan hada sa ni ya ja masa kunne ya daina xuwa min gida don baya tsinanani da komae da ma, sae dae in dafa in basa ya ci ya bar min kwanukan a nn ya kara gaba" Rayyanah tayi murmushi kawae tace "bbu komae inna" saliha da ko kadan bata ji ddin abinda yayan nata yyi ma Rayyanah ba ta ja ta a sanyaye suka fice daga falon don xuwa inda xa su.
 Sae da suka fita daga gidan Saliha tace "kiyi hkuri Rayyanah hka yaya yake wani lkcn" Rayyanah tayi murmushi tace "A'a ni bn ji haushi ba wllh," saliha tace "yauwa, kuma don Allah ki dinga gaishesa in kun hadu" Murmushi kawae Rayyanat tayi bata ce komae ba, saliha tace "ke komae murmushi, ba sae ki ce min to ba" Rayyanat ta kuma yi mata murmushin tace "toh naji Saliha" saliha tayi dariya tace "yauwa ko ke fa."

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮





```Na Billy giro😊```



28/12/2016



*🔮```12```🔮*
Washe gari  kaf gidan Rayyanat ce ta gyare shi har wajen gidan wato gun faka motoci duk sae da ta share tsaf koina  ya haskaka.
   Snn taje kitchen don taya baaba hurera aikin abinci, baaba hurera tace "Aa Rayyanah yau kinyi aiki da yawa je kawai kiyi wanka kinsan yau juma'a qaramin lokaci ce," Rayyana tace "aa baaba bari kawai na tayaki wlh," "wlh jeki ai saura kad'an na qarasa tafi kiyi wanka kinji er albarka," cewar baaba hurera knn, murmushi kawai Rayyanat tayi ta juya ta fice daga kitchen.
wanka ta je tayi ta shirya cikin riga da skirt na atamfa da inna tayi mata, sukayi mata kyau kmr ba tashin qauye ba kan yanda sukayi d'as a jikinta.
 qur'ani ta d'auko ta shiga karatun suratul kahfi, a dakin da inna ta bata ita kadae duk da ba kwana take ciki ba don tsoro.


Tunda daga kan gate da mohd ya shigo gidan yake qare ma ko ina na gidan kallo ganin yanda gidan yayi haske yayi kyau, as in very neat ba wai don ba a share gurin ba a'a sae don ganin sharar yau ta daban ce da kullum.

Faka motar sa yayi ya fito cikin motar cike da tafiyar sa ta qasaita ya isa cikin gidan yana duba agogon wrist dinsa.
  Inna ya samu xaune a falo ta miqe qafafu tana casbi har yana jin sautin salati na fita a bakinta, murmushi yyi hade da mata sallama, kin amsawa tayi sae ma wani kallon masifa da ta watsa mai tace "idan kasan yau ma tambad'ar ce ta kawo ka ftr min daga gida!"
Muhd yayi murmushi ya karaso cikin falon tare da ajiye ledar hannunsa gefenta yana kallonta yace "ni abinci naxo ci" inna bata kula sa ba sae hannu da takai tana bud'e ledojin da ya ajiye mata 'ya'yan fruits ne da gasasshen naman rago sae gassashiyar qullin hantar rago gefe, lkci daya inna ta washe baki tace "Auu! sannu da xuwa mai gida, Allahu yyi maka albarka ya kuma nuna min aurenka" daga haka ta qwalawa Rayyanah kira.
  Cikin hanzari Rayyanat ta fito daga d'aki tana ganin muhd zaune ta rage saurin da take inna na washe da baki har lkcn tace "zo er albarka ki kai ma hurera 'ya'yan itacen nn ta yanyanka mana daga nn ki biyo ma maigidana da nasa abinci idan an kammala."
  Rayyanah tace "to" ta kar6i ledar fruit wacce sae a snn ta gaida muhd, dake bin ta da harara tun shigowarta, ba yabo ba fallasa ya amsa.

Rayyanah ce ta yanka 'ya'yan fruits din da kanta ta had'o komai har da abincin mohd da inna tace, ta kawo ta ajiye ta wuce inna sae sa mata albarka take, inna ta dubi muhd washe da baki har lkcn  tace "d'an albarka nn ina son muyi wata magana da kai a game da yarinyar nn Rayyanah ashe wae primary kawai tayi sae jiya nake ji a bakin saliha shine nace ka binciko min makaranta mai kyau mai tsada kabiru ya biya a sata, in yaso duk safe sae ka riqa zowa kana kai min ita, Nasir kuma yana dawo da ita idan an tashi"
  Wani irin murmushi yayi da jin zancen inna kamar sa6o dan har ma sae da yayi istigifari a cikin rnsa had'e da shafo sajen fuskarsa yana kallonta har lkcn murmushi dauke a lebbansa yace "to ynxu dae duk yawancin makarantu an fara jarabawan second term, kawae ki bari idan shekara ta zagayo hkn xae fi kyau" inna ta yi shiru tana kallonsa sae kuma tace "to muhammadu idan shekara ta zagayo dan Allah kar ka manta da zancen nn dan dai wlh ina son naga Rayyanah tayi karatu kmr kowa ga ta da kkri sosai in ji saliha"
 Yyi murmushi yace "to Allah kaimu" tace "amin" shi kuma ya jawo abinci ya fara ci.

2:30pm
Rayyanat ce zaune kan carpet ta gama sallah tana addu'o'i inna ta shigo d'akin kowane hannunta yana d'auke da plate d'ayan 'ya'yan itace ne da aka yanyanka, d'ayan plate din kuma naman rago ne da kuma hanta ta ajiye tana fad'in "Rayyanah keda nace kici abinci tun da'zu ashe baki ci ba sae yanzu da na fito naga komai inda na bar shi" Rayyanat tace "yanzu dama xan tashi idan na gama sallah" "to ai kin gama sllr tashi muje kici abinci a gaban ido na don na fhmci hlnki ba kya son cin abinci" ba yanda Rayyanat ta iya ta tashi tana linke sallaya had'e da d'an guntun murmushi a fuskarta don dai ita gsky tana jin dad'in yanda inna ke kula da ita.
  Falo suka je inna ta kunna musu kallo Rayyanah na cin abinci suna kallon su cike da nishad'i.

Washe gari ranr ta kasance ranr asabar Rayyanat tayi shirin ta tsaf na zuwa islamiya da hijabinta sky blue har qasa na islamiya ta saka safar ta klr hijabin ta d'auko niqab ta d'aura bata dai sake shi a fuskarta ta ba ta d'auko Jakarta ta islamiyya ta riqe a hannnu snn ta nufi d'akin inna ta mata sae ta dawo, inna tace "a dawo lafiya er albarka"
 Fuskar ta wasai ta fito d'akin ta saka takalmi ta rufe fuskarta da niqab snn ta fita, da kafa take xuwa makarantar don bbu wani nisa daga gidan can saman layi ne, yawanci duk gidajen masu da shi ne a layin don hka layin is vry cylnt, yau ma kmr kullum xaune ta gansa gaban kantamemen gate din gidan as usual, sae dae yau ba shi daya bne, shi da wani ne, bin ta yyi da kallo kmr ko da yaushe, ta wuce su da sauri tana harhardewa, ta rasa dalilin wnn kallon na mutumin nn da take gani kullum xata makaranta, ita dae fuskarta a rufe yake ko da yaushe, tsaki ta ja tana tunanin kila hanya kawae xata canxa don a rayuwarta ta tsani kallo.
Har aka tashi daga makaranta bata da wani walwala, ta hada litattafan da suka yi ranan ta xuba cikin jakarta snn ta sakale shi a hannu, ta dauki Qur'an dinta ta rungume a kirji ta sallami yan kawayenta da suka dan fara sabawa a ajin ta fito ta kama hanyar gida da sauri da sauri don Karfe shidda dama suke tashi, xaune ta sami mutumin daxu har lkcn sae dae wnn karan shi kadae ne, tsallakawa tayi ta d'ayan side din ta ci gaba da tafiyarta da sauri, sae da ta dan yi nisa snn ta dan juya don ganin ko yana kallonta,Xuciyarta ya kusa shigewa cikinta ganin biyo ta ma yake, ta kara sauri gabanta na faduwa ssae, gashi bbu alamar mutum a layin, ganin duk saurinta har ya kusa cim mata yasa ta kwasa a guje ko minti biyar ba ayi ba ta isa gida har lkcn gudu take har da kukanta, mai gadi na tambayarta me ya faru bata ko sauraresa ba ta nufi kofar shiga falo da gudu, a bakin kofa suka ci karo da Muhd dake tsaye yana jujjuya makulin motarsa alamar xae tafi, suna mgna da inna, hkn yasa Rayyanat ta fasa ihu, ya koma baya da sauri lkci daya ya turata da karfi ta fadi nn kasan falon, inna ta mike da sauri ta karaso bakin kofar tana salati tana tambayar me ya faru, Rayyanat da ke mayar da numfashi ta fashe da kuka ssae, inna duk ta rude ita ma ta saka kukan ta xube nn gabanta, baaba hurera ta fito da sauri tana tambayar lfya, sae ga mai gadi shima ya taho da sauri yana tambayar me ya faru, Muhd kam don takaici komawa gefe yyi ya tsaya, cikin kuka inna ke kallon mai gadi da Baaba hurera tace "nima ban san kukan da take ba" baaba hurera ta shiga tambayar Rayyanat me ya faru, da kyar ta tsaida kukanta muryarta na rawa tace "wani mutumi ne sae yyi ta kallona idan xa ni makaranta, shine yau ya biyo ni sae na fara gudu yana ta bi na kuma" ta karashe mgnr cikin matsanancin kuka, juyawa Muhd yyi ya fice daga falon mai gadi ya bi bayansa, lkci daya inna ta tsuke fuska ta miqe tana share hawayen fuskarta tana huci tace "dan gidan uban waye shi xae biyo min ke da gudu, hurera dauko min gyale na" hurera tace "A'a inna, ba ga su Muhammadu sun fita ba" inna tace "da'alla bani mayafina in je in masa rashin mutunci" hurera ta dauko mata gyalenta ta bata, ta fixge ta fice daga falon kmr xata tashi sama, a bakin gate suka hadu da Muhd da mai gadi, Muhd yace "ina xa ki kuma inna" ba tare da ta kallesa ba tace "nemo dan iskan xan je yi mana" yace "bbu kowa a waje na duba, ita bakauyiyar wace gari ce da xata d'aga ma mutane hankali hka, kila ma harkan gabansa kawae yake xata shigo ta daga ma mutanen gida hnkli, tsiyar yan kauyen nn knn"

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮





```Na Billy giro😊```



30/12/2016



🔮```13```🔮
Cikin gida suka koma tunda ba a ga wanda ake neman ba, inna dai sae masifa take tayi kmr wacce ta sami wanda ake nema a gabanta.
    Mohd kan takaici tun daga kan gate bai ma dawo ba jan motar sa kawai yayi yabar gidan.
Inna ta rarrashi Rayyanat ta samu har ta daina kukan da take taje d'akinta ta ajiye jakarta ta cire niqab da hijab da socks  ta nemi guri xata kwanta sbd har yanxu jikinta bai daina rawar tsoro ba.      Inna ce ta shigo d'akin riqe da kofin fura a hannunta,
 ba ita tabar d'akin ba har sae da Rayyanat ta shanye furar tas.


Har dare Rayyanat bata sake kmr kullum ba kallo suke amma sae tunanin gobe take idan zata je islamiya.
  Nasir ne ya shigo gidan da sallamar sa ,suna gama gaisawa inna ta bashi lbrn abinda ya faru da Rayyanat d'azun ,
ya kalli Rayyanah da kulawa yace"bai dai maki komai ba ko? Sae da ta girgiza kanta snn tace"bai min komai ba amma nasan ko gobe zan ganshi in na fita don kullum sae na ganshi idan zan tafi makaranta"
ta qarashe mgnr kmr wacce zata yi kuka.
 Nasir ya nisa yace har da safe kike ganin sa idan zaki tafi makaranta? Aa bana ganinsa da safe sae da yamma"
  To shikenan da yamma zanzo kiyi tafiyar ki kar ki nuna tsoron komai don so nake na gane dalilin bibiyarki da yake,kar kisa tsoro dmn ina nn a bayanki kinji,a sanyaye ta gyad'a masa kai .
Inna tace"ai kowane d'an iskan ne gobe ma kwashe ta nida shi"
  Nasir yace"ai ba girmanki bane inna ki barni dashi kawai"...yo shi girma ya sani ne da zai biyo er qaramar yarinya haka duk yabi ya tayar mata da hnkli gabad'aya yau ta rasa sukuni.
  Ai inna ina ganin irin en iskan samarin nn ne da basa da abinyi sae zaman banxa.
   Inna ta tsuke fuska tace"to Rayyanah kam baza tayi komai dashi ba don ya ma kama
gabansa tun wuri.
   Nasir yayi murmushi ya sauya wata firar suka ci gaba dayi,
 can inna ke tambayar sa wai ina er banzar nn Fatima ta shige da na daina jin d'uriyar ta, Nasir ya shafi kansa yana murmushi snn yace"inna ai pretty ta jima bata jin dad'i sbd laulayin da take fama dashi"
   Dad'i inna taji sosai har da su taka rawa ta kusa samun kama kunne tace"ai bari shi kuma d'an banzan nn yazo marar son aure ,yazo yayi auren nn ko shima zanga abinda ya haifa kafin nabar duniya.
  Duk cikin taka rawa inna ke maganar nn Rayyanat har da er dariyar ta don rawar inna ta bata dariya sosai.


Washe gari da yamma har Rayyanat taje ta dawo bata had'u da kowa ba,
 tare suka shigo ita da Nasir inna na ganin su ta shiga tambayar ko anga mutumin ?Nasir yace"ba muga kowa ba sae wasu masu zama gurin"
wani  dogon tsaki muhd dake kishingid'e yaja yace"wai inna me yasa kike  biyewa bagidajiyar yarinyar nn nikam,kawai mutane na harkar gaban su ta wani  ce ya biyota in miji take nema taje can qauyen su mana ta samo irinta ba tazo nn tana fakewa da wani  ya biyota ba,
 wane kidahumi ma zata samu a nn da har zai yi lokacin ta in ba wanda uwar sa ta masa baki ba.
   Sosai maganar mohd tayi wa Rayyanat baqiqirin a rai duk yanda taso 6oye hawayenta sae da suka gangaro kan kumatunta tayi saurin share hawayen ta shige daga ciki ,mohd dake kallonta cikin 6acin rai sae a snn ya kauda idonsa ya maida su gun inna da ta shiga sirfa mai masifa kan yafita harkar Rayyanah har tana fad'in "sae na had'a ka da ubanka kabiru idan baka fita harkarta ba wlh.
  Nasir ne ya shiga bata haquri shida baaba hurera dake aiki kitchen ta jiyo fad'an ta fito"
mohd kam barin gidan yayi sai haushin inna yake ji dake fifita Rayyanah akan shi har tana sako ubansa a ciki.


Yau kusan kwana biyu mohd bai zo gidan inna ba inna bata damu ba sai ma harkar gabanta take.

Rayyanah ce a bayan gida ta gama wankin kayanta dana inna tana shanya wacce sae ta sharce zannuwan kafin take shanyawa.

 inna tazo ta same ta tace"oh ni wai Rayyanah wanki kika xo kina mana keda ya kamata ace kinyi shirin islamiya !uhm inna ai na kammala yanzu zanje in shirya "to Rayyanah yi maza amma dan Allah ki daina wankin nn nasha gaya maki akwai mai min wanki har ma naki d'in duk ki daina wankewa idan sun taru ki kawo na had'a da nawa kayan na bawa abu mai wanki ya riqa wanke mana kinji.
   Rayyanat ta gyad'a mata kai inna ta washe baki snn tace"to yayi er albarka  yi maza ki shirya ki tafi makaranta.

Tafe take cike da fargaba don har yanzu bata cire ran zata sake ganin wanda ke bibiyar ta ba gashi yanxu nasir yayi tafiya bare ya rakota kmr yanda yayi mata a kwana biyun nn da suka wuce.
   Sai sauri take har tana hard'e qafafu jin alamar ana binta a baya dmn har sautin tafiya tana ji ,
kan tsananin tsoro bata iya juyawa ba sae ma duqawa tayi zata kwashi takalmanta ta banka da gudu.
  Sae taji an mata sallama cikin murya mai mugun taushi da sanya natsuwa ga duk wanda yaji hkn yasa ta fasa abinda tayi niyya sae dai cike da 6acin rai ta miqe dmn ganin wanda ke neman takurata a rayuwa.


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮





```Na Billy giro😊```



30/12/2016



🔮```14```🔮
Murmushi ya sakar mata duk da ba ganin fuskar tata yake ba kansancewar niqab d'inda ke sanye da ita.
   Kafin ya ce komai ta buga mai uban tsaki tace"wai malam lfy kake faman bibiyar rayuwata!wani  murmushi ya sake sakar mata yakai  hannu cike da natsuwa ya shafo sumar kanshi snn yace"sbd ina sonki"harara ta dallah mai had'e da tsaki "ta tafi ta barshi nn tsaye,
  Bai bita ba sae tsayuwar sa ya gyara tare da hard'e hannuwan sa a qirji yana kallonta har ta 6ace ma ganin sa.
  Juyowar da zaiyi ne sukayi ido hud'u da Man dake masa wani mugun kallo na tsana yace"kai amma ka bani kunya wlh kai yanxu baka ga abin bibiya ba sae wnn abar "uhm man kenan wnn ce abar yrnyr da ta koina ta amsa kiran mace har mace ga natsuwa da kamala .....mtsw! Man yaja tsaki yace"ga dukkan alama ka fara shaye shaye shiyasa kake ganin abu baibai,nn ya tafi ya barshi kmr wanda zai tashi sama.
   Gidan inna ya nufa ya sami inna da baaba hurera zaune a tsakiyar gidan suna fira.
  Ya gaida su sae baaba hurera kad'ai ce ta amsa gaisuwar ,
inna dake harararsa ganin zai shigar mata d'aki tace"me kuma zakayi min a cikin d'aki bayan duk gamu nn a waje"baaba hurera tace"ke ko dai inna mai gida ne fa ai kya tashi ku shiga ciki kiji dame yazo,
 ai nasan ba abinda yazo dashi face tambad'a da iya shege,ni kwana biyun nn ma da baka zo ba sae naji sat kmr an cire min qaya.

  Kujerar zaman mata naga man ya jawo wacce su inna ke zaune kan irinta yasa farin handkerchief d'insa ya share snn ya zauna yana fuskantar inna d'auke da murmushi a fuskar sa yace"ashe inna in na mutu kin huta dani kenan... zaro ido tayi tace"me kuma ya kawo zancen mutuwa ana zaune qalau, to inna ke kika ce kinji dad'i da banzo kwana biyun nn ba, yo dan nace haka Muhammadu ai bazan yi ftr ka mutu ba nida nake son ganin 'ya'yanka kafin na bar duniya tukuna ma wai kai don ubanka yaushe zakayi auren ne kullum kana mana yawo da hnkli baka ko son ana zancen,
 ni ka gaya min idan kana fama da rashin lafiya ne inji dan insan ta inda zan fara nemar ma magani, sajen fuskar sa ya shafo yana kallon inna wanda har lokacin da murmushi d'auke a fuskar sa yace"inna me kuka dafa yau? Ban sani ba ina ma magana kana wani  zancen, oh ni Hajara wai ko dai muhamnadu gamo kayi da aljana da duk ana ma zancen aure sae ka canza da wata maganar,ta qarashe mgnr cikin kuka irin na tsafi d'in nn, mohd ya kalle ta da kulawa yace"nifa inna kinsan na tsani na ganki kina kuka indai aure ne  nayi kusa nn bada jimawa ba inshaAllah"
   Kai zo kuka farin ciki gun inna har da su rawa tana yiwa man kari kan irin farin cikin da yasa ta yau ta jashi zuwa d'aki sae zuba
masa albarka take yayinda baaba hurera tabi su da kallo tana dariya dn har lokacin inna rawa take man kuwa sae murmushi yake don shi yana son ko yaushe yaga inna cikin farin ciki .
  Inna da kanta taje ta kawo mai abinci wacce yinin rnr duk cikin farin ciki tayi shi.


6:5pm
Rayyanat ce ta shigo gidan ta dawo daga makaranta ta sami man kwance  a falo kan 3 seater kmr mai bacci don idanuwan sa a rufe suke, tsaye tayi tare da yaye niqab d'in fuskar ta tana masa kallo mai cike da tsana,
karaf idanuwansu suka had'u tayi saurin kauda idonta tare da  gaishe shi ba tare da ta damu da ya amsa ko kar ya amsa ba tayi ficewar ta zuwa d'akinta.
  Da sauri man ya tashi ya bita ya finciko hannunta da qarfin tsiya har sae da jikinsu ya had'u sae kuma yayi saurin ture ta daga jikin nashi ya nuna ta da yatsa yana fad'in"ba nayi warning d'inki kan wnn d'an iskan kallon da kike min ba ,wlh ina mai gaya miki duk na qara kama ki kina min irin wnn kallon na lafira sae yafi ki jin d'adi!dan ubanki inni sa'anki ne ko kuma abokin wasarki!
Zama d'aya qwalla ta ciko a  idon Rayyanah kan jin zafin zagin da ya mata,ta d'ago tana kallonsa haka shima kallonta yake har hawaye suka fara sakkowa a hnkli kan kumatunta .
   Ya watsa mata mugun kallo snn ya bar d'akin  Rayyanah kuwa share hawayenta tayi snn ta ajiye jakar hannunta ta cire hijab da socks ta kai su a muhallinsu.
  Tayi zamanta a d'aki har sae da ta tabbatar mohd ya bar gidan snn ta fito taje d'akin inna wacce tana ganinta ta washe baki tana tarbon ta da murna kyace ta kwana bata ganta bane.



Bayan sati d'aya da faruwar haka Mohd ne zaune a office d'insa yana waya kan cewa "a bashi ixini ya shigo"ya ajiye wyr ba jimawa aka turo qofa ya kafe wanda ya shigo da ido har ya zauna.
   Hannu suka bawa juna suka gaisa snn wanda ya shigo ke cewa"Man magana naxo muyi mai muhimmanci kuma dan Allah kar kayi poking d'ina"man dake jingine ya lumshe ido tare da sauke ajiyar zuciya snn yace"ina jinka"
  Kallon sa yayi da kyau yace"about wnn yarinyar ne da nake bibiya idan zata tafi islamiya ashe ma ka santa"da sauri man ya bud'e idonsa dake rufe yace"aka ce maka na santa who say so? Nop ba wanda yace kawai ni naga hkn sbd a kullum gidan inna nake ganin tana shiga haka kuma gidan take fitowa"to ban santa ba nima ganinta kawai nake a gidan"
  A sanyaye mutumin yace"to naji ganin ta kawai kake da haka nake so ka taimaka min kamin jagora muje ko yrnyr nn zata fara kulani dmn wlh nayi nayi ta kulani taqi gashi ni kuma dgske nake sonta wlh"
 Man da tunda ya fara zancen sa yake masa kallon ka ta6u yaja dogon tsaki tare da girgiza kansa yace"tabbas munir ynx na tabbatar ka fara shaye shaye amma ka 6ata kanka wlh ka kuma cuci iyayenka da tarbiyar da suka maka"
   Cikin damuwa munir yace"wai Man meye hk duk a cikin frnds kafi kowa sanin halina fa....banda yanzu da ka sauya halayen ka don haka ni ka ma ftr min daga office,pls man.... Munir!nace ka fita ko!
 Cikin 6acin rai munir ya tashi ya fita ya bar mohd dake juyi a hnkli kan kujerarsa yaja guntun tsaki yace"na rasa wace irin qwaya ce yake sha dake sauya mai tunani gabad'aya da har ya fad'a jin son wnn abar har ma wai yake cewa na masa jagora sae kace ni d'an makauniya ne ko makaho"


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮





```Na Billy giro😊```



1/1/2017



🔮```15```🔮
Munir yaro ne kyakkyawa mai matuqar mutunci da kamala haka kuma yaro ne mai girmama manyansa ya kasance mai tausayin talakawa sosai sbd haka ya taso ya sami iyayen shi da son taimakon talakawa duk da irin kud'in sa kuwa basa da wulaqanci ko kad'an asali ma gidan su munir gida ne da ko yaushe zaka sami jama'a wad'anda ake bawa taimako.
  Su biyar ne a gun iyayen su ,shine na farko snn hameed ,Hasheem,Hafsat snn er autar su safiyya.
  Munir ya jima yana son yayi aure amma bai sami wacce ta kwanta mai a rai ba sae akan Rayyanat wacce ko da kuskure bai ta6a ganin fuskarta ba amma rnr farko da ya fara ganin ta yaji ta kwanta mai a rai ya kuma ji a ransa irin matar da yake son aura ce.


Ranar alhamis ba islamiya hakan yasa Rayyanat tayi zaune tana ta mitar littafanta,
 ita kad'ai ce a falon tana karantawa da larabci tana fassarawa tamkar tana a gaban malami yanda ta taqarqare.
   Ba komai yasa taxo falo tana yin karatun ba sae don inna ta fita anguwa baaba hurera kuma tana kitchen,gashi inna tace xa'a kawo saqo shiyasa taxo falo ta zauna kar wanda inna tace zai zo ya kawo saqo yazo basu ji ba.
   Rayyanah yarinya ce mai tattara hnklinta gabad'aya akan abinda ta sa ma gaba hkn yasa bata san da shigowar  Mohd ba duk da kuwa sallamar da yayi sae ganin mutum kawai tayi tsaye a kanta, a tsorace ta saki ihu tare da jefar da littafanda ke hannunta zata kwasa da gudu kenan man ya dakatar da ita cikin daka mata tsawa, sae kawai ta fashe masa da kuka tana kallon shi ,wacce sae a snn ta gane waye,ai kuwa kai tsaye ta had'e girar sama da ta qasa tare da share hawayen fuskarta, Mohd kuwa tsaki yaja yayi tsaye yana kallonta yayinda hannyen sa ke cikin aljihun wandonsa,ciki ciki ta gaida shi ta duqa ta kwashi littafan ta ta wuce ta kaisu d'akinta ta ajiye snn ta nufi kitchen dai dai baaba hurera ta shigo ta qofar baya duk a rud'e, tace"Rayyanah ba kece naji ihun ki ba ina bayi?
 Kmr wata qaramar yarinya ta 6ata fuskarta tace"nice Baaba wnn d'in nn ne ya shigo ban sani ba sae ganin sa nayi shine na tsorata"
   Baaba hurera tace"waye kuma wnn d'in nn ?Rayyanah tace"wnn d'in nn dake zuwa gun inna kullum.
  Baaba hurare kam bata gane ba sae  falo ta tafi dan ganewa idonta ,
tana ganin mohd ta washe baki snn tace"ayyo wai muhammadu kaine Rayyanah ke cewa wnn d'in nn sae duk ban gane ba shine nace bara na fito naga waye.
  Murmushi ya sakar mata tare da gaida ta snn yace"inna fa na shiga d'akin nata ban same ta ba"
  Baaba hurera da har lokacin murmushi take tace"ai ta d'an fita ne ita da Nasiru amma tace bazata jima ba zata duba Fatima (pretty) ne dake jin jiki,to Baaba ace da wnn yrnyr ta kawo min abinci na,Baaba hurera tace "to"snn ta koma kitchen ta snr da Rayyanat.


Tun daga qofar kitchen mohd ya tsare Rayyanat da mugun kallo har ta qaraso ta ajiye masa abinci zata juya yace"ke xo nn"
   Juyowa tayi tare da watsa masa manyan idanuwanta a cikin nashi,
 guntun tsaki yayi ya kauda nashi idanun sae kuma ya sake kallonta snn yace"wae ke wace ce da kika raina ni haka meye matsalar ki dani?kauda idonta kawai tayi ba tare da tace dashi komai ba, ya saki tsaki yace"tafi ki bani guri amma wlh duk rnr da na qara jin kince min wnn d'in nn sae bakin ki ya gaya miki"

Ta juyo had'e da ta6e baki ta fara tako kenan taji yo sallama ta amsa sallamar ta tafi ta kar6o saqo ,
kitchen ta tafi da saqon dan inna ta gaya mata abinda za'a kawo wato nmn kaji,tas Rayyanat ta wanke nmn ta zuba a freezer.

Washe gari rnr juma'a Rayyanat taci er kwalliyarta ta juma'a tana zaune abinta a d'aki ta gama karatun srtl kahfi ta jawo litattafanta na islamiya tana mita.
  Tana cikin haka taji inna na qwala mata kira ta fito da sauri taje falo ta sami inna dasu saliha da Ameera nn ta saki fuska suka gaisa  da saliha akasin Ameera da ta qi ko kallon gefen Rayyanat.
  Inna ta kalli Rayyanat washe da baki tace"dama yanzu nake shirin kiranki kixo kici abinci sae ga su saliha sun shigo kinga sae kije ki d'ebo maku abincin kuci tare"
  Rayyanat taje ta d'ebo masu abinci a  qaton plate ,
fried rice ce da akayita ta da qoda tayi kyau sosai har ta gaji d'auke da paper chicken  da aka d'ora a gefe.
   A nn falon sukayi zaune zasu ci ,
saliha ta kalli Ameera wacce ta maida hnkli kan TV bata da niyyar tasowa suci abinci ,tace"Ameera taso muci abinci ke muke jira fa"da d'an mamaki Ameera ta kalli saliha snn ta nuna kanta da yatsa tace"ni d'in nn'sae kuma ta wani  yamutse fuska tana kallon Rayyanat kmr wata abar qyama tace"kuci kawai ni a qoshe nake sae dai zuwa anjima ko zanci"kafin saliha tace komai inna tace"kinga bana son iya shege tashi kuje kici cikin taro ai yafi"
  Wlh inna a qoshe nake sae dai zuwa anjima,ke kika sani cewar saliha wacce tuni ta fhmci dalilin da yasa Ameera taqi tasowa suci abincin.
  Suna cikin cin abinci saliha ke cewa "yauwa Ameera idan mun qarasa cin abinci ina son muje ki rakani gidan su yaya munir gun safiyya na kar6o house wears d'ina sbd dai dai su nake son amin sabbin da za'a d'inka min"
  Ameera tace"to gama d'in muje ko banza ina son naje naga safiyya"
 Wlh kam safiyya nada qoqarin ziyartarmu"cewar saliha wacce ta kalli Rayyanat tace"tare fa zamuje dan ki hanzarta cin abinci naga sae ci kike kmr ba kya so"Rayyanat tayi murmushi tace"to so kike ina cin abinci sauri sauri naje har ya sarqe ni ai komai sannu a hnkli yafi"
  Murmushi saliha tayi tana mai kallon Rayyanat tace"hakane amma kin fiye shiririta gun cin abincin naki in nice ma sae ya girshe ni kafin na qoshi, shiyasa nake sauri abuna sae na kammala cin abincin ina mai marmarin sa don nafi son haka,kema idan kika gwada yin haka zaki fi jin dad'i.
    A sanyaye Rayyanat ta kalli saliha tace"har abada bana son sauya tsarin cin abinci na sbd haka na taso na sami Abbana yana ciyadda ni.
  Tana kawowa nn hawaye suka sakko kan kumatun ta tayi saurin tashi ta bar gurin yayinda saliha ta bita da ido cike da tausayi.
  Ameera ta ta6e baki tace"kukan name kuma ana zaune qalau? Ajiyar zuciya saliha ta sauke tace"bari kawai Ameera wlh Rayyanat abin tausayi ce dmn ta bani labarin rayuwarta ciki har da mutuwar mahaifinta da shi kad'ai ne gatan ta a duniya kinga dole tayi kuka a duk lokacin da ta tuna shi,Ameera ta wani  ta6e baki tace" to Allah ji qan mamata"
  Amin cewar saliha wacce ta tashi taje ta lallaso Rayyanat ta shiryo suka fito .
  Ameera kam ganin da Rayyanat za a tafi tace ta fasa bata zuwa su dai gaida safiyya, ko kad'an saliha bata damu ba duk da ta fhmci dalilinta.
  Inna suka je sukayiwa sallama suka fita ta bisu da Allah  dawo daku lafiya.

Gidan ba nisa sosai dan qasa ma suka bi ,suna shiga gidan Rayyanat ta tsaya ta kasa shiga ba don komai ba sae don hango munir da tayi zai shiga mota,
 sosai gabanta ya fad'i don ta rasa wane irin mutum ne shi da duk inda taje sae ta had'u dashi.
  Saliha ce ta riqo hannunta tana fad'in"zo muje mana"
  Haka Rayyanat ta dake tabi saliha sbd tasan idan ba gamo tayi ba ba zai gane taba tunda kullum cikin niqab yake ganinta.
  Da sauri ta sadda kanta qasa ganin irin kallon da yake mata har ma ya fasa shiga mota ya nufo su yazo ya tsaya gab da ita,gam ta qara riqe saliha dmn ta gama yarda gamo tayi, saliha kuwa sae washe baki tayi tana kallon munir tace"yaya munir ina wuni? Fuskar sa wasai ya amsa mata har yana tmbyr ya su umma tace"duk suna lafiya.

nn taja Rayyanah zasu wuce, yayi saurin dakatar da ita kan cewa "ki shiga kawai qawar ki zata same ki daga baya"
da qyar saliha ta iya qwace hannunta daga na Rayyanat ta tafi ta barsu d'auke da murmushi a fuskarta.
  Da hanzari Rayyanat ke qoqarin bin saliha munir yayi saurin shan gabanta yace"yau kam ba inda zaki sae kin saurareni"
 Kuka kawai ta fashe masa dashi  dan gabad'aya ta gama tsorata dashi.

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮





```Na Billy giro😊```



2/1/2017



🔮```16```🔮
 Cikin muryar sa mai saka natsuwa ya shiga bata haquri har ta tsagaita kukanta da takeyi marar sauti.
  Cikin kulawa ya kalleta da kyau snn  yace"kin tsorata dani ko shiyasa kike kuka,ko kad'an baki da laifi a bisa tsoratar da kikayi sbd ban ta6a ganin fuskar ki ba amma yau ina ganin ki na gane kece ,
 kin san sbd me na gane ki?
  D'agowa tayi tana kallon shi ,
Shi kuma kmr wanda ke tsaye da er shekara shida  yace"to yi min magana man sae na gaya miki"
  A sanyaye tace"sae ka fad'a"
  Murmushi yayi tare da nuna gefen zuciyar sa yace"ta nn na gane kece sbd duk lokacinda na gnki zaki tafi islamiyya bugun xuciyata ya kan canxa har sae kin 6acewa gani na,shiyasa nake tunanin idan na rasa ki ya zanyi dmn nasan zuciyata zata iya lalacewa ta bar jikina,da haka nake roqon ki kan dan Allah ki amince dani kinji.
  Kallon sa tayi shaye da toka tace"kaga malam ni zan shiga ciki"
  Sosai ya langwa6ar da kansa cike da son kora mata wani bayani tayi saurin girgiza kanta alamar bazata saurare shi ba ta kuma kama hnya ta bar gidan sae kiranta yake yana rarrashi kan ta dawo ya shigar da ita cikin gida amma fafau taqi tsayawa.

Tana isa gida dai dai ta kai tsakiyar falo sae kawai taji ta fashe da kukan da ta rasa dalilinsa ai kuwa da gudu ta shige d'akinta don bata son wani  yaga tana kuka,sbd sam hnklinta bai bata ganin kowa a falon ba alhali kuwa Mohd da Ameera suna nn zaune.
  Ameera ta kalli mohd da ya tsure qofar Rayyanat da kallo kmr mai wani  nazari can ya maida duban sa ga Amira yace"ita wnn daga ina ta fito? ta6e baki tayi snn tace"gidan su yaya munir ta raka saliha ,saurin kallonta yayi jin gidan da ta ambata ita kuma ta qarasa da cewa"wata qil qauyanci  ta nuna musu shiyasa suka koro ta"
  Komai bai ce mata ba sae tashi yayi ya fita.

Rayyanat na cikin kukanta taji an turo qofa tayi saurin tashi ta share hawayenta ,saliha wacce ta shigo taxo gab da ita ta zauna ta riqo hannyenta cikin murya mai kama da ta rarrashi tace"haba Rayyanat meyasa kike ma yaya munir haka yace tsawon lokaci yake bibiyarki amma kinqi ki saurare shi,don Allah Rayyanat ki taimaki yaya munir wlh na fhmci mugun sonki yake ,Hawaye ne suka gangaro kan kumatun Rayyanat tace"saliha ki bawa yayanki haquri dmn tunda yaya anwar ya mutu na ajiye soyayya ba kuma zan qara ba ko banza ma bazan iya soyayya da mutumin birni ba ,meyasa zaki ce haka Rayyanat naga ko yaya anwar a labarin ki da kika bani shi d'an birni ne,eh amma shi asalinsa d'an qauyen mu ne nace maki ba tashin birni bane ,amma Rayyanat d'an birni da na qauya ai duk abu d'aya ne dmn duk Allah ya yisu'"um um ba d'aya bane saliha,akan me zaki ce haka? Sbd ba d'aya bane,ajiyar zuciya saliha ta sauke tana mai kallon Rayyanat tace"indai hali kike tunani to wlh yaya munir yana da halin kirki....a zahiri ba dmn baki san meye bad'inin sa ba"
amma kinji ance labarin zuciya a tambayi fuska "banda hali saliha ba kuma xaki gane dalilin da yasa na tsani d'an birni ba sae nn gaba,da mamaki saliha tace"tsana kuma,to wani  abu d'an birni ya miki ne dmn naga a cikin labarinki anwar kad'ai ne d'an birni kuma kince lfy kuka rabu dashi asali ma in rashin mutnci ne ai d'an qauyen naku ya muku wato bala da yasa kuka koma daji da zama,ko kuma kin 6oye min wani  abu a labarinki ne?idanuwan Rayyanat tap da qwallah take kallon saliha tace"Saliha ki daina min tambayoyi haka don Allah"
  Saliha ta nisa tace "shike nn amma ga dukkan alamu ba duka kika gaya min labarinki ba"shiru Rayyanat tayi dmn tasan tabbas bata snr da saliha dalilin mutuwar Baffanta ba kawai dai tace mata ya rasu.
  Tace"hm saliha ki yarda dani mana ni ban rage miki komai ba a labarina ba,kawai dai bana ra'ayin soyayya har da d'an  qauyen ma dmn tunda yaya anwar ya mutu naji bazan iya soyayya da duk wani  d'a namiji ba wnn alqawari ne nayiwa kaina dmn inaji idan na kula wani tmkr nayiwa yaya anwar butulce ne.
   Hm Rayyanat kenan kina nufin haka zaki tabbata ba aure, d'an guntun murmushi Rayyanat tayi snn tace"To ce maki akayi rayuwar tawa tsawo ne da ita nida ma nake roqon Allah yasa rayuwata zata kai ga na cika burina" hm har akwai wani  buri a gun 'ya mace da ya wuce aure? Kallonta kawai Rayyanat tayi ta kauda kanta,snn tace"inada wnn burin amma a da wato kafin yaya anwar ya mutu.
 saliha tace"nidai Rayyanat al'amuranki na bani mamaki rayuwar ki idan mutum ya kalla kmr so simple n easy amma ashe in kika dake kan abu kin dake
 kenan.
  Ba hk bane saliha yaya anwar yana da matuqar muhimmancin da bazan iya kula kowa ba.
  Cikin nuna 6acin rai saliha ta tashi tace"tunda haka kikace shikenan shi kuma yaya munir Allah ya bashi wacce ta fiki da komai ma"
 Nn ta fito falo ta sami mohd zaune yana cin abinci ya tsare ta da ido kmr wani  mai tuhumar ta,ta sadda kanta qasa tare da gaida shi snn tace da Ameera tashi muje gida ,nn ta tashi sukayi wa inna sallama zasu fita mohd ya kira saliha tare da zaro kud'i a aljihunsa,
 saliha taxo cike da ladabi,
 Ameera kuwa ta biyota cikin rawar kai ,
mohd ya dalla mata harara yace"bana son shisshiga fa ke na kira ko saliha"
kmr zata yi kuka tace"saliha"
  Girgiza kansa kawai yayi had'e da d'an guntun tsaki don ko kad'an baya son hali irin na Ameera nn ya miqawa saliha two thousand a cewar suyi kud'in a daidaita tayi masa godiya suka wuce.

Bayan ya kammala cin abinci yaje d'akin inna zai mata sallama inna dake zaune tana lazimi tace"yauwa d'an albarka yanzu nake qoqarin tashi na same ka,sbd ina son zamu yi wata magana mai muhimmanci da kai,a natse man ya zauna kan gefen gadon inna yace"ina jinki inna".



Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮





```Na Billy giro😊```



3/1/2017



🔮```17```🔮
Muhammadu tafiya nake son zanyi a cikin satin nn zuwa qauyen mu dmn na jima rabona da zuwa shine nake son zan kai Rayyanah a can gidan ku har idan na dawo.
   A natse mohd ya d'ago yana kallonta snn yace"shike nn inna amma kinyi magana dasu Abba kuwa.....Yo sae da izinin su zanyi tafiyar ne ko kuwa Rayyanah d'in ce baka son ta zauna gidan naku! Ba haka bane inna sanin dai nayi tafiyar ki idan kika yita sae wanda ya ganki,inna ta washe baki tace"ayyo ai muhammadu kasan en uwa dad'i ne dasu shiyasa nake d'an jimawa idan naje.
  To inna wace rnr zaki tafi? Eh to rnr laraba nake son na tafi in Allah yaso,to Allah ya kaimu lokacin inna, Amin Amin d'an Albarka.
   Tare suka fito shida inna ta nufi d'akin Rayyanat shi kuma ya fita daga gidan.

Zancen tafiyarta ne taje ta snr da Rayyanat ta fita ta bar Rayyanat cikin rashin jin dad'i da tunani sae take jin kmr kar inna tayi tafiyar nn ba don komai ba sae don sabon da tayi da inna.

Bayan kwana uku da faruwar haka cikin ikon Allah ynx munir ya fara shawo kan Rayyanat dan yanzu har tana d'an tsayi ta saurare shi.

Ko yauma tafe suke ta dawo daga islamiyya sae janta yake da fira ita dai iyakarta murmushi da kuma wasa da en yatsunta.
  Har qofar gida ya rakota tana shiga gidan sae ga Muhummad ya fito zai tafi masallaci dan har an fara kirayen kirayen sllr magrib.
  Cikin sakin fuska munir ya miqa masa hannu suka gaisa inda shaye da toka man ya zare hannun sa daga na munir ya wuce, munir ya bisa da murmushi dmn inda sabo ya saba da halin abokin nasa.
  munir yaje ya nemi buta yayi arwala ya shiga masallaci sbd dama masallacin kusa da gidan yake .

Rayyanat kuwa tana shiga gida ta cire hijab, niqab da socks, ta jawo er akwatin ta da inna ta saya mata,ta ciro kayanta a wardrobe tana tsarawa da yake fashin sallah take shiyasa bata yi zancen sallah ba.

Komai da tasan zata buqata sae da ta zuba a ciki snn tayi zaune tana tunanin yanda zata yi rayuwa a gidan su man ,
sae roqon Allah take a ranta kan Allah yasa 6angaren su saliha zata zauna in hkne kam da sauqi.


Guraren qarfe takwas da rabi zaune suke a falo ita da inna suna cin abinci suna kallo inna tace"Rayyanah ina ce kin harhad'a kayanki dan kinsan na gaya miki sammako zanyi shiyasa ma na sallami baaba hurera tun yau, eh inna na harhad'a komai tun d'azun, tayi mgnr ne a sanyaye,inna kuwa ta washe haqora tace"to Allah miki albarka 'yannan idan kinje ki sakin jikin ki sosai don tamkar gidan ku ne kinji, Rayyanat ta gyad'a kanta wanda yayi dai dai da shigowar nasir d'auke da sallama a bakin shi,
inna ce ta amsa masa sallama, Rayyanat kuwa ta gaida shi cikin ladabi snn ta d'auki kwanon tuwonta ta shiga daga ciki.
 Nasir kuwa bayan ya amsa gaisuwar Rayyanat ya gaida inna wacce ta amsa gaisuwar washe da baki snn tace"ka dai ji zancen tafiyar tamu yanda na snr da kai a waya ko, eh inna inshaAllah tunda sassafe zaki ganni,tace "amma fa ina son sae mun sauke Rayyanah a gidan naku, eh inna ai duk kin snr dani hk a waya.
  To ya jikin Fatima da sauqi dai ko, wlh Alhmdlh inna taji sauqi sosai don harma tana cin abinci yanxu, to madallah Allah ya nuna mana ta sauke abinda ke cikin cikinta lafiya ,Amin amin inna.
 Daga haka suka ta6a er fira ,
guraren tara da rabi snn ya wuce.

Washe gari tun da safe nasir yazo ya kwashi inna da Rayyanah suka tafi gidan nasu, inna taje kowane 6angare ta musu bankwana wacce duk 6angaren da taje tana riqe da hannun Rayyanah har saida tazo gun mota zata shiga snn ta saki hannun Rayyant tana mata sae ta dawo.
  Su inna na wucewa Rayyanh ta ajiye kuka amma marar sauti,mohd dake tsaye sae kallonta yake don ya fahimci ba qaramar shagwa6a Rayyant zata yi ba.
   Shida kanshi ya ja mata akwatin ta suka tafi 6angaren su,yana tafe Rayyant na bayanshi har suka tafi d'akin Ameera,sae da ya kalli Rayyanat ganin har lokacin kuka take snn ya kai hannu a hnkli ya fara qwanqwasa qofar.


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮





```Na Billy giro😊```



4/1/2017



🔮```18```🔮
Ya jima yana knocking snn aka bud'e qofar,wani  mugun kallo ya watsa ma Ameera wacce ta fito cike da jin bacci sae miqa take ,tayi saurin daina miqar ganin kallonda yayanta ke mata, kmr da tsoro tace"yi haquri yaya ina bacci koda kake ta qwanqwasa min,bai ce da ita komai ba sae akwatin Rayyanat ya miqa mata tare da fad'in"ki ware mata gurin da zata saka kayanta a nn zata zauna har sae  inna ta dawo.
  Ba musu ta kar6i akwatin ta shigar da ita mohd kuwa ba tare da ya kalli Rynt ba yace"shiga daga ciki idan kika buqaci wani  abu ki snr da ita Ameeran, daga haka ya wuce ita kuma tasa qafa zata shiga dai dai Ameera zata fito sae qunquni take ta bangaji rynt da qarfi har sae da ta nemi fad'uwa bata damu ba don dama da niya tayi snn tayi ficewarta sae d'akin hjyr su.
  Ta shiga cikin kuka mai d'auke da shagwa6a tace"umma wlh ni bazan iya rayuwa da wnn yrnyr a d'aki d'aya ba, xaro ido Umma tayi tace"au wai a 6angaren nn zata zauna?eh yaya ne ya kawota wae har sae inna ta dawo daga qauye,ta qarashe mgnr cikin muryar kuka sosai snn ta d'ora da cewa"gsky umma ni d'akin masu aiki zan maida ta dn tafi cancanta a can"Umma ta nisa tace"kinsan hln yayanki ko dukan ki zai iyayi akan haka dn yafi son duk inda ya ajiye abu to yazo ya same sa a nn"uhm uhm umma dan Allah  nidai ki masa magana ya sauya mata wani d'akin ai akwai d'akunan baqi ma,to shike nn zan masa magana,nn Ameera ta fita tana mai share qwallah.
 Tana zuwa d'aki ta sami Rynt  tsaye riqe da akwatin ta ,ta kalle ta a wulaqance snn tace" fita waje ki jira yaya zai zo ya baki wani  d'akin, ba musu Rynt taja akwatin ta ta fita don sae ftr take ma a sauya mata 6angaren gabad'aya.
  Ta jima tsaye a bakin qofar Ameera kuwa tuni ta shige blanket ta koma bacci.
  Ganin ta gaji da tsayuwa yasa ta rage tsawonta bata jima da haka ba sae ga man ya shigo 6angaren cikin shirin sa na fita aiki yayi tsaye da mamaki yana kallonta snn yace"ke ba cewa nayi ki shiga ciki ba shine sbd qauyanci kika yiwa mutane durqushe a bakin qofa!shaye da toka ta d'ago tana kallon sa snn tace"to ai bayan na shiga wnn qanwar taka tace wai na fito zaka canza min d'aki"
  Komai bai ce mata ba sae kutsa kai yayi ya shiga d'akin sae ihun Ameera taji ta fito aguje tana kuka awa wacce aka fasawa kai wanda hkn yasa iyayensu suka fito a rud'e ,
ta tafi da gudu jikin umma tana kuka Abbansu yace" lfy me yake faruwa ?Abba yaya ne ya mareni ban masa komai ba, Abba ya kalli mohd da ya fito yace"me Ameera ta maka ne wae? Abba kunfa san hln Ameera ta iya wa mutum qarya da fad'ar abinda ba'ayi ba,shine wae yau har abin ya fara kawowa kaina!nn ya matsa gab da Ameera kmr wanda zai bugota yace"yaushe nayi dake zan canza mata d'aki!dake nake magana ki bani amsa koni sa'anki ne! a razane tace"yi haquri yaya wlh qarya na mata baka yi dani haka ba.....er iska yrny wlh duk rnr da kika qara fad'ar abinda bance ba sae nayi maganinki fiye da na yau, daga haka ya wuce kmr wanda zai tashi sama.
   Abba ya sauke ajiyar zuciya yace da Rynt shiga ki ajiye kayanki.
  Umma kuwa taja Ameera suka tafi d'aki sae fad'a take mata tana fad'in keda nace zan masa magana me kuma ya kaiki yin haka gashi ynx kin 6arar da komai don yanzu dole ki zauna da ita d'aki d'aya ba kuwa zan nema maki alfarmar sa ba, Ameera dai sae kuka take bata ce komai ba don tasan ta riga da ta jama kanta.


Rayyanat na shiga d'akin ta nemi guri ta ajiye akwatin ta snn ta kalli agogon bangon da ke d'akin qarfe tara da rabi time d'in islamiyya ya tafi don ta makara sae dai zuwa yamma sae duk bata ji dad'i ba hkn yasa ta ciro littafanta tana mita.

Kwana Rynt hud'u a gidan kullum sae Ameera ta nemi tayi fad'a da ita amma tana basarwa duk da tana jin zafin abubuwan da take mata kuwa.
  Haka kwata kwata hjy bata sakar mata fuska ko gaisuwa da qyar take amsa mata sauqinta d'aya saliha na zowa suyita fira abinsu snn duk zata je islamiyya Abba ke bata kud'in napep.
   Sae dai babbar matsalarta shine abinci wanda sae da kulawar Abba ake kawo mata abinci idan bai kula ba haka zasu barta da yunwa,mohd kuwa kmr ma baya garin don tun daga rnr bata qara ganin sa ba.
  Cikin shirin ta tsaf na islamiyya ta fito ta sami Abba zaune a falo ta durqusa har qasa ta gaida shi cike da ladabi ,ya amsa mata cikin sakin fuska tare da zaro dubu d'aya a aljihu zai bata ta girgiza kanta snn ta qara sadda kanta qasa tace"Abba ai kullum kud'in da kake bani sunyi yawa har ma ynx akwai canjin da zasu kaini yau da gobe, dad'i Abba yaji har ransa ba don komai ba sae don halayen Rynt dake matuqar birge shi,yace"to shike nn tashi ki tafi Allah yayi miki albarka"

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN  BARSHI BA! ```🔮







_1/06/2017_






            🔮🔮🔮
_*page*_ ```20```

Zumbur umma ta miqe tace"haba Alhj! ni na d'auka ko zancen arziqi ne zanji ashe na tsiya ne.... Kina da hnkli shi zancen aure ne na tsiya...yo zancen tsiya man idan ba haka ba meye had'in mohd da wnn yrnyr er matsiyata er qauye ga 'ya'yan manya a gari,haba dan Allah! ,dan Allah Alhj ni ka ma daina wnn zancen.
  Baxan daina sa ba kuma aure tsakanin mohd da Rynt kmr anyi an gama ne, ai bake keda iko dani ba haka shima ba ajiye ni yayi ba da ko yaushe na masa zancen aure se yace tukuna sbd ya maida mutane en iska shasha.... Amma alhj tsakani fa da wnn cutar dashi kake sonyi ai gwanda ya zauna ba aure da ace wnn yrnyr ce matar sa sae kace bakin uwa a rasa wacce za'a ce ya aura sae ita haba dan Allah!
   Mtsw sae yau na fhmci rashin hnklinki ne kika yarfawa 'ya'yanki da kaf famlyn nn ba wanda yayi rashin mutuncin su ,na dai ji amma nikam sam bazan yarda da wnn zancen ba don wlh bazata sa6u ba wai bindiga a ruwa.

Fuuu!Abba ya fita yana mai fad'in"tsakanin ni da ke sae aga wanda keda iko akan wani .
   Bai zarce koina ba sae downstairs ya samu still mohd na kan cin abinci
yace da mohd idan ka kammala cin abincin ka same ni a d'aki.

Nn take mohd ya kammala cin abincinsa yaje ga kiran Abba.
  Abba ya kalli mohd da ya nemi guri ya zauna a qasa yace"mohd ina son ka saurare ni da kyau kaji,kuma bana son kazo min da wani  shashanci, zancen auren ka shin har yanzu baka sami wacce ta maka bane ko yaya? Aa Abba dama malika nake jira ta kammala karatun ta kuma ta kammala yanzu ni a shirye nake inshaAllh, Abba yayi shiru na tsawon lokaci can yace"er gidan wacece ita malika? ba wani  bane Abba sananen mutum ne wato Alhj ilyas na Allah..... Alhj ilyas na Allah ,yace"eh Abba da wata matsala ne? Abba da yayi shiru yana mai nazari yace"Aa ba komai jeka"
  Cikin farin ciki mohd ya fito ya sami Rynt ta fito kenan tana neman shi.
  Yayi tsaye daga inda yake har ta qaraso gurin shi ,ba yabo ba fallasa ta miqa masa  wyr tare da fad'in"ngde" snn ta juyo tayi ficewarta.


Bayan kwana biyu da faruwar haka ne Abba ya sake kiran mohd.
  Yace"mohd a gsky zancen aurenka da wnn yrnyr malika sae dai nace kayi haquri sbd ba er mutunci bace kwata kwata shiyasa tun lokacin da ka snr dani waye mahaifinta na shiga nazari dmn nasha jin cewa baya ganin kowa da mutunci,sae gashi kuwa da mukaje hakane ta faru damu,dmn wasu banzan sharudda ya shiga snr damu kan auren ka da er sa wad'anda sam hnkli ba zai d'auka ba,don haka tunda ersa ba er gwal bace ka haqura da ita.
  Mohd da tun lokacin da Abba ya fara zancen sa yaji zufa na karyo masa.
 cikin rawar muryar yace"Abba malika yarinya ce mai mutunci kayi haquri kabar ni na aureta tunda ba cewa yayi bazai bada aurenta ba"Abba ya kalle sa kafin yake cewa
"wae mohd ka koji irin maganganun da yake fad'a ne da kowanen mu sae da ya fito cikin 6acin rai wai ace hatta mahaifinku sa'eed da Allah yayi masa sanyin hali matuqa sae da yayi magana kan rashin mutuncin Alhj ilyas na Allah,
 gaskiya da sake don nikam baza ka kwaso min er gidan Alhj Ilyas na Allah ba ,koda kuwà ace ita kad'aice 'ya a duniya tofa sae dai ka hqr don baza ka aureta ba.
  Komai mohd bai iya cewa da mahaifinsa ba sbd gabad'aya lissafi ya kunce masa .
  Abba yace"gaka mohd ina wnn yrnyr Rynt er gidan inna? eh Abba ,to na yanke hukunci zan aura maka ita don wlh ta kwanta min arai kuma inaji a jikina ita alhairi ce a gare mu, cikin tsananin mamaki ya kalli Abbanshi yace"Abba wnn yrnyr fa kace"
eh wnn d'in nn itafa Rynt ba.....ina Abba wlh ni bazan iya aurenta ba kawai dai ka bani dama wlh zan saisaita tsakanin ku da Abban malika, hm mohd kenan kaje dai kayi nazari akan aurenka da Rynt amma malika kam sae dai ka haqura da ita.
  Tashi ka bani guri!

Da qyar mohd ya iya tashi ya bar gurin don gabad'aya jikin sa ya mace.

Ya tafi 6angaren sa cike da tunani kala kala a ransa ya zauna kan sofa tare da dafe kansa ,can kmr wanda aka tsakura ya zari makullin motar sa ya fita.


Wani  katafaren gida ya nufa yayinda anguwar ta kasance very cylent ,ya parkar a bakin gate d'in gidan snn ya d'auko waya ya kira malika ,yana gama wyr ya d'aura kansa kan sitari ba jimawa sae gata ta fito cikin wani  banzan dressing awa arniya ,kyau kam ba laifi akwaishi haka ma qirar jiki Alhmdlh kamar ita tayo kanta.
  Cikin isa da yanga ta shiga motar tare da fad'in "my man ya baka shiga ciki ba ka tsaya a nn kmr wani  baqo?
   Mohd ya d'ago yana kallonta da idanuwansa da suka rine zuwa ja,yace cikin harsh voice"malika meyasa mahaifinki zai mana haka!"ta kauda fuskar ta gefe inda cikin sanyin murya tace"kayi hqr my man wlh nima banji dad'in abinda Abbana yayi ba,kasan hlin Abba sae a hnkli ,ba kace ga wanda yake mutunci dashi ba kowa ciwa mutunci yake..... Gud! ai gashi yanxu ya jamana baza mu auri juna ba ....ta zaro ido tare da fad'in "haba my man me yayi zafi haka? Sae da ya watsa mata mugun kallo kafin yake cewa"hln su iyayena duwtsu ne ko kuma basada zcy a qirji da Abbanki zai gaggaya musu maganganu ransu bai 6aci ba!,calm down my man sharudda ne fa ya kafa musu ba maganganu ya gaggaya musu ba,wane sharudda ne wai?tayi shiru tana kallon shi ,yace cikin d'aga murya "ki gaya min mana!kukan shagwa6a ta fashe masa dashi tace"nidai kayi haquri ba sae kaji ba wlh ba dad'in ji kuma don Allah ka ajiye zancen ba aure tsakanin mu wlh i cnt be wit a u,
yace"malika ke da sauqi ma shin kinsan chakwakiyar da nake ciki ma ta had'ani aure da ake shirin yi da wata banza can er qauye !
  A rikice tace"bangane ba"baza ki gane ba kam tunda mahafinki ya 6arar mana da lissafi.
 Ta wani  marairai ce fuska tace"don Allah kamin bayani wlh ban fhmta ba"yace"malika Abbana ya hana min aurenki sbd zafin abinda Abbanki ya musu shine har yake qoqarin had'ani aure da wata kucaka,Komai kasa ce masa tayi sae kallon sa take hawaye na fmn zarya kan kumatun ta yace"take it easy don ko mutuwa nake bazan auri wnn yrnyr ba,abu d'aya nake so dake yanzu shine kisan yanda zakiyi Abbanki ya bawa iyayena haquri ya kuma janye banzayen sharuddansa to idan kika yi haka inshaAllah  Abbana zai haqura.
  Share hawayenta tayi tare da fad'in"shikenan my man inshaAllah i will try my best"

 Kusan kwana hud'u amma malika ta rasa ta yanda zatayi ta shayo kan mahaifinta don ta sanshi kaifi d'aya ne in ya fad'i abu tofa shikenan.

Mohd kuwa kullum bayada aiki sae na roqon Abbansa kan yayi haquri ya janye aurensa da Rynt amma sam yaqi .
  Rynt kuwa kwata kwata bata ma san da zancen ba ga soyayyar ta da munir sae abinda ya qaru wanda yanzu munir jiran dawowar inna kawai yake dmn ya snr da ita abinda ke tsakanin sa da Rynt ya kuma snr da ita yana so zai aure ta.


Mohd ne durqushe a gaban iyayen shi kmr kullum yazo bada haquri a janye zancen aurensa da Rynt Abba yace"bafa zan janye ba idan har kaga na janye tofa lallai inna ce ta buqaci haka"haba Alhj gaskiyar magana kana son takura yaron nn ai kasan halin inna zama d'aya take amincewa da duk wani  zancenka,kawai kar ma ka snr da ita zancen nn dan Allah ka bar yaron nn ya auri wacce yake so...na barshi ya auri wacce ya keso ai inace kinji abinda uban nata ya mana wae har mu yake cewa yaji ya amince zai bada er shi ga d'anmu amma fa mu sani shi er shi ba tunkiya bace ko akuya da zata je tana haifawa d'anmu 'ya'ya barkatai kmr yanda yake ganin a familyn mu ana haifo mana 'ya'ya hkn nn ba tsari,shi a tsarin sa bazai wuce ace ersa ta haifawa mohd 'ya'ya biyu ba idan ba haka ba tofa sae dai d'anmu ya haqura da ersa,wnn wace irin magana ce babu dad'in ji snn har kike tunanin zan amince na had'a surukuta dashi.
  To Alhj sae akace don ya fad'i tsarin sa shi zai sa dole abi ,muradi kawai ersa ta shigo hannun mu ,mu kuwa sae yanda mukayi da ita tunda ta rigada ta dawo a qarqashin ikon mu..... Sam bazan yarda da auren da za'ayi ana dinga ci min mutunci ba, dmn nida shi ba wanda zai nunawa wani kud'i ba kuwa zai zo yana dinga nuna min iko ba don kawai d'ana yana auren ersa!
   Cikin damuwa sosai mohd yace"don Allah Abba kayi haquri  wlh a guna ba matsala ai yara biyun ma sun ishe mu jin dad'in rayuwa.....kul!na qara jin zancen nn ya fito a bakin ka!kuma maganata ta qarshe shine ba zan janye aurenka da Rynt ba wlh,sae idan ita Rynt d'ince ta furta da kanta cewa bata sonka, kuma ko bayan raina ban yafe maka ba idan ka auri malika!



Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮





```Na Billy giro😊```



5/1/2017



🔮```19```🔮
Cikin yanayi najin kunya tace"amin Abba ngde snn ta tashi ta fita ,Abba ya bita da kallo d'auke da murmushi a fskrsa.


6:15pm
 Rynt ce tsaye tana kallon rayuwar 'ya da mahaifi mai cike da ban sha'awa rayuwar su kmr rayuwar ta da Baffanta,a kullum sae ya rako ersa safe da yamma kuma idan aka tashi zata samu yazo yana jiran er tashi, da qafa suke zowa kuma da  qafa suke komawa sbd  ba wani jayawa da inda yake fitowa,sak yrnyr zata iya maida kanta gida amma so irin na 'ya da mahaifi kesa kullum yake zowa d'aukar er shi,hkn ba qaramin tuna mata rayuwarta da baffanta suke yi ba,sbd itama haka Baffanta ke mata a lokacin da take primary mkrntr ba wani nisa da gidansu amma kullum baffanta sae ya rakata haka kuma duk aka tashi zata samu yazo yana jiranta su koma gida.
  Baffa shine sunan da yrnyr ke kiran Abbanta dashi hkn ke dawo ma Rynt da ryuwar ta sabuwa fil,shiyasa kullum bata da aiki sae na kuka idan tana kallon rayuwar su.
   Ko yanzu hawaye ne suka silalo a hnkli kan kumatunta ta kai hnnu a cikin niqab d'inta ta share hawayen yayinda take magana a ranta cewa
_"Bazan yafe maka ba ba kuma zan ta6a barin ka ba, ka yanke min farin cikin rayuwata haka nima zanyi silar yanke taka"_

"Rynt"cewar munir wanda yazo gab da ita ya tsaya har tana jiyo qamshin turaren shi, bata kalle sa ba sbd lokacin wasu hawaye ne ke faman zarya kan kumatun ta,duk
 da cewa da niqabi sanye a fuskarta sae take ganin kmr zai iya hangowa idan ta kalle shi.
  A hakan ta gaida shi ya amsa yana mai kallon gefen da take kallo wato 'ya da mahaifi da sukayi er nisa a tafiyar su, ya nisa tare da fad'in"dama na jima ina son nayi miki wata tamvaya Rynt, meyasa kullum sae na ganki kina kallon mutanen nn shin kin san su ne? Cikin sanyin murya tace"ko d'aya haka kawai suke bani sha'wa"
 Gama fad'ar hk takai hannu zata tsaida napep yayi saurin dakatar da ita ta hnyr cewa"dan Allah Rynt yau ki barni na kaiki gida kinji"Aa wlh ka barashi kawai ngde"pls Rynt baki san yanda nakeji ba wlh sam bana son ganin kina shiga napep bayan ni inada abinda zan riqa kaiki gida"um um nidai ka barshi nagode"
 daga hk ta shige napep ta barshi.
 
Tana isa gida ta samu sae lokacin malamin su saliha ya tashe su sbd su a cikin gida ake karantar dasu.
   Sae da ta d'an gyra fuskarta sbd har lokacin kuka take,snn ta cire niqab sae kawai sukayi ido hud'u da malamin su saliha zai fita,ga mamakinta kallonta yake har sae da ta gaishe shi snn ya kauda idonsa,ta maida dubanta gun saliha wacce ta qaraso gurinta sake da fuska Rynt tace"wae ku sae yanzu aka tashe ku?eh wlh kedai makara yayi bai zo da wuri ba,Rynt tace"wae nikam meyasa Abba bazai barku ku riqa zuwa isalimiyya ba don kmr hkn zai fi..... Mtsw!Ameera da ta biyo zata wuce taja wani  dogon tsaki tana mai hararar Rynt kmr idanuwanta zasu fad'o tace"to wacce ta san dai dai ai sae kije da kanki ki snr da Abban namu abinda yake dai dai tunda shi bai sani ba, banxa er qauye mai banzar rayuwa!mtsw ta koma jan wani  tsaki ta wuce.
  Ita dai Rynt kallonta kawai tayi saliha tace"don Allah kiyi haquri haka hln Ameera yake kowa bata gani da gashi,murmushi Rynt tayi snn tace"nikam ko kad'an banji zafi ba wlh,nn dai saliha ta qara bata haquri snn kowa ta kama gabanta.

Rynt na shiga ciki ta had'u da Abba ya fito zai tafi masallaci tayi saurin durqusawa har qasa ta gaida shi, fuskar sa wasae ya amsa mata snn yace"Rynt an dawo daga islamiya?
 Can murya qasa mai d'auke da tsantsar ladabi tace"eh Abba"
yace"to Allah taimaka tashi ki shiga daga ciki kiyi sallah ki kuma sami abinda kika ci kafin dinner kinji"tace
"to Abba" snn ta tashi ta wuce shi kuma ya wuce masallaci.

Yau satin inna d'aya da zuwa qauye.
  A washe garin rnr ba islamiya sbd rnr alhamis ce Rynt ta shiga cikin en aikin gidan tana taya su aiki.
 Abba ne ya fito ya same ta tana goge kan dining tana ganinsa ta durqusa ta gaida shi ya amsa
Yana mai kallon yanda idanuwanta suka kumbura yace"lfy Rynt me ya sami idanuwanki? Sadda kanta qasa tayi don dai baza ta iya cemai kuka tayi ba,sae dai ta gaya mai abinda tayi bayan kukan tace"Abba kwana nayi ina karatu"
  Hln kun kusa fara jarabawa ne?Aa hardar qur'ani nakeyi,
 Abba ya jinjina kansa snn yace"haqiqa kinyi dabara Allah ya qara miki kaifin baseera"
  cikin sanyin murya tace"amin Abba nagode"
   Yace "to ya naga kina aiki saki akayi ?Aa ina taya su ne kawai,to idan dai kinji kin gaji kar ki tilasta kanki ga qarasa aikin ki komawar ki kiyi zamanki kinji.
  Gyad'a masa kai tayi yayinda ya ciro wyrsa a aljihu dake faman ruri ya d'aga ya tafi,Rnyt kuwa taci gaba da nata aiki.

umma ce a d'aki ita da Ameera yayinda umma ke matsawa Ameera kan ta tashi taje ta gyarawa mohd 6angarensa sbd yau zai dawo,cikin kukan shagwa6a tace"wlh umma kinsan halin yaya duk yanda aka gyra masa guri sae yayi fad'a wae bai yi ba, au kinsan dai baya son en aiki su gyra masa d'aki ko,ko kuma ni kike son naje na gyara masa? Aa umma ga wnn yrnyr mana mai baqin son aiki tana can yanzu haka tana taya su sahura aiki, don Allah umma kice taje ta gyara masa, to shikenan naji jeki snr da ita ki kuma nuna mata 6angaren snn ki dawo.


Sosai 6angaren ya matuqar birge Rynt har ganin take kaf gidan ba inda yakai  6angaren mohd kyau .
  Sae da ta gama qauyancinta snn ta gyra dak'in tsaf har bathroom ta kuma feshe d'akin da room fresh kala kala da ta samu kan dressing mirro d'insa.

Bayan tayi wanka taci abinci ta tafi 6angaren su saliha ta sami umman saliha zaune a falo saliha na cire mata qumba, ta gaishe ta cikin ladabi yayinda mamar ta amsa cikin sakin fuska har tana cewa"er halak kmr kinsan zancen ki muke ina fad'in yau dai shiru saliha bata je ba baki shigo ba, Rynt tai murmushi tace"wlh mama na d'anyi wani  aiki ne"
to sannu ,zaki  iya zuwa kasuwa yau kuwa saliha ce ta matsa min wae tana son ku siyo inner wears da kayan kwalliya nace ta bari na bayar a siyo muku tace ita tafi son kuje da kanku, ta gefen ido Rynt ke kallon saliha dake faman roqonta kan tace eh, dako d'an murmushinta tace"eh mama xan iya"
  To shike nn kuje ku rubuto duk abinda kuke so se kuxo na baku kud'i...a'a mama ki bamu kud'i kawai in munje zamu ga abinda muke so ai, Aa saliha nafi son ku rubuta sae na baku kud'in enuf, amma fa kar a manta da er autata ita ma a siyo mata nata, "to shike nn mama ai baza mu manta ta ta ba"nn taja hannun Rynt tace "muje ko"

Bayan sun shiga ne saliha ke cewa"Rynt ni kuwa wane aiki ne kikayi da duk yawan en aikin gidan baza suyi ba sae ke?hm na gyarawa yayanku d'akinsa ne wae zai dawo....cabd'i Allah ya cece ki da masifar sa, Rynt ta zaro ido tace"me?saliha tace "ba wani  abu bane fa shidai matsalar sa d'aya duk yanda aka gyara masa d'aki sae yace bai yi ba yayita masifa kuwa.
  Hm ni ba masifar sa ba ma ,zagin da yake yi ne bana so don wlh na tsani a zagar min uba ,"shi kuma yanada wnn"
cewar saliha snn tace" sae dai kiyi haquri don muma wlh haka yake zagin mu in ya tashi masifar sa.
  Cikin muryar kuka Rynt tace"Ai gwanda ku naku iyayen suna raye ba zafi kmr ni da basa raye"
  Saliha tace "haba Rynt meye na kuka kuma
"Baffa"cewar Rynt wacce ta rungume saliha tana kuka tace"saliha wlh ina mutuwar son baffana amma an raba ni dashi zama d'aya, ba a barni da zafin ba ana kuma zagar min shi"
  Saliha tace"kiyi haquri Rynt haka mutuwa take bata barin wani don wani....
_shiyasa nima Bazan bar wanda ya kashe min shi ba koshi waye_
Haka Rynt ta fad'a a ranta yayinda saliha taci gaba da cewa"shi kuma yaya dake zagin ki ai kansa ya zaga ba kowa ba"
  Nn ta samu ta rarrashe ta har ta daina kuka,snn ta rubuta abinda suke so ta kaiwa mama ta basu kud'i suka tafi kasuwa.


Guraren qarfe 3 mohd ya dawo shi kad'ai ba tare da kowa ba.
  6angaren sa ya nufa yana bud'e 6angaren wani  qamshin dad'i ya daki hancinsa ya kuma ga komai tas tas very neat ba kmr yanda ake gyra masa d'aki ba, dmn har bathroom ya duba bai ga matsalar komai ba sae ma wani  qyalli da yake ,
ya fito ya durqusa tare da d'ora d'an yatsansa akan tiles ya shafo ba wani  datti,
 har ransa yaji dad'in gyaran ya kuma qudiri kyauta ga wanda yayi gyaran,don yauce rnr farko da ya ta6a samun d'akin sa hundred percent .

Sae bayan qarfe hud'u su Rynt suka shigo 6angaren su Ameera wad'an da dama tuni sun dawo da kasuwa suna can 6angaren su saliha zamansu.
  Mohd suka samu jingine a jikin motar sa yana waya wanda kallo d'aya zaka yi masa kasan da masoyiyar sa yake waya.
  Gaida shi sukayi ya d'aga musu hannu kawai, bayan sun d'an wuce saliha ke cewa"waeh!na miki murna kin huta da bala'in sa yau"
  Cikin rashin fahimta Rynt tace" ko meyasa"sbd yana waya ne da masoyiyar sa Anti malika
da yake mutuwar so,wacce baya samun suyi waya kullum sbd aikinsa da kuma yanayin karatun ta shiyasa duk rnr da yayi waya da ita tofa bazai yi masifa a rnr ba,,Rynt ta girgiza kanta tare da fad'in"hm mugun gaye ashe yana soyayya har wae ma kuka sani"
 tayi mgnr ne a ranta ashe ta fito
Har Saliha ke cewa"wa! ai ba wanda ya sani koni qanwarta qawata ce sosai a school shiyasa na san komai,dmn ma akanta yayi tafiyar nn zuwa UK don tayata murnar kammala karatun ta shine ya jirata suka dawo tare wanda inshaAllah mun kusa shan biki sbd tuni ita yake jira.
    "Yayi Allah taimaka" cewar Rynt kafin take cewa
_"abin tausayi malika rnr aure mijinki gawa"_

Basu jima da shiga ba mohd ya shigo ya sami Ameera na saukowa ta fito daga d'akin umma yace"ke wa ya gyra min 6angarena "cikin inna inna na jin tsoron sa tace"bani bace wlh wnn yrnyr ce Rynt"
je kiramin ita"
ta tafi sae dad'i take ji yau kam fad'an bazai qare kanta ba.

 Rynt ta fito sanye da qaton hijab d'inta har qasa ,
ta same shi zaune kan dining har ya fara cin abinci.
   Taje kawai tayi masa tsaye tare da kauda kanta gefe ,ya d'ago fuskar sa a hnkli yana kallonta snn yace"kece kika gyra min d'akina wae?a taqaice tace"eh"
  Ya ta6e baki yace"hm abun mamaki a qauyen naku ke ke gyarawa sarkin garin ku d'aki ne?eh har ma da sarkin kd duk ni ke gyara musu d'aki,da sauri ya kalleta sbd su asalin en kd ne yasan agun inna taji, baqa ta masa kenan,yace"ke ina wasa dake ne? um um kaidai ka nemi na maka haka amma ni ba halina bane raina wanda ya kama girmansa,d'an fari da ido yayi sae kuma yayi murmushi yace"to naji a wuce gun ga wnn ladan gyara min 6angare na da kikayi,Rynt ta kalli kud'in da ya ajiye gabanta zasuyi 20k tace"nayi dan Allah ne ba don wani  abu ba"
 Eh na sani ai kyauta ce na baki.... Kyautar ce bana so ,ya d'ago da d'an mamakinsa sae kuma ya basar yace"to me kike so? Har tayi niyyar saka mai wata maganar sae kuma ta fasa ,tace"waya nake son nayi da inna"
  Ga mamakinta sae ya ciro waya a aljihunsa ya kira mata inna ya bata, bata san lokacinda murmushi ya su6uce mata ba ta kar6i wyr ta kwasa da gudu zuwa d'aki, mohd kuwa binta yayi da shu'umin murushi yayinda a ransa yake mamakin raina sa da tayi.

Duk abin nn da suke Abba na kallon su sae ya musu wata fahimta ta daban wacce tasa yaji dad'i har ransa,
da saukowa zai yi amma ya fasa ya juya zuwa d'akin umma ,
ganin yanda yake murmushi yasa ita ma ta shiga murmushi tace"yadai Alhj?
Sai da ya zauna snn yace"zauna tukun"
nn kusa dashi ta xauna.
  Yayi gyran murya snn ya fara da cewa" haqiqa tun zuwan Rynt a gidan nn na yaba da hnklnta da kuma natsuwarta har hakan yasa na kwad'aitu da son ace  ta zamo cikin wnn family namu ma'ana ta kasance suruka a gidan nn mata ga mohd.


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN  BARSHI BA! ```🔮









          🔮🔮🔮
_*page*_ ```21```

Amma Alhj Allah ya isa tsakanin mu dakai don wnn cutuwa ce wlh!
  Cikin nuna fushi Abba ya nuna ta da yatsa yace"wlh Rabi'a ki kiyaye ni da banzan kalaman nn naki dake shirin janyo miki mutuwar aurenki!
  Gama fad'ar haka ya tafi kmr wanda zai tashi sama.
   Umma kuwà ta bishi da kallo ta6e da baki tace"indai wnn kalmar ce ba yau na saba jinta a bakinka ba bare ta tayar min da hnkli,snn ta kalli mohd da ya shiga cikin tsañanin tashin hnkli tace"kaga kwantar da hnklinka aurenka da malika kmr anyi an gama kuma baza ka auri wnn er qauyen ba indai ina numfashi a doron qasa,kmr wanda zai yi kuka yace"umma ta yaya kike ganin hkn zai yiyu bayan kinaji Abba rantsuwaa yayi kawai ma umma dan Allah ki daina sa bakin ki a zancen nn sbd ko kad'an banji dad'in yanda Abba ya sako rabuwar aure a zancen nn ba .... Yo ai ba yau ya fara ba kuma dan ya rantse sae me! Kaidai tashi ka tafi kawai ai er iskar yrnyr zata dawo daga islamiyya ta sameni.....Aa ki barni da ita kawai umma ni nasan yanda zanyi da ita....ai da ka barni da ita wlh...No umma bana son kwata kwata wani  abu ya had'aki da ita ne bare ta raina ki.
 
6:00pm
Rynt ce tafe kan hnyr dawowa islamiyya ita da munir sae er fira suke mai cike da nishad'i yayinda Rynt ke d'an duba kan titi ko zata hango napep.

 Kmr daga sama ta hango motar man tafe ya zo gab dasu ya tsaya kmr mai shirin taka musu qafafu don tsirif ya rage har sae da sukayi saurin ja da baya.
 Dukkan su da mugun kallo ya fito yana binsu dashi,yace da Rynt shiga mota"kallon sa ta tsaya yayi ya daka mata tsawa yace"shiga mota nace!cikin 6acin rai taje ta shiga motar ya zagaya ya shiga yaja motar a tsiyace had'e da bazawa munir qura.

Tafiya yayi da ita mai nisa snn ya samu guri ya parker ya kalli Rynt da tun lokacinda yaja motar gabanta ke dukan tara tara kaddai ace ya gane ko ita wace ce,yace"oya cire wnn baqin abun dake kan fuskar ki magana nake son zanyi dake"
   Ba musu ta yaye niqab d'inta ba tare da ta kalle sa ba.
Sae da yakai hannu ya d'ago fuskarta yana kallonta shaye da toka snn yace"abu zan nema agunki wanda ban ta6a nema agun kowa ba wato alfarma, alfarmar itace ina son dan Allah idan Abbana ya kiraki ya tambaye ki ko kina sona kice masa A'a shine kawai ni kuma idan kika min haka nayi miki alqawarin duk wani  abu da kike so a rayuwa ki tambaye ni zan miki shi koma mene ne kuwa"amma wlh kar ganin na had'aki da Allah ki raina min da wayo dmn duk kika yi gigin amincewa buqatar Abbana sae dai a nemi wata bake ba!
  Manyan idanuwanta  farare tas take ci gaba da kallon shi dasu snn ta ta6e baki tace"ai sae ka fayyace min komai ta yanda zan fhmta"
  Mugun kallo ya watsa mata yace"daqiqiyar inace ke da bazaki fhmta ba ,da Allah ni ftr min daga mota kuma wlh ki tabbatar kinyi abinda na saki!
  Ba musu kuwa ta fita motar don yanda taga yanayinsa ko tura ta zai iya yi ta fad'i, sae dai da gani akwai mgnr da takeyi a ranta haka kuma akwai nazarin da takeyi shi kuma mohd har lokacin kallon takaici yake mata snn yaja motarsa a tsiyace ya bar gurin.

  Da qyar Rynt taga ta sami napep sbd yanayin anguwar da ba kwaramniya bare abin hawa ya yawaita.
  Nazari take yi kam har ta isa gida ko kuma nace har akayi sllr isha'i bata daina nazarin ba yayinda tuni zuciyarta ta ganar da ita abinda ke shirin faruwa sae dai taqi bawa kanta damar amincewa da hkn har sae Abba ya kirata tukun taji koma mene ne.

Tana gama cin abinci Abba ya aiko Ameera yana son ganin ta.
  Taje ta same shi shi kadai zaune a falo.
  Ta nemi guri a qasa ta zauna ta kuma gaida shi cikin ladabi kmr koyaushe.
   Cikin sakin fuska ya amsa snn yayi gyran murya yace"Rynt haqiqa duk mutumin da ya zauna dake zai yi sha'awar kyawawan halayenki da kuma d'abiunki,a dalilin hakane ma yasa nayi sha'awar had'aki aure da mohd,amma kuma ba dole sae idan kina ra'ayi kuma dan Allah kar ki 6oye komai a ranki,dmn ita rayuwar aure wata sabuwar rayuwace da ta banbanta da kowace rayuwa wacce dad'inta ka auri wanda kake so yake sonka, shiyasa nake son ki snr dani gskyr abinda ke ranki ma'ana idan ba kya ra'ayin auren ki da mohd kar kiji shayin komai ki snr dani idan kuma kina ra'ayi sae dai nace Alhmdh dmn zanfi kowa farin ciki da haka.
  Tun farkon fara zancen sa ba qaramin girgiza Rynt tayi da jin zancen ba amma sae ta dake bata yarda ya fhmci halinda take ciki ba.
  Bata son mohd bata kuma jin zata soshi har abada!amma kuma ko don ta d'auki fansarta a sauqaqe zaisa ta amince da aurensa to kuma ya zata ce da yaya munir dake matuqar son ya aureta.
  Duk a cikin ranta take wnn tunanin ,Abba ya katse ta da cewa ke nake saurare Rynt ,sae da ta qara sadda kanta qasa snn tace"na Amince Abba zan aure shi"Abba yace "kin tabbatar Rynt ba cutar kanki kikayi ba? eh wlh Abba har raina na amince.
  Wani  irin dad'i Abba yaji har ransa, yace"Allah yayi miki albarka Rynt, ya kuma sa ki gama lfy da duniya"da qyar ta iya cewa amin kan kukan da ke qoqarin zo mata sbd tuna baffanta da tayi da kusan kullum sae yayi mata irin addu'ar nn.

Koda ta koma d'aki ba kowa sae tayi kwance abinta tana ta kukan tuna Baffanta har sae da tayi mai isarta snn ta tashi tana tunanin me zai faru idan mohd yaji ta amince da buqatar abbanshi ko ita ma kasheta zai yi kmr yanda ya kashe mata Abbanta.


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[ 1/8/2017]
🔮```BAZAN  BARSHI BA!```🔮









          🔮🔮🔮
_*page*_ *```22```*
Don tasan a rashin imaninsa zai iya aiwatar da abinda ma yafi haka in akwai, amma kuma bari taga shin me yake nufi da sae dai wata ba ita ba.
   Abba kuwa  da mohd har umma ba wanda ya kira cikin su bare ya snr dasu yanda sukayi shi da Rynt kawai ya yanke hukunci sae inna ta dawo su yanke shawara shi da ita asa rnr aure.

washe gari hnklinta a kwance  tayi shirinta na islamiyya ta fita.

Ko minti 5 batayi da fita ba inna ta dawo daga qauye kuma a nn gidan ta sauka sae murna ake da dawowar ta yayinda ita kuma ta matsu taga Rynt nn Abba ke snr da ita ai ta tafi islamiyya.


Bayan inna taci abinci ta d'an huta Abba ya shiga snr da ita shawarar da ya yanke kan zancen had'a mohd aure da Rynt har yanda sukayi da Abban malika duk sae da ya snr da ita.
   Sosai inna tayi murna ba kad'an ba haka kuma itama bata bada goyon bayan mohd ya auri malika ba wanda duk zancen nn da suke yana kunnen hjyrsu mohd wacce tana gama sauraren kaf abinda suka tsara ta koma d'aki cike da masifa ta kira mohd a waya ta snr dashi  tace"ga irinta nn sae da nace kbr ni da yarinyar nn ni nasan yanda zanyi da ita wanda ko da kuskure baza ta yarda ta amince da zancen Abbanka ba wlh, amma kace a'a  wae kar ta rainani ,raini duk ya wuce ace kmrta  baqauya er matsiyata ta had'a surukuta dani,mohd yace"yanzu umma kina nufin duk yanda nayi da ita  ta amince da buqatar Abba? Hm!na nawa kuma gashi har sun tsara anjima da dare iyayenka zasu tafi gidan inna asa ranar aurenku!ai wlh kayi wa kanka!don yanzu sae kasan yanda zakayi ka ftr da kanka ko kuma ka nemi wata uwar don muddin ka rasa mafita har takai ga an aura ma ita tofa bani ba kai tunda tun farko sae da nace kabarni da ita kaqi.
  Daga haka ta katse wayar sae huci take
tace"in shi mai hnkli ne ko islamiyya baxata dawo ba sae dai wata ba ita ba amma bari nasa ido naga ko dabara ta tayi!in yaso ni kuma na tayasa da wani  aikin ta yanda baza ace dasa hannun mu kan 6acewar ta ba.

Mohd kuwa hjyrsa na kashe waya ya rasa ta inda zai sa kansa kan baqin ciki da kuma tunanin hukuncin da zai yiwa Rynt.
     Ya zama dole yaje ya jirata kan hnyrsu ta islamiya don yau sae ta fad'i wanda ya aiketa .

Yana fita da motar sa yayi kici6is da Malika ta parker motar ta ta fito, dole ya tsaida tasa motar ya fito yaje gab da ita ya tsaya yana mata wani  irin kallo,ita kuwa ta wani  langwa6ar da kanta snn tace"my man wai ya ake ciki ne tun jiya da mukayi waya naji shiru har yau "
yace"to shine zaki wani biyo ni har gida da kuma wnn banzan dressing d'inki salon Abbana ya ganki yace bakida kamun kai kuma,in yaso Komai ya qara cakud'e mana! Kayi haquri my man wlh banda wasu kaya sae ire iren su kuma ka sani,to me ya hana ki kirani a waya muyi magana? Ina mgnr zata yiyu a waya nida kwata kwata daren jiya ban samu nayi bacci ba,amma malika kinsan bana son damuwa koma mene ne ai zanje na sameki har gida,kayi haquri na damu ne sosai ,tayi mgnr cike da qwallah tap a idonta, yayi saurin cewa"shikenan kar kiyi kuka gaya min me kike so yanzu?so nake ka gaya min abinda ake ciki ,ajiyar zuciya ya sauke snn yace"wnn yrnyr ta lalata mana komai don ta amince da buqatar Abba snn kuma Abbana har yanzu dai yana kan bakarsa na bazan aureki ba,amma kar ki damu zan shawo kan matsalar komai inshaAllah ,matsalata d'aya yanzu shine anjima za'a sa rnr aurena da wnn yrnr shiyasa at all kaina ya kunce bansan ma wane hukunci zan yanke ba, ga umma ta sani cikin wata chakwakiyar wae bani ba ita idan ban nemo mafita ba har akayi aurena da wnn yrnyr.... Wae da kana nufin zaka yarda ayi auren ne to! Malika uba ba abin wasa bane idan kuma ya yanke hukunci ba yanda za'ayi kuma ya rantse cewa in ta amince tofa shikenan ba fashi aurena da ita, but my man be wise mana,idan ba yrnyr ai ba auren shike nn dole Abba ya haqura, aikin hnkli dai malika ina mai gaya miki 6atar wnn yrnyr tmkr tsinuwace na jawa kaina don dole Abba yasan nine, kawai dai zan aureta amma na d'an wani lokaci .....Wlh! my man bari kaji in gaya ma ba maccen da ta isa ta aure ka bayan ni don ka ma daina wnn sa6on!daga haka taja motar ta a tsiyace ta bar gurin.
  Har  zai shiga mota sae ga kiran Abba yana son ganin shi,dole ya juya ya tafi ga kiran Abba.

Yau Rynt ita kad'aice  kan hnyr dawowa islamiya sbd da safe munir bai cika zowa ba sae da yamma.
  Tana cikin tafiyar ta har takai titi zata tsaida napep sae ga wata tsaleliyar mota ta tsaya a gabanta.
  Malika ce ta fito daga motar taje gab da Rynt tare da kai hannu ta yaye mata niqabi,nn malika ta yamutse fuska kmr wacce taga kashi tace"hm rainin wayo wai kece ke shirin shiga tsakani na da my man,ta nuna ta da yatsa snn taci gaba da cewa" lemmi tell u 1 thing  ruwa ba sa'ar kwando bane  haka kuma ramin kura ba gurin shigar akuya bane,a bisa yanda ma na fhmta kwata kwata tsabar talauci ne ke d'ibar ki da haka zan taimaka miki na baki check ki rubuta duk iya kud'in da kike so after that ki sani inda dare ya miki ma'ana kwata kwata ki 6acewa duniyar mu ki tafi can taku duniyar ta matsiyata wnn umarni ne dmn in kika sake kika dawo gare mu wlh sunanki gawa!
gama fad'ar haka ta zaro cheque da biro ta miqawa Rynt ,sae kuma tace "koda yake nasan duhun kai na tattare dake bare har ki iya rubuta wani  abu nn ta rubuta million biyar snn ta ce ungo kud'i ne masu yawan gaske da nsn ko ubanki bai ta6a riqa irin su ba bare ke!
  Kallonta kawai Rynt keyi wacce batada niyar kai hannu  bare har ta kar6i cheque d'in .
  Malika tace"gwanda ki kar6a don wlh kanki kika yiwa idan baki kar6a ba sbd ynzu hk ni a shirye nake da nasa a yanke miki hukuncin da yake dai dai a guna.
  Komai Rynt bata ce mata ba sae ma ra6awa tayi ta gefenta zata wuce ,sae kawai ta sami kanta da ganin qarti  zagaye da ita.



Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[ 1/9/2017]
 🔮```BAZAN  BARSHI BA!```🔮









          🔮🔮🔮
_*page*_ *```23```*
wayar malika ce tayi qara koda ta duba Man ne mai kiran,
 ta d'aga wyr sae jin tayi yace"malika kibar er mutane ta wuce"
tace "my man.... sae taga ya katse kiran.
  Kallon mutanen ta tayi tace"ku barta ta tafi.
 Bayan Rynt ta wuce suma mutanen nata ta basu izinin wucewa snn ta shiga rarraba ido ta inda zata hango man dmn tasan tabbas yana gurin.
  Kmr daga sama tana juyawa ta ganshi a bayanta kallonta yake da mamakin yanda akayi tasan Rynt har tasan makarantar su sae kuma nn take ya basar sbd sanin bincike ba abinda baiyi yace"daso kikayi mahaifina ya tsine min ko kuwa?my man.....No kawai kar ki sake min shisshigi irin wnn bana so!
  Daga hk yayi tafiyar sa ya barta.

Hjyr su pretty kuwa sae sa ido take taga ko Rynt zata dawo amma shiru haka Man bai dawo gidan ba.
   Wasa wasa kuwa har yamma ba Rynt ba labarinta, dad'i taji sosai har ranta don ganin take dabarar tace  tayi.
  Taja Ameera zuwa d'aki wae ta rubuta takarda a cewar Rynt ce ta rubuta  ta yanda idan Abba ya gani ba zai zarge su ba haka kuma ba zaisa neman Rynt ba.
  umma ce ke fad'in abinda za'a sa Ameera na rubutawa har suka gama tace "yi maza kije kisa a qarqashin pillown ta kina jin shigowar Abbanku kije masa cikin kuka a cewar kin nemi duk gwalgwalanki ki ransa har ma kud'in provision dinki da ya baki jiya da dare ni kuma zan fito da nawa tuggun ta yanda koshi waye bai isa ya gane plan bane wlh,yi maza jeki........ Ameera!Ameera! kiran ya fito daga Abba umma tayi saurin kar6ar takardar dake hannun Ameera ta tura mata cikin zane,nn suka ji knocking umma ta bud'e qofa Abba ya kalli Ameera yace"ke je ki ftr da kayan Rynt za'a maida su gidan inna ne, umma tace"ina ita Rynt d'in da baza ta ftr ba sae Ameera? Da mamaki Abba yace"ai Rynt bata dawo gidan nn ba tun safe sbd ana tashi daga makaranta inna ta aika Nasir ya d'auko ta, yanxu haka ma tana gidan inna har ma taje islamiyyar yamma ta dawo.
   wani  irin baqin ciki umma taji tace"ai sae tazo da kanta ta ftr da kayan tunda Ameera ba boyar gidansu bace"tsawa ya dakawa Ameera yace "ke je ftr min da kayan Rynt nace"
Ameera ta wuce kmr xata yi kuka,ya kalli umma yace"keda kanki wae kike lalata rayuwr 'ya'yanki Allah dai ya shirye ki".
   Abba ya fita ya bar umma cikin takaici da jin haushin mohd.

7:00pm
Mohd  ne ya shigo gidan inna,inna ta fito daga kitchen kenan tana ganin mohd ta washe baki tace"ka ganmu muna can nida baaba hurera da Rynh muna had'awa iyayenka liyafar da xasu ci idan sunxo sa rnr aurenku kaida Rynh.
  Kauda kansa gefe yayi dan shi ko sunan Rynt baya son ji.
  Inna tace"akawo maka naka abinci? Aa inna magana nazo muyi, inna ta washe baki tace"ayyo to bari na kira ma Rynh d'in"ransa ne ya qara 6aci yace"na mata me ni dake zanyi magana"
   Washe da baki inna ta nemi guri ta zauna shima haka tace "ina jinka maigidana angon Rynh"
 Ba yanda ya iya hk ya dake ya basar awa bai ji ta ba yace "inna so nake dan Allah ki roqa min Abba ya barni na auri malika.... Inna ta fiddo ido waje tace"yau naga shashashan yaro ita Rynh d'in fa? Ai inna ba ina nufin wani abu a kanta ba kawai dai so nake Abba ya barni harda malika d'in na had'a na aura sbd gsky ni ita ce za6ina.... To bakaji da kyau ba wnn er marasa mutunci tayi kad'an ta shigo cikin dangin mu ta watsa mana mugun iri,dan Allah inna ki saurare ni fad'in ra'ayin Abbanta ba shine rashin mutunci ba ai ,kaga mohd indai wnn maganar ce zaka tamin gwanda ka tashi kayi tafiyarka don ba saurarar ka zanyi ba,cikin damuwa sosai yake kallon inna kmr zai mata kuka yace"inna wae dan Allah meye dad'in aure ba ka auri wanda kake so yake sonka ba... Yo mu kenan duk kana nufin ba muji dad'in aure ba muda duk had'in iyayene amma muke zaune qalau har Allah ya d'auki ran marigayi,amma inna daa da yanzu ba d'aya bane kin sani...ina ko zasu zama d'aya tunda daa iyaye ke za6awar 'ya'yansu mata kuma ba'a jin kansu amma kai yanzu gashi kazo min da zancen za6in ka kake son ka aura mu daa har akwai wani  za6i da ya wuce na iyaye.
  Nidai inna kiyi haquri  ki roqa min Abba kafin su shiga meeting d'in nn....yo kana nufin za'a had'a baki dani ne a cuci Rynh ,haba inna aini ake shirin cuta shin ba kya jin tausayi nane a matsayina na jikan ki ace duk tsawon shekarunda na d'auka a matsayina na lafiyayye banyi aure ba ina nn ina jiran malika ta kammala karatu se kuma ace bazan aureta ba,fisabilillah inna ya kamata a duba min,ya qarashe mgnr ne ta yanda duk wanda ke saurarensa dole ya tausaya masa,inna ta sauke ajiyar zcy tace"shikenan mohammadu zanyi magana da mahafin naka amma idan bai amince ba tofa sae dai ka haqura don bazan tilasta masa ba.
  Ba komai inna nagode ya tashi zai fita tace"abincin ka fa?
sae anjima idan na dawo, to a dawo fly.
  Daga haka ya fita ita kuma ta koma kitchen.


Sae tara da rabi mohd ya dawo gidan ya samu Abba a nn falo shida inna sauran iyaye kuwa an kammala meeting d'in sun tafi.
  Cike da ladabi ya gaida Abbanshi  ya juya zai fita Abba yace"zauna dama kai nake jira muyi magana.
  Bayan ya zauna Abba ke cewa naji na kuma amince da buqatar ka amma fa ka sani ya zama dole kayi adalci a tsakanin su snn bayan aure idan term ya zagayo zaka saka Rynt a makaranta yayinda nauyin karatun ta zai kasance a qarqashin ka.
  Abinda ya rage yanzu shine ka snr da iyayen malika zancen auren naku wanda za'a d'aura a qarshen wnn satin rnr juma'a idan kuma basu shiryi hakan ba su suka sani don baza a fasa naka dana Rynt ba.
  Daga haka Abba ya tashi ya fita mohd ya d'ago ya kalli inna tare da fad'in nagode inna.

Yana fita gidan inna bai zarce koina ba sae gidan su malika ya snr da ita Abban sa ya amince suyi aure amma cikin satin nn za'ayi komai dad'i taji sosai har da su hugging d'inshi wacce kwata kwata bai nuna mata still auren Rynh na kanshi ba,ita kuwa ta d'auka an fita zancen Rynt.

Sae shirye shirye ake tayi a cikin satin har ma ya zamo inna ta hana Rynt fita ko ina wae ta shiga lalle kenan saliha kuwa tarewa ma tayi a gidan, Rynt kuwa sae kallon su take tana tunanin hln da munir zai shiga idan yaji.

6angaren hjyr mohd kuwa tun daga rnr ko gaisuwar mohd bata amsawa wae a cewar fushi take dashi tunda yaqi neman mafita duk da cewa wani  6angaren taji dad'i jin cewa harda malika zai aura.

Rnr juma'a aka d'aura aure akayi walima  6angaren su malika kam shagugula akayi ba kad'an ba.
  Da dare za'a kai Rynt sae kuka take kan rabuwa da inna haka ma inna kukan take kmr baza su qara had'uwa ba.


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[ 1/10/2017]
 🔮```BAZAN  BARSHI BA!```🔮









          🔮🔮🔮
_*page*_ *```24```*
Bayan ankaita kowa ya watse ita kad'ai a d'aki sae autar su saliha da suke kira da mami.
  Ambar mata ita ne sbd ita Rynh d'in ta nemi haka sbd mugun tsoron bacci ita kad'ai take ji.

6angaren su mohd kuwa bayan an kawo amarya suka tsiri wani  party maxa da mata sae shagali suke duk Rynt ta kasa samun baccin kirki sbd hayaniyar su hkn yasa ta tashi ta d'auro arwala ta shiga yin nafilfili yayinda autar mama keta sharar baccinta.

Sae kusan qarfe d'aya da rabi en party suka watse amma hkn bai hana mohd da malika suka sha amarcin su ba.

Washe gari sae da Rynt tayiwa mami wanka snn ita ma tayi nata wnkn.
  Ta gama shiri kenan taji an turo qofa saliha ta shigo mami taje da gudu ta rungumeta Rynt kuwa tazo cikin sakin fuska saliha tace "amarsu ta ango ya amarci?murmushi kawai Rnyt tayi snn tace"nidai yasu umma? Lafiyar su qalau tana ma gaida ke ,ta fad'i hkne tare da ajiye basket d'inda ke hannunta tace"ga break fast inji umma,Rynt tace"mun gode"
Byn sun zauna saliha
ke cewa yaya fa?Rynt tayi kmr ma bata ji ta ba tace"wai shin saliha yaushe ne kika ce zaku koma makaranta?
  Saliha tace "kinsan na gaya miki cikin satin nn hutun mu ya qare sae aurenku yazo ya tsaida mu amma yanzu rnr lahadin nn zamu koma,Rynt tayi  shiru can tace"to yaushe ne ake saka sabbin d'auka? Da zarar mun tafi yanzu munyi third term muka dawo gida mukayi hutu se mu koma  first term to a lokacin ne ake kai sabbin d'auka sbd anyi canjin aji,yanzu za'ayi kmr wata nawa kafin haka don ni tunda inna tamin albishir d'in bokon nn na qagu naga na fara boko nn wlh,saliha tace"hm boko ko wahala ,komai wahalar sa zan so nayi saliha sbd a rayuwa ba abinda ke birge ni kmr ilimi, gskyr ki ne Rynt sbd ba abinda ya kai ilimi dad'i.....qofa suka ga an tura koda suka duba Ameera ce yamutse da fuska tace da saliha"wae ke a nn kika shigo, nikam ki sameni 6angaren anti malika, saliha tace"to sae idan zamu koma xaki ganni"
nn Ameera ta ka6a kai ta fita,Rynt tace"ai da kin bita kun tafi d'in"saliha ta ta6e baki  tace"um um sae idan zamu koma"
 Rynt bata sake cewa komai ba sae zama sukayi zasu ci abinci sae ga wani saqon  abinci daga gurin inna, sosai Rynt taji dad'i sbd abincin da take mugun so ne inna ta aiko mata.

Ameera kuwa koda taje 6angaren su malika ko bud'e qofa basuyi ba sae da tayi ta fmn danna door bell snn sae can ta samu aka bud'e .
  Man ne da malika rungume a jikinshi da gani yanzu ne tashin su don malika farin bedsheets ma ne a jikinta man kuwa yana sanye da white bathrobe yayinda fuskar sa take d'aure tamau yana kallon Ameera yace"lfy zaki mana wnn sammako hk?kafin Ameera tace"komai malika tace"haba my man ba qanwar ka bace? Ko qanwa tace sae tazo ta takura ni, kiss ta d'ora masa a gefen fuska tace"kuma fa tayi laifi amma ayi haquri ta shigo ta zauna sae muje muyi wanka ko,lumshe mata ido yayi alamar suje d'in ,ba tare da kowanen su yace da Ameera ta shiga ta zauna ba suka juya zasu tafi, malika ta kalli mohd tace"my man me xai hana ta d'aura mana break fast kafin mu fito don wlh yunwa nake ji"ba musu ya juyo ya kalli Ameera da bata riga ta shigo ba yace"ke shigo kije kitchen ki d'aura mana girki"
   Ameera ta shigo tare da rufe qofa tana ji kmr ta fasa ihu don ta tsani aiki ba kad'an ba.
  Mohd kuwa suna shiga d'aki malika ta jefar da bedsheets din jikinta ta dawo nakedness,hm mohd sae d'aukar ta yayi suka je toilet.

Bayan sati 1 da faruwar haka tuni su saliha sun koma school ,mohd da malika kuwa sae cin amarcin suke inda ko sau d'aya mohd bai ta6a leqa 6angaren Rynt ba.
 Sam Rynt bata damu ba wacce har yanzu  inna na aiko mata abinci,kuma bata da wani kad'ai ci sbd still mami na nn da kullum tare suke cin abincin su suna kallo.

Yau tun da safe da suka tashi mami keta kuka ita gida take son zuwa gun ummarta duk Rynt ta shiga damuwa tayi rarrashi har ta gaji amma fafau taqi shiru ita sae taje taga mamarta.
   Ba yanda Rynt ta iya dole ta shirya dmn kaita gida tunda ba waya ne da ita ba bare ta kira azo a d'auke ta kuma ko banza tana son zuwa gida don zaman banzan nn ya isheta tana son komawa islamiyya.
 Hijabinta har qasa ta zuba ta jawo hannun mami suka fito suna kawowa harabar gidan ta sami kanta da mamakin ganin mohd zaune kan resting chair shida wani mai kama dashi sak har ma baka babance su,sam mami bata kula dasu ba sae kuka ta ajiye wae Rynt ta d'auketa ita bacci take ji,nn Rynt ta d'auke ta tare da d'aura ta kan kafad'a sae jin tayi tace "lah anti ga yaya da anti amarya sun fito"a hnkali Rynt ta juya bayanta don ganin wad'anda mami ke nufi sae kawai taga mohd shida malika ta kalli gun resting chair taga still wad'an can su biyun suna nn zaune abinsu suna fira ga kuma mohd shida malika tsaye mutum uku kenan fa iri d'aya nn kan Rynt ya d'aure sosai tana tunanin shin dama su en uku ne.

Kuyi hqr da wnn.

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[ 1/11/2017]
 🔮```BAZAN  BARSHI BA!```🔮









          🔮🔮🔮
_*page*_ *```25```*
Ita tasan a qauyen su akwai en uku amma biyu ke kama da juna se d'ayar ta fita daban amma su wad'anan su duka uku kama suke har ba'a banbance su........Malika ce ta katse ta da tunanin da take da tace"my man me wnn abar ta shigo yi mana a gida!
fita batun malika yayi  yace da Rynt "ina zaki tafi?tace"gida mana"wa kika tambaya?ta6e baki tayi tace"tambaya"sae kawai ta juyawar ta zata wuce mami ta qwace daga jikinta ta tafi da gudu gun wad'an can mutane dake fira,man kuwa ya dakawa Rynt tsawa yace  "kar ki kuskura ki qara ko tako d'aya!Rynt ta juyo shaye da toka tare da watsa masa idanuwanta a cikin nashi kafin yace komai
Malika ta riga shi da cewa "wae bala'i ni ban gane ba!ko kana nufin ka aureta d'in!yace"wace magana ce kuma wnn koma daga ciki ki jirani,tace"kam bala'i har akwai wata mace da ta isa!hm!ai kuwa yanzun nn zaki bar duniyar nn baki shirya ba!nn ta duqa cikin zafin nama ta ciro takalminta mai d'an karan tsini tayi kan Rynt zata doka mata a ka,mohd ya riqe takalmin ya kuma riqe malika dake fizge fizge zata qwace kanta,yace"meye haka ne malika aurenta dake kaina dashi da babu fa duk d'aya don ba kulata zanyi ba kinsani, cikin masifa tace"wlh koma yaya ne bazata rayu a matsayin mtr ka ba don sae na rabata da duniyar nn idan har baka sake ta ba,,a natse yace be wise mana malika na gaya miki fa aurena da ita na d'an wani  lokaci ne kuma kinsan halina duk abinda nace hk ne koda sama da qasa zasu had'e kuwa,
 ya fad'i hakane tare da rungume ta a qirjinsa,ita ko ta fashe masa da kukan shagwa6a tace"to kasan yanda zakayi da ita don wlh bana son na qara ganinta a gidan nn!to naji daina kukan ,nn yajata yana rarrashi ya shigar da ita cikin gida ya dawo.
  Ya samu Rynt bata nn da ita har mami, kenan ta fita yayi shu'umin murmushi snn ya qarasa gurin en uwanshi, yace"ina wnn yrnyr take? D'ayan yace " ta fita yanzu but me yake faruwa ne kaida matn naka? Yace"is nothing ku tashi muje kuyi sallama da malika d'in sbd fita zamuyi yanzu zuwa gaida su Abba,nn suka tashi suka shiga daga cikin gidan.

Rynt kuwa da qyar ta sami napep sbd  yanayin anguwar ,
basu zarce koina ba sae gidan su man suna shiga suka had'u da Abba zai fita, Rynt ta durqusa da ladabi tana gaida shi, fuskar shi wasae yake amsa mata gaisuwar  snn ya dafa kan mami yace"autar mama ya sabuwar anguwar taku? ba dad'i kullum mu kad'ai a cikin gida daga ni sae anti ba mai kawo mana fira kuma mu kad'ai ke baccin mu yaya baya zuwa taya mu,kai Abba gabad'aya ma tunda mukaje gidan sae yau kad'ai da zamu fita naga yaya sun fito shida anti amarya  zasu tafi anguwa har mai wae Anti amarya ta tashi du......Rynt ce tayi saurin kwa6ar ta Abba kuwa ya shiga jinjina kai yace"lallai yau zai zo ya same ni a gidan  nn"
ya sake cewa "shiga daga ciki Rynh zai zo ya sameni ne yau"

6angaren su saliha suka tafi wanda kafin su shiga sae da Rynt ta kwa6i mami kan kar ta sake irin srtn nn. 
     Murna sosai umman saliha tayi da ganin su,
 sae dai Rnyt bata wani  jima sosai ba tace"zata je ta kaida hjyr su pretty da kuma sauran mutanen gidan snn se ta tafi gidan inna.

Haka ko akayi ta tafi kowane 6angare ta kaida su sae dai 6angaren hjyr pretty ba irin sallamar da bata yi ba aka qi amsa mata bayan kuwa pretty da hjy suna jinta sukayi banza da ita, tayi zama har ta gaji da qarshe tayi tafiyarta.


Mohd kuwa suna shigowa gidan shida malika ya had'u da fushin Abba don yayi masa fad'a sosai ,mohd ya cika fam dan duk d'aukar sa Rynt ce ta kawo qarar shi,don har quduri ya d'auka a ransa sae yayi maganin ta idan suka koma gida,don ba abinda ya qara 6ata masa rai irin yanda Abba ya tilasta shi kan cewa  duk safiya dole sae yaje duba lfyr Rynt ko ba ita keda duty ba kuwa.


Rynt kuwa tana zuwa gidan inna ta had'u da motar man a nn harabar gidan bata damu ba ta shiga abinta cikin gidan ta same su su biyu suna ta fira da inñà ta gaishe su shaye da toka dan ta d'auka ko man na cikin su ,snn ta gaida inna cikin sakin fuska yayinda ta washe haqora tana fad'in marhabin lale da Rynh nn ta shiga tmbyr lfyr gidan su Rynt tace"duk lfy qalau inna tace" ina er tafiyar ki mami? Tana can gun mama wae sae gobe ko zata dawo guna,ayyo to inace lafiya qalau kuke zaune da abokiyar zaman taki ko?lfy qalau inna ina baaba hurera ?ai baaba hurera taje qauye bikin wata jikarta ta barni ni kad'ai cikin kewa, Rynt tace" Allah sarki yaushe zata dawo?inna ta d'aga kai sama tana tunani can tace"yauwa inaga gobe ne don rnr litanin tace min zata dawo,Rynt tayi shiru tana ji kmr  tayi zamanta har sae gobe ta koma dai dai an maida mata mami don dai baccin nn ita kad'ai take yiwa tunani.....tunaninta ya katse da jin wad'anda ta samu sunà sallàma da innà yayinda inna keta zuba musu albarka tana godiya kan irin damen kud'in da suka ajiye mata ta bisu da rakiya tana fad'in"har zaku tafi to Allah kiyaye hanya sae kuma kun sake zagayo mu duk da dai ba nan kusa ba kam tunda ba zowa kuke ba sae da lalura ,d'ayan yace"to inna kinsan yanayin aikin mu ne sae a hnkli daga haka Rynt ta daina jiyo zancen su sbd sun mata nisa.

Bayan inna ta dawo ta d'auki kud'in da suka ajiye mata washe da baki tace"kin gansu en albarka abokan haifuwar muhammadu ne dake zama qasashen turai tare da matansu.
  Rynt tace"en uku ne kenan inna? Eh ai en uku ne,tace am inna ya  naga motar maigidanki amma kuma baya cikin su?yo ai wad'an nn da kika gani maida abin wani  naka ne haka suka taso tun suna yara bakya banbance wnn abin wnn ne a tsakanin su sae dai idan kinsan ainihin mai shi don yanzu kinga sun taho  cikin motar muhammadu shi  kuma yana can cikin motar d'ayan su.
  Rynt tayi shiru yanzu kenan ya zatayi ta fhmci waye ya kashe mata mahaifi a cikin su ukku nn can ta d'ago a hnkli tace"inna hln yaushe ne rabon su da zowa nn qasar naji kince suna jimawa kafin suzo,inna tace "sosai kam suna jimawa don zasuyi shekara kafin su sake zowa amma a cikin wnn shekara kusan zuwan su uku kenan sbd bukukuwan da akayi tayi a dangi sbd ko nasiru da Fatima a cikin shekarar nn akayi bikin su kuma sunzo snn da za'ayi bikin zainaba ma sunxo wato wacce ke biwa nasiru inace kina jinta a bakin saliha,kuma ai kinga ma tazo bikin nn naku wacce tun daga bauci mijinta ya kawota akayi biki tare dashi snn suka koma.
  Nn inna ta kawo qarshen zancen, Rynt kuwa gabad'aya taji lissafinta ya kunce yayinda take ji a ranta bafa zata iya barin ko waye ba har sae ta d'au fansa amma kuma a cikin su ukkun nn taya zata san waye yaje qauyen su har ya kashe mata baffanta ko kisa na wulaqanci da rashin tausayi ,haqiqa ta yarda da qaddara amma baxata d'auki kisan mahaifinta a qaddara ba sbd ya shigo da gayya a cikin shi dmn da ba don reverse d'inda yayi kan mahaifinta ba da inshaAllah mahaifinta zai rayu shine abinda ke qara qona mata rai idan ta tuno da hkn......a cikin tunanin tane wani  6angaren zuciyarta ke bata shawara ta yanda xata sami mafitar gano waye a cikin su shine ta jure ta kasance mai kusanci da mohd sannu sannu har shima ya d'an fara sake mata da haka da haka zata gano waye a cikin su ta hnyr masa wata tambaya......inna ta katse ta da cewa "lfy Rnyh tun d'axu kinyi shiru kmr mai wani  tunani,a kafaice Rynt ta share en hawayenda suka zubo mata tace"ba komai inna kawai dama ina son muyi zancen komawa ta islamiyya ne ,inna tace"to Rynh ai mijin naki ya kamata ki tuntu6a sae ya samar miki wata makarantar ta matan aure,Rynt tace"to inna"


9:00pm
Tuni Rynt ta koma gida ita kad'ai a d'aki duk kewar mami ta cika ta don yrnyr akwai surutu sosai wacce da ace tana nn da yanxu duk ta cika ta da srt shiyasa tayi kewarta ba kad'an ba.
    Tayi minti 30 tana tunanin yanda zata shiga bayi tayi wanka kan baqin tsoro sae can tayi addu'ar ta ta shiga,haka tayi wankanta ba tare da ta wanke fuska ba don ganin take in ta rufe ido koda zata bud'e zata ga wani  abin tsoro, wacce duk qarin jin tsoron nn bai wuce sanin ita kad'ai ce a d'aki ba don lokacinda mami na nn lafiya lau take yin wankanta ba wani  shamaki.
 Tana fitowa idonta ya hango mata abu tsaye a qofar d'akin a razane ta buga ihu ta kwasa aguje zata koma bayi, mohd da dama shine tsaye yayi hanzarin jawota da qarfi har sae da ta fad'o kan qirjinsa ta koma sakin wani  ihun sbd zanin ta da ya rabu da jikinta ,sae duk ta rud'e tana wani  kakkama jikinta bayan cewa sanye take da qaton hijab har wuce guiwa,wani  kallon banza mohd ke mata snn ya kalli zanin ta da ya sa6ule ya sake d'ago idonsa yana kallon fuskarta ya kamo wuyan hijabinta yace"idan na raba ki da wnn hijabin sae ki gaya min dalilin fitar ki gidan nn da kuma qarata da kika kai a gurin Abba,sosai ta fiddo manyan idanuwnta masu cike da jin tsoro tace"Aa dan Allah kayi haquri wlh shi kad'ai ne a jikina!


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[1/12/2017]
 🔮```BAZAN  BARSHI BA!```🔮









          🔮🔮🔮
_*page*_ *```26```*
   Kauda kansa yayi gefe dan shi sam tunanin hkn bai fad'o masa ba shidai kawai  dukan ta yaso yi har sae jikinta ya gaya mata.
 Ya kalle ta ta6e da baki yace"badai akwai fata a jikin ki ba wacce zata aika miki da saqona har ixuwa daqiqiyar qwaqwalwarki"
Rynt ta wani  qara bud'e manyan idanuwanta ganin yana zare belt d'in wandonsa ,
ta fizgi jikinta da qarfi tace"wae dukana zakayi, don Allah kayi baquri wlh duka fa da zafi"
   Yace"da zafi?eh wlh don Allah kayi haquri bazan sake fita ba sae da izinin ka na rantse!bai kula ta ba yayi cikinta ya fara dukanta kan qafafunta gunda hijab bai qarasa kai ba ,
ihu take sosai tana bashi haquri amma fafau yaqi haqura sae da ya zane mata qafafu tas snn ya dakata tare da nuna ta da yatsa yace"idan har tunanin kike kinzo nn gidan don jin dad'i shine har kike fita anguwanni to ki cire kisa a ranki nn tmkr kurkuku kika shigo don haka daga yau ko qafar ki kar na qara ganin ta fito daga d'akin,nn ya kama kunnen sa yace"kinji me na gaya miki? da sauri ta gyad'a masa kai cikin kuka,nn wyr sa tayi qara ya d'aga had'e da fita d'akin Rynt kuwa ta had'e kanta da guiwa tana ci gaba da kuka ,takai hannunta cikin hijab tana shafa qafafuwanta da duk sukayi shatar belt.
   Tana jin za'a shigo d'akin tayi saurin d'aukar zanin ta ta d'aura ,mohd ne riqe da hannun mami ta tafi da gudu ta rungume Rynh wacce tayi saurin share hawayenta kar mami ta gani ,
mami tace"Anti na dawo ne sbd inajin dad'in zama gurinki sbd kullum kina koya min karatun islamiyya ko yau zaki koya min kafin muyi bacci ko? Dan guntun murmushi Rynt ta qirqiro ta gyad'a mata kai kawai don har lokacin man na tsaye yana kallon su, mami ta maida dubanta gare shi tace"yauwa yaya d'azun da mukaje gida nida anti har nake gaya ma Abba cewa kullum kullum mu kad'ai ne a cikin gida ba mai kawo mana fira daga ni sae anti har kai bama gani sae yau kad'ai muka ganka kaida anti amarya zaku tafi anguwa sae naji Abba yace wae zaka zo ka same shi ne ai,to yaya kaje ka same shi d'in don wata qil aiken ka zai yi ko?kallon su yayi da ita har Rnyh d'in kafin yace komai mami tace"yaya wai anti d'azun da mukaje gida har na gaya ma Abba haka tace min wae kar na qara gayawa kowa haka kuma wae na rage yawan srt ba kyau wae hakane yaya?hakane mami,yayi mgnr ne a takaice ya kuma juya zai bar d'akin ,
mami taje da gudu ta riqo hannun shi tare da d'aga kanta tana kallon shi tace"yaya yau ma baza ka taya mu fira ba tafiyar ka zakayi?eh zan tafi ne naci abinci,nima yaya zan bika muci abinci,yace"to muje"Rynh na kallo suka fita  taje ta kwanta ruf da ciki tana ci gaba da kukanta .
   Sae goma da rabi mohd ya dawo d'auke da mami wacce tayi bacci ya samu ita ma Rynt tayi bacci sae dai kallo d'aya xakayi mata kasan da tsoro baccin ya d'auketa don duk ta cusa fuskarta cikin pillow ta kuma damke pillow kmr wacce za'a qwacewa shi ,
yaje a hnkli ya kwantar da mami snn ya kalli Rynt wacce cikin qaton hijabinta tayi baccinta nn idonsa ya fad'a kan santala santalan qafafuwanta da hijab bai ida rufewa ba da har yanzun suna d'auke da shatar dukan da ya mata,ya kauda idonsa snn ya fita yaja musu qofa ya rufe.


Washe gari Rynt ta tashi cike da jin yunwa sbd jiya da dare bata ci abinci ba tayi bacci.
   Tana gama yi ma mami wanka ta shiryata,mami tace zata je gun yayanta nn mami ta fita ita kuma Rynt taje kan bed ta zauna cike da tunanin inda zata sami abinci tunda yanzu kam inna bazata qara aiko mata ba.
  Tana nn zaune yunwa ta cita har ta gode Allah sae duk rayuwarta ta baya ta dawo mata nn ta had'e kai da guiwa ta fara kukan tuna baffanta, sae jin tayi an turo qofa ta d'ago fuskarta a hnkli don ganin wanda ya shigo.
  Mohd ne yaja ya tsaya a nn bakin qofar ya jingina tare da sanya hannuwansa a aljihun wadonsa yana kallonta ita ma tana kallon shi da idanuwanta da suke cike tap da qwallah ta taso cikin tafiya kmr bata so har ta qaraso gurin shi tayi tsaye tare da sadda kanta qasa tana kallon farin tiles d'in d'akin,mohd ya fiddo d'ayan hannunsa a aljihu ya d'ago fuskarta dashi yayinda hawayen idonta ke silalowa a hnkli kan kumatunta sae dai still idonta na qasa sae da yace"mene ne"snn ta kalle shi tare da fad'in yunwa nakeji tun jiya banci komai ba"
  To shine zaki wani ajiyewa ma mutane kuka !ni ba yunwa nake ma kuka ba ai,to me kike ma kuka? tace"nidai ka taimaka min da abinda zanci.... idan anqi fa, Allah zai taimake ni,au kinsan da Allah kuma kika ce ni na taimaka miki,shiru ta mishi ta komawarta kan gado tayi kwancinta ya saki guntun tsaki ya fita daga d'akin.
  Ba jimawa sae ga kukun gidan ya kawo mata abinci tayi mamaki don ita kanta roqonsa kawai tayi bata d'auka zatayi nasara ba ,
don a nn kwancen da take har ta fara tunanin tashi ta sami  ruwa tasha kmr yanda ta saba yi a qauye.

 Sama Sama taci abincin sbd abincin duk rabinsa ganye ne ita kuwa ba son ganyen take ba tunda ba'a saba ba, don ko yanzu ture ganye tayi gefe taci abinda take iya ci tabar saura, bayan d'ayan plate d'inda ta ajiyewa mami.

Bayan kwana d'aya da faruwar haka Rynt na zaune a tsakiyar gado ta lanqwashe qafafu  tana karatun qur'ani cikin muryar ta mai dad'in sauraro ga duk wanda yaji,mohd ya shigo d'akin yayi tsaye tsawon lokaci bata sani ba sae karatu take abinta, sae da yayi gyaran murya snn tasan da shigowar shi ,kallon sa take ba yabo ba fallasa haka shima sae dai kuma zama d'aya ya sha mata toka ya juya tare da fad'in "biyoni muje ki gyara min d'akina"
  Ba musu ta ajiye qur'aninta ta bishi.
     Tsarin gidan tsari ne da d'akunan matan shi suka saka shi tsaka wanda dole duk wacce zata je d'akin shi sae tazo ta main falo take zuwa kuma in  an shiga qofar da zata sada ka da 6angaren shi sae an hau upstairs kafin ka kai ga d'akinshi.
  Rynt sae rarraba ido take tana kallon koina don dai gurin ya zamar mata kmr aljannar duniya,suna shiga d'akin mohd ya juyo gareta yace"kinga d'akin sae kiyi ki gyara  min kan lokaci"
  Gyad'a masa kai kawai tayi,shi kuma ya fita yaje 6angaren malika,ya sami malika jikin wardrobe yaje ya rungumo ta ta baya tare da fad'in"malika had'a min kayana dake d'akin nn zan koma d'akina ne yau"ta juyo tare da qara rungume shi snn tace"gsky ba inda zaka je muyi zaman mu guri d'aya yafi don ni bazan iya whlr jeka ka dawo ba"
yace"hqr dai zakiyi malika sbd komawata d'akina shine saiti "ta d'ago a fusace tace"ok kana nufin zaka raba mana duty tsakani na da wnn abar! girgixa kansa yayi yace"ko d'aya kuma kwata kwata ki cire wnn tunani a ranki kawai dai ina buqatar komawa ne"to gsky ni bana buqatar ka koma can! yace"A'a fah!cikin masifa tace"to wlh duk ka koma sae na bika!ya gyad'a kafad'a tare da fad'in "no vex yanzu sae ki had'a mana kayan ko? murmushi tayi snn tace"yanzun naji bayani don wlh ban yarda da zamanka kai kad'ai ba"yace"to da sharad'i ba gabad'aya fa xaki tare guna ba...kmr ya?kawai bacci zaki riqa kai min sbd bana son kowa na shigar min 6angare,sbd frnds d'inki sun fiye zowa kin sani ba kuwa zai yiyu kina zuwar min dasu 6angarena ba,ta wani 6ata fuska tana kallon shi tace"to meye a ciki don naje dasu kawai kai dai na fhmce ka so kake da rana ka riqa zuwa kana holewa da wnn yrnyr,cikin daka mata tsawa yace"wlh kar na koma jin kin ambata min wnn yrnyr idan muna zancen mu!bcs i am absolutely hate her!don haka yawan yimin zancenta kan iya sa qiyayyar da nake mata ta dawo gare ki be careful!daga haka ya juya zai fita daga d'akin ,
malika tayi saurin rungumoshi ta baya, tare da fad'in "my man yi hqr zan kiyaye kaji"sae da ya sauke ajiyar zuciya snn ya juyo tare da riqo kumatunta yace"malika ina mata d'aukar  baiwa ne ba mata ba amma ke kinxo kina alaqantani da ita a matsayin matata wlh malika da kinsan baqin cikin da nake ji da hkn da ko da kuskure baza ki ambata min ita ba,kayi hqr my man bazan sake ba,fuskarta ya shafo tare da fad'in "shi kenan ya wuce muje mu had'a kayan ko?murmushi ta sakar mai taja hannun shi suka nufi wardrobe.


Rynt kuwa nn take ta gyara d'akin tsaf don dama ba wani  datti ne dashi ba ,zata fita kenan idonta ya hango mata wani  photo na mohd su uku wato shida abokan haifuwar shi, ta d'auko d'an frame d'in tana kallo nn ta fhmci akwai rubutun da akayi kmr fulawa dan sae ka kula da kyau kake fhmtar rubutu ne akayi ,
Aamil,Amir &Aminullah shine a rubuce ta qasan kowanensu.
  Shafa rubutun ta shigayi sbd ba qaramin kyau ya mata ba yayinda ta shiga kallon fuskokin su cike da son gano meye banbancin su,sae ga mohd rungume da malika sun shigo d'akin,malika na ganin abinda Rynt keyi tayi saurin d'agowa daga jikin man tace"kaga er iska photonka fa take kallo shine har da wani  shafawa!
taje fuuu!ta fizgi photon tare da kife Rynt da mari tace"keda aka sa gyaran d'aki me kuma ya kaiki ga photon mijina er iska ,tambadaddiya dake nake! ki gaya min ko wlh na qara miki wani  marin ynx!nn mohd yazo gun Rynt wacce ta dafe kuncenta yace cikin kakkausar murya"dan ubanki aikin da na saki kenan ko kuma ni sa'anki ne da zaki d'auko photon mu kina kallo!bari kiji wlh daga yau duk nasaki aiki naga sa6anin haka ubanki na lafira ma sae yafi ki jin dad'i!da sauri Rnyt ta d'ago idanuwanta da sukayi jajir suka ciko da qwallah tana kallon shi.


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[1/13/2017]
 🔮```BAZAN  BARSHI BA!```🔮









          🔮🔮🔮
_*page*_ *```27```*
Tsawa mohd ya daka mata mai firgitarwa tare da fad'in"get out!da sauri Rynt ta tafi har tana had'awa da gudu taje d'aki ta fad'a ruf da ciki kan bed tare da  fashewa da wani  irin kuka mai ban tausayi.
   _Ta yaya zan barshi! bayan shine silar rabani da farin cikina kuma shine silar zuwana birni har na had'u da qaddararren aurenda nake ganin wlqnci haka, lallai idan mohd ya kasance shine wanda ya kashe min mahaifi a cikin su ukun nn fansar da zan d'auka akanshi mai munin gske ce._
_Allah sarki yaya anwar nsn da kana raye haka ta faru dani da ka bimin haqqina ba tare da na aiwatar da abinda bai dace dani ba._
  Tana magana ne a cikin zuciyarta yayinda take ci gaba da kuka mai cin rai.

 Tana cikin hakane mami ta shigo d'akin, Rynt tayi saurin share hawayenta  wasu suka sake zubowa dai dai mami ta hau gadon d'auke da ledodi a hannunta ta kalli Rynt tace"anti wa ya dake ki kike yin kuka?share hawayen tayi tace"ba wanda ya dake ni"amma kuma kikeyin kuka ko wani  ne ba lfy  don naga yau da mukaje asibiti nida yaya Nasir duba wani  yaya munir abokin yaya man ummansa sae kuka take tayi sbd ko magana baya yi ance ma sae an fita waje dashi ko zai sami lafiya,wasu hawaye ne suka sake zubowa Rynt tace"yaya munir yayan su safiyya? Eh anti shi ashe kin sanshi,kuka ta shiga yi mara sauti ,mami tace"anti umma fa tace min ba kuka ake yiwa mara lafiya ba addu'a, kinji anti ki daina kuka ki masa addu'a, had'e kai da guiwa Rynt tayi tana ci gaba da kuka ,mami ta dafa ta tana fad'in"anti addu'a fa zaki masa ba kuka ba,nima da nake er qararrama ban masa kuka ba sae cewa nayi Allah ya bashi lfy,naji mami zan masa addu'a nima, ta fad'i hkne yayinda ta d'ago tana share hawayenta, mami ta jawo ledodin da ta shigo dasu guda biyu tace"Anti yaya nasir ne ya saya mana chocolate nida ke ga ledar ki kar6i,Rynt ta kar6i d'ayar leda ta d'aura kan bedside drawer,mami kuwa sae kallon idanun Rynt take da sukayi jajir  tace"Anti hln yaji ya shiga miki ido da na samu kina kuka"girgiza kanta kawai tayi,snn tace"tashi muyi sllr zhr sae mu yiwa yaya munir addu'a ko?to anti daga nn ma mu roqi Allah yasa mu anjannah muci kayan dad'i ko?Rynt tayi d'an murmushi snn taja hannun mami suka nufi bathroom tare sbd  haka suke kullum in zasuyi arwala tare suke shiga dmn arwala Rynt ke koyawa mami amma wani  lokacin sae ta fara shiga in ta kama ruwa snn ta kira mami ta shigo.

Bayan sun gama sallah mami ta d'auko ledar chocolate d'inta tace"Anti zanje na kaiwa anti amarya chocolate taci"
Rynt tace"to sae kin dawo"
ba jimawa sae gata ta dawo tana cin chocolate  tace"Anti qofar anti Amarya a rufe take inaga ta fita,na bari gobe na sake kaimata ko? "eh"shine kad'ai abinda Rynt tace don sae tunanin rashin lfyr munir take.


Washe gari da safe ko break fast basuyi ba mami ta jawo ledar chocolate ta fita wae zata kaiwa anti amarya ta d'iba.
  Fitar ta keda wuya ta jiyo kukan mami ta fito da sauri har tana had'awa da gudu tana isowa main falo ta had'u  da mohd shima ya fito sbd jin kukan mami da yayi ,mami taje da gudu jikin Rynt inda cikin kuka sosai take nuna malika ,mohd yace da malika me kika mata ne! shaye da toka tace"sanin kanka ne qanwar nn taka baqin srt tsiya ne da ita ,tazo ta sameni ina bacci daga kawo min ledar chocolate tayi wae na d'iba nace mata bana so bai isheta ba sae da ta wani cika ni da srt shine ni kuma na mareta,
 jiki sanyaye ya kalli mami wacce bakinta ke fitar da jini ya jawo hannunta yasa tissue ya goge mata jinin yace"ki daina takura anti amarya idan tana bacci kinji, cikin muryar kuka tace"Allah yaya qarya take ba bacci take ba "malika ta dallah mata harara tace"dan ubanki ni ke qarya "a fusace ya d'ago yace"malika mind ur tongue qanwata ce fa kike zagin ubanta"to kai baka ji me tace min bane!kuma indai zagin ubana ne ai akanka na koya ,tsaki yayi ya kalli Rynt wacce yake ganin kmr duk laifin ta ne yace"da Allah malama jata ku tafi!
   Rynt ta kalle shi snn ta d'auki mami tana  share mata hawaye tace"yi hqr Allah zai isar miki"
Malika tace"jar uba! ke ni kike gaya ma magana!
ta tafi fuuu!zata kaiwa Rynt duka ,mohd ya jawota yace"barta kawai zanyi maganin ta ne,nn ya tafi da ita sae masifa take tana sirfàwa Rynt zagi har suka shige 6angaren mohd.
 ta6e baki Rynt tayi snn ta wuce d'auke da mami.

Da dare mohd ya shigo d'akin Rynt ya sami Rynt da mami suna pillow fight sae dariya suke suna dukan pillown juna har Rynt tayi nasarar da pillown mami ya qwace ya fad'i qasa nn Rynt ta tashi cikin dariya tana mata gwalo tana fad'in "ko yanzu na cinye ki"cikin shagw6a mami ta turo baki,sae kuma ta washe baki ta tashi da sauri ta bud'e wardrobe ta d'auko qatuwar teddyn ta da tasan Rynt na mugun jin tsoro tayo kan  Rynh aguje zata liqa mata,Rynt da ko ganin ta bata son yi ta rufe  ido ta kuma kwasa da gudu zata bar d'akin,sae jin tayi ta fad'a jikin mutum nn ta fasa wani  irin ihu ta zube gabad'aya a jikin man.


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[ 1/16/2017]
 🔮```BAZAN  BARSHI BA!```🔮










          🔮🔮🔮
_*page*_ *```28&29```*
Tsaki mohd yaja tare da ture ta daga jikin shi, kan ta kai qasa yayi saurin tarbota dan sae a lokacin ya fhmci suma tayi,ya kwantar da ita nan qasan tiles ,mami kuwa ta jefar da teddy tazo da gudu gun Rynt ta saki ido tana kallon Rynt dake kwance,
mohd yace"je 6oye teddy ki d'ebo min ruwa"
  Mami taje ta maida teddy snn ta kawo masa ruwa ya kar6i ruwan ya shiga yayyafa ma Rynt a fuska,firgigit ta tashi tana ihu tana fad'in"mami ki daina liqa min wnn abun bana so dan Allah"ta qarashe mgnr kmr qaramar yarinyar da zatayi kuka,wacce sae a lokacin ta kula da mohd da ko lokacinda taci karo dashi ta d'auka ko teddy ce,shiyasa ta qara firgicewa har ta kaita ga suma .
  Mami tazo gab da ita tana kallon Rynt wacce tayi zaune ta had'e kai da guiwa yayinda jikinta ke ta rawar tsoro ta dafa ta snn tace"anti kiyi haquri kinji bazan sake ba"kafin Rynt tace komai mohd yace da mami,"d'auko min teddyn naje dashi d'akina idan kin buqata sae kije d'akina kiyi wasa a can ko? Mami ta gyad'a kanta tare da tashi ta d'auko mai teddyn ta bashi ya kar6a tare da duqawa zai d'auki agogon sa da ya fad'i kusa da Rynt,dai dai Rynt ta d'ago fuskarta da idanunta ke cike tap da qwallah,ganin teddy a hannun shi yasa tayi saurin matsawa tare da tura masa agogon sa da ta fhmci zai d'auka, sae da ya kalleta snn ya d'auki agogon ya fita.
 Mami tazo jiki sanyaye gun Rynt tace"Anti kin haqura ko?Rynt ta gyad'a mata kai tare da share hawayenda suka zubo mata,snn tayi d'an murmushi tace"ba komai ya wuce"
 Daga haka ta  tashi sukayi shirin bacci suka kwanta.

Mohd kuwa 6angarensa ya nufa yana shiga ya jefar da teddy kan sofa snn yaje ya kwanta kan bed tare da ciro wyrsa a aljihu ya fara latse latse.
  Malika ce ta shigo d'akin cikin rgrta ta bacci dani da babu taje kusa dashi ta kwanta tana kallon abinda yake yi a waya, ta kalli fuskar shi snn tace"my man ashe kana game"yace"in tamin dad'i ba"ta mirgino kan jikin sa tare da kai hannu tana shafa sajen fuskar shi tace"my man nifa ban gane ba har mun shigo cikin sati na biyu da aure amma banji kana zancen zamuje honeymoon ba"
yace "malika nida ke son komawa bakin aiki ina kuma zancen wani honeymoon"
ta 6ata fuska tana kallon shi tace"ba wani  nn gsky ni sae munje honeymoon tunda ba fina akayi ba"to shikenan zamu je d'in"
kiss ta bashi tare da fad'in "tank u"yayi murmushi yaci gaba da aikin sa kawai,nn malika ta shiga qoqarin hana mishi game d'in don sae wasu abubuwa take mishi a jiki har ta kai ga ta qwace wyr tana qoqarin had'e bakin su, ya kauda bakinsa gefe  snn ya koma kallonta sbd buttons d'in rgr sa da ta shiga 6allewa ya riqo hannunta yace"malika wae ke ba kya gajiya ne,naga yaushe yaushe ne muka rabu"
to my man kai d'in na daban ne kasani shiyasa bana gajiyawa da kai"ta qarashe mgnr tare da kashe mai ido d'aya ,yace"to muyi bacci har gobe don yanzu kam ngji"ta wani 6ata fuska tace"gsky nifa ina buqata"
ya salam shine abinda ya fad'a a ransa har ga Allah baya son yawan laluboshi da take wace irin mace ce da tun auransu bata ta6a bashi rana d'aya ya huta ba har yau,nn yace"ok ina zuwa"ya tashi ya fita sae gashi ya dawo d'auke da fresh milk da cups ya kalleta d'auke da murmushi yace"bari musha tukun ko" bai jira amsarta ba ya tsiyaya mata fresh milk ya bata,
har ta shanye cup d'in tas shi bai ko fara shan wacce ya zuba ma kanshi ba,ya kar6i nata cup yace"na qara miki ne? Ta girgiza kanta tare da matsowa kusa dashi ta kwantar da kanta a qirjin sa, daga nn tayi bacci don dama maganin bacci ya zuba mata don kawai ya huta da jarabarta.

 Bayan kwana uku da faruwar hakane zuwa honeymoon d'insu ya tashi dan har ma ga gobe zasu tafi shiyasa tun safe yakai malika gidan iyayenta  don ta musu ban kwana, Rynt kam bata san abinda ake ciki ba kawai dai kullum da safe mohd na shigowa 6angarenta yaja mami suyi breakfast ita kuma kuku ake aikowa ya kawo mata nata,kuma in banda gaisuwa ba abinda ke had'a ta da mohd.

Zaune suke ita da mami a d'aki kan bed tana koyadda mami karatun qur'ani, ya shigo ya same su ,
Rynt na had'a ido  dashi ta kauda kai amma shi still kallonta yake sae ma cewa yayi ki taso keda mami zamu fita, daga haka ya juyawar sa ya fita mami ta bishi da gudu tana jin dad'i.

Koda Rynt ta fito harabar gidan ta samu har sun shiga mota ita kad'ai suke jira,taje ta shiga motar itama.
  Basu zarce koina ba sae family house,mami ta tafi da gudu zuwa 6angaren su,mohd  kuwa ya nufi nasu 6angare shida Rynt ,
suna shiga falo suka sami Abba zaune ta durqusa ta gaidashi  cike da ladabi ,ya amsa mata cikin sakin fuska.
 Byn sun zauna da ita har mohd d'in snn Abba yace" nine nace yazo min dake kan wani  rashin adalci da naji yana shirin yi da na masa magana se yace kece baki buqaci hkn ba,Rynt ta kalli Abba don ita bata gane inda zancen nasa ya dosa ba, Abba yace"batun zuwan su honeymoon ne shida malika shin kinsan da batun zuwan?
Rynt da batasan meye honeymoon ba illa kawai abinda ta fhmta wani guri zasu, zuwansu da rashin zuwansu kuwa duk d'aya ne a gurinta se tace"eh"
to meyasa baza ki bisu bane ko kuma shi ya hana miki? Aa Abba kawai dai ina son zan koma islamiyya ne, Abba ya kalli mohd yace"to kaji idan ita waccan d'in honeymoon ta buqaci zuwa kaji wnn islamiyya take buqatar komawa don haka sae kayi adalci a tsakanin su"yace"inshaAllah Abba, nn mohd ya tashi ya fita Rynt kuwa ta tashi zata haura sama dmn gaida hjyr su mohd Abba yace"Ai bata nn ta fita,
  tafi kawai abinki ku koma gida, tace"to snn ta fita"

 Koda ta fito mohd na jingine jikin mota yana jiran fitowar ta,bata nufi gunshi ba sae 6angaren su saliha ta nufa yace"ke ina kuma zuwa?tace " Zanje gaida mama ne daga haka bata jira amsar shi ba ta shige abinta.
   Bata wani jima ba ta fito ita kad'ai ba tare da mami ba don dama tun cikin mota da suna kan hnyr zowa tace in sunxo sae dare zata koma.


Tafe suke kan hanya ba mai ce ma wani  can Rynt tace"gidan inna fa"kallon ta kawai yayi ba tare da yace komai ba yaci gaba da tuqin sa har suka isa gida.


Da dare  ta fito daga wanka mohd ya shigo d'akin riqe da hannun mami ya same ta sanye da qaton hijab d'inta as usual ,ta d'auko Vaseline zata je kan bed ta shafa,ya tsaya bakin qofa mami kuwa taje da gudu gun Rynt snn ya juya ya bar d'akin yana mai jiyo yanda mami ta fara cika Rynt da srt.



Washe gari tunda ya dawo daga masallaci sllr asuba ya tafi d'akin ya samu duk bacci suke da ita har mami kasancewar fashin sll Rynt keyi shiyasa bata tashi sllr asuba ba.
    Rynt bata da nauyin bacci ko kad'an shiyasa taji lokacin da mohd ya shigo,yana jin yanda sautin addu'ar tashi daga bacci ke fita a hnkli daga bknta snn ta tashi zaune had'e da blanket d'in  jikinta wacce still tana sanye da hijabinta.
 Ta amsa masa sallama tare da had'e kanta da guiwa tana mishi ina kwana,ya amsa ba yabo ba fallasa sae kuma ya fita bai ce mata komai ba hkn yasa ta komawarta ta kwanta.

Koda ya koma d'akin shi ,malika na kwance bata tashi ba sae sharar bacci take bayan ba irin tashin da bai mata ba kafin ya tafi masallaci, ya kalli yanda take kwance  bata da maraba da tsiraici sbd gabad'aya abin rufan ta kad'an ya saura ya sauka kan jikinta,guntun tsaki yayi snn ya fara tashin ta da qyar ya samu ta motsa sbd baqin bacci ne da ita ,a maimakon ta tashi sae ma gyra kwanciya tayi,cike da takaici yace"wlh duk kika koma wani  bacci za'a fasa tfyr nn ne!firgigit ta tashi tana miqa had'e da hamma tace"wayyo my man bacci bai ishe ni ba fa"komai kasa ce mata yayi don duk ta cika shi da takaici ganin ba komai a jikinta amma ko kunya babu sae wani  miqa take a gabanshi, haka ta tashi ta nufi bathroom ba tare da ta yafa komai a jikinta ba.

   Guraren qarfe tara mohd ya koma d'akin Rynt cikin shirin sa tsaf sae qamshi yake zubawa ,ya same ta zaune da breakfast a gabanta yace"mami fa ?tace"tana bayi"
yace "ok mu zamu tafi" tayi saurin kallon shi tace"to mufa zamu koma gidan inna ne, snn zancen komawata islamiyya fa ?yace"zancen islamiyyar ki babu"kmr zatayi kuka tace"amma ba haka mukayi da kai ba gurin Abba,,wani  mugun kallo ya watsa mata yasa kai zai fita tayi saurin tashi ta bishi hkn yasa ya dakata tace"bafa zan iya kwana daga ni sae mami a gidan nn ba,yace "wnn kuma ya rage naki"
  Ya fita hk ta koma binshi ya daka mata tsawa yace"kikayi gigin na sake taka qafa ki tako taki ko wlh sae na mare ki"kuka ta fashe mai dashi  tace"nidai kayi haquri dan Allah mu tafi gidan inna kuma na koma islamiyya wlh na sa raina a islamiyyan nn"
  A sae ki cire tunda ba gidnku bane da zakiyi abinda kika ga dama!
  Sautin kukanta ne ya soma fitowa ta hana faruwar hkn ta komawarta ta zauna tana jin mami zata fito bathroom tayi saurin share hawayenta yayinda mami ta fito tana fad'in " gufranaka ya Allah"
ta washe baki tare da fad'in"hkne ko Anti?Rynt ta qirqiro murmushi tare da gyad'a mata kai"snn takai dubanta gun mohd da har lokacin yana tsaye bai fita ba mami taje gurin shi da gudu  yaja hannunta suka fita.


Tayi awa d'aya kafin taga dawowar mami.
  Wacce ta dawo d'auke da kayan wasa kala kala sae murna take taje kan bed tana fad'in"Anti yaya ne ya sayamin kayan wasa yace in ta wasa har su dawo wai baza su jima ba"Rynt tace"to zo kici abinci?ai anti sae da nayi breakfast kafin naje raka su yaya a airpot ,Rynt da ba tasan meye haka ba ta basar da zancen. can mami tace"lah anti na manta yaya nasir fa yana falo wae kije.

Koda Rynt taje kuwa ta same shi zaune a falo cikin ladabi ta gaida shi ya amsa ba yabo ba fallasa snn yace"ko da akwai wani  abunda kike buqata?ta gyad'a masa kai tare da fad'in "eh"yace"me kenan"
tace"ina son na koma gidan inna da zama ne har idan sun dawo snn kuma ina son na koma islamiyya"yace"meyasa kike son komawa gidan inna? Sbd bana jin zan iya bacci daga ni sae mami a gidan, gidan nn ya mana girma sosai"indai wnn ne ai mai sauqi ne Rynh don da sannu zaki saba kuma  idan wani  abu kike tunanin zai faru ai akwai masu tsaro sosai a gidan kuma da yardar Allah ba abinda zai faru kinji? ta gyad'a masa kai snn yace"zancen islamiyya kuma gobe inshaAllah nn cikin anguwar zan nema miki wata islamiyya ta matan aure "tace"to nagode yaya nasir"
yace"sae kuma me kike buqata? Shike nn komai bana buqata, to ga wnn  ki riqa a hannun ki, tace"Aa wlh ka barsu kawai nagode inada kud'i a hannu na da inna ta ban"murmurshi kawai yayi ya ajiye kud'in kan center table ya tafi tace"masa nagode snn ta d'auki kud'in ta juya cike da jin dad'in zata koma islamiyya,yayinda nasir ya fita cike da mamakin mohd ace zai yi tafiya  bai bawa mtrsa komai ba.


Da dare kuwa duk ta cire wani tsoro a ranta sukayi baccin su ita da mami.


Washe gari da kanta taje kitchen tayi musu break fast sbd yinin jiya duk bata ga kuku ba bai kuma kawo musu abinci ba.

8:pm nn falo suke zaune  su biyu abinsu suna kallon tom and jerry.
 Sae ga nasir ya shigo da sallamar sa.
  Bayan sun gaisa ya bata leda yace" hijabin makarantar ne a ciki kuma da qarfe biyu ake zuwa a dawo qarfe hud'u .
makarantar tana a nn bayan gidan ba nisa amma gobe zan zo na kaiki don kiga makarantar.
  Sosai tayi mai godiya snn ya tafi.


 Haka ko akayi washe gari nasir  yazo ya  kaita islamiyya mami kuwa ya kaita gida.
  To tun daga rnr ita ke kai kanta ta kuma  maida kanta amma sae da qarfe biyar ake maida mata mami.

Su mohd kuwa kusan sati uku sukayi a yawon honeymoon d'insu.

Rynt kuwa sosai ta maida hnklinta zuwa islamiyya kuma rashin kuku bai kawo mata wata matsala ba don koda 1:30 keyi har ta gama musu abincin su na rana sunci ita da mami bcs kafin qarfe biyu nasir ke zowa yakai mami gida,sbd Rynt ta samu taje islamiyya kan lokaci,idan kuma ta dawo qarfe hudu sae tayi sll snn take d'aura musu girkin dare,kuma duk abinda tayi ra'ayin dafawa akwai shi a gidan matsalar ta d'aya itace kewar inna da take sosai.

Rnr wata assabar ne Rynt ta dawo daga islamiyya ita da wata qawar ta suka shigo gidan kowanen su cikin niqabi,da kuma hijab d'insu har qasa da socks .
A nn harabar gidan ta had'u da malika da mohd wa'anda saukar su kenan, gaban Rnynt yayi mugun fad'uwa  sbd tunanin abinda zai biyo baya ita da mohd idan yaga ta koma islamiyya bada sanin sa ba, hkn yasa ko gaida shi taqi tayi dan kar ya balbaleta gaban qawar ta.
  Dashi har malika kallonta suke har suka shige, malika ta kalli mohd ta6e da baki tace"my man lokaci fa yayi da zaka gargad'a mana yrnyr nn, jifa har da wani  kwashe kwashe take maka ,mohd yace"zanyi maganin ta ne ai ,in ni sa'anta ne ko kuma gidan nawa an gaya mata qwai da dunge duk shigowa suke suyi abinda suka ga dama"hm rainaka tayi wlh ita d'in kanta wace ce da har zata yo maka wani  jajube jajube.


Su Rynt kuwa har suka shiga d'aki gabanta na dukan uku uku .
Byn ta nunawa wacce suka shigo tare bathroom tayo fitsari ta fito take ce ma Rynt "nikuwa Rynt
 ba mai gidan ki bane ya dawo?Rynt tace"shine"
tace"ikon Allah sae kikayi kmr baki sanshi ba,"uhm"cewar Rynt  yayinda er makarantar tasu bata sake cewa komai ba ta fita had'e da yiwa Rynt godiya.

Nn kan saukowa upstairs ta had'u da mohd ta gaida shi ya amsa ba yabo ba fallasa snn ya wuce sae d'akin Rynt wacce ya samu ta cire niqab d'inta kenan ,tana had'a ido dashi tasha mai toka, shima fuskar sa tamau yake cewa "wace ce kika shigo min da ita a gida?tace"qawata ce"
da wane dalilin ta shigo min gida? Lalura, shine kad'ai abinda tace ta kuma  kama hanya zuwa bathroom haka shima bai sake cewa komai ba ya fitawar sa, fasa shiga batroom d'in tayi don dama tsoron kar ya dake ta yasa tayi niyar shiga bathroom,shiyasa ma tayi mamakin ganin ya fita bai yi mata fad'an ftr ta ba da kuma inda ta fito,ko meyasa,oho.


Da dare mohd ya dawo daga masallaci sllr isha'i ya tafi d'akin malika ya sameta kwance  tana waya tayi saurin katse wyr  ta tashi ta tarbo shi cike da kisisina tace"ya akayi my man ko wnn abar ce takai ma koina don naga fuskar ka kmr ba annuri ,yace"yunwa ce wlh na rasa ina d'an iskan kukun nn ya shiga ace tun d'azu da muka dawo bai kawo mana abinci ba kuma har yanzu ba alamar za'a kawo,,tace"oh no am sorry my man ai baya nn, ina yaje? Wlh nice na sallame shi da zamu tafi honeymoon ,da sauri ya kalleta snn yace "meyasa?
tace"me zai xauna yi to tunda bama nn"
yace"haba malika mami fa?
 tace "naga fa a gabana ka damqa kulawar mami a gun yayanta nasir kuma kasan komai mami ke buqata nasir ba baqonta bane zata gaya mai kuma zai mata tunda ko baka bashi kulawarta ba ai dole ya kula da ita tunda qanwar sa ce,,kuma ai tun lokacinda mukayi tafiyar nn kullum a gida mami ke yini ko ba haka naji kana waya da shi nasir d'in ba?naji hkne ,kira shi kukun yazo ya dafa mana abinda zamu ci da daren nn don nikam ina buqatar naci abinci kafin  na kwanta, to my man amma don Allah zanso na roqeka wani abu, fad'i inajinki,dama ina son naje gida ynz zuwa qarfe goma sae na dawo kaji, ya shafo cikinta tare da fad'in"to ki bari idan kinci abinci ko"um um lokaci zai tafi kuma idan naje gida ai zanci,to shike nn kira min kukun ni yazo ya dafa min nawa, tace"ok"snn ya fita.


Yana nn kwance  a d'aki ta shigo cikin shiri na qananan kaya amma ta d'aura after dress akai sae zuba qamshi take kallon ta yake har ta qaraso inda yake kwance  kan sofa ,ta duqa gab dashi d'auke da murmushi a fuskarta takai bakinta kan nashi ta had'e,inda cikin minti 1 ta zare bakinta
tana mai  fad'in"ur food is ready sae kaje kaci then ni zan tafi "yayi murmushi yace"ok ki gaida su mama"tace"zasuji" snn ta fita.

Shi kuma mohd ya fito ya nufi gun dining ya zauna har zai fara cin abinci sae kuma ya tashi ya nufi d'akin Rynt,
Kai tsaye Rynt ta ganshi amma hkn bai hana tayi saurin 6oye littafanta na islamiya ba da ta ftr tana d'an dubawa,snn ta kalle shi kmr marar gsky ga hannyenta takai baya tana qara 6oye littafan a bayanta.
shaye da toka yace"lafiyar ki? tayi saurin cewa"lafiya ba komai"
ya qara shan mur snn yace"da bama nn a ina kuke samun abinda kuke ci keda mami? Tace"ina dafa mana ne kullum"
to ina mami take ne yanzu?tana gida har yanzu bata dawo ba"yace"shike nn amma ki sani daga yau kar na qara ganin kucakar qafar ki a kitchen"ta gyad'a masa kai kawai shi kuma ya fita
sae kawai ya had'u da mami ta wani  maqalqaleshi tana mai murnar ganin shi.

Washe gari da qarfe biyu Rynt tayi shirin ta tsaf na islamiyya ta fito cike da tunanin yanda zata kaya da mohd idan ya ganta.
     koda ta fito gate d'in gidan sae ko tayi kici6is dashi zai kunna hancin motar sa a cikin gidan.
  Yana ganin ta ya fasa shiga gidan sae ma tsaida motar sa da yayi ya fito,a lokacin Rynt jin tayi kmr ta kwasa aguje kafin ya qaraso gareta amma hkn ta dake tayi tsayinta har ya qaraso gab da ita har ma tana jiyo qamshin turaren shi.

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[1/18/2017]

 🔮```BAZAN  BARSHI BA!```🔮









          🔮🔮🔮
_*page*_ *```30```*
Taja baya da sauri tana fad'in"dan Allah kayi haquri ka barni na ci gaba da zuwa islamiyyar nn"
tsaki yaja yace"kinga ba wnn ba abinda nake son sani shine kin gyara min d'akina ko kuwa?
  wane d'akin kuma,what!bangane wane d'akin ba kina nufin mami bata gaya miki saqona ba tun da safe? tace"bata gaya min ba"yace"to ai yanzu na gaya miki sae kije ki gyra min"badai yanzu ba kam don ni islamiyya zan tafi,yanzu kuwa er rainin wayo idan ba haka ba daga yau ma kin daina zuwa islamiyyar gabad'aya!
   Kmr zatayi kuka ta yaye niqabinta tana kallon shi tace"kayi haquri wlh in na dawo zan gyra maka,ke kina hauka ne da Allah koma daga ciki kije ki gyara min d'aki bana son wani  shirme,tace"bafa wani jimawa mukeyi ba da qarfe hud'u muke tashi"ok so kike na zauna har qarfe hud'u banje d'aki ba,ko kuma so kike na shiga d'akin da datti.
Kayi hqr kaje d'akin mtrka har in na dawo" kallonta kawai yayi ba tare da yace mata komai ba ya shigewar sa mota"
   Rynt ta sauke niqabinta ta kama hnyr islamiyya dmn abinda ta fhmta da kallon da ya mata yana nufin ta tafi.

 Mohd kuwa yana shiga  gidan ya parker motarsa  ya nufi cikin gidan bai zarce koina ba sae d'akin  malika ya samu ummarta tazo.
  Sae bayan sun gama gaisawa snn ya fito yaje falon downstairs ya zauna zaman jiran dawowar Rynt nn ne ya ciro laptop d'insa yana wani  aiki sae ga kuku ya kawo mai abinci yace"no bana buqatar abinci yau fruits kawai nake buqata kuma sae idan nayi wanka tukun,
"ok sir"cewar kuku snn ya kwashi abincin ya mayar.


Koda Rynt ta dawo ta same shi still zaune a falo sae aikin gaban sa yake,tayi kmr ma bata ganshi ba tasa kai zata wuce yace"ke zo nn"
 ba musu taje"
yace"Kin raina ni ko? Tace"me kuma nayi"yace"kin sani zaman jiranki kuma shine kika shigo kmr ma baki ganni ba har kike qoqarin ficewa sbd tsabar raini ko,tace"to......shiii! bana son jin komai,je kawai ki gyara min d'akina ,kuma ki tabbatar kin fara da bathroom,tace"to idan nayi sallah zanje"ta fad'i hakane tare da Kama hnya zata wuce d'akinta, ya daka mata tsawa  yace"wlh kafin na dawo masallaci na same ki a d'aki na na gaya miki"daga haka ya tafi zuwa masallaci ita kuma ta tafi d'akinta.

Tana gama sallah ta nufi d'akin shi ta fara wanke bathroom kmr yanda ya buqata don tasan meye bathroom sbd tanaji a bakin mami.

Ta fito snn ta fara gyra mishi bedroom ya shigo d'akin shaye da toka  yace"kin wanke bathroom d'in ?tace"eh"yace"oya fita nn da minti d'aya sae ki dawo"ba musu ta fita shi kuma ya cire kayan jikin shi ya sanya white bathrobe ya nufi bayi.
    Koda ya fito daga wanka ya samu har ta gyra koina tsaf har ma tana batun fita yace"ke dawo ciro min kayan da zan sa"da sauri ta kalle shi sbd jin zancen sa wani iri ta dae basar tace "a ina kenan?bai yi mata magana ba sae nuna mata wardrobe da yayi ,ta nufi wardrobe d'in cike da tunanin ta ina zata bud'e don bata san kanta ba asali ma bata ta6a ganin irinta ba ko a film.
  Hkn ta dake zata kai hannu a jikin wardrobe d'in kenan sae kawai taga wardrobe d'in ta bud'e da kanta ta hnyr sliding, ai kuwa Rynt ta saki ihu tare da ja baya ,sae tsaki taji mohd yayi yace"bagidajiya kawai! ni je ciro min kayana kar ki 6ata min lokaci.
   Kmr zata yi kuka tace"kayi hqr bazan iya ba inajin tsoro".
  Tsaki ya koma yi yaje ya ciro kynsa da kansa snn ya danna wani abu a jikin wardrobe ta rufe duk Rynt na tsaye na kallon shi ya juyo yace"malama ai sae ki tafi ko?kmr dama command d'insa take jira ta fita abinta.

Fitowar ta kenan ta had'u da malika zata raka mahaifiyarta ,yi tayi kmr ma bata gansu ba tayi ficewar ta.
   Mhfyr malika tace"me zan gani haka ita wace ce da har zata je 6angaren mijinki?malika ta ta6e baki snn tace"umma ai itace er matsiyata nñ wacce nake gaya miki Abbansa ya tilasta masa ya aura........ Iyye cabd'i zafa ayi er iskar yrny jibi fa yanda ta wuce mu kmr ta had'u da wasu gumaka ko wata gaisuwa babu, to umma me zakiyi da gaisuwarta ma nikam,mhfyrta tace"ba wnn ba ma me takeyi a d'akin mijin naki byn kince ba sonta yake yi ba? Ita ke gyara masa d'aki daman....... Kul! kar ki koma yarda ta shigar miki d'akin miji,kina hauka ne da baza ki gyara masa d'akin da knki ba,ni gsky umma bazan iya...... kwa6e mata baki mhfyrta tayi snn tace"ai kuwa in kika ce lalaci kina sake da baki zata qwace miki mijin,ni kinga tafiyata.
  Daga haka ta fita malika tace"wae tashin bomb ai ko sama da qasa zasu had'e tayi kad'an wlh!hm umma kenan ai ruwa ba sa'an kwando bane.
  Nn dai ta wuce sae d'akin mohd ta same shi yana sanya kaya  tace"wae sae yanzu kayi wanka "
,to ba kin share ni ba wae ke umma tazo ,to my man umma ce fa, yace"ko ba umma bace hlnki ne idan kika yi baqi sae ki shareni, hm my man kenan kaida ba yaron goye ba har wata kulawa zan maka da baza ka iya yiwa knka ba,kallonta kawai yayi yace"jeki ga kuku nn a bakin qofa"
  Da yake dama duk wanda zai shigo 6angarensa yana sane don yana gani a jikin na'urar sa da ya saita.
 Malika taje ta bud'ewa kukun qofa tace"ya shigo"
  Wani  qaton bowl ne kuku ya shigo dashi cike tap da 'ya'yan fruits kyace wani  basarake ne zaici.
  Byn ya ajiye ya fita malika ta d'auki Apple d'aya tana ci,mohd dake kallonta yace"tashi ciro min freshmilk a fridge "taje ta d'auko tana mai fad'in "hln dae baka ci abinci bane my man? Yace"ina zaki sani to"shiru ta mishi dan ta fhmci yau kmr baya in gud mood.


 Bayan wata d'aya da faruwar haka kullum kuwa Rynt na zuwa islamiyyarta mohd baya hanata,sae dai duk zata tafi islamiyya in ta had'u da malika a falo sae tayi ta gaya mata maganganu marasa dad'in ji har da su zagi,ta uwa har ta uba duk don Rynt ta tanka ta,amma ko tak Rynt bata ce mata asali ma a marar tarbiya take kallonta.


Mohd ne shida malika suna zaune a balcony sae firar su suke cike da nishad'i.
  Nan suka hango Rynt ta dawo daga islamiyya mohd ya duba wrist watch d'in shi 4:30 yace"me yarnyr nn ta tsaya yi har 4:30 bata dawo ba sae ynz"
malika tace"au kai yau ka fara gani kenan,ai kusan kullum haka take bata dawowa kan lokaci kuma har rnr da ba'a zuwa islamiyya,fita take, what!har rnr da ba islamiyya fita ke?ta6e baki tayi snn tace"hm to kana da tabbacin ko ranakun islamiyya ,islamiyyar take zuwa ne,kullum ace bata ta6a tsallake lokaci ai ko nn abin dubawa ne,kuma ni abinda yasa tun farko ban gaya ma ba sbd kace baka so ina maka zancenta, mohd yace"dani take zancen"nn ya tashi ya nufi d'akin Rynt,koda yaje ya samu har ta fara sallah hkn yasa ya fito.


Washe gari ta kasance rnr alhamis ba islamiyya gashi mami bata gidan tana gidan pretty ta kai musu yawo, Rynt kuwa ba inda take son zuwa irin gidan inna amma tunanin yanda zata tunkari mohd take.
  Har dai akayi sllr zuhur tana tunani akai da ta gama sll ta yanke shawarar zata fita idan ta ganshi ta tambayeshi ko Allah zai sa tayi sa'a.


Koda ta fito kuwa yana nn zaune a falo sae dai shida wani  abokin sa ne, ta juyawar ta zata koma d'aki yace"ke zo nn"

Tana isa gurin su bata iya ko gaida su ba yace"dama kuwa an gaya min fita kike har rnr da ba'a zuwa islamiyya, shine yanzu kin fito kika ganmu kika koma sae idan mun tashi sae ki sake fitowa ko?cikin rashin fhmta Rynt tace"nifa ba fita zanyi ba kawai na fito ne na tambayeka ina son zanje gidan inna sae na ganka tare da baqo"
qarya kike yawon iskancin ki dai ya fito dake, yawo kuma nida koina bana fita sae zuwa islamiyya,yau d'in ma islamiyya ta fito dake kenan? Gidan inna fa nace maka zan tafi....wace innar byn kullum sae ta tasani gaba na baki wayata kuyi waya! cikin muryar kuka tace"to ai waya daban  yanzu ina son zan ganta ne.....to ba inda zakije don haka koma daga ciki! Uhm Uhm dan Allah.....ya tashi daga zaunen da yake had'e da daka mata kafurar tsawa  har sae da hawayen da suka cika mata ido suka sauko ba shiri, yace"ki wuce nace!
  Jiki ba qwari ta koma d'aki tana kuka.

Shi kuma ya buga tsaki ya koma ya zauna .
  Abokin sa yace"ya kana dakawa mace tsawa haka,irin haka idan tana d'auke da juna biyu ai sae ya zube,wani  mugun kallo mohd ya watsawa abokin nasa snn yace"wane uban ne zai mata juna biyu, to kaddai ka zage ni abu mai sauqi kawai ka sallami ynyr nn ni na samu na aureta don wlh tayi min,da takaici mohd ya sake kallon abokin nasa, abokin yace"to wae naga baka sonta ni kuma da Allah ya hore min sonta ba sae naji da ita ba"mtsw ga dukkan alama sae da kasha ka zo min gida"eh kam amma kafi kowa sanin ni na daban ne don nasha bashi zai sa na fita hayyacina ba,to ka cire sonta don wnn ba mtr aurenka bace, hhhhh wae don tana mtrka hm kamanta waye ni kenan, ko d'aya kawai ba mtr aurenka bace kmr yanda na fad'a ma, ko meyasa?sbd talaka ce er matsiyata shiyasa sam bata cikin tsarina kuma kai nasan ma zaka fi tsanar ta akaina....ai har sonda nake mata ma ya koma tsana don kasan ba abinda na tsana a duniya kmr talaka kuma su da kiyashi duk d'aya ne a gurina sae na taka su na wuce ba komai bane,amma kai ya akayi har ka aureta? Abba ne wlh, wae ya tilasta maka? Eh, hm abinda bazan ta6a d'auka agun iyayena ba kenan,don sun haifeni bashi zaisa su tilasta min kan abinda bnyi niyya ba wlh, gsky Abba ya cuceka,mohd yace"abinda umma ke fad'a masa kenan, wacce tun lokacinda nayi auren nn take fushi dani,nayi vata haquri har ngji tace idan ina son ta hqra sai idan na rabu da wnn yrnyr ko zata janye fushin....mtsw amma kuma shine kake tare da ita har yanzun,hm ina kan hnyar rabuwa da ita amma tsinuwar Abba nake yiwa gudu.... Ya tsine maka man sae me, ai ba akan ka aka fara ba,hm jamil kenan gwanda dai ka rabu da iyayenka lfy shi yafi,kaji matsalarka kullum biyayya wa iyaye ai gashi ka fara ganin illar hkn ansa ka auri mata har biyu kmr wani  bagidajen mutum,murmushi kawai mohd yayi yayinda abokin nasa ya tashi yana fad'in"kaga ni sae anjima dan bazan iya zama ina jin wnn takaicin ba.


Bayan kwna d'aya da faruwar hkn rnr ta ksnce rnr assabar ,Rynt tayi shirin ta na islamiyya tsaf ta fito zata tafi ,a nn falo tayi kici6is da mohd shida malika da suka lula duniyar romance ,da sauri ta kauda idonta zata fita, mohd ya dakatar da ita,ta tsaya ba tare da ta juyo ba ya taso tare da fad'in "ina kuma zuwa?tace"islamiyya mana zan tafi,to na soke islamiyya daga yau!da sauri ta kalle shi tace"meyasa? Malika ta taso tace "amma fa ta rainaka har tmbyr ka takeyi ,yace"ubanta ta raina bani ba,kuma daga yau duk na qara yanke miki hknci kika tambaye ni dalili ni nsn hnkncin da zan miki,snn daga ynx kar na qara ganin kin tako qafar ki a falon nn...kayi dai dai my man don kullum ba abinda nake ji maka tsoro irin kar ta kwaso ciki gurin baqin yawonta azo ace naka ne tunda kaine mijinta,ko yanzun dai Allah ya tsare idan ba a riga an kwason ba, tunda kullum gata nn cikin hijabi kmr wata tsohuwar malama,
Rynt ta kalle ta da kyau snn tace"Shi wanda ya haifeki d'in ma har ya kasa baki tarbiya bai isa yamin ciki ba bare har ayi tunanin laqawa wani  banza can".




Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[1/19/2017]
 🔮```BAZAN  BARSHI BA!```🔮









          🔮🔮🔮
_*page*_ *```31```*
Malika tayi tsaye sororo sbd tsananin mamaki,mohd kuwa kallon Rynt yake kmr wanda yaga abin burgiewa a tare da ita, sbd a cikin kwanciyar hnkli ta saki mgnr kmr ma ba ita ba.
   Rynt kuwa na gama fad'ar mgnr ta juyawar ta zuwa d'aki ,sae a lokacin malika ta saki wani  irin zagi ta tafi fuuu!tabi Rynt tana fad'in"cabd'i lallai yau sae kinsan wa kika ta6o,har ni zaki zaga ki kwashe lfy!

   Koda ta isa d'akin Rynt tuni Rynt ta rufe d'akinta tasa makulli ta kuma je tayi kwanciyarta akan bed, malika ta shiga sirfa bala'i tana dukan qofa kmr zata 6alle qofa, duk Rynt na jinta tayi banza da ita.
   Mohd ne yazo yaja  malika yana fad'in"don't mind her xo mu tafi kawai"tace"banni da er iska tambadaddiya idan ba tsoro ba ta fito mana,wlh ta fito!taga yanda ake quliqulin kubra da mutum.
  Da qyar dae mohd ya samu ya jata suka bar gurin .

2 days a go
Kwata kwata mohd ya daina zuwa d'akin Rynt  dmn zuwa duba lfyrta kmr yanda Abbansa ya tilasta mai, haka kuma bai qara ganin ta fito ba, sam bai damu ba sbd a cewar shi dokar da yasa mata ce tabi.

 Malika kuwa tun a rnr da abin ya faru tayi tafiya da yamma zuwa garin kd gun bikin wata qawarta yayinda ta tafi d'auke da alwashin duk ta dawo sae tayi ma Rynt dukan ftr hnkli.

Kwance  yake a falo shi kad'ai yana hutawa sae ga mami tazo ta same shi tace"dan Allah yaya ina son naci chocolate"sae da ya kalleta snn
ya tashi zaune tare da zaunar da ita kusa dashi yace"to bari na byr a siyo miki"um um yaya inada shi a d'aki amma hannu na bazai kai inda Anti ta ajiye min ba, to kice Antin ta d'auko miki mana, ai bazata iya bane, meyasa bayan ita ta ajiye? Anti bata da lfy fa, ko abinci ma ta daina ci,kullum sae kuka take tayi ,gashi kai baka zuwa kullum bare ma kasani ynx haka ma tun dazu  take son ta tashi amma ta kasa sbd jiri ke d'ibar ta"man yayi shiru yana kallon mami can yace"naji jeki zanzo na duba ta.

Ya jima kafin yake zuwa d'akin don koda ma yaje ya samu har  mami tayi bacci sbd dama dare ne, ya sami Rynt zaune kan bed ta had'e kai da guiwa,sallamar sa yasa ta d'ago wanda kallo d'aya ya mata ya fhmci tana jin jiki,
  fararen idanuwnta duk sunyi jajir yayinda eyelashes d'inta sukayi warawara sbd hawayen da suka ta6a su ,
snn fuskarta fayau ba kwalliya kmr kullum,maida kanta ta koma yi tsakiyar qafafuwanta shi kuma yaje kusa da ita ya zauna kan bedside drawer yace"me yake damunki ne?tayi shiru kmr bata jinsa yace"kina jina fa"tace"nima ban sani ba"yace"to ki shirya zan miki allura ne"tace"bana so"baice mata komai ba sae tashi yayi yabar d'akin,Rynt kuwa sae tashi take sonyi amma ta kasa sbd jiri wacce dama idan tana zazza6i haka yake mata.
  Can ta samu ta tashi tsaye se kawai jiri ya d'ebe taje zuwa fad'uwa,bata fad'in ba sae jin tayi an kamata, a firgice ta juyo tare da fad'in"baffa"sae kawai taga ashe mohd ne riqe da ledar magunguna a hannun shi, wani  irin baqinci taji don ta d'auka ko Baffanta ne ya dawo gareta kmr yanda take mafarki a kowane dare,hawaye ne suka zubo mata bata damu da ta share ba sae jaye jikinta daga nashi tayi snn ta koma ta zauna, mohd kuwa ya d'aura ledar magunguna kan bedside drawer yaje ya d'auko gorar ruwa da cup snn yaje ya zauna kan gadon tare da tsiyaya mata ruwa a cup, ya bata ta kar6a shi kuma ya shiga 6alle magunguna ,ya bata taqi kar6a sae ruwa takai a bakinta tana sha, tayi saurin ajiye ruwan sbd wani  irin abu da taji cikinta nayi na rashin abinci ga ruwa ta kora akai, nn take taji amai ta yunqura zata tashi amma jiri bai barta ba tayi saurin dafa kan gadon gudun kar ta fad'i, mohd yakai  hannu zai taimaka mata, tayi saurin dakatar dashi ta hnyr cewa"bana so"bai kula ta ba sae janta yayi suka tafi bayi don ya fhmci gab take da kwaro aman, suna shiga ta warce hannunta daga nashi ta dafa washbasin tana kwara amai a ciki,kalar aman ya soma tsorata mohd yace"ke wnn aman fa? wani  kallon takaici ta watsa mai tare da fad'in" juna biyu nake d'auke dashi ko da wata matsala ne!
d'an shu'umin murmushi mohd yayi tare da kauda kansa gefe nn idon sa ya hango masa bayan hijabin Rynt da yayi staining da jini, yakai  hannu ya riqo hijabin ya nuna ma Rynt snn yace"ya haka kuma keda ke d'auke da juna biyu sae na sami wnn qazantar a hijabinki ko kuma jin ciwo ne? Kunya Rynt taji sosai tayi saurin kauda kanta tare da fizge hijabinta ta 6oye gurin da yayi staining,murmushi yayi tare da fita bayin.

Hannu takai kan mixer tap ta kunna famfo ta kuskure bakinta ta wanke washbasin taje
a daddafe ta saka key a qofa snn ta cire hijabi har kayan jikinta, ta saka su a bucket ta zuba ruwa da klin bata iya wanke wa ba sae wanka tayi koshi da qyar taga ta samu ta kammala ta d'aura towel ta fito toilet corner ta jawo qaton hijab d'inta har qasa ta zuba snn ta fito,ta sami mohd zaune yana jiran fitowarta wanda baiji fitowarta ba sae qamshin sabulun da yaji sosai hkn yasa ya d'ago ya ganta,ya tashi tare da fad'in "idan kin shirya zan dawo"bata bar sun had'a ido ba ta kauda kanta gefe har sae da taji ya fita snn ta nufi wardrobe ta shirya taje tayi kwance  tare da jan blanket ta rufe jikinta har kanta, sae ga mohd ya shigo d'akin d'auke da freshmilk da kuma plate d'in abinci don ya fhmci aman da tayi na yunwa ne.
   Yaje tare da ajiye abincin kan bedside drawer snn yace"ga abinci nn kici snn kisha magani"
 Nn ya juya zai bar d'akin tace"ni bana cin abinci ka koma dashi"
  Ya dawo tare da fad'in "dolen ki kici don ba ajiye ni kikayi ba da zan kawo maki abu na koma dashi"
   Nn ya tilasta ta kan dole ta tashi zaune, ya dungura mata plate d'in a jikinta ,takai hannu ta ture plate d'in tace"nifa na gaya ma bazan ci ba" kallonta kawai yayi bai ce mata komai ba sae hannuwan rgrsa da ya shiga linkewa shaye da toka yayinda Rynt ke kallon sa da mamaki kaddai d'ura mata abincin zai yi ta qarfi,tana kallo ya d'auki plate d'in  ya d'ibi abincin a spoon ya nufo bakinta dashi kmr zatayi kuka tace"nace maka bana so dan Allah ka barni"daga nn kawai ta fara kukanta a hnkli ba don komai ba sae don tuna baffanta da tayi wanda sam baya takura ta akan komai. Haqiqa tayi rashi babba wanda har abada bazata sami kmr sa ba.
  Tayi minti biyar tana kukanta mai ban tausayi mohd sae kallonta yake wanda ga dukkan alama ta fara bashi tausayi ,a hnkli ya sauke numfashi snn yace"idan kinci zan barki ki koma islamiyya kuma zan barki kije gidan inna"da sauri ta kalle shi snn tayi magana cikin muryarta ta marasa lafiya tace"dagaske kake?ya gyad'a mata kai snn takai hannu takar6i plate d'in abinci tana mai kallon shi tace"ka tafi kawai zanci"
ba musu ya tashi ya fita don ya fhmci bata iya cin abinci a gaban idon sa ne.
  Sae da yayi wanka ya kuma yi shirin bacci snn ya dawo d'akin ya samu taci abinci kmr yanda tace ta kuma sha duk wasu magunguna da ya 6alle mata,yakai hannu ya d'auki plate wanda ke d'auke da ragowar abinci snn ya kalleta sae sharar baccin ta take cikin natsuwa.

Wayar sa ce tayi qara ya saka ta a silent snn ya d'aga had'e da fita d'akin.

Washe gari Alhmdlh jiki ya fara yiwa Rynt sauqi don da taje wanka har kayan da ta jiqa cikin bucket jiya ta wanke abinta tas taje ta shanya.
   Byn ta shirya snn tayi breakfast ta koma ta kwanta sbd zazza6in bai qarasa sakinta ba,ba jimawa bacci ya kwasheta sae ga mohd ya shigo d'akin riqe da hannun mami,yaje kan bedside drawer ya zauna mami kuwa ta hau kan gadon tana fad'in"anti ma tayi bacci"
Komai mohd bai ce ba sae hannun sa ya d'ora kan goshin Rynt,sae kawai yaga ta bud'e idanuwanta a hnkali ta sauke su akan nashi, ba tare da ya sauke hannun sa da ke kan goshinta ba yake tambayar ta "jikin fa?


Billy giro
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[1/20/2017]
 🔮```BAZAN  BARSHI BA!```🔮









          🔮🔮🔮
_*page*_ *```32```*
Shaye da toka ta janye hannunsa snn tace "Alhmdlh"
Shi kuma ya màida dubañsa gun mami yace"bani ruwa gasu can a bayanki kan bedside drawer, mami ta kawo mai ruwan ya kalli Rynt da tun d'azu ta juya bayanta dmn ci gaba da bacci,yace"tashi kisha magunguna idan ba haka ba ciwon zai sake dawo maki ne"
  Ba musu ta tashi zaune ,har zai 6alla magungunan sae kuma ya kalleta yace"ko kina so na had'a miki da allura sbd naji jikin naki da zafi kuma zaki fi jin sauqi a take"kallon sa tayi ,sae kuma tayi shiru don dai tana son samun sauqi nn take kam ko don zuwa islamiyya ta kuma samu taje gidan inna, amma bata jin zata iya  bashi wani  guri a jikinta ya mata allura,cikin sanyin murya tace"Aa bana son allura zansha magani kawai"
  Bai musa mata ba ya bata magungunan tasha, snn ya tashi zai fita,mami tace"nazo mu tafi yaya"yace"Aa mami asibiti zan tafi"tace"yaya ina zuwa ko can d'in ne"yace"mami idan yawo kike so bari gobe zaku fita keda Anti kinji"yaya to ai anti bata da lfy kawai wayo kake so kamin"ta qarashe mgnr ne kmr zatayi kuka yace"zo"
tazo gurin shi ,ya rage tsawon sa tare da kai hannu ya shafo fuskarta yace"kar kiyi kuka ba wayo nake miki ba dgske nake zaku tafi yawo gidan inna idan anti taji sauqi kinji"to yaya haka ko jiya da dare nayi ta jiranka kazo ka d'auko min chocolate har nayi bacci baka zo ba"eyyah mami ai kina ficewa aka sallama min sae ya kasance koda na dawo na samu har kinyi bacci amma yanzu nuna min inda chocolate d'in yake sae na d'auko miki ko"hannunsa taja tana fad'in "muje kaga ai a wardrobe d'ina ne amma can sama, nn ta bud'e wardrobe d'inta ya d'auko mata ya vata, ta kar6a cike da murna shi kuma ya fita, Rynt dake kallon su sae mamaki take irin yanda yake shiri da mami amma kaf sauran qannan sa tsoronsa suke ji.

A washe gari ne mohd ya cikawa Rynt alqawarinta yakaita gidan inna ita da mami suka yini sae dare ya maida su.

D next day Rynt ce a d'akin mohd tana gyara mishi d'aki sae ga malika ta shigo d'akin wacce saukar ta kenan, wani  irin farin ciki ta sami kanta dashi ganin Rynt a d'akin,ta rufe qofa da makulli ta kuma cire makullin ta jefa a jakarta a cewar yau ko ita ko Rynt dole ne a kwashi gawar d'ayan  su,sae da tayi d'amara snn ta shiga dube dube taga ko zata sami wani makamin da zai raba Rynt da duniya zama d'aya ,can taga tunda ta rasa makami , abnda yafi kawai taje da qarfin tsiya ta kwashi qafafun Rynt ta yanda idan takai qasa sae dai wata ba ita ba.
   Tana gama yanke  shawara ta nufi Rynt gadan gadan wacce sam bata san da shigowar malika ba sae aikin gabanta take,ai kuwa kai tsaye taji an kwashi qafafunta kafin takai qasa ta buga ihu cike da mugun jin tsoro,malika kuwa a maimakon taga Rynt qasa sae ganin ta tayi a jikin mohd,wani  baqinci ne ya tokare ta a wuya ganin Rynt male male a qirjin mohd sae baqin ciki biyu suka tara mata,cikin azama ta ciro takalmin ta mai d'an karan tsini zata dokawa Rynt shi a ka mohd ya riqe mata hannu da d'ayan hannunsa sbd d'ayan hannun yana rungume da Rynt ne wacce tuni ta some kan tsoratar da tayi,ya fizge takalmin had'e da
daka mata tsawa yace"meye haka,me ta miki keda yanzu ne dawowar ki!bata kula shi ba sae d'ayan takalminta ta ciro tana fad'in"cabd'i har ka manta zagin ubana da tayi kenan,wlh yau sae tasan ba irin mu ake zagi a zauna lfy ba!tsaki yayi ya sake fizge takalmin ya kuma ture ta, tayo kukan kura ta ture Rynt daga jikin shi,
 nn Rynt ta fad'i kanta ya daki gefen gado,bata barta ba tayi kanta zata fara kai mata duka,mohd ya rirriqeta ta shiga kokawa dashi na ganin ta qwace kanta,bata iya qwatar kanta ba sae mohd d'in ne yaga dama ya saketa tare da fad'in" can't u see she is unconscious,to bari kiji wlh duk kika ta6a ta zanyi maganin ki ne kuma ki gwada ki gani kin dai san hali na ba sae an gaya miki"
  Tace"wlh ko ba yau ba sae na hallaka ta kuma bari ka gani kul ba dad'e kul ba jima kuwa"
 Daga nn taje ta bud'e qofa ta fita sae masifa take tayi.
  Mohd kuwa d'aukar Rynt yayi ya d'ora ta kan bed, snn ya samo ruwa ya shiga yayyafa mata a fuska, cikin ihu da firgici ta tashi ta qanqame mohd tana karanto addu'o'i sbd duk d'aukar ta aljanu ne suka cirata sama,duk tabi ta firgice tana ta mai kuka,ya qara rungume ta a jikin shi yana kwantar mata da hankali,sae can ya samu hnklinta ya d'an fara dawowa gareta,inda a hnkli yaga takai hannu kan gefen goshinta gurin da kanta ya daki gefen gado, ta d'ago hawaye tap a idonta tana kallon shi,yace"da zafi? tace"wlh d'akin nn naka aljanu ne dashi kaga har sun jimin ciwo"kallonta kawai yake bai ce komai ba sae hannun ta ya janye yana duba gurin, gurin yayi ja har ma yad'anyi lolo kad'an, nn ya lumshe ido tare da shirin maida ta kan qirjinsa had'e da cewa "sorry".
  Cikin tsananin mamaki da jin haushi ta kalli abinda yake shirin yi don sae a lokacin hnklinta ya gama dawowa jikinta,ai kuwa tayi saurin hana faruwar hkn ta tashi da sauri zata bar gadon ,by mistake hannunta ya latsa wani guri a jikin gadon abin mamaki da ban tsoro a gun Rynt sae kawai taga wasu silalan fararen qarafe na fitowa kowane gefe  ta jikin gadon,ihu ta saki ta sake komawa jikin mohd ta qanqame shi amma ta kasa d'auke idon ta akan abinda ke ci gaba da faruwa don wani farin qyalle tagani shar shar kmr net yana biyo ta jikin qarafen har ya lullu6e su sae gadon ya zama kmr suna cikin wata kyakkyawar rumfa ne mai kyan gaske.
  Kuka ta fashe masa dashi tace"wlh na gaya ma d'akin nn aljanu ne dashi dan Allah ka ftr dani ,na roqe ka"
  Kallon ta mohd keyi yanda ta rud'e sosai tana kuka don jikinta har qyarma yake,yakai  hannu ya danna wani  guri a jikin gadon sae kawai komai ya shiga komawa a hnkli har gadon ya zama tamkr ba shine ya musu rumfa a d'azun ba.
    Ya kalli Rynt dake qanqame a jikin shi snn yace ni d'akina ba aljanu gidadanci ne kawai irin naki sae ki tashi ki fita duk kin wani  cumuimuyen min a jiki haka"cikin kuka had'e da masifa tace ba aljanu amma d'azun aka kwasheni akayi sama dani"yace"wnn kuma ya rage naki nidai ki fita nace"tace"ai ko baka ce va ynxn fita zanyi"
ta fad'i hakane kawai amma kuma bata iya sauka kan gadon sbd tsoron kar ta sake ta6a wani  gurin, ganin haka yasa mohd ya saukar da ita, ta kalle shi shaye da toka snn tabar d'akin,cike da alqawri a ranta bazata qara tako qafar ta a d'akin ba.

Haka ko akayi don tun daga rnr Rynt bata qara komawa d'akin mohd ba ,wanda yanzu an d'auki lokaci sosai don har su saliha sun dawo hutun makaranta suna batun komawa first term.
 Duk tsawon lokacin nn mohd shi ke gyara ma kansa d'aki sbd duk lokacinda ya aika mami Rynt taxo ta gyara mai d'aki sae tace bata jin dad'i.
  Malika kuwa takaici ma ne yace ta gyara mai d'aki don acewar shi in banda qara lalata mai d'aki ba abinda ta iya.

Yau ya dawo a gajiye daga asibiti ga d'akin nasa yana buqatar gyara ya aika mami yace taje ta gaya ma Antinta tazo ta gyara mai d'aki ta dawo masa tare da saqon wae anti tace bata jin dad'i.
  Tashi kawai yayi ya tafi sae d'akin Rynt ya sameta zaune tana duba littattafanta na islamiyya sbd rnr,rnr alhamis ce basa zuwa islamiyya .
  A fusace ya d'auke littattafan ya d'aura su kan bedside drawer snn yace"bana son raini tashi kije ki gyara min d'akina! Shaye da toka tace"nifa bana jin dad'i"da Allah maza tashi ai baki zo nn gidan dan kiji dad'i ba!tace"nifa ina nufin bana da lafiya.....cikin mugun hasala ya nuna ta da yatsa yace"kar ki kuskura na koma jin wnn kalmar a bakin ki, yau wata kusan nawa kenan duk nace ki gyara min d'aki kice ba kya jin dad'i sbd kin raina ni ko shine har kike tunanin zan ci gaba d'aukar miki rainin,to bari kiji wlh duk baki je kin gyara min d'aki ba ,ba ke ba zancen bokon nn kuma ba wanda ya isa ya tilsatani na saki!daga haka ya fita kmr zai tashi sama, yabar Rynt qwallah cike tap a idonta tana tunanin in taje aljanun d'akinsa zasu iya sake cirata sama su yar wata qil ma wnn karon mutuwa zatayi ba suma ba, gashi kuma bokon nn tayi bala'in qwallafa ranta akai har kullum ma qidayar kwanaki take inda yau sauran ta kwana uku ta fara zuwa mkntr boko gashi har ma an d'inka mata uniform saura littattafai da takalmi.
       Tana cikin share hawayenta ne sae ga saliha ta shigo, tace"Rynt lafiyar yaya naga yaja mota a hasale  ya fita! Rynt tace"Yauwa saliha tun da ya fita dan Allah taimakamin kije ki gyara masa d'akin sa...ke wlh ni bazan iya da halin yaya ba kawai kije ki gyara masa keda yasa,saliha bazan iya bane d'akinsa tsoro ake ban dan Allah ki taimakamin kije ki gyara masa kafin ya dawo wlh yace idan ban gyara masa ba bazan yi boko ba kuma kinfi kowa sanin yanda nake son nayi bokon nn"ta qarashe mgnr kmr zatayi kuka saliha tace"nifa fad'an sa nake yiwa gudu ba komai ba"Rynt tace"kawai kije ki gyara duk fad'an da zaiyi aini zai yiwa tunda bai san cewa ke kika gyara d'akin ba, shiyasa ma nake son kiyi sauri kafin ya dawo dan Allah.
  Da qyar dai saliha ta yarda ta tafi,wacce ta fara gyra masa d'akin kenan sae ga mohd ya shigo d'akin fuskar d'auke da 6acin rai sosai.

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[1/22/2017]
 🔮```BAZAN  BARSHI BA!```🔮









          🔮🔮🔮
_*page*_ *```33```*
 Gabad'aya saliha ta gama tsorata da ganin yanayinsa,yayinda take roqon Allah yasa ta 6ace 6at kafin ya qaraso gareta.
   Mohd kuwa a fusace ya qaraso gab da ita  sae huci yake yace"uban me kika zo yimin a d'aki !dake nake ki bani amsa!! A tsorace tace"yaya wlh  qaddara ce amma don Allah kayi haquri wlh Allah bazan sake ba"
   Kunnen ta ya kama ya shiga yi mata fad'a sosai sae kuka take tana bashi hqr sae can ya sakar mata kunne yace"Oya fita na daina ganin ki a nn stupid gal!da sauri ta fita d'akin har tana had'awa da gudu,sae ga malika ta shigo  d'akin wacce dama ita ce ta kira mohd a waya ta snr dashi cewa Rynt fa taqi zuwa ta gyra mai d'aki kmr yanda yace,sae saliha tasa a cewar ita ta gaji da gyarawa qaton banza d'aki.


Dmn duk wani  abu da ya faru na fad'an da mohd yaje yayiwa Rynt tana la6e,har ma lokacinda saliha tazo duk sae da taje ta la6e,shine fa ta had'e qarya da gsky ta gaya mai.

 Tace "wlh my man wnn abar ta rainaka da yawa amma ka kasa maganin ta na rasa meyasa,yace"ni kaina malika na rasa meyasa ta raina ni haka wlh!
  Hm my man maganinta ne bakayi shiyasa.
  Tsaki kawai yayi ya fita daga d'akin.

Saliha kuwa tana fita d'akin Rynt ta nufa tana shiga Rynt tace"ya akayi ne saliha ko ya dawo ne? Komai saliha bata ce ba sae d'aukar jakarta tayi ta fita.
  Rynt ta biyota tana fad'in "saliha kimin bayani mana"
sam saliha bata saurara mata ba tayi ficewarta.
  Ita kuwa Rynt tana kawowa bakin qofa tayi kici6is da mohd da qarfi ya turata ta koma ciki ya kuma rufe qofar da key.
  Inda kai tsaye ya yakai hannu kan wuyan hijabinta ya rabashi biyu, a firgice Rynt tayi saurin kama hijabin ta riqe tace"malam meye haka dan Allah!
bai kulata ba sae hijabin ya fizge ya yar ,ta koma d'auka ta rufe jikinta.
 Sai kawai yaje yayi zaune abinsa kan sofa  ya d'aura qafa kan qafa yana juya belt d'in hannunsa a hnkli snn ya kalli Rynt da taje jikin wardrobe zata nemo wani  hijabin yace"ki ma daina wahaladar da kanki don kaf kayan jikin ki ne zan raba ki dasu sbd ni sam bana dukan mutum da kaya a jikin shi, ta fiddo ido waje cike da tsoro tace"kenan kai d'an iska ne"yace"eh sosai yanzu kuwa zan nuna miki"ya taso gadan gadan zai zo gurinta.
  Tace"Aa dan Allah kayi haquri wlh zanje na gyra ma d'akin ka indan shine "
   Idan na gama dukan ki ba ya fad'i hankane tare da fizge hijabinta ya jefar ya kamo wyn rgrta zai yaga...tace"wayyo dan Allah kayi hqr"ta qarashe mgnr tare da fashe masa da kuka tana roqon shi yace"shin saliha bata gaya miki horon da nake musu bane da suna en yara"cikin kuka sosai had'e da girgiza kanta tace"wlh Aa bata gaya min ba"yace"to kiji kaf qannai na duk wanda yamin laifin duka se ya cire tufafin sa nake dukan sa sbd ni ba sakaran mutum bane da zan daki mutum da kaya a jikin shi, kuma duk na daki mutum sau d'aya to ko da kuskure bazai qara min laifin da zan sake dukan shi ba, amma ke sbd a iya qafafun ki kad'ai na daka shine kika sake min wani  laifin duka wae har ni zaki duba ki kira qaton banza,yana kawo nn sae jin tayi bata tare da rgr jikinta don zama d'aya ya yage ta ya jefar ,ya zamo vest kad'ai ke jikinta sae kuma zani ,wani  irin kuka ta fashe dashi mai cin rai had'e da saurin durqushewa qasa,tana girgiza mai kai tana ja baya sbd yanda yake matsowa kusa da ita, cikin zafin nama ya miqar da ita tsaye tayi saurin sa hannayenta ta kare qirjinta tace"idan kai musulmi ne na roqe ka da girman Allahn da muke bauta ma kar ka rabani da kayan jikina"hannu yakai ya jaye tsorayen kalabarda suka soma rufe mata fuska snn ya d'ora hannayensa kan kumatun ta da hawaye keta fmn sintiri yace"na barki sbd girman fiyayyen halitta amma ki sani bake ba boko har abada!
  Nn ya juya ya fita ,ita kuwa taje kan bed cikin tsananin kuka taja blanket ta rufe jikinta har wuya nn ta had'e kai da guiwa tana ci gaba da kukan da duk wanda ya gani zai d'auka ko kaf duniya an mutu ita kad'ai aka bari a raye sbd baqin cikin yanda ya rabata da hijabinta har rgrta sae duk taji duk duniya ba wanda ta tsana kmr shi,sbd still cikin su ukun nn tafi yarda a ranta cewa shine dai makashin babanta.
  Qofa taji an turo tayi saurin d'agowa don ta d'auka ko shine ya dawo, sae taga malika ce wacce ke d'auke da shu'umin murmushi a fuskar ta tace"kad'an kenan daga cikin sharrin na,dmn ni ba'a taka ni a zauna dai dai,inace yanzu kin fara ganin kuskuren ki na auren mijin da ba naki ba,wanda kwata kwata ba'a halitto shi wa kowa ba sae ni kad'ai,amma sbd kwad'ayin duniya irin naki kika shigo sabgar da ba taki ba,kika lalata min tsarin rayuwata gabad'aya, to bari kiji wlh idan har bakiyi gaggawar rabuwa da mijina ba nice zan zamo ajalinki.
  Kmr bada Rynt take zancen ba don tun lokacinda Rynt ta d'ago taga wace ce ta maida kanta kawai taci gaba da kukanta,har kuwa ta fita.

Har kusan kwana biyu Rynt bata bar kukan abinda mohd ya mata ba sbd taji ciwo sosai fiye da zaton mai karatu,dmn idan aka cire mutuwar mahaifinta to shine abu na farko da tafi jin ciwon sa a duniya.

Duk kwana biyun nn mohd na shigowa d'akin Rynt da safe kafin ya tafi asibiti,wanda duk shigowar da yake ganin ta yake zaune kan bed ta had'e kai da guiwa kuma har ya fita bata d'agowa bare zancen gaida shi.

 Sallar zuhur ta gama snn ta tashi tayi shirin islamiyya ta fita.
  Bayan sun tashi da qarfe hud'u a maimakon ta koma gida sae napep ta nema ta tafi gidan inna.


Mohd na zaune shida malika kan dining inna ta kirashi a waya sae masifa take mai,
 kan dole ya ajiye zancen cin abinci ya tafi gidan inna.
   Inna tasa shi d'aki shida Rynt tace"sae naji Rynt tazo min da wani  zance wae ba zaka  barta tayi boko ba,yace"bata snr da ke laifin da tamin bane inna.....Yo dan bata je ta gyara ma d'aki ba har shine wani  laifin da za kace ba za tayi boko ba,to bari kaji ubanka kabiru ma bai isa ya hanata bokon nn ba bare kai,boko kam sae Rynh tayi shi kmr kowa don ba za'a barta a baya ba,kuma dolenka ka d'auki nauyin krtn tunda mtrka ce,yace"gsky inna kiyi hqr don na riga da yanke hukunci.....inna ta dunqule yatsu ta watsa mai tace"ubanka! nace ubanka kabiru! yo har ni zaka duba kace ka rigada ka yanke hknci sbd ban haifeka ba ko,ko d'aya ba hk bane inna sae fa da na gaya mata duk bata je ta gyara min d'aki ba bokon ta ne haka wae shine don ta raina ni ta saka saliha wai ita ta gaji da gyrawa qaton banza d'aki har ni zata kira qaton banza !Rynt tace"wlh Allah inna bance masa qaton banxa ba..... A fusace mohd ya taso xai bugewa Rynt baki, tayi saurin tashi ta koma bayan inna ta la6e ,inna ta tashi tace"yo da dukanta zakayi to"cikin yanayi na 6acin rai yace"to inna ni sa'anta ne da zata qaryata"
inna tace" lallai Muhammadu sam albasa bata biyo hln ruwa ba indai kace dukan mace kake, don ubanka kabiru duk iya shegenda uwarka take mai bai ta6a sa hannu ya dake ta ba, kai kaf ubannanka ba mai dukan matar sa, sae kai zaka ce ka fara sbd baqin zuciya irin taka,
 nn ta maidà dubanta gun Rynt da ta soma kuka tace" zo zauna abinki ya dake inga inshi shashan yaro ne.
 Sae da ya koma ya zauna snn Rynt ta iya zama yace"inna ki barni kawai da yrnyr dan Allah ki ftr da bakin ki a cikin zancen nn......naqi na ftr d'in shashan yaro ai kwanaki kafin aurenka zowa kayi nn ka nemi na roqa maka alfarma agun mahaifinka don ka samu kaga ka auri wnn yrnyr er marasa mutunci ,shine yanzu tunda burinka ya gama cika har ni kake cewa na daina sako bakina a cikin zancen ka ,iye lallai Muhammadu yau ka nuna min ban isa dakai ba.
  Ta qarashe mgnr ne cikin muryar kuka irin nasu na tsafi d'in nn.
  Cikin nuna damuwa mohd yace"inna ba haka bane wlh yrnyr nn tafa ranani sosai wanda dole ya kamata ace na d'auki mataki akai......yo muhammadu ita Rynh d'ince ta rainaka yrnyr er albarka wacce ba ruwanta da kowa, kuma ai tunda na sako bakina a ciki ya kamata ka haqura koma mene ne idan kuma banda wani  matsayi a gurinka shikenan sae ka tashi ka tafi ai inada kud'in da zan sata mkrntr ba wai rasawa nayi ba.
  Kauda kansa yayi gefe cike da takaici yace"ki barshi kawai zan sata d'in"
  inna tace"bama so! kuma idan kaje gidan naka ka aiko min da duk kayan Rynh don a nn zata zauna tayi bokon ta"
  Nan Mohd ya shiga ba inna hqr ba don yaso ba har ya samu ta haqura.

A tare suka fito shida Rynt wacce har takai hannu zata bud'e murfin mota ta shiga ya daka mata tsawa yace"bana son raini tare mukazo ne!
  Kallon sa kawai Rynt tayi snn ta juyawarta ta kama hnyr fita riqe da er ledar ta da inna ta bata mai d'auke da kular d'an wanke a ciki.

Tana fitowa gate d'in gidan sae mota ta gani a gabanta ta faka, snn aka zuge glass d'in motar a hnkli
qoqarin kaucewa take sae taji muryar munir yana cewa"Rynt ina yini"kallon sa tayi sae kuma tayi saurin sadda kanta qasa tace "yaya munir barka da wuni"yace"lfy lau yasu inna da mohd tace"suna lafiya"

Dukkan su sukayi shiru can munir yace" Rynt sae kuma naji.... yayi shiru sbd hawayenda suka cika mai ido, Rynt ma hkn ce ta kasance a gurinta,kmr daga sama taji muryar mohd yana cewa"ke je shiga mota gani nn zuwa.
  Ba musu ta wuce sbd kar kukan da take ji ya qwace mata mohd kuwa ba yabo ba fallasa ya ba munir hannu suka gaisa har ma yana tmbyrsa mutanen gida.

Sai da suka gama gaisawa snn munir yaja motarsa shi ma mohd yaje ya shiga tasa motar,
 Da shigar sa ya kalli Rynt wacce tayi saurin sa hannu tana share hawayenta,kauda kansa yayi had'e da tsaki snn yace"da kina sonsa meyasa baki aure sa ba sae ni kika cutar"komai dae Rynt bata ce mai ba sae kauda kanta tayi gefe tana kallon titi.


Da dare Rynt ce ta gama sllr isha'i  tayi zaune shiru tana tuna  irin wnn lokaci ne byn sllr isha'i mutanen qauyen su suka d'auki gawar mahaifinta izuwa maqabarta har tabi su tana ta kuka har sae da matan qauyen suka rirriqe ta......shigowar mohd ne ya katse ta ta kalle shi sau d'aya ta kauda kai tare da kai hannu ta share hawayen fuskarta.
  Yazo ya miqa mata wata babbar leda dake hannunshi  yace"kar6i"ta kai hannu ta kar6a ba tare da ta ko kalle shi ba"yace"fito da duk abubuwan da ke cikin ledar"
  Sae da ta qara share hawayenta snn tayi komai yanda yace.
School bag ce baqa mai kyau wankan gefe da littafan makaranta  da biros da duk wani abu dai na aikin aji sae takalman mktrnta baqaqe da farar socks har da sabon niqabi yace" ki gwada takalman idan sun miki shikenan idan kuma basuyi ba kibawa mami ta maida min"
   Still sae da ta sake share qwallah snn ta gyad'a masa kai, shi kuma ya fita ba tare da ya damu da ganin kukan da take ba.


Koda ta gwada takalmin dai dai qafar ta takai ta ajiye komai a cikin wardrobe d'inta sae ga mami ta shigo d'akin itama da nata kayan makarntar sae murna take itama za'a sata boko.

Washe gari da safe mohd ya shigo d'akin yace da Rynt ya kyn komai yayi?tace"eh amma uniform sun min yawa, yace"u are very stupid! tun yaushe uniform d'in suke hannun ki baki tashi gaya min ba sae yau, wae ke bagidajiya ko, nifa ba haka bane ban duba kayan bane sae yau, oya je gwada kayan kixo in gani,tace"kawai  ni a rage min ba sae na gwada ba"yace"ai sae kiyi ta zama dasu hkn nn tunda baza ki iya gwadawa ba, ya fad'i haka ne tare da juyawa zai bar d'akin tayi saurin cewa "dawo zan gwada,nn yaje kan sofa ya zauna ita kuma ta nufi toilet ta sako kayan ta fito tana d'an kame kame, qyar Man ke kallonta don bai ga abin kame kame a jikin ta ba, kawai dai ya fhmci yrnya ce sosai har dai da ta sanya uniform amma duk da haka dai   baza tayi J.s.s ba  SS one yake da burin sata in yaso ya kira mai lesson ya qara fhmtar da ita a gida.
  Yace"je cire kayan ki kawo taje ta cire ta kawo mai

Bai kar6i kayan ba sae tsaki ya mata snn yace"to haka kike nufin zan fita da kayan ba leda"
  Kai tsaye taje ta saka kayan a leda ta kawo mai ya kar6a ya fita.
  Ajiyar zuciya ta sauke sbd ganin masifa irin tashi koba komai dai zata bishi a hnkli don ganin ta samu tayi bokon nn tukun.

Sae dare ya maida mata kayan yace taje ta koma gwadawa ya gani idan sunyi,ta nufi toilet taje ta sako ta fito,abin mamaki idon sa ya kasa d'aukewa akan albarkatattun qirjinta da suka ciko rgr sae rgr ta mata mugun kyau,har dai da ta kasance farar riga ce mai dogon hannu da kuma corler ,saurin kauda idon sa yayi ya maida duban sa ga baby face d'inta yana mamakin jiya da ta saka kayan bai ma ga qirji a tare da ita ba ko don tufafin sun mata yawa sosai ne ,
nn dai ya basar  yace"oya je cire rgr ki kawo min"taje bathroom ta cire uniform d'in ta kawo mai ,riga kawai ya kar6a ya bar wando a hannunta,tana tsaye ya bud'e buttons d'in rgr ya birkice ta,yaga da aka rage rgr ba'a yanke ta ba,hkn yayi masa dad'i don walwale d'inkin yake so zai yi ya maida ta er gidan jiya.
  Ya d'ago ya kalli Rynt tare da fad'in"bani reza"tace"me kuma zakayi?yace"har kya tambaya ke baki ga yanda rgr ta miki bane"tace"nifa dai dai tamin kuma haka nake son abuta"yace"kina da hknli ya zaki je da wnn riga a makaranta"tace"to ai da hijabi akai...koda hijabi akai idan aka yi rashin sa'a iska mai qarfi ya kad'a hijabin yazo ya kwashe malaman mkrntr suka ga yanda rgr ta miki kice me!shaye da toka tace"me kuma ya kawo wnn tunanin"tsaki kawai yaja tare da jefar da rgr ya fita daga d'akin.
  Ta bishi da ido tare da ta6e baki snn taje ta d'auki rgr ta linke kayan ta saka a wardrobe.

Washe gari ne Monday tasha fad'a sosai a gun man kafin take gama shiri sbd tayi lettin tashi.

Sunyi kyau sosai ita da mami dmn uniform d'in sun kar6e su.
  White hijab ,white head tight ,farar riga da kuma blue d'in wando, amma ita mami akan fara rgr ta akwai handlees jacket snn hijab d'in qarami ne sosai don da kad'an ya wuce wuya,na Rynh kuwa ya kai mata a cinya wanda tsaf ya rufe farar rgr da ke ciki.
  Duk makaranta d'aya za'a kaisu sbd makarantar tun daga kan nursery up to  secondary school ake yi a ciki kuma mkrntr intanational ce ba laifi.

Malika ce can sama a balcony tana shan iskar safiyar rnr ,sae dariya take hango Rynt da tayi wae ace zago zago da ita sae yanzun zata fara secondary school ko ya en j.s.s one d'in zasu kalleta ne oho,nn ta koma kwashewa da wata dry.

 6angaren su Rynt kuwa man ne ya fito gidan sauri sauri wanda duk fad'an da Rynt tasha kan lettin da tayi sae gashi ta riga shi kammala komai ita da har mami sae da ta shirya ma.
  Yana isowa gurin ya kalli Rynt yace"bangane ba haka kike nufin zaki tafi fuskar ki a sake sae kace mai tallar fuska"tace"kmr ya bangane ba? Yace"bana son raini ina niqab d'inda kika gani a tare da kayan ne"tace"niqab a boko kuma ba sae lokacin islamiyya ko zan saka ba"ya watsa mata mugun kallo snn yace"da Allah malama ciro ki saka bana son raini!
  Rai 6ace ta bud'e jakarta ta shiga fito da littafan ta long books da suka nemi cika mata hannu bata kuma kai ga niqab d'in ba.
  Mohd yace"kar ki 6ata mana lokaci malama a ina niqab d'in yake? Tace" yana  a cikin jakar"nn yasa hannu ya ciro niqab d'in,inda kai tsaye ya d'oro goshinta a qirjinsa yana d'aura mata niqab d'in sbd baya jin zai iya jiranta har ta mayarda littafan da ke hannun ta.
  Niqab d'in sae ya mata kyau sosai sbd yanda yalwatacciyar girarta ta fito tmkr ansa gazal had'e da manyan idanuwanta farare  da kuma rabin karan hancinta ba kmr nata na islamiya ba da ba'a ganin komai na fuskarta.
 Mohd kuwa kallon wuyanta yake ta jikin hijabinta da yaga alamar bata kwantar da  kwalar rgr ta ba.
  Guntun tsaki yayi had'e da zira hannun sa cikin hijabinta yana gyara mata kwalar rigar.

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[ 1/24/2017]
 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮









         🔮🔮🔮
*page* *34*
Saurin ja baya Rynt tayi shaye da toka tace"meye haka wae? Mohd ya dalla mata harara yace"bana son raini fa daga kawai kin samu na taimaka miki,da haka zakije collar riga a tsaye kina nuna musu asalin ke bagidajiya ce"
  Kallon sa tayi rai 6ace wacce ko niqabin da ya d'aura mata wani irin haushi ya bata har niyyar tayi ma ta ture shi sae kuma ta tuna mami na gurin.
  Yace"da Allah shiga mota kinyi tsaye kina kallon uwa wani  baqonki!
  Nan taje ta shiga motar zuciyar ta sae quna take.
  Malika kuwa tun lokacinda taga man zai d'aurawa Rynt niqab ta sami kanta da miqewa zumbur sae kawai taga abinda yafi hkn wato hannun sa da ya zira a cikin hijabin Rynt.
A zafafe cikin masifa ta kama hnyr saukowa ,sae dae koda ta fito tuni motar su tabar gidan.
  Wani  irin qololon baqin ciki ne ya tokare ta a wuya, tace"kut zai dawo ya same ni ne wlh"

Nan tayi zaune a falo sae zaman jiran sa take wanda yayi 30 mnt kafin yake dawowa, yana shiga ta tari gaban shi riqe da qugu  ,yace"ke lfyrki meye hk? cikin masifa tace "har ka tambaya wane irin abin kunya ne naga kana aikatawa a d'azun ,bayan ka d'aura mata niqab bai ishe ka ba shine ka wani  xira haunnunka a cikin hijabinta tir!A fusace yace"ba a hijabinta na zira hannu na ba a cikin rgrta na zira, very stupid in ke uwar cikina ce da zaki wani  tasa ni gaba kina tuhuma ta da wani  banzan shirmen ki can.
 Nn ya buga uban tsaki ya ra6a ta gefenta zai wuce, tayi saurin shan gaban shi ya dalla mata muguwar harara, da kanta tayi saurin bashi hnya ya wuce ta bishi da ido har sae da ya shige 6angaren shi snn tace"cabd'i lallai sae na tashi tsaye akan wnn er iskar yrnya,kai kuma dani kake zancen wlh zamu had'u a d'aki ne ai!snn ta tafi fuuu!zuwa d'akinta.

Rynt kuwa gurin assembly students sae tsegumin ta suke ganin ta sanye da niqab kowa sae fad'in albarkacin bakinsa yake masamman da suka shiga class daga mai fad'in"ita wnn fa daga ina muka had'u da ita, sae me cewa qara'i sa niqab a secondary school ban ta6a gani ba, wata tace"hm koda kud'i wlh ba abinda zai sa na laqa wnn abun a fuska ta, wata tace inaga fa mtr aure ce don bazata sa niqab hk kawai ba, tace"wace mtr auren er qarama hk da ita kuma a ina kika ta6a ganin mtr aure a secondary school ai ko aure aka mata bata qare secondary school ba to sae dai kawai azo a zana mata waec n neco ,kawai dai inaga ma wani  ciwo take d'auke dashi daya lalata mata duk rabin fuska shine akayi dabara da hkn.
 Duk  zancen nn Rynt na jin su sae duk haushin man ya turniqeta don ganin take duk shine yaja mata wnn srtn gashi ta tsani irin haka,ai kuwa kai tsaye tasa hannu ta cire niqab d'in,masu gulmar ta suka ce"lah ashe yrnyr lafiyarta qalau ra'ayi ne kawai,yayinda wata ta kusa da seat d'in Rynt ta matso a hnkli tace da Rynt"sister meyasa kika cire niqabin nn kinyi kyau wlh bare gashi klr wandon uniform kuma yadin sa mai laushi da santsi baki ga yanda yayi kyau akan hijabin ki fari ba wlh da kin mayar zaifi ,tayi magana ne yayinda ta kar6i  niqabin a hannun Rynt tana dubawa sbd ita dgske take yayi kyau,tace"ki myr kinji sister"Rynt tayi d'an guntun murmushi tace"ai zan mayar"ta fad'i hk ne kawai don ta huta da srtn yrnyr.
Yrnyr tace"ok"
  Daga nn sukayi shiru sae ga wani uncle ya shigo riqe da register a hannun shi duk suka tashi tsaye suka gaida shi sae da ya amsa snn ya basu ixinin zama shima yaje ya zauna ya fara kiran sunayen su d'ayan bayan d'aya har ya kawo gun sunan Rynt da ya ji sunan ya soma masa wuyar fad'a sbd ba bahaushe bane shiyasa wasu abubuwa ke masa wuyar fad'a,wanda a lokacin da Rynt ta amsa sae da ya kalle ta dan ganin mai sunan.

Sae five aka tada su sbd makarntar had'e take da islamiyya.

  Suna a tsaye ita da mami suna jiran tahowar man,nn Rynt ta ciro niqabinta ta  d'aura sbd gudun masifar man, d'aura niqabin keda wuya sae ga  motar man ta kunno kai.

Da kanshi ya fito motar mami taje  aguje ta rungume masa qafafu ,d'aukar ta yayi tare da kallon Rynt ta gaida shi ya amsa snn suka je cikin mota.
  Kan hanya mami ta kalli man da ke gefen hagunta yana driven sbd a gaban mota take zaune Rynt kuwa na baya.
  Tace yaya"Allah mkrntr nn da dad'i wata anti ta shigo ajinmu sae waqa take mana muna ta rawa kuma kasan me yaya? yace sae kin fad'a,tace"duk uncle d'inda da ya shigo ko aunty da waqa muke gaida shi na maka kaji,yace"yimin inji"
 Tace"kaga anti na shigowa zamu tashi tsaye ne "nn ta tashi tsaye snn tace"sae mu fara da cewa.
  _"Good morning aunty!we are very happy to see u!God bless u as u come today! Paa! pa papapa paaa!_
 Muna tafawa itama tana tafawa snn sae tace "how are u? Muce we are fine aunty .
  Man yayi murmushi yace"to shikenan zauna ki huta"turo baki tayi tace "yaya ban fa gama baka labari ba"sae da ya shafi fuskarta snn yace"to mami zauna sae kici gaba da gaya min"
  Bata zaunan ba sae cewa tayi"bayan mun zauna sae ta mana waqa mai dad'i muna ta rawa abin mu kuma itama tana kama mana,na maka kaji ita ma?eh inaji, ta fara da
 _"1,2 bought my shoes! 3,4 knock at d door!5,6 pick up sticks! 7,8 let them straight !9,10 a big fat hen!11,12 shoot ur gun! du! du!dudu! duu! I said shoot ur gun du!du!dudu! duuu!"_

Dariya ce ta qwacewa Rynt wacce tun d'azun take fmn danne ta amma ta kasa.
  Sbd yanda mami ke  rawar waqar abin dariya ne sosai.
  Ta jikin mirror man ya hango Rynt dake fmn dariya sbd fuskarta ba niqab da shigar ta motar ta cire ta kad'a jaka.
 Rynt ta tsagaita da dariyar ta yayinda mami ke cewa"Anti ai kuma yau kunyi ta rawa da waqa ko? Tace"Aa mami ai mu ba yara bane kmr ku"to Anti ai auntyn mu ma babbace amma takeyin rawa"eh ita malamar yara ce shiyasa, to anti meyasa kullum sae naga anti amarya nasa kid'a tana ta rawa bayan ita ba malamar yara bace?
Nn Rynt tayi rashin sa'ar had'a ido da man ta jikin mirror sae kawai ta kauda idonta tayi kmr ma bata ganshi ba tace da mami"wae mami ba islamiyya aka tashi ba yanzun nn amma sae zancen boko kike mana da tun qarfe biyu aka wuce gun" tace"yauwa anti a lokacin islamiyya ko, wani  malami yace yana sona qanwa tunda na iya alfun ba'un har qarshe kuma ba kuskure ko d'aya ,nace masa ai antina ce kullum take koya min a gida har ma nace ko shi idan yana so yazo zaki koya masa,ko anti zaki koya mai in yazo ko?Rynt tace"uhm mami ai shi malami ne yafi ni iyawa sae dai ma ya koya min, to anti ai da na gaya mai a mkrntar kike yace yana so zai ganki sbd yaji dad'in yanda aka bani kulawa har ma nafi en ajinmu iya karatun qur'ani.
  Mohd yace"mami ba kya gajiya da surutu ne wae nikam, a ajiye zancen nn haka kinji, kuma ki daina fad'ar abinda ba'a tambaye ki ba kinji,tace" to yaya zan tambayeka gobe idan zaka kawo mu school zaka saya min chocolate kan hanya sbd wanda ka saya min a kwanaki ya qare gashi yau da mukaje breakfast ina ta gani agun en ajin mu suna ci har da biscuit amma ni banda"
  Yace"ai mami na siyo miki komai suna but na manta dasu ne.
  Yauwa yaya na gode yanzu in muka isa gida sae a ftr ko? Yace "eh"nn ta kama waqar ta.
  _pawpaw is a kind of fruit,sweet like sugar yellow like fanta every body like pawpaw ,pawpaw!_
  _A lion !a lion!a lion has a tail he has a big head and a very small waist._

Haka tayi ta en waqoqinta sbd dama ta iya duk wasu waqoqi da take ji a bakin en gidan su.
  Man dai da Rynt ba mai magana a cikin har suka isa gida.


Tun daga rnr man bai qara kaisu school ba driver ke kaisu yana d'aukosu.
  Rynt kud'in break fast yake bata mami kuwa kuku ke had'a mata breakfast asa a lunch box.
  Haka kuma tun daga rnr Rynt bata qara yadda taje da niqab a school ba sae dai idan zasu je takan sa da sun isa mkrnt se ta cire idan kuma zasu koma gida ta saka.
  Yanzu har sunyi kusan sati biyu da fara zuwa makaranta amma har yanzu mohd bai nemowa Rynt mai lesson ba.

Rnr wata juma'a da qarfe 12:05pm man ne tsaye a parking lot ya bud'e gambun mota zai shiga sae ga su Rynt an dawo dasu daga school.
  Ko tsayuwa motar su bata gama yi ba Rynt ta bud'e gambu ta fito mota ta tafi aguje cikin kuka ta shiga gidan.

  Man dake qoqarin shiga mota sae fasawa  yayi ya rufe gambun mota snn yabi Rynt cikin gida.

 Ya same ta zaune kan bed ta had'e kai da guiwa tana ta kukanta.
  Zama yayi kan bed d'in had'e da kai hannu ya riqo hannun ta da yaga duk shatar bulala ne akai, yace"waye ya dake ki?warce hannun tayi tare da d'ago fuskarta nn hawaye suka silalo a hnkli kan kumatun  ta ,ta share hawayen wasu suka koma zubowa tace"wani  malami ne ya daken"me kika masa?wae cewa yayi nayi kuskuren fad'ar wata kalma a cikin wani  littafin turanci da yake karanta mana tun satin da ya gabata shine yau yace kowa sae ya karanta d'aya byn d'aya,to shine da ina karantawa na kawo gun wata kalma ya dakatar dani yace na sake maimaitawa na maimaita masa ,sae kawai ya shiga min fad'a wae irin mu ne basa maida hnkli a aji gashi har nakai ss one amma bana bawa kowace kalma haqqinta,sae yace kuma bazan zauna ba har sae na iya kalmar.
 nn yace duk ya fad'a na fad'a mukayi hkn har sau uku,amm yace bnyi dai dai ba nn kawai ya kira wata yace ta fad'i kalmar yaji ,tana fad'a yace a tafa mata ni kuma ya zane ni ya kuma sa aka min kuwa.
ta qarashe mgnr cikin kuka sosai snn ta d'ora da cewa "kuma wlh dai dai nake jin ina fad'a amma shi sae yace banyi dai dai ba"
  Man da tun lokacin da Rynt ta fara zancenta ya kafe ta da ido,
 ya sauke numfashi a hnkli snn yace"fad'i kalmar naji"
tace"retyfe"
yace"retype"tace"eh"yace"kinyin kuskuren fad'a mana,dmn kinsa harafin da bashi ne a cikin kalmar ba, ma'ana p ake son sautin ta ya fito ba F ba"tace nifa bangane ba, yace"ok saurareni kiga kuma ki kalli bakina yanda iskan kalmar zai fito a bakina"ta gyad'a mai kai tare da tsure bakin shi da kallo"yace"retype,retype,retype har sau uku snn yace kinji yanda nake fad'a ba kmr naki ba? cikin murya kuka tace"gsky ni banji wani  banbanci ba"yace"bani aron yatsan ki d'aya"shaye da toka ta kalle shi don ita ta tsani haraka da yace zai ta6a ta, sae dai kuma tana son ta gano meye kuskuren ta a cikin fad'ar kalmar.
  Haka ta daure ta miqa masa d'ayan yatsan ta ,ya riqo yatsan a hnkli yakai  saitin la66an sa yace"retyfe"
kmr yanda take fad'a kenan yace"to ya kika ji iskan bakina ya sauka a yatsan ki da qarfi ko a hnkli? Tace a hnkli naji, yace "yauwa yanda kike fad'a kenan amma yanda ainihin ftr sautin kalmar yake shine "retype"to ya kika ji wnn iskan nata ya sauka?a hnkli ko da qarfi? tace"da qarfi"ya sakar mata yatsa snn yace"to haka nake son ki fad'i kalmar sau uku inji tace"retyfe,retyf.....ba haka ba, look kalli la66a na da kyau kiga yanda nake had'a la66ana gurin fad'ar kalmar musamman gurin p kinji ko,a sanyaye tace "to"snn ta tsure la66ansa da kallo ya fad'i kalmar kusan sau biyar snn yace"oya fad'i naki inji"sae da ta rufe ido tana mai tuno yanda la66ansa ke had'uwa da kuma yanda yake ftr da p, ta fara da cewa"Retype ,retype,retype"har sau uku snn ta bud'e idanuwanta kmr zatayi kuka don har sun d'an ciko tace"hkne kokuwa har yanzu ban fad'a dai dai ba? A hnkli ya lumshe ido ya kuma ware su a kanta snn yace"kinyi dai dai.

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[ 1/25/2017]
 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮









      🔮🔮🔮
*page* *35*
Ya tashi zai fita ,har ma yakai bakin qofa ya juya gun Rynt yace "mami fa?
Tace"tana gida muka ajiye ta sbd tace tana son tabi mama anguwa ne"
  Sae a snn ya tuna da safe kafin su fita ya ba mami waya tayi waya da ummarta.

   Yace"ok ki shirya anjima da qarfe 4 mai lesson d'inki zai fara zowa"
  Dad'i taji sosai don har godiya sae da ta masa snn ya fita.

 Yana fitowa ya had'u da malika zaune a falo,kafin ya qarasa gareta ta wani  sha toka  yaje ya zauna kusa da ita tare da rungumo kafad'ar ta yana mai kallon fuskar ta yace"lfy me akayi kuma? Tace"nifa bangane ba don naga kmr ka fara kula yrnyr nn "
yace"kin manta yanda mukayi dake ne?ban manta ba amma ai.... um um kin fasan bana son qananun maganganu da zasu riqa zowa suna kawo sa6ani a stakanin mu,tace"to shikenan ya alqawarina da kamin, yana nn amma ai ce maki nayi ki bari idan an dawo daga masallaci ko,eh to na shirya kenan kafin ka dawo? Eh.
  Ya tashi ya fita ita kuma ta koma d'akinta.

Bayan ya dawo daga masallaci ne suka fita anguwa shida malika.

Gidan wata qawarta  ce ya kaita.
   Bayan sun gaisa har qawar ta kawo mata abin sha da na motsa baki tace"oya gareki"malika tace"hm tukuna dae nifa kinsan na gaya miki ina cikin damuwa"qawar tace "damuwar me kuma gudar mtr man dake"hm fa'iza kenan man d'in da ke qoqarin juya akalar sa  wni gurin"
kmr ya ban gane ba?ina nufin ya fara kula wnn abar mana da ubansa ya aura masa......mtsw ita wnn abar ce har zata saki a damuwa wlh da nice ai da tuni nayi waje da ita,,ta yaya bayan dole sae ya saketa ne ko zata bar gidan..... Kaji wata tsiyar sae kace ba mace bace ke kai inama nice da wlh tun rnr da aka kawo ta gidan bazata kwana ba ,fa'iza kin manta sae da akayi sati d'aya nsn cewa tana gidan, to byn nn me kika iya yi gashi har yanzu kin kasa aiwatar da komai.
  Dafa na mai mgnr ta sae ya cemin baya son jin zancen ta kwanaki har dukana fa ya tashi yi akn hkn....kayya! me ya shafe ki da yi mishi zancenta kawai ki guma mata uban sharrin da zai rubuta mata saki uku zama d'aya!hm aike na fara gwada hkn ashe er iskar yrnya baki ne da ita, tamin zagi mai ciwo ta alaqanta Abbana da sharrin da na mata,nn ta gaya mata labarin yanda sukayi snn tace"wlh har  yau ina da burin cin qaniyar ta don ba barin ta zanyi ba"
kai!! Kutumar uba!
Cewar qawarta wacce duk ta cika da jin haushin malika.
   Tace"malika gaya min abinda man yafi so a rayuwar sa"tace"ko meyasa?kedai gaya min nace!
malika ta ta6e baki snñ tace"hm to shifa wae ba abinda yafi so irin yaga na sami ciki ni kuma wlh bazan bari ba don ban shiryi haifuwa yanzu ba"
  Tace"common bari kawai ki sami ciki"tace"cabd'i kan me!tace "bani kunnen ki kiji,
nn ta rad'a mata magana malika ta washe baki tace"Allah?
Qwr tace"wlh kuwa ba boka ba malam kuma buqatar ki ta biya.
 Malika tace"wlh kin bani gud idea don wlh yanda yake son in samu ciki ko, duk na mata sharrin nn da kika gaya min to wlh ido rufe zai saketa don ubanta har wae boko ya sakata.... Ya akayi kika barshi... Wa kin fa san ko waye man ba irin mazan da ake tanqwasawa bane wlh duk yanda naso yimai rashin mutunci sae ya taka min birki kuma wlh idan yana min fad'a zaki rantse auren qiyayya mukayi nida shi, sbd shi komai baya sakawa cikin wani ,don lokacin soyayya kam zamu zubata nida shine kmr zamu kashe juna amma da nayi mai laifi to fa zai ajiye so gefe har sae yayi min tas snn ko zamu dawo dai dai daga baya.
  Qwr tace"lallai man d'in nn naki da wuyar sha'ani yake ni mijina ya ma isa ya tunkare ni yace zai min fad'a hm wa albarkacin gawa ta zagi mai mata wanka!kin ganni nn  wlh tun ina amarya bana ko kauda kara duk aikin da nazo yi sae kiga ya kar6e yanayi wae shi baya so na wahala ae kuwa nace da kyau aini dama ta sameni don maida shi nayi tmkr shine mtr nice mijin ,Allan dgske fa'iza? Wlh kuwa ba taqamar sa baya son na wahala ba ai kuwa wahalar zata tabbata akanshi,hm cabd'i ni na isa nace zan juya man ai sae dai ko aikin boka, don kinga ko yanzu cewa nayi ya jirani a waje ba wani  jimawa zanyi ba in na fito sae yakai  ni gida,yace"shifa baya d'aukar irin wnn raini tunda tun farko nn kad'ai nace masa zan zo don haka zancen gida sae kuma wani  lokaci, sae da na d'an had'a masa da kukan shagwa6a snn fa yace to zai je ya dawo ya kaini ,au da sauqi kenan tunda idan kinyi shagwa6a yana duba miki, hm ai mayen son shaw6a ne in gaya miki yafi son ya ganni narke kan jikin shi ina ta zuba mai shagwa6a sae kiga yana ta min abubuwa a jiki  sae wani  tatta6a ni yake yana wani  romancing d'ina,ni kuma ba abinda nafi so irin aje ga babbar haraka amma shi bai cika son wnn abun ba yafi so muyi ta wasa ko za'a kwana ma ransa bazai 6aci ba.
   Qawar tayi dariya tace"lallai gayen nn naki sae shi,hm basshi ai wani  lokacin har fad'a mukeyi dashi wae na fiye buqata yace idan har wani abu nake sha gwanda ma na daina bcs too much sex ba'a cika marmarin juna d'in nn kmr idan aka jima ba'ayi ba.
  In gaya miki nidai jinsa kawai nake don wani  lokacin har zuba mai desire tablet nayi a coffee ai kuwa rnr kaf dare muka kashe  muna abu d'aya sae safe nayi ta mai sharri nace su oga ya akayi  jiya ka tsunduma a haraka sosai kaida naga baka son haka ,da yake gayen nawa baya son raini sae ya wani  tsare gida yace"rnr jiya ta daban ce shiyasa",kuma kin san me ashe ya gano ni fa don washe gari dana zuba masa maganin a coffee wlh cikin dabara ya d'ura min shi tas na shanye shi bai sha ba,kuma yamin qeta ya rufe ni a d'aki ya tafiyar shi,hm wlh kasa bacci nayi rnr har safe.
  Qawar tayi dariya snn tace"wlh ki rage yawan buqata don ina gaya miki yana sa ki fita a ransa tace"hm wlh ni kuwa ba abinda nafi so irin naji inada buqata shiyasa bana ta6a yarda desire tablet ya yanke min,kema ki koya don zaki fi jin dad'in rayuwarki haka.

Hm wata jaraba ce kuma wnn.

Fa'iza tace"hm laila, ni mijina ma da sae ya min kuka nake barin shi....nn wyr malika tayi qara ta kalli fa'iza tace"kinga tafiyata my man ya dawo ,
tace"to yayi sae nazo a gaida shi tace"to snn ta  d'aga wyr ta fita.

Rynt kuwa koda qarfe hud'u tayi ta gama shirin ta tsaf sae jiran mae lesson take  amma shiru har aka qara minti goma sae ga man ya shigo d'akin yace da Rynt"zo ga mai lesson d'in naki yazo"ta taso zata fita ya kalle ta shaye da toka yace"bana son raini
fuskar ki zai karantar ko ke!
da zaki wani je masa fuska sake ba niqabi"
 Tace"wae nikam meyasa kake son takurani ne kace komai sae nasa niqab"
  Yace"kika dae takura kanki ai na gaya miki tunda kikayi gigin amincewa aurena baxa ki ta6a jin dad'i ba,rayuwarki da mami ne yasa nake d'an sauqaqa miki ba wae don wani  abu ba!
  Don hk ki tabbatar kin saka niqab kafin ki tafi  idan ba hk ba kin  haramta da lesson d'in gabad'aya!
  Nn ya tafi ya varta tsaye ta ta6e baki tace"auren naka in banda qaddara me ma zai sa na amince ko yanzu cikar burina kad'ai nake jira na fecewa aurenka"
  Taje ta ciro niqab ta saka snn ta fita.

Man na zaune ake mata lesson d'in hkn yasa yaga yanda Rynt keda saurin fahimta duk da cewa hnklin sa ba duka yana kansu ba sbd wani  aiki da yake a laptop.
  Sae da ana kusa fara kirayen kirayen sllr magrib mai lesson d'in ya tafi.
  Ita kuma ta tashi zata tafi kenan man ya tsaida ta yace"gaya min kalmar da na koyadda ke a d'azun "sae da ta kauda kanta gefe snn tace"retype"ya d'an d'ago ya kalleta snn yace jeki.

Bayan sati d'aya da faruwar haka fhmtar Rynt sae qaruwa take akan lesson d'inda ake mata don yanzu ta fara fhmtr  wasu  kalmomi na turanci da ake fassara mata su zuwa hausa,hkn kuma akan nuna mata yanda ake ftr da sautin kowane harafi da kuma sauran abubuwa da dama.
  Mohd kuwa duk za'ayi mata lesson sae yazo yayi zaune a falo sae ya fake da wani  aiki ne yake kan laptop  hkn bai hana Rynt ta kasa sakewa ba a gurin lesson d'in sbd sosai take son ta fahimci komai ko don yanda a class take jin ana fad'in wasu kalmomi da dama na turanci da bata san su ba.
 Gefen islamiyya kam Alhmdlh bata da wata matsala gurin, kuma still tana ci gaba da maida hankalinta sosai akai.

  Ko yanzu ma lesson ake mata man na zaune yana aiki da laptop  d'inshi .
Yatsun sa na kan laptop amma sae kallon Rynt yake sbd yanda ta bada dukkanin hnklinta akan lesson d'inda ake mata da kuma wasu tambayoyi da yaji an mata ta bada amsa kai tsaye.
   Can Rynt taji a jikinta ana kallonta hkn yasa ta d'ago sae kawai ta sami idanuwanta a cikin nashi still bai daina kallonta ba sae itace ta maida hnklinta ga lesson yayinda kyawawan yatsun ta ke riqe da marker ta fara rubutu akan whiteboard d'inda ke gabanta zata had'a sentence akan wata kalma da lesson teacher d'in ya bata ta rubutu sentence akai dmn yaga idan ta fahmci ainihin inda ake saka kalmar a cikin magana,kmr yanda ya mata bayani.
   Shiyasa man ya kasa d'auke idonsa dmn yaga shin zata iya.
   Tsaf kuwa Rynt ta had'a sentence ba wani gargada ko shirme a ciki, qoqarinta man ya gani ba don komai ba sae don sanin ba wani  gud foundation ta samu ba amma gashi tayi trying much better akan lesson d'inda ake mata da ba'a wani  jima da farashi ba.
    Numfashi ya ftr a hnkli had'e da maida duban shi gun laptop yayinda su kuma suka ci gaba da lesson d'insu.

 Washe gari da qarfe kusan uku malika ce zaune a falo ita kad'ai tana jujjuya wasu ruwan gora dake hannunta nn wayarta tayi qara ta d'aga wyr tare da tashi ta nufi fridge d'in falon ta saka gorar a ciki snn ta nufi d'aki ta d'auko mayafinta ta fita.

Ba jimawa sae ga Rynt ta fito falon riqe da magani a hannunta zata sha sbd kanta da taji yana d'an mata ciwo gashi to 4 mai lesson d'inta zai zo.
   Tana bud'e frigde d'in sae ga man ya shigo gidan ya nufi fridge d'in ya buga tsaki ganin gorar ruwa qwara d'aya wanda tun jiya ya kamata ace ya siyo ruwa a gidan amma sae gashi yau ya fita ya manta.
  Ya kalli Rynt tare da fad'in "ke kin gyara min d'akina kuwa? Tace" bana jin dad'i ne amma yanzu zan tafi idan nasha magani "
  Yace"kin fara ko? tace"nifa ba hk bane kuma kasan bana iya gyara d'akin naka ba kowa a ciki, mami ce ke tsaya min kuma bacci take tun d'azu amma idan zaka tsaya min zan gyara maka ynz"
 Bai ce mata komai ba sae gorar ruwa ya jawo ya tsiyaya mata ruwan a cup ya bata snn shima ya tsiyaya ma kansa yasha.

Malika na cikin mota ita da qawarta fa'iza tana driven zasu tafi kasuwa sae fira suke  malika ta katse firar da cewa"oh my goodness!fa'iza na manta na saka gorar ruwana a fridge d'in falo a maimakon nakai d'akina"fa'iza tace "to meye matsalar ko gidan naku tsiyar ruwa ake yi ne"
 Cikin ba'a fa'iza ta fad'i mgnr ,malika tayi murmushi tace"ba haka bane desire tablet ne a cikin su kuma mai qarfin ne da sae dare nake shan shi idan zamu kwanta nida my man.
  Fa'iza tace"to ai sae ki bari idan kin koma  kya cire"
 Malika tace" Eh dama ai"




Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[ 1/27/2017]

 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮









      🔮🔮🔮
*page* *36*
6angaren su Rynt kuwa man yana gama shan ruwa ya tafi d'akin shi riqe da sauran ruwan da ke cikin gora,sae a snn ne Rynt tasha magani tabi bayan shi dmn gyara mishi d'aki.
    Ta same shi yana qarasa shanye ruwan da ke cikin gora, sae da ya shanye ruwan tas snn ya jefa gorar a dustbin ya zauna kan sofa tare da jingina bayan shi ya kuma  lumshe ido kmr wanda zaiyi bacci.
  Ita kuwa taje ta fara gyara mishi bed yayinda man ya fara jin wani  yanayi a jikin shi na daban  yadai basar ya tashi zai je bayi Rynt tace"nifa kar ka tafi koina kabari  har na gama gyara ma d'aki tukun don ni tsoro nkeji,kmr bada shi take zancen ba ya shige abinshi ya watsa ruwa sauri sauri ya fito sanye da white bathrobe yazo yayi tsaya a bakin qofa yana kallon Rynt  yace"ke ajiye gyran gadon kixo ki wanke min bathroom tukun.
  Rai 6ace ta ajiye gyaran gadon taje da niyyar shiga bathroom d'in amma man bai bata hanya ba sae kallonta yake sbd wata irin mahaukaciyar sha'awa da yaji tana fizgar shi.
  Rynt kuwa ganin baya da niyyar bata hanya sae tsaki ta buga ta juya zatayi tafiyarta ya fizgo hannunta da qarfi ta fad'o kan qirjin shi, tayi sauri zata fizge kanta  ya qara matse ta sosai a qirjin shi,yana binta da wani  irin kallo, tace"wae meye haka ne"
 yace "ni zaki ma tsaki"tace"to ai kaine kaqi ka ban hanya"
  Ya saketa tare da kashe wutar d'akin ya koma jawota ya rungume ,cike da tsoro tayi saurin kallon shi tace "meye haka kuma"yace"zan kar6i haqqina ne"
 Cikin mugun tsorata da jin zancen sa tace"haqqin ka kuma! Yace"eh ko zaki hanani kar6a ne?
Bata bashi amsa ba sae fizge kanta tayi ta tafi aguje  zata bar d'akin yayi hanazarin kamotà ya cicci6e ta yakaita kan bed ya jefar kmr wata kayan  banza.
  Kafin tayi yunqurin tashi sai jinsa tayi kan jikinta ya mata rumfa tare da daddane mata hannuwa .
Nan ta shiga qoqarin qwatar kanta tana fad'in"wae me kake nufi da haka ne,ni dan Allah ka sake ni natafi kar mai lesson yazo ya samu ban shirya ba"
   Bai kula ta ba sae hjbnta yake kiciniyar cirewa.
Yayinda Rynt taji wata irin kasala da sabon yanayi sun fara saukar mata a jiki"
Da har man ya iya nasarar cire mata hjb yakai  hannu yana bin fuskarta da shafa har izuwa wuyanta ya kuma kwanto sosai a qirjinta zai had'e bakin su.
 Tayi saurin kauda bakin ta tare da fashe mishi da kuka tace"don Allah kayi haquri wlh nayi qanqanta da wnn abun "yace kinsan kinyi qanqanta amma kika amince da aurena"tace"nidai dan Allah kayi haquri kaje gun mtr......bakinsa kawai taji cikin nata ya   kuma kai hannu cikin rgrta yana wasa da na fulaninta,
tana ji har yayi nasarar rabata da komai na jikinta ya fara wata sabuwar wasa da jikin nata.
A mamakinta sae taji ta kasa hanashi komai sae ma wani qara narke mai da take jin tanayi sbd sharrin desire tablet d'inda yayi galaba a kanta ,sae dai man ya fita tsunduma dmn tuni shi yayi nisa da barin hayyacin sa.
 wanda ba wani  lalla6awa yake yunqurin zuwa hnyrda a hnkli ya kamata ace ya bita.
Rynt kuwa duk da irin kamun da desire tablet ya mata sae da ta shiga kokawar hana faruwar hkn amma sam bata da wani qarfi.
   Ihu take tana kuka sbd jin zafin baqon al'amarin da ya shiga faruwa da ita, amma sam man bai saurara mata ba har sae da yaji ya samu kanshi yanda yake so.
 Snn  ya wani  tashi zumbur daga kan jikin Rynt da ke wani  irin wahallalen kuka,da sauri yakai  hannu ya murza idon sa wae ko zae samu mfrki yake,ya tuna tabbas ba mafrki bane sbd yanda komai ya shiga dawo mai tun daga farko.
  Sosai ya shiga mamakin kansa wae ace shine ya neme ta da knshi,
wane irin abune ya same shi yau shikam.
  Jiki sanyaye ya jawo bathrobe d'insa ya saka had'e da kallon Rynt cike da tausayi ganin yanda ya mata liga liga,ya kauda idon sa gefe ya fara sauka kan gadon bai qarasa sauka ba sae qafafuwan sa da ya saukar tare da dafe kansa, ya d'auki lokaci mai tsawo a hk snn ya tashi ya bar gadon ya nufi bathroom yayi wanka ya fito.
Ga mamakin sa bai sami Rynt ba ta fita d'akin.
  Zuwa yayi ya cire bedsheets din gadon yaje bathroom ya saka a washing machine ya fito.
Yana fitowa ya samu wyrsa na ruri koda ya duba mae lesson d'in Rynt ne nn ya d'aga wyr .
  Bayan sun gama gaisawa mai lesson ke ce mishi tun d'axu yazo yayi ta danna door bell ba alamar akwai kowa a gidan,mohd yace"muna ciki ba muji bane amma kayi hqr ka tafi kawai sae gobe don yau bata jin dad'i ,nan ya mai Allah sauwaqa snn suka ajiye wyr.

Ya nemo farar jallabiyar sa ya zira ya tafi masallaci yayi sallar la'asar ya dawo yayi zaune a nn falo yana mai kallon gefen d'akin Rynt wacce yasan ba lallai bane ta iya ta6ukawa kanta wani  abu amma sam baya jin zai iya zuwa ya taimaka mata don bai san da wane irin klr raini zata zo mai dashi ba.

 Tashi yayi ya nufi fridge dmn ya samu yasha ruwan sanyi ko zai ji sauqin haushin kansa da yake ji.
  Sae da ya bud'e fridge d'in ya tuna ba ruwa hkn yasa ya ciro fresh milk ya tsiyaya a cup yasha snn ya ciro wyrsa a aljihu ya kira kuku.
 Suna gama waya dashi ya tafi d'aki ya d'auko kud'i ya fito dai dai kuku ya shigo gidan ya miqa mishi kud'in tare da list d'in abubuwan da zai siyo sbd wayr da sukayi akan zai siyo abubuwan da babu ne a gidan.

Malika kuwa ba ita ta dawo gidan ba sae byn isha'i ta sami man zaune a falo yana kallon labaru sae dae hknlinsu kwata kwata baya gurin don har lokacin tunanin abinda ya faru shida Rynt yake wacce har yanzu bai sa ta a ido ba.

Kan jikinsa malika taje ta kwanta tare da fad'in "waeh Allah my man yau nagaji da yawa har ma wani  baccin wahala nakeji"
  Yace "aikin me kika yi ne?kasuwa mana my man,wace kasuwar ce tun d'axun baki dawo ba sae yanzu?gida na tafi my man umma ce bata jin dad'i kuma nayi ta kiran wyrka baka d'aga ba, shiru yayi don  sae a lokcn ya tuna yaga miscalls d'inta har uku, yace "to ya jikin nata tace" jiki da sauqi"
  Tana gama fad'ar haka ta tashi tare da fad'in ni zan tafi na d'an watsa ruwa.
  Yace"ok"tace"ko zakayi ne mu tafi? Yace"Aa"ta kallesa da kyau dmn ta fhmci kmr yana cikin damuwa tace"my man meyake damunka ne? Kallon ta yayi yace"ba komai"
 Bata sake tmbyr sa ba ta nufi fridge ta bud'e.
 A maimakon taga gora d'aya sae tagansu da yawa da sauri ta shiga duba bakin kowace dmn ta bud'e tata gorar sha ne kawai batayi ba,sae kuwa tayi sa'ar samun gorar da aka bud'e ba'a sha ba,ta d'auki gorar zata wuce man yace"bani gorar ruwa d'aya a gurin ta d'auko ta bashi ya kar6a ya kai hannu zai bud'e gorar sae ya tuna d'azu ya bud'e wata gorar ruwa bai sha ba ya maida a fridge,nan  dae kawai ya basar ya bud'e gorar ya tsiyaya ruwan a cup yasha .
  Malika kuwa tana bashi ruwan ta wuce zuwa d'aki riqe da ruwanda ta d'auka ko sune ruwanta.
 Mohd na gama shan ruwa sae ga mami tazo gurin shi tare da jawo hannun shi tace"yaya zo muje kaga Anti tun d'azu sae kuka take tayi kuma idan na tmbaye ta me take ma kuka bata min magana.
  Ba musu ya bita sukaje d'akin Rynt wacce ke zaune kan sallaya ta had'e kai da guiwa tana fmn kuka.


Kuyi hqr da wnn snn kuma kuyi hqr da rashin samun shi kullum muna fama da mtslr nepa ne.



Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[1/28/2017]
 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮









      🔮🔮🔮
*page* *37*
Mohd yaje ya durqusa gab da ita yana mata magana amma taqi ko d'ago kanta bare zancen bashi amsa sae ma sautin kukanta da yake qaruwa.
 Man yayi shiru yana tunanin kodai ya mata rauni ne.
   Yace"Ki min magana naji idan kin samu rauni ne na baki magani"
  Mami tace"yaya hln me ya sami anti da zata ji rauni? Yayi saurin kallonta don ya manta ma tana d'akin yace"ba abinda ya sameta kawai bata jin dad'i ne ,je downstairs ki d'auko mata ruwa a fridge tasha magani"tace"to" snn ta tafi da gudu.
  Shi kuma bai sake ce ma Rynt komai ba sae bedside drawer yaje ya bud'e ya ciro magunguna ya kawo gabanta ya ajiye.
    Dai dai mami ta kawo ruwan ya kar6a ya ajiye a gbn Rynt ya tashi tare da riqo hannun mami suka fita.
  Suna fita Rynt ta ture gorar ruwan har ma da magunguna ta fashe da kuka sosai, ta samu ta miqe tsaye da qyar wacce hjibinta duk yayi sharkaf da hawaye ga idanuwanta da suka kumbura sukayi jajir kan kuka.
  Bata damu da ta cire hijabin ba sbd baqin ciki da damuwar da take ciki kad'ai sun ishe ta.
   Taje kan bed tayi kwance tana ci gaba da kukan da ya fara saukar mata da zazza6i.

 10:00pm
Man ne kwance cikin shirin sa na bacci malika ta shigo d'akin taje gab dashi ta kwanta suna masu fuskantar juna ta shafo gefen fuskar shi snn takai hannu tana scrolling din wyrta tace "my man style d'in kwanciya na samar mana duba kaga, wata muguwar harara ya watsa mata yace"wae bana hanaki kallon abubuwan nn ba!
 ta 6ata fuska tace"nifa matsala ta dakai zafin zuciya wnn fa photo ne ba video ba,kuma wlh da gani style d'in zamu ji dad'in shi sosai don ina ganinsa sae duk na kasa samun natsuwata.
Yace"wae ke ce maki akayi anayin aure ne wa abu d'aya,da kullum bakida wata magana sae ta kwanciya"
yayi tsaki ya juya mata baya yana fad'in"
  wata in kuka take a rnr farkonta wae ke a taki rnr har ma kin fini  zu6ud'i.
   Tace"me kace?yayi banza da ita,
Ita kuma ta buga tsaki ta fita ta bar d'akin rai 6ace.

 Washe gari ta kasance rnr lahadi.
 Mami kad'ai aka kai islamiyya sbd zazza6in da ya rufe Rynt sosai wacce ba yanda man bai yi ba kan ta bari ya mata allura amma taqi da qarshe ma inna yaje ya d'auko ya tafo da ita.
  inna sae lallashin Rynt take ,Rynt tace"Bana son allura inna kuma don Allah kice ya tafiyar shi"inna tace "jikin ki yayi zafi sosai Rynh kiyi hqr ya maki allura kinji"
  Tace"Ni inna a bani magani kawai nasha"
Inna tace"to kaji had'o mata magunguna tasha"
Mohd yace"inna dole ne fa sae an mata allura snn ko zata d'ora da magani"
   Nn inna ta koma lallashin Rynt har ta yadda a mata allura amma a hannu .
  Man na had'a allura sae kallon Rynt yake wacce ta 6oye fuskarta a jikin inna sbd bata son ganin tsinin allura.

Bayan ya mata allura ne inna ta kai hannu tana murza mata gurin.
  Snn tace"to sauko qasa kici abinci don nsn ko lafiyar ki qalau ba wani  cin abinci kike ba bare babu lafiya,ga muhammadu ba kula ne dashi ba shidai cikin sa kawai ya sani.
    Komai dae mohd bai ce ba sae  harhad'a kayan allura yake ya kai drawer ya ciro magunguna ya ajiye a cewar idan taci abinci sae tasha.
 Har ya kama hanya zai fita yayi saurin juyowa sbd Rynt da yaji tace"wash Allah inna bazan iya ba bari kawai naci abincina a nn kan gado"inna tace"yo Rynh ai ba kyau cin abinci kan gado"
   Tace "to inna a ajiye kawai har idan na tashi zanci"Aa ba'ayi hk ba zan dae baki kwanon abincin ki riqa a hannunki sae kici tunda dae ya zama lalura"
 Inna ta d'auko plate d'in abinci ta miqawa Rynt wacce garin kar6a ne idonta ya fad'a kan man rai 6ace tayi saurin kauda idonta shi kuma ya fita.

 Inna ta jima kafin take barin gidan wacce bata san ainihin abinda ke faruwa da Rynt ba ta d'auka ko ciwo ne kawai.

Bayan sllr la'asar mai lesson d'in Rynt yazo.
  Bayan man ya gama gaisawa dashi ne ya nufi d'akin Rynt ya samu sae bacci take qudundune cikin blanket ya matsa gab da ita da niyyar ta6o jikinta yaji idan ya rage zafi sae kuma ya fasa sbd tuna cewa zai iya tasheta tunda ba wani  nauyin bacci ne da ita ba, kuma alamu sun nuna mae bata jima da yin baccin ba sbd eyelashes d'inta da ya gani d'auke da sanyin hawaye.
   Juyawa yayi ya bar d'akin yana tunanin ina ma mami na nn da sae a mata lesson don dama yana da niyyar a had'a har da ita a riqa musu lesson amma ba'a lokaci d'aya ba tunda abubuwan ba d'aya bane idan dae an gama ma wnn sae ayima wnn.

Haquri yaje yana ba mae lesson d'in sae ga malika ta fito ,
mai lesson yayi saurin kauda idon sa ya fita sbd kayan jikin malika ba na kirki bane.
  Man ya kalleta yace"kin manta kayanda ke jikin ki ne da zaki ganni da wani  kuma ki fasa komawa"ta6e baki tayi tace"to yi hqr, but waye shi? Sai da yaje ya zauna snn yace"Mae lesson d'in wnn yrnyr ne"
Itama zama taje tayi kusa dashi tace"hm wlh ni nama d'auka ko mami ce akeyiwa lesson kullum ashe wnn abar ce,gsky Abban nn naka mutum ne mai takurawa don nsn duk shine ya matsa maka akan haka.
    Yace"to kar dai kiyi gigin fad'ar banzar magana wa Abbana"
Ta kwanto mae tare da fad'in"nama isa kawai dae na tsani yrnyr ne wlh,wae ace ga er gida ba'ayiwa lesson ba sae ita, yace"itama ai za'a fara yi mata ne,yau ma naso ace an fara mata sae gashi bata nn "
ina ta tafi ne ko sun fita ne itada wnn abar?
Yace" tabi inna ne"
Ta d'an yamutsa fuska tace"waye kuma inna?kallon kin raina ni ya mata tace" oh kakar ka ko na manta ne amma kuma me ya kawota?Yace"dubiya"waye ba lfy badai kai ba"
  Yace"wnn yrnyr ce"
 Allah yasa ta mutu kowa ma ya huta, da sauri man ya kalleta tace"eh gsky na fad'a ai don ko bata mutu ba ni sae na zamo ajalinta,don ba'ayi macen da zata ra6eka ba wlh ni kad'ai ce ba qari"
   Shiru yayi kmr ma baya jinta sae danne danne yake a wyrsa.

Washe gari ta kasance Monday Rynt ce ta fito harabar gidan sanye da uniform d'in ta.
   Ita kad'ai ake jira don har mami ta shiga mota shiyasa sae son take tayi sauri amma kuma bazata iyaba sbd har yanzu gurin na mata ciwo wacce duk ta taka qafarta sae ta qara jin tsanar man a cikin ranta.
  Tun lokacin da ta fito man ke kallonta wanda ke zaune kan resting chair riqe da jarida yana karatu yana shan iska.
  Samun kansa yayi dajin tausayinta sosai har dai da ya tuna yanda abin ya faru tsakanin shi da ita wanda har yanzu yana matuqar mamakin kansa da kusantar ta da yayi,haka kuma yana jin haushin kansa.

 Ajiye jarida yayi ya nufo gun Rynt wacce tana ganin sa tafe ta kauda kai ta kuma tsaya cak ta daina tafiya, har ya qaraso gab da ita ya tsaya nn suka kalli juna
hkn yasa man ya hango tsantsar tsanar sa a cikin idanuwanta.
 Da sauri Rynt ta kauda kanta gefe
haka shima
  Snn yace "bazaki iya zuwa school d'in nn ba kiyi zamanki kawai har kiji sauqi.
 Daga hk ya juya yace da driver"tafi kawai ka kai mami"
  Rynt kmr zatayi kuka tace muna da test ne fa"
Kallonta yayi a natse yace"naji amma muje ciki ayi maganin matsalar tukun sae na kaiki school"
 Shaye da toka tace"bana so"
Daga haka ta ra6a ta gefen sa zata wuce yasha gabanta tare da
 Fad'in "bana son raini muje ciki nace kuma idan kika musa min wlh sae nace mkrntr ma baxa ki je ba!
  Komai bata sake cewa ba sae kuka ta fashe mai dashi yaja hannunta ya tafi da ita sae d'akinta.
 Sae da ya sake mata hannu snn ya shiga bathroom ya had'a ruwan zafi da dettol ya fito ya sameta tsaye inda ya barta sae kukanta take.



Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[ 1/30/2017

 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```










           🔮🔮🔮🔮
*page* *```39```*
Girshi Rynt ta ga mami close to her ga kuma teddyn da ta gani a hannunta hkn yasa ta buga razanannen ihu had'e jefar da trayn hannunta.
  kafin trayn yakai  qasa ita kuwa mami ta fasa nata ihu tare da jefar da teddy sbd yanda taliya ta watso mata a hannu a rikice Rynt tayi kanta tana cire mata taliyar ita kuka mami kuka sbd har ftr gurin ta d'an kwaye ya kuma yi ja sosai.
   D'aki suka je amma gabad'aya Rynt ta rasa natsuwarta don mami sae kuka take tayi. gashi tasan cewa man baya nn wacce taji hkne a bakin malika da zata sallami kuku hkn yasa ta yanke shawarar zuwa gidan inna.
 Hijabi kawai ta zira ta d'auki mami suka tafi.

 Bayan har sun wuce ne malika ta fito cike da murna don a lokacin da su Rynt sukayi ihu har kunnenta yaje sae ta d'auka ko ihun hauka ne ta jiyo sunayi.
  Ta tafi kitchen ta same shi kaca kaca tray yayi nasa gefe taliya ma haka da kuma teddyn mami,nn ta kwashe da wata irin dariya tace"lallai aiki yayi kyau kmr yankan wuqa wata qil loma d'aya kawai sukàyi amma har sun bi sun haukata kitchen hk yanzu koina suka nufa ne oho Allah yasa ma sufi ruwa gudu"
  Daga nn ta tafi d'akin Rynt don ta qara tabbatarwa kanta ta samu kuwa koina basa nn har bathroom,
 farin ciki taji fal har ranta don sae kwasar dry take tana fad'in"matsiyaciya bake ba mijina har abada kai ko a lafira wlh, bari ma na kirashi naji ko ya isa lafiya.
 Nn ta kira man suka jima suna waya cike da nishad'i byn sun gama tasa aka gyare kitchen tsaf ta kuma kira kuku a cewar ya dawo yaci gaba da aikin sa.
  Sae a bayan snn ta kira pretty ta gaya mata sae dariya suke ta kwasa.
 Sae dai bata snr da ita cewa har da mami ba.

Rynt kuwa suna zuwa gidan inna suka sami nasir a can shine ya d'auki mami suka je asibiti akayi treatment nata suka dawo.
 Da yake inna tasan mohd yayi tfy tace da Rynt suyi zaman su har sae idan ya dawo sae su koma,har ma take cewa nasir yaje da Rynt gidan ta d'ebo musu en kyn sawa,
hkn kuwa yayi ma Rynt dad'i sosai duk da bata san ko kwanaki nawa man zaiyi bai dawo ba.

Da byn sllr isha'i ne suka je gidan Rynt ta d'ebo musu kayan sawa ita da mami sae dai bata had'o musu da uniform ba sbd an kusa shiga weekend kuma ta fiso sae mami taji sauqi snn ko zasu koma sbd ba wani sosai d'in nn ta qone ba.
  Shigar su gidan har  fitowar su basu had'u da kowa ba sae mai gadi kad'ai.

Bayan sun koma gidan inna ne nasir ya koma gida ,pretty tazo da murna ta tarbe shi ta kuma kawo mishi abinci ,ba kmr kullum da sae yace takawo mai take kawowa ba.
  Zuba mishi abinci take har ta gama idonsa na kanta ,sae da ta zauna ne yake cewa"wae yau wane irin farin ciki ne kike ciki haka naga har bakin ki baya rufuwa,kallon sa take tana murmushi tace"ba komai kawai dai kati nake so zan kira umma,tun d'azu nake jiranka da kace zaka turo min naji shiru.
 Nn yasa hannu a aljihu ya ciro kati ya miqa mata snn yace "kwata kwata mantawa nayi wlh"tace"to ngde"snn ta tafi d'aki ta sanya kati ta kira ummarta tana gaya mata lbrn da malika ta snr da ita,umma tace"da kyau qwarai kaddai ki sake Nasir yaji tace" haba ina hauka ne umma aini bana son kowa ma yaji har sae tayi nisanda ba'a iya gano ta ,umma tace"ai ta tafi kenan ba dawowa er matsiyata taje can ta qarata ba ita ba d'ana bare a tatse min shi"
pretty ta kwashe da dariya tace"umma zan kiraki anjima naji nasir na qwala min kira.
 Nn suka katse wyr ta tafi gun kiran nasir da ta samu ruwa ne yake buqata.

Bayan kwana biyu da fauruwar hakane da yamma sosai man ya dawo daga tafiyar da yayi.
 malika ta tarbe shi sae murna take tana wani  nn nn dashi  don kawai ta samu ta mantar dashi komai sbd bata son yayi saurin gano su Rynt basa gidan har dai mami da ta kasance abokiyar cin abincinsa.
   Shi kuwa a gjye ya dawo shiyasa sam bai leqa d'akin Rynt ba sae a washe gari da ya dawo sllr asuba ya shiga bai gansu ba,yaje koina a gidan basa nn .
Da mamaki yaje yana tmbyr malika cewa ina wnn yrnyr ta tafi tunda safe haka?ta6e baki tayi snn tace"oho kawai dae tun rnr da kayi tafiya itama tasa qafa ta fita"yace"tasa qafa ta fita kuma shine har yau bata dawo ba,d'ibar kayanta tayi ta tafi dasu ko yaya? Oho ni ina zan sani Yace" lallai yrnyr nn ta raina ni da yawa wlh"
  Daga hk ya wuce d'akinshi rae 6ace ,malika kuwa ta bishi da ido ta6e da baki.

Sae guraren 11 man ya fita gidan bai zarce koina ba sae gidan inna.
  Ya sami inna, nasir, Rynt ,da kuma mami a nn harabar gidan sun fito zasu shiga mota.
  Yana fitowa mota mami taje da gudu ta tarbo shi ya riqo hannunta suka qaraso gurin su Rynt .
 Bayan sun gama gaisawa shida nasir da inna har suna mai ya hanya yace dasu alhmdlh snn yaje gab da Rynt ya tsaya yana mata kallon tuhuma,sau d'aya ta kalle shi ta sadda kanta qasa.
  Mohd ya maida duban sa gun inna yace"inna me yrnyr nn taxo yi a gidan nn?tace"ayyo ai da baka nn ne tsautsayi ya sami mami ta qone a hannu duba ma kaga ga hannun nn ta fad'i hkne had'e da riqo hannun mami ta nuna mae ya duba hannun yaga qonuwar ba sosai bace kuma har ta soma warkewa dan kad'an ma ya saura,
yace"garin ya hk ta faru, Rynt ce tayi mae bayani inna ta d'aura da cewa shine nace suyi zaman su har sae ka dawo tukun tunda ba mae kula dasu can, yace"haba inna ai ko nasir mai zuwa yana duba su ne ba sae kin wani ce su zauna a nn ba"
    Inna tace"yo kai  Muhammadu kai kafi son kullum mutum yayi ta zama qunqushe cikin gida baya fitowa yaga en uwa"
 A d'an qufule yace "shike nn inna naji yanzu ina kuma zuwa kun wani  kwaso ku duka haka"
  Sae da inna ta washe baki snn tace"wae zamu tafi ne gurin su saliha kasan yau ake bizitin "
yace"inna haka ai sae ku cika musu mkrnta ku kuje gida ma suje  haba kar kusa a d'auke ku gidadawa mana.....yo muhammadu alqawari fa na musu akan zanje ko so kake na karya?
  Yace"bance ba  amma dae bazaku je da wnn yrnyr ba"ya fad'i hkne tare da nuna Rynt wacce tayi saurin d'agowa ta kalle shi yayinda inna ta gwalo ido cike da masifa tace"kan me! yace"kuje kawai ni zan kawo ta daga baya"
 Inna tace"bakaji da kyau ba tare dae zamu tafi"
 Nasir yace"Aa inna wata qil akwai unxurin da yake da shine"
  Tace"yo kai baka san hln muhammadu bane, ba wani uzurin da yake da hana mata tfyr kawai yake sonyi"

Nasir yace" inna kawai dae muje tunda yace zai kawota d'in ai zai kawota"
 Inna bata wani  gamsu sosai ba amma hk tayi sallama da Rynt a cewar sae sunzo.
 Daga nn suka shiga mota ita da nasir har mami.
  Rynt kuwa ta kalli man idonta tap da qwalla sbd tasan hanata zuwan ne yayi,kallonta yake ta kauda kanta cike da son ta fashe da kuka amma ta danne sbd mami da taji ta qwala mata kira tana mata bye bye nn ita ma ta shiga yi mata bye bye har motar su tafita ta sake kallon man tare da fashe mai da kuka marar sauti,ta shiga roqon dan Allah yayi hqr ya barta taje bai kulata ba sae hannunta yaja zuwa mota tirje mai take amma haka ya d'ura ta mota ya rufe  sae jin yayi ta fasa ihu yayi saurin bud'e gambun yana tmbyrta lafiya ?
bata
iya bashi amsa ba sae fitowa tayi ta fad'i nn qasa riqe da qaramin yatsanta na qafa sae kuka take tana yawo da qafar ,man ya rikice yana tmbyr mene ne wae tace"wani  abune ya cije ni..... What bana son qarya fa a motar tawa! Tace"wlh Allah kuwa ka duba zaka ga koma mene ne, ba musu yaje yana duba motar tashi da ta kasance tsaf tsaf sae kawai yaga kunama ai kuwa da mugun mamaki yake ci gaba da kallonta yana kuma mamakin ina aka shigar mae da mota da baya nn har kunama ta sami damar shiga ciki kaddai d'an iskan driver ya samu mai shigar mae da mota koina ya samu,tsaki ya buga had'e da ciro takalmi ya kashe kunamar snn yayi kan Rynt da sauri ya cire necktie d'insa ya d'aure mata yatsa ya samu da qyar ta shiga motar don sae kuka take ita bazata sake shiga motar ba.
  Bayan ta shiga motar yaja motar da sauri sae chemist aka mata allura a yatsar aka kuma bata magani snn sukayo gida wacce koda suka iso gidan tuni Rynt tayi bacci da kanshi ya d'auke ta ya shiga da ita gidan yayi kici6is da malika zata fita.





Billy giro😊

?Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
        (admin
   Arewa hausa novels
       Novels villa
     Duniyan novels
   Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
          And
Cool novel, makeup and cooking)

      WHATSAPP NO:
    +2347039625239?🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2/4, 9:39 PM] ‪+234 703 962 5239‬: [ 1/30/2017

 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```










           🔮🔮🔮🔮
*page* *```39```*
Girshi Rynt ta ga mami close to her ga kuma teddyn da ta gani a hannunta hkn yasa ta buga razanannen ihu had'e jefar da trayn hannunta.
  kafin trayn yakai  qasa ita kuwa mami ta fasa nata ihu tare da jefar da teddy sbd yanda taliya ta watso mata a hannu a rikice Rynt tayi kanta tana cire mata taliyar ita kuka mami kuka sbd har ftr gurin ta d'an kwaye ya kuma yi ja sosai.
   D'aki suka je amma gabad'aya Rynt ta rasa natsuwarta don mami sae kuka take tayi. gashi tasan cewa man baya nn wacce taji hkne a bakin malika da zata sallami kuku hkn yasa ta yanke shawarar zuwa gidan inna.
 Hijabi kawai ta zira ta d'auki mami suka tafi.

 Bayan har sun wuce ne malika ta fito cike da murna don a lokacin da su Rynt sukayi ihu har kunnenta yaje sae ta d'auka ko ihun hauka ne ta jiyo sunayi.
  Ta tafi kitchen ta same shi kaca kaca tray yayi nasa gefe taliya ma haka da kuma teddyn mami,nn ta kwashe da wata irin dariya tace"lallai aiki yayi kyau kmr yankan wuqa wata qil loma d'aya kawai sukàyi amma har sun bi sun haukata kitchen hk yanzu koina suka nufa ne oho Allah yasa ma sufi ruwa gudu"
  Daga nn ta tafi d'akin Rynt don ta qara tabbatarwa kanta ta samu kuwa koina basa nn har bathroom,
 farin ciki taji fal har ranta don sae kwasar dry take tana fad'in"matsiyaciya bake ba mijina har abada kai ko a lafira wlh, bari ma na kirashi naji ko ya isa lafiya.
 Nn ta kira man suka jima suna waya cike da nishad'i byn sun gama tasa aka gyare kitchen tsaf ta kuma kira kuku a cewar ya dawo yaci gaba da aikin sa.
  Sae a bayan snn ta kira pretty ta gaya mata sae dariya suke ta kwasa.
 Sae dai bata snr da ita cewa har da mami ba.

Rynt kuwa suna zuwa gidan inna suka sami nasir a can shine ya d'auki mami suka je asibiti akayi treatment nata suka dawo.
 Da yake inna tasan mohd yayi tfy tace da Rynt suyi zaman su har sae idan ya dawo sae su koma,har ma take cewa nasir yaje da Rynt gidan ta d'ebo musu en kyn sawa,
hkn kuwa yayi ma Rynt dad'i sosai duk da bata san ko kwanaki nawa man zaiyi bai dawo ba.

Da byn sllr isha'i ne suka je gidan Rynt ta d'ebo musu kayan sawa ita da mami sae dai bata had'o musu da uniform ba sbd an kusa shiga weekend kuma ta fiso sae mami taji sauqi snn ko zasu koma sbd ba wani sosai d'in nn ta qone ba.
  Shigar su gidan har  fitowar su basu had'u da kowa ba sae mai gadi kad'ai.

Bayan sun koma gidan inna ne nasir ya koma gida ,pretty tazo da murna ta tarbe shi ta kuma kawo mishi abinci ,ba kmr kullum da sae yace takawo mai take kawowa ba.
  Zuba mishi abinci take har ta gama idonsa na kanta ,sae da ta zauna ne yake cewa"wae yau wane irin farin ciki ne kike ciki haka naga har bakin ki baya rufuwa,kallon sa take tana murmushi tace"ba komai kawai dai kati nake so zan kira umma,tun d'azu nake jiranka da kace zaka turo min naji shiru.
 Nn yasa hannu a aljihu ya ciro kati ya miqa mata snn yace "kwata kwata mantawa nayi wlh"tace"to ngde"snn ta tafi d'aki ta sanya kati ta kira ummarta tana gaya mata lbrn da malika ta snr da ita,umma tace"da kyau qwarai kaddai ki sake Nasir yaji tace" haba ina hauka ne umma aini bana son kowa ma yaji har sae tayi nisanda ba'a iya gano ta ,umma tace"ai ta tafi kenan ba dawowa er matsiyata taje can ta qarata ba ita ba d'ana bare a tatse min shi"
pretty ta kwashe da dariya tace"umma zan kiraki anjima naji nasir na qwala min kira.
 Nn suka katse wyr ta tafi gun kiran nasir da ta samu ruwa ne yake buqata.

Bayan kwana biyu da fauruwar hakane da yamma sosai man ya dawo daga tafiyar da yayi.
 malika ta tarbe shi sae murna take tana wani  nn nn dashi  don kawai ta samu ta mantar dashi komai sbd bata son yayi saurin gano su Rynt basa gidan har dai mami da ta kasance abokiyar cin abincinsa.
   Shi kuwa a gjye ya dawo shiyasa sam bai leqa d'akin Rynt ba sae a washe gari da ya dawo sllr asuba ya shiga bai gansu ba,yaje koina a gidan basa nn .
Da mamaki yaje yana tmbyr malika cewa ina wnn yrnyr ta tafi tunda safe haka?ta6e baki tayi snn tace"oho kawai dae tun rnr da kayi tafiya itama tasa qafa ta fita"yace"tasa qafa ta fita kuma shine har yau bata dawo ba,d'ibar kayanta tayi ta tafi dasu ko yaya? Oho ni ina zan sani Yace" lallai yrnyr nn ta raina ni da yawa wlh"
  Daga hk ya wuce d'akinshi rae 6ace ,malika kuwa ta bishi da ido ta6e da baki.

Sae guraren 11 man ya fita gidan bai zarce koina ba sae gidan inna.
  Ya sami inna, nasir, Rynt ,da kuma mami a nn harabar gidan sun fito zasu shiga mota.
  Yana fitowa mota mami taje da gudu ta tarbo shi ya riqo hannunta suka qaraso gurin su Rynt .
 Bayan sun gama gaisawa shida nasir da inna har suna mai ya hanya yace dasu alhmdlh snn yaje gab da Rynt ya tsaya yana mata kallon tuhuma,sau d'aya ta kalle shi ta sadda kanta qasa.
  Mohd ya maida duban sa gun inna yace"inna me yrnyr nn taxo yi a gidan nn?tace"ayyo ai da baka nn ne tsautsayi ya sami mami ta qone a hannu duba ma kaga ga hannun nn ta fad'i hkne had'e da riqo hannun mami ta nuna mae ya duba hannun yaga qonuwar ba sosai bace kuma har ta soma warkewa dan kad'an ma ya saura,
yace"garin ya hk ta faru, Rynt ce tayi mae bayani inna ta d'aura da cewa shine nace suyi zaman su har sae ka dawo tukun tunda ba mae kula dasu can, yace"haba inna ai ko nasir mai zuwa yana duba su ne ba sae kin wani ce su zauna a nn ba"
    Inna tace"yo kai  Muhammadu kai kafi son kullum mutum yayi ta zama qunqushe cikin gida baya fitowa yaga en uwa"
 A d'an qufule yace "shike nn inna naji yanzu ina kuma zuwa kun wani  kwaso ku duka haka"
  Sae da inna ta washe baki snn tace"wae zamu tafi ne gurin su saliha kasan yau ake bizitin "
yace"inna haka ai sae ku cika musu mkrnta ku kuje gida ma suje  haba kar kusa a d'auke ku gidadawa mana.....yo muhammadu alqawari fa na musu akan zanje ko so kake na karya?
  Yace"bance ba  amma dae bazaku je da wnn yrnyr ba"ya fad'i hkne tare da nuna Rynt wacce tayi saurin d'agowa ta kalle shi yayinda inna ta gwalo ido cike da masifa tace"kan me! yace"kuje kawai ni zan kawo ta daga baya"
 Inna tace"bakaji da kyau ba tare dae zamu tafi"
 Nasir yace"Aa inna wata qil akwai unxurin da yake da shine"
  Tace"yo kai baka san hln muhammadu bane, ba wani uzurin da yake da hana mata tfyr kawai yake sonyi"

Nasir yace" inna kawai dae muje tunda yace zai kawota d'in ai zai kawota"
 Inna bata wani  gamsu sosai ba amma hk tayi sallama da Rynt a cewar sae sunzo.
 Daga nn suka shiga mota ita da nasir har mami.
  Rynt kuwa ta kalli man idonta tap da qwalla sbd tasan hanata zuwan ne yayi,kallonta yake ta kauda kanta cike da son ta fashe da kuka amma ta danne sbd mami da taji ta qwala mata kira tana mata bye bye nn ita ma ta shiga yi mata bye bye har motar su tafita ta sake kallon man tare da fashe mai da kuka marar sauti,ta shiga roqon dan Allah yayi hqr ya barta taje bai kulata ba sae hannunta yaja zuwa mota tirje mai take amma haka ya d'ura ta mota ya rufe  sae jin yayi ta fasa ihu yayi saurin bud'e gambun yana tmbyrta lafiya ?
bata
iya bashi amsa ba sae fitowa tayi ta fad'i nn qasa riqe da qaramin yatsanta na qafa sae kuka take tana yawo da qafar ,man ya rikice yana tmbyr mene ne wae tace"wani  abune ya cije ni..... What bana son qarya fa a motar tawa! Tace"wlh Allah kuwa ka duba zaka ga koma mene ne, ba musu yaje yana duba motar tashi da ta kasance tsaf tsaf sae kawai yaga kunama ai kuwa da mugun mamaki yake ci gaba da kallonta yana kuma mamakin ina aka shigar mae da mota da baya nn har kunama ta sami damar shiga ciki kaddai d'an iskan driver ya samu mai shigar mae da mota koina ya samu,tsaki ya buga had'e da ciro takalmi ya kashe kunamar snn yayi kan Rynt da sauri ya cire necktie d'insa ya d'aure mata yatsa ya samu da qyar ta shiga motar don sae kuka take ita bazata sake shiga motar ba.
  Bayan ta shiga motar yaja motar da sauri sae chemist aka mata allura a yatsar aka kuma bata magani snn sukayo gida wacce koda suka iso gidan tuni Rynt tayi bacci da kanshi ya d'auke ta ya shiga da ita gidan yayi kici6is da malika zata fita.





Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2/4, 9:39 PM] ‪+234 703 962 5239‬: [ 1/31/2017]
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```










           🔮🔮🔮🔮
*page* *```40```*
Waya malika keyi bata san lokacinda wyr ta sa6ule  a hannun ta ta fad'i qasa ba.
   Bata damu da kula wyr ba sae kallon Rynt take da mugun mamaki tace"kai! me zan gani!
kan uba! badai wnn abar ce nake gani ba kuma d'auke a hannun ka!
       Kallonta kawai mohd yayi ya ra6a ta gefenta ya wuce, bai zarce koina ba sae d'akin Rynt yayinda malika ke biye dashi cike da masifa tana mae tambayoyi ,sae da ya ajiye Rnyt snn ya jawo hannunta suka baro d'akin suna saukowa downstairs ta wani fizge hannunta da qarfi snn tace"kamin bayani nace a ina kaganta ne wae!da har zaka wani  tallabota haka!
 Yace"ha'a! a ina kuwa banda gidan inna! Da mamaki tace"gidan inna kuma?yace"eh mana da to ina zan ganta a tunanin ki? A d'an daburce tace "dole nayi mamaki mana byn nsn.....sae kuma tayi saurin katse kanta da cewa"abinda ma yafi d'aure min kai shine ya akayi ka tallabota wae?
Yace"bacci tamin a mota....what!amm kaji kunya wlh ai ko gawa ce wlh bai kamata ka zamo d'aya daga cikin masu tallabar gawar ba bare wae don ta ma bacci a mota iyye lallai wlh na yarda yrnyr nn ba'a banza ta bar ka ba!
   Tsaki kawai ya buga ya fita yana qwalawa drivern sa kira.

Da sauri driver ya qaraso gare shi man ya kalle sa a fusace snn yace"dan gidanku ina ka shigar min da mota ne da bana nn yace"wlh koina ban shigar ma da mota ba yalla6ai!mohd yace wlh idan kamin qarya a bakin aikin ka tayaya to zan sami kunama a mota ta ka wani cemin bakaje da motar koina ba!
 Driver yace"wlh na rantse yalla6ai ba inda naje da ita amma kuma nayi mamakin da kace ka sami kunama a ciki sae dae kuma gsky nasan jiya da dare na wanke motar har ma na shanya car mats akan flowers kuma gskyr magana da suka bushe ciro su kawai nayi na maida mota ba tare da na kakka6e ba don ban ko kawo cewa wani  abu zai hau akai ba,nn kawai mohd ya shiga qwalawa baba mai gadi kira, wani dattijo yazo da sauri zai durkusa mai, mohd yayin saurin cewa"a'a basae ka durqusa min ba ina so zan kora ma bayani ne akan flowers d''in gidan nn ,bawai aikinka kawai ka riqa  basu ruwa ba,
har tsaftar su sae ka kula da ita inace har maganin qwari sae da na siyo na baka wanda ga dukkan alama baka amfani dashi Baba, wlh haka ne yaro amma zan kiyaye daga yau ayi hqr,mohd yace"kaga Baba idan har kasan baza ka iya kula da flowers d'in nn ba kawai ka tsaya a iya gadinka na samo wani  wanda zai kular min da flowers"
Baba maigadi  yace"yaro wlh nayi ma alqawarin zan kula dasu yanda kake so"
  Yace"to baba yanzu kaje ka saka maganin da na baka snn ka share duk wani  datti dake qarqashin flowers d'in  yace "to shikienan"ya tafi cikin hanzari yayinda man yace"da driver kai kuma kaje ka bud'e boot d'in motar ka ciro wnn car mat da na kashe kunama akai ka wanke shi tas snn itama motar ka bincika min ita da kyau ka kuma sake wanke ta then ina warning d'inka akan kar ka sake maida min abubuwan mota haka kawai ba tare da ka kakka6e ba idan ba hk ba wlh  a bakin aikin ka .
yace "inshaAllah yalla6ai an gama"
 Nn mohd ya juya ya koma cikin gida.

Malika kuwa lokacinda man ya buga tsaki ya fita taji kaman ta fasa ihu don takaici ga kuma tsananin  mamakin da take d'auke dashi na ganin Rynt bata haukace ba kan dole  ta duqa ta d'auki wyrta taje d'aki ta kira pretty ta gaya mata abun mamaki da haushi da suka faru da ita yanzu, pretty tace"abin da d'aurewar kai wae ma kin tabbatar taci abincin kuwa? Hm pretty ina d'aki fa na jiwo ihunta kuma koda nazo na sami kitchen duk a hargitse na kuma duba koina a d'akinta bata nn"pretty tace"me man yace miki taje yi a gidan inna? Ni ina naga natsuwar tmbyrsa haka don wlh ji nayi kmr zuciyata zata fashe a lokacin da naganshi d'auke da ita gani kuma d'auke da mamakin ya akayi ya samota don tuni na gama sata cikin jerin shafaffin mutane sae dai kuma a lokacinda na ganshi d'auke da ita nayi tunanin ko tsinto ta yayi garin haukarta shine aka mata allurar bacci,wae sae yace min bacci tamai a mota,pretty tace"kinsan hln yaya da baqar magana amma kuma dole idan taci wnn abinci sefa ta haukace kuma baxa a ta6a samota ba sbd qa'idar maganin kenan but yanzu kije gun yaya cikin hikima da nuna komai ya wuce a gurin kiji shin me taje yi gidan inna da har tayi kwanaki bata dawo  ba,malika tace shikenan i will call u back idan nayi hkn.
  Nn suka katse wayar ta nufi d'akin man ta same shi zaune kan sofa ya tasa 'ya'yan fruits gaba yana sha.
Taje gab dashi ta zauna ya kalle ta sau d'aya  ya kauda kai.
   Hannun takai ta juyo fuskar shi saitin fuskarta yayinda ta qirqiro hawayen qaryanda suka cika mata ido tap inda cikin muryar kuka tace"my man na fhmci ka daina sona kwata wata yanzu wnn abar kake so"
  Ajiyar zuciya ya sauke yana mai kallon yanda hawaye suka fara sauka akan kumatun ta
 yace"malika ta yaya kike tunanin zan daina sonki naso wnn abar da kwata kwata kinsan ita ba tsarina bace"
  Tace"idan baso ba to meyasa  don tayi bacci zaka wani  d'aukota ai tashin ta ya kamata ace kayi,malika nifa tausaya mata kawai ne nayi sbd allurar baccin da take d'auke da ita,
Allurar bacci kuma?eh kunama ce ta harbe ta shine da muka je chemist nasa aka had'a mata har da allurar bacci,amma ai gwanda kabarta a motarka idan tafarka ai ta shigo da kanta dn sam ba ajinka bace a ganka d'auke da ita,yakai hannu yana share mata hawaye yace"naji abar zancen ya wuce"
  Nan ya rungume ta sukayi shiru sae can malika ta kalle shi  tace"hln me taje yi gidan inna da har ta kwana biyu ko inna ce ba lafiya? Yace"mami ce ta qone a hannu "garin me? Nn ya gaya mata bayanin da Rynt tayi mae tayi tsaki a ranta wacce a cikin ran nata take cewa
_"matsiyaciya bata ci ba kenan ai da na nasn hk zata faru da bazan bar mami ta tafi ba"_

Nn ta buga tsaki a fili zata fita man yace"yadai lafiya? Tace "haushi ta ban ne wlh in banda gidadanci teddy ce abin tsoro da har zata 6arar da abinci har ta kai ga qona mami"
  Kallonta kawai man  yayi yakai hannu kan wyrs da ta shiga ruri ya d'aga ita kuma ta fita taje d'aki ta kira pretty byn pretty ta d'aga tace"ke ashe matsiyaciyar bata ci abincin ba 6arewa yayi  har ya sami mami a hannu ta qone shine suka je gidan inna"pretty tace"haba kam ni nsn idan taci sae dai wata ba ita ba,amma kar ki damu yanzu zan kira umma na gaya mata ta kar6o miki wani,malika tace"to shike nn bye tank u"
  Ta katse wyr had'e da tsaki tana fad'in"niko kun sake kawo min maganin ba aiki zanyi dashi ba tunda har ana iya gujewa sharrin sa amma nawa sharrin ko waye ubanta tayi kad'an ta guje mishi wlh.
  Mtsalar kawai ban san yaushe zan sami ciki ba ga man Dr ne bare na iya cikin qarya har na cimma burina bai gano ni ba....qarar wyrta ne ya katseta ta d'aga wyr had'e da shiga bathroom


  Rynt kuwa tun lokacinda da man ya ajiye ta take bacci har akayi zuhur bata farka ba.
 Man ne ya shigo d'akin wanda ya fito daga masallaci kenan yaje gab da ita ya zauna yana mae duba yatsar wanda yana kai hannunsa akan yatsar ne Rynt ta farka had'e da tashi zaune snn takai idonta akan yatsar da take d'an d'auke da kumburi, man yace"har yanzu kinajin zafin harbin ne? Ta girgiza mae kai snn tace kawai dai allurar tana min zafi"
yace"tashi kije kiyi sallah zai daina ne"
 Ba musu ta tashi ta nufi bathroom inda kallonta yake har ta shige bathroom d'in snn ya tashi ya bar d'akin.

Tun daga lokacin bai sake komawa d'akin ba sae a washe gari  da safe su Rynt na shirin school ita da mami sae ga man ya fad'o d'akin Rynt tayi kmr bata ganshi ba sae jin tayi ya jata ya zaunar ya durqusa had'e da riqo qafarta yana duba yatsar ya kalleta snn yace "kumburin ya sauka kenan ? Ta gyad'a mai kai tare da yunqurin tashi ya maida ta had'e da fad'in "zafin allurar fa?shaye da toka ta kalle shi kmr shima yanda yake kallonta ta kauda tata fuskar snn tace"ta daina min zafi"
   Nn ya tashi tsaye ya kalli mami da taxo gurin shi tana fad'in"yaya amma yau kae zaka kaimu school ko?um um mami driver dae zai kaiku,uhm uhm pls yaya ka kaimu kar amana bulala kan kwanakin da mukayi bamuje ba kasan inna ta gaya ma kuma idan ba'ayi musu bayani ba zasu dake mu ne,yace"to shike nn idan kun shirya ku sameni a downstairs,tace"to yaya yanzu da mun gama shiri zamu zo"
  Nn ya fita sukuwa suna gama shiri suka je suka sameshi yakai  su school.

Bayan wata d'aya da faruwar haka Alhmdlh komai na bi dai dai yanda Rynt keso na harakar karatunta wacce ashe kwanyar ban mamaki ce da ita don qwarai qoqarinta ya shiga bayyana sbd duk wata test ko Assignmen kaf take lashewa haka ma class duk wata tambaya da malamai keyi ita ke farkon bada amsa ,
Kan qoqarinta ne wani malami yake mutuwar sonta sbd kaf makarantar ba wanda yasan ita mtr aure ce har frnds d'inta kuwa.
  Kullum idan taje school sae ya aika a kirata amma bata zuwa, ba yanda bai yi ba ya samu ta kulashi ko sau d'aya ne amma fir taqi.

  Rnr wata alhamis yayi aike har ya gaji taqi zuwa kan dole yaje da kanshi har class d'insu ya samu tana wani  Assignment yaje kan desk d'inta ya d'aura hannyensa akai had'e da russunawa yana mata magana cikin yanayi na kmr wanda ke duba mata Assignment d'in itakuwa tayi kmr bada ita yake zancen ba sbd dama tsanar sa take tun farko dmn kowa ya sanshi makarantar d'an iska ne kuma mugu.
   Da yaga taqi kulashi ne ya kar6e Assignment d'inda takeyi ta tashi a fusace cikin d'aga murya tace"kaga malam nifa ba irin en matan nn bace don hk ka daina bibiyar rayuwata haka nagaji!"
  Mgnrta ta tinzirashi  sosai musamman da yaga students duk hnklin su yayo kansu nn yasa ta kneel down ya nemi bulalar dorina sae zabgarta yake har sae da ya gaji don ganshi  yabarta sae kuka take en class na bata hqr a cikin haka ne aka buga tashi wacce har aka zo d'aukar su suka isa gida kuka take ta tafi d'aki aguje zata fad'a kan bed sae jin tayi kawai an fizgota koda ta duba man ne yajata zuwa jikin shi ,
sosai taso qwatar kanta  amma ta kasa sbd riqonda ya mata kan dole ta fad'a kan qirjinsa ta fashe mai da wani sabon kuka.
 A hnkli ya kai hannunsa ya jaye hannuwanta da tasa a tsakanin qirjinsu ya shigar da ita gabad'aya cikin qirjinsa yana mai tmbyr abinda aka mata,saurin ture shi tayi daga jikinta ta nufi bathroom da gudu.



Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2/4, 9:39 PM] ‪+234 703 962 5239‬: [ 2/1/2017]
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```










           🔮🔮🔮🔮
*page* *```41```*
 Ta rufe qofa tare da zamewa jikin qofar ta had'e kai da guiwa tana ci gaba da kukanta.
  Mohd kuwa juyawar sa yayi zai fita d'akin sae ga mami ta shigo riqe da hijab, school bag, da takalmi da socks ta jefarda su kan sofa  ta riqo hannun sa tare da kallon fuskar sa snn tace"yaya anti ta gaya maka me take ma kuka?
  Yace"bata gaya min ba ko kinsan me take ma kukan ne"
 um um nima ban sani ba kawai na ganta tana kuka"
    Bai sake cewa komai ba sai hannunta yaja suka tafi downstairs ya kira kuku ya kawo abinci plate biyu mohd ya kar6a yaba mami d'aya ya tashi ya nufi d'akin Rynt da d'aya.
Wanda yana shiga d'akin yaga giftawar Rynt ta koma bathroom, ya ajiye abincin yabi bayanta .
Yana tsaye ta cire hijb da riga takai hannu zata cire vest kenan ta hango shi ta jikin mirror ai kuwa ta buga ihu had'e da kare qirjinta ta duqe qasa tana fad'in ya fita! bai fita ba sae bayan banta yake kallo da duk ya kasance d'auke da shatar bulala,rai 6ace  ya tayar da da ita tsaye ya juyota yana kallon fuskarta snn yace "wane d'an iskan malami ne ya dake ki haka!
  Shaye da toka ta sake juya mai baya tace"to ni ka fita ai zan zo na maka bayani ne"
  Fixgota yayi ya sake juyo da ita yace"bana son raini wlh gaya min wa ya dake ki nace!ko kuma iskancin da kike min ne suma malamman kika je kina musu,kut!zaki daina bokon nn ne wlh tunda ba kya ji,tayi saurin kallon shi le6ace da baki zuwa kuka tace"wlh Aa shine yake takurani kullum wae shi a dole sae naje office d'insa..... What! kije office d'insa fa!
tace"eh wlh hk  kullum yake aikowa ni kuma bana zuwa shine yau yaje har class d'in mu ya same ni yana gaya min wae shi sona yake shine na mai tsawa nace ya fita haraka ta ni ba irin en matan nn bace shine kawai ya sami bulala ya daken"
  Cikin mugun 6acin rai ya damqota kafad'unta yana kallon fuskarta yace"kinga bana son qarya fa!meye abin so a tare dake da zai wani  nace miki!
kawai dai kin mae iskanci kmr yanda kike min ko!
  Tace"wlh gobe ma kaje ka tambayi en class d'inmu kaji"
  Ya nunata da yatsa snn yace"idan na samu laifin ki ne fa"
Tace"kawai ka cire ni daga bokon"
 yace"yayi kyau Allah kaimu goben"
 Nn ya tafi awa zai tashi sama ita kuma ta rufe bathroom d'in ta watsa ruwa ta fito tayi sallar zuhur.

Washe gari Friday tun safe yazo d'akin Rynt yace da ita"mami kad'ai zaki yi ma shirin school bada ke ba"kmr zatayi kuka tace"meyasa? yace"sae na gama bincikena tukun"
  Ajiyar zuciya ta sauke tace"to"
 Har zai fita sae kuma ya juyo yace"ya sunan malamin?
 Tace" malam a shaqata....
bana son raini sunan sa na qwarai zaki gaya min,to ni ban sani ba ai da haka kawai nake jin ana kiranshi,
 Tsaki kawai yayi tare da fita d'akin yana fad'in"zai shaqata a cell don ubanshi"

4:05pm
Rynt ce zaune ta gama sallah wacce tun sha biyu da mami ta dawo school take jiran shigowar man amma taji shiru sae roqon Allah take kar malamin ya lauye ta bokon ta ko ya sami matsala tana cikin hakane sae ga man ya fad'o d'akin yaje kan bed ya zauna ya tasa ta gaba yana kallo sae can ya girgiza kai yace"kin rainani ko?a rikice tace"me yace maka ne wlh ko mene ne qarya ya maka"
 Yace"kinga yi min shiru! Dan ubanki ashe ba kya saka niqabi cirewa kike idan kinje school!
   A d'an daburce tace"ni kuma"
  Yace"akwai wata ne banda ke to bari kiji bake ba bokon nn kuma wlh ba inna ba ko Abba zaki kai  qarata agunshi baza kiyi nasara ba kuma ki gwada ki gani shege ka fasa!
 Nn ya tashi zai fita ta tashi da hanzari tasha gaban shi inda cikin marairaicewa tace"kayi hqr dan Allah"
 Tsaki yayi ya tureta ya wuce wanda har yakai  bakin qofa ya mird'a handle tasha gaban shi tare da riqe handle d'in tace"kar ka fita dan Allah kabari nama bayani"
  Yace"wane bayani kin tallata fuskar ki kuma kin samu an yaba sae kuma me!
 Tace"bafa haka bane wlh en makarantar ne suka takurani suna ta magana akai shine na cire"
   Gud idea kin kyauta ma kanki.
 Oya!bani hanya na wuce!
  Tace"nidai don Allah kayi haquri ka barni na ci gaba da boko na"
  Yace"kije su da suka saki daina sa niqab d'in su maida ke makarantar very stupid!
  Nn ya mird'a handle zai fita tasa hannunta duka biyu ta riqe tana roqon yayi haquri,
   A fusace ya d'aga hannu zai mareta tayi saurin sake handle d'in   ta kare fuskarta cike da tsoro had'e da  fashewa da kuka tana bashi hqr,bai marenta ba sae ture ta yayi daga jikin qofa ya bud'e qofar ya fita.

Haka Rynt tayi weekend cike da damuwa ganin bakin rai bata zuwa school mami kad'ai ake kaiwa haka ma lesson ana gama ma mami lesson teacher ke tafiya .
  Rnr lahadi da qarfe hud'u tana jin mae lesson yazo ta had"a komai nata na lesson taje tayi zaune falo ta fake yana gama ma mami tazo zata zauna ya kwashi kayansa yace"kiyi hqr yace qaramar nn kawai za'a ci gaba da yi ma lesson "
gyad'a mae kai tayi tana mai danne hawayenda ke qoqorin zo mata.
  Zata haura sama kenan taji fitowar man yana magana a waya taje gurin sa ta tsaya tare da sadda kanta qasa yana gama wyr yace lafiyar kin wani  zo kimmin tsaye ,hawayen idonta kmr zasu zubo take kallon shi tace"don Allah kayi haquri ka barni naci gaba da karatuna kaji"
  Kallon ta kawai yayi yace"naji amma je ki gyara min d'akina"
 Da sauri ta fiddo ido waje tace"cab! Allah sauwaqe wlh bazan sake gyara ma d'aki ba"
 Ya kalleta da kyau yace"ke me kike nufi ne to idan har ma wnn abun kike tunani ki cire dmn sanin kanki ne qaddara ce ta afka min a wnn rnr ina kuma roqon Allah da kar ya sake had'a ni da irin wnn qaddarar,cikin 6acin rai mai had'e da muryar kuka tace"ai dole kace haka tunda ka gama cutar dani,mugu kawai wlh bazan barka ba!
Nn ta fashe da kuka ta tafi da gudu tabar shi nn tsaye cike da mamakin yanda renin wayonta ke qaruwa a kanshi,sae jin yayi malika ta rungume shi ta baya tare da fad'in "my man albishirinka" ya kalleta d'ai ,ita kuma ta rad'a mai magana a kunne da tasa shi wani  irin matsanancin farin ciki kai tsaye ,
ya ta6o cikinta yace"dagske malika! tace"wlh kuwa my man muje ma ka duba a PT strip"
   Nn yaja hannunta cike da farin ciki suka tafi d'akin shi.

 Bayan sllr isha'i Rynt  ta gama sallah d'auke da hawaye a fuskarta tana tunanin hanyar da zata bi ta samu taci gaba da bokon nn don dai kam koda kuskure bata son ta sake zuwa d'akin man bare har yayi galabar  sake cutar da ita.
 Tana cikin hkne taji qarar bud'e gate ta tashi a hnkli ta yaye labulen windonta ta hango motar man ce ta fita ta saki labulen tana mae tunanin idan har zai barta ta koma school in ta gyara mae d'aki ,gwanda kawai tayi sauri taje ta gyra mae kafin ya dawo nn ta kalli mami dake kallon tom and jerry tace"mami muje ki rakani a d'akin yayanki sae ki kunna kallon ki a can kinji"
  Ba musu mami ta tashi suka je Rynt ta gyare  koina tsaf cikin en mintinan da basu fi 30 ba wacce har ta gama gyara d'akin gabanta na dukan uku uku.
  Tana gamawa taja mami suka koma d'aki.
  Sae bayan awa 1 da komawar su d'aki ne taji qarar bud'e gate ta tashi ta duba taga motar man ce ta kunno kai.
Byn an  parker motar driver ya fito da sauri yaje ganbun baya ya bud'e ya kuma zagaya da sauri ya bud'e d'ayan,nn man da malika suka fito kowannen su d'auke da fara'a a fuskar shi man ya riqa hannun malika suka shiga gida yayinda driver ya bisu da kaya niqi niqi.

Rynt ta saki labulen ta koma ta zauna.


  Har sha d'aya na dare Rynt batayi bacci ba sbd jiran ko man zai shigo idan yaga ta gyara mae d'aki amma shiru kmr shirwa ta cinye d'an tsako.
  Gashi sosai take jin bacci amma tasan ko ta kwanta bazata iya yinsa ba idan ba taji, ko zai barta ta  koma school ba.
  Har sha biyu shiru bai zo ba, gata kwance  amma fir bacci yaqi d'aukarta sae juyi take, ta kalli gefen mami da tuni tayi bacci abinta ,ta tashi zaune tare da had'e kai da guiwa sae jin tayi an bud'e qofa tayi saurin d'ago kanta yayinda hawaye ke silalowa a hnkli kan kumatun ta.
  Man ne ya shigo yayi tsaye a bakin qofa yana kallonta ita kuwa sau d'aya ta kalle shi ta kauda fuska tare da share hawayenda suka zubo mata ya qarasa cikin d'akin yaje kan bedside drawern da ke kusa da Rynt ya zauna snn ya kalleta ba yabo ba fallasa yace"lafiyarki kike kuka da daren nn"
  Tace"kace idan na gyara ma d'aki zaka barni na koma school ko"yace"yaushe nayi dake haka? kmr zata yi kuka tace "d'azun kmr hk fa ka nuna min"
  A tunanin ki kenan amma ni ba hk bane,ya fad'i hkne tare da kallon fuskarta sae yaga nn take hawaye sun zubo mata nn  yaji ta burge shi sosai sbd yanda take son karatu.
 ya sauke numfashi snn yace"zan barki ki koma d'in amma fa da sharad'i"da sauri ta kalle shi tace"ina jinka gaya min"
 Yace"Duk kika bar wani  malami ya sake  fad'awa sonki ko wlh bake ba makarantar koma nace gabad'aya bokon don ba kud'in banza nake dashi  da zan kai ki karatu kije kina soyayya ba idan kuma har kince soyayya zakiyi ni kinma hutar dani kuma kin hutar da kud'ina don sallamar ki zanyi ki koma can gidan inna da taji zata iya.
  Rynt ta sauke ajiyar zuciya tace" naji zan kiyaye,yace"idan ma kin kasa kiyayewa wa kanki,
 Nn ya fita tayi hamdala wa ubangiji ta kashe wutar d'akin ta kwanta.

 Washe gari da taje school wata qawar ta da suke shiri sosai take ce mata
"bari Rynt yanyanki yayi wlh don naji dad'in da yasa aka kori malam a shaqata daga mkrntr nn shikenan yanzu mun huta da muguntar shi"
   Rynt tace"hm korar sa yasa akayi?au bai gaya miki bane? tace"um um"
 Hm bari kedai naso ace rnr Friday d'in nn kinzo wlh don  qaramin yaqi aka tashi yi a makarantar nn  dmn en sanda fa yayanki ya kiro mishi yace a tafi dashi sae da qyar principal ta shawo kan yayanki a cewar yayi hqr kar yasa a kama shi zata sa ayi mai transfer zuwa mkrntr maza don dama ta jima da jin wasu halayen shi maras kyau da ake fad'i.
  Rynt ta kalli qawar ta tace"to a bakin wa yaji cewa bana sa niqab hln?tace"gsky ban sani ba kawai dai munji hayaniyar fad'an su ne"
  Qawar tace"amma yayanki yayi aure ko? Rynt tace"eh"
 tace"kai amma fa ko waye matarsa tayi sa'ar miji kuma kema kinyi sa'ar yaya"
 Ta6e baki kawai Rynt tayi ta jawo littafinta tana dubawa sbd haka take ko yaushe ko ba test idan dai basa komai a aji ,bazatyi strn banza ba sae dai ta jawo littanfanta tana karatu.

5:00pm
Rynt ce da mami sun dawo daga school suka sami malika da mohd zaune a falo ,malika nata zubawa man kukan shwaga6a wae ita yunwa takeje bata iya cin abincin kuku don ko warinsa bata son ji.
  Tana ganin su Rynt sun shigo tace"yauwa my man kasa wnn abar ta dafa min  abinci wata qil ko zan iya cin nata.
  Rynt na jinta taji sa6o ma take bata dai kula su ba tayi ficewar ta ita da mami.
  Shi kuwa mohd kmr ma ince tare suka shigo d'akin shida su Rynt ,
Ya kalli rynt dake qoqarin ajiye school bag yace "ke yi sauri ki cire uniform kije ki d'aurawa malika abinci"
  Rynt ta ta6e baki tace"hm wae sa6o idan bazata d'aurawa kanta ba ai sae ta zauna da yunwar"
  Yace"bana son raini wlh maxa ki cire uniform kije ki d'aura mata girki "
  Tace"wae ya zaka ce na d'aura mata girki wane irin ma rashin tausayine ynx daga dawowata daga mkrnta"
  Yace"haka zaki ce to bari kiji idan har kina son ci gaban karatunki to fa lallai sae kinyi abinda nake so wlh"
  Tace"naji amma bafa zan d'aurawa qatuwar banza girki ba"
 Yace"well ya rage naki idan kina son ci gaban karatun ki kije ki d'aura mata girkin idan kuma ba kya so ba dole sae kiyi zamanki.


Billy Giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2/4, 9:40 PM] ‪+234 703 962 5239‬: [2/2/2017]
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```










           🔮🔮🔮🔮
*page* *```42```*
Yana gama fad'ar hk ya fita.
 Wani  irin baqin ciki ne ya tokare Rynt a wuya da har ta sami kanta dajin qwalla sun cika mata ida bata dae bar sun zubo ba ta ajiye school bag ta cire takalmi da socks takai su inda ya dace snn ta fito downstairs ta wuce su man zaune a falo ta tafi kitchen ba tare da tako kalli gefen su ba.
     Malika tace"matsiyaciya ai da na d'auka ko bazata fito ba"
 Man yace"dolenta mana tunda tana son ci gaban karatun ta.
    malika ta tashi tare da fad'in "bari ma naje naga wane d'an iskan abinci ne take da niyyar dafa min.

Rynt kuwa tana shiga kitchen ba abinda tayi niyyar dafawa sae indomie har ta d'aura c pot ta zuba ruwa sae ga malika ta shigo  ta kalli Rynt a yatsine tace"ke matsiyaciya me kike shirin dafa min ne "Rynt tayi banza da ita ,malika tace"idan kin iya kar ki bani amsa amma wlh ina mae gaya miki kar ki kuskura ki dafa taliya ko indomie,sakwara zaki min da miyar agusi"
   Still dae Rynt bata tanka ta ba har ta fita taje gurin man cikin masifa  tace"wae da yrnyr indomie na samu zata dafa min don ta rainani"
   Yace"wae da to me kike son ta dafa miki? Sakwara mana da miyar agusi,ya kalleta yace"amma kinsan tana da lesson 5:30 to six har yaushe ta gama,da dai kin barta kawai ta dafa miki indomie d'in, kallon sa tayi tace"ban gane ba tausayinta kake ji ne ko yaya?
  Yace"ko d'aya mae lesson d'in ne bana son ta 6atawa lokaci"
  Tace"to ai sae a farawa mami idan ta gama min girkina sae a mata"
  Yace"ok"

 Suna nn zaune cikin en mintina sae ga Rynt ta fito riqe da plate d'in indomie takai kan center table d'inda ke kusa da su ta ajiye ta kuma yi ficewarta.
 malika ta bita da ido sake da baki snn ta kalli man da ya gama waya knn
 tace"kaga er iska indomie d'in fa ta dafa min"
  Ya tashi tare da fad'in "bari ina zuwa"
  Yaje ya sami Rynt tana shirin shiga bathroom tayiwa mami wanka ,
ya dakatar da ita cikin cewa"ke zo nn "bata je ba sae kallon sa da tayi yace"me malikà tace miki ki dafa mata? tace"sanin kanka ne ban iya wnn abincin ba don ni abu biyu kawai na iya dafawa daga taliya sae iñdomie....bana son raini da kike dafawa a gidàn inna fa?
Tace"Bani ba kam sae dai ko baba hurera"
kallonta yayi kmr zai ce wani  abu sae kuma ya fasa ya fita, Rynt ta ta6e baki ta bishi da ido wacce ba klr abincinda bata iya ba a gidan inna qin yine kawai tayi.
  Taja hannun mami dake fad'in"wae anti meyasa anti amarya yau tace bata cin abincin kuku? Rynt tace" oho mata kedai muje ayi wanka muci abinci kafin mae lesson yazo ko"
 Mami tayi murmushi dan da murmushi Rynt tayi mata mgnr,
 wa enda tuni sun shigo bathroom sae ruwa Rynt ta had'a tayiwa mami wanka byn ta gama mata mami ta fita ita kuma tayi nata.

Mohd kuwa koda yaje ya snr da malika cewa Rynt bata iya wnn abincin da tasa ta ba sae masifa take ita lallai sae Rynt tazo kuku ya nuna mata yanda ake don ita kam baza taci indomie ba da qyar man ya samu ya lalla6ata har ta yarda taci indomie a cewar gobe sae Rynt ta dafa mata duk abinda take so.

 Rynt tana fitowa wanka sharp sharp ta shirya suka ci abinci sae dai koda suka gama har sun shigo cikin lokacin lesson d'inta tayi saurin kwasar littafanta ta tafi ta samu kuwa har mai lesson d'in yazo yana jiranta.
 Wnn karon man baizo ya fake kmr ko yaushe ba don yana can shida malikarsa a d'aki.
 6:00 ake gama mata lesson d'in sae ya farawa mami ana yin magrib ake gama mata ita kuma.
But rnr Thursday ,Friday Saturday and Sunday suna samun enuf time da ake yi musu lesson bcs thursday 2:00 ake tashi friday 12:00 then asabar da lahadi islamiya ce 8am suke zuwa su dawo after 2 yayinda duk ranakun nn hud'u da qarfe hud'u lesson tearcher d'in ke zowa bashi yake barin gidan ba sae anyi magrib.

 Bayan 2 dayz duk kwanan nn biyu Rynt ke dafawa malika abinci idan sun dawo daga school amma ba wani  abinci bane face indomie wacce take silalawa sama sama takai ba tare da ta damu da ta nina ko bata nina ba.
  Gashi kullum malika sae masifa take yiwa man ita tgji da cin indomie a kira kuku ya nunawa Rynt kallolin abinci ta riqa dafa mata,Man kuwa sae rarrashinta yake yana lala6ata sbd  hk kawai yaji baya son kuku ya koyawa Rynt abinci inda dae mace ce.
  Rnr dai ta matsa mai kan dole ya kira kuku suka sami Rynt a kitchen ,man ya dakatar da Rynt dake shirin d'aura indomie snn yace da malika"me kike son ta dafa miki ?
Nn ta shiga shafa cikinta a yangace snn tace"inaga yau jellop rice muke ra'ayi nida babynka amma taji busasshen kifi da manja a kuma zuba ganyen alanyafu snn ayita da yaji sosai"
 Yace"shikenan abinda kk so? Tace"eh ni zanje na kwanta na huta nagaji da tsayuwar nn yace"ok"snn ta fita nn ya maida dubansa gun Rynt yace"oya ga kuku nn zai nuna miki komai yanda zakiyi".
 Kallon sa kawai tayi snn ta kalli kuku shi kuma man ya nemi kujera ya zauna yana duba jarida.
  Kuku yazo gaban Rynt ya had'a komai da za'a sa a jellof d'in snn ya d'ura c pot  ya zuba manja a cewar idan ya d'auko zafi sae ta saka niqaqqin tattasai da albasa da tarugunda aka niqa sama sama bayan en yankakkin da ke ajiye gefe da sae jellop d'in ta d'auko dafuwa xa'a saka su.

 Hanklin kuku nakan  busasshen kifin da yake d'an qara gyrawa yayinda Rynt ke kallon manja har yayi mugun zafi ,ta d'auko kofin ruwa kai tsaye ta kwara cikin manjan,
baaa! belar wuta ta fito tayi sama! ai kuwa Rynt ta buga ihu da ita har kuku ba mae kama wani sae qoqarin 6ira suke su fad'i wanda tsirif ya rage Rynt ta fad'a kan jikin kuku man yayi saurin tashi ya fizgota zuwa jikin shi,
Yayinda cikin mugun 6acin rae man ya kalli rynt yace"u are very stupid! ke ba kya ganin inda zaki fad'a ne!
 Ta rufe ido gam had'e da fashe mai da kuka wacce da gayya ta zuba ruwan amma tayi mugun tsorata da ganin yanda wutar ta fito a manja, dan ynz hk jikinta sae qyarma yake.
  Man kuwa ganin yanda  Rynt ta rufe idanunta sosai tana  kuka ,ya d'auka ko manja ya shiga mata a ido nn yakai hannu zai bud'e ya hura mata idon amma taqi yarda sae tsalle take tana kuka bayan ba abinda ya shiga mata a idon pretending ne kawai don ta samu ta zillewa girkin.
  Da hk ta qirqiro tari tana tayi se duk Man ya damu ya rasa yanda zai mata ya kalli kuku cikin daka mae tsawa yace"dan Allah qaton banza tashi kaje ka kashe wancan abun duk yabi ya damu mutane!
  Da hnzari kuku ya tashi yaje ya kashe gas cooker,
man kuwa yaja Rynt har zuwa d'akinta wacce sae tari take ga kuma idanuwanta dake rufe still .
  Bathroom ya nufa da ita ya wanke mata fuska ya ciro farin handkerchief d'insa ya share mata fuska snn ya fito da ita ya zaunar kan bed tana d'an ci gaba da tari kad'an kad'an nn yaje ya tsiyayo ruwa a glass cup ya zauna snn yace"bud'e idonki ga  ruwa kisha "
  Qin bud'e idon tayi sae hannu takai tana lalube sae jin tayi yakai cup d'in ruwa a bakinta tasha ruwan kad'an ta kwanta shi kuma yasa blanket ya rufa mata jikinta ya fita sae a snn Rynt ta bud'e idonta a hnkli tare da saurin yaye blanket ta tashi ta watsa da gudu bathroom sbd fitsarin da yayi mugun matsar ta.



Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2/4, 9:46 PM] ‪+234 703 962 5239‬: [2/4/2017]
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```










           🔮🔮🔮🔮
*page* *```43```*
Mohd kuwa d'akin malika ya nufa ya sameta kwance  kan bed sae chat take tana qyalqyatar dry.
  Ya  zauna kusa da ita
ta mirgino tayi pillow da cinyoyinshi tana ci gaba da chat d'inta,ya kar6i wyr yace"wnn yrnyr fa in banda shirme ba abinda ta iya kawai kiyi hqr na nemo wata yrnyr da zàta riqà mana girki shi kuma kuku ya kama gabansa don ynz sam bana son ina ganin sa a gidan nn, da hanzari ta tashi zaune tare da fad'in"ban gane ba nifa gsky wnn abar nake son ta riqa min abinci don ma ka daina zancen d'auko wata kuma kuku meye mtslr shi, shida ma zai riqa koya mata kalolin girki.
  Malika na gaya miki bazata iyaba don in banda shirme da  qoqarin qona min gida ba abinda ta iya .
  Tace"wae kamar ya ban gane ba?
Yace"baza ki gane bane tunda ba'a a gaban ki ta tafka shirmen ba.
  Tace"to ai koma yaya ne yau da gobe zata iya"
 Mtsw mohd yayi d'an guntun tsaki yace"malika bana son gardama kin sani, ki bari kawai a nemo maki wata yrny ba dole sae ita ba"
  Cikin fushi ta sauka kan gadon tace"wlh  gsky ni ita zata ci gaba da girka min abinci idan ba hk ba kuwa wlh sae dai a zubar da cikin nn kowa ma ya huta"
  Kmr saukar guduma yaji zancen ya sauka a kunnen shi ya tashi da hanzarinsa ya qarasa gurinta ya riqo kafad'unta cikin mugun damuwa yana kallon fuskar ta yace"malika kinsan me kike fad'a kuwa ,a zubar da cikin nn fa kika ce"
  Kuka ta fashe dashi snn tace"eh mana ina son cikin nn amma dole zan zubar dashi tunda baka iya d'aukar lalura ta da duk wani  abu da nake so"
  Rungume ta yayi yace"is ok naji zata ci gaba da yi miki girkin amma sae abinda ta iya zata girka miki kin yarda"
  Ya fad'i hkne yayinda ya d'ago fuskarta yana kallonta ,ta share hawayen funafurcin dake kan fuskarta tace"to ya zanyi my man  tunda babynka ya d'aura min lalurar son cin abincinta,amma kuma gsky yau bazan ci indomie ba sae dai ko fita zamuyi a siyo min gasasshiyar kaza na d'aura da hollandia milk"
  Yace "to ai wnn mae sauqi ne shirya muje"
  Tace"ai a shirye nake mayafi kawai zan d'auko nn taje ta ciro mayafi ta  yafa suka fita.


9:00pm
Rynt ce kwance cikin tunanin anya ko za'a maida mami kuwa sbd  yau suna dawowa school abinci kawae suka ci aka kai mami gida.
 Tana cikin hkne taji qarar bud'e qofa tayi saurin kallon qofar don a tunaninta ko mami ce sae taga man.
    A bakin qofa ya tsaya yana tmbyrta mami fa?
tace"ka manta tana gida"
 Agogon hannusa kawai ya kalla ya juya zai fita Rynt tayi saurin katse shi da cewa"don Allah idan d'auko ta zakaje zan bika"
 wani  kallon kin raina ni ya mata snn yace"me zakije yi a gidan ?tace"zan gaida su mama ne na jima banje ba wlh"
  Yace"shikenan ki same ni a waje idan kuma kin jima zaki samu bana nn"
 Yana fita tayi saurin zuwa ga wardrobe ta bud'e ta nemo wata doguwar rgr atamfa ta cire riga da wandon baccin da ke jikinta ta saka ta nemo hjb ta fesa turare tasa snn ta d'auko takalmi tasa ta fita da sauri har tana hard'e qafafuwa.
  Koda taje har ta samu ya tada motar shiga kawae tayi yaja suka tafi.

Suna isa gidan 6anfaren su mohd suka fara nufa ,ummar sa suka samu zaune a falo sukayi sallama sae kallon su tayi ba tare da ta amsa ba,har qasa Rynt ta durqusa tana gaida umar tashi wacce ta watsa mata muguwar harara Rynt ta tashi abinta zasu bar 6angaren da ita hr man da shima ya gaida ummar tashi bata amsa ba.
    Lokacin da suke qoqarin fita ne Abba ya sauko nn downstairs Rynt na ganin shi tayi saurin durqusawa tana gaida shi, ya amsa da fara'ar sa yana fad'in"yau kune a gidan "
 Tace"eh Abba"
 Yace "to ya gida ya karatu tace"duk Alhmdlh"
  Byn nn ne man ya gaisa da Abbanshi snn yace"mu zamu tafi Abba dama mami ce muka xo d'auka "
   Nn Abba ya ciro 5k a aljihu ya bama Rynt wacce taqi kar6a har sae da qyar Abba ya samu ta kar6i kud'in tayi mai godiya snn suka fita.

Tare suka je 6angaren su saliha mami na ganin su tazo da gudu ta riqo hannun kowanen su.
  Umman mami har Abbanta duk suna nn zaune a falo nn su Rynt suka gaida su man ya fita a cewar yana jiran su a waje,da yake mami a shirye take sae bin yayan nata tayi, hkn yasa itama Rynt ta tafi zata bisu umma ta kirata suka tafi d'aki.

Turarukka ne masu qamshi umma ta bata da kuma kayan kwalliya wad'anda dama a tsare suke cikin  ledar su da aka yo shopping tayi niyyar bawa mami ne ta kai mata sae gashj taxo.
  Rynt ta kar6i ledar tana yiwa umma godiya,,umma tace"ai inshaAllh kwanakin zan zo gidan naku"tace"to mama sae kinxo"
  Har Rynt zata fita umma tace"af na manta fa rnr da mukaje visiting akwai wani  saqo da saliha ta bani tace na baki har ma tace tana gaida ke,Rynt tace"Allah sarki mama bata ce dake fushi take dani ba?
 um um ko d'aya kawai dai ta shiga damuwa sosai dajin kinso zowa mohd ya hana,Rynt tace"hln inna ce ta gaya mata ko"
  Mama tace"eh kam don inna sae fad'a take tayi ganin har za'a tashi visiting baki zo ba,don tace mana har zaku shiga mota mohd ya same ku yace mata su su tafi wae zai kaiki daga baya"
 Rynt tace"Hm hk yace mata mama"
  Mama tace"to ko meyasa yayi hkn kuma sae bae kaiki d'in ba, koda yake hln mohd sae shi.
 ta fad'i hkne tare da d'auko wata er qaramar leda tace"kinga saqon amma kuma ban san ya akayi ledar ta yage ba, bari na cire nasa maki a cikin ledar kynki.
 Nn mama ta ciro kayan ta saka a cikin ledar turarukka da kyn kwalliyar da taba Rynt,Rynt tayi godiya tafita tana sauri don tasan man ya gama suqewa da jiranta.
   koda tazo sae fira ma ta samu sunayi shida mami a cikin mota.
 Tana shiga ya tashi motar suka wuce.
 A maimakon yaje dasu gida sae wani  babban mall ya tafi dasu.

Shida mami kawai suka shiga suka bar Rynt cikin mota.
  Chocolate, biscuit,sweet n drinks ne suka siyo wato kayan  mami da ake d'ibar mata tana zuwa school dasu.
   Bayan su basu riqo komai ba sae ice cream .

Tun a mota mami ke shan ice cream d'inta wacce koda suka iso gida ta shanye har tayi bacci.
 Da suka iso gida man ne ya d'auki mami da tayi bacci,
 Rynt kuwa kyn hannunta kawai ta d'auka ta shiga cikin gida shi kuma man kuku ne yazo yana jidar kyn da suka siyo yana shigar dasu.

 Rynt da shigarta d'aki ta d'auki kyn baccinta ta nufi bathroom ta saka ta fito linke da wad'an da ta cire taje ta saka a wardrobe taje ta kwanta sbd wani  irin bacci da take ji .
Sae a snn man ya shigo ya shinfid'e mami yaje ya shigo da kayayyakin da suka siyo.
  Yakai ledar ice cream kan bedside drawer ya ajiyewa Rynt nn idonsa ya qyalla kan ledar Rynt dake ajiye a gun.
Har zai wuce sae kuma ya tsaya yana kallon farin abinda yake hangowa ciki,
 kai tsaye yakai  hannu ya ciro kyakkawar sabuwar farar bra da kuma farin pant,ya cira kyn sama yana kallo yayinda Rynt ta rufe idonta cikin mugun jin kunya wacce kwata kwata bata lura da sune mamar saliha tasa a ciki ba duk a tunaninta farar vest ce saliha ta siyo ta aiko mata.
    mohd ya ajiye kyn snn ya kalli Rynt da taqi yarda ta bud'e idonta yace"dama don kije ki roqo wasu kayan ne yasa kika bini"
  Bata bud'e idon ba sae cewa tayi"Allah sauwaqe ni wlh roqo ba halina bane"
 Yace"ok idan har baki akayi to meyasa kika kar6o byn duk tulin irin kyn nn da kk da su a cikin akwatinanki ko kuma kina nufin kaf kin murje su"
  Komai qin ce masa tayi hkn yasa ya tafi sae gurin akwatinan ta ya bud'e wacce undies ke ciki ,
komai na ciki ba abinda tayi aiki dashi sae qwarorin vest da pant amma kuma se duk baiga bras ba sae wata babbar farar leda ya gani da qunshin kayanda bai san meye a ciki ba, bud'e ledar yayi ya zazzage kaf abinda ke ciki ga mamakinsa sae yaga duk brasseries d'in ne ba wacce aka ta6a, nn yaje ya jawo Rynt yazo da ita gurin akwatinan ya nuna brassieres d'in yace"uban wa kk son ya saka wad'an nn kyn da har yazun ba alamar ansa ko d'aya!
  Komai bata ce masa ba asalima ko gefen akwatinn taqi yarda ta kalla sbd bra na d'aya daga cikin abinda Rynt tafi kunyar gani sosai.
Mohd kuwa tsawa ya daka mata yace "wae bada ke nake magana bane!
   Kmr zatayi kuka ta kalle sa tace"to ai ni ban fara sawa ba nayi qanqanta"
 Qirjin ta ya kalla tare da fad'in"what!sae kuma yayi tsaki yace"kaji mtslr bagidajen mutum  kuda kanku ke 6atawa kanku tsari snn ya kalleta tare da fad'in" to wlh bari kiji by tomorrow ki tabbatar kin fara sakawa idan kuma kika qi nida da kaina zan saka miki, kuma kiqi d'in kiga ikon Allah.
  Daga hk ya fita yabar d'akin ,
Yayinda Rynt tayi saurin rufe akwatin undies tana qunquni ita wlh bazata sa wnn abin kunyar ba.
  Taje ta d'auki wad'anda saliha ta aiko mata har ta ware ta kalla sae kuma tayi saurin rufe idonta ta dunqule taje ta tura cikin akwatin undies.



Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2/5, 11:55 PM] ‪+234 703 962 5239‬: [ 2/4/2017]

 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```











           🔮🔮🔮🔮
*page* *```44```*
Washe gari da safe Rynt ce ta fito daga wanka d'aure da towel  sae sauri take zata d'auko hjb a wardrobe sbd wanda ta shiga dashi wanka tayi rashin sa'a garin d'aukowa ya fad'i ya jiqe se ma ta wanke shi gabad'aya.
  Kafin takai gun wardrobe sae ga man ya fad'o d'akin tayi saurin komawa bathroom tana fad'in wae meye hk dan Allah  sae ka shigowa mutane d'aki ba sallama.
      Qala bae ce da ita ba sae time ya kalla snn ya kalli mami dake kwance  tana sharar bacci.
  Yace da Rynt"fito ki tashi yrnyr nn ki mata wanka lokaci ya tafi"
  Tace"to kafita mana"
Yace"gaya min abinda zaki d'auko na kawo maki"
  Tace"hijabi nake so yana cikin wardrobe"
 Nn ya tashi a maimakon yaje wardrobe sae ya nufi gurin akwatinan ta ya bud'e akwatin undies ya ciro bra da pant d'inda saliha ta aiko mata yaje dasu har bakin qofar bathroom yace"kar6i"
 Ta bud'e qofa kad'an ta turo hannunta ya d'aura mata bra da pant,tayi saurin jefar dasu tace" wae meye hk dan Allah nifa hjb nace"
  Ya d'auko kyn tare da fad'in ki fara saka wad'an nn tukun,
tace" wlh bazan sa wnn abir kunyar ba,
  Yace"gud baki tashi fitowa ba knn"
  Tace"Aa dan Allah kar kasa muyi letti"
 Baice da ita komai ba sae mami yaje ya tayar yaje da ita qofar bathroom yace"bud'e ga mami ki mata wanka"
  Kad'an ta bud'e qofa ta leqo ta hango mami tsaye snn ta d'an qara bud'e qofar ,mami ta shiga ta rufe.
 Bai fita ba yayi zaman sa har ta gama ma mami wanka da zata turo mami ta hango shi kwance  abinshi kan bed yayi pillow da hannyensa ya kuma d'aura qafa kan qafa yayinda idanuwansa ke rufe wanda ga dukkan alama ya soma yin bacci.
nn ta rad'awa mami magana a kunne tace"idan kinje ki d'auko min hjb amma kar ki bari yayanki yaji motsin ki "
tace"to Anti"
  Taje a hnkli a hnkli ta bud'e wardrobe sannu,  ta hango hijabban Rynt duk sama suke bata cimma ko d'aya, daga nn inda take ta bud'e murya tace"Anti gurin hijabbayanki ya min nisa"
  Firfigit man ya farka daga d'an guntun baccin da ya d'auke shi wanda kai tsaye idonsa ya fad'a gun Rynt dake la6e a bayan qofar bathroom ta fiddo kanta yatsanta akan lips d'inta tana fad'in mami tayi shiru.
  Tashi zaune yayi tare da watsa mata mugun kallo ta rufe qofa da qarfi cikin jin haushi mai had'e da son tayi kuka.
  Man ya kalli mami wacce ke fad'in "yauwa yaya ka tashi? anti ke son a d'auko mata hijabi zaka d'auko mata?
  Ya lumshe ido a hnkl ya kuma ware su snn yace"je d'auko Vaseline ki shafa  tukun "
  Nn ta nufi dressing mirror shi  kuma ya tashi ya ciro mata uniform a wardrobe d'inta.
 Byn ta shafa Vaseline ya bata uniform ta saka tare da taimakon shi,snn yace"taje ta kar6o break fast a gurin kuku mami na fita Rynt na bud'e bathroom da sauri dan ta d'auka ko man ne ya fita.
  Ido hud'u sukayi ita da man yayinda ta marairaice mae fuska kmr zatayi kuka yace"Allah ina gaya miki idan ba kin saka wnn bra ba ko, ba inda zaki"
  Cikin murya kuka ta rufe bathroom d'in tana fad'in "wlh bazan saba uhm uhm"
   Bai sake ce mata komai ba har mami ta dawo d'auke da plate biyu tace"har da anti na kar6owa"
 yace"to ci naki idan ta fito sae taci nata"
  Tace"to yaya anti zata sa muyi letti fa kabata hjb ta fito"
  Yace"ai ke bazakiyi letti ba kina gamawa za'a kaiki"
  Tace"ita anti fa?
Yace"ita ma idan ta shirya za'a kaita"
  Daga nn mami tayi shirunta tayi breakfast d'inta tana gamawa ta d'auki koman ta na zuwa school har dasu chocolates,biscuit da drink,
 Mohd yace"idan kin kar6i lunch box d'inki a gun kuku sae kije driver ya kaiki kinji"
  Tace"to yaya amma pls ka d'aukowa anti hjb tayi sauri ta shirya kar tayi letti a mata bulala"
 Yace"naji"
 Nn ta fita shi kuma ya tashi ya d'auki bra yaje jikin qofar bathroom yace"oya bud'e ga hijab d'in"
  Ba musu Rynt ta bud'e tare da turo hannunta sae jin tayi yaja hannun ya fito da ita a toilet corner ta fasa ihu tana qoqarin komawa  bathroom ya fizgota ya kama duk hannuwanta ya maida baya ya riqe da d'ayan hannun sa snn ya manna ta a jikin bangon toilet corner d'in.
  Kuka ta soma yimae yace"shiiii bana son jin kukanki,meyasa ke mutum baya binki da lalama ne?
  Dake nake ki gaya min!
 To ni bazan iya sawa bane don Allah ka rabu dani, yace"ke ko kunya ba kya ji duk wnn ubañ qirjin naki kice ba kya saka bra sbd gidadanci irin naki ko ,bari kiji ni taimaka miki ne zanyi don idan baki fara sa bra a yanzu ba nn gaba zasu dawo miki ne tmkr ledar pure water"
  Turo baki tayi tace"ba wani  nn kuma ni Allah tsare ni wlh can da bakinka"
    Tsawa ya daka mata har sae da ta tsorata yace"dan ubanki meyasa kika raina ni wae!gaya min meyasa!
 A rud'e ta qara manna
 jikinta a bango.
 Ya sake daka mata tsawa yace "wlh idan baki gaya min ba zan rabaki da towel d'in nn na kuma zaneki!
  Gama fad'ar hk yakai  hannu zai fizge mata towel,
 Ta fasa ihu a rikice
tace"wayyo Allah zan fad'a"
 Yace"oya inajinki gaya min"
 Sae da ta turo baki snn tace"to ai duk kaine ka siya abinka"
  Da mamaki yace"ni d'in da kaina lallai ma yryr nn keda at all bansan ko ke er gidan uban waye ba daga kawai ina ganin ki gidan inna shine kika wani rainani,ko kuma gani na da kike ya kawo rainin!
  Tace
_"kashe min mahaifi dae dakayi kuma wlh bazan barka ba"_
tayi mgnr ne a rai yayinda a fili ta fashe da kuka snn tace "nidae kayi hqr ka barni na tafi school dan Allah"
  Yace"ai school ke kika hana kanki zuwa"
  Tace"wae don Allah meyasa kake son takura ni ne wlh ni bazan iya sa wnn abar ba"
  Yace"ai ni zan iya sa miki d'in"
  Tayi saurin cewa "nifa ba hk nake nufi ba"Yace"ai kinsan na gaya miki duk baki saba da kaina zan sa miki"
  Tace"wlh bana so"
Bai kula ta ba sae hannuwanta da yake riqe dasu ya sake yana qoqarin sakà matà bra, tayi sauri zata kwasa aguje ya damqo towel d'inta ai kuwa ya rabu da jikinta ta fasa ihu ta koma bayan shi da gudu ta 6uya tana fad'in"don Allah kar ka juyo kayi hqr kaban towel d'ina"
  Sosai abin ya soma ba man dariya don gabad'aya ta daddamqe shi sae roqon take kar ya juyo danne dryr da yake ji yayi yace"meye kuma ban gani ba bayan a gaban idona towel d'in ya zame"
  Tace"ba abinda ka gani wlh"
kai tsaye taji ya jawota ya mannata a qirjin shi yace"wae bakin ki baya mutuwa ne ke kam"
  Bata iya ce masa komai ba sae qoqarin komawa bayansa take ta 6uya yayinda shi kuma yake qara mannata a qirjinsa,yace "wae meye abin 6oyo a jikin naki ne keda kan qwailancin ki bra ma baki fara sakawa ba,
 tace"wlh kasan ba don hk ba kam sae don ra'ayi"
  Au haba naji
nn yakai hannu da wasa zai ta6o qirjinta tayi saurin buge hannun tace"wea meye hk dan Allah"
    Bae kulata ba sae hannunsa yakai  yana yawo dashi a hnkli kan jikinta yana yi kmr zai ta6o qirjinta sae kuma ya wuce zuwa bayan banta yana shafawa yayinda Rynt ke kuka tana buge masa hannu shi kuma yaqi ya daina har abun  ya zamo musu kmr wasa,gashi still taqi yarda ta d'ago daga kan qirjinsa gudun kar ya ganta.
  Daina wasa yayi da jikinta ya d'ago fuskar ta yaga duk hawaye ce,yace"kinga zanyi magana dake amma bana son tsiwa mgnr hnkli nake so"
  Da kin min hk bazan takura ki akan dole sae kinsa bra ba"tace to ina jikinka"
  Sae da yakai hannu ya share mata hawaye snn yace"meyasa ba kya son saka bra ko kinada wata matsala ne?
  Tace"Aa ni kunyar ganin ta nakeji shiyasa bazan iya sawa ba"
  Yace"bazan 6oye maki ba kinada qirji mai kyau da bai kamata ace kin bar ya lalace ba don hk ki ajiye kunya ki fara bashi kulawar da ta dace"
   Shiru tayi don ita gabad'aya jin kunyar zancen sa ma take ji.
   Bai damu da jin amsar ta ba sae jayeta yake qoqarin yi daga jikin shi  taqi yarda da hkn don sae qara 6oye qirjinta take a jikin shi,nn ya cire farar suit d'in jikin shi ya saka mata yana mae kallon fuskarta kmr wanda ke neman wani abu a jikin fuskar.
yace"ba zancen school yau kin riga da kinyi letti don kar kice zaki tafi"
  Daga hk ya wuce ya barta nn tsaye wacce har ya fita kallon sa take snn ta kalli rgr jikinta da ya saka mata mae da'auke da wani irin qamshin dad'i.
   Fitowa tayi ta bar towel d'inta can ayashe ,
taje jikin wardrobe ta bud'e snn takai hannu jikin wata rgr atamfa har zata ciro sae kuma bata ciro ba ta rufe wardrobe kawai taje ta kwanta kan bed ta rufe jikinta da blanket har izuwa wuyanta daga nn ba jimawa bacci ya kwashe ta.



Billy giro😊
 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2/6, 10:15 AM] ‪+234 703 962 5239‬: [ 2/5/2017]
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```










           🔮🔮🔮🔮
*page* *```45```*
Man kuwa yana fita d'akinsa ya tafi ya sami malika zaune kan sofa tana shan 'ya'yan fruits yaje kusa da ita ya zauna ta kaimai slice d'in kankana a baki tare da fad'in"ya baka fita ba ko kun fasa ne? Eh an d'aga meeting d'in sae zuwa 12,tace"OK" daga hk suka ci gaba da shan fruits suna er firar su a cikin firar ne man ya d'auko laptop d'inshi yana nuna mata wasu kayan jarirai da ya gani masu kyau yace"duk a England ake samun su,tace "wow yaushe zamu je siyo kyn? Yace"na fison sae cikinki ya farà qwari muje har sae idan kin haifu snn ko zamu dawo amma zan riqa yi ina dawowa sbd aiki na,kiss ta d'aura mai tace"wnn ba matsala bane"
 Yayi d'an guntun murmushi yana ci gaba da nuna mata wasu kyn jarirai.

Rynt kuwa ta jima kwance  abinta tana baccinda ya mata dad'i fiye da kowanne.

11:30
Man ya shigo d'akin still sae bacci take,dube dube ya shiga yi ta inda zai ga suit jacket d'insa wanda har bathroom ya duba amma bae ganta ba.
  Hkn yasa yazo ya durqusa gab da ita yakai  hannu ya d'an yaye mata blanket  kad'an, nn yaga jacket d'in na jikinta hannuwanta na jikin qirjinta da ta kama magamar jacket d'in ta riqe gam.
   Ganin hkne yasa ya janye hannuwanta a hnkli ya rufe mata buttons wanda garin hkne ya hango d'an bum short d'inda ke jikinta kauda idonsa kawae yayi ya rufa mata blanket ya fita .

Ba ita ta tashi ba sae qarfe d'aya.
Ta tashi zaune tana mai kama mgmr jacket d'in,ga mamakinta taga an sanya mata buttons d'in rgr,ai kuwa taji  fad'uwar gaba don tasan mohd ne ya shigo qila ma ya ganan mata jiki nn taji wani  irin haushinsa ya kamata meye ruwansa da ita da har zai zo ya samu tana bacci ya yaye mata blanket har yakai  ga sa mata buttons, ta buga tsaki tare da mamakin wane irin ma bacci ne tayi da har hkn ta faru bata jiba ita da sam bata da nauyin bacci .
  Rae 6ace ta d'auko towel ta cire jacket d'in ta jefar kan sofa snn ta nufi bathroom ta watsa ruwa sbd ta samu jikinta ya sake mata kan baccin da tayi.

  Koda ta gama shiri duk yunwa ta cika ta sae a lokacin ta tuna ko break fast ma batayi ba a nn ta kula da plate d'inta na break fast ,ta d'auki plate d'in ta fita ta kar6o wani abinci gun kuku.

Sama sama ta samu taci abincin sbd tana jin jikin nata ba dad'i shiyasa ko cinye abincin ma ta kasa yi taje takai ragowar ta dawo har zata kwanta taji kiraye kirayen sllr zhr sae a lokacin ta kalli agogo taga biyu saura dama tayi arwala da taje wanka kuskure bakinta kawae taje tayi tazo tayi sallah.
  Tana idar da addu'a ta jawo pillow ta kwanta nn kan sallaya wacce sae son take ta tashi ta d'an dudduba littafanta amma tana jin kmr jikin bazai barta ba.

Haka ta yini bata jin dad'i sae da tasha magani ne ta samu jin sauqi.

Wacce har washe gari bata sake jin komai ba.
  Sae dai koda suka dawo school gabad'aya zazza6in ya dawo mata don ko uniform bata iya cirewa ba ta kwanta sae bacci.
  Mami kuwa ta cire uniform taje ta watsa ruwa ta saka er doguwar rgrta ta kanti da iyakarta guiwa taje d'akin yayanta ya bata abinci taci byn ta gama ya sama ta kallo nn malika taxo ta same su tace"my man wnn abar fa banga ta fito ba bare zancen d'aura min girki kuma kaga dae ba yanzun ne dawowar su ba zamanta ne kawae tayi "Yace"jeki zanje na taso ta "
 Nifa i cnt wait any more don yunwa nakeji sosai kuma kar ma mai lesson d'insu yazo ta wani ce zata zauna ma lesson ,hannun ta yaja suka fito yana mai fad'in "ai mae lesson d'in nasu bazai sami zuwa ba yau yayi tafiya"
   Ta6e baki tayi tace"hm lesson d'in ma nsn ba komai take ganewa ba don da gani kwañyar kifi ce da ita....wyr tace tayi qara tana ganin qawar ta faiza ce mae kiran ta nufi d'akinta shi kuma man ya wuce zuwa d'akin Rynt.
  Tsaki yayi ganin ko uniform bata cire ba amma tayi kwance  tana bacci yace"lallai yrynr nn kinji dad'inki"
  Nn yaje yana tashinta da doka mata jiki ta tashi cikin mugun 6acin rae tana kallon shi tace"wae meye!?
  Yace"tambayata ma kike oya tashi  kije ki d'aurawa malika girki"
 Tace"cab ni wlh bazan iya ba don bana jin dad'i"
  Yace"bana son raini maza tashi kije ki d'aura mata girki ko kuma wlh nayi maganin ki"
  Cikin marairaicewa tace"wlh bana jin dad'i ko tsayuwa ma fa da qyar nake yi"
 Yace"Bari kiji ko a kwance ne sae kin d'aura mata girkin stupid girl!
  Cikin muryar kuka tace"wae kai meyasa baka da tausayi ne,na gaya maka bazan iya ba bana jin dad'i wlh.
  Zowa yayi gab da ita yakai  hannu ya d'ago fuskarta da kyau yana kallon ta yace"shin kin manta abinda na gaya miki ne na dole kibi abinda nace idan ba haka ba karatunki"
  Da mugun tsana take kallon shi tace a ranta
_"mugu kayi abinka lokacinka ne nawa na nn zowa da zan rabaka da farin cikin ka gabad'aya don wlh bazan barka ba"_

  Daga hk tafita ta bar shi tana saukowa downstairs ta had'u da malika wacce ta sha gabanta tana gaya mata maganganun banza.
Tsaki kawai Rynt tayi ta ra6a ta gefenta ta wuce.
 Cike da azama malika tayi niyyar fizgo Rynt sae kawae ta hango man tafe nn tayi saurin sakin glass cup d'inda ke hannunta ya fad'i qasa ya tarwatse ta duqa kmr zata tsince glasses d'in dae dae man ya iso ya tada ta tsaye yana fad'in"ya akayi cup d'in ya fashe kuma har kk qoqarin saka hannun ki,da mamaki
 tace"hm wnn abar ce fa hk kawae ta biyo tamin muguwar bangaza ta wuce har ma tana fad'in wae zan gani"
 Yace"what!
Tace"hm wlh"
A fusace ya kama hanya zai tafi kitchen tayi saurin shan gabanshi tace"no my man kayi hqr ka barta kawae ni yanxu bana son wani  tashin hnkli"
  Yace"da zanso naji me take nufi da zaki gani"
  common my man wnn abar me ta isa tamin ne shirme ne kawae take fad'i kaima ka sani,yi hqr kaji barta.
  Tsaki yayi yace "ya zama dole nayi maganin yrnyr nn sbd rainin nata ya fara isata"
   Tace"da Allah shareta ta zo muje"

Nan taja shi suka je suka zauna kan two seater malika ta kira cleaners aka kwashe glasses d'in,snn ta kalli man tare da jawo hannunsa ta d'aura kan cikinta tace"my man wae nikam yaushe babyn mu zai fara motsi duk na qagu wlh"
  Wani  murmushi yayi mae nuna jin dad'i har ransa yace"3 to 4 month ne yake farawa"
  Ta kalle shi zata ce wani  abu knn wyrta tayi qara tana ganin qawar ta faiza ce tace da mohd "ina zuwa umma ce mae kiran"
 Bata jira me zai ce ba ta tafi.
  Tana shiga d'aki ta d'aga wyr .
faiza"tace ya ake ciki ne kinsha maganin?
 Tace "Aa ynz nake shirin sha dae sbd so nake dai dai wnn abar ta gama min abinci maganin ya fara min aiki sbd zan fi son ina saka loma d'aya ta biyu sae kawae na fasa ihu kan aje asibiti na tabbatar cikin ya gama lallacewa,amma kuma wlh ina tsoron azabar da zanji kafin cikin ya zube
  Faiza"ta kwashe da dariya tace"kin fiye tsoro azabar da kwata kwata ta minti nawa ce yayinda ita waccan matsiciyar kin rabata da mijinki har abada"
  Tace"wlh kam yau dolenta ta rabu dashi,bari kedai nayi sauri nasha maganin kar taje ta gama abincin bansha ba,tace"ok bye sae mun had'u asibiti knn.
   Nan suka katse wyr malika ta ciro tablet a jakarta tasha snn ta fito ta sami man zaune inda ta barshi sae waya yake.
  Taje ta zauna kusa dashi tare da jinginwa a jikinsa wanda bae wani jima sosai ba ya gama wayar.

 Rynt kuwa da qyar taga ta kammala dafa indomie sbd wani irin bacci da takeji.
 Tana gamawa ta zuba indomie a plate ta fito wacce tun lokacinda ta fito kitchen man ke mata mugun kallo har ta qaraso gurin su,shi ya kar6i plate d'in indomie da taikaci yayinda Rynt bata damu da ganin yanda ya kar6i plate d'in ba tayi ficewarta ita dae ta samu ta ganta kan bed.


 Rynt na wucewa malika takai hannu zata kar6i plate d'in don har ta fara jin maganin ya fara mata aiki.
 Man yace"da zafi malika bari ta d'an sha iska tukun"
 Tace"my man yunwa fa nakeji sosai"
   Yace"Baza kici da zafi haka ba kam"
nn gabanta ya shiga fad'uwa don in har  yace sae abincin ya rage zafi asirinta zai iya tonuwa don gadan gadan ta fara jin maganin na mata aiki.
  Nan ta shagwa6e mae tace"pls my man kawae barni naci don zan ma fi jin dad'inta"
  Ba musu kuwa ya bata plate d'in ta kar6a ta fara ci tayi loma d'aya biyu a ta ukun ta ajiye plate ta fara riqe ciki man yayi saurin kallonta ya kuma kalli plate d'in indomie yace"lafiya?
 Tace"nima dae haka kawae ina fara cin indomie na fara jin  cikina yana 6ird'a min"
 Yace"what!me tasa miki a indomien ne to?
 Bata iya bashi amsa ba sae  zamewa tayi daga kan seater tana yarfi da hannu yayinda ta matse cikinta sosai da d'ayan hannunta.
 A take man ya rud'e ya jawota jikinsa ita kuwa sae ihu ta fara tana fad'in"wayyo my man cikina zan mutu na shiga uku ka taimaka min da magani nasha"
  Da sauri man ya tashi yaje d'akinshi yana shiga ya sami mami kwance kan sofa tayi bacci tana qoqarin fad'owa da saurin sa ya d'auketa ya maida kan bed snn ya d'auko magani da ruwa ya fito yana isowa ya saki magani har cup d'in ruwa sbd ganin yanda malika ta fara bleeding ba wata wata ya d'auke ta ya fita da ita yana qwalawa driver kira,driver yazo suka shiga mota aguje sae asibiti.

Duk wani qoqari na ganin jinin ya daina zuba man yayi amma bai yi nasarar ceto cikin ba ya riga da ya zube,baqin ciki bai bar ya qarasa kula da malika ba sae wata docta yasa ,ya baro asibitin yayo gida a fusace wanda bai zarce koina ba sae d'akin Rynt riqe da belt a hannun shi.
Rynt dake bacci sae  saukar duka ta fara ji ta koina.


  Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2/6, 4:41 PM] ‪+234 703 962 5239‬: [ 2/5/2017]
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```










           🔮🔮🔮🔮
*page* *```45```*
Man kuwa yana fita d'akinsa ya tafi ya sami malika zaune kan sofa tana shan 'ya'yan fruits yaje kusa da ita ya zauna ta kaimai slice d'in kankana a baki tare da fad'in"ya baka fita ba ko kun fasa ne? Eh an d'aga meeting d'in sae zuwa 12,tace"OK" daga hk suka ci gaba da shan fruits suna er firar su a cikin firar ne man ya d'auko laptop d'inshi yana nuna mata wasu kayan jarirai da ya gani masu kyau yace"duk a England ake samun su,tace "wow yaushe zamu je siyo kyn? Yace"na fison sae cikinki ya farà qwari muje har sae idan kin haifu snn ko zamu dawo amma zan riqa yi ina dawowa sbd aiki na,kiss ta d'aura mai tace"wnn ba matsala bane"
 Yayi d'an guntun murmushi yana ci gaba da nuna mata wasu kyn jarirai.

Rynt kuwa ta jima kwance  abinta tana baccinda ya mata dad'i fiye da kowanne.

11:30
Man ya shigo d'akin still sae bacci take,dube dube ya shiga yi ta inda zai ga suit jacket d'insa wanda har bathroom ya duba amma bae ganta ba.
  Hkn yasa yazo ya durqusa gab da ita yakai  hannu ya d'an yaye mata blanket  kad'an, nn yaga jacket d'in na jikinta hannuwanta na jikin qirjinta da ta kama magamar jacket d'in ta riqe gam.
   Ganin hkne yasa ya janye hannuwanta a hnkli ya rufe mata buttons wanda garin hkne ya hango d'an bum short d'inda ke jikinta kauda idonsa kawae yayi ya rufa mata blanket ya fita .

Ba ita ta tashi ba sae qarfe d'aya.
Ta tashi zaune tana mai kama mgmr jacket d'in,ga mamakinta taga an sanya mata buttons d'in rgr,ai kuwa taji  fad'uwar gaba don tasan mohd ne ya shigo qila ma ya ganan mata jiki nn taji wani  irin haushinsa ya kamata meye ruwansa da ita da har zai zo ya samu tana bacci ya yaye mata blanket har yakai  ga sa mata buttons, ta buga tsaki tare da mamakin wane irin ma bacci ne tayi da har hkn ta faru bata jiba ita da sam bata da nauyin bacci .
  Rae 6ace ta d'auko towel ta cire jacket d'in ta jefar kan sofa snn ta nufi bathroom ta watsa ruwa sbd ta samu jikinta ya sake mata kan baccin da tayi.

  Koda ta gama shiri duk yunwa ta cika ta sae a lokacin ta tuna ko break fast ma batayi ba a nn ta kula da plate d'inta na break fast ,ta d'auki plate d'in ta fita ta kar6o wani abinci gun kuku.

Sama sama ta samu taci abincin sbd tana jin jikin nata ba dad'i shiyasa ko cinye abincin ma ta kasa yi taje takai ragowar ta dawo har zata kwanta taji kiraye kirayen sllr zhr sae a lokacin ta kalli agogo taga biyu saura dama tayi arwala da taje wanka kuskure bakinta kawae taje tayi tazo tayi sallah.
  Tana idar da addu'a ta jawo pillow ta kwanta nn kan sallaya wacce sae son take ta tashi ta d'an dudduba littafanta amma tana jin kmr jikin bazai barta ba.

Haka ta yini bata jin dad'i sae da tasha magani ne ta samu jin sauqi.

Wacce har washe gari bata sake jin komai ba.
  Sae dai koda suka dawo school gabad'aya zazza6in ya dawo mata don ko uniform bata iya cirewa ba ta kwanta sae bacci.
  Mami kuwa ta cire uniform taje ta watsa ruwa ta saka er doguwar rgrta ta kanti da iyakarta guiwa taje d'akin yayanta ya bata abinci taci byn ta gama ya sama ta kallo nn malika taxo ta same su tace"my man wnn abar fa banga ta fito ba bare zancen d'aura min girki kuma kaga dae ba yanzun ne dawowar su ba zamanta ne kawae tayi "Yace"jeki zanje na taso ta "
 Nifa i cnt wait any more don yunwa nakeji sosai kuma kar ma mai lesson d'insu yazo ta wani ce zata zauna ma lesson ,hannun ta yaja suka fito yana mai fad'in "ai mae lesson d'in nasu bazai sami zuwa ba yau yayi tafiya"
   Ta6e baki tayi tace"hm lesson d'in ma nsn ba komai take ganewa ba don da gani kwañyar kifi ce da ita....wyr tace tayi qara tana ganin qawar ta faiza ce mae kiran ta nufi d'akinta shi kuma man ya wuce zuwa d'akin Rynt.
  Tsaki yayi ganin ko uniform bata cire ba amma tayi kwance  tana bacci yace"lallai yrynr nn kinji dad'inki"
  Nn yaje yana tashinta da doka mata jiki ta tashi cikin mugun 6acin rae tana kallon shi tace"wae meye!?
  Yace"tambayata ma kike oya tashi  kije ki d'aurawa malika girki"
 Tace"cab ni wlh bazan iya ba don bana jin dad'i"
  Yace"bana son raini maza tashi kije ki d'aura mata girki ko kuma wlh nayi maganin ki"
  Cikin marairaicewa tace"wlh bana jin dad'i ko tsayuwa ma fa da qyar nake yi"
 Yace"Bari kiji ko a kwance ne sae kin d'aura mata girkin stupid girl!
  Cikin muryar kuka tace"wae kai meyasa baka da tausayi ne,na gaya maka bazan iya ba bana jin dad'i wlh.
  Zowa yayi gab da ita yakai  hannu ya d'ago fuskarta da kyau yana kallon ta yace"shin kin manta abinda na gaya miki ne na dole kibi abinda nace idan ba haka ba karatunki"
  Da mugun tsana take kallon shi tace a ranta
_"mugu kayi abinka lokacinka ne nawa na nn zowa da zan rabaka da farin cikin ka gabad'aya don wlh bazan barka ba"_

  Daga hk tafita ta bar shi tana saukowa downstairs ta had'u da malika wacce ta sha gabanta tana gaya mata maganganun banza.
Tsaki kawai Rynt tayi ta ra6a ta gefenta ta wuce.
 Cike da azama malika tayi niyyar fizgo Rynt sae kawae ta hango man tafe nn tayi saurin sakin glass cup d'inda ke hannunta ya fad'i qasa ya tarwatse ta duqa kmr zata tsince glasses d'in dae dae man ya iso ya tada ta tsaye yana fad'in"ya akayi cup d'in ya fashe kuma har kk qoqarin saka hannun ki,da mamaki
 tace"hm wnn abar ce fa hk kawae ta biyo tamin muguwar bangaza ta wuce har ma tana fad'in wae zan gani"
 Yace"what!
Tace"hm wlh"
A fusace ya kama hanya zai tafi kitchen tayi saurin shan gabanshi tace"no my man kayi hqr ka barta kawae ni yanxu bana son wani  tashin hnkli"
  Yace"da zanso naji me take nufi da zaki gani"
  common my man wnn abar me ta isa tamin ne shirme ne kawae take fad'i kaima ka sani,yi hqr kaji barta.
  Tsaki yayi yace "ya zama dole nayi maganin yrnyr nn sbd rainin nata ya fara isata"
   Tace"da Allah shareta ta zo muje"

Nan taja shi suka je suka zauna kan two seater malika ta kira cleaners aka kwashe glasses d'in,snn ta kalli man tare da jawo hannunsa ta d'aura kan cikinta tace"my man wae nikam yaushe babyn mu zai fara motsi duk na qagu wlh"
  Wani  murmushi yayi mae nuna jin dad'i har ransa yace"3 to 4 month ne yake farawa"
  Ta kalle shi zata ce wani  abu knn wyrta tayi qara tana ganin qawar ta faiza ce tace da mohd "ina zuwa umma ce mae kiran"
 Bata jira me zai ce ba ta tafi.
  Tana shiga d'aki ta d'aga wyr .
faiza"tace ya ake ciki ne kinsha maganin?
 Tace "Aa ynz nake shirin sha dae sbd so nake dai dai wnn abar ta gama min abinci maganin ya fara min aiki sbd zan fi son ina saka loma d'aya ta biyu sae kawae na fasa ihu kan aje asibiti na tabbatar cikin ya gama lallacewa,amma kuma wlh ina tsoron azabar da zanji kafin cikin ya zube
  Faiza"ta kwashe da dariya tace"kin fiye tsoro azabar da kwata kwata ta minti nawa ce yayinda ita waccan matsiciyar kin rabata da mijinki har abada"
  Tace"wlh kam yau dolenta ta rabu dashi,bari kedai nayi sauri nasha maganin kar taje ta gama abincin bansha ba,tace"ok bye sae mun had'u asibiti knn.
   Nan suka katse wyr malika ta ciro tablet a jakarta tasha snn ta fito ta sami man zaune inda ta barshi sae waya yake.
  Taje ta zauna kusa dashi tare da jinginwa a jikinsa wanda bae wani jima sosai ba ya gama wayar.

 Rynt kuwa da qyar taga ta kammala dafa indomie sbd wani irin bacci da takeji.
 Tana gamawa ta zuba indomie a plate ta fito wacce tun lokacinda ta fito kitchen man ke mata mugun kallo har ta qaraso gurin su,shi ya kar6i plate d'in indomie da taikaci yayinda Rynt bata damu da ganin yanda ya kar6i plate d'in ba tayi ficewarta ita dae ta samu ta ganta kan bed.


 Rynt na wucewa malika takai hannu zata kar6i plate d'in don har ta fara jin maganin ya fara mata aiki.
 Man yace"da zafi malika bari ta d'an sha iska tukun"
 Tace"my man yunwa fa nakeji sosai"
   Yace"Baza kici da zafi haka ba kam"
nn gabanta ya shiga fad'uwa don in har  yace sae abincin ya rage zafi asirinta zai iya tonuwa don gadan gadan ta fara jin maganin na mata aiki.
  Nan ta shagwa6e mae tace"pls my man kawae barni naci don zan ma fi jin dad'inta"
  Ba musu kuwa ya bata plate d'in ta kar6a ta fara ci tayi loma d'aya biyu a ta ukun ta ajiye plate ta fara riqe ciki man yayi saurin kallonta ya kuma kalli plate d'in indomie yace"lafiya?
 Tace"nima dae haka kawae ina fara cin indomie na fara jin  cikina yana 6ird'a min"
 Yace"what!me tasa miki a indomien ne to?
 Bata iya bashi amsa ba sae  zamewa tayi daga kan seater tana yarfi da hannu yayinda ta matse cikinta sosai da d'ayan hannunta.
 A take man ya rud'e ya jawota jikinsa ita kuwa sae ihu ta fara tana fad'in"wayyo my man cikina zan mutu na shiga uku ka taimaka min da magani nasha"
  Da sauri man ya tashi yaje d'akinshi yana shiga ya sami mami kwance kan sofa tayi bacci tana qoqarin fad'owa da saurin sa ya d'auketa ya maida kan bed snn ya d'auko magani da ruwa ya fito yana isowa ya saki magani har cup d'in ruwa sbd ganin yanda malika ta fara bleeding ba wata wata ya d'auke ta ya fita da ita yana qwalawa driver kira,driver yazo suka shiga mota aguje sae asibiti.

Duk wani qoqari na ganin jinin ya daina zuba man yayi amma bai yi nasarar ceto cikin ba ya riga da ya zube,baqin ciki bai bar ya qarasa kula da malika ba sae wata docta yasa ,ya baro asibitin yayo gida a fusace wanda bai zarce koina ba sae d'akin Rynt riqe da belt a hannun shi.
Rynt dake bacci sae  saukar duka ta fara ji ta koina.


  Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2/7, 7:16 PM] ‪+234 703 962 5239‬: [ 2/7/2017]
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```










           🔮🔮🔮🔮
*page* *```46```*
Cikin firgici ta tashi tana ihu tana neman guduwa man kuwa sae binta yake yana ci gaba da kai mata duka ta koina baji ba gani.
 Can ta samu ta  fito d'akin aguje shima ya biyo ta yana duka harsuka sauko downstairs nn sukayi kici6is da umman saliha ta shigo ita da nasir,cikin kuka Rynt ta fizge daga hannun man zata je gun umman saliha kafin ta qarasa jiri ya d'ebe
ta tafi suu zata fad'i umman saliha tayi hanzarin tarbota ta fad'a jikinta,yayinda nasir ke kallon man da mugun mamaki.
  Man kuwa qala bae ce dasu ba sae ma murtuqe fuskar sa da yayi ya fita yaja motar sa ya bar gidan.
   Umman saliha da ita ma duk mamaki ya cikata ta kalli nasir da yabi man da kallo tace"kama min ita mukai kan seater"
  Nan nasir ya kamata suka kaita kan 3 seater snn ya d'auko ruwa a fridge ya yayyafa mata,bata iya bud'e idonta ba sae ajiyar zuciya kawai ta ftr.
  Umman saliha ta kira sunanta kusan sau biyu amma Rynt bata amsa ba, nn umma ta kalli Nasir tace"ai da mun kaita d'akinta sae a kira Dr"
  Nasir yace"Aa umma kawae muje asibiti tukun daga can sae mu kaita gidan inna sbd nsn fa'iz mai iya zuwa ne yana ci gaba da dubata"
  Fa'iz ( cewa da wani abokin sa likita).

 Umman nasir tace"meyasa zamu kaita gidan inn ai sae hnklinta ya tashi kawai mu maida ta nn gdn in yaso kullum na riqa zowa ina dubata.
  Nasir yayi saurin yace"Aa umma baza mu maida ta gidan nn ba dmn wnn rashin tausayi da cin zali yayi yawa gsky bazan iya barin Rynt a cikin halin nan ba ai ko me ta masa bai kamata ace ya dake ta ba kodan kasancewar ta qaramar yarinya snn umma idan har kinzo da rana wa zai riqa kula da ita da dare har zuwa wayewar gari  don wnn uban dukan rashin imani da ya mata ya kamata ace koyaushe  tana da mae kula da ita shiyasa naga gsky  ba inda ya dace aje da ita face gidan inna don shi dae na tabbatar bazai kula da ita ba.
   Umman saliha ta sauke ajiyar zuciya tace"shikenan nasir kamata muje mu saka ta a mota"
 Bayan sun saka ta a mota ne suka bar gidan suka nufi asibiti.
  Tafe suke kan hnya umman
Saliha dake seat d'in baya rungume da Rynt sae kallon Rynt take cike da tausayi wacce in banda numfashi ba abinda take iya yi.
Umman saliha ta nisa snn tace da nasir"ni ina mamakin wane irin abune Rynt tayiwa mohd da har ya iya mata wnn dukan"
 Nasir yace"ni nasan ba abinda Rynt ta masa da yakai ga duka kawae dae rashin imanin sa ne ya motsa,kuma umma  dama fa Rynt zaman haquri kawae takeyi a gidan shiyasa nake son inna tasani ko hkn zai sa man ya daina quntata mata sbd idan inna taji tamkar Abbansa yaji ne , Abba kuwa kai tsaye zai gyara masa zamansa ne don bazai ta6a barin sa ya ci gaba da cutar da Rynt ba.
   Umma tace"lallai kam ba makawa zai gyara masa xamansa"

Daga haka basu sake cewa komai ba sae Nasir da ya ciro wyrsa a aljihu ya kira abokinsa yana gama waya dashi se  juya alkalar motar sa yayi zuwa canza hanya ummar shi ta tambaye shi lafiya
 yace"Fa'iz ne yace mu had'u can gidan inna sbd ya rigada ya baro asibiti.
 Tace" haka yafi sauqi amma hlnda inna zata ga Rynt nake tunani"
  Nasir bae ce komai ba don shima nazarin da yake yi kenan don yaso ace koda zata ga Rynt an ciyo kan matsalar sae dae kawae taji lbrn abinda ya faru.

Suna isa shima abokin nashi na isowa.

 Dukkan su suka shiga gidan har shi fa'iz d'in wanda ga dukkan alama ya saba shiga gidan dan shine gaba sai sauri yake ya bud'ewa nasir qyallen qofa.
 Nasir dake d'auke da Rynt ya ajiye ta kan 3 seater abokin nasa ya shiga dubata sbd sunyi sallama har sun gaji ba amsa.

  Bayan abokin yayi en gwaje gwajen sa akan Rynt  ya nemi akaita kan bed sbd yana son zai mata qarin ruwa .
  D'akin inna aka kaita snn aka d'aura mata ruwan sae a snn ne inna ta shigo gidan wacce ga dukkan alama maqota ta fito dan riqe take da qullin nono da fura a hannu,ai kuwa tana shiga d'akinta ta saki furar da nono tana taslima inda a rud'e ta shiga tambayar abinda ke faruwa da Rynt.
  Sae da nasir ya kwantar mata da hnkli snn ya snr da ita abinda ya faru.

Kukan su na tsafi ta shiga yi tana sirfawa mohd zagi ciki da waje snn ta d'auko waya a cewar zata kira Abban mohd yazo yaga d'ayen aikin da yayi wa Rynt.....bata kae ga kiran sa ba taji abokin nasir na cewa da nasir
 "Haqiqa anyi babbar nasara dan duk irin dukan nn da tasha  juna biyun da ke jikinta yana nn lfyrsa qalau"
Da kmr mamaki Nasir yace"juna biyu ne da ita? Yace"tabbas kuwa tana d'auke da juna biyu don hk sae a kiyaye a riqa bata kulawar da ta dace"
  "InshaAllah"
Shine abinda nasir yace kafin abokin sa ke rubuta masa magunguna ya bashi.
  Nn Nasir ya maida dubansa gun ummar sa da inna wad'anda kallo d'aya zakayi musu kasan sunyi farin ciki matuqa da jin zancen Dr musamman inna da kukanta ya koma dariya.
 Yace musu"zanje siyo magani na dawo"
  Inna tace"to d'an albarka sae ka dawo ,kai kuma Hafizu Allah sa ka gama da iyayenka lafiya don wnn lbr da na ji a bakinka ya kore min duk wani  baqin ciki.
  Da shi har nasir sae da sukayi murmushi suka fita sbd fa'iz yasha fhmtar da ita sunan shi amma sae tayi ta kiran shi da hafizu tun yana gyara mata har ya daina sae dae kawai yayi murmushi idan ta kirashi da Hafizu.
 Suna fita inna taje kusa da Rynt dake ta sharar bacci tace "um! um! baiwar Allah, Allah iskar miki ga shashan yaron nn muhammadu ai zai zo ya sameni ne zai kuma had'u da ubansa kabiru dan sae na snr dashi komai kaf ba abinda zan rage shashan yaro kawai marar tausayi da baisan daraja mace ba.
Nn ta d'auki  fura da nonon da tayar a kan fridge wad'anda umman saliha ce ta d'auke ta d'aura akai.
  Ta d'auki furar tana mae fad'in"bari naje na dama ma er albarkar nn Rynh ita kafin ta tashi tayi sanyi sae tasha"
 Tana gama fad'ar hk ta kama hnyr fita d'akin umman saliha ta tashi da sauri tana qoqarin cewa da inna ta kawo furar ta dama sae ga man ya shigo d'akin shaye da toka riqe da mami a hannun shi wacce taje da gudu kan jikin mamarta.
  Mohd kuwa yana had'a idô da inna ya wani qara d'aure fuska  dan karma inna taga damar shi .
  Amma hkn bai hana inna ta shiga sirfa mae masifa tana"fad'in shashan yaro me kuma ya kawoka ko kazo ka qarasata ne iye!
 Komai mohd bai ce da ita ba sae zuwa yayi kan gadon da Rynt ke kwance  ya ajiye wata farar takarda ya fita .


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2/8/2017]
Billy giro😊:
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```










           🔮🔮🔮🔮
*page* *```47```*
 Inna tace yau naga shahan yaro me kuma ka ajiye mata kan gadon da har ina ma magana zaka wani  wuce ni.
Nn  umman saliha ta tashi taje ta d'auki takardar ta karanta wacce tana gama krntawà ta saki takardar ta zauna sakwaf kan gado tana taslima had'e da fad'in innalillahi wa inna ilaihi raji'un!
 A rud'e inna ta d'auki takardar tace"lafiya me ya rubuta mata a takardar ne?
  Umman saliha tace"saki ne inna!
  Da qarfi inna ta dafe qirjinta tare da fiddo ido waje tace"saki!
  Sae kawai ta fashe da kuka tana"fad'in innalillahi wa inna ilahi raji'una anya kuwa muhammadu yana son ya gama lfy, me wnn er albarkar ta masa da zai had'a mata zafi biyu a lokaci d'aya nn ta koma fashewa da wani kuka inda cikin kukan ne ta kira Abban mohd ta snr dashi komai.

Kafin yazo sae ga nasir ya dawo da siyen magani ya qaraso jiki sanyaye ganin yanda inna keta fmn shar6ar kuka har da su fyace majina, a hnkli ya ajiye ledar maganin hannunsa kan bed yaje ga inna yana tmbyr me kuma ya faru?
   Takardar hannunta ta miqa mae tace"gane ma idonka abinda d'an banzan yaron nn ya rubutawa Rynh ,yana kar6ar takardar ya hango saki 6aro 6aro nn ya cire hular kanshi tare da kallon Rynt dake  kwance still tana bacci yace"ya saketa!
  Daga nn shima ya zauna  gefen gadon dafe da kai yana tunanin me Rynh ta ma mohd ne wae.
  Yana cikin hkne yaji sallamar Abban mohd.

A hnkli ya d'go tare da zamewa kan gadon ya durqusa yana gaida shi ya amsa ba yabo ba fallasa yayinda ita ma umman saliha ta gaida shi ya amsa snn suka fito d'akin suka barshi shida inna.

Cikin damuwa Abban mohd yaje gun Rynt  yana mae kallon yanayinda take ciki can ya nisa yace da inna"shi mohd d'in bai ce ga abinda ya had'a su bane?
  Inna tace"meko yace sae shigowa kawai da yayi yaje ya ajiye mata takarda ya fita wanda har ma magana nake  masa amma yaqi ko kulani.
  Abba ya jinjina kansa snn yakai hannu ya ciro wyrsa a aljihu ya kira mohd
Yana d'agawa yace"duk abinda kake ka ajiye shi kazo ka sameni a gidan inna.
  Daga hk Abba ya katse wyr.
 Mohd dake zaune a asibiti gurin malika wacce tasa shi gaba tana ta kuka wae ita kukan baqin cikin zubewar cikinta take yayinda shi kuma duk ya wani sukui kuice yana fmn lallashinta.
  Shine ya samu da qyar ya lalla6ata tabar shi ya fita.
 Fa'iza wacce daman tana cikin d'akin.
  Tana ganin mohd ya fita taje ta ba malika hannu suka lale ,malika tace"Abbansa ne ya kira shi nsn kan sakin nn ne da yayiwa wnn abar "
 Faiza tace"hln bai ji dalilin sakin bane?
  Ta6e baki malika tayi snn tace"oho masa nidai tunda buqata ta riga ta biya komai yayi"
  Faiza tace"wae dae tukuna saki nawa ne ya rubuta mata"
 Malika tace"har kya tambaya ai kinsan uku ne ba tantama,shiyasa kika ji nace buqata ta ta gama biya don ba zancen ace ya maida ta kuma sun rabu knn har abada yayinda ni kuma zan zame masa mutu ka raba takalmin kaza.
  Nan suka koma lalewa suna kyakkewa.

6angaren mohd kuwa da isar shi gidan inna kai tsaye ya tafi sae d'akinta ya samu guri a qasa ya zauna yayinda inna ke zaune kan bed Abbansa kuwa yana kan sofa.
  Abba ya kalle sa da kyau snn yace"Ashe baka da hnkli ban sani ba mene ne ya had'aka da Rynt da har ka iya dukanta ka kuma had'a ta da takardar saki?
 Shiru mohd yayi .
  A fusace Abba yace"shin bada kai nake magana bane!
  Kallon mahaifin nasa yayi ya koma duqar da kanshi qasa snn yace"Abba da ka bari idan ta farka sae kaji a bakinta"
 Abba yace"don uwarka ni sa'an ka ne da zan tambaye ka kace min na bari har Rynt ta farka ,kai dai zaka gaya min d'an iskan yaro kawai shashasha wanda baisan darajar mace ba,wae karasa inda zakayi zalunci sae akan mace.
  Ran mohd ne ya soma 6aci da jin irin zagin da Abba ke mae ya daure yace"Abba ka daina ganin laifina akan abinda baka ji ba,  yrnyr nn fa kwata kwata bata da gsky haka kuma hkncin da na d'auka akanta shine dai dai "
  Abba yace" wane laifi ne  Rynt zata maka da zata ci wnn banzan hukuncin naka na masara imani da rashin tausayi"

 Mohd Yace"Abba cikina  ta 6arar min dake jikin malika ta hnyar sanya mata magani a abinci"
  Cikin d'aga murya Abba yace" sam! wnn qarya ne kwata kwata Rynt bazata aikata hk ba idan har zarginta kake to kayi gaggawa cirewa"
 Abba ba zarginta nakeyi ba ta aikata ne don a gaban idona komai ya faru.....Qarya kake munafukin Allah Rynt bazata ta6a  aikata hk ba kawae dama can ba son auren nata kake ba shine ka 6ullo da wnn hnyr na ganin ka yakice aurenta dake smn kanka to kasani wlh daga yau kar na koma ganin qafar ka a gidana tunda ni ban isa da kaiba koma nace baka d'auke ni a uba ba,don hk sae ka nemi wani  uban bani ba!
  Cikin fad'a ita kuma inna ta kama da cewa"marar kunyan yaro da baka santa meyasa to ka mata ciki!
Da sauri mohd ya d'ago ya kalli inna yace"ciki"
  Inna tace"eh ko kuma cewa zakayi bakai kayi cikin bane iye!
  Sadda kansa kawae yayi qasa ba tare da yace komai ba.
Abban sa ya daka mae tsawa yace"ka bata amsa mana bada kai take magana bane!
   Yace"nawane"
Shi ne kad'ai abinda yace
Yayinda Abba yace"oya maza tashi ka bamu guri shasha!
 kuma wlh kasani har nn gidan d'in ma ban yarda ka sake tako qafar ka ba kaji na gaya ma!
 Daga hk Abba ya fita fuu yana mae gyara babbar rgr shi wanda yana kai falo yace da nasir"ina son gobe da safe kaje gidan nashi ka kwaso kaf kyn Rynt kazo dasu nn gidan"
  Da ladabi nasir yace"to"
Snn Abba ya fita haka shima man ya fita yabar gidan cike da tunanin cikin da ke jikin Rynt.

9:00pm
 Rynt ce ta shiga motsi a hnkli inna dake gefenta tayi hanzarin matsawa kusa da ita tace"Rynh kin tashi?
 Komai Rynt bata ce ba sae yunqurin tashi zaune take nn inna ta taimaka mata ta tashi zaune.
  Snn inna taje da hnzri ta bud'e fridge ta d'auko damammar fura a cikin kwanan shan ruwa wacce umman saliha ce ta dama ta kafin ta tafi.
  Ta di'bar wa Rynt a kofi taje ta kai mata ,Rynt takai hannu ta kar6i kofin furar tana mae kallon inna'
Inna tace"Sha kinji Rynh"
ba musu takai kofin fura a bakinta tasha kad'an tace"inna bana son furar idan da kunu zan sha amma nafi son mai d'an tsami da sanyi"
    Inna tace"Rynh za'a sami kunu mai sanyi amma baya da tsami sbd d'azu da rana Baaba hurare ta daman min shi sae dai idan kina so na sa maki ruwan tsamiyà a ciki"
 Tace"Eh inna ina so"
Nn inna ta kar6i kofin furar ta saka shi a fridge snn ta fita zuwa kitchen ba jimawa sae gata ta dawo d'auke da kofin kunu ta ba Rynt wacce ta kar6a ta shiga sha"
  Inna kuwa ta d'auko magunguna tana 6alla mata kmr yanda nasir ya gaya mata kafin ya tafi.
 Tana gama 6allewa ta ba Rynt ta kar6a tasha snn ta tashi ta nufi bathroom tayo arwala tazo tayi sllr dake kanta .

Washe gari  Nasir ne ya shigo gidan shida abokin sa fa'iz .
 Da shigar su suka had'u  da inna ta fito kitchen d'auke da ruwan zafi a cup zata had'awa Rynt shayi,sun gaidata had'e da tmbyrta mai jiki.
 Tace "Alhmdlh mu shiga tana daga ciki"
   Nn suka shiga suka sami Rynt kan gado ta had'e kai da guiwa.
 Sallamar su yasa ta d'ago ta d'an saki fuska ta musu ina kwana suka amsa tare da fad'in ya jikin naki?
 Tace"Alhmdlh"
  Faiz yace"da akwai abinda ke maki ciwo ko kuwa"
  Tace"Aa ba inda ke min ciwo kawai...sae tayi shiru.
 Yace"zafin duka ko?
  Kai ta gyad'a mishi tare da qoqarin mayarda hawayen da ke son zubo mata"
  Fa'iz yace"kici gaba da shan magunguna kafin gobe inshaAllah zaki ji jikin ki dai dai kinji"
  Tace"to"
Snn nasir yace"jiya kinsha magunguna?
 Tace"eh inna taban"
 Yace"to yau fa"
Tace"tukuna ban sha ba"
 Inna dake zuba madara a ruwan tea tace"ai yanzu nake shirin d'auko mata magungunan idan ta gama shan shayi sae tasha"
 Nasir yace"To inna mu zamu d'an fita mu dawo"
  Tace"to d'an Albarka sae kun dawo"
   Nan suka fita inna ta bawa Rynt shayin da ta gama had'a mata snn ta d'auko mata magunguna had'e da kofin kunu ta ajiye mata,taje ta bud'e fridge ta d'ibi fura ta zauna zata sha knn sae taji sallamar Abban nasir.
  Washe da baki ta fita ta same shi a falo yayinda shi kuma yana ganin ta ya durqusa har qasa yana gaida mahaifiyar tashi.
  Bayan sun gama gaisawa ya koma kan cushion ya zauna itama inna ta nemi guri ta zauna.
 Yace"inna ya jikin Rynt?
Tace"taji sauqi don yanzu haka ma karyawa take,ko na kira ma ita ku gaisa ne?
 Eh inna don akwai mgnr da ma nake son nayi da ita.
  Nn inna ta qwalawa Rynt kira wacce sae da ta amsa kiran snn taxo falon ta durqusa cike da ladabi ta gaida Abban nasir.
 Byn ya amsa yake cewa"Rynh ina so zan tambaye ki ne,shin meye ainihin abinda ya had'a ki da mohd?
 A sanyaye tace"Abba ni ban san na masa komai ba kawai ina cikin bacci naji yana dukana amma banda shi ba abinda na sani"
  Abban  nasir ya nisa yace"amma kuma mohd yace abu kika sawa mtrsa a abinci taci cikinta ya zube"
 Da sauri Rynt ta kalli Abban nasir cikin muryar kuka tace"wlh Abba ba haka bane ni ba abinda nasa mata a abinci"
   Shiru Abban nasir yayi can yace"shikenan tashi tafiyarki"
  Rynt ta tashi tana mae share qwalla ta koma daga ciki.
 Bayan ta shiga ciki ne taji Abban nasir na cewa da inna"ni na rasa gane kan wnn al'amarin shi mohd da na kirashi na tambayesa har rantsuwa yamin kan cewa a gabon idonsa malika taci abincin da Rynt ta dafa ta kawo mata wacce ko spoon uku bata samu tayi ba cikin ta ya shiga 6ird'a daga hk ne ta soma zuvar da jini ya kwashe ta zuwa asibiti wanda koda suka isa cikin ya riga da ya zube bai iya ceto rayuwar abinda ke cikin ba"
  Inna tace"yo kae ka yarda da zancen nasa knn ni nsn ba wani  ciki da mtrsa keda makirci ne kawae suka qulla shida mtr tashi na ganin sun fitar da Rynh a gidan.
 Abban nasir yace"kodai mtr tasa ce ta qulla makircin don bana tunanin mohd zai biye wa shirmen mata har a had'a irin wnn makirci dashi......yo tunda ba son auren yake ba ai zai biye mata ne.
 Yace"to inna abar wnn zancen ni yanzu abinda nake so shine a sasanta tsakanin su, Rynt ta koma d'akin mijinta tunda saki d'aya ne ya mata.....yo so kake ta koma ya idata knn in yaso na rasa abinda zan cewa mai garinsu da ya damqa min amanar ta, to ba'ayi hk dani ba, fatana Allah ya sauke ta lafiya ya bata wani  mijin mae sonta tsakani da Allah wanda kuma zai riqe ta da gsky,ba irin shashashan yaron nn da ba abinda ya iya sae cutar da ita ba.

 Abban nasir yace"inna ki daina wnn zancen dmn ba abinda yafi dacewa irin a maida Rynt d'akin mijinta ko don qaruwar da suka samu a tsakanin su.
  inna tace"kaga Bello idan wnn zancen kad'ai ya kawo ka gidan nn gwara ka tashi ka tafi don Rynh kam bazata koma gidan wnn marar imanin yaron ba,idan kuwa ka koma zowa ka matsa min da zancen wlh zan d'auki Rynh ne mu koma can qauyen nasu da zama kuma ba wanda yà isa ya sani na dawo.
 Haquri kawae Abban nasir ya bata ya fita ya bar gidan cike da damuwa.

Inna kuwa rae 6ace ta koma d'aki ta sami Rynt sae kuka take kmr ranta zai fita wacce ba komai take yiwa kukan ba sae jin cewa tana d'auke da ciki.
 Inna kuwa ba abinda ya fad'o ranta sae tunanin ko qazafin da mohd ya mata ne take yiwa kuka.
 Nan taje gun Rynt sae dae kafin tace komai Rynt ta kalleta cikin kuka sosai tace"dan Allah inna kisa a cire min cikin nn wlh nayi qanqanta,dmn nasan mutuwa kawae zanyi gurin haifuwa"
 Inna tayi er dariya tace "Rynt bazaki mutu ba zaki haifu lafiya kinji"
 Tace"amma inna karatu na fa?
 Tace"zaki ci gaba da karatun ki a nn kinji"
 Inna to ta yaya zanyi karatu da ciki wlh kinsan da kmr wuya dan Allah kisa a cire min inna "
Inna tayi shiru tana kallon Rynh sae can tace"bazan 6oye miki ba Rynh kinzo dani gaa6ar da bazan iya ba don har gwara ma kice min kina son komawa gidan muhammadu da kice min a cire wnn cikin.
Daga hk inna ta tashi tabar d'akin.
 Rynt kuwa ta qara fashewa da wani  sabon kuka dan ganin take shike nn man ya 6ata mata tsarin rayuwar ta,ya kuma lalata mata duk wani  lissafin  karatun ta.
Lallai idan ba'a cire mata cikin nn ba,ba abinda yafi cancanta a gareta yanzu shine ta d'auki fansar ta kawae ta qara gaba.

Duk a cikin kukanta ne take wnn tunanin .
  Yayinda inna ta dawo d'akin tana ta bata baki amma Rynt bata iya daina kukan ba don ma yini zungur  ta kwashe tana abu d'aya.
 Ai kuwa duk inna tabi ta damu sosai sbd ko abinci Rynt taqi ci wacce ko karin kumallon da ta fara da safe bata qarasa ba.

Cikin hkne nasir ya fad'o gidan inna ta tarbe shi da cewa"yauwa Nasiru dama kai nake shirin kira yanzu.
 Yarinyar nn Rayyanah tun d'azu sae kuka take tayi ita sae an cire cikin da ke jikinta, ko abinci taqi taci tun safe har yanzu.

 Nan nasir ya tambayi inna ko meye dalili ,
Inna ta gaya mae duk yanda sukayi da Rynt.
 Yayi shiru snn yace "bari naje gurin ita Rynt d'in"
 Bai jira me inna zata ce ba ya shiga inner room ya sami Rynt  zaune kan sallaya ta had'e kai da guiwa tana ta kuka.
  A hnkli nasir yaje ya durqusa kusa da ita tare da kiran sunanta

Nn ta d'ago a hnkli tana kallon shi da jajayen idanuwanta da duk suka kumbura yace"kukan ya isa haka indae ciki ne zan sa a cire maki kinji"
 Cikin dasasshiyar muryar ta da tasha kuka tace"nagode"
  Yace"to share hawayenki"
 Ba musu takai hannu ta share hawayenta Yace"kici abinci kuma kisha magani idan na dawo gobe sae naje dake a cire cikin ko"
  Nan ta gyad'a mae kai shi kuma ya tashi ya fita,
 yaje ya sami inna yace "inna shikenan ta daina kukan yanzu kije ki bata abinci taci"
  Inna ta washe baki tace"yo kai Nasiru me kace da ita ne da har tayi shiru kai tsaye?
 Murmushi yayi yace"inna ina sauri yanzu amma gobe idan na dawo mayi magana"
 Tace"to d'an albarka Allah kaimu goben"
 Nn ya fita inna kuma ta shiga d'aki washe da baki".

Billy Giro😊
[ 2/9/2017]
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```










           🔮🔮🔮🔮
*page* *```48```*
Ta sami Rynt ta tashi tana linke carpet d'in sallah.
  Inna ta kar6i carpet d'in ta koma shimfid'a mata a nn kusa da gefen gado tace da ita "zauna bari naje na kawo maki abinci kici ko"
 Rynt ta gyad'a mata kai snn ta zauna,
 inna ta kai hannu nn kusa da bedside drawer ta d'auki abincin rnr da Rynt bata ci ba taje dashi kitchen ta kawo mata tuyon shinkafa da miyar ganye wacce taji qassan nmn rago .
Ta kai kusa da Rynt ta ajiye snn ta kawo mata ruwa da kunu da magunguna a cewar idan ta gama cin abinci sae tasha.
  Sae da Rynt ta yiwa inna godiya snn ta kai hannu had'e da  bisimillah ta fara cin abinci.
  Da ta kammala ne takai kwanika a kitchen ta dawo ta fad'a bathroom tayi wanka koda ta fito ta sami inna na waya cike da murna tana gama wyr ne take ce ma Rynt"Ashe saurin da na Nasiru keyi fatima ce a asibiti shine yanzu aka kirani aka snr dani ta sauka lfy ta sami d'a"
 Rynt ta d'an saki fuska snn tace"to Allah ya raya masa shi akan sunna"
 Inna ta washe haqora tace"Amin amin ai ba dan dare ba da naje naga sabon mae gidana"
  Murmushi kawae Rynt tayi taje ta nemo kyn bacci ta saka ta kwanta.

Washe gari Rynt taji sauqi sosai don ita ma ta gyare gidan tsaf ta kuma je kitchen tana ragewa Baaba hurera aiki wacce tana zowa bata fara aiki ba suka tafi gidan su mohd gun barkar pretty ita da inna.

Tana cikin aikin ne suka dawo  Baaba hurera ta shigo tana mata sannu da aiki snn tace taje inna na kiranta a falo.
 Koda taje falon ta sami inna da Abban mohd taje ta durqusa cike da ladabi tana gaida shi ya amsa mata cikin sakin fuska snn yace"ya jikin naki?
 Tace"Alhmdlh"snn yace"dama zançen karatun ki ne tunda kinji sauqi gobe
zan turo driver wanda zai riqa kai ki makaranta yana maida ki,snn kmr yanda ake maki lesson a can gidan nn ma zan nemo maki wanda zai riqa zowa yana maki lesson d'in,snn kuma duk wani  abu da kk buqata ki snr da inna sae ta snr dani"
 Tace"to Abba nagode"
 Yace"shikenan tashi ki tafi"
 Bayan ta wuce ne ya ciro kud'i a aljihun sa bandir d'in 1k guda biyu yaba inna yace"d'aya naki ne d'aya kuma ki riqa bawa Rynt d'ari biyar biyar duk safiya ta na samun na cin abinci  idan taje mkrnta dn naga mkrntar tasu yini ake"
 Ina ta kar6i kud'in had'e da sa mishi albarka yace"nagode inna ni zan tafi"
   Tace"to d'an albarka Allah kai ka lfy"
Yace"amin"
 snn ya fita.
Ita kuma taje d'aki ta adana kud'in.

          *****
Kwance  yake kan bed sanye da farar singlet da farin boxer malika ta shigo d'akin ta kalli yanda ya d'ora qafa kan qafa yana mai kallon silin.
  Taje ta zauna kusa dashi tana mai kallon fuskar shi snn tace"my man ya kamata ka haqura ka daina tunani akan rashin da mukayi,ai Allah zai sake bamu wani ne komai baqin cikin wnn abar kuwa.
 Lumshe idonsa kawae yayi ba tare da yace komai ba tace"ya zancen zuwa gidan naku ?
Yace"ki tafi kawai"
 Tace"baza kaje ganin jariri ba knn ?
   Kallonta kawae yayi bai ce mata komai ba sae kwanciyar sa da ya gyra.
  Tasan ba amsar zata samu ba shiyasa kawae ta tashi tabar d'akin taje ta shirya ta fita.

Gidan su man d'in ta nufa wacce da shigar ta 6angaren su man kai tsaye ta haura sama zuwa d'akin mhfyr man ta bud'e qofar d'akin ta shiga ba ko sallama,pretty dake zaune kan bed tana shayarwa ta saki murmushi tace"sae yanzun"
Sae da malika ta zauna snn tace"hm nida nake ganin ma nayi sammako"
   Pretty ta bata jariri tare da fad'in"yaya fa?
Tace"wlh yana can cikin damuwar rashin babyn mu har magana ma bai cika son yi ba"
  Pretty ta cije le6e tace"wlh Allah matsiyar yarnr nn taci uban rainin wayo! ni kuna me wae ma har tayi nasarar 6arar miki da ciki?
  Malika ta ta6e baki had'e da murmushi snn ta duba koina idan ba mai ganin su  ta kai bakinta a kunnen pretty ta rad'a mata magana ,pretty ta fiddo ido had'e da washe baki snn tace"kai haba!
malika tace"Allah kuwa
snn tace"amma fa bakin ki qanin idonki wlh kar ki bari kowa yaji zancen nn don ina gudun ya koma kunnen yayanki"
 Tace"haba dan Allah sae kace ban san me nakeyi ba ai ko umma bazata ji wnn zancen ba,,kuma kin san Allah da har kin ban haushi da naga na koma kai miki magani amma naji shiru ashe kinsan abinda kk shirin yiwa matsiyaciyar.
Malika tace"ai ke ajiye maganin gefe nayi nace sae na gwada plan d'ina tukun.
  Pretty tace"shiyasa da muka je dubaki lkcn da umma keta masifa tana fad'in duk laifinki ne dan da kinsa mata maganin a abinci taci ta haukace da duk hkn bata faru ba sae naga kin kalle ta kawae kinyi shiru .
  Malika tayi dariya tace"wae ina umma take ne ma?
 Pretty tace"Wlh tana kitchen da fitar ta mane ba jimawa se kika shigo.

 8:30pm
Inna ce zaune a falo ita da Rynt suna cin abinci bayan sun gama Rynt tace"inna nifa gobe bana da kayan sawa idan zanje makaranta duk suna gidan can"
  Inna tace"ayyo ai tuni an kwaso maki kayanki suna a d'akin ki nasa nasiru yakai  ,
ai a cikin kayan ne ma na d'ebo wasu en kyn sawa nakai miki a d'akina"
  Tace"inna kayan mami fa?
  Tace"yo ai kaji fa amma bari na kira nasiru naji da yaje kwaso maki kaya har da kayan mami ya kwaso ya had'o ko kuwa"
 Nan ta d'auki wayarta ta kira nasir bayan sun gama wyr ne tace ma Rynt yace duka har kyn mami d'in ya had'o ya kwaso wanda tun d'azun yaso yazo ya d'auki kayn nata yakai  gida sae bae sami lokaci ba amma yace yanzu zai zo ya d'auki kayan"
 Rynt tace"to bari naje na had'a masa kayan kafin ya iso"
 Inna tace"to"
 Snn Rynt ta tashi ta nufi d'akinta da take zama a daa.
  Kan gado ta sami kayan nasu  komai har akwatinan lefenta wad'anda kallo d'aya ta musu ta kauda idonta ta d'auki akwatin mami ta bud'e taga komai nata na ciki ta rufe akwatin ta ajiye ta gefe kusa da qofar d'akin snn taje ta bud'e akwatin ta wacce inna ta saya mata ta samu itama komai nata na ciki zata rufe kenan akwatin ta sa6ule ta fad'i sae duk kayan suka fita nn ta hango tsofuwar ajiyar ta ,ta kai hannu a hnkli ta d'auki viva ledar ta bud'e .
 Kayan da marigayi anwar ya bata ne a ciki nn ta shiga ciro kayan d'ai d'ai tana kallo.
 Hawayenda suka cika mata ido ne suka shiga gangarowa a hankali yayinda ta ciro bandir d'in 1k guda biyu masu d'auke da jini a jikin su nn taji inna ta qwala mata kira tayi saurin mayarda kud'in har kynda anwar ya bata snn ta amsa kiran da inna ke mata had'e da share hawaye ta kama hanya zata fita sae ga nasir ya shigo d'akin yace"har kin gama had'a kayan?
 tace"na samu kayan a had'e suke"
 Yace "eh hkne ni na had'a kyn tun can sbd a wardrobe d'inta na sami akwatin ta shine na saka mata duk kayan da ke cikin wardrobe d'in haka kema"
 Tace"mungode"
Snn yace"zancen da mukayi jiya dake ban manta ba ina son sae na sami lokaci ne sae nazo muje a cire cikin ko?
 Tace"to"
Yace"yauwa sae ki maida hnkli ki ci gaba da zuwa mkrnta kinji"
  Nn ta gyad'a mishi kae shi kuma yaja akwatin mami ya fita.
 Ita kuma taje ta gyra kayan akwatinta da suka zube ta rufe sae dae kafin ta rufe akwatin sae da ta cire kynta na zuwa school ta d'auke su ta tafi dasu d'akin inna.

12:00 na dare
Man ne ya fito d'akin shi wanda bai zarce koina ba sae d'akin Rynt .
 A nn bakin qofa yayi tsaye yana qarewa d'akin kallo sae can ya qarasa shiga d'akin yaje gun wardrobes ya bud'e yaga ba komai kaf an kwashe ya maida wardrobes d'in ya rufe .
Har zai fita sae ya hango farar suit jacket d'inshi kan sofa yaje ya d'auki jacket d'in a hnkli yana kallo,
Se kuma yayi saurin kauda idonsa kan jacket d'in ya kuma jefar da ita kan sofa ya fita.



Washe gari da safe Rynt ce ta kammala shirinta tsaf na school inna ta ciro d'ari biyar ta bata Rynt ta kar6i kud'in tace"ba canji ne inna?
 Inna tace"canjin me kud'in ki ne fa da zaki tafi dasu makaranta na cin abinci ko basa isar ki?
 Rynt ta bud'e ido tace"inna ai kud'in sunyi yawa ai d'ari biyu ma sun isa kuma ina ma da kud'i a hannu na da kin barshi kawae inna"
 Inna tace"yo Rynh kud'in hannunki ai naki ne,wad'an nn kuma na cin abincin mkrntr ki ne kabiru ya bayar a riqa baki"
 Tace"to inna nagode amma dae zan dawo da sauran canji dan sun min yawa"
  Inna tace"to er albarka a dawo lafiya Allah tsare min ke ya kuma bada sa'ar karatu"
 Tace"amin inna"snn ta fita ta samu driver na jiranta a qofar gida taje ta shiga motar yaja suka tafi.



Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```










           🔮🔮🔮🔮
*page* *```49```*
Ana sauke Rynt a school sae kawai taji ihun mami tazo aguje ta rungumeta.
cike da murmushi Rynt ke kallonta tace"mami kece waya ya kawo ki?
Washe da baki tace"Abbana ne yanzu ya wuce"
Sae kuma tasha toka tare da fad'in"Anti wae meyasa kika koma gidan inna da zama?
  Rynt tayi shiru tana kallonta can tace"to ai dama can gidan inna nake zama ko kin manta"
 Tace"Aa ni nafi son ki koma gidan yaya sbd na fi son a riqa kawo mu school tare"
  Rynt tace"ai ko ba'a kawo mu tare ba, ba gashi muna had'uwa ba"
 Turo baki tayi tace"um um anti hk ba dad'i"
  Rynt tace"kinga jeki 6angaren ku za'a fara assembly kar kiyi letti kinji"
 Mami tace"to Anti gsky ni sae kin gaya min yaushe zamu koma gidan yaya"
 Rynt tace"to kisa ido duk rnr da kika ga raqumi ya shiga akurki kizo da gudu ki gaya min sae mu koma ko"
  Da murna mami tace"dgske anti!
 Rynt tace"eh"
 Mami tace"meye ma raqumi wnn abun mae girma kmr doki ko"
  Rynt tace"eh"
Mami ta daka tsalle tace"Allah kuwa da jimawa na ta6a ganin shi hnyar kasuwa,gobe ma zan cewa umma muje kasuwa da na ganshi zanyi ta kallon shi har sae naga ya shiga akurki sae nazo har gidan inna na gaya miki,sae mu koma abin mu gobe gidan yaya ko.
 Rynt tayi murmushi had'e da girgiza kanta ta tafi  tana  fad'in"to naji zan neme ki a break"
 Tace"ok anti bye"


 5:00pm
Rynt ce ta dawo daga mkrnta ta sami inna a falo duk ta raja'a gun kallo har sallama tayi kusan sau biyu amma bata ji ba, tayi tsaye d'auke da murmushi tana kallon inna snn taje a hnkli kan jikin inna ta rungumeta,
a tsorace inna ta juyo ganin Rynt ce ta sauke numfashi tace"yo Rynh kece aini har kinsa na tashi guduwa ,
Rynt tace"haba dae inna da tsufanki kk shirin guduwa?inna tace"yo ai shi tsoro ba ruwan shi da tsufa "
 Dariya Rynt tayi tace"hln ma meya tsorota ki ne inna?
Tace"yo Rynh ina zaune qalau kawae naji an hau kan jikina bayan nsn ni kad'ai ce a falon ban kuma ji shigowarki ba
Tace"to inna ai nayi sallama har sau biyu kece dae bakiji ba sae kallo kike tayi abinki"
  Inna tace"ayyo inafa zanji na maida hnkli gun shiriritar  banzar nn da ba zata fisshe ni ba"
Murmushi kawae Rynt tayi ta tashi tare da fad'in "inna ni zanje na d'an watsa ruwa"
  Tace"to er Albarka sae kin fito"
  Nan Rynt ta wuce inna kuwa taci gaba da kallo.

Tana gama wanka ta shirya ta ciro wata baqar leda a cikin jakarta ta mkrnta ta fito ta tafi kitchen sae gata ta dawo d'auke da agwalima cikin bowl.
 Taje ta zauna qasa kusa da kujerar da inna ke zaune akai ta d'auki d'aya zata fara sha tare da fad'in" inna ga agwalima"
   Inna tace"yo Rnynh ni na d'auka ko abinci ne kika d'ebo"
 Tace"Uhm agwalima ce na wanko na d'an sha ko d'aya ce sae naci abinci "
 Inna tace"lallai kam ki hanzarta kici abinci kafin mai miki dasarin yazo"
   Tace"inna ni idan ma da fura ita kawae zansha ba sae naci abinci ba dan bana jin yunwa"
  Tace"to tashi kije ki d'ebo furar tana can a cikin firijin tayi sanyi kuwa.
  Ba musu Rynt ta tashi ta d'ebo furar tazo tayi zaune ta shanye agwalimar hannunta snn tasha fura tana gamawa taje ta had'o komai nata na lesson ta fito ta samu inna na kar6a sallama inna na ganinta tace yauwa je d'auko tabarma don inaga mae miki dasarin ne yazo,nn Rynt ta koma d'aki ta d'auko tabarma ta fita.


6angaren mohd kuwa kwance yake a falo shi kad'ai kan 3 seater ya lumshe ido kmr mae bacci.
  Da damuwa ya bud'e idonsa had'e da guntun tsaki sbd door bell d'inda yaji ana fmn dannawa kan dole ya tashi yaje ya bud'e qofa, ganin wanda ke tsaye yasa ya d'an saki fuskar shi ya bashi hannu suka gaisa har yana masa ya hanya.
  Wanda ba kowa bane face lesson teacher d'in su Rynt wanda tun lokacinda yayi tafiya sae yau ne ya dawo.
   Man bai iya bashi hanya ba sae nazarin abinda zai ce masa yake can ya kallesa yace"kayi hqr fa yaran basa nn sunyi tafiya"
 Lesson teacher yace"to shikenn amma yaushe ne zasu dawo?
  Shiru man yayi can yace"ka tafi kawae dae"
Ba musu lesson teacher d'in yayi sallama dashi ya wuce.
  Man ya rufe qofar ya juya ya sami malika a tsaye tace"my man waye ne?
 Yace" Lesson teacher ne
Tace"au shi baisan matsiyaciyar tayiwa kanta tsiya ba"
  Komai bai ce da ita ba sae zama yayi ya jingina bayansa tare da lumshe idonsa .
   Nn taje ta zauna kusa dashi tare da kwanciya kan qirjinsa yace "pls malika im nt in mood n i just wnt me alone ki tafi d'akin ki kinji "
Zata ce wani  abu knn yace"pls just go"
 Jiki sanyaye ta tashi ta tafi zuwa d'akinta,haka shima ya tashi ya bar falon ya tafi d'akin shi.

2 dayz later
haka mohd ya cigaba da rashin son damuwa komai qanqantar ta kuwa shiyasa ko yaushe yafi son ya kasance shi kad'ai wanda ko asibiti yaje baya wani jimawa yake dawowa.

 Rynt kuwa sae karatun ta tasa ma gaba wacce ko yanzu zaune take a d'akinta ta tasa agwalima gaba tana sha yayinda take duba littafan mkrntar ta na boko dana islamiyya ,
kasancewar yanzu ta gyara d'akinta ta dawo ciki da zama sae bacci ke kaita d'akin inna.
  Tana cikin duba littanfanta ne taji inna na qwala mata kira taje ta sami inna a falo inna taba ta waya tace"nasiru ne wae ki gaya mae abubuwanda aka ce ku siyo a makrnta.
  Nan ta kar6i wyr ta snr dashi snn taba inna wayarta ta koma d'aki taci gaba da duba littafanta.
     Ba ita ta tattara littafan ta ajiye ba sae da ta soma jin bacci duk da cewa dare bai wani yi sosai ba don qarfe tara ne a lokacin.
  Bathroom ta shiga tayi wanka ta fito tayi shirin bacci cikin riga da wando ta zuba qaton hijabinta ta fito riqe da agwalimar ta guda biyu a hannu.
 Nan ta had'u da Nasir ya fito d'akin inna zaije d'akinta hannun sa riqe da farar leda mai hoton littafai da kuma al'amin bookshop a rubuce ta gaida shi ya amsa tare da miqa mata ledar yace "duba kiga littafan ne "
 Ta duba tace "eh sune nagode"
 Har ya juya zai fita sae kuma ya juyo ya kalleta tayi saurin sadda kanta qasa yace"ki qara hqr kwana biyu kinji ni shiru har yanzu ban sami kaina bane"
  Tace"ba komai yaya ai ka barshi kawae sae ka sami lokaci"
   Yace"to sae da safe"
Snn ya fita ita kuma taje ta ajiye littafan a d'akinta taje d'akin inna.
 Da shigarta ta bud'e fridge ta saka agwalimar ta a ciki.
 
 Washe gari an sauke Rynt a makaranta sae dube dube take ta inda zata hango mami sbd kwana biyun nn duk suna had'uwa da safe idan an sauke su.
 Tana cikin dube dube ne sae ga mami ta shigo gate d'in mkrntar da gudu Rynt ta saki murmushi taje ta tarbota tana mae fad'in"wnn gudu haka mami ba kya tsoron kije ki fad'i"
 Tace"Anti sauri nake kar baki ganni ba ki tafi don na hango lokacinda aka sauke ki mu kuma muna baya da nisa har ma nayi ta kiranki baki ji ba,
to kince da nisa ya zan jiki mami,
Mami bata ce komai ba sae lunch box d'inta ta ajiye qasa snn ta ciro school bag d'inta dake bayanta ta bud'e ta ciro er wata container rubber mai marfi taba Rynt tace"umma tace na kawo maki"
Rynt ta kar6a takai hannu a hnkli ta bud'e.
 Wacce tana bud'ewa qamshi mai dad'i ya daki hancinta nn taga
 awara ce wacce taji cabbage da albasa bayan sauce d'in hantar rago da aka zuba akai mai had'e da kayan lambunda aka yanka su slice by slice ta yanda kallo d'aya zakayiwa awarar ka sami kanka da tsinkewar yawu.
  Cikin nuna jin dad'i ta rufe snn ta kalli mami tace "kice ma mama nagode sosai kinji"
  Mami tace"yauwa anti nifa har yanzu bamu je kasuwa ba bare naga raqumi ya shiga akurki,idan ma nayiwa umma magana se dariya kawae take min,ta qarashe mgnr ne shaye da toka.
  Rynt tayi murmushi tace"umma da kanta take miki dariya"
 Tace"eh mana"
 To yi hqr jeki kar a fara maku assembly"
 Daga hk kuwa sukayi wa juna bye bye suka wuce.

10:00pm
Man ne zaune kan bed ya rufe laptop d'inshi ya d'aura kan bedside drawer ya kwanta  sae ga malika ta shigo d'akin taje ta kwanta kusa dashi had'e da kai hannu tana shafa sajen fuskar shi har izuwa qirjin shi,
 kallonta yayi tare da janye hannunta daga kan jikinshi ya kashe wuta had'e da juya bayan shi,nn yaji ta matso gab dashi ta rungume shi ta baya
 yace"pls malika bana son damuwa kin sani,ki matsa kusa dani bana son jinki a bayana.
  Kmr kazar da qwai ya fashewa ta jaye jikinta daga nashi.


Billy Giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```










           🔮🔮🔮🔮
*page* *```50```*
Washe gari guraren qarfe goma na safe mohd ne ya fito daga bathroom sanye da white bathrobe wanda kai tsaye gun wardrobe ya nufa ya ciro black suit ya ajiye kan bed yayinda malika ke kwance  akan bed d'in tana ta sharar bacci.
 Bayan ya gama shirin sa tsaf ya d'auki makullin motar sa ya fita,ya bud'e motar sa zai shiga knn sae ga driver yazo byn sun gama gaisawa ne yake cewa "yalla6ai lafiya kwana biyu naga mami da yayarta  basa fitowa zuwa mkrnta ko anyi hutu ne banida labari?
   Ba tare da yako kalle sa ba yace"sunyi tafiya ne"
 Daga hk kuma ya shigewar sa mota yaja ya tafi.

 Yana shiga office wayar sa ta shiga ruri  ya ciro wyr a aljihu ya d'aga tare da fad'in"Aamil ya akayi ne"
 Daga d'ayan 6angaren  yace"man muna son zamu shigo 9ja ne but no actual time,bcs akwai wani  aikin da Amir keson qarasawa da sae idan ya kammala shi ne snn ko zamu zo,but idan mun zo d'in wnn karon ba a gida zamu sauka ba a gidajen mu zamu sauka shine muke son kasa a fara gyara mana gidajen sbd may be gyaran zai d'an d'auki lokaci kan irin yanda aka jima ba'a shiga gidajen ba,if ma gidajen na buqatar canjin komai pls duk kasa canza a mana.
Man yace"ok naji ka gaida Amir bye"
 Daga hk ya katse wayar yaje ya zauna kan kujerar sa mai shillo tare da kai hannu kan landline ya latsa lambobi ya kira, ba jimawa sae ga wata er kyakkyawar farar yarinya ta shigo da bazata wuce 22 yrs ba d'auke da teacup n saucer a hannunta taje kan desk ta ajiye masa snn ta juya ta fita.
    Mohd dake latse latse da laptop d'insa yakai hannu a hnkli kan teacup d'inda ke kan saucer ya d'auka had'e da kai bakinsa yana shan tean da ke ciki yayinda yake ci gaba da latse latse da d'ayan hannunsa.


Malika kuwa tunda ya barta ba ita ta farka ba sae 12 wacce da tashin ta ta fad'a bathroom tayi wanka ta fito taje  d'akinta ta shirya kafin take sa cleaner ya gyrawa mohd d'akin shi.
 Bayan ta gama shiri ne tazo downstairs tayi breakfast taje kan 3seater ta kwanta sae chat take.
     Sae jin tayi an fizge wyr tayi saurin tashi zaune had'e da kallon wanda ya fizge wyr.
 Qawar ta Fa'iza ce ta gani tana mata dariya itama dariyar ta mata snn tace"yau kuma bazata kika min"
  Tace"wlh kedai kan hanya muke nida hubby zamu je gidan su shine nace ya d'an biyo dani nn mu gaisa mun kwana biyu bamu had'u ba tun asibiti"
  Malika tace"aini fushi ma nake yi dake wae ace tun asibiti ba waya ba text ba chat"
 Sae da Fa'iza ta nemi guri ta zauna kusa da ita snn tace"wlh banji dad'i bane kwanakin nn shiyasa banida lokacin waya don  kashe ta ma nayi  sae yau na kunna"

 Malika tace"eyyah to ya jikin?
 Allah naji sauqi sosai ya man da haqurin rashin babyn shi da yake fama?
 Malika tayi er dariya snn tace"in gaya miki har yanzu ya kasa haqura ya cire abun a ranshi har ma baya son damuwa kwata kwata he is so lonely.
 Fa'iza tace"lallai yana son baby sosai sae ki hanzarta ki samar mai wani "
 Tace"Hm ba yanzu ba sae mun gama baje soyayyar mu tukun"
 Fa'iza tace"ta bayan fa da akayi?
 Aikin san wnn soma ta6i ne ga kuma wnn abar wacce duk da nasan ba kulata yake ba amma idan na tuna cewa wae mtr my man ce sae na nemi farin cikina kaf na rasa but now nsn cewa ni kad'ai ce nayi waje da matsiyaciyar banida wata damuwa sae hln damuwa da my man d'ina yake ciki a yanzu wanda ko shi na d'an kwanaki ne zai ajiye shi mu dawo normal.
   Fa'iz tace"hkne kam kinga bari na tashi naje nabar hubby shi kad'ai a mota"
 Nan malika ta tashi taje har mota ta rakata suka gaisa da mijin fa'iza snn ta dawo.


Rynt ce a class ita da qawar ta sae er fira suke yayinda Rynt ke d'anyi tana duba littafinta kasancewar free period suke malami ba zai shigo ba.
 A cikin firar ne qawarta ta riqo hannun Rynt tace"ni kuwa Rynt kinga wani haske da kika soma yi harda er qiba da kuma wani irin laushi da jikin ki ya qara gaya min meye sirrin"
 Ta qarashe mgnr tana murmushi haka ma Rynt murmushin tayi snn tace"hm yanayi ne kawae....da kuma hutawa ba,cewa da qawarta, Rynt wacce still murmushi nakan fuskarta ta girgiza kanta tace"Sarah knn ba kya rabo da wasa"
  Sarah tace"Allah ki tambaya kiji duk wanda ya kalli ftr jikin ki yasan cewa ke er hutu ce"
Rynt tace"jikin ne kawae"
Sarah tace"ba wani nn kedai kawae ba kya son a fad'a ne"
Rynt dae bata sake cewa komai ba sae murmushi kawae da tayi yayinda Sarah ta d'aura da cewa keda yayanki skin nature d'inku d'aya sae dai ya fiki kyau da haske"
   Da wasa Rynt ta bugo ta tace"is not gud mun sami time mu 6ata shi a banza karatu ya kamata muyi ba surutu ba"
 Sarah tace"to qanwar biro da takarda ke kullum karatu dae karatu  ba hutu"
  Rynt tace"naji dae muyi karatun idan kuma kince srt sae na qara gaba"
  Ta fad'i hkne had'e da yunqurin tashi Sarah tayi saurin cewa "no yi hqr muyi karatun to"
  Da haka kuwa kowaccen su ta kama litfafinta suna dubawa yayinda wasu en class d'in keta fmn hayaniyar su har da su tsokane tsokane da guje guje"
   Can Rynt tayi d'an guntun tsaki ta kàlli sarah tace"Sarah nifa surutun nn ya isheni muje library"
  Nan kawae sarah ta bud'e tsakiyar littafinta ta 6alli paper tare da bud'e murya tace"noise maker!kuma d'iya ko dogon motsi kikayi wlh sae na rubuta sunanki na kuma had'aki da uncle ci ubaka"
  Sae kaji take class d'in yayi tsit sbd kowa na tsoron malamin ga kuma Sarah no mercy ce kan shine ma yasa aka bata class monitor.
  Kan desk Sarah ta hau ta zauna inda take fuskantar kowa ta kalli Rynt tare da d'aga mata gira snn tace"to reader master gareki sae kiyi ta krtn ai ko"
     Rynt tayi nurmushi had'e da girgiza kanta ta jawo littafinta taci gaba da dubawa.

 Bayan sati d'aya da faruwar haka.
  Nasir ne shi da Rynt a office d'in abokin sa fa'iz yayinda fa'iz ke snr da nasir cewa "a gsky idan akace a cire mata cikin nn yanzu ba qarama wahala zata sha ba koma nace zata iya rasa ranta gabad'aya dmn watannin cikin sunyi qanqanta da a cire mata shi yanzu sae dae zuwa nn gaba idan ya qara wasu watanni tukun"
 Nasir ya sauke numfashi had'e da kallon Rynt da kanta ke qasa yace"kinji abinda yace a cire maki ne ko kuwa?
Jiki sanyaye ta d'ago ta kalli nasir tace"Aa a barshi idan ya qara watanin sae a cire"
  Nan Nasir ya kalli fa'iz wanda ya shiga rubuce rubuce akan takarda da ya gama ya bawa nasir yace"a siya mata wad'an nn magungunan ta riqa sha kafin lokaci yayi"
 Nasir ya kar6a had'e da yi masa godiya snn suka fita.

Bayan sun iso gidan inna ne Rynt ta nufi d'akinta Nasir kuwa ya shiga d'akin inna wacce tana ganin shi ta tarbe shi da fad'in"inace anyi nasara?
 Nasir yace"anyi nasara inna dmn sam bata fhmci wayo ne ake mata ba"
  Inna ta washe baki tace"kai Rynh knn akwai quriciya shike nn ta yarda idan ya qara wasu watannin zuvarwa za'ayi"
  Nasir yayi murmushi yace"to inna kinsan fa qaramar yarinyar ce sosai"
    Wlh kuwa shiyasa na tausaya mata da cikin nn da ta samu da wuri haka da akayi auren na d'auka ko muhammadu zai yi mata en dibarun su ne har ta kammala karatun ta amma da yake shashashan yaro ne ya d'ura mata ciki ya kuma saki"
  Nasir yace"ayi ta hqr kawae inna da sannu komai zai wuce"
    Tace"hkne kam amma ya kake gani idan cikin nn ya tsufa haka zatayi ta zuwa mkrnta d'auke dashi kuwa?
  Eh to nima abinda nake tunani knn har ma nake d'anyin wata shawara a raina sae dae na gama yanke shawar sae nazo mu tattauna,snn kuma akwae wasu magunguna a hannun Rynt da zata riqa sha.
Inna tace"to kaddai wata matsalar aka samu a tare da cikin?
 Ko d'aya kawae na qarin jini ne da kuma lafiya fa'iz ya rubuta mata shine muka  tsaya kan hanya na siyo mata" inna tace"ayyo d'an albarka to sannu da qoqari Allah ya qara maka bud'i da qarfin taimako"
 Yace"amin snn ya fita.
 Fitar sa keda wuya sae ga Rynt ta shigo d'akin d'auke da murmushi a fuskarta tace "inna kinga yaya nasir ya saya min agwalima mae yawa daga kawae yaganni ina kallon gurin shine ya tsaya da mota ya saya min"
Ta fad'i hakane yayinda ta miqawa inna wata er baqar leda cike da agwalima,inna ta kar6a washe da baki tace"d'an albarka shidae akwài shi da qoqàri ,ai wnn sae ki kwana biyu kina shà"
   Rynt tayi murmushi tace"inna amma yau zaki sha ko"
  Inna tace"yo ina na iya da harakar tsami kaiwa baaba hurera dae ko ita zata iya sha"
 Rynt tayi dariya had'e da fita d'akin wacce tasan ko baaba hurerar basha zatayi ba .


Washe gari guraren 11 na safe mohd ne zaune a cikin office d'insa yayinda ya jingina bayan sa akan kujerar da yake zaune idanun sa a lumshe sae juyi yake a hnkli.
  Knocking akayi had'e da shigowa office d'in ba tare da izini ba hkn yasa mohd yayi saurin bud'e idonsa suka fad'a kan abokin sa jamil wanda ya ta6a samun sa gida da jimawa.
  Man bai ce dashi komai ba har jamil yaja kujera ya zauna sae a snn yace da shi saukar yaushe?
  Jamil yace"saukar jiya jiya har ma na had'u da matarka sun fito asibiti ita da Nasir, ya ma sunanta?
   Man dake jingine yana kallon sa ya lumshe ido had'e da fad'in"Rayyanat"
 Jamil yace"nyc name,amma kuma wae kana nufin har yanzu baka fara kula yrnyr bane da har za'a d'auketa aje da ita wani  asibitin bayan ga ka"
  Man yace"jamil shin me ya kawo ka office d'ina?
  Murmushin mamaki jamil yayi snn yace"mugun gaye tambaya ta ma kake, to zo nayi mu gaisa idan kuma zan fita na bar ma office d'in ne to"
  Man ya d'ago daga jinginen da yake had'e da murmushi yace"wato jamil ka fiye surutu har kazo kan abinda bashi bane"
 Jamil yace"wane zancen ne nayi da bashi bane na matarka ko kuwa?
   Shi d'in sbd zancenta yana qara min damuwar da nake ciki da kuma qunci sbd abinda na aikata a gareta tun daga rnr ban qara samun sukuni ba,
 wlh jamil ban....mts kawai dai barshi zan warware matsalar wa ni kad'ai,jamil ya numfasa yace"mtsw shine matsalar ka wlh me zaka ragu dashi dan ka gaya min matsalar ka mun warwareta a tare,shin ka manta ni sau nawa nake gaya ma tawa matsalar mu kuma zauna mu warwareta nida kai"
  Man yace"wato Jamil  tawa matsalar babba ce dani kaina ban san ta inda zan fara warware matsalar ba.
  Jamil ya tashi tare da fad'in "olryt shikenan ai sae kayi ta fama da matsalar a ranka har taci ka ta cinye"
  Nn ya kama hnya ya fita man kuwa sae binsa da ido yayi.

Billy Giro😊
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```






_Fateema m Abdul haqiqa jiya saqon ki ya qaraso guna wanda yasa naji dad'i kan irin qaunar littafin nn da kike amma dan Allah ina bai baki hqr sbd a gsky bani da enuf time d'in da zan riqa yi maku two pages a rana but i will try my best na ganin cewa na riqa yi maku d'an dogon page_ _inshaAllah😊._
  _Luv u all❤_



           🔮🔮🔮🔮
*page* *```51```*
A hnkli ya furzadda iskan bakin shi had'e da komawa kan kujera ya jingina bayanshi ya kuma lumshe ido yana mai shafa sumar kanshi.
   Ya jima a haka snn daga baya ya tashi ya harhad'a komansa ya rufe office ya fita.

Rynt na zaune cikin class  as usual tana duba littafinta sae ga wani  malami ya shigo nemanta a cewar tazo wani  na son ganinta nn ta rufe littafinta ta jawo locker ta saka littafinta snn tabi bayanshi.
   Suna kaiwa harabar mkrnta ta tsaya cak sbd hango man da tayi tsaye can a qarqashin wata bishiya ya parker motar sa ya jingina yana waya.
     Cikin 6acin rai ta buga dogon tsaki had'e da juyawa zata koma class,
 malamin da ke tare da ita ne ya dakatar da ita ta hanyar kiran sunanta
wanda hakan yasa man dake waya ya katse wayar yana mai kallon Rynt da tayi tsayinta taqi juyowa nn ya qarasa gurin su yace da malamin
"tafi kawae malam nagode"
 Nan malamin ya wuce shi kuma ya riqo hannunta tayi saurin fizgewa had'e da watsa masa mugun kallo bai kulata ba sae sake riqo hannun nata yayi tana fizge fizge tana qari har ya tafi da ita cikin mota nn seat d'in baya,
 qam ya matse ta a qirjinsa yana mai kallon fuskarta yayinda ita kuma take ta son ta fizge kanta.
   Yace"kinga dakata natsuwar ki nake so zan tamvaye ki abu d'aya kacal idan kin bani amsa zan barki ki tafi"
   Tace"to ai sae ka sake ni"
Ba musu ya saketa tare da fad'in "me kuka je yi asibiti ne keda nasir?
  Tsaki kawae tayi had'e da saurin fita motar,
 yayinda shima yayi hanzarin binta ya fizgota da qarfi yace"bana son raini bani amsar abinda na tambayeki"
 Cike da tsiwa tace"ciki naje zubarwa kuma an zubar sae me!
  Da mugun razana yace what!
  Bata kula shi ba sae fizge hannunta tayi da qarfi ta tafi ta bar shi nn tsaye  sororo wanda a fusace yaje ya shiga mota ya fizge ta da gudu ya tafi.
  Bai zarce koina ba sae gidan Nasir bai sami nasir ba sai labari ya samu a gun makwabcinsa cewa tun da safe nasir yayi tafiya baya gari.
 Cike da 6acin rai ya koma gida wanda da shigar sa d'aki kai tsaye gun fridge ya nufa ya bud'e ya ciro gorar ruwan da sukayi mugun sanyi ya kafa a bakinsa bashi ya janye gorar ba sae da ya shanye ruwan kaf snn ya jefar da gorar ya kuma cire kayan jikin sa ya  fad'a bathroom ya watsa ruwa ya fito  a tunanin sa hkn da yayi zai rage masa zafin zuciyar sa da yake jin yana ratsa mai ta koina amma ina abin sae qaruwa yake sbd jin yake mgnr Rynt nata maimatuwa a cikin kunnen shi.
   Da azama yaje ya bud'e fridge ya ciro kwalin fresh milk ya kafa a bakinsa sae sha yake kmr mashayinda ya sami kwalbar giya.
  Nan malika ta fad'o d'akin ta kalli yanda yake shan freshmilk d'in a haukace har tana  kwararo mai a jiki ,
taje da sauri ta fizge kwalin taja hannun sa taje dashi kan sofa ta zaunar yakai bayansa ya jinginar yana sauke numfashi ita kuma ta zaro tissue ta goge mai bakinsa har izuwa qirjinsa snn ta jawo shi ta kwantar kan qirjinta tana wani shafa bayan  shi a hnkli kmr wani  qaramin yaro wacce duk a tunanin ta damuwar rashin unborn child d'insa ne ya motsa  mae da yawa hk.
  Sannu sannu take ci gaba da bin jikin sa tana shafa  har ta juyarda abin zuwa wani salon na daban da ya soma sanya man jin relief  ya kuma fara jin kanshi cikin yanayi na buqatuwa  hkn yasa ya kama mata suka shiga wasannin ma'aurata baji ba gani wanda a nn kan sofa suke yunqurin cimma burin su sae kawai man yayi saurin ture malika daga jikinshi yana mata wani irin mugun kallo.
Malika dake fmn sauke numfashi bata damu da kallon da yake mata ba sae dick d'insa da ta miqe take kallo takai hannu zata riqo abun ya daka mata uwar tsawa tare da sa towel ya rufe jikinshi.
 Cikin 6acin rai Malika ta kalle shi inda cikin muryar kuka tace"wae my man wane irin abu ne haka kullum ka kasa cire damuwa a ranka,idan kace kaci gaba da haka to ta yaya zamu sake samun wani baby ne iye!
  Komai bai ce da ita ba sae tashi yayi ya nufi wardrobe xai saka  tufafi taje tasha gaban shi tace"ka gaya min shin ko wnn abar ka had'u da ita ta baka wani abu kasha don na tabbatar da sa hannunta ne kake min abubuwan nn ba wae damuwar rashin baby mu kad'ai bane.
  Yace"kinga fitar min d'aki da banzan shirmen ki....my man....I said get out!
   Rai 6ace ta kama hanya ta bar d'akin sae qunquni take yayinda man ya bita da kallo mai d'auke  tsana.

Tun daga ranar man bai sake sa malika a idonsa ba har aka kwashe sati biyu wanda kwata kwata bai damu ba bare ma ya nemi inda taje abinda kawae ya damu dashi shine ya samu ganin nasir dmn yaji dalilin zubar mae da ciki da sukaje sukayi shida Rynt.
 Shiyasa kullum yana kan hanyar zuwa gidan nasir amma baya samun sa sbd bai dawo daga tafiyar da yayi ba.


Yau juma'a da wuri Rynt ta dawo daga school ta samu inna ta fita anguwa wanda taji hkne a bakin baaba hurera da ta samu kitchen tana aiki wacce ba abinda yakaita kitchen d'in sae wanke agwalima tana gama wanke agwalimar ne taje d'akinta tasha kusan uku snn ta fad'a bathroom tayi wanka ta fito d'aure da towel  iya guiwa ,
taje gaban dressing mirror tana taje gashin kanta da ta wanke .
Wacce gashin kanta kawae ta iya gyarawa ko mae bata shafa ba bare zancen nemo tufafin sawa sbd wani irin bacci da take jin yana fizgarta amma hkn bai hana ta d'auki agwalima d'aya ta hau kan bed ta kwanta tana mammatsa agwalimar daga hakane  bacci yayi awon gaba da ita ba tare da tasha agwalimar ba.


Man kuwa still bai fasa zuwa gidan nasir ba wanda dagà sllr juma'a ma ya fito amma bai zarce koinà ba sae gidan nasir,
Inda gun maqwabcin sa ya sami labarin cewa ya dawo amma yanzu yanzu daga dawowar sa masallaci ya fita yana jin haka  yaja motar sa zuwa  gidan inna cike da niyyar in ya sami Nasir a gidan  sae dae a kwashi gawar d'ayan su.

Yana shiga gidan yaje har d'akin inna ba kowa nn ya tafi kai tsaye sae d'akin Rynt ya same ta kwance  abinta sae sharar bacci take riqe da er agwalimar ta a hannu.

Kallonta yake bako qyaftawa sbd wani irin kyau da yaga ta qara mae da haske ga koinan ta duk ya ciko abin sha'awa ,
nn kawai ya sami kansa da hawa kan gadon yana mai ci gaba da kallonta musamman sumarta da yaga ta qara cika da tsayi sosai ba kmr rnr da ya ta6a ganin ta ba.
 yakai hannun sannu yana shafa sumar wacce ta kasance shimfid'e kan bayanta.
   Shafar sumar da yake yine yasa Rynt ta motsa tare da gyara kwanciyar ta wacce juyinda tayi ne yasa towel d'inta ya rabu da jikinta amma a iya qirjinta kad'ai hakan yasa man ya qure qirjin nata da kallo sbd wasu alamomi da ya hango a tare dashi na masu ciki.
   A hnkli yakai  hannu yana qarasa yaye towel d'in ya tsayadda shi iya qugunta yana mai kallon cikin ta,sannu a hnkli ya d'aura hannun sa akai ya shiga latsa cikin kad'an kad'an yana mai kallon fuskarta cike da farin cikin jin cewa cikin sa yana nn.
    Nan ya jawo Rynt izuwa qirjin sa yana mai kallon hannunta dake jimqe da agwalima yasa hannunsa zai ciro agwalimar,
 Rynt dake jin abun kmr a mafarki ta qara jimqe agwalimar had'e da qara lafewa a qirjin sa da ta d'auko ko kan bed take.
    Nan man ya fasa ciro agwalimar sae yatsan sa  yakai yana shafa lips d'inta a hnkli daga nn ya soma bin jikinta da shafa cikin wani irin salonda ya qara sa Rynt ta d'auka ko mafarki ne don sae motsi take a hnkli tana qara liqe mai a jiki shi kuma yana ci gaba da wasa da jikin nata,
 cikin hakane yakai bakinsa a hnkli kan lips d'inta ya fara tsotsa had'e da d'aura hannuwan sa a kan qirjinta yana shafa abinshi cikin natsuwa.
  A nn fa Rynt ta soma dogon motsi wacce sannu sannu take bud'e idanunta har ta ware su akan shi.


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```











           🔮🔮🔮🔮
*page* *```52```*
A razane ta fasa Ihu tare da ture shi daga kan jikinta taje can qarshen gado ta kame  wacce sae a lokacin ta lura da cewa pant kad'ai take tare dashi a jikinta nn tayi saurin jawo towel zata rufe jikinta man ya riqe towel d'in tare da matsawa gab da ita yana mae mata wani  irin kallon sha'awa yace"da wane dalilin zaki rufe jikinki byn ban gama abinda nakeyi ba"
    Wata irin muguwar harara ta watsa mae ta shiga yunqurin ganin ta qwace towel d'inta da ya riqe.
Bata iya qwatar towel d'in ba sbd da d'ayan hannu ne take fmn kokawa dashi kasancewar d'ayan hannunta nakan qirjinta ta rufe.
 Ganin ta kasa qwatar towel d'in ta sakar mae taje zuwa jawo blanket ya riqe mata hannu ya kuma warce d'ayan hannun da ta kare qirjinta dashi duk ya kama hannayen ya riqe ya kuma kwantar da ita  cike da niyar kai bakinsa a nata bata bar hkn ta faru ba sbd qafafunta tasa ta ture shi nn ya hau kan jikinta gabad'aya ya danne ta ya kuma kai bakin sa kan nata ya had'e
Ba shiri ya zare bakin sa da sauri sbd wani  irin cixo da ta gantsara mae a harshe,
Wanda cikin yanayi najin zafin cizon ya lumshe idonsa sae can ya bud'e idanun yana kallon Rynt dake ta son ta ture shi daga jikinta.
    Nan ya qara matse ta har sae da tayi er qara yace" zaki san wa kika ciza dan ramawa zanyi kuma sae na ftr miki da jini kmr yanda kika min"
    Yana gama fad'ar hk ya nufeta zuwa ramawa wanda a maimakon ya nufi bakinta sae qirjinta ya nufa a rud'e Rynt ta shiga ihu tana dukan shi ya kama hannun ya riqe had'e da kai bakin sa a qirjin nata a nn Rynt tayi saurin lumshe idonta sbd wani  irin abu da taji man na mata a qirji da ya fara kashe mata jiki kai tsaye ,
nn ta shiga yi masa kuka tana son qwatar kanta amma bae barta ba har sae da ya luguiguita ta son ranshi snn ya tashi kan jikinta yana mai gyara buttons d'in rgr shi da suka 6alle yayinda Rynt tayi saurin tashi taja blanket ta rufe jikinta har wuya .
man dake kallonta ya saki shu'umin murmushi yace"me kuma zaki rufe wanda ban gani ba"
  Ta watsa mae harara tare da fad'in"d'an iskan mutum wlh Allah ya isana ban yafe ba mugu kawae"
  Da qarfi ya damqo gashin kanta yace"mind ur tongue idan ba haka ba zaki had'u da fushin ubangiji"
  Ta fixge kanta tace"kai dae zaka had'u da fushin ubangiji macuci wlh Allah ba zai barka ba"
ta qarashe mgnr had'e da fashewa da kuka nn man ya tsaya yana kallonta sae kuka take can yakae hannu zai share mata hawaye tayi saurin buge masa hannu.
  Bai damu ba sae  hannun yakei kan cikinta tare da fad'in"gobe ma zan zo na kawo ma babyna ziyara na kuma yi wasa da maman baby kmr irin ta yau koma fiye don hk sae ki shirya dmn wasar ta mu biyu ce bani kad'ai ba"
Cikin qunar Rynt ta ture masa hannu tare da fad'in"wlh duk kazo kuwa sae na maka ihu qato"
  Man ya gyad'a kafad'unsa yace"kiyi man sae me ko an gaya miki ina tsoron ihun ne"
 Daga haka y tashi ya nufi hnyr fita d'akin Rynt ta bishi da kallon tsana har ya fita snn ta share hawayenta ta jawo towel d'inta da ya jefar ta d'aura ta gyara gadon ta fad'a bathroom tayi arwala ta fito ta saka tufafi ta nemo hjb da sallah carpet wacce sae da ta saka hjb snn ta shimfid'a carpet ta fara sallah.


Mohd kuwa da ftr sa gida ya nufa wanda  yana shiga falo ya taradda mhfyr sa da ummar malika  da kuma malika.
   Yayi kmr bai ga malika ba sae iyayen ya gaisar,inda ba wacce ta amsa mai a cikin su sae ma  masifa da ummar sa ta shiga yi tana fad'in "wane irin abu ne ke damunka mohd ko akan ka aka fara rashi ne da za'ace tunda kuka baro asibiti kake fama da baqin hali wae kai damuwa aiko damuwa ce ita ya kamata ta fika shiga damuwar ita da tayi fama da whlr cikin ba kai ba amma sae kazo kanata qara mata takaici akai da har kasa hqrnta ya qare takai ga yin yaji
wae kuma ta iya kwashe har sati biyu ko leqe ko rege ba zancen zuwa kayo biko.
  Mohd yace"umma nifa fad'an nn bana so akan me dan tayi yaji zan je biko ni nace tayi yajin ne"
  Iyye lallai yaron nn na qara yarda wnn matsiyaciyar bata barka a banza ba, 6ace  na daina ganin ka a nn shashasha!
  Nan ya bar gurin cikin 6acin rae ita kuma hjyrsa tayi saurin shan gaban mhfyr malika da taja hannun malika a cewar ita erta ba wulaqantacciya  bace da zata zauna ana zaman wulaqanta ta.
  Hjyr man tace da mahaifiyar malika"ba'ayi haka ba haquri zakuyi dmn na fhmci yaron nn ba a kanshi yake ba,amma nsn abinyi"
 nn ta ciro wani  qullin magani a jakarta ta bawa malika tace"a abinsha zaki saka masa da zarar yasha ina gaya miki komai qarfin asirin da matsiyaciyar tamae sae ya karye yayinda sheqar zata koma kanta.
   Malika bata kar6i maganin ba sae yatsine fuska tayi snn tace"ta yaya zan bashi abu ya kar6a har yasha bayan kuna gani da ya shigo ko kallona baya sonyi"
  Mhfiyarta ta kwa6e mata baki tace"tafi can ai ma kece matsiyaciyar ba ita ba,ace kina mace baki san ta yanda zaki mar ba ya sauko har ki samu ki had'a mae abun sha yasha"
    Tayi tsaki had'e da kar6ar maganin a hannun hjyr man ta ba malika tace"kar6i ana saki a hanya kina kaucewa kmr baki je class ba"
 malika ta kar6i maganin tana juya shi cike da tunanin yanda zata shawo kan man wacce a cikin tunanin ne ta saki murmushi had'e da kallon mhfyrta da hjyr man da suka ce su zasu tafi"
  Nan taje ta raka su ta ta dawo ta wuce sae d'akinta.

6angaren Rynt kuwa bayan ta gama sallah taje kitchen bata sami baaba hurera ba sae a bayan gida taje ta sameta ta shimfid'a tabarma a qarqashin bishiyar da ke gurin tana ta sharar bacci abinta.
 Dawowa kitchen tayi ta d'ebi abinci taje ta zauna falo tana ci jiki sanyaye don sae tuna abubuwan da man ya mata take cikin qunci da qunar rae.
  Bata wani ci abincin sosai ba takai ta ajiye ta koma d'aki ta d'auki agwalima  tana son sha amma ta kasa sae kuka da ta soma yi.
  Tana cikin hkne ta jiyo sallamar inna tayi saurin share hawayenta ta fito ta tarbe ta tana mai yi mata sannu da zuwa.
  Daga haka ta juya zata koma d'aki inna tace"zo er albarka kiga tsarabar da nasiru ya kawo mana"
  Rynt ta saki murmushi tare da fad'in" hln yaushe ya dawo ne inna?
 Inna tace"ayyo ai tun da safe kina zuwa mkrnta ya dawo shine ma yakaini anguwa kuma yaje ya d'auko ni yanzu haka yana waje yana gaisawa shida wani  abokin sa"
 ta qarashe fad'in hk ne yayinda suka shigo
 d'aki ,
Rynt ta zauna gefen gado inna kuwa taje ta bud'e wardrobe ta ciro wata babbar leda takai kusa da Rynt dake zaune kan gefen gado ta ajiye snn ta shiga ciro kayan d'ai d'ai tana mai nunawa Rynt had'e da mata bayani.
  Atamfa ce mai kyau da turaren fesawa da kuma flat shoes, kyn inna knn na Rynt kuma less ne da turaren fesawa da kuma waya sabuwa fil cikin kwalinta.
  Sosai Rynt tayi farin ciki har bakinta ma  baya rufuwa nn nasir ya shigo tayi mae godiya sosai snn ta fita ta basu guri shida inna,taje d'aki sae tsallen murna take tayi waya.


Da dare malika ce taci kwalliya ta ftr rai ga wani irin qamshi da take zubawa ta saka wata rigar bacci da komai nata ana hangowa ,
taje kitchen ta had'a coffee ta zuba maganin da aka bata ta kuma zuba desire tablet snn ta nufi d'akin man ta same shi zaune kan bed yana wani aki da laptop d'inshi ta qarasa gurin shi cike da yanga ta zauna very close to him tare da kwantar da kanta akan kafad'ar shi takai d'ayan hannunta tana shafa bayanshi had'e da mishi sannu da aiki komai baice da ita ba,
 bata damu ba sae coffee ta miqa mae tace"my man ur coffee is ready,pls ka ajiye aikin nn kad'an sha ko"
 Ba tare da ya kalle ta ba yace"da wa kikayi zaki had'a mai coffee"

Sorry 4 dis one
Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2/15/2017]
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```













                🔮🔮🔮🔮
*```Page 53```*
Hannu takai ta juyo fuskar shi izuwa gareta ta wani marairai ce fuska kmr zatayi kuka sñn tace"my man a iya sani na ban maka wani  laifi ba amma sae naga kana min abubuwa kmr kana hukuntani akan wani  laifi da nayi,pls am beggin u ka gaya min idan har wani  laifi na ma a rashin sani wlh zan gyara zan kuma baka hqr akan koma mene ne ,kaji dan Allah ka gaya min kar kace zaka ci gaba da hukunta ni dmn wlh bazan iya jure fushin ka ba"ta qarashe mgnr cikin muryar kuka sosai.
   Yayinda man ke kallonta cikin yanayi na tausayawa nn ya kai hannu ya share mata hawayen da suka zubo mata kan fuska ya kuma rungumeta a hnkli yana mae bubbuga bayanta alamar rarrashi.
  Sae da suka d'an d'auki lokaci a haka snn malika ta d'ago tare da qara share hawayen fuskar ta tace"na baka coffeen zaka sha?
  Lumshe idonsa yayi had'e da gyad'a mata kai tayi murmushi tare da  kai kofin cofee a bakin shi ta shiga bashi da kanta har ya shanye tas snn ta ajiye cup had'e da rungume shi qam a jikinta tace"I luv u so much my man i luv u so much"
   Kmr da shakku ya shafo bayanta tare da fad'in "luv u more"
     Nan malika ta d'ago d'auke da murmushi a fuskar ta takai bakinta ta had'e da nashi tana mae abubuwa shima yana mata yayinda er mutan giro ta fito ta basu guri .
Nsn dae ta samu kanshi don ban sake jin wata hayaniya ba har washe gari kuwa.
  Na leqa na same su sae bacci suke rungume da juna.
   Man ne ya fara tashi ya yaye blanket d'inda suka rufa dashi zai sauka yaji malika ta riqe mae hannu tare da fad'in"my man meye hk ina zaka je?
 A hnkli ya duqa ya shafi gefen fuskarta snn yace "zanyi wanka ne"
  Tace"nima zanyi"
 Yace"ok to tashi muje"
 Ba musu ta yaye blanket d'in da shi kad'ae ne a jikinta akasin man da ya kasance yana sanye da farin boxer taje kan cinyoyinsa ta zauna tare ta riqo hanunsa ta d'aura kan qirjintq tana yawo dashi,
 a hnkli man ya janye hannun sa ya tafi dashi izuwa bayanta ita kuma ta kwanta kan qirjinsa tana shafa bayanshi kmr yanda yake mata.
Ta d'ago had'e da kai bakinta gefen wuyanshi  ta d'aura mai kiss tare da fad'in"thank u my man daren jiya ka faranta min sosai har ma naji kmr mu tabbata a hkn"
  Da murnushi ya d'aura mata kiss gefen wuyanta yace"me too tanks"
   Daga hk ya jata suka tafi bathroom basu suka fito ba sae da suka kwashe kusan awa d'aya.
   Da fitowar su malika taje kan dressing mirror ta d'auko man shafawa taja hannun Man suka je kan bed.
  Nan ta cire towel d'in jikinta ta yar snn takai hannu ta cirewa man nashi towel ba tare da ya hanata ba sae kallonta ma da yake.
   Ita ta fara d'ibar Vaseline tana shafa masa snn shima ya d'iba ya shiga shafa mata har suka gama shafawa juna ,
man ya tashi zuwa shiri ita kuma ta d'aura towel d'inta ta nufi d'akinta.


Har ya gama shirin sa tsaf malika bata dawo ba yaje falo yayi zaune yana mae juya wani abortion tablet dake hannun shi.
  Yana cikin hkne sae gata ta fito yayi saurin 6oye maganin ya tarbe ta d'auke da murmushi a fuskar shi.
  A nn sukayi break fast byn sun gama man ya tashi xai tafi d'aki sae kawae wnn abortion tablet d'in ya fad'i malika tayi saurin cewa my man abunka ya fa.... bata qarasa fad'a ba ta katse kanta tare da saurin sa qafa ta take maganin.
   Man ya juya tare da fad'in me kika ce?
 A d'an daburce tace"jeka kawae ba komai"
  Ya juya cikin wani  shu'umin murmushi dmn da sanin sa ya yadda maganin kuma yaga lokacin da tayi saurin sa qafa ta take maganin amma sae yayi kmr bae gani ba ya tafiyar shi.
  Malika na ganin ya fice tayi saurin d'aukar maganin tana kallo cike da mamakin ya akayi ya kawo nn bayan cikin dustbin tasan ta saka shi sae gashi ya fad'o daga kan seater nn dae ta basar tare da sauke ajiyar zuciya don a tunaninta man bae gani ba.


Shi kuwa man yana shiga d'aki makullin motar sa ya d'auko ya fita.

3:00pm
Rynt ce zaune akan bed tana waya da maman saliha da sabuwar wayarta wacce jiya kafin nasir ya tafi sae da ya nuna mata yanda ake aiki da ita ya kuma saka mata lamvar inna da tashi snn da ta maman saliha wato mhfyrshi.
   D'auke da murmushi Rynt ke waya da maman saliha har suka gama wayar.
  Tana gama wyr ta kai wyr kan bedside drawer ta tashi zata nufi bathroom sae kawae taga mohd  tsaye a bakin qofar d'akin nn kawae ta hau bakinta tana ihu tana kiran inna.
  A rud'e inna ta shigo d'akin tana tambayar Rynh lafiya?
  Rynt ta nuna mohd  dake tsaye tace"inna kice ya tafi bana son ganin shi"
  Inna ta kalli wanda ke tsaye d'auke da fuskar mamaki tace"ayyo ai wnn ba Muhammadu bane Aamil ne yanzu suka shigo shida Amir"
  Da mamaki Rynt tace"Aamil?
Inna tace "eh mana abokan haifuwar muhammadu yau da safe suka zo shine suka kawo min gaisuwa"
  A nn Rynt ta sadda kanta qasa tace da Aamil "dan Allah kayi hqr ban san bashi bane"
  A sukuikuice yace"no ba komai ai ni zan baki hqr nida na shigo maki d'aki hk kawae"
  Tace"ba komai"
Nan ya fita inna taja hannunta a cewar tazo su gaisa da Amir dake d'akinta.
   Bayan Rynt taje sun gaisa ta kama hanya zata koma d'akinta Aamil sae kallonta yake tayi har ta 6ace ma ganin sa snn daga baya ya kauda fuskar sa had'e da fitar da numfashi a hnkli.


Rynt kuwa tana Komawa d'aki sae safa da marwa ta shiga yi dmn sun sake dawo mata da kwankwanto a tsakanin su uku waye ya kashe mata mahaifi  tana cikin hkne sae kawae taje da sauri ta bud'e wardrobe ta d'auko ajiyar ta wato viva ledar ta da ta fito da ita qauye ta bud'e ta ciro wani tsadadden abin hannu na maza wanda ta same shi ne akan kud'in da aka jefo kan jikin Baffanta a lokacin da aka kad'e shi.
  Juya abun hannun take tayi tana tunanin taya zata gane mai shi a cikin su ukun.
     Gashi dae abun hannun yana da suna a jikin shi amma sam Rynt bata lura ba sae ma juya shi da take ci gaba dayi.
  Mohd ne ya fad'o d'akin Rynt tayi saurin  6oye hannunta dake riqe da abin hannun a cikin hjb tare da sadda kanta qasa dan ta d'auka Aamil ko Amir ne wanin su ya shigo"
  Mohd ya gane cewa bata fhmci waye shi ba dmn yasan Aamil da Amir na cikin gidan.

 Kallonta yake still kanta a qasa yayi guntun murmushi tare da qarasawa gurinta,
 Wacce tana d'ago fuskarta sae jin tayi ya had'e bakinta da nashi a rud'e tayi saurin fizge kanta tana kallon sa da mugun mamaki,yayinda shi kuma ya saki shu'umin murmushi tare da fad'in"don't be surprise mijinki ne mohd wnn alama ce da zan riqa maki idan na shigo gidan nn sbd ki riqa fhmtar waye ni a cikin mu uku hope getit?
  Nan ta bud'e baki zata mai ihu yayi saurin jawota ya had'e bakin sa da nata wnn karon bata iya qwace kanta ba dmn wani salo na daban ne yake matà da har tsayuwa ta nemi ta gagareta sae qoqarin zubewa qasa take, binta mohd yayi suka zube qasa inda still bakinsa na kan nata yaqi ya zare sae can ya zare bakinsa Rynt tayi saurin matsawa baya had'e da kallon shi sae kuma tayi saurin kauda fuskarta tana sauke numfashi yayinda ta kai hannu tana share lips d'inta.
    Bata ce dashi komai ba sae yunqurin tashi tsaye take cike da niyar tana tashi ihu zata fasa mai,hk ko akayi don tana tashi tsaye ta bud'e baki ta fasa ihu ,ihun bae fita ba don sae jin bakinta tayi cikin na mohd.
  kuka ta shiga yi tana dukanshi sbd wnn karon cikin mugunta yake tsutsar lips d'inta.
   Sae da ya zare bakinsa snn ya riqe hannuwanta da take fmn dukan shi dasu ya matse ta sosai a qirjin sa had'e da kai bakinsa saitin kunnen ta yace"wlh duk kika sake yunqurin yimin ihu sae na miki wanda yafi wnn zafi don har jini sae na fitar miki dashi"
  Kuka Rynt keyi sosai gashi taso qwatar kanta amma man sae qara matse ta a qirjin sa yake gashi tana jin zafin matsar sosai shiyasa ta hqr ta daina yunqurin qwatar kanta sae kuka da taci gaba dayi"
  A nn man ya shiga sassauta riqonda ya mata ya d'ago fuskarta yana kallonta, hawaye sae wasar tsera suke akan kumatunta,
 bae share mata hawayen ba sae tsinin hancinsa ya d'aura akan nata nn Rynt ta qara fashewa da wani sabon kuka don ta d'auka ko hkn da yayi zai sake had'e bakin su ne,bata ji ya had'e bakin su ba sae wani  iska mae sanyin dad'i da taji yana sauka kan lips d'inta nn ta lumshe idonta a hnkli tana mae ci gaba da sauraren yanda iskan ke sauka a hnkli kan lips d'inta.
  Mohd dake hura mata iskan bakin shi ya d'ago a hnkli yana mai kallon yanda ta rufe idonta sae ta mai kyau sosai har dae yanda eyelashes d'inta sukayi zara zara.
Ita kuwa Rynt  jin iskan ya daina saukar mata yasa ta shiga bud'e idonta a hnkli har ta ware su a cikin idanun mohd,ta kauda fuskarta gefe yayinda man ya maida ta kan qirjin sa ya kwantar.
  Yana jin zata fizge kanta yayi saurin cewa"um um bana so natsuwar ki nake so dmn zan tambaye ki ne idan kin gaya min gskyr amsa zan barki na tafi idan kumà kika min qarya ko kika min tsiwa ina nn dake har safe ba inda zanje.
   Bata ce komai ba ya ci gaba da cewa ina son ki gaya min dalilin da yasa kika sakawa malika magani a abinci.
 Tayi saurin d'agowa ta kalle shi cike da niyyar masa tsiwa se mohd ya girgiza kansa a hnkli alamar kar ta mae ,sae kuwa ta sadda kanta qasa tace"ni ba abinda na sa mata a abinci idan har ma ce maka tayi to qarya ta ma"
  Yace"idan kin 6oye min?
 Bazan 6oye wa ubangiji na ba.
Ya sauke numfashi yace"to meyasa kika ce mata zata gani a lokacinda zaki je girka mata abinci har kika bangaje ta kika wuce"
  Cikin natsuwa tace"tsarine kawae irin nata dmn ni ba abinda nace mata a lokacinda muka had'u haka kuma ni bansan na bangaje ta ba"
  Mohd dake kallonta yayi shiru sae can yace"to kina son ki koma gidana?
  Tayi saurin girgiza kanta tana mae wani  kallo na tsana snn daga bisani tace"Allah sauwaqe wlh bana so"
  Yace"to ni ina so kuma sae kin koma don na riga da na maida auren mu tun ba yau ba"
 Tace"kayi a banza don wlh ba inda zan koma"
 yace"dolenki ki koma ko don cikina dake jikin ki"
  Wnn karon fizge kanta tayi daga jikin shi tare da fad'in"ka ma cire ranka a wnn cikin dmn wlh zubar dashi zanyi don ba abinda zanyi da qaddararren abu a jikina"
 Ta fad'i hnke tare da bud'e wardrobe zata saka abin hannun da take ta fmn 6oyo a hannunta bata so ya gani.
  Mohd da ya fusata kan jin zancenta ya kama murfin wardrobe d'inda ta bud'e ya rufe da qarfi.
Nn Rynt ta fasa wani  irin ihu dmn da yatsanta ya had'a ya rufe bae sani ba.
 Kan kace me sae ga su inna da gudu sun shigo ita da su Aamil da Amir har ma da Baaba hurera.
   Rynt dake riqe da yatsanta ta tafi da gudu jikin inna tana kuka yayinda man ya biyota a rud'e zai kama hannun ya gani.  A fusace inna ta buge mai hannu had'e da kai masa wani irin gigitaccen mari ta kuma rufe ido tace"wlh maza fita a gidan nn in daina ganin ka kafin na bud'e idona!
  Ba musu man dake dafe da kunce  ya fita ya bar gidan yayinda en uwanshi suka shiga mamaki sosai.


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2/18, 10:06 PM] ‪+234 816 124 4732‬: [ 2/16/2017]
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```













                🔮🔮🔮🔮
*```Page 54```*
Da fitar sa Inna ta kai hannu ta riqo hannun Rynt ta duba yatsar ,yatsar tayi jajir ga kuma jini da ya taru ya kwanta akan jikin qunba.
  Cikin tausayi inna tace"garin ya hk ta faru?
 Rynt bata iya cewa komai ba sae kuka da take tana yarfi da hannu.
  Nan Inna ta ja hannunta suka je d'aki yayinda Amir da Aamil suka bi bayan su, Baaba Hurera kuwa kitchen ta koma dmn qarasa aikinta.
  Bayan sun shiga d'aki ne inna ta zaunar da Rynt gefen gado snn ta kalli su Amir da suka nemi guri kan sofa suka zauna
Tace"d'ayan ku yazo ya duba mata yatsar ko da akwai maganin da za'a siyo mata tasha"
   Aamil ne ya taso ya duba yatsar yaje da kanshi ya bud'e fridge ya ciro freshmilk ya tsiyaya a cup snn ya koma gun Rynt ya ciro farin handkerchief ya bata a cewar ta share hawayena ta,
  Rynt bata kar6a ba sae cewa tayi"Aa nagode"
snn takai hannu ta share hawayen fuskarta .
Aamil dake kallonta ya bata fresh milk ta kar6a tasha kad'an ta bashi yaje ya ajiye  ya kuma fita a cewar zai je ya siyo mata magani ya dawo.
   Inna tace"to d'an Albarka a  dawo lfy"
snn ta kama yatsar Rynt tana qara dubawa tace"shashashan yaro wae me ya daka miki a yatsar ne to don nsn ba makawa shine yaji maki ciwo"
 A sanyaye Rynt tace"haka kawae ina bud'e wardrobe ya maida murfin da qarfi shine murfin ya daki yatsana"
   Inna tace"kaji macucin yaro Allah zai isar miki ai yanzu kiran ubansa kabiru zanyi......
 Yunqurin aman da Rynt ta shiga yi ne ya katse inna,
 Rynt kuwa ta kwasa aguje sae bathroom tana ta kwara amae ta samu da qyar ya tsaya mata inna dake gefenta ta bata ruwa ta kuskure bakinta snn ta riqo hannunta suka fito taje da ita gefen gado ta zaunar tare da fad'in"sannu kinji"
  Rynt ta gyad'a kanta tare da fad'in"inna zan sha agwalima"
   Nan inna taje ta bud'e fridge ta d'auko mata sae ga Aamil ya shigo d'akin riqe da ledar magani a hannun shi yana waya.
  Bayan ya gama wayar ne ya ba inna ledar maganin yace"kowanne d'ad'd'aya zata sha"
  Inna ta kar6i ledar tace"to d'an Albarka sannu kaaji"
  Aamil bai ce komai ba sae duban sa yakai gun Amir dake kishingid'e abinshi kan sofa yana ta aikin fmn dannar waya  yace"tashi muje gida Abba ke son ganin mu"
   Ba musu Amir ya tashi sukayi wa inna sallama suka tafi.
    Sae a snn Rynt ta kar6i agwalima a hannun inna,inna tace"anya kinci abinci kuwa Rynh?
 Rynt tace"Aa inna dama ina so zan sha fura ne"
  Inna ta girgiza kai bata dae ce komai ba taje ta d'ebo mata furar, Rynt ta kar6a tare da ajiye agwalimar hannun ta da ta fara sha ta shiga shan furar yayinda inna ta 6alla magungunan da Aamil ya siyo ta ba Rynt ta had'iye had'e da furar da take sha.
    Koda ta kammala shan furar inna ta shiga bathroom dmn yin arwalar sallar la'asar nn ita ma ta tashi taje d'aki wacce da shigarta d'aki tayi kici6is da abin hannun da ta tayar tayi saurin kai hannu ta d'auka taje ta 6oye snn ta tafi bathroom tayi arwala ta fito tayi sallah.


 5:00pm
Man ne kishingid'e kan resting chair a cikin garden idanuwan sa a rufe kmr mai bacci.
  Sae ga Amir ya shigo gurin d'auke da sallama ya nemi guri ya zauna yana mai kallon man da ya amsa mae sallama had'e da yunqurin tashi zaune cikin yanayi na kmr mara lafiya musamman launin idanuwansa da suka sauya zuwa ja.
   Ya zauna yana mae kallon Amir  yace"ya akayi kasan ina nn ne?
 Amir yace"gateman ya snr dani bcs nayi kiran phone d'inka yafi a qirka baka yi picking ba"
  Cikin damuwa man yayi d'an guntun tsaki snn yace"sorry na bar phone d'ina a mota ne"
 Amir yace"No vex,but  me yake faruwa tsakanin ka da inna ne haka?
  Shiru man yayi sae can ya shiga snr da Amir abinda ya faru.
  Amir ya sauke ajiyar zuciya
 yace"to meyasa ka saki yarinya kuma kazo kana bibiyarta?
  Man yace"Ina son maida ta ne"
  Amir yace"kan me?
 Yace"wato Amir sae bayan komai ya gama faruwa na fhmci cewa abinda nake zarginta dashi bata da hannu a ciki,it seems malika ce ta aikata hkn sbd kawae ta samu yrnr ta bar gidan"
  Amir yace"ta yaya ka fhmci haka?
  Man yace"waya na samu tana yi sae dae ban samu naji komai da suke cewa ba amma still ina kan bincikena da zan ga cewa na kama malika red handed.
   But abinda na fiso farko shine na samu na maida wnn yarinyr sbd cikin da ke jikinta nafi son ta raine shi a gabana dmn nima na samu na bashi kulawar da nake so"
 Amir yace"kaje ka bawa Abba haquri  mana ko zai barka ka maida ta "
 No Amir kasan da kamar wuya Abba ya barni na maida ta amma nasan tabbas idan itace ta nuna tana son ta dawo ba makawa Abba zai barta,amma sae gashi ita sam bata son dawowa"
  Amir yace"meyasa ko tana fushi akan abinda ka mata ne?
Mohd yace"Aa dama fa yarinyar ba sona take ba ta amince da aure na ne sbd biyayya wa Abba,kaga kuwa dole Abba yaji zafi ace wacce ba er sa ba ma ta mai biyayya amma nida nake d'a a gurin shi ban mae ba dmn duk a tunanin sa na sake ta ne kan bana son ta bai yarda cewa laifi tamin ba.
  Amir ya numfasa snn yace"kaga bari kawae zanje gun Abba na bashi haquri.....kai wae ka manta waye Abba wlh in kaje ma ka qara min laifi kawae abinda nake so dakai yanzu ka tashi kaje gun inna kafin ta kira Abba ta sanar dashi cewa naje gidan, ka bata hqr kar ta kirashi don in yaji naje gidan zai qara ganin na mai wata rashin d'a'ar ne tunda ya hanani zuwa gidan amma naje"
  Amir yace"ai kayi letti don tun kafin mu baro gidan naji tace zata kirashi ta snr dashi"
 No bata kira shi ba dmn da ya kirani ya min fad'a,
Amir yace" Ina fa zaka sani wayar ka na a mota"
  Man yayi guntun tsaki yace"hkne fa, but muje naga idan bae kirani ba sae kaje ka bata hqrn.
 Nan suka fito zuwa parking lot man ya nufi motar shi ya bud'e ya d'auko wayar shi ya duba miscalls ba na Abban su a ciki,ya kalli Amir yace"inaga bata snr dashi ba don bae kirani ba"
   Amir yace"ok bari naje d'in"
Nn ya shiga motar shi yaja ya tafi ,man kuwa wayar sa ce tayi qara koda ya duba malika ce bai yi mamakin ganin kiran ba sbd yasan bata san cewa yana cikin gidan ba dmn koda ya shigo gidan 6acin ran marin da inna ta mae bai bar ya shiga cikin gida ba sae garden da ya nufa.
  Wanda ko yanzu niyyar sa ya koma garden amma ganin kiranta yasa ya nufi cikin gidan.

Guraren qarfe tara da rabi na dare Rynt ce kwance  tana bacci sae ga man ya shigo d'akin yaje a hankali ya zauna gefen gadon yana mai kallon fuskarta snn ya kai duban sa gun yatsar ta da ya jiwa ciwo.
  Yakai  hannu ya riqo yatsar yana dubawa wanda yana d'aura yatsar sa akan kunbarta sae kuwa ta tashi firgigit had'e da yarfi da hannu tana kallon shi kmr zata yi kuka.



Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2/18, 10:06 PM] ‪+234 816 124 4732‬: [ 2/17/2017]
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```











_Mommy Ameena n Nafisat nagode sosai akan qaunarku a gare ni nayi matuqar farin ciki da samun saqon ku nagode!nagode!nagode! haka ma dukkan masoyana ina miqa saqon godiyata a gareku masu kirana har ma wad'anda basa kirana duk na gaida ku, n Luv u all❤_

                🔮🔮🔮🔮
*```Page 55```*
Da sauri ta sauka kan gadon tana mae ci gaba da kallon shi.  man kuwa ya tashi yaje gab da ita tare da jawota zuwa qirjin sa yana kallon d'an qaramin bakinta da yake qoqarin kai nashi akai ,
Rynt ta kauda fuskarta da sauri tace"um um bana so dan Allah kar ka min"
   Bai mata ba d'in sae kumatun ta da ya riqo yana kallonta yace"kin gane ni knn"
  Komai bata ce masa ba sae kallon sa da take shaye da toka tana yunqurin qwatar kanta tace"wlh ka sake ni ko yanzu na ma ihu"
ya riqo yatsar ta mai ciwo yace"kina min ihu zan matse yatsar nn ne sae kiyi ihu da dalili"
      Bata kula shi ba sae yatsar ta taje zuwa fixgewa ya matse yatsar zata  fasa ihu knn yasa hannunsa ya rufe mata baki yana mai kallon idanuwanta da suka ciko tap da qwallah, yace"duba ki kawae nazo yi amma tsiwar ki tasa na ji maki ciwo"
 Ya fad'i hkne tare da janye hannunsa akan bakinta da ya rufe ,snn yakai hannun kan cikinta ya d'aura yana shafawa,
  Rynt dake kuka riqe da yatsar ta sae ture hannun tayi ta fizge jikinta daga nashi ta kuma matsa nesa dashi.
  Man ya tafi zai je gurinta ta fashe mae da kuka tace"wlh duk kazo sae na ma ihu sae dae ka kashe ni"
   Ya tsaya cak yana kallonta snn yace"yi hqr kinji babyna kawae zan duba se na tafi"
   Ta maqale kafad'a had'e da qara ja baya,ya kalle ta kawae yace"shike nn na tafi sae da safe"
   Nan ya kama hnya ya fita d'akin.
 Rynt da ta bishi da kallo shaye da toka ta share hawayen fuskarta snn ta fito taje d'akin inna zuwa bacci don dama daga kawae ta kwanta zata d'an huta ne bacci yayi awon gaba da ita.

 Washe gari ta fito cikin shirinta na zuwa school sae sauri take dan ta soma makara amma koda ta fito bata samu drivern ta yazo ba sae wata had'ad'd'iyar farar mota ta gani fake a qofar gidan.
  Bata bar ta ga wanda ke ciki ba sae dube dube ta shiga yi ko zata hango 6ullowar motar drivern ta.
   Man dake cikin farar motar yana hango  yanda Rynt ta jima tsaye tana faman dube dube wanda yasan jiran banza take don drivern nata yazo yace da drivern ya tafi abinshi shi zai kaita.
  Gudun kar ya sata tayi letti ya bud'e gambun motar ya fito  wanda har ya qaraso gurinta kallon shi take shima yana kallon ta,
 bata gane cewa man bane haka shima bae nuna mata shine ba sae ma ina kwana da yayi mata.
  Jin ya mata ina kwana yasa ta sadda kanta qasa had'e da mishi ina kwana.
  Yace"lafiya lau,school zaki tafi ne?
  Tace"eh"
Yace"taxi kk nema?
 Tace"Aa mai kaini school nake jiran yazo"
   Agogon hannun sa ya duba snn yace"muje na sauke ki"
  Tace"Aa idan sauri kake ka tafi kawae zan nemi napep"
  Yace"no muje kawae"
  Ba musu tabi shi suka je suka shiga mota a nn ya tambaye ta sunan mrntar su da kuma anguwar da makarantar tasu take, ta gaya mai snn yaja motar suka tafi.
    Cikin mota sukayi shiru ba mae ce ma wani har suka isa  mkrntar,
 Rynt tayi mae godiya snn ta bud'e gambun  mota ta fita.
  Mami ya hango taje da gudu ta rungume Rynt yayinda Rynt ta riqa hannun mami d'auke da murmushi a fuskar ta taja ta suka shiga makarantar.
  Sae a snn yaja motar sa ya tafi wanda bai zarce koina ba sae gida.

Ya nufi d'akinsa ya sami malika kwance  kmr yanda ya barta sae bacci take.
  Kayan jikin sa ya rage yaje yayi kwance kan sofa  yana tunanin hanyar da zai bi ya dawo da Rynt gidan shi.
  Ya jima kwance a cikin tunanin sae wayar sa ta shiga ruri koda ya duba Aamil ne mai kiran ya d'aga wayar.
bayan ya gama wayar ne yaje ya tashi malika wacce ta tashi cikin yanayi na wacce bacci bae isa ba sae miqa take tana kallon shi.
  Yace"tashi zaki yi baqi ne to 12"
  Tace"su waye zasu zo?
Tsaki yayi yace"kinga ki tashi idan zaki tashi dole sae kinji ko su waye zasu zo"
  Tace"me kuma yayi zafi my man daga tambaya"
  Nan ta sauko kan gadon had'e da zowa gab dashi ta riqo kumatunsa tace"waya 6ata min ranka da safen nn pls koma waye kayi hqr ka gaya min su waye zasu zo don ya kamata na sani"
  A hnkli ya janye hannuwanta da ta d'aura kan fuskar shi snn yace" su Aamil ne zasu zo tare da matan su"
   Tayi murmushi tace"ok bari naje nayi wanka se nasa kuku ya girka musu kalolin abinci"
    Bai ce komai ba sae kan sofa da yaje ya kwanta ita kuma taje ta shiga bathroom.


12:00
Sae kuwa ga su Aamil sun shigo gidan tare da kyakkywa matan su farare  tas da kuma 'ya'yansu.
  Matar Amir janye take da hannun d'anta kyakkywa d'an shekara uku mai kyau dashi.
Matar Aamil kuwa mace ce riqe a hannunta er 3yrs mai kama da ita sak .

Man suka tarar a falo wanda ya gaisa dasu cikin sakin fuska snn yaje ya kira musu malika da itama tazo ta tarbe su cikin murna da nuna farin cikin zuwansu.

 Bayan sunci sun sha ne man yaja yaran ya tafi dasu shopping complex ya siyo musu kayan tand'e tand'e da na wasa suka dawo gidan sae murna suke suna wasa da abubuwan da aka siyo musu na wasa yayinda kowannen su ke riqe da giant lollipop suna sha.
 Iyayen su kuwa suna nn zaune a falon sae fira ake tayi cike da nishad'i.
Basu suka bar gidan ba sae 4 suka nufi gidan inna.

Suna shiga gidan suka had'u da Rynt ta fito lesson teacher d'inta yazo zata fita.
  Ba yabo ba fallasa suka gaisa da juna sae kallon yaran su take da sukayi matuqar bata sha'awa amma hkn bai sa taji kwad'ayin barin cikin dake jikinta ba.

Bayan ta dawo daga lesson ne taja yaran suka je suna ta wasa har da su wasan 6uya da guje guje,inna kuwa nacan d'aki ita da baqinta.

Sae qarfe 9 na dare suka bar gidan Rynt taji kmr kar yaran su tafi dmn akwaita da son yara sosai shiyasa duk ta had'u da yaro zata biye mae suyi ta wasa.


  Washe gari koda ta tashi tana d'an jin kanta ba d'adi bata bar inna ta fahimta ba har tayi shirin ta na makaranta ta tafi.

A can makaranta ciwon yayi mata but har ma zaman class ya gagare ta sae clinic taje ta kwanta.

Da aka tashi da qyar ta iya kai kanta gate wacce a maimakon taga drivernta sae man ta gani yazo zae ja hannunta su tafi tayi saurin matsawa baya wacce garin hkne taje zuwa fad'uwa yayin saurin riqo hannunta a nn yaji jikinta da mugun zafi.
  Cikin damuwa ya kalleta yace"baki da lafiya ne?
  Bata bashi amsa sae hannunta ta fizge taje zuwa siyen agwalimar da ta hango ,
man dake biye da ita shi ya biya kud'in agwalimar ya kuma kar6i ledar agwalimar  sbd qin kar6a tayi a cewar bata son agwalimar tunda shi ya biya kud'in.

Bai damu ba sae hannunta yaja sbd ya fhmci sosai take jin jiki wacce ba yanda bata yi ba na ganin ta fizge hannunta amma ta kasa har yaje ya saka ta mota yaja ya tafi da ita sae zuwa asibitir shi.

 Bayan sun iso ne yayi yayi ta fito mota taqi wae sae dae ya kaita gida shi kuwa yace sae ya dubata ko yana kaita.
 Suna cikin hakane  amai ya qwace mata a nn cikin motar sae kwara shi take tayi duk tabi ta 6ata uniform d'in jikinta har motar.
   Bai damu da ganin motar shi ta lallace ba sae ta kanta yake dan duk ta galabaita sae numfashi da take fitarwa.
  Haka ya d'auke ta ya tafi da ita sae office d'inshi yakai  ta bathroom zai cire mata uniform d'inta da suka 6aci ta hanashi sae kuka take ita ya kaita  gida.
 Nan ya shiga lallashinta a cewar ta cire uniform d'in ta wanke jikinta se ya siyo mata wasu kayan tasa snn ya maida ta gida.
  Bata yarda da hakan ba sae da qyar ya samu ta yarda snn ya fita bathroom d'in ya barta yaje ya siyo mata arabian gown ya dawo.
  Wanda ya jima zaune yana zaman jiran fitowarta bathroom amma yaji shiru hkn yasa yaje ya mata knocking yaji shiru kamar ma ba kowa a ciki.
  Nan ya shiga bathroom d'in yayi tsaye turus yana kallonta kwance  qasan tiles d'in tana ta bacci daga ita sae  vest da bum short ta jefar da uniform d'inda ta cire gefe.
  A hnkli yakai hannu ya d'auko ta ya fito da ita ya kwantar kan sofa yakai hannu yana ta6a jikinta da har yanzu mugun zafi ne dashi.
 Nan ya tashi ya nemo  ruwa a d'an silver bowl yazo ya gurfana gab da ita had'e da ciro farin handkerchief a aljihunsa ya sanya shi a cikin ruwan snn yakai  hannu ya yaye mata vest d'in jikinta ya ciro handkerchief d'inda ya saka a ruwa ya matse ya shiga daddanna mata jikinta tun daga kan goshinta qirjinta har izuwa cikinta yayinda yake yi yana qara saka handkerchief d'in a ruwa yana matsewa har ya samu jikin nata ya rage zafi sosai.
    Rynt dake bacci sae taji jikin nata ya mata dad'i har da su gyara kwanciya zuwa ruf da ciki man yayi tsaye kawae yana kallonta kamar ya gyara mata kwanciyar yake ji amma kuma baya son ya tashe ta baccin bae isheta ba hkn yasa ya cire suit jacket d'in jikin sa ya rufe mata jikinta snn yaje yayi zaune kan kujerar sa mae shillo yana jiran farkawarta.




Billy Giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```













                🔮🔮🔮🔮
*```Page 56```*
Tayi kusan awa d'aya tana bacci yayinda man ke fmn wani aiki da laptop da hanklinsa ya tafi gabad'aya a gurin.
  A nn Rynt ta shiga motsi tana juyi wacce duk a tunanin ta kan bed take bata ankara ba sae jin kanta tayi  qasa tumus.
  Man da duk ya tsunduma cikin aikin da yake sae jin qarar ta yayi.
Yayi saurin ajiye aikinda yake yaje gareta bata bar ya ta6a ta ba tayi saurin matsawa baya cikin jin haushin ganin bata tare da vest d'in  jikinta sae jacket da ta samu a jikin nata.
   Cikin muryar kuka sosai tace"wlh Allah ya isana daka ganar min jiki uhm uhm"
   Man dake kallonta
bai ce komai ba sae tashi yayi yaje ya bud'e fridge ya tsiyayo mata fresh milk a glass cup ya kawo mata had'e da magunguna,
 bata kar6a ba sae ma buge cup d'in da tayi ya fad'i qasa ya fashe.
   Kallonta man yayi snn yakai  dubansa gun 6arnar da tayi yaje yayi zaune kan kujerar sa yana ci gaba da aikin shi.
    Rynt kuwa tashi tayi ta nufi bathroom sae gata ta dawo sanye da arabian gown d'inda ya siyo mata wacce ta same ta ne cikin leda  ajiye a bakin qofar bathroom .
  Koda ta fito riqe take da ledar da ta cire arabian gown kasancewar uniform d'inta da ta saka a ciki.
  Ta kama hanya ba tare da ta ko kalli gefen da yake zaune ba ta nufi qofa zata bud'e taji ta gam a rufe.
  Sae a snn ta kalle shi tace"ni kazo ka bud'e qofa na tafi gida"
  Banza yayi da ita yaci gaba da aikin shi.
  Rai 6ace tace"kana jina fa"
Still bae kula ta ba yaci gaba da aikin shi .
  A fusace taje zata ture laptop d'inda yake aiki da ita ya tashi had'e da riqe mata hannu cikin mugun hasala yana kallonta.
  Sosai ta tsorata da ganin yanayinsa ta shiga ja baya tana son fizge hannunta ,
shi kuma yana biye da ita riqe da hannun nata da yayi wa muguwar damqa.
  Da haka har suka kai jikin gina Rynt ta kalle shi le6ace da baki zuwa kuka tace"dan Allah kar ka daken"
   Yace"wlh ba don cikin da ke jikin ki ba da yau sae na ladabda taki ta yanda ko wani kika ga zai min renin wayo zaki hana shi"
 Tace"nidae yi hqr ka bud'e min qofa na tafi"
Yace"ba inda zaki je sae kin kwashe 6arnar da kikayi ki kuma goge gurin tas"
  Kallon gurin tayi shaye da toka tace"nifa bana jin dad'i kasàni kuma bana son ayi la'asar banyi zuhur ba"

 Yace"bana son raini je kiyi abinda nace"
   ya fad'i hkne tare da sake mata hannun da ya jima damqe dashi.
   A nn Rynt ta turo baki ta kalle shi shaye da toka tana murza hannunta cike da jin zafin damqar da ya mata.
 Ya kalle ta kawae ya tafi yaje ya zauna kan kujerar sa mai shillo ya  jingina bayan sa akai had'e da lumshe ido.
  Rynt kuwa tana  nn tsaye inda ya barta ba alamar zata je ta gyra gurin sae ma wani  kallo take masa mai d'auke da harara bako qyaftawa yayinda take ci gaba da murzar hannunta a hnkli.
   Man da yaji a jikin sa tana kallonshi ya bud'e idon shi a hnkli yana kallonta ita kuma ta kauda fuskarta gefe shaye da toka.
  A nn jinginen da yake yace"idan kika qara ko minti biyu tsaye a gurin ko wlh zan fita na barki na kuma rufe office d'in dake ba kuma zan dawo ba sae gobe idan kuma kin musa ki qara minti biyu tsaye a gurin ki ga"

Sanin zai iya abinda ya fad'a yasa Rynt taje rae 6ace tana gyra gurin wacce tana cikin gyara gurin ne jiri ya d'ebeta ta fad'i.
Bata ga tasowar man ba sae ganin kanta tayi rungume a qirjin sa yana fad'in"baki ji ciwo ba?
  Girgiza kanta tayi tare da kai hannu ta dafe cikinta cike da son tayi kuka.
  Yayi saurin  janye hannunta ya d'aura nashi akai snn ya kalleta a rud'e yana fad'in"me ya faru da cikin ne?
  Cikin muryar kuka tace"yunwa nake ji"
  Ajiyar zuciya ya sauke yakai  hannu yana share mata hawayen da suka gangaro kan fuskarta snn ya tashi tare da fad'in"ina zuwa kinji"
  Tace"nifa bazan tsaya cin komai ba kawae ka maida ni gida"
   Bai kula ta ba se  fridge ya nufa ya bud'e ya ciro hollandia yogurt ya had'o da cup yazo gurinta ya zauna ya tsiyaya ya bata taqi kar6a sae kallon shi tayi ta bud'e baki zata yi magana sae kawae ta sami kanta da jin hollandia yogurt na shiga a cikin bakinta.
   A hnkli ta ture kofin tare da share bakinta tana mae kallon shi kmr yanda yake kallonta.
 Ta yunqura zata tashi ya maida ta zaune yace" sha ko kad'an ne sae na maida ki gida kinji yi hqr"
   Rynt da still kallon sa take se ta sami kanta da kasa masa musu ta kar6a ta sha har kusan rabin cup d'in snn ta ajiye.
   A nn ya 6alla mata magunguna ya bata ta kar6a ta kora da sauran hollandia yogurt d'inda ta ajiye.
    Bayan ta gama ne suka fito suka shiga mota Rynt sae kallon motar take kmr ba ita ce ta 6ata da amae ba an gyara komai tsaf sae ma qamshi da take.
 Yana jan motar ta jingina bayanta kan seat ta rufe idanuwanta a hnkli man dake tuqi sae yi yake yana kallonta ya rasa meyasa duk ta rufe idonta wani  irin kyau take mae.
  Rynt ba ita ta bud'e idonta ba sae da taji motar ta tsaya snn ta bud'e idonta a hnkli ta sami idon man akanta bata damu ba sae dubanta takai seats d'in baya ta jawo school bag d'inta ta bud'e ta ciro kud'i ta miqa mae tare da fad'in"bani agwalima ta ga kud'in ka"
  Ba musu ya kar6i kud'in yasa aljihu ita kuwa ta jawo ledar agwalima dake seat d'in baya ta saka a cikin jakarta snn  ta fita shi kuma yaja motar ya tafi.

 Ta shiga gidan cike da tunanin me zata ce ma inna don tasan dole inna ta shiga rud'un rashin dawowarta akan lokaci .

 Da tunanin haka ne ta qarasa ciki bata sami kowa a falo ba ta wuce sae d'akin inna ta sami inna sae bacci take nn ta fito taje d'akinta wacce da shigarta ta nufi bathroom tayi arwala ta fito tayi sllr zuhur tana idarwa aka shiga kiran sllr la'asar nn ta tashi tayi la'asar d'in bayan ta idar  taje d'akin inna da niyyar tashin ta tayi sallah  sae ta samu inna ta tashi har ma ta d'auro arwala zata shimfid'a dardumar sallah,bata shimfid'a ba sae  kallon Rynt
tayi tace"Rynh an dawo?
  Tace"eh inna"
 Inna ta shimfid'a dardumar tana fad'in "kunyi sa'a yau sun tashe ku da wuri knn dan naga biyar bata ko yi ba yanzu ma ake la'asar"
  Rynt tayi shiru kawae don ta fhmci inna ta manta yau alhamis da wuri suke tashi.
 Inna ta katse ta da cewa"da ganin ki kin kwaso yunwa je d'ebo abinci kici kafin mae miki darasi yazo"
  Rynt tace"to"snn ta fita taje kitchen ta d'ebo abinci ta tsaya nn falo sae ci take sauri sauri don tasan mae lesson d'in nata na hanya.

Bayan ta kammala cin abinci ne har mae lesson d'in nata yazo ya tafi.
   Ta fito d'akinta sae waya take tana dariya ta nufi d'akin inna ta bawa inna wayar a cewar mami ce,inna ta kar6i wayar washe da baki ta kara a kunnenta wacce har ta gama wayar d'auke da nishad'i a fuskarta.
  Ta bawa Rynt waya tare da fad'in "mami iyayen surutu haka kike ta fama da ita a makaranta idan kun had'u ko?
  Rynt tace"hkne inna,shiyasa qawata Sarah ke sonta sosai sbd itama srtn ne da ita"
Rynt na gama fad'ar hakane sae ga nasir ya fad'o d'akin had'e da sallama a bakinshi.
  Inna ce ta amsa sallamar Rynt kuwa ta gaida shi ya amsa fuskar sa a sake tare da kallon wyrta dake hannunta ya kar6a yana fad'in"inace bata baki matsala ko?
 Kanta ta girgiza had'e da fad'in "a'a"
  Yace"katin da ke ciki fa ya qare ko kuwa?
  Tace"bai qare ba da saura"
Bai ce komai ba sae hannunsa yasa a aljihu ya ciro katin d'ari hud'u ya had'a da wayarta ya bata tare da fad'in"to gashi idan wnn ta qare sae ki saka wnn ko?
  Ta kar6a sae godiya take mai snn ta fita yayinda take jin inna na qara yimae godiya had'e da tambayar sa lafiyar d'anshi da kuma matar sa.
 Yace "duk suna lafiya"
Da haka bata sake jiyo me suke cewa ba ta shiga d'akinta.

Washe gari tun da sassafe ta fito daga gurin wanka knn d'aure da towel sae ga man ya fad'o dakin nata tayi saurin komawa bathroom shi kuma yaje ya ajiye wata leda kan bed ya fita .
 Nan Rynt ta fito taje ta bud'e ledar dan ganin mene ne.
 Uniform d'inta ne an wanke su an goge sae qamshi ke tashi.
 Kallon kayan Rynt keyi don gabad'aya bata san cewa ta manta kayan ba sae yanzu .
nn ta sauke ajiyar zuciya had'e da murmushi ta kai hannu a hnkli ta d'auki en canjin da ta samu akai wato kud'in agwalimar da ta bashi sune ya mayar mata.
  Ta ajiye kud'in had'e da kar6a kiran da taji inna na qwala mata.
  Bata kai ga fitowa d'akin ba sae ga inna ta sameta riqe da waya tana fad'in"kin bar wayarki sae fmn kiranki ake tayi har takae ga tsinkewa.
  Rynt ta kar6i wayar knn aka sake kira ta d'aga wayar yayinda inna ta fita tabar d'akin

 Bayan Rynt ta d'aga wayar ne take cewa"eh sarah naji sauqi har ma gani ina shirin zuwa school, ok to sae mun had'u ki gaida su umma"
  Daga haka suka  katse wayar ta d'auki uniform d'inta taje zuwa shiri.

Bayan ta gama shiri ne taje d'akin inna ta samu inna ta had'a mata abin kari tayi zaune taci da ta gama ta tashi taje ta bud'e fridge tasha ruwa snn ta d'ebi agwalima ta zuba a jakarta kafin inna ke bata kud'in breakfast ta kar6a had'e da godiya snn ta fita.
  Da fitarta ta qofar gida drivern nata ya iso taje zata shiga motor sae kawae taji an riqe mata hannu.
  Koda ta juya mohd ne ya kalle ta yace"ina kwana"
  Bata amsa mae ba sae hannunta ta zame a hnkli daga nashi.
   Bai damu ba sae hannunsa ya d'aura kan goshinta yace"ya jikin?
  Ta janye hannun tare da fad'in"Alhmdlh"
 Daga haka ta juyawarta ta shiga mota shi kuma ya saka hannyensa a aljihu yayi tsaye yana kallon su har suka tafi.
  Snn ya sauke ajiyar zuciya yaje ya shiga mota ya tafi gida.
   
Yana kwance  akan sofa malika tazo ta same shi wacce kallo d'aya tayi masa ta fhmci yana d'auke da damuwa.
  A hnkli ta gurfana gab dashi takai hannu ta shafo gefen fuskar sa snn tace"my man mene ne?
   Yace"ba komai"
Amma my man sae naga kamar kana cikin damuwa ko mun fasa yin tafiyar ne"
  Yace"eh na fasa yin tafiyar dake"
 Tayi saurin kallon shi tace"meyasa?
 Yace"haka kawae"
Ta wani  maraerai ce fuska tace"pls my man na fasa raina a tafiyar nn"
 Yace"sae ki cire"
 Tace"my man..... Yace"malika bana son damuwa fitar min d'aki"
  Kallon sa tayi shaye da toka snn ta tashi tabar d'akin shi kuma ya gyara kwanciyar sa cike da tunanin ina ma Rynt na a gidan shi da da ita zai yi tafiyar.


Da qarfe goma ya fito cikin shirin sa na tafiya malika dake zaune falo tana kallo har ya Rita bata ce dashi komai ba.
 Wacce niyyar ta yana fita itama zata sa qafa ta fita ne sae kuma ya dawo ko zata dawo.
   Tana jin tashin motar sa kuwa ta tashi taje  d'aki tayi waya snn ta shirya kayanta tayi wani sabon wanka ta ca6a ado ta fito cike da yanga janye da trolley bag d'inta har ta fita gate d'in gidan ta nufi gurin wata dakakkiyar motar da ke fake a nn bakin gate d'in ,
kafin ta qarasa sae ga wani  gaye  ya fito cikin motar d'auke da murmushi yazo ya bata hug had'e da kiss snn yaja hannunta suka shiga motar suka tafi.


Sati biyu man ya kwashe a tafiyar da yayi snn ya dawo wanda koda ya dawo ya sami malika tasa an shirya masa abinci kala kala sae murna take da dawowar sa kamar ba ita ce ya tafi ya bar tana fushi dashi ba.
Yayinda shi kuma ba abinda ya matsu yaje ya gani irin Rynt dake d'auke da babyn shi.


 2:30
Rynt ce a bakin gate d'in school ita da qawar ta Sarah ko waccen su na jiran azo d'aukarta.
  "Lah Rynt ga yayanki"
cewar Sarah wacce ta ta6o Rynt ta nuna mata man dake tafe zuwa gurin su ,
 idon sa qyar akan rynt da yaga ta qara mae wani  irin kyau da haske.
   Itama Rynt haka taga man yayi haske ya kuma qara kyau sae dae ita kallo d'aya tayi masa ta kauda fuskarta  akasin shi da har ya qaraso gurin su kallonta yake.
  Bata ce dashi komai ba sae Sarah ce ta gaida shi ya amsa ba yabo ba fallasa yayinda Sarah tace da Rynt"kinga nima yayana yazo sae gobe Sunday idan mun had'u"
   Rynt tace"to Allah kaimu"
Tana gama fad'ar hakane man ya d'ago fuskarta yana kallonta snn yace"ke baki iya gausuwa bane?
   Shiru tamae kamar bata ji ba sae ma wani  gefe da take kallo.
  Yace"muje na sauke ki"
Tace"bana so"
 Yace"ai gwanda kizo muje don drivernki naki ba zowa zai yi ba nace yayi zaman sa"
  Tace"idan bai zo ba ma ai akwae napep"
Guntun tsaki yayi had'e da jan hannunta tayi saurin fizge hannun.
  Yace"so kike na d'auke ki a gaban bainar jama'ar nn ko"
Tayi saurin kallon shi yace"ko kina musu ne?
    Still kallon sa kawae take.
Ganin ya gyara hannuwan rgsa yasa tayi saurin ja baya sae kawai taji d'ayan takalminta ya tsinke ta kalli takalmin rae 6ace snn ta kalli man idonta tap da qwalla tace"ka gani ko"
Ya kalli takalmin snn ya kalleta yace"laifin ki ne ae"
  Cikin muryar kuka tace"wane irin lafina ne bayan kaine kazo kana takurani"
    Shiru mohd yayi ya hard'e hannyensa a qirji yana mae kallon yanda hawaye suka fara sakkowa a hnkli kan kumatun ta.
Inda cikin yanayi na shagwa6a Rynt takai hannu ta share hawayen .
Man dake kallonta yace"muje na saya miki wasu takalmin"
 Ya fad'i hkne tare da riqo hannunta yayinda ita kuma bata musa mai ba tabi shi sbd ba gidan inna tayi kai tsaye ba gurin maman mami zata je duba mami dake jin jiki har ma yau kusan kwanan ta biyu knn bata zo school ba.
Suna isa gun mota Rynt ta warce hannunta taje ta bud'e gambun baya ta shiga.
   Man da har ya bud'e 6angaren driver zai shiga sae mayarda ganbum yayi ya rufe.
  Ya dawo nn seat d'in baya inda Rynt ta shiga shima ya shiga ya zauna yana mai kallon Rynt da ita ma shi take kallo.



Billy Giro😊
[2/20/2017]
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```












_Sarat Sale wnn page in nàki ne Allah ya bar min ke akan qaunar da kk min luv u ❤_

                🔮🔮🔮🔮
*```Page 57```*
Yace" ke dan ubanki ni kk nufin na zamo drivern ki"
 Cikin mugun 6acin rai Rynt ta kauda fuskarta had'e da hanzarin kai hannu zata bud'e gambun motar zuwa fita.
  Man yayi saurin jawota yana mae kallon fuskarta yayinda Rynt ke kallon shi cike da tsana d'auke da qwallah tap a idonta.
  Jikinsa ne yayi sanyi yana mae ci gaba da kallon yanda Rynt ke mae kallon tsana da kuma hawayenda suka soma gangarowa a hnkli kan fuskarta yayinda take yunqurin qwatar kanta daga gareshi.
 A nn ya sami kanshi da rungume ta tare da kai bakin shi saitin kunnenta yace"sorry bazan sake zagin ki ba kinji"
  Komai bata ce dashi ba sae kuka ta fashe mae dashi .
Nn ya sassauta riqonda yayi mata don ya fahimci zafin riqon ne yasa ta fashe da kuka.
  Bata daina kukan ba taci gaba da yin abinta a nn kan qirjinsa.
   Yayinda mohd  ya shiga shafa bayanta a hnkli alamar rarrashi.
   Minti d'aya sukayi a hk mohd ya soma jin kukan nata na mae zafi a rae a nn ya d'ago fuskarta zai had'e bakin su sae tayi saurin cusa fuskarta sosai a qirjin shi tana ci gaba da kukanta.
  A sanyaye yace"to ki daina kuka idan ba kya so na miki .
   Yana gama fad'ar hkne ta janye jikinta gabad'aya daga nashi ta kuma juya bayanta tana mae share hawayen fuskarta had'e da kai hannu ta bud'e ganbun mota ta fita.
  Shima man fitowa yayi wanda duk a tunanin sa gidan gaba Rynt zataje sae kawae yaga ta tafi abinta tana neman napep.
  Nan yaje yayi ta rarrashinta har ya samu da qyar ta koma cikin mota wacce still gidan bayan taje ta zauna.
 Yayinda mohd yaje 6angaren driver seat ya shiga ya zauna yaja motar yana mae kallon Rynt ta jikin mirror can dae ya maida hnklinsa gun tuqi har suka iso  wani  babban shagon saeda takalmi ya faka mota ya fita yaje ya siyo mata takalma ya dawo ya bud'e 6angarenta ya shiga tare da fitar da takalman a leda  yana nuna mata.
 Takalmi ne masu kyau da tsada flat ba sosai ba ya kalli Rynt da ke kallon takalman don itama sosai sun bata sha'awa yace"sa muga idan zasu maki"
 ba musu ta kar6i d'ayan takalmi ta sanya a qafar ta sae kuwa yayi dae dae a qafar ta.
  Nan man ya bata  d'ayan ta saka ta duqa zuwa d'auko tsinkakkin takalminta da suka tafi under seat bata kai ga d'aukowar ba man ya tada ta a hnkli yana kallon ta snn yace"kin manta da babyna dake jikin ki ne?
 Kallon sa kawai tayi ta kauda fuskarta shi kuma ya kai hannu a under seat ya ciro takalman snn ya fita ya koma driver seat yaja musu motar.
    A nn Rynt ta snr dashi inda zata.
Komai bai ce da ita ba sae kallonta kawae da yayi ta jikin mirror yaci gaba da tuqin sa har suka isa gidan nasu.

Tana fita yaja motar sa ya tafi ita kuma ta shiga gidan ta nufi 6angaren su mami .
  Ta sami mami kwance a falo ita kad'ai wacce tana ganin Rynt ta tashi had'e da buga wani irin ihun murna tazo da gudu ta qanqame ta.

 Umma dake kitchen ta fito a rud'e har tana had'awa da gudu se tayi tsaye turus tana kallon Rynt da ta d'auki mami sama zuwa jikinta.
Nn ta girgiza kanta d'auke da murmushi a fuskarta snn ta qarasa gurin su.
 Rynt na ganinta ta saki murmushi had'e da gaida ta.
  Cikin sakin fuska ta amsa mata har tana tambayarta inna tace"tana lfy"snn ta nemi guri ta zauna kmr yanda uman saliha ta buqata.
 Umman saliha kuwa taje ta kawo ma Rynt abinsha da abinci ta ajiye tana mae kallon mami dake zaune gefen Rynt da ta fara cika Rynt da surutu tace"keh kam ko ba lfy bakin dae baya mutuwa ko"
  Rynt tayi murmushi kawae tana kallon mami da ta tura baki tana kallon ummarta wacce takai hannu zata buge bakin tana mae fad'in"wae bana hanaki ba"
  Mami kuwa tayi saurin 6oye fuskarta a jikin Rynt tana fad'in"yi hqr umma na daina.
  Nan umma tayi dariya kawae tace da Rynt"kinga sauko kuci abinci tun d'azun ke kad'ai mami ke jira kixo kuci abincin nn har dae da taga lokacin tashi mkrnta yayi sae zuwa gate take tana dubowo idan kinzo .
  Rynt ta kalli mami tace"ba kya jin jiki ne hln da kike faman yawo mami"
  Umma tace"hm  sauqi dae ta samu don jiya sae kuka take tamin har bata iya cin komai"
  Rynt tace"Allah sarki Allah ya qara sauqi"
Umma tace"Amin sauko kuci abincin nn Rynh"
  Ta fad'i hkne tare da bud'e kulolin abincin.
D'ayar kula alala ce d'ayar  kuma sauce d'in qoda ne a ciki sae kunun aya dake gefe cikin jug  yayi sanyi har ya gaji.
  Ta zuba musu alalar a plate had'e da sauce d'in qoda gefe snn ta zuba musu kunun aya a cups tace"oya sae ku hanzarta kuci kar abincin ya sha iska.
  Nan ta tafi ta barsu da suka gama ne umma ta dawo d'auke da ledar magunguna taba Rynt a cewar taba mami tasha kowanne spoon d'ad'ad'aya .
Rynt ta kar6a umman saliha kuwa taje da sauri ta d'auki wayarta da ke faman ruri kan dining wacce koda ta gama wayar har Rynt  ta gama ba mami magungunan ,
nn ta kar6i  ledar magungunan ta tafi dasu d'aki.
   Sae ga Abban mami ya shigo ,
Rynt ta russuna har qasa tana gaida shi wanda cikin sakin fuska ya amsa mata snn ya shiga daga ciki.


Sae kusan qarfe hud'u     Rynt tabar gidan koshi sbd tana da lesson ne amma taso ko zuwa yamai ne snn ko zata koma.

Da dare bayan sllr isha'i Rynt na zaune ita da inna,inna na cin abinci ita kuwa ta gama cin abincinta tana shan agwalima.

 Sae ga Abban mohd ya shigo d'auke da sallama a bakinshi.
  Inna ce ta amsa sallamar yayinda Rynt ta gaida shi cike da ladabi ,
ya amsa had'e da tambayarta ya karatu "tace"Alhmdlh"
Yace"baku fara Exams ba?
Tace"a'a mundae kusa"
Yace"To Allah taimaka tace"Amin"
  Snn ta wuce.
 Sae a snn suka gaisa shida inna bayan sun gama gaisawar ne yace"inna inshaAllah idan su Rynh sunyi hutu zamu je qauyen su mu kaiwa mae garin nasu gaisuwa sbd bae kamata ace tun lokacinda muka je neman aurenta ba bamu koma jewayarsu  ba"
  Inna tace"hkne kam nima na jima ina wnn tunanin sae naga Rynt makaranta take zuwa kuma kai kanka baka zauna ba sae tafiye tafiye kake shiyasa ban tuntun6e ka da maganar ba.
  Yace"hakane gsky amma yanzu har izuwa lokacinda zasuyi hutu inshaAllah inada lokaci"
  Inna tace"To Allah nuna mana lokaci ya kuma kaimu lafiya ya dawo damu lafiya"
  Yace"Amin inna, bari na tashi dan ba daga gida na fito ba kan hanya nake"
  Tace"ayyo to ko a kawo ma abinci kaci ne?
Yace"Aa inna ga dae wnn"
 Ya fad'i hakane tare da ajiye mata leda a gefenta.
 Inna tace"to Allah shiyi Albarka mungode"
Yace"Amin"had'e da fita.
Nan inna ta bud'e ledar ta sami gasasshen naman rago da ya gasu yayi kyau ga timatir da albasar da aka yanyanka akai da kuma qullin yaji gefe.
   Rufe ledar tayi sae da ta kammala cin abincinta snn ta kira Rynt ta d'ibar mata  nata sukayi zaune a nn falon suna kallo suna ci had'e da er firar da sukeyi jefi jefi.

Zuwa qarfe tara ne suka tashi Inna ta nufi d'akinta haka ma Rynt wacce da shigar ta ta cire kayan jikinta ta fad'a bathroom koda ta fito kawae ta sami mutum kwance kan gadon ta ya wani d'aura qafa kan qafa yana duba littafanta da ta bari kan gadon.
  Mugun tsoro taji kafin ta fahimci waye .
 Nan ta kama hanya rae 6ace zata fita d'akin had'e da kiran inna.
  Man da ke kwance  bai san lokacinda ya fizgota ta fad'o kan gadon ba ya kuma sa hannu ya rufe mata baki.
  Sae kawae ya tsinkayo muryar inna tafe tana fad'in"Rynh gani ya akayi ne"
  Nan yaja Rynt ya shiga da ita bathroom ya rufe wanda still hannunsa na kan bakinta ya rufe gam.
  Nan yaji muryar inna tazo gab da bathroom d'in tana fad'in"Rynh me ya faru ne?
   A nn Rynt ta shiga qoqarin magana ta qasan maqoshinta , man yayi hanzarin had'e bakinsa da nata  yayinda inna ta d'auka ko gyaran murya ne Rynt tayi na alamar tana bayi hkn yasa ta fita.
  Man kuwa sae da ya tabbatar inna tabar d'akin snn ya zare bakinsa suna kallon juna shida Rynt kmr wasu zakarun da sukayi fad'a.
      Rynt ce ta fara kauda fuskarta had'e da sa hannu ta share lips d'in ta.
   Ta juya rae 6ace zata bar bathroom d'in ya riqo towel d'inta  tayi saurin kai hannu a qirjinta ta riqe towel d'in had'e da juyowa ta kalle shi nn kawae ya sami kansa da jin wani  yanayi a jikin shi kan yanda ta damqe qirjinta had'e da towel sae duk rabin mammanta ya taso har yana ji kamar ya d'aura hannunsa akae.
    Nan ya qara jan towel d'in had'e da jawota zuwa jikin shi yana kallon qirjin nata da yake tajin yakai hannun shi.
   Bai d'aura hannun sa ba sae saurin kauda idonsa da yayi had'e da sauke numfashi a hnkli tare da sake mata towel d'inta da ya riqe.
      Inda cikin kasalalliyar murya ya kalli Rynt da zata bar bathroom d'in yace"kar ki fita zo muyi wata magana kinji"
     Rynt ta kallesa  tace"to  bari na sa kaya tukun"
  Wacce ta fad'i hkne kawae amma niyar ta  da ta fita rufe d'akin zatayi dashi snn kuma ta kira inna.
 Mohd kuwa ba musu Yace"Ok je kisa kayan kizo amma kimin alqawarin baza ki kira inna ba"
Tace"nima kamin alqawarin idan na dawo na saurare ka ba zaka sake dawowa gidan nn ba haka kuma ko school kar ka sake zuwa ka sameni"
 Yace"meyasa?
Tace"sbd bana so"
Nan ya kalle ta kawae had'e da sauke numfashi yace"naji na kuma yi alqawarin amma idan kika karya naki nima zan karya nawa"
  Nan ta lumshe ido had'e da gyad'a mae kai snn ta fitav bathroom d'in ta sako kayan baccinta riga da wando ta dawo wacce tana shiga bathroom d'in man ke binta da kallo cike da sha'awa.
  Rynt bata ankara ba sae jin tayi ya jata zuwa jikinsa yana mata abubuwa masu mugun rikitarwa wacce lokaci d'aya ta sukuikuice ta fara mai kuka tana qoqarin qwatar kanta amma bata da wnn qarfin sbd ya gama kashe mata jiki gabad'aya sae ma kayan jikinta da ya shiga yunqriñ rabata dasu.

Naso na d'an qara maku but wasunku na qorafi sosai akan daren da nakeyi.


Billy giro😊
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```













               🔮🔮🔮🔮
*```Page 58```*
A nn Rynt ta shiga kuka sosai tana kai masa duka ta koina.
Amma aikin banza dan tuni ya rabata da kayan jikinta ya shiga wasa da albarkatattun kirjinta dake ci gaba rikitar dashi.
  Wanda sae yana gab  da cimma burin sa ne kukan Rynt ya soma dawo dashi hayyacin sa,nn ya samu da qyar ya saesaita  kanshi had'e da rungume ta yana lallashinta.
  Tayi saurin fizge kanta a rud'e zata bar bathroom d'in ,
Bata kai ga fitar ba sae jin tayi ya rungumeta ta baya had'e da kai hannun sa kan d'an cikin ta da ya soma tasowa yana shafa cikin sannu ahnkli kmr wani mae shafa qwae,yayinda lips d'insa ke kan wuyanta yana wasa da harsen sa akai.
  Nan taji qafafuwanta sun kasa d'aukarta sae zubewa qasa da tayi ya bita yana qoqarin janye hannunwanta da ta rufe qirjinta.
  Bai iya janye hannyen ba sae d'agowa yayi yana kallon yanda jikinta ke rawa sosai ga hawaye dake gangarowa a hnkli kan fuskarta.
  Nan yakai  hannu zai share mata hawayen tayi saurin matsawa had'e da d'aukar kayanta ta rufe jikinta tare da fashe masa da kuka.
   Nan kawae ya kalleta ya tashi ya kimtsa kanshi ya fita bathroom d'in ya barta sae kuka take can ta tashi tasa kayan baccin ta ta fito batroom ta share fuskarta da tasha kuka snn ta fita a d'akin taje d'akin inna,
 ta samu inna na shafa'i da wuturi taje tayi kwance  kan bed kamar wata marar lafiya dan har wani  kamewa guri d'aya tayi kamar mae jin sanyi.

Inna da ta gama sallah ta d'auka ko sanyi Rynt keji shiyasa da taje zata kwanta taja blanket ta rufa mata jikinta.
Rynt naji amma ta lafe kamar mae bacci sae ajiyar zuciya da ta fitar a hnkli.


Washe gari Rynt ta gama shirin ta tsaf na zuwa school zata fita inna ke ce mata na manta ban gaya miki ba Rynh jiya da kabiru yazo yace yana son idan kunyi hutu zamu je qauyen ku gurin mai gari mu kai masa ziyara".
  Jikin  Rynt ne yayi sanyi don inna na d'auko maganar qauyen su sae ta sami kanta da tuna baffanta ta kalli inna kawae tace"to"had'e da fita.


 Yanda taje school jiki sanyaye haka ta kasance har aka tashi tazo bakin gate tana rarraba ido inda zata hango motar drivernta  sae roqon Allah take idan ba mohd ne zai zo ba duk da cewa yayi mata alqawarin ba zai koma dawowa ba amma tasan ba lallai bane ya cika alqawarin.
 Tana cikin hkne ta hango motar drivernta yazo nn ta sauke ajiyar zuciya taje ta shiga motar suka tafi.

 Koda aka sauke ta ta   shiga se ta had'u da Aamil zai fita gidan wacce tana ganin sa sae da gabanta ya fad'i don ta d'auka ko mohd ne har dae yanda ya bita da kallo sae kawae tasha toka bata ce dashi komai ba ta wuce.
  Sae ga inna ta fito da sauri riqe da waya a hannunta tana kiran Aamil da ya manta wayar shi.
 Aamil ya juyo yayinda inna taba Rynt waya tace takai mishi wyr.
    Taje ta kai masa waya had'e da gaida shi wanda sae da ya kar6i wayar snn ya amsa gaisuwar yana mai kallonta har sae da ta juya ta tafi snn ya kauda idonsa akanta ya wuce.


Rynt kuwa da shigarta d'akinta taje ta rage kayan jikinta tayi wanka ta fito ta shirya ta fita ta sami inna zaune a falo tana kallo nn ta qarasa ta zauna qasa kusa da kujerar da inna ke zaune akai inna ta dafa kanta tace"wae Rynh me yake damunki ne na fhmci tun da safe kike cikin damuwa"
    Rynt ta girgiza kanta had'e da cewa "ba komai inna"
  Inna tace"ko kina jin jiki ne?
Tace"um um bacci ne kawae inna"
  Inna tace"to tashi kije ki d'ebo abinci kici sae ki d'an kwanta kafin qarfe hud'u tayi mae miki darasi yazo"
   Rynt tace to had'e da tashi ta nufi kitchen ta d'ebo abinci tazo nn falo ta zauna ta shiga cin abincin cikin natsuwa.
  Bayan ta gama cin abincin ne tayi kwanciyarta akan 3 seater ba jimawa kuwa bacci ya kwashe ta inna ta kalleta kawae ta ci gaba da kallonta wacce tana cikin kallon ne ta jiyo  sallamar Aamil ya dawo gidan ,
inna ta amsa sallamar yayinda ya shigo riqe da wata leda a hannun shi yayi tsaye kawae yana kallon Rynt dake bacci sae can ya sauke numfashi had'e da lumshe ido ya kauda fuskarsa ya kalli inna da tace"ya akayi ne Aamil?
  Bai ce komai ba sae ledar hannun sa da yaje ya ajiye kusa da ita snn yace"wae fruit ne na siyo maku d'azun da zan shigo shine na manta su a mota har sai da na koma gida snn na tuna.
  Inna tace"ayyo d'an albarka shine ka koma dawowa to Allah shiyi  albarka mungode"
  Yace "amin"had'e da zama kusa da kujerar da Rynt ke kwance .
  Inna kuwa tashi tayi taje kitchen ta d'auko kayan gyaran fruits tazo tayi zaune a qasa ta miqe qafafu zata fara gyara fruit d'in Aamil yace"inna da kanki ina wnn Baabar take ne?
  Inna tace"ayyo ai Baaba hurera bata sami shigowa ba yau sai dae ko gobe "
   Yace"to inna bari na taya ki"
Ya fad'i hkne tare da tashi yaje gaban inna ya zauna had'e da lanqwashe qafafuwan sa yana mai kwashe hannuwan rgrsa.
  Dariya kawae inna tayi ta bashi tray da wuqa don ba yau suka fara ba.
  Nan ya fara gyara fruits d'in sae yi yake yana kallon Rynt dake baccinta.
   wanda yana gab da kammala gyara fruits d'in ne yaga Rynt ta shigo motsi tana juyi kmr zata fad'o kan sitar yayi sauri zai tashi sae kawai yaga bata fad'in ba sae tashi zaune da tayi tana mustsuke ido.
   Bayan ta gama mustsuke  idonta ne ta shiga kallon Aamil da mamaki kan aikin da ta gani a gaban sa yana yi ta dae san ba mohd ba kam sae dai ko wanda ta gani d'azun ko d'ayan shi.
  Inna ta katse ta da cewa"Rynt kin tashi?
 Tace"eh inna"
 tace"zaki sha 'ya'yan itacen nn ko sae sunyi sanyi tukun"
  Tace "Aa sae sunyi sanyi inna"
  Inna tace"wae naga kina son 'ya'yan itace sosai shiyasa na d'auka ko zaki d'an sha kafin suyi sanyi"
  Uhm hakane inna amma yanzu so nake na fara shirin lesson don naji kmr an fara kiraye kirayen sllr la'asar.
  inna tace"to shike nn jeki muma ai tashi zamuyi ynx.
  Nan  Rynt ta wuce Aamil da ya bita da kallo ya maida duban sa gun inna kmr wanda zai tamvaye ta wani  abu sae kuma ya fasa.
   Ya tashi ya d'auki kayan gyaran fruits d'in da ya gama aiki dasu yakai kitchen ya dawo yayi ma inna sallama a cewar daga masallaci zai wuce.
 inna tayi masa Allah kai lafiya snn ta d'auki bowl d'in da fruits ke ciki taje d'aki ta saka a fridge ta nufi bathroom zuwa arwala.

Sorry 4 dis one.

Billy giro😊
[2/23/2017]
 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```













               🔮🔮🔮🔮
*```Page 59```*
Koda 8:30 tayi na dare tuni Rynt ta kammala duk wani abu da tasan tanayi a d'akinta ta rufe d'akin taje d'akin inna.
  Wacce  don mohd kad'ai tayi hkn sbd ta fhmci guraren qarfe tara da wani  abu ne yake zowa,ba wae don ta manta alqawarin da yayi ba sae dan ta tsorata sosai da abinda ya tashi faruwa jiya da ita haka kuma bata da tabbacin cewa  zai cika alqawarin.


6angaren mohd kuwa kwance yake kan bed yana dubin silin daga shi sae farar singlet da farin boxer ya lumshe ido kmr wani mae bacci  sae ga malika ta shigo d'akin riqe da cup a hannun ta ta ajiye cup d'in kan bedside drawer ta zauna gefen gado nn kusa da man tana mae kallon fuskar sa snn ta d'aura hannunta a hnkli kan sajen fuskar sa tace"my man ga ruwan Lipton d'in na had'a ma"
  A hnkli ya tashi daga kwancen da yake ya zauna malika ta d'auki cup d'in zata kai bakin shi ya dakatar da ita ta hanyar kar6ar cup d'in ya maida kan bedside drawer ya ajiye ya kuma koma abinsa ya kwanta.
D'auke da mamaki malika tace"my man lafiya?
  Yace"malika bana jin zan iya sha"
    Cikin damuwa ta lumshe ido ta ware su akan shi snn ta riqo  hannun sa tana mae kallon fuskar sa tace"my man na rasa me yake damunka tun daren jiya har izuwa yau kuma idan na tambayeka sae kace min wae ba komai shin banyi matsayin da zaka gaya min damuwar ka bane ko kuwa?
    Man dake kallonta ya jawota tare da kwantar da ita kan qirjin sa yana shafa bayanta ba tare da yace da ita komai ba.
  Malika dake lafe a qirjin nasa tace"my man baza ka gaya min damuwar ka ba"
   Yace"malika na gaya miki ba komai"
 Tashi tayi daga kan qirjinsa tana kallon sa tace"kawae dae baza ka gaya min ba amma wlh kana d'auke da damuwa"
  Ta qarashe mgnr ne cikin 6acin rae mae had'e da muryar kuka snn ta d'aura da cewa" a duk duniya kaine mutum na farko da na fison naga na sharewa damuwar shi idañ na gañshi a ciki amma sae gashi kai sam baka son ma ka gaya min damuwar ka bare har nayi yunqurin ganin na kawar ma da ita.
 Tana kaiwa nn ta fashe da kuka ta tashi ta bar d'akin .
  Man ya bita da kallo kawae har ta fita snn ya gyara kwanciyar sa zuwa gefen hannunsa na dama yana mae kallon agogon bangon d'akin yaga 9:00pm nn ya lumshe idonsa a hnkli had'e da kai hannu ya kashe wutar d'akin.

Washe gari ya fito daga wanka sanye da white bathrobe a jikin shi ya sami malika zaune kan bed wacce tana ganin sa tayi saurin tasowa taje gab da shi tayi tsaye tana kallon sa  d'auke da idanuwanta da sukayi jajir kan kuka,
 nn kawae ta fashe da wani  kukan ta fad'a jikinsa ta rungume shi tana fad'in"my man na fhmci ynz ka daina sona kwata kwata na rasa meyasa"
Dagà hk taci gaba da kukà man ya qara rungumeta yanà   lallashinta yanà bàta màgaña har ya samu tayi shiru ta kuma manta komai nn take.
 Wacçe d'auke da murmushi a fuskarta ya jata suka je kan bed zai shafa Vaseline,  ta kar6i Vaseline d'in ta shiga shafa masa.
  Tana gama shafa masa ne ya yunqura zai tashi zuwa saka tufafi ,
 ta maida shi zaune tana kallon sa cike da sha'awa snn takai hannu ta shafo sajen fuskar sa cikin marairaicewa tace"my man u know i really missed u"
Shiru kawae man yayi yana kallonta ita kuwa sae ci gaba take da shàfa sajen fuskar shi yayinda takai fuskarta a hnkli kan tashi ta had'e bakinta da nashi tare dà kai hannu tana shàfa jikiñsà ta koiña bae hanata ba ya biye mata don baya son shiga haqqinta,duk da ba irin abinda yafi so irin ace Rynt ce ya samu ba ita ba.


              ******
 Aamil ne fake cikin motar sa a nn bakin gate d'in gidan inna da shima kanshi bae san dalilin zuwan shi da sassafen nn ba.
  Nan dae ya fito motar ya shiga gidan bai sami kowa a falon ba sae fruits salad da ya samu an had'a cikin d'an wani transparent rober bowl mae marfi an ajiye kan center table.
 Ya kauda idonsa had'e da sallama inna ta amsa sallamar snn ta fito.
  Wacce tana ganin Aamil ta washe baki zuwa murmushi tace"Aamil kaine da sassafen nn ina ce dae lafiya ko?
  Yace"lafiya qalau inna na shigo ne kawae"
  Inna zata yi magana knn idonta ya fad'a kan fruits salad d'in da ke ajiye kan center table taje ta d'auka had'e da fad'in"ayyo ashe Rynh haka ta tafi mkrnta ta manta  'ya'yan itacen nn nata"
  Aamil da yaje xai zauna sae fasa zaman  yayi yace" eyyah ina ne makarantar tasu sae na kaimata?
  Inna tace"da kuwa ka kyauta min Aamil dan wlh Rynh na son 'ya'ya itace nsn yanzu haka tana can tana fama da zullumin mantasu da tayi.
  Ta fad'i hkne yayinda Aamil ya kai hannu ya kar6i fruits salad d'in had'e da cewa"wace makaranta take ne?
  Inna tace"yo ai kaji fa ni zaune kawae nake da ita ban ko san sunan makarantar tasu ba amma kira nasir a waya zai gaya ma"
  Nan ya fita had'e da zaro wayar sa a aljihu ya kira nasir wanda sae da suka gaisa snn ya tambaye shi.
   Bayan nasir ya gaya masa ne yaja motar sa ya tafi,
 bai zarce koina ba kuwa sae makaratar su Rynt.


Rynt na zaune cikin class za'a fara teaching d'insu d'auke da damuwar mantuwar da tayi don ana sauketa gate ta tuna cewa tayi mantuwa.
 Tana cikin hkne kuwa se ga security an aiko ana kiranta.
  Yi tayi kmr bata ji ba dan ta d'auka ko mohd ne yazo kmr rnr da ya ta6a zowa shiyasa tayi zamanta har sae da teachern su ya mata magana snn ta tashi ta fita  wacce tana ganin Aamil ta yarda cewa mohd d'in ne yazo taje shaye da toka tana kallon sa tace"me kuma ya kawo ka?

 Da mamaki Aamil yace"Aamil ne fa"
  Da sauri ta sadda kanta qasa tace"dan Allah yi hqr bana banbance ku ne"
   Yace"no ba komai  had'e da bata robar fruits salad d'inta da yasa abu yayi wrapping ba'a ganin meye a ciki kmr gift  ,bata kar6a ba sae kallon sa da tayi, yace"fruits salad d'inki ne da kika manta"
  Dad'i taji har ranta don d'auke da murmushi ma takai hannu ta kar6a had'e da yi masa godiya.
   Murmushi kawae ya mata snn ya juya ya tafi ita kuma ta koma class.

 Man kuwa bayan sun gama abinda sukeyi ne yayi wanka ya fito cikin shirin sa na zuwa asibiti wanda har zai shiga mota sae  yaga motar Amir ta kunno  kai a cikin gidan ,
nn ya fasa shiga motar tasa ya tsaya jiran Amir da ya faka motar sa ya fito ya same shi had'e da bashi hannu suka gaisa .
  Snn yace" zaka je asibiti ne?
 "Eh"
cewar mohd kafin yake cewa "ya akayi ne"
  Amir yace" wae gidan inna fa zanje sae kawae nayi sha'awar  nazo nn "
  Mohd yayi murmushi yace"ai ka kyauta dan da Aamil ne bazai zo ba ,rabona dashi ma har na manta"
 Amir yace"ksn shi Aamil kmr kaine gidan inna yafi zuwa akan koina"
Mohd yace"hkne amma yaushe zaku koma ne nikam?
   Eh to tukuna bamu sa rana ba dan wlh ni har ji ma nake kmr mu dawo da zaman mu a nn har aikin mu"
Man yace"kan ku ake ji  nidae idan kaje gun inna kace ina gaida ta"
  Amir ya kalle sa yace"inna kuma dake fushi dakai"
Yace"to ai so nake ta daina fushin dani ko zan sami hanyar bawa Abba hqr dmn naga cewa na dawo da wnn yrnyr"
  Yace"hkne ni na tafi"
Nan sukayi sallama da juna kowanen su ya shiga motar sa suka bar gidan.

 3 dayz later
 Aamil ne zaune a falon inna shida inna suna firar su yana yanka fruits wanda tunda yaji cewa Rynt na son fruits kullum sae ya siyo ya kawo  kuma duk ya kawo shi keyin zaune da kanshi ya gyara.
  Suna cikin hkne sae ga Rynt ta dawo daga school wacce tana shigowa idonta ya sauka akan Aamil dake gyaran fruits kanta qasa ta gaida shi d'auke da er alamar dariya a fuskarta.
 Aamil dake kallon ta ya amsa had'e da kallon inna yace"inna Rynt fa da kmr dariya nake bata idan ta ganni ina aikin nn ko meyasa?
   Inna ta washe baki ta kalli Rynt wacce  tayi saurin barin gurin cikin jin kunya
 Innà tace"ni kuwa ina zan sani wata qil bata saba ganin namiji na aikin nn ba"
   Yace"inaga hakane inna don naga har kunya takeji idan ta samu ina aikin nn"
  Inna tace"ai ita Rynh komai kunyar sa take ji"
  Aamil yace"wlh inna shiyasa take matuqar bani sha'awa"
  Inna tace"ai Rynh abin so ce ga kowa don yrnyr ba ruwanta wlh"
   Aamil yayi murmushi zai yi magana wayar sa ta shiga ruri ya d'aga wayar had'e da fita wanda sae da ya jima kafin yake dawowa ya sami Rynt ta maye gurbinsa tana ci gaba da aikin da ya bari.
 Yayi tsaye kawae yana  ta kallon ta  yayinda Rynt keta aikinta bata ko san yana yi ba sae inna ce ta lura dashi  tace"yadai  Aamil ko zata tashi ne ta bar ma aikin ka qarasa abinka?
  Ya kalli inna kawae snn ya kalli Rynt yace"hln yau mai lesson d'in naki ba zai zo bane"
 Ba tare da ta kalle sa ba tace"zai zo"
  Yace"amma kuma shine kika zauna ma aikin nn da dawowarki school ko abinci ma baki ci ba"
 Inna tace"kai fad'i ba yanda banyi da ita ba nace ta bari ni na qarasa ita taje taci abinci tace Aa"
  Aamil dake kallon Rynt yaje ya durqusa a hnkli kusa da ita snn yakai hannu ya  kar6i wuqar da ke hannunta yace"bani aikin tashi kije kici abinci kinji kafin mai lesson d'in naki yazo"
  Sae da Rynt ta kàlle  shi snn ta tashi ta tafi d'akin inna ta d'ebo fura a cup taje d'akinta tayi zaune tana sha.


A washe garin rnr mohd ne zaune a office d'in shi da kallo d'aya zakayi masa kasan cewa yana d'auke da damuwa a ransa wanda tun daga wnn rnr bai qara zuwa gidan inna ba haka kuma bai sake bibiyar Rynt a school ba kan alqawarin da ya d'aukar mata da ya soma jin ba zai iya ba.
D'auke da damuwar da yake ciki ne ya kalli Amir dake zaune suna fuskantar juna yace"wae Amir a wnn rnr da zakaje gidan inna har nace kace ina gaidata ka snr da ita kuwa?
 Amir yace"eh na gaya mata mana sae dae yi tayi kmr bata ji ba"
  Mohd yayi shiru can yace"Amir a gskiya ina cikin damuwar rashin wnn yarinyar a kusa dani bazan 6oye maka ba ina son ta dawo gareni ne sbd ina sonta ba wae dan babyna kad'ai ba.
 Amir ya sauke numfashi snn ya kalle sa yace"to ai tunda hkne ka tashi muje kawae ka bawa Abba hqr "
  Man ya girgiza kansa had'e da fad'in" no Amir ina gudun naje na qara tinzira Abba ne.......Kaga kawae kasa a ranka cewa idan munje ka bashi hqr zai haqura da haka kuwa sae kaga Allah ya taimake ka ya haqura.
  Mohd yace"haka kake gani?
 "InshaAllah"cewar Amir
Yayinda mohd ya kalle sa jiki sanyaye yace"shiken nn muje d'in".
 
Nan suka tashi suka d'unguma sae gida suka nufi 6angaren su kai tsaye  suna shiga dae dae Abba na saukowa kan staircase suka had'u dashi ,
a nn mohd ya tsaya cak ko tako d'aya ya kasa qarawa sae kansa da ya sadda qasa sbd wani  irin mugun kallo da Abba ya tsaya yana musu dashi har Amir.




Daga yau inshaAllah na canza lokaciñ posting sae ku daina tsammàni na dare sae dae da safe,rana ko yamma.
     Luv u❤

Billy Giro😊
?```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```













               🔮🔮🔮🔮
*```Page 60```*
A fusace Abba ya qaraso gurin su wanda kai tsaye gun mohd ya nufa ya d'aga hannunsa cikin zafin nama ya kai masa mari had'e da nuna shi yace "Ba nace kar na qara ganin qafar ka a gidan nn ba ko kuwa rashin d'a'arka ce kazo ka qara nuna min ne, to bari kaji wlh idan har ka sake kuskure irin wnn sae na maka abinda baka taba tunani ba shashasha kawae, get out of this house!"
 Juyawa mohd yayi idonsa ya kada yyi jazur yyi saurin fita daga gidan, yayin da Amir ya kalli Abba cikin yana yi na son bashi haquri Abba yayi saurin dakatar dashi ta hanyar d'aga masa hannu yace "Amir idan har ba so kake laifin mohd ya shafe ka ba to kaima kayi gaggawar fita a nn in daina ganin ka"
  Amir ya girgixa kai da damuwa yace "Dan....." cikin d'aga murya Abba yace "ka fita nace!
   Jiki a sanyaye Amir ya fita ya samu har mohd yaja motar sa ya bar gidan.
  Nan yaje ya shiga tasa motar ya tafi sae gidan mohd.
 A nn falo ya tarda Muhd kwance  kan doguwar kujera idonsa lumshe sae girgixa kafa yake, Amir ya xauna kujerar dake kallon Wanda yake ya kirasa a nutse, da kyar mohd ya iya bude ido yana kallon dan uwan nasa.
  Cikin muryar rarrashi Amir yace"pls am really sorry ban san cewa haka abin yake ba"
 Mohd dake kallon sa yace"Inafa zaka sani ina ma bayani kaqi ka fhmta yanzu gashi meye riba in banda qara 6ata min tsari da kayi"
  Yana gama fad'ar hk ya buga tsaki ya tashi ya bar masa falon Amir da ya bisa da ido ya girgiza kansa kawae snn ya tashi ya fita.


5:00pm
Rynt ce zaune a falo ta tasa littafanta gaba tana dubawa sae ga Aamil ya shigo had'e da sallama ta amsa sallamar yayin da ta d'ago ta kalle shi bata kawo kowà ba sae shi Aamil d'in don ta fhmci yanzu kusan ko yaushe shine ke zowa.
  Nn ta gaida shi fuskarta ba yabo ba fallasa ya amsa mata cikin sakin fuska snn yace inna fa.
  Tace"inna tana maqota amma tace bazata jima ba  zata dawo"
  Yace"OK"snn ya zauna yana mae kallon Rynt da ta maida hnklinta gun duba littafanta yace"kuna da test ne?
 Tace"um um ina dubawa ne kawae"
 Yace"gud haka nada kyau ,but yaushe zaku fara exam ne?
 Rynt tace"wani sati mai zowa inshaAllah"
  Yace"olryt next week knn ,inga littafin"
Ba musu ta bashi ya kar6a yana dubawa nn yaga rubutun nata mai kyau dashi.
  Yace" zaki koya min rubutun nn naki mae kyau"
Ya fad'i hkne d'auke da murmushi a fuskar sa yana kallon ta"
  Kallon sa tayi ta kauda kanta d'auke da d'an guntun murmushi ba tare da tace komai ba,shima d'in dae bai ce komai ba sae sauka yayi kan kujerar da yake, ya zauna nn qasa inda yake fuskantar ta ya lanqawshe qafafu kmr yanda take zaune itama snn ya d'aura littafi a nn tsakiyar su ya kalle ta yace "a ina kika tsaya da karatun naki?
  Tace"topic d'in yau ne kawae kuma shima tun a school na fara dubashi kuma shine kazo ka tarar ina dubawa"
Yace"shikenan zan tambaye ki abinda kika fhmta akan kowanne topic dake ciki"
  Ta gyad'a masa kai yayin da shi kuma yaje ga topic d'in farko ya fara mata tambayoyi  tana bashi amsa shi kuwa ya kafe idon shi akanta se kallon d'an qaramin bakinta yake dake ta koro bayani filla filla kmr malami na koyar da d'alibi.
  Sallamar inna ce ta katse su nn Aamil ya fitar da numfashi a hnkli ya kalli inna tare da amsa mata sallamar snn ya gaidata.
 Washe da baki ta amsa had'e da tambayar sa mutan gida
  Yace"duk suna lafiya kuma suna gaida ke"
  Tace"madallah ina amsawa"
Kafin take kallon yanda suke zaune da kuma littafin da ke hannun Aamil tace"Au yau kaine ka maye gurbin mai darasin nata knn "
  Nan Aamil yayi saurin duba agogon hannun sa yace"af inna ai na
 manta cewa lokacin lesson d'in nata yayi wata qil ma har yazo yayita sallama ba muji ba"
  Inna tace"Aa ai yau ba zai zo ba sbd rnr yau an ke6e mata ita ne dan ta samu ta huta"
  Aamil ya kalli Rynt yace"to inna ai karatu kuma na samu tanayi ba hutun ba"
  Inna tace "yo ai ita Rynh ko yaushe haka take kullum cikin karatu take uwa ta jika takardar ta shanye"
   Aamil dake kallon inna ya maida duban sa gun Rynt yana murmushi yace "Rynt is gud kid'an riqa hutawa kinji ko"
  Gyad'a masa kai tayi shi kuma ya bata littafin ta tare da fad'in"to jeki ajiye gobe idan na dawo ma qarasa ko"
  Tace"tohm" had'e da kar6ar littafin ta had'a da sauran snn ta tashi ta nufi d'aki yayin da Aamil ya bita da ido har ta shige d'aki yace "inna wae ina kika samo yarinyar nn ne wlh se naji ta kwanta min a rai sosai, ga ta da hnkli"
  Jin shiru yasa ya maida duban sa gun inda inna ke tsaye yaga ashe ta d'aga bata nn.
 Mikewa yyi a hnkli ya dauki makullin motar ya fita daga falon. Bayan 'yan mintina inna ta dawo falon rike da kofin fura tana cewa "gashi nn sauran na Ryynt ne...." Bude ido tayi tace "Au har ya tafi ko me?" Kwala ma Ryynt kira tayi ta fito inna tace "ina wnn yaron ba dae ya tafi ba" Ryynt tace "ban sani ba inna ina ciki" inna ta tsuke fuska tace "to in gidan uwarsa yaje xae tafi bae mata sallama ba dan bnxan yaro kawae, inda Muhd ya fi su knn" Rayyanat dae murmushi kawae tayi bata ce komae ba ta juya ta koma daki.
  Karfe takwas da kusan rabi Ryynt na xaune falo suna kallo da baaba hurera inna kuma na daki tana sallah aka bude kofar falon hade da sallama, Amir ne ya shigo ya karaso cikin falon murmushi dauke a fuskarsa, baaba Hurera ya gaidar snn ya xauna yana kallon Ryynt, ta dan sake fuska had'e da  gaishesa dan ta d'auka ko Aamil ne da ta d'an fara sabawa dàshi ,ya amsà gaisuwar yana màe ci gàba dà kàllonta yayin da Baaba hurera tace "Yau kaine a gidan namu shugaba"
sae a snn ryynt ta gane Amir ne don sunan da baaba hurera ke kiransa knn, yyi murmushi yana shafa kai yace "nine baaba, innar fa"Baaba Hurera tace "tana ciki tana sallah" shiru yyi bae ce komae ba yana dan satan kallon ryynt da ta maida dubanta ga kallon da take, mikewa baabà hurera tayi tace "bari in kawo maka abinsha ko" kmr jira yake yace "to baaba" ta mike ta nufi kitchen, sakkowa kasa yyi da sauri yana kallon ryynt yace "Rayyanat ina son muyi wata magana da ke don Allah, ko idan xan tafi xa ki dan fito na jiraki" hade rai tayi tace "nifa sanyi nake ji" shiru yyi yana kallonta snn yace "ae ba wani ddewa xa muyi ba" fitowar inna daga daki ne ya sanya shi yin shiru ya maida dubansa ga tv kmr me kallo, inna tayi michi michi da ido tace "waye wnn nake gani kmr Muhd a falona" Amir yyi yar dariya yace "A'a nine inna" tace "ayyo wace gulmar ce to naga kamar kana yi" dariya yyi ya mike yana kallon ryynt yace "ni kinga tafiyata ma inna tun daxu na shigo gaishe ki" bae jira cewarta ba ya fice daga falon.
  Yayin da inna tace"to Allah kiyaye"snn ta nufi kitchen.
Rynt kuwa ba dan ran ta ya so ba ta tashi da sauri tabi Amir ta samu har ya fita gate, dan tsaki ta ja ta bi bayansa, jingine ta samesa jikin motarsa ta karasa tace "gani" bata rufe baki ba aka bude motar, kamshin turarensa kawae ya bugi hancinta ta juya a tsorace xata bar gurin ya fizgota, kuka ta saki tana kallon Amir tace "amma ka cuceni wllh," Amir ya girgixa mata kai yace "ki tsaya ki sauraremu Ryynt, mgnr fahimta muka xo ayi"cikin kuka tace " bana bukata, ni ku rabu dani kawae kar in maku ihu ko ana dole ne"
Nn ta gatsara wa mohd cixo ya cikata ba shiri tayi cikin gida a guje, Amir ya fuzar da iska yace "sae da nace maka kadda ka fito man ban san me ya fito da kai ba mtsw c wat you've caused now" Muhd ya dafe kansa yace "I just can't control my self ne" Amir yyi tsaki ya shige mota, Muhd ma ya bude motar a sanyaye ya shiga Amir ya tada suka bar layin. Ryynt na shigowa falo ta had'u da inna ta fito daga kitchen tace "Aa ina kika fito ne Rynh? ryynt dake kkrin boye hawayen fuskarta tace "na d'an fita ne kawai" snn ta nufi daki da sauri don xuwa yin kukan dake cinta ko xata ji ddi, wani mugun tsanar Muhd na mata yawo a xuciya.
  Washegari ya kasance lahadi Ryynt na kitchen tana soye soyen kajin da Abba ya aiko masu da shi safiyar ranan Baaba hurera na can bakin famfo tana wanki, inna kuma ta tafi anguwa  awanni biyu da suka wuce, gajiya ryynt tayi da soye soyen don wani mugun bacci kawae take ji gashi bata dad'e da farawa ba, tana kwashe Wanda ya soyu ta xuba wani ta xauna kan yar kujerar dake kitchen din ta jingina jikin bango ko minti biyu bata kara ba bacci me shegen nauyi ya dauketa, kiranta taji ana yi a nutse cikin bacci ta farka a tsorace lkci daya ta mike tsaye shi ma ya mike, kallonsa take har lkcn a tsorace tana son gane waye, ya sakar mata murmushi da ya bayyana fararen hakoransa, juyawa tayi da sauri tana kallon gas ta ganshi a kashe ta karasa gun da sauri don ganin suyan da take ta ga saura kadan ya qone, karasawa  yyi kusa da ita yace "don me baki bari kin tashi daga bacci ba kika yi aikin," bata basa amsa ba sae ma gaishesa da tayi ta soma kkrin kwashe naman dake cikin mai.






Dan Allah kuyi hqr da na bar ku kuna ta zuba ido wato kwata kwata sabo da posting d'in dare ya mantar dani yanda nayi daku.
      Gashi kuma yau na d'an samu kaina busy but am really sorry pls n pls 🙏🏻
Luv u all❤




Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮?🔮🔮🔮🔮🔮?```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```













               🔮🔮🔮🔮
*```Page 61```*
Tsaye kawae yayi yana kallonta har ta gama kwashe naman ta zuba wani snn ta kalle shi tace"nifa kasan ba gane ku nakeyi ba waye kai?
   Aamil da still kallonta yake ya lumshe idonsa a hknli ya kuma ware su akanta snn yace"Aamil ne"
  Tace"oh yi hqr ai na d'auka ko wancan d'ayan ne"
  Yayi murmushi snn yace"ba komai je ki qarasa baccin naki idan naman ya soyu se na kwashe maki ko"
Murmushi tayi had'e da girgiza kai snn tace"ai baccin ma ya tafi"
  Yace"eyyah sorry ashe da ban tashe ki ba"
Tace"ai ba komai dama karatu nake da niya idan na kammala suyar"
Yace"wae ke kam ba kya hutu ne Rynt"
 Ta kalle sa tace"uhm jarabawa fa zamu fara gobe"
  Yace"hkne fa gobe ne monday ko?
Ta gyad'a masa kai had'e da fad'in eh"yayinda ta d'auki abun tsama tana juya suyar da naman ya soyu ta kwashe suka koma falo Aamil yace ta d'auko littafanta ya taya ta dubawa.
  Ba musu taje d'aki ta dau'ko littafinta da za'ayi masu jarrabawar sa gobe.
  Sukayi zaune a nn tsakiyar falon yana mata tambayoyi tana bashi amsa cikin natsuwa shi kuma sae kallonta yake tayi dan gabad'aya ta tafi da hnklinshi  ganin komai ya tamvaye ta kai tsaye take bashi amsa da kuma bayani gamsasshe wanda har ya gama mata tambayoyi akan all topics d'in da ke cikin littafin en kurarra kad'an tayi ya gyra mata.
   Ya bata littafinta d'auke da murmushi a fuskar sa yace"na yaba da qoqarin ki sosai Rynt ina roqon Allah yasa kifi haka "
 Cikin nuna jin dad'i tace"Amin nagode"
Kafin Aamil ke cewa to d'auko wani  littafin sae mu duba ko"
  Kallon sa tayi cikin yanayi na shagwa6a da sam bata san tayi ba tace"Allah bacci nakeji sosai"
   Sae dai ya d'an jima yana kallonta kan yanayin shagwa6ar da tayi snn yace"ok jeki kiyi baccin"
  Tace"to"snn ta tashi ta tafi d'aki.
  A nn Aamil ya furzadda iskan bakin sa a hnkli tare da jingina bayansa a jikin doguwar kujera yana mae bin qofar Rynt da kallo dan ko kad'an bai so ta tashi ba.
 Inna da nasir ne suka shigo ya miqe had'e da amsa sallamarsu snn yaba nasir hannu suka gaisa ya kalli inna yace"wae inna dama ba kya nn ne?
 Inna tace"yo naji shashasha da to a gurin wa kazo da har baka san bana nn ba"
  Sae da yayi murmushi snn yace"inna gurin wa zan zo kuwa banda ke kawae dae da ban ganki ba na d'auka ko kina ciki kina bacci"
  Tace"au ai ka tambayi Rynh kaji inda nake ko kuma baka ga Ryynh d'in bane itama"
 yace"na ganta har ma mu kayi karatu yanzu ma ta shiga daga ciki zatayi bacci.
   Inna tace"wato kama ga Rynh sae baka tambaye ta inda nake ba dan ba ina uwarka ba ko"
  Er dariya Aamil da nasir su kayi snn Aamil yace"ko d'aya inna ba hk bane kin sani"
   Tace"to ya kabaro mutan gida?
 Yace"suna lfy ,ai ilham har so tayi nazo da ita sae gashi koda zan fito tayi bacci"
   Inna tace"ayyo ai sae kazo min da ita gobe idan zaka zo ko"
  Yace"to inna"kafin yake cewa ni zan tafi"
   inna tace"au ko gaisawa ba muyi ba har zaka tafi"
 Yace"inna akwai d'an wani  aiki da nake son naje gida nayi ne amma inshaAllah zan dawo anjima"
 Tace"to a dawo lafiya"
  Nan suka fita shida nasir wanda shima sae da yayiwa inna sallama kafin suke fita.

Washe gari man ne da Amir a bakin mkrntar su Rynt fake cikin mota sae ga Rynt ta fito gate wacce kai tsaye ta nufi motar drivernta da yazo d'aukar ta yayin da Amir ya kalli man dake kallon Rynt har ta shiga motar suka tafi bae ce komai ba sae jan tashi motar yayi yabi bayan su har suka iso gidan inna,
 Rynt da drivernta sam basu lura cewa ana bibiyar su a baya ba.
  Wacce koda ta fito motar hnklinta na gun Aamil da ta hango shigar sa gidan riqe da hannun er sa ilham ta kwasa aguje ta shiga gidan tana kiran ilham.

Ba shiri man dake cikin mota ya bud'e gambu motar zai fito Amir ya riqe shi yace"ya kake hkne wae"
  Cikin damuwa man ya kalle sa yace"kai baka ga yanda ta kwasa aguje bane bayan ba ita kad'ai bace ka sani"
  Yace"its all ur fault da ka mata ciki bayan kasan qaramar yarinya ce"
Rai 6ace yace"abinda  zaka ce knn"
 Amir yayi er dariya yace"yanzu dae meyasa muka biyota tun daga school har nn nida na d'auka ko da ta fito d'in nn zaka je ka sameta ne kuyi magana amma sae  naga kana kallo har wae taje ta shiga mota driver yaja suka tafi baka ce komai ba sae wani  biyo su da mukayi"
   Man yace"Amir dama fa ina so na ganta ne kawae"
    Amir yace"to ya zancen mgnr da muke son muyi da ita ne?
  Zan same ta anjima muyi maganar,
  A ina knn ?a nn gidan mana ,ta yaya tunda dae kasan yanzu bazata qara yarda ta fito ba,hkne zan sameta ne a d'akinta ,kana nufin cikin gidan zaka shiga knn? Eh ai ba yau na saba ba,hm amma kasan dae idan inna ta ganka baza ku kwashe ta dae dae ba ko, inshaAllah ma bazata ganni ba.
  Allah yasa cewar Amir man yace"Amin had'e da jan motar suka bar gurin.
  Rynt kuwa tana qwalawa ilham kira suka jiyo da ita har Aamil nn ilham taje da gudu jikin Rynt ta rungume ta yayinda Aamil yayi tsaye d'auke da murmushi yana mamakin yaushe suka san juna ne da har suka saba haka.
     Rynt d'auke da ilham ta qaraso gurin shi ta gaida shi ya amsa tare da fad'in ya exam?
Cikin sakin fuska tace"Alhmdlh"
Snn suka qarasa daga ciki yana mai fad'in "yaushe kuka san juna ke da ilham ne?
  Tace"ranar ne fa kawae da suka kawo wa inna yini"
  Aamil yayi murmushi had'e da jinjina kai don ya tuna rnr har wasa ya gansu sunayi.
  A nn Rynt ta fice d'aki da ilham yayinda shi kuma ya nufi d'akin inna yana mai jiyo Rynt dake tambayar ilham Sadiq fa? (cewa da d'an Amir).



 Da dare  mohd ne ya shigo gidan wanda kai tsaye d'akin Rynt ya nufa koda ya mird'a handle yaji sa gam a rufe ya dafe kai cikin damuwa had'e da kallon qofar inna ya nufi qofar a hnkli cikin sand'a ya leqa.
  Da sauri ya shiga d'akin ganin inna bata ciki sae Rynt dake kwance  kan bed riqe da littafi a hannunta ta kare fuskarta.
  Koda ya qarasa shiga d'akin yaji saukar ruwa a batroom alamar inna na ciki tana wanka yaje gab da Rynt had'e da d'auke littafin da ke kan fuskarta nn yaga ashe bacci take ,
ajiye littafin yayi gefe yana ta kallon fuskarta sae can ya maida duban sa a kan cikinta tare da d'aura hannun sa akai yana shafawa a hnkli Rynt ta motsa had'e da juya kwanciyar ta nn kawae yaji inna ta bud'e bathroom zata fito  ya tashi da sauri zai bar d'akin sae kawae makullin motar sa ya fad'i a nn tsakiyar d'akin bae iya d'aukar makullin ba ya fita sbd a lokacin har inna ta fito tana fad'in"waye ne?
 "Nine"cewar Amir wanda ya duqa tare da d'aukar makullin ,
inna tace"yau kuma zuwan dare aka min?
  Cikin sakin fuska Amir yace" na shigo ne kawae mu gaisa na tafi dan kan hanya nake"
 Inna ta washe baki tace"to sannu d'an albarka ai ka kyauta ya Maryam da sadiqu duk suna lfy dae ko.
    Yace"lafiya qalau suke"
Tace"madallah" kafin yake cewa" to inna a kwana lafiya zan tafi sae gobe idan na shigo inshaAllah"
  Tace"to a gaida gida Allah kai lafiya"
 Yace"Amin kafin yake fita.

 A wajen gate ya sami man jingine a jikin motar sa ya qarasa gab dashi yana kallon sa yace"u see yanzu da banzo ba fa ya knn kaida kace d'akinta zaka sameta shine ka wani  je ka sameta har d'akin inna"
  Man dake kallon Amir cikin damuwa  yace"Amir ban same ta d'akin ta bane shiyasa"
  Da baka same ta can d'in ba ai se ka haqura har gobe ba wae kaje d'akin inna ba,Amir wane irin haquri ka kuwa san irin yanayin da nake ciki ko kuwa don ba kai bane.
   A natse Amir ya kai hannu ya dafa shi yace"man duk da bani bane na fhmci irin yanayin da kake ciki sosai amma zan fi so kabi komai a sannu  har ka cimma yin nasarar shawo kanta.
   Hakane amma dae kasan bazan iya haqura ba sae na dawo gobe ko,ai ba wae nace kar ka dawo gobe bane a sannu nace kabi komai ta yanda har ka samu ka shawo kanta ba a sami wata matsala ba but anjima da yamma zan rako ka muzo kai sae ka tsaya a qofar gida ni kuma se na shiga dmn naje na samu na janye hnklin inna da fira zuwa d'akinta so a nn zan maka flash sae ka shigo kaje d'akin Ryynt sae kuyi magana.
   Man ya sauke ajiyar zuciya yace"shike nn"
  Nan Amir ya bashi makullin motar sa  man ya kar6a ya shiga motar yayinda Amir yaje ga tashi motar ya shiga suka bar qofar gidan.


Da yamma sae ga su sun dawo kamar yanda suka tsara man ya tsaya a qofar gidan shi kuma Amir ya shiga daga ciki.
  Bai wani  jima ba sae gashi ya dawo jiki sanyaye,
 mohd yayi saurin qarasawa gurin sa yace"ya akayi ne?
  Amir yace"Rynt d'in bata da lafiya"
 A rud'e man yace "me yake damunta ne?
  Amai take tayi sosai kuma byn ya tsaya mata sae fmn yunqurin aman take baya zowa duk ta wahala sae kuka take.
  Cikin damuwa sosai mohd ya dafa Amir yace"Amir dan Allah muje na ganta"
 Amir yace"ka ganta fa kace?
Eh mana Amir to so kake tayi ta fmn wahala ne baka tsaya ka duba ta ba ka wani  zo kana gaya min .
 Calm down laulayi ne fa ka sani baya da magani,
Don baya da magani  sae a bar yarinya tana wahala gsky ni shiga zanyi koma me zai faru sae dae ya faru! yana gama fad'ar hkn ya tafi fuuu! zai shiga gidan.....
Amir ya riqe sa yace"kaga dakata ai ba wae haka kawae za'a barta ba inna tace idan tasha agwalima abun zai mata sauqi so agwalimar ce aka rasa bcs babu ita a gidn kuma ta kirà nasir ta snr dashi bata same sa ba.
 Ni kuma ba sanin inda ake saeda agwalimar nayi ba shiyasa na fito dmn na snr da kai.
  Man yace" kaga yi sauri da Allah shiga mota muje koma a ina ne ai ma samota.
  Nan suka shiga mota mohd yaja suka tafi sae bin gari suke guraren da ake sae da fruits amma basu samu ba sae can kan hanya suka had'u da mai agwalima man ya tsaida mota suka fito sae gun mai agwalima,
Man yace"malam nawa gabad'aya agwalimar taka take ne "
  Da sauri Amir ya kalli man yace"kai kana haukane muda baza mu wuce siyen ta d'ari biyu ko uku ba kake zancen gabad'aya ai sae ta lalace bata kai ga shanye ta ba ma"
   Mohd yace"taya zata lalace bayan a fridge za'a zuba kaga malam juye min agwalimar ka kaf a leda ka fad'i kud'in ka na baka"
  Dariya Amir yayi yace"haba man aikin hnkli dae"
Snn yace da mai agwalima"malam yi hqr sa mana ta d'ari biyar kawae ta isa"
   Nan mai Agwalima ya shiga qirga agwalima yana sakawa a leda yayinda man ya kalli Amir cike da niyar magana Amir ya riga sa da cewa"kar fa ka manta tana can tana fmn yunqurin amai idan muka qara 6ata lokacin mu a nn zata wahala da yawa ne"
  Nan man ya fasa maganar da yayi niyya  ya maida duban sa gun mai agwalima da ya gama saka ta d'ari biyar a leda ya bawa man ya kar6a yayinda Amir ya ciro dubu d'aya a aljihu ya bawa mae agwalima yace ya riqe canjin kawae,
 nn mai agwalima ya washe baki yana musu godiya su kuma suka shiga mota suka bar gurin sae gidan inna.
  Wanda da isar su Amir ya fito da sauri riqe da ledar agwalimar ya shiga gidan.
  Kusan minti goma da shigar sa ne ya fito ya sami man sae kai komo yake a qofar gidan yana ganin Amir yace"ya ake ciki ne ta daina yunqurin aman? Eh har ma ta shiga bathroom zata d'an watsa ruwa"
  A nn man ya fitar da ajiyar zuciya yace"olryt amma dae zamu dawo anjima don na samu naga yanda jikin nata yayi ko"
  Amir yace"shikenan Allah kaimu".
  Daga haka suka shiga mota suka bar layin.

Ana fitowa masallaci sallr isha'i sae gasu sun  dawo gidan ,Amir ne ya shiga wanda bayan en mintina kad'an da shigar sa gidan ne man yaga flash d'insa a nn ya shiga gidan ya nufi d'akin Ryynt kai tsaye ya sameta kwance  kan darduma ta idar da sallah idanunta a rufe kmr mae bacci.
 Nn yaje ya durqusa gab da ita tare da d'aura hannun sa a kan gefen fuskarta,ta bud'e idonta a tsorace tare da saurin tashi zaune tana kallon shi ya sake mata d'an guntun murmushi ita kuwa lokaci d'aya tasha masa toka dan ta fhmci mohd ne sbd qamshin turaren sa da taji.
  Fuskar ta a murtuqe ta miqe zata bar d'akin mohd ya jawota zuwa jikin sa bata yi yunqurin qwatar kanta ba sae goshin ta da tayi saurin kai hannu ta dafe sbd kanta da taji yayi mugun sara mata.
   Cikin damuwa mohd ke kallonta dan ya fhmci irin ciwon kan da take d'auke dashi nn ya tafi da ita kan bed suka zauna ya kwantar da kanta a qirjin sa had'e da kai  hannu yana murza mata goshin nata a hnkli, Rynt kuwa se  hancinta ta shiga cusawa a hnkli cikin rigar sa sbd wani irin qamshin dad'i da taji turaren sa na mata.
   Man bae hana ta ba sae kallonta da yake har ta shigar da hancinta gabad'aya cikin suit jacket d'in shi.





Billy giro😊?🔮
?```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```







_wuhuu!Really! Really!!Really!!! appreciate! my dearest family, Aunty zygiro,Nanà giro, Shamsiya giro,Hafsat giro,Apeeya giro n Rayyanat giro wnn page in naku ne  and these hearts goes to u ❤❤❤❤❤❤_


               🔮🔮🔮🔮
*```Page 62```*
Sun jima a haka d'akin tsit kmr ba kowa mohd ya katse shirun yayin da ya shafo bayanta yace"ina son zanyi magana dake kinji"
Nn yaji shiru ba amsa yakae hannu ya d'ago fuskarta yaga ashe tayi bacci abinta.
   ya lumshe idonsa a hnkli yana kallon yanda ta koma maida fuskarta a qirjinsa ta lafe sosai kmr wacce zata sha mamma.
Nan kawae ya d'aura hannun sa kan cikinta yana ta kallonta lokaci mai tsawo se can ya tashi ya kwantar da ita kan bed  ya kama hanya zai bar d'akin sae kawae yaji qarar waya nn ya tsaya da d'an mamaki yana kallon wayar Rynt dake fmn ruri kan bedside drawer a hnkli ya qarasa gun bedside drawer d'in ya d'auki wayar yana mae kallon Rynt snn  ya kalli mae kiran wato Sarah bayan kiran ya tsinke ne ya danna wasu lambobi ya kira nn wayar sa dake  cikin aljihu ta shiga ruri ya katse kiran ta jikin wayar Rynt snn ya maida wayar ya ajiye kafin yake ciro tasa  wayar a cikin aljihu yayi saving number d'in Rynt ya fito falo zai bar gidan yana mai jiyo sautin firar inna da Amir .

Bayan ya fita ne Amir dake ta fmn ci gaba da jan inna da fira yaji shigowar text a wayar sa koda ya duba mohd ne ,
sae da ya d'an qara lokaci snn yayiwa inna sallama ya fito ya sami mohd jingine a jikin mota yace"Hope ta amince"
  Mohd yace"no ko mgnr ma ban samu nayi da ita ba tayi bacci but i got her number zan kirata sae muyi magana a waya"
  Amir yace"to shikenn ai haka ma yafi"
 Daga haka suka shiga mota suka bar gurin.

Mohd na komawa gida ya rage kayan jikin sa ya fad'a bathroom wanda sae da ya kwashe kusan awa d'aya kafin yake fitowa sanye da white bathrobe ya nufi fridge ya bud'e ya ciro fresh milk ya tsiyaya a cup yaje ya zauna kan sofa ya jingina bayan sa tare da d'aura qafafunsa kan footstool ya fara shan fresh milk cike da tunanin idan Rynt bata amince da zancen sa ba wace hanyar kuma zai bi.
    Yana cikin hakane malika ta fad'o d'akin ya kalle ta kawae ya kauda kai taje gab dashi ta zauna had'e da riqo hannunsa tana kallon sa snn tace"my man umma ce bata jin dad'i shine nake son naje na dubo ta"
  Hannunsa ya zare daga nata yana kallonta shaye da toka.
 Ta wani maràiraice fuska tace"ba wani  jimawa zanyi ba dan ko 10  bazan kai ba pls kaji?
  "Ba inda zaki je"
 Pls my.....bata iya qarasawa ba sbd wani  irin mugun kallo da ya mata had'e da nuna mata qofar fita d'akin.
 Rae 6ace ta tashi ta fita d'akin taje d'akinta.
  Wacce da shigarta ta jawo wayarta ta kira ana d'aga wayar  ne tace"wlh d'an banzan bai bar ni ba ka bari kawae gobe idan ya tafi aiki zan zo na same ka.......tana kaiwa nn ta katse wayar ba shiri tana kallon man dake tsaye a bakin qofar d'akin ,
ya qaraso gurinta yana mata kallon tuhuma snn yace"da uban wa kike waya!?
   Malika dake kallon sa a tsorace ta samu da qyar tace"umma ce fa......bana son raini meyasa to da kika ganni kika katse wyr a tsorace iye!
  Banga shigowar ka bane sae ganin ka da nayi shiyasa na tsorata.
 Cikin kallon tuhumar da yake binta dashi ya kai hannu ya fizge wayar hannunta ya shiga call logs ,sweetheart2 shine last call nata ya kalle ta kawae ya cillar da wayar kan bed ya fita sbd sweetheart shine sunan da tayi saving number d'in mamarta dashi ,
sweetheart2 kuma numbar gayen da ta gama yawa da shine,shine man ya d'auka ko wata number mamar ta sake yi shiyasa ya fita kawae ya barta.
  Malika kuwa man yana fita ta dafe qirji had'e da fitar da wani irin numfashi na ganin bae gano ta ba.

 Rynt kuwa tana cikin baccinta mae dad'i taji inna tana qwala mata kira ta tashi firgigit tana kallon inna da ta shigo d'akin snn ta kalli inda take kwance  tana d'an dube dube a d'akin inna tace"me kike nema ne?
  Tace "ba komai"
Inna tace "to tashi muje d'aki ki kwanta ko"
  Ba musu Rynt ta tashi had'e da d'aukar wayarta da kuma littafinta da suke da jarrbawar sa gobe don tana son da dare idan ta farka tayi karatu.
   Nan suka rufo d'akin suka fito wacce da shigar su d'akin inna ko hijabin jikinta bata iya cirewa ba ta fad'a kan bed ta ci gaba da baccinta.
  Ba ita ta farka ba sae
11:40pm ta tashi a hnkli had'e da bisimillah tana miqa taje bathroom bata jima ba ta fito ta koma kan gado ta zauna tare da jawo littafinta ta kunna fitilar wayar ta tana karatu.
  Tana tsaka da karatun ne wayar ta ta shiga qara tayi saurin sakata a silent tana kallon numbar da ke yawo akai, d'auke da mamaki a fuskarta na ganin baquwar numbar da bata sani ba kuma da daren nn.
  Kiran na gab da tsinkewa ne tayi saurin d'aga kiran dan a take ta shiga tunanin  ko Sarah ce.
   Sae dai duk da hkn bai sa da ta d'aga wayar tayi magana ba se shiru tayi tana sauraren muryar da zata ji.
  A natse taji ance "kin tashi?
  Bata ce komai ba sae shan toka da tayi dan lokaci d'aya ta gane muryar mohd ce yayinda ta shiga tunanin a ina ya sami numbar ta,
 ya katse ta da cewa"kina jina mijinki ne mohd ina son zanyi magana ta fhmta dake ne kinji"
  Kmr yana ganin ta ta qara murtuqe fuska,murya can ciki tace"nifa ynx karatu nakeyi bani da wnn lokacin"
   Yace"kun fara exam ne?
A qufule tace"eh"
Yace"olryt gobe zan kira ki idan kin dawo daga school"
  Komai bata ce dashi ba ta katse kiran taci gaba da karatun ta.

Washe gari da yamma Rynt na zaune a falo ita da Aamil yana mata tambayoyi akan littafin da zasu yi exam next day.
   Wayar Rynt dake ajiye gefe ta shiga qara Rynt ta kalli wayar kawae ta kauda fuskarta don ta fhmci numbar mohd ce Aamil dake kallonta yace"ya baki d'aga kiran ba?
 Tace"ba komai kawae bana son in katse karatun da muke yine"
   Bae ce komai ba suka ci gaba da aikin su har kiran ya tsinke aka koma kira Rynt ta kalli wayar had'e da  kai hannu zata d'auki wayar se kawae wayar ta nuna battery low ta mutu hkn ya mata dad'i dan dama niyyarta tana d'aukar wayar katse kiran zatayi ta kuma kashe wayar gabad'aya.
    Aamil da har ya soma jin haushin mae kiran dan hk kawae ransa ya basa cewa namiji.
  Ya kalli Rynt kmr wanda zae ce wani  abu sae kuma ya fasa suka ci gaba da yin karatun su kawae.

Bayan sun gama karatun ne ta saka wayarta a chaji da dare tana shirin bacci wayar ta ta shiga ruri tana ganin mohd ne mae kiran ta buga  tsaki ta d'aga wayar had'e da fad'in"wae me?
   Mohd yace"kan me d'azun na kiraki baki d'aga ba da qarshe  ma dan kin rainani kika kashe wayar ko"
     Komai bata ce ba sae tsaki da tayi ta kuma cillar da wayar kan bed taje taci gaba da shirin baccinta shi kuma se magana yake tayi ba amsa har sae da ya gaji ya tsinke wayar.
    Sae da ta gama shirinta tsaf snn ta d'auki wayarta ta fito ta rufe d'akin ta tafi d'akin inna.
 Washe gari da safe ta fito daga wanka knn mohd ya kirata kallon wayar kawae tayi ta kauda kai taje ta jawo Vaseline tana shafawa , tana ji har yayi kusan 3 missed calls bata d'aga ba wacce tana gama shirinta ta kashe wayar ta jawo drawer ta saka wayar a ciki snn ta d'auki school bag d'inta ta bar d'akin taje d'akin inna tasha fura a gaggauce ta fita.

 Mohd kuwa rashin d'aukar wayar Rynt ba qaramin 6ata masa rae yayi ba shiyasa tun daga rnr bae sake d'aukar wayarsa da sunan kiranta ba har kuwa aka kwashe kusan sati d'aya sae harakar gabansa yake haka ma Rynt wacce yanxu wata irin shaquwa ce ta ban mamaki ta shiga tsakanin ta da Aamil wanda yanzu shi ke kaita school ya kuma je ya d'auko ta wani  lokacin ma har d'aukar ta ya ta6a yi suka je  shopping da dare ya kwaso mata kaya niqi niqi tamkar bai ta6a sanin meye zafin kud'i ba inna dae sae kallon su take dan duk a tunaninta Aamil tausayawa Rynt ne kawae yake.

Rnr litinin da yamma Man ne tafe cikin mota shida Amir yayinda Amir ke cewa"gsky man ka fiye gajen haquri dan kawae ka kirata taqi ta d'aga sae kawae ka fita harakarta "
  Man yace"hm Amir knn ta yaya kake tunanin zan iya fita harakarta bayan ina sonta ina kuma son abinda ke cikinta,just na bata lokaci ne har ta gama nata ikon kafin nake fara nawa ikon.
  Amir yace"ta yaya yarinyar da ko saurararka taqi tayi?
  Shiru mohd yayi dan baya son kowa yasan abinda ke ransa na d'auke Rynt da zai yi ya tafi da ita waje.
  Amir kuwa bae sake ce masa komai ba har suka iso gidan shi ya bud'e gambun motar zai fita Man yace"ka shirya anjima byn sllr isha'i zan zo na d'auke ka ka rakani muje gidan inna"
  Gurin Rynt zaka je ne?
  Ba tare da ya kalle sa ba yace"eh"
 Amir ya fita had'e da fad'in"sae ka zo"snn ya rufe gambun motar ,
man kuwa yaja motar tasa ya tafi.


6angaren su Aamil kuwa Rynt ce ya d'auko daga school ya kawota gidan inna ya ajiye ta wacce kafin ta fita motar sae da ta kalle sa d'auke da murmushi a fuskarta tana mae godiya shi kuma cikin sakiñ fuska ya lumshe ido had'e da ware su a kanta snn yace"ki gaida inna zan shigo anjima "
tace"to"snn ta tafi sae shillo take da ledar agwalimar da ke hannun ta wacce ya saya mata.
  Aamil kuwa a maimakon yaja motar sa ya tafi sae kallonta yake tayi cike da tunanin yau zae kawo qarshen haqurin sa dan anjima idan ya dawo kai tsaye zai je ya gaya wa inna abinda ke ransa na game da Rynt koma kawae zae je ya sami Abba ya gaya masa dan inna tasan cewa lallai da gaske yake.
  Da tunanin hkne yaja motar sa ya tafi.

Rynt kuwa tana shiga gida tayi wanka taci abinci tayi zaune a d'akinta ta tasa agwalimar ta gaba tana sha a nn ta miqa hannu ta bud'e drawer dan nn inda take zaune da drawer ba nisa ta ciro wayarta ta kunna sae kawae taji shigowar text murmushi tayi ganin Aamil ne ya turo saqon wacce ta san ba komai bane face kati don kullum sae ya turo mata katin dubu d'aya, hkn kuwa na mata dad'i sosai don sae ta kira en uwa da abokan arziki suyita waya wato Sarah da kuma umman saliha wacce bayan sun gama waya da ita sae ta bawa mami,suyi ta waya da Rynt cike da nishad'i suna dariya.

Da dare bayan isha'i Rynt ta idar da sallah  ta miqe had'e da linke darduma ta saka a wardrobe ta kai hannu zata cire hijab bata cire hijab d'in ba sae tsaye tayi tana kallon cikin ta da har ya d'an fara turo hijab ,
a hnkli ta d'aura hannunta kan cikin sae kuma tayi saurin d'auke hannun ba shiri sbd motsa mata da taji yayi cikin takaici mai d'auke da alamar zata yi kuka takai hannu tana doka cikin.
  Mohd dake tsaye a bakin qofa yana kallonta ya qarasa gurin ta da sauri har yana hard'e qafa ya riqe hannuwanta duka biyu ya kalle ta rae 6ace yace"kinyi haukane idan kika kashe abinda ke ciki fa"
  Shaye da toka ta ture shi tace"dan ya mutu sae me ko ce maka akayi dama barin sa zanyi!
    A fusace ya fizgota zuwa jikin sa yace"wlh  idan har na koma jin kince zaki cire cikin nn zanyi mugun sa6a miki"
  Tace"wlh sae na cire cikin nn kayi abinda zakayi"
  Rufe bakinta keda wuya taji saukar duka a bakin nata wanda zama d'aya ya 6are da jini ,
sosai ta fashe da kuka tana kallon jinin da ta shafo a hannun ta.
   Man kuwa sae farin  handkerchief d'insa ya zaro zae share mata d'an jinin da ke gefen bakinta, ta buge masa hannu tana masa muguwar harara tare da fad'in mugu Allah ya isana wlh.
   Ta qarashe maganar ne cikin muryar kuka sosai ,komai man bai ce mata ba sae janta yayi tana fmn fizge fizge har yaje da ita kan bed suka zauna taje zuwa tashi ya maida ta had'e da rungumeta yakai bakinsa saitin kunnen ta yana gaya mata magana cikin natsuwa, a nn ta d'ago ta kalle shi tace"da gaske kake yi"
  Yace"eh"yayin da ya maida ta kan qirjinsa ya kwantar,sae ga Aamil ya fad'o d'akin ya tsaya da mugun mamaki yana kallon man da ya d'ago fuskar Rynt zai had'e bakinsa da nata yaga bata hana shi ba sae ma lumshe idonta da tayi har man yakai ga saka harshen sa a cikin bakinta.
    Aamil cikin rud'u da kuma mamakin da yake d'auke dashi ya shiga ja baya har ya fita d'akin ya nufi d'akin inna dmn jin shin wace ce Rynt❓



Dan Allah Kuyi haquri da fmn jirana da kukayi tayi jiya kuma sae gashi baku samu ba .
Then
Ku qara min afuwa dmn gobe bazan samu yi ba sbd tafiyar da zanyi.
   Luv u all❤


Billy Giro 😊?🔮
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```













               🔮🔮🔮🔮
*```Page 63```*
   Aamil na fita d'akin Rynt ta zare bakinta cike da jin kunya ta kwantar da kanta a hnkli kan qirjinsa tana shaqar qamshin turaren sa.
   Shi kuma mohd sae wani  qara kwantar da ita yayi a qirjin nasa yana mae shafa bayanta a hnkli cikin natsuwa.
  Aamil kuwa yana shiga d'akin inna ya sami Abba da zuwansa knn ko zama bai yi ba sae Amir da ya samu ya zame kan kujera yana gaida shi bai kula su ba sae gun inna yaje a rud'e wacce taje zuwa bud'e fridge knn yace"inna zan so naji wace ce Rynt kuma ya take da mohd da na gansu a d'aki tare"
 Abba dake kallonsa yace"mohd fa kace a gidan nn!
 Aamil bai iya cewa komai ba sae kansa da ya gyad'awa Abba cikin rashin fhmtr yanayin da yaga Abba ya shiga ciki wanda yaga ya tafi fuuuu! a fusace yana fad'in lallai kuwa yau zan nuna masa haifo sa akayi ba haifar kansa yayi ba!
A nn Man da Rynt suka tsinkayo muryar Abba tafe hkn yasa suka miqe tsaye zumbur sae ga su Abba,inna, Aamil da kuma Amir duk sun shigo d'akin,inda kai tsaye Abba ya nufi mohd ya watsa masa mari biyu masu kyau ya kuma nuna kansa da yatsa yace"dan uwarka ni zaka mayar d'an iska ko kuwa shima nn gidan ban hanaka shigowa bane iye!
 A natse mohd ya kalli Abba cikin damuwa sosai yace"dan Allah Abba....kaga yi gaggawar fita a nn  kuma duk ka kuskura na koma ganin qafar ka a nn gidan ko a gidana to kuwa zan furta abinda baka ta6a tsammanin zan furta a gare ka ba!
  mohd ya kalli Abba d'auke da idanuwansa da suka kad'a  sukayi jajur yace"dan Allah Abba kayi haquri ka saurare ni wlh nazo ne dmn na bawa Rynt haquri na maida ta..... Kul!har abada Rayyanat baza ta ta6a komawa gare ka ba don ba shashashan mutum bane ni da zan aura ma ita ka sakota ka kuma yi tunanin zan barka ka maida ta,
Mohd yace"Abba itama fa tana son komawa"
  Nan Abba yayi saurin kallon Rayyanat wacce ke kallon mohd shaye da toka yace"Rynt abinda yace hakane?
 Ta kauda fuskarta da kallon da take yiwa mohd  had'e da girgiza kanta snn tace"Aa Abba gsky ni bana son komawa"
 Abba ya kalli Man dake kallon Rynt yace"maqaryacin banza shashasha fita a nn in daina ganin ka!
Mohd da ya duqar da kansa qasa yace"pls Abba dan Allah ko don abinda ke cikinta ka bar ta ta koma"
 Kafin Abba yace "komai Inna ta riga sa da cewa" bafa zata koma ba shashasha marar mutunci idan har dan abinda ke cikin ta ne da ta haife shi zata baka abunka kaje can ka qarata dashi dan baza ta raina maka shi ba karatun ta zata ci gaba dayi.
 Abba yace"Ba ma wnn kad'ai ba inna Aamil yaje min da wani  zance na yana son zai auri Rynt na kuma yi na'am da zancen nasa dmn  Aamil mutum ne da nsn zae  riqe ta amana ko da kuwa ace baya sonta aka aura mae bare shi da kanshi yace yana so da haka na yanke shawarar idan Rynt ta haifu zan had'a aurensu sae taci gaba da karatun ta a can d'akinta.
  Tun lokacin da Abba ya fara zancen sa mohd ya shiga wani  irin tashin hankali yana kallon Aamil cikin mugun mamaki haka ma a gurin Amir ,Rynt kuwa banbarakwae taji zancen ta bud'e ido tana kallon Aamil yayinda  Aamil duk ya sukuikuice yana kallon Abba cike da son cewa wani  abu.
 Sae dae kafin suce komai sae kukan kura suka ji mohd yayi zai afkawa Aamil Abba ya dakatar da dashi ta hanyar ture shi had'e da kife sa da mari yace "dan uwarka borin kunyar ne zaka saukar akanshi dan zae min abinda kai ka kasa min,to bari kaji Aamil yafi min kai sau dubu dmn yau ya yaye min duk wani  baqin ciki da na shiga a knka,kuma aure shida Rynt ba fashi!
A nn Idanuwan mohd suka qara yin jajur har ana hango jijiyoyin goshinsa duk sun tashi yace"Abba wane irin zance ne wnn ace Aamil zai auri Rynt....gaya min inda yake haramun dan Aamil ya auri matar da ka saka!
Kmr zae yi kuka yace"haba Abba wnn ai abin kunya ne aji cewa wae Aamil zae auri matar da na saka kuma ai Abba ni wlh na mai......cikin daka tsawa Abba yace"kaga maza fita  bana son sake jin zancen ka a nn idan ba haka ba wlh kasan sauran shashasha kawae!
  Mohd bai iya fita ba sae wani irin mugun kallo da yake yi wa Aamil kmr zae je ya bugoshi dan jikin sa har ya soma rawa ma sae Amir ne yayi saurin jan hannunsa suka fita  yayinda shi kuma Aamil yaja hannun inna suka tafi d'aki,Abba kuwa gun Rynt ya tsaya dmn jin ra'ayin ta wacce ya kalla a natse yace"Rynt gaya min gsky kina son komawa gidan mohd koh?
 Tace"wlh Abba bana so"
  Yace"to kina ganin zaki iya auren Aamil bayan kin haifu?
  Shiru tayi sbd shirin da take yi da Aamil muqaddari ne da ta samu kanta dashi haka kuma bata da tabbacin wanda ya kashe mata baffanta a cikin su ukun ,
kawae dai tafi zargin cewa mohd ne.
 Abba dake kallonta jin shirun yasa ya bud'e baki zuwa magana sae kawai wayar sa tayi qara ya ciro wyr a aljihu ya d'aga yayinda ni kuma na garzaya gun su inna dmn jin abinda Aamil zai ce da inna.
  Cikin yanayin damuwa sosai na samu Aamil yana cewa da inna"inna wlh kwata kwata ban gane cewa Rynt matar man bace shiyasa naje wa Abba da zancen cewa ina son zan aureta, ba wae dan nasan cewa sun rabu ba"
  Inna ta sauke numfashi tace"to Aamil ynx dan kaji cewa mtr da muhammadu ya saka ce meye matsala ko kuma sonta ne kaji ba kayi da kaji cewa ta ta6a aure har tana d'auke da juna biyu"
  Ko d'aya inna ba ciki ba ko 'ya'ya goma ne da Rynt ni mae iya aurenta ne amma kasancewar ta mtr da man ya saka ce yasa bazan iya auren ta ba  inna"
 Aamil inace ba haramun bane dan muhammadu ya saki Rynt ka aura ,
Aamil yace"duk da haka dae inna ana barin halak dan kunya dmn man jini na ne da bazan iya masa haka ba"
 Inna tace"Dan muhamadu yana jinin ka shi kuwa ubanka kabiru da yake ikirarin ka wanke mai baqincin da yake d'auke dashi fa ko kowa kaima so kake ka watsa mae qasa a ido ne iye!
ko d'aya inna bana son haka amma na fi son Abba ya haqura ya bar man ya maida matar sa tunda har ya nuna yana son maida ta"
 Inna tace" Rynt fa bazata koma gidan muhammadu ba dan kaji in gaya ma idan kai d'in bazaka aureta ba ai bazata rasa wani  masoyin ba"
Aamil ya fitar da numfashi yace"dan Allah inna me yasa ba kwa son ta koma ne?
  Ajiyar zuciya inna ta sauke kafin take bashi kaf labarin abinda ya faru tsakanin man da Rynt. 
Nan Aamil ya jima shiru yana tuna lokacinda inna ta mari man har abin ya d'aure masa kai wanda sosai yaso yaji dalilin faruwar hakan amma kuma sae bai san ya akayi bae tambayi dalilin ba,haka kuma ya tuna lokacinda ya shiga d'akin Rynt ta mai ihu a tunanin ta man ne kuma duk ta ganshi sae taji waye tukun kafin take sakewa dashi,ko hkn kad'ai abune da ya kamata ace ya fhmci wani  abu amma kuma sae bai fhmta ba ,sae yanxu da inna ta bashi lbr.
 Aamil ya ajiye tunanin sa da kallon inna yace"a gsky inna mohd bai kyauta ba amma tunda yayi nadama ayi haquri abar shi ya maida ta"
Inna tace"yo wa ya gaya ma nadama ce yayi kawae yana son abinda ke cikin Rynh ne dmn na tabbatar idan muka barta ta koma to kuwa ina gaya ma da ta haife mae abinda ke cikinta zaici gaba da wulaqanta ta ne,amma kai nsn zaka riqe Rynt amana tun da har ka iya riqe khadija tsawon lokaci ba'a ta6a jin kanku ba duk da kuwa cewa auren had'i ne a tsakanin ku da ita ba wae dan kuna son juna ba.
Aamil kam baya ko jinta dan yayi shiru yana tunanin shidae a ganin sa mohd ba don cikin sa kad'ai ne yake son Ryynt ta koma ba,dmn ya fhmci sosai mohd ya shiga damuwa a lokacinda  Abba yace idan Rynt ta haifu zai had'a auren sa da Rynt.
Kuma ko abinda ya samu yana mata a d'aki abune dake nuna soyayya a tsakanin su, sae dai kuma Rynt d'in ce da ban mamaki da tace bata son komawa gidan mohd ko meyasa?
  Baya da amsa kan dole ya sauke numfashi ya kalli inna yace"shike nn inna zan yi shawara"

 Inna ta washe baki tace"to ko kaifa d'an albarka"
 Shidae Aamil komai bai ce ba sae fita da yayi ya had'u da Abba ya fito d'akin Rynt ya sadda kansa kawae ya wuce zuwa d'akin Rynt Abba kuwa ya shiga d'akin inna,wanda sae da ya nemi guri ya zauna snn ya kalli inna dake zaune kan gefen gado wacce ke kallon sa tana fad'in"da kmr magana ka tsaya yi da Rynh  ko?
Abba yace"eh inna hkne na tambaye ta ra'ayin ta ne kan had'a aurenta da Aamil sae bata iya cewa komai ba tamin  shiru, daga baya da nace ko bata ra'ayin auren ne, tace ita a gsky tafi so tayi karatu, nace indai karatu ne kar ta damu dmn Aamil mai barinta ne ta qarasa karatun ta cikin jin dad'i da kwanciyar hnkli amma idan tafi son sae ta kammala karatun to,
sae ta min shiru kuma bata ce komai ba shine na fito na barta dmn na fhmci shawara take a ranta kmr wacce na fhmci yanzu tsoron aure take ganin irin wahalar da tasha a gun mohd shine take ganin kmr duk inda taje hkne.
  Inna tace"dole ne fa tayi wnn tunanin amma ni mai fhmtar da ita ne sannu sannu har ta fahimci cewa ba duka a aka taru aka zama d'aya ba.
  Abba yace"to shikenn inna ni zan tafi Allah sa a dace"
  Tace"Amin d'an albarka Allah kiyaye hanya a gaida gida yace"to"snn ya fita.

  Aamil kuwa a lokacin da ya nufi d'akin Rynt sae da yayi sallama Rynt ta amsa mar snn ya shiga ya sameta zaune gefen gado kanta qasa yace"Rynt dan Allah kiyi haquri sam ban gane ki ba bare na fhmci cewa ke mtr man ce shiyasa kika ji wani  irin zance a bakin Abba da yake farin ciki da shi amma ni tunda na fhmci wace ce ke banida farin cikin da ya wuce ki koma d'akin ki, kiyi haquri ki manta komai kije ku gina sabuwar rayuwa keda man dmn nafhmci dgske yake son maida ke sbd irin damuwar da naga ya shiga a yau ban ta6a ganin sa a cikin irin ta,kuma ko don qaruwar da ke tsakanin ku ya kamata ace kinyi haquri kin koma kinji"
  Muryar can ciki tace"to"
Dan kawai ta samu ta huta dashi dmn ita sam bata son jin ana zancen qaruwar da suka samu tsakanin ta da man abinda ko yaushe ftr ta taga an cire cikin ta huta amma sae wani zancen sa ake mata.
  Aamil dake kallonta yace"naje na gaya ma Abba kin amince zaki koma gidan mohd d'in?
  Tayi saurin kallon sa had'e da girgiza kai snn tace"sae nayi shawara tukun"
 Yace "shikenn idan kin gama yanke shawarar sae ki gaya min"
  Ta gyad'a masa kai kawae shi kuma ya fita ya bar d'akin.


6angaren su mohd kuwa a lokacin da Amir  yaja shi suka fita da qyar ya samu mohd ya shiga mota wae a cewar yau in shi in Aamil dole a kwashi gawar d'ayan su don ba zai ta6a yarda ya auri Rynt ba sae dai ko idan da gawar Aamil za'a d'aura auren to zae gani.
  Shine Amir ya samu da qyar da lallami ya kaisa gida ya dawo kan hnya sae mamakin Aamil yake da kuma mamakin Abba da ya yarda zai ba Aamil Rynt ya aura.

Guraren goma Amil ya tafi gidan Amir wanda yazo masa shaye da toka yana kallon sa  Aamil ya sadda kansa qasa kawai ya shiga mai bayanin komai kan cewa shi bai san cewa Rynt mtr man bace shiyasa yajewa Abba da zancen yana son zai aureta ba wae dan yasan sun rabu ba.
  Tun lokacinda Aamil ya fara  zancen sa Amir ke kallon sa da mamaki se can yace"shine matsalar kai kwata kwata ba ruwanka da kowa bare ka san wnn waye ya kuma yake damu abinda kasa ma gaba kawae ka damu dashi wace irin rayuwa ce wnn kuma inace damu akayi bikin su kuma har gidan sa munje byn auren wanda muna zaune ta biyo ta wuce har ta gaida mu,haka ma a gidan inna mun had'u da ita ka sani,
  Aamil yace"Amir wlh sam ban gane ta ba kawae dai d'ayar matar sa na sani malika da dama nsnta kafin auren.
  Amir yace"to naji yanzu ya kake so ayi bayan duk kabi ka qara lallata komai"
  Wàto Amir so nake ka raka ni muje gurin man na masa bayani na kuma basa haquri.
  Amir ya girgiza kai snn yace"let tomorrow dan yanzu idan mukaje komai zai iya faruwa sbd ransa a 6ace yake sosai ba zai ta6a saurararka ba.
  A sanyaye Aamil yace"shikenan Allah kaimu goben"
  Amir yace"Amin"
Snn sukayi sallama kowa ya kama gabansa.

Washe gari da safe Rynt ce cikin shirin makarantar ta tsaf riqe da kofin tea a hannunta ta kasa sha don tun jiya har yau ta kasa sakewa sae tunani take tayi inna kuwa lalla6a ta shiga yi ta samu har tasha tean byn ta gama sae ga Aamil ya shigo gidan zai kaita school wanda ba don komai yake son ci gaba da kaita school ba sae don ya samu ya riqa bata magana har ta amince da komawar ta gidan man .
  Inna na ganin Aamil ta washe baki suka gaisa cikin sakin fuska yayinda Rynt ta gaida shi ba yabo ba fallasa.
   Snn suka fito suka kama hanyar makaranta.
  Suna cikin tafiya ne sae kawai Aamil yaga motar man tasha gaban su kai tsaye har sae da yayi saurin cije birki ya tsaida motar ya fito yana kallon d'an uwan nasa da ya fito  cikin mota a fusace,nn  ya tafi zai qarasa gurinsa cike da niyar mai bayani man bai saurara masa ba sae kukan kura da yayi ya cakumi collar rigar sa had'e da kai sa ya manna sa jikin mota ya kuma shaqe mai wuya da hannunwansa duka biyu.
 Aamil da bai ta6a tunanin abinda mohd zae masa ba knn sae qoqarin qwatar kansa ya shiga yi amma ya kasa nn Rynt ta fito mota a tsorace ta nufo su tayi tsaye a rud'e tana kallon yanda man ya shaqe Aamil da har idanuwan sa sun fara firfitowa,ai kuwa nn ta shiga ihu tana neman taimako.
 Da qarshe ganin ba sarki sae Allah taje da kanta ta fizgo hannun mohd zata janye shi daga jikin Aamil bata iya janye shi ba sae abun hannu taji ta sa6ulo a hannun sa had'e da wani irin turi da mohd ya mata wanda bata an kara ba sae jin kanta tayi kamas! mota ta banke ta, nn ta saki wani irin ihun da yasa mohd ya jiyo cikin muguwar razana yayo kanta  ya kwashe ta a rud'e ganin yanda jini ke fita a kanta yaje ya sakata a mota yaja motar aguje ya tafi ba tare da ya damu da sanin wanda ya kad'e ta ba da kuma Aamil da ya bari riqe da wuyan sa yana fmn tari.

Billy giro
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮

















                 🔮🔮🔮🔮
*```Page 64```*
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!
shine kake taji a bakin mutum biyu wato Nasir da Amir da sune suka fito cikin motar da aka kad'e Ryynt da ita wanda koda suka fito tuni man ya fice da Ryynt sai gun Aamil suka nufa da ke durqushe kan guiwoyinsa yana fmn ci gaba da tari.
   A nn Nasir ya bud'e motar Aamil ya d'auko ruwan gora a mota ya ba Amir dake riqe da Aamil a cewar ya ba Aamil ruwan se su hanzarta zuwa asibiti dmn ganin halin da Ryynt ke ciki.
   Bayan Aamil yasha ruwan ne suka d'aunguma gabad'ayan su se asibiti.
 Wato Man specialist hospital inda kai tsaye A&E ward suka nufa suka samu an riga an shiga da ita zuwa dubata nn suka zauna zaman jiran a fito da ita, sae yi suke suna safa da marwa musamman Amir da shine ke tuqa motar koda abin ya faru.


Bayan awa d'aya da faruwar haka ne,inna Abba,Nasir, Aamil da kuma Amir zaune suke zugum a d'akin da akayi admitting d'in Ryynt wacce har an fito da ita sae jiran farfad'owarta suke yayinda mohd ke gefenta zaune cikin damuwa yana kallon fuskarta d'auke da goshinta da akayi rolling da bandage.
  Yana cikin kallonta ne ta shiga motsi a hnkli had'e da fara ware hannunta da ke jimqe riqe a hannun man dashi kansa bai lura hannun nata a jimqe yake ba sae da yaji tana yunqurin ware hannun nn ya saki hannun a hnkli yana kallon hannun nata da take ci gaba da warewa har ta ware sa gabad'aya  nn yaga ashe abin hannun sa ne riqe a hannun nata, ya d'ago yana kallonta ita kuwa sae kallon abun hannun take wanda sak irin wanda ta tsinta ne a tare da kud'in da aka jefawa baffanta,
 a hnkli
ta d'ago ido sukayi 4 eyes ita da man wacce take idanuwanta suka ciko tap da qwalla har ma suka soma gangarowa gefen fuskarta.
 Cikin tausayi mohd ya kai hannu zai share mata hawayen ,tayi saurin tashi zaune had'e da fad'in"wlh kar ka ta6a ni!mugu dama kai nake zargi kuma sae gashi kuwa tabbas kai d'in ne wlh ina gaya ma bazan barka ba sae na d'auki fansar abinda kayiwa Baffana ko da kuwa zan rasa raina.
  Tana kaiwa nn ta had'e kai da guiwa had'e da fashewa da wani irin kuka mohd ya shiga kallonta cikin rashin fhmtar abinda tace,
haka ma su inna dake zagaye dasu wani  iri suka ji zancen nata.
   Abba yace"mohd me take cewa ne da kayi tsaye kawai kana kallonta"
Abba ya qarashe maganar ne yayinda Rynt ta d'ago da sauri tana kallon su d'aya bayan d'aya dan kwata kwata bata lura cewa akwai mutane a d'akin ba ta d'auka ko su kad'ai ne ita da mohd.
  Tana cikin kallon su ne ta tsinkayo muryar mohd yana cewa"Abba nima ban fhmci inda zancen nata ya nufa ba asali ma tsoro nake idan ba wata matsala ce ta samu a qwaqwalwarta ba dmn zancen nata yayi kama da hkn.
  Nan kawai suka ji inna ta fashe da kuka tana fad'in innalillahi wa inna ilaihi raji'una na shiga uku yau Rynh wace irin qaddara ce ta same ki da safiyar nn haka.
 Rynt dake kallon mohd rai 6ace kan mgnr da taji yayi,
tayi saurin kallon inna tace"Allah inna ba abinda ya sameni lafiyata qalau ya fad'a ne kawae dan wlh ya duk san abinda nake magana akai"
  Mohd yace"Rynt ni kuma wlh ban san abinda kike magana akai ba yi min bayani ta yanda zan fi fhmta kinji"
  Wani irin kallon takaici tamai yayinda shi kuma yake kallonta with innocent face d'inshi.
  Abba dake kallon su  yace"kaga mohd nsn hlnka sarai ka iya maida mutane shashasha tun d'azu da muka zo muke tambayar ku dalilin faruwar wnn accident d'in nata amma kunqi gaya mana sae ce mana da kukayi qaddara ce yanzu kuma tazo da wani  zancen kace kai baka sani ba bayan ba makawa kasani don nsn hln Rynt bata da banzar tabi'ar yin qarya"
Mohd ya kalli Abba yace"wlh na rantse Abba ni ban san me take magana akai ba"
  Cikin muryar kuka mai d'auke da takaici Rynt tace"wlh ka sa....bata qarasa fad'a ba sae ihu da ta fasa tare da saurin dafe cikin ta,
a rud'e mohd ya matsa gab da ita zai riqota,ta sauka kan gadon ba shiri har tana qoqarin fad'uwa sae inna ce tayi saurin tarbo ta zuwa jikinta inda cikin tsananin 6acin rai inna ta kalli mohd da ya nufo su tace"kar ka kuskura kace zaka matso nn shashasha marar mutunci.
   Cikin nuna damuwa mohd ya kalli Abba yace"dan Allah Abba a barni na dubata idan ba wata matsala bace cikin ya samu"
   Abba yace"ko matsalar ce ai kai ka jawo shashasha kawai.
Nan mohd yaje zuwa sake magana Abba ya watsa masa mugun kallo kafin yake maida dubansa gun inna  wacce taja Ryynt suka zauna kan bed yaje gab dasu cikin kulawa yace da Ryynt "a kira likita tazo ta dubaki ?
   Ryynt wacce dama motsin cikin ne kawae ya sata ihu,
 ta girgiza kanta tace"a'a Abba ba wata matsala bace dama"
Inna tace" Aa fa Rynh kin tabbatar"
ta gyad'a mata kai had'e da kallon man shaye da toka nn kawae ta fashe da wani sabon kuka sbd jin tayi komai ya dawo mata sabo har tana mamakin rashin imani irin nasa ta yanda ya kashe mata mahaifi wanda ya rage mata qwaya d'aya tal  a duniya.
 Nan fa taci gaba da kuka sosai inna na bata hqr amma bata iya daina kukan ba sae ma qaruwa da yake.

Inna ta kalli mohd dake tsaye a sukuikuice yana ta kallon ryynt,
Cikin 6acin rae tace"ja'irin yaro wae me ka mata ne kasa er mutane sae kuka take tayi ne iye!
Yace"inna nifa na gaya muku ban san me na mata ba"
Abba yace"kaga wlh kar ka maida mutane shashashu kan me to zata zauna tana irin wnn kukan hk "
  Mohd yaje zuwa magana Abba bai barshi ba sae fad'a da yaci gaba da yimae sosai.
 A nn ran mohd ya soma 6aci yace"haba Abba wae ya za'a yarda da shirmen zancenta ne nikam kawai a barni na duba ta tukun idan ba wata matsala ce ta samu a qwaqwalwarta ba idan kuma har dgske take cewa lafiyar ta qalau ai sae tayi bayani ta yanda kowa zai fi fahimta ba wae ta wani cumuimuye magana azo anata ganin laifi na a kan abinda sam banida masaniya akanshi.
   Rynt dake kuka ta miqe tsaya tana kallon sa da idanuwan ta dake d'auke da tsanar sa qarara wacce taso ace ta bar abin daga ita sae shi amma ya soma kaita qololuwa ta yanda bazata iya barin abun ba har sae ta fallasa sirrin,duk da cewa tasan idan ta snr dasu ba lallai bane su barta ta d'auki fansar abinda tayi niyya amma tunda tana da evidence ko ta hanyar hukuma ne sae ta nemi fansar ta.
 Nan ta kauda fuskar ta ba tare da tace dashi komai  ba sae  duban ta da ta maida gun Abba da inna kafin ta iya ce musu komai sae hawaye taji suna silalowa a hnkli kan kumatun ta inda cikin sanyin murya mai d'auke da rawar kuka tace"Abba ,inna, ina roqon ku da kuyi haquri da jin abinda zai fito bakina da kuma jin ainihin dalilin da yasa na zauna ina rayuwa tare da ku,nn wasu hawaye suka sake gangarowa akan fuskarta snn taci gaba da cewa"inna a gsky ina rayuwa daku ne kawai dmn d'aukar fansar abinda mohd ya min wato na kashe min baffana na da yayi"
ta qarashe mgnr ne had'e da fashewa da kuka yayinda mutanen d'akin suka ji zancen nata kmr saukar guduma a kunnen su inda cikin gwalo ido mai d'auke da tsananin mamaki kowa ke kallon mohd yayinda shi kuma mohd ya dasqare guri d'aya ya saki baki yana kallon Ryynt cikin fiddo ido mai d'auke da mamaki,
 wanda kowa a gurin ya kasa cewa komai sae Abba ne yayi qarfin hln cewa"innalillahi wa inna ilaihi raji'un mohd me zanji!
  Cikin rud'un da Mohd yake d'auke dashi yayi saurin girgiza kansa yace"No Abba wlh  kwata kwata zancen ta ba gsky aciki kawai nafi yarda cewa accident d'in nn ya bawa qwaqwal war ta matsala, abarni na dubata dan Allah Abba"
   Abba ya kalli Rynt wanda kafin yace komai ta riga sa da cewa"Aa Abba abinda nake so shine dan Allah muje gida  gabad'ya mu dmn na nuna muku shaida ta ta yanda zaku fi fhmtar cewa da hnkli na nake zancen nn"
  Ta qarashe mgnr had'e da kai hannu ta share hawayen da ke kan fuskarta.
  Abba kuwa bai musa mata ba suka d'unguma gabad'ayan su har su Aamil sae zuwa gidan inna.
 Bayan sun isa ne Ryynt taje sae d'akinta ta d'auko kud'i da abin hannu irin na man tazo zata bawa Abba wanda kafin ya kar6a Aamil ya miqe xumbur cikin tsananin tashin hnkli yana kallon abun hannun da kuma kud'in.



Billy giro😊
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮















                🔮🔮🔮🔮
*```Page 65```*
Bai iya ci gaba da tsayuwa ba sae jin yayi ya zube qasa kan guiwoyin sa yana ci gaba da kallon kud'in yayinda idanuwansa suka kad'a zama d'aya sukayi jajur snn bakinsa ya shiga rawa kmr zai ce wani  abu amma ya kasa sae kansa da ya dafe had'e da rufe idanun sa yana mai tuna komai sak yanda ya faru.
   Nan kowa yayo kansa yana tambayar Aamil lafiya me yake faruwa,
 kuka ya fashe dashi sosai ,
ya bud'e ido yana kallon Abba dake gaban sa dafe dashi riqe da kud'in da abin hannun da Ryynt ta bashi a nn ya rumtse idon sa da sauri dan ko kad'an baya son ganin kayan.
   Abba ya ajiye abubuwan da sauri yana tambayar lafiya Aamil wani abu ya sami idanun naka ne?
   Bud'e idanuwan nasa yayi  yana kallon Abba cikin kuka yace"Abba nine wlh ba mohd bane nine Abba.......kaine me Aamil?
 Cikin rawar murya  Aamil yace"Abba nine na kashewa Ryynt Baffanta!
 Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!!!
shine abinda kowa ya shiga fad'i ba adadi akasin Ryynt da komai ta kasa cewa sae ja baya tayi da qarfi tana kallon Aamil d'auke da hawayen da suka zubo mata kai tsaye kmr yanda shima yake kallonta da nashi hawaye akan fuskar sa.
   Nan kawai ta fashe da kuka ta tafi da gudu zuwa d'aki man ya tashi da sauri ya bita sae dai bai iya shiga d'akin ba sae jikin qofar ya tsaya  sbd tasa makulli ta rufe d'akin amma ana jiyo tsaf sautin kukanta sbd a nn jikin qofar ta zame tana kuka.
    Aamil ne yazo ya sami man tsaye a bakin qofar ya gurfana kan guiwoyin sa ya rungume qafafuwan man cikin kuka yace"i beg u yhu ka bata haquri wlh ba a kan hnkli na nayi kisan ba qaddara ce......
Abba ne yazo a fusace ya tada shi tsaye ya kifa masa wawan mari yace"wace irin qaddara ce wnn Aamil ko ka fara shaye shaye ne ban sani ba!
   Aamil yayi shiru dmn tabbas ba zai ta6a mantawa ba yafi to daga gurin shaye shayen sa ya kad'e Baffan Ryynt.
Abba ya daka mai tsawa yace "dan uwarka gaya min garin ya ka kashe mata mahaifi kuma akan wane dalili!
   Aamil yace"Abba qaddara ce wlh ba nayi kisan da niya bane asalima ban san cewa ya mutu ba"
   Kaga bashi nake son ji ba ka gaya min ta yaya akayi har ka kashe mata mahaifi?
   Ba musu Aamil ya gayawa Abba komai yanda abin ya faru ba tare da ya 6oye masa komai ba har magagin giyar da yake ciki kuwa duk sae da ya gaya mae.
   Innalillahi wa inna ilaihi raji'un shine abinda Abba ke ta furtawa, yayinda ya cire hular kanshi yana fifita ta a jikin sa sbd wani irin zafin bala'i da gumi dake tsastsafo mai ta koina a jikin sa had'e da wani  irin ciwo da yake ji ta 6angaren zuciyarsa,
 ya dafe gurin da sauri yaje zuwa fad'uwa Nasir da man sukayi hanzarin tarbarsa inda a rud'e suka tafi dashi kan doguwar kujera suka kwantar ,
inna ta tafi cikin rud'u da firgici ta bud'e fridge ta ciro ruwa ta kawo musu suka yayyafa masa.
Amma bai farfad'o ba  sae d'aukar sa sukayi zuwa asibiti yayinda man da Amir ne ke kansa har suka samu ya farfad'o suka mai allurai ciki har da ta bacci.
Koda suka fito suka sami inna sae kuka take tana fmn sirfawa Aamil zagi yayinda Nasir ke gefen ta yana ta fmn lallashi wacce tana ganin su Amir sun fito ta nufe su tana tambayar halin da Abba ke ciki nn suka nuna mata ba wata matsala bace dan har ma ya farfad'o sun mai allurar bacci,
 a nn ta nemi ta ganshi basu hanata ba suka barta ta shiga tare da Nasir yayinda su ma suka juya zasu bi bayansu sae ga hjyr su da man ya kira tazo cikin rud'u tana tambayar sa abinda ya faru da Abban su,
Man yayi shiru kawae yana kallonta ya kasa ce mata komai sae Amir ne ya bud'e baki yace"umma muje dae kiga Abba tukun"
 Bata musa musu ba tabi bayan su suka shiga dan dama ta matsu taje ta ganshi.
  Ta sami Nasir ya jawo wa inna kujera ta zauna nn gefen gadon da Abba ke kwance  akai.
  Ta qarasa ciki tare da gaida inna yayinda ita kuma nasir ya gaida ta ta amsa tana mai kallon Abba dake kwance  yana bacci ,
ta sauke numfashi tana ci gaba da kallon sa snn ta kalli su man tace"na tambaye ku tun a waje me yake damun sa baku gaya min ba sae cewa kukayi na shigo na ganshi"
 Amir ne ya sadda kansa qasa cikin jimamin baqin cikin abinda zae snr da ita ya d'ago had'e da share er qwallar baqin cikin da ta fito masa ta gefen ido snn ya shiga snr da ita lbrn komai abinda ya faru cikin nuna baqin ciki da damuwa"
  Yana gama bata labarin ne kafin tace komai sae Aamil ta hango tsaye a bakin qofar d'akin yazo gab da ita ya durqusa a gabanta d'auke da idanuwan sa da sukayi jajur kan kuka,ita kuwa sae kallon sa take cikin mugun 6acin rae yace"umma ki yafe min,a yau nayi babbar nadamar qin daina abinda kika hana ni wato shan giya da ke kad'ai kika sani sae kuma Amir,kuma kunyi iya bakin qoqarin ku na ganin na daina amma sae na kasa har takai ga na aikata babbar 6arna,wacce tun daga rnr wlh ban sake yarda nasha giya ba umma duk da cewa ban san nayi kisa ba amma ko kad'an banji dad'in abinda ya faru ba a lokacinda hnkli na ya dawo gare ni wanda tun daga rnr nake fmn istigifari a gurin ubangiji na ina neman yafiya a gurin shi,dmn dama tun farko bada niya na fara ba sharrin frnds ne da kuma sharrin shaid'an da har ta kai ga na aikata abinda har mutuwa ta ba zae ta6a kankaruwa ba.
  Ya qarasa maganar ne cikin muryar kuka mai qunshe da baqin ciki,
 umma kuwa sae kuka ta fashe dashi tace"lallai Aamil ka  riga ka cuci rayuwar ka tun farko sae da na gaya maka wnn banzar tabi'ar sam bata dace dakai ba ka daina ta amma kaqi yanzu gashi ka aikata abinda har mu mutuwar mu baza mu manta ba ,ka 6ata mana suna ka wulaqanta mutuncin gidan ku da kaf dangi ma baki d'aya,
shashasha kawae fita a nn in daina ganin ka!

 Hawaye ne suka sailalo a hknli kan kumatun sa snn ya kama hanya ya fita d'akin jiki sanyaye.
    Nan man ya kama hanya zai fita d'akin, umma ta takadar dashi ta hnyr cewa "ba dai bin Aamil d'in zakayi ba"
man ya girgiza kansa yana kallon ta sbd shi ba inda zae je ba knn gun Ryynt yake son ya tafi.
 Bata ce dashi komai ba sae Abba ta kalla da ya soma tari wanda ya bud'e idonsa a hnkli had'e da tashi zaune ,
umma ta qarasa gurin sa tana mai sannu haka ma inna da su Amir duk suka  mae sannu yayinda Man yaje ya kawo masa ruwa had'e da masa sannu Abba ya kar6i ruwan yasha.
  Bayan ya gama shan ruwan ne ya kalli man yace"Ryynt fa?
  A hnkli man ya sadda kansa qasa yace"tana gida"
Nan Abba ya maida duban sa gun nasir yace"je ka zo min da ita"
  Nasir yace"to"snn ya fita d'akin wanda ya d'an jima kafin yake dawowa suka shigo d'akin shida Ryynt wacce kallo d'aya zakayi mata kasan taci kuka har na fita rai don duk idanunta sun kumbura sunyi jajur tayi tsaye kawae a bakin qofa kanta qasa ta kasa kallon kowa.
  Abba dake kallonta yace"qaraso daga ciki Ryynt"
  Cikin tako mai natsuwa ta qarasa gurin Abba wanda ya kalleta da kulawa yace"Ryynt ko kad'an banji dad'in abinda kikayi niyya ba amma kuma banga laifin ki ba dmn babban mai laifi shine Aamil da duk shine yayi silar haddasa faruwar komai ,
ya haddasa miki baqin ciki da quncin rayuwar da kika shiga a matsayin ki na er qaramar yarinya da har yasa kika yi tunanin abinda bai dace dake ba,da hk nake son kiyi haquri ki ajiye wnn tunanin  ki bar komai a hannu na  dmn nida kaina zan sa a kama Aamil a kuma yanke masa hukunci dae dai dashi  ta yanda duk wani  mai banzar tabi'a irin tasa bazai ta6a sha'awar aikata abinda ya aikata ba.
  Girgiza kanta tayi had'e da share qwallar da suka zubo mata tace"Abba ka barshi,
 dama duk a tunani da gayya yayi kisan shiyasa na d'auki wnn alqawarin wanda na d'auki
alqawarin ne cikin baqin ciki da jin zafin  yanda aka kad'e Baffana da kuma sanin cewa ko na kai qara a hukuma ba lallai bane abi min haqqina a wnn lokacin kasancewar mu talakawa en qauye da ba'a d'auke mu a bakin komai ba shiyasa amma ni ynx na yafe masa Abba"
  Abba ya girgiza kansa yace"ai ba ubanda ya ake sa shan giyar dn hk sae na nuna masa kuskuren sa ta yanda zaiyi babbar nadamar fara shan giya a rayuwar sa"
 Ryynt ta sake share qwallar da suka zubo mata tana tunanin hallaci irin nasu tace"Abba dsgke na yafe masa kawai ka barshi"

Abba yace" ko d'aya Ryynt ke yarinya ce mai kirki da mutunci da ya zama dole abi maki haqqin ki kan zaluntar da ya miki,dmn ya zalunce ki mafi zalunta .
  Inna ta kama masa sae masifa ita ma take kan lallai fa sae an hukunta shi tun da shi yajawa kansa ba wanda yaja masa.
  Ryynt tayi shiru kawai tana sauraren su sae hawaye dake fmn sauka kan fuskarta yayinda taji har ranta mutanen sun qara shiga ranta wad'anda had'i da hallacin da suka mata ne yasa taji ta yafewa Aamil dmn sun cancanci fiye da haka a gurinta sae dai kunyar su da kuma tsanar Aamil da zata zauna a ranta bazata bar ta iya ci gaba da zama tare dasu ba shiyasa ta shiga tunanin suna komawa gida tafiyar ta kawae zatayi ba tare da kowa ya sani ba.

Bayan sun koma gida bayan sllr magrib Ryynt ce riqe da abun hannun man sae fmn juyashi take tana kallo wacce still bata ga sunan da ke jikin abun hannun ba sbd cikin wani salon qawa da ba kai tsaye ake ganewa ba akayi rubutun.
qwallah ne suka zubo zar kan fuskarta sbd ko kad'an bata ji dad'in zargin da ta d'aura akan wanda ba shi bane sai dai baqin hallinsa ne ya janyo tafi zargin cewa shine.
   Inna dake tsaye a bakin qofa sae kallon ta take don ita ko kad'an bata ji haushin dalilin zamanda tayi a tare dasu ba sae d'inbin tausayin ta da taji nn ta girgiza kanta kawae ta juya zuwa d'akinta ,ba tare da Ryynt tasan da tsayuwar ta a bakin qofar ba har ficewarta.
  Ryynt kuwa tana cikin hkne wayar ta ta shiga qara ta tashi a hnkli ta d'auko wayar taga umman saliha ce mai kiran ,ta d'aga wyr jiki sanyaye dan duk sae ta soma jin kewar su.
   Koda ta gama wyr sae hawaye ta shiga sharewa sbd lbr ne yakai kunnen umman saliha na komai abinda ya faru.

Da dare guraren qarfe tara Ryynt ta fito gidan ba wanda ya sani riqe da er viva ledar ta wacce kayan ta da tazo dasu daga qauye ne kad'ai a ciki wato kayan da marigayi anwar ya bata haka ma na jikinta kala d'aya daga cikin su ne ta saka.
  Tafe take tana waiwayen gidan cike da jin kewar inna har ta fito gate d'auke da hawayen da ke ta fmn zarya a kan fuskarta ba tare da ta damu da ta share hawayen ba.
   koda ta fito gate d'in sae wani  irin hasken mota ya sauka kan fuskarta har sae da tayi saurin sa hannu ta kare fuskar tata wacce bata ankara ba sae jin qamshin turaren man taji gab da ita.
  Nan ta janye hannun ta da ta kare fuskarta had'e da kallon man dake tsaye a gabanta ta kauda fuskarta gefe snn taja baya a hnkli sbd bata son qamshin turaren sa yana shiga hancin ta sbd qamshin turaren kaita yake ya baro don sae tayi ta son jin kasancewa a jikin sa.

Man dake tsaye yana kallonta kanta qasa ta wani kai viva leda a bayanta ta 6oye yace"ina zaki tafi da daren nn?
  Shiru tayi had'e da d'an qara matsawa baya dashi sbd ko magana yayi wani irin qamshin dad'i mai rikitarwa take jin yana fita a cikin bakin sa.
  Man ya kalleta kawai yace"da ke nake magana kinyi shiru"
   Still shiru ta mai tare da qara matsawa,
 shi kuwa yakai  hannu zae riqo ta tayi saurin cewa"kar ka ta6a ni bana so"
 Wacce tayi mgnr ne cikin sanyin murya yayinda shi kuma ya sauke numfashi yace"to koma daga ciki idan ba so kike na d'auke ki na kaiki da kaina ba"
   Cikin muryar kuka tace"ni ka bar ni na fita"
 Yace"kiyi me wae idan kika fita"

Bata riga tace komai ba sae muryar inna suka tsinkayo tana fmn qwalawa Rynt kira,
  Aamil dake can la6e a bayan su yayi saurin barin gurin wanda yazo ne dmn bawa Ryynt hqr amma kuma yana jin kunyar had'a ido da ita.
  Man kuwa a lokacin da yaji muryar inna sae d'aga tasa muryar yayi a natse yace"inna zo gata a nn"
  Rynt ta kalle sa rae 6ace don hannunta ya riqo ya kuma jata ya kaita sae gun inna wacce suna had'a ido tayi saurin sadda kanta qasa inna kuwa sae taslima ta shiga yi tana kallon viva ledar da ke hannun Ryynt.



Kuyi haquri uzururruka suna ta shigo ni a kwanakin nn shiyasa bana samun yi maku posting inda ko gobe sae kunyi hqr sbd tafiyar da zanyi.
   Shiyasa na muku mai shegen yawan da zai kài ku har jibi 😜🙈

Billy giro😊
🔮🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮















                🔮🔮🔮🔮
*```Page 66```*
Snn ta riqe baki tace"Ikon Allah ashe kuwa hasashe na ne ya tabbata dmn tun da muka dawo daga asibiti na fhmci wani yanayi da ynryr nn take ciki da ya bani cewa tafiya take so tayi,da to idan kin tafi ina zaki je ne iye!ko kuwa a tunanin ki idan kinje qauyen naku  zan barki ne banje na dawo dake ba.
    Cikin sanyin murya can ciki Ryyñt tace"inna yi haquri"
 Inna ta kalle ta kawae taja hannun ta suka je daga ciki yayinda man ke biye dasu.
 Falo suka zauna inna ta kalli Ryynt a natse cikin kulawa tace"Ryynh haqiqa na fhmci dalilin da yasa kk so ki tafi ,
a wani  6angaren naga laifin ki a wani 6angaren kuma banga laifinki ba,laifin ki da na gani shine ya muna zaune qalau cikin aminci da juna kice zaki tafi bayan duk irin shaquwar da mukayi Ryynh ,
idan har dan a dalilin zaman da kika yi damu ne ai ba laifin ki bane laifin wnn banzan yaron ne da ba abinda zance sae dai nace Allah isar miki ,
kuma hukunci ya zama dole a kanshi amma zancen tafiya ki bar mu sam bai taso ba ,
idan ba so kike nima na biki mu koma can qauyen naku da zama ba.
ko kuwa kin gaji da zama damu ne Ryynh.
 Da sauri Ryynt ta girgiza kanta tace"Allah inna ba haka bane"
  Inna tace"to Ryyñh idan ba haka bane ai sae kiyi zamanki muci gaba da zaman mu kinji er albarka"
  Ryynt ta gyad'a mata kai inna ta washe baki tace"yauwa er albarka to je maida kayanki a d'aki kinji"
  Nan Ryynt ta tashi a natse ta nufi d'akinta.
  Yayinda inna ta bita da kallo tana fad'in"wlh yarinyar nn sosai ta kwanta min a rae tun rnr da na fara ganinta kuma har yau ban soma jin ta fita a ran nawa ba,sbd ko yaushe qara ganin hankalinta nake wlh.
  Man da duk ynx tausayin Ryynt yake ji da kuma wani  irin sonta da ya qara shigar sa ya sauke numfashi yace"shiyasa inna nake son kuyi haquri ku barni na maida ta wlh ina sonta har raina ba wae don abinda take d'auke dashi kad'ai ba"
  Inna ta kallesa tace"Hm muhammadu knn ba inda Ryynt zata koma taci gaba da ganin wulaqanci kaji in gaya ma"
   Mohd yace"wlh inna ni banada nufin sake wulaqantata"
  Inna tace"yo ai kace haka tunda so kake ka maida ta"
   Mohd yace" inna ko d'aya ba haka bane na rantse"
  Inna tace
"Yo kai ka sani da wani  rantse rantsen ka can ai ba yau na soma sanin halin yaran zamani irinku ba"
    Kmr zai yi kuka yace"haba inna sae kace ban san muhummancin rantsuwa ba"
 Inna dake kallonsa tace"kaga ni duk ka cika ni da surutu je ka sami ubanka kabiru ka gaya mai"
  Man ya kalleta a sanyaye yace"shike nn inna zanje amma idan yaqi amincewa zaki sa bakinki dan Allah inna.
  Inna tace"bari kaji bafa zanyi ba don ka sani dmn bazan ta6a yarda a had'a hannu dani a cuci marainiyar Allah ba.
  Ta fad'i hakane tare da tashi ta bashi guri ba tare da ta tsaya jin me zai ce ba.
  Shi kuwa har zai fita yaji yana son ganin Ryynt ya tafi sae d'akinta bai ganta ba tana bathroom ya fito jiki sanyaye yana tunanin ko Abba zai saurare shi idan yaje.
 Haka dae ya bar gidan cike da tunani a ransa.

6angaren Aamil kuwa a lokacin da ya fice family house ya tafi da niyyar xuwa gun Abba amma kuma ya kasa shiga gate d'in gidan ko ma nace ko cikin motar sa ya kasa fitowa dan bai san ya zaiyi ya had'a ido da Abba ba sae zaman sa yayi a cikin motar yana ta kuka cike da nadamar fara shan giya a rayuwar sa inda ba kowa ne ya janyo masa haka ba sae frnds d'insa na waje wanda idan yaga suna sha kallon su kawai yake a asararru dan ya musu magana har ya gaji sunqi dainawa sae gashi bai san ya akayi ba daga kallon su har shima ya soma ra'ayi ya fara sha.
   Wnn knn.
Bai iya shiga gidan ba dae sae jan motar sa yayi ya koma gidan sa ya sami matar sa wacce tun lokacinda taji labarin abinda ya faru sae kuka take tayi ya bata haquri har ya gaji taqi dainawa sae ma takadar saki da ta nema a gurinsa a cewar bata iya ci gaba da zama dashi a matsayin miji hkn ne ya qara masa damuwa sosai ya rasa ta inda zae sa kansa yaji sanyi.


Washe gari koda aka wayi gari ba Aamil  yayi tafiyar sa sae saqon wasiqar sa Abba ya samu ya dawo daga sllr asuba wanda koda ya gama karanta wasiqar sae numfashi ya fitar cikin yananyin damuwa ya shiga gidan ya sami hjyr su man, ya bata wasiqar ta karanta sae kuka don kalamai ne na ban haquri masu karya zuciya kai tsaye.

Koda gari ya gama waye labari yakai gun kowa family don iyaye maza har meeting suka had'a a cewar Abba yayi haquri a nemo Aamil ya dawo gida tun da Ryynt dae ta yafe masa.
  Abba ya nuna musu kawai su barshi kan dole kowa ya kama gabansa cikin damuwa dan sunyi sunyi dashi ya kafe kan A'a.
   Bayan an watse meeting d'in ne Abba ya kira Amir da mohd a cewar suje gidan Aamil su dawo da matar sa Khadija gida don dama da ita har matar Amir duk en familyn ne wato 'ya'yan Alhj sa'eed qanin Abban Nasir.


Koda man da Amir suka je gidan suka same ta zaune a falo ta had'e kai da guiwa sai kuka take tayi riqe da takadar da ta samu Aamil ya bar mata ta ban hqr.
  Lallashin ta suka shiga yi sosai don duk sai ta basu tausayi har dae ilham dake gefen ta itama tana tayata kukan.

Bayan sunzo dasu gida ne Abba ya zaunar da ita ya bata magana ya kuma rarrashe ta sosai har damuwar da ke ranta ta d'an soma rage mata.


6angaren su Ryynt kuwa suma duk sunji labarin tafiyar Aamil dan tun da asuba wani  yayi wa inna sallama ya bata takarda a cewar Aamil ne ya bada a bawa Ryynt wanda koda Ryynt ta gama karanta wasiqar sae qwalla ta sami kanta dashi dan itama kalamai ne sosai na ban haquri masu karya zuciya da suka sa ta rage jin tsanar sa sae ma tausayin sa da ta soma ji kan irin hukuncin da yaje yiwa kansa a inda ya tafi ba tare da ya snr da kowa inda yaje d'in ba.

   Malika kuwa bazan ce taji labarin ba don tayi tafiya zuwa dubai ita da mahaifiyar ta.

Washe garin rnr da dare mohd ne tafe cikin mota zai tafi family house  gun Abba cike da fargaba yayinda yake ta fmn addu'a a ransa na Allah yasa Abba ya amince ya barshi ya maida Ryynt don tun rnr fargaba bata bar yaje ba duk da cewa yanzu kmr kar abubuwan nn su faru yaga Abba ya d'an fara sake mai.

Zaune ya sami Abba a falo shi kad'ai yana sauraren labarai ya sami guri a qasa ya zauna inda cikin ladabi ya gaida shi ,Abba ya amsa ba yabo ba fallasa.
Mohd yayi shiru ya kasa cewa komai sae kansa da ya sadda qasa.
  Abba dake kallon sa yace"ya akayi ne?
 Cikin inda inda Mohd yace"Abba dama nazo baka haquri ne akan dan Allah kayi haquri ka barni na maida Ryynt wlh bana da nufin sake cutar da ita"
  Abba da still kallon sa yake ya numfasa snn yace"mohd sanin kanka ne Ryynt bata son komawa gidan ka kuma ni baxan ta6a tursasa ta akan abinda bata so ba don haka sae ka tashi ka bani guri"
  Cikin marairaicewa mohd yace"Dan Allah Abba kayi haquri kasa bakin ka inshaa Allah zata yarda ta koma"
  Abba yace"Da zaka saketa kayi shawara da ni ne da har kake tunanin xan saka bakina akan ta koma,to bari kaji ni bazan yi wnn ba dmn Ryynt ba jakar gidan ku bace da zaka daka ka kuma d'aura mata sharri had'i da saki ka kuma yi tunanin zan saka bakina akan ta koma gidan ka sam ba zai ta6a yiyuwa ba  .
 A nn mohd yayi shiru cikin damuwa sosai sae can yace"Abba  dan Allah kayi haquri wlh inshaa Allah hkn baxai sake faruwa ba nayi alqawari.
  Abba ya girgiza kansa yace"kaga tashi ka bani guri kuma kar na sake ganin qafar ka a nn gidan da sunan wnn mgnr"
    A nn fa idanun mohd suka kad'a sukayi jajur ya kasa tashi ya kuma kasa cewa komai.
 Abba ya tashi zai bar gurin mohd ya kalle sa inda cikin murya mai d'auke da tsananin damuwa yace" Abba dan Allah kayi haquri   ka bani dama ta qarshe "
Abba ya tsaya ya kalle sa snn yace"naji kaje ka sameta kuyi magana idan ta amince to idan kuma bata amince ba wlh wnn kai ka sani"
   Cikin jin dad'i sosai mohd ya d'ago yana kallon Abba ya masa godiya snn ya tashi da hanzarin sa ya fita.
  Abba kuwa koda ya juya  sae umma ya gani tsaye gun staircase wacce tun lokacinda mohd ya shigo take tsaye a gurin tana jin duk abinda suke fad'a.
  Ta kalli Abba fuskar ta ba yabo ba fallasa sae dae kuma bata ce komai ba har ya ra6a ta gefen ta ya wucewar sa xuwa d'aki  ita ma dae hkn ta koma d'aki abinta.

Mohd kuwa da fitar sa kai tsaye gidan inna ya nufa ya sami falon ba kowa ya qarasa d'akin inna had'e da sallama,ya sami inna na shaf'i da wuturi,
 ya nemi guri kan sofa ya zauna yana mai kallon Ryynt dake kwance  kan gado sae sharar bacci take abinta.
 
Bayan inna ta idar da salla ne suka gaisa snn mohd ya gaya mata yanda sukayi da Abba.
  Inna tace"shike nn ai sae ka tuntu6i Ryynh d'in kaji sae dai kuma yanzu kaga bacci take"
  Yace"haka ne sae gobe da safe idan na dawo"
  Inna tace"da safe fa kasan makaranta take zuwa"
  Yace"wae basuyi hutu bane har yanzu?
  Inna tace"ai gobe ne hutun nasu don sun gama jarrbawa tun ba yau ba.
  Yace"shike nn Allah taimaka inna tace"Amin"shi kuma ya tashi ya fita had'e da yi mata sae da safe"
  Inna ta bisa da ido har ya fita snn ta kalli Ryynt dake kwance  tana bacci ta kauda idonta takai dubanta gun ledar da Mohd ya ajiye mata da zai fita koda ta duba daqwalen kaji ne guda biyu gasasshi da hollandia yogurt wanda ya siye su ne kan hanya da zai zo.

Washe gari cikin farin ciki Ryynt da ta dawo daga school tana shigowa falo ta fad'a jikin inna tare da nuna mata result d'inta da tazo ta d'aya.
  Washe da baki Inna ta kar6i result d'in tana ta murna tana sa albarka.

 Mohd da shigowar sa knn ya kar6i result d'in yana kallo d'auke da murmushi a fuskar sa ya kalli Ryynh yace"sosai kinyi qoqari Allah qara miki basira"
  Inna tace"Amin yayinda Ryynt ke gaida Nasir da kusan tare suka shigo shida mohd wanda shima ya kar6i result d'in cikin murna yace"MashaAllah kinyi qoqari sosai gaskiya Allah yasa ki d'ore da hakan"tace amin tare da sadda kanta qasa tana wasa da en yatsunta yayinda man keta kallonta sae son yake su had'a ido amma ita bata ma kallon gefen sa,
 yana kallo ta ficewar ta d'aki shi kuma yayiwa inna sallama ya fita wanda dama akan ta kad'ai ya shigo gidan yaga idan ta dawo sbd yaje school d'in su d'aukart bai same ta ba.

 Bayan awa d'aya da faruwar haka ne Ryynt ce ta fito daga kitchen ta wanko agwalimarta cikin bowl sae ga saliha ta shigo gidan ihun murna Ryynt ta saki tare da ajiye bowl d'in agwalimar ta a qasa taje da gudu ta fad'a jikin saliha suka rungume juna suna masu murnar ganin juna ,
 Ryynt ta d'ago cike da mamaki tana kallon saliha don bata ji a bakin kowa cewa sun dawo ba.
  Tace"yaushe kuka dawo ne saliha?
  Saliha tace"yau muka dawo inna bata snr dake ba, dan har kiranta nayi nace ina nn shigowa"
  Ryynt ta girgiza kanta tace"um um inaga ta manta,ya baki zo min da mami ba?
 Wlh mami fita sukayi ita da Ameera.
  Ryynt tace"ya umma to"
  Saliha tace"umma tana qalau ta ma ce a gaida ke"
  Ta fad'i hkne yayinda suka shiga d'akin inna wacce tana ganin saliha ta washe baki tana mata oyoyo,inda cikin sakin fuska sosai
saliha ta shiga gaidata.

Sun d'an jima a d'akin kafin suke fitowa suka je d'akin Ryynt sukayi zaune sae firar bayan rabuwa suke yayinda saliha keta kallon Ryynt da taga ta canza mata ftr ta tayi haske da laushi had'e da er qibar da ta qara mata kyau.
 Haka ma sae kallon d'akin take ganin komai na Ryynt a cikin d'akin don bata san cewa Ryynt ta dawo gidan inna ba duk a tunanin ta yini taxo yi.
  Bata dae ce komai ba suka ci gaba da firar su suna shan agwalima .
 Suna cikin hkne suka jiyo sallamar mohd saliha ta amsa sallamar had'e da gaida shi snn ta fita ta basu guri.
  Mohd ya qarasa daga cikin d'akin ya zauna kan bed yana mai kallon Rynt.



Billy Giro 😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮













_Inaga gaskiya kuyi haquri naci gaba da muku posting d'in daren nn sbd gsky da rana banida enuf time d'inda zan kammala typing har na samu na muku posting,dan haka daga yau inshaa Allah zamu koma er gidan jiya_

                🔮🔮🔮🔮
*```Page 67```*
   Wacce ta kauda fuskarta gefe sbd qamshin turaren sa.
  Mohd  yakai  hannu ya juyo fuskarta ,
ta watsa masa manyan idanuwan ta a cikin nashi cikin yanayi na alamar mene ne?
  Yace"Ina son zamuyi magana ne"
  Ta maida fuskar ta gefe tace"inajinka"
  Yace"ba wata magana bace magana d'aya ce wacce kika sani wato zancen komawar ki gidana"
   Ta girgiza kanta a natse ba tare da kalle sa ba tace"Aa ni bazan koma ba"
 Yace"yi haquri dae kinji"
Tace"kawae kayi haquri kaima"
 Yace"ni bazan iya bane"
Tace"amma kake tunanin ni zan iya"
  Tayi mgnr ne yayinda ta kalle sa snn ta kauda kai.
 Yace"meyasa baza ki iya haqura ba"
  Tace"sbd rayuwar gidanka rayuwa ce da bazan iya taba"
  Mohd yace"wnn rayuwar da kike tunani ae a dane amma ynz sabuwar rayuwa ce zamu gina nida ke"
  Tace"Aa ni nafi son rayuwata a nn sbd nafi samun kwanciyar hankali"
   Mohd yace"can ma d'in zaki sami kwanciyar hnkli fiye da tunanin ki"
   Tace"fiye da tunani na zan sha duka na sani amma dai ba kwanciyar hnkli ba kam"
   No Ryynt ki ajiye duka gefe dmn nayi miki alqawarin bazan ta6a sake kai hannu na a jikin da niyyar sake dukanki ba.
Tace" ta yaya bayan idan ranka ya 6aci baka da wani  hukunci sae duka ,
rayuwar zo mu zauna kuwa bawai kullum cikin farin ciki ake zaune ba dole yau da gobe sae an sami sa6ani kuma ta yaya kake tunanin zan koma gidanka byn idan aka gaya ma magana yarda kake har ka d'auki hukunci ba tare da kayi bincike akai ba.
  Numfashi ya fitar d'auke da alamar damuwa yace"Ryynt abinda ya faru ya riga da ya faru ina son dan Allah ki manta shi ki d'auka cewa yanzu wata sabuwar rayuwa ce zakiyi mai dad'in gaske da ba wani  qunci ko tashin hnkli a cikinta"
  Ryynt ta girgiza kanta a natse tace"ko d'aya bazan ta6a hangen abinda bashi bane"
  Mohd yace"plz Ryynt ki fhmce ni.......
Ryynt da duk qamshin turaren sa ya soma fizgarta na son taji kanta a jikin sa tana mae shaqar qamshin ,
ta miqe tsaye da sauri tace"Dan Allah ka fita na gaya maka baxan koma ba wlh"
      Cikin yanayi na alamar zai rarrasheta yaje zuwa riqo hannunta,taja baya da sauri had'e da fad'in "kar ka ta6ani bana so kuma dan Allah ka fita"
    Mohd yace"yi haquri ki saurareni"
  Tace"wlh indae akan komawa gidanka ne bazan ta6a saurararka ba don haka kawai ka fita"
   Cikin mugun damuwa kmr zai yi kuka ya jawota da sauri zuwa jikin sa yace"haba Ryynt wae ta yaya kike tunanin zan iya rayuwa ne ba ke"
  Ryynt dake yunqurin qwatar kanta tace"kan me wae ni to tunda dama can bada ni kake rayuwa ba"
      Idanuwansa ya d'aura a cikin nata cikin muyar natsuwa yace"sbd ina sonki Ryynt"
    Wani irin kallo ta mae snn ta girgiza kanta le6ace da baki tace"ni kuwa meye abin so a tare dani,nida sae wanda uwar sa ta mae baki ko zai soni"
    Kallon ta yayi a sanyaye dan ya fhmci inda ta dosa yace"pls Ryynt  ki daina zancen da ya riga ya wuce dan Allah"
  Ta fizge kanta daga jikin sa rae 6ace tace"Dan Allah ka fita to"
  Numfashi ya fitar cikin yanayin damuwa yana kallonta d'auke da idanuwansa da duk ya shiga damuwa sae sunyi jajur sun canza kala.
  Bata tare da yace komai ba ya juya ya fita daga d'akin.
 Ya wuce Saliha dake zaune a falo tana kallo,wacce ta bisa da kallo har ya fita sbd yanayin damuwar da ta gani a tare da shi.
  Nan ta tashi ta nufi d'akin Ryynt wacce ta sama rae 6ace.
  Taja hannunta suka zauna kan bed snn tace"Me yake faruwa ne Ryynt ko gida yake so ku koma baki tashi bane"
  Ryynt ta kalle ta kawae dan ta fhmci bata san komai ba.
  Saliha tace"kinga idan a kaina ne kawae ki koma gida gobe zanje can sae ma naje miki da mami ko"
  Ryynt ta qirqiro d'an guntun murmushi tace"saliha knn nifa a nn nake zama yanzu rabona da wancan gidan har na manta"
  Cikin mamaki saliha tace"kmr ya ban gane ba?
 Ryynt tace"uhm kedai mu bar zancen muci gaba da firar mu kawai"
  Saliha ta girgiza kanta tace"ina fa zancen fira kin d'auko min wata magana da najita banbarakwai me ya faru da kika dawo gidan inna da zama ko kin kusa haifuwa ne?
  Da sauri Ryynt tace" haifuwa?
Saliha tace"eh mana ba kmr ciki na gani a jikin ki ba yanzun da na shigo.
  Ryynt da ko kad'an bata ta6a kawo cikin yayi girman da za'a gane ba ta kalli saliha kmr zata yi kuka tace"wae ana ganin cikin?
  Saliha tace"eh nima sae yanzu na fahimta da na shigo"
  Kuka Ryynt ta fashe dashi saliha tace"kan me to tunda ba shege bane"
  Ryynt bata ce komai ba sae kukanta take don ba abinda take tunani irin qila ma a school kowa ya gane tana d'auke da ciki byn ko da kuskure  bata ta6a yarda ta nuna cewa mtr aure bace sbd bata so a sani.
  Saliha dake kallonta za tayi magana knn wayar Ryynt ta shiga ruri saliha ce ta d'auko mata wayar kan bedside drawer ta bata wacce kafin ta kar6a sae da ta tsagaita kukanta ta kalli mae kiran wato umman saliha snn ta d'aga had'e da kara wayar a kunnen ta.
  Tace"Na'am mama,eh ina ji"
Daga haka se tayi shiru lokaci mai tsawo tana sauraren umman saliha dake ta bata magana cikin rarrashi kan tayi haquri ta koma gidan mohd,wanda da fitar sa bai zarce koina ba sae gurinta dan yasan Ryynt zata ji maganar ta.
  Ryynt sae sauraren umman saliha take cike da qwalla tap a idonta don ko kad'an bata son komawa gidan mohd amma ba yanda ta iya dole ta amince akan zata koma d'in sbd ta d'auki umman saliha tamkar uwa da bazata iya musa mata ba.
  Tana gama wayar ne da en mintina sae ga kuma nasir ya sallamo da shima Man ne ya turo shi akan yaxo dan Allah ya qara bawa Ryynt haquri.
   wanda duk da cewa yasan irin zamanda Ryynt tayi a gidan man yana son ta koma dmn ya fhmci irin nadamar da man yayi,kuma ko don qaruwar da suka samu a tsakanin su yana son ta koma.
  Bayan sun amsa masa sallama ne ya shigo yasa Ryynt gaba yana rarrashi da ban haquri had'e da fhhmtr da ita ta kwantar da hnklinta inshaa Allah wnn karon zata ji dad'in zama ba kmr wancan karon ba.
  Ita dae saliha sae sauraren su take har nasir ya gama rarrashin da yake ya fita ita kuma ta d'aura da nata dmn a iya abinda  ta fhmta sa6ani Ryynt ta samu da man,wacce ta fhmci hkne tun daga kan wayar da taji tana yi da ummarta da kuma haqurin da nasir yazo yana qara bata.

Ita dae Ryynt gabad'aya jikin ta yayi sanyi dan ganin take shike nn rayuwar ta zata koma cikin qunci da rashin walwala.

Da dare guraren qarfe tara mohd ne ya shigo gidan ya sami inna a falo tana kallo ,ya gaida ta ta amsa ba yabo ba fallasa ya zauna jim kad'an snn yace"Ryynt fa?
 Inna tace"tana ciki na rasa meke damunta kmr wata marar lfy nake ganin ta yau"
  Man yayi shiru kawai don yasan ba wani  abu bane ke damunta sae rashin son komawarta gidan shi.
  Yace da inna "bari naje na ganta to"
 Tace"to"
snn ya tashi ya tafi d'akin Ryynt ya sameta kwance tana bacci yaje gab da ita ya duqa a hnkli yana kallon fuskarta da ke mai mugun kyau idan tana bacci.
  Ya jima a haka kafin yake maida dubàn sa kan jikinta da komai ya cicciko 6ul 6ul ya qara kyau da haske a nn idonsa yakai kan qirjinta da ya taso saman rgrta sbd yanda rgr ta d'an kama ta,
 kai tsaye ya kauda idon sa a gun ya maida duban sa kan cikinta had'e da d'aura hannunsa akai ya shafa d'an cikinta da ya taso snn ya kai hannu zuwa yaye rgr jikinta dmn yaga cikin.
  Se Ryynt ta shiga juyi a hnkli had'e da gyara kwanciyarta ta juya mishi baya.
   Nan ya miqe tsaye ya kalle ta kawae snn ya juya ya bar d'akin yayinda Ryynt ta bisa da ido dan dama ba bacci take ba jin zai shigo yasa ta qirqiro baccin qarya.

Shi kuwa mohd a nn falo ya sami inna naci gaba da kallonta ya zauna yayinda inna ta kalle sa tace"ya akayi  jikin ne ko kuwa?
Yace"Aa inna inaga bacci ne kawai don naji jikin nata ba zafi sae vacci da na samu tana yi"
Inna tace"inaga fa hkne sbd yau duk bata samu tayi baccin da ta saba yi ba sae fira da suka zauna ma yi ita da saliha wacce sae da yamma sosai ta bar gidan nn,
Mohd bai ce komai ba sae cewa yayi"to inna yaushe za'a bani Ryynt mu koma tunda dae ta amince zata koma.
  Inna tayi shiru don tun d'azu da yamma yazo da kanshi ya snr da ita cewa Ryynt ta amince zata koma gidan sa har taji dad'i a ranta don ynx sae taji tana son Ryynt ta koma sbd ko kad'an bata son idan sunje qauyen su Ryynt mai gari yaji cewa har auren Ryynt ya mutu shiyasa ta qara jawa mohd kunne sosai kan ya riqe Ryynt amana  kmr yanda Abba ya masa da yaje ya snr dashi.
  Inna tace"muhammadu ai kasan ko zata koma sae munje qauyen su tukun don tun ba yau ba kabiru ke jiran idan Ryynt sunyi hutu se muje"
 Mohd yace"inna idan qauyen nasu ba wani  nisa me zae hana gobe muje don Allàh dmn so nake jibi mu fara shiryen shiryen tafiyar mu nida Ryynt.
  Inna da dama tasan da zancen tafiyar sbd d'azun da yazo ya snr da ita ,
tace"to ai sae kaje ka snr da kabiru duk abinda yace kaga sae kazo ka snr dani.
 Mohd yace"to"snn ya tashi ya fita.

Yaje ya sami Abba ya snr dashi buqatar sa Abba bae musa mae ba ya amince ya dawo ya snr da inna, inna tace"to Allah kaimu goben"
  Yace"Amin snn ya fita"kafin yake yi mata sallama.

Koda ya fito gate ya  had'u da Amir ya faka motar sa knn ,
nn ya jira Amir d'in har ya fito suka gaisa .
  Bayan sun gama gaisawa ne Amir ke cewa"yaushe ne zakuyi tafiyar kaida Ryynt dan nima kwanakin nn so nake nayi tafiya zuwa wajen nn"
  Mohd yace"eh to idan na samu gsky ending of dis week nake son muje sbd nafi soñ nasha amarci na da Ryynt a waje"
  Amir yayi er dariya yace"ai fa ,hln wacce qasa zakuje ne to?
 Wlh abinda ya kawo ni knn jin ra'ayin qasar da take so muje so sae nazo na samu tana bacci wacce ko ba bacci take ba nsn baza ma ta gaya min ba.
  Amir yace"kawai to kuzo muje India a Mumbai city"
  Mohd yace"uhm kaji ka sbd kaima can kayi d'in ba"
  Amir yayi murmushi yace"eh kam shiyasa nake neman abokan tafiya sbd tafiyar zata fi dad'i"
  Mohd yace"haka ne gsky amma da germany naso muje sbd wasu kayan yara da na gani ina son siyowa a can but zamu fara zuwa India d'in dae daga baya sae muje Germany.
  Amir yace"olryt what about gyaran gidanka da naji kace kana so zaka yi"
  Eh yana nn har ma na yiwa nasir magana bcs so nake koda zamu dawo ya kasance an kammala canza komai na gidan sbd Ryynt nake son yiwa surprise.
  Amir yace"that's gud to ai indai Nasir ne ai kasan zai sa a maka komai kan time"
  Mohd yace"hakane ne gaskiya that's y na bashi kula da aikin ai "
Yana gama fad'ar haka ya d'aura da cewa"ni zan tafi akwai wani  aiki da nake son yi ne yanzu"
  Daga haka sukayi sallama ya fice shi kuma Amir ya shiga daga ciki.


Washe gari guraren 11am suka kama hanyar zuwa qauyen su Ryynt ,Abba inna,Nasir ,Amir,mohd,Ryynt saliha ,mami har umman saliha duk suna cikin masu tafiyar shiyasa suka  cika kusan mota biyu ,yayinda motar mohd ke d'auke da mohd dake jan motar se Amir ,inna da kuma Ryynt, motar Nasir kuwa shida Abba ne a gaba ,umman saliha, Saliha da kuma mami sune a baya.

Da suka isa qauyen cikin mutunci da karamci mai gari ya tarbe su cikin nuna matuqar farin ciki da zuwan su inda mai gari da kanshi ya shiga dasu gidan shi nn cikin wani babban falo na saukar baqi da aka qawata sosai da kuma hadaddiyar liyafar da aka shirya musu wa su kad'ai dan dama yasan da zuwan su, wanda kafin su fara sa albarka a liyafar sae da matan mai gari har 'ya'yan shi suka zo suka gaida su had'e da yi musu ya hanya yayinda kowanen su ya saki fuska yana mai fad'in "Alhmdlh"
ya muka same ku?
suka ce "lfy lau"

 Bayan sun sa albarka a liyafar da aka kawo musu ne en tsaran Ryynt dake nn qauyen sae zowa suke suna ganin Ryynt wacce ta saki fuska sosai suna maraba da ganin juna a nn ne wata er maqotan su Ryynt wato a lokacinda sukayi zama cikin gari taja Ryynt sae yawata wa suke a qauyen tare da saliha da kuma mami da suke janye da ita yayinda man ke can duk ya matsu yaga dawowar su haka kawai dashi kansa bai san dalilin matsuwar tasa ba.

Sun jima sosai a qauyen don sae yamma suka kamo hanyar dawowa wanda kafin su baro qauyen sae da sukayi wa mai gari d'inbin alhairi dashi har mutanen qauyen sa wanda hakan ba qaramin dad'i ya masa ba don sae godiya yayi ta musu ya kuma tara duk mutanen qauyen akan suyi musu  godiya kan alhairin da suka musu.

 Haka ma a gurin Ryynt sosai taji dad'in alhairin da aka yiwa mai gari da mutanen qauyen su amma kuma cikin mota sae kuka take ta son tayi sbd baffanta da ta tuna wacce gurin yawon su da suka je har inda aka kad'e Baffanta sae da taje  da kuma dajin da sukayi zama ita da baffanta ,
ga mamakinta bukkar su na nn daram ba a rushe ba shiyasa komai ya dawo mata sabo wacce a lokacin har sae da tayi er qwalla kan ganin bukkar dan ta d'auka koda zasu ga bukkar duk gara ta cinye sae ta samu abokin mahaifinta ne a ciki da shine ke kula da gonar sarki yanxu.

Mohd tuqi yake amma gabad'aya ya rasa natsuwar sa dan ta jikin mirror yana kule da irin yanayin da Ryynt take ciki amma haka ya dake har suka dawo garin kano Nasir dake tare dasu Abba shi ya sauka a family house mohd kuwa kai tsaye gidan inna ya nufa.

Wanda yana faka motar suka fito suka d'unguma gabad'ayan su cikin gidan inna yayinda mohd yabi Ryynt kai tsaye zuwa d'akinta wacce sam bata san cewa yana biye da ita ba don da shigarta d'aki kukan da ta matsu tayi shi ta fashe dashi zata fad'a kan bed mohd ya jawota ya rungume qam a qirjinsa had'e da kai bakin sa saitin kunnen ta yana rarrashin ta ba tare da yasan dalilin kukan nata ba.



Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮?🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮












_Wnn page in naku ne maryam sifawa n ummi bunxa Allah ya bar min ku akan qaunar da kuke min Luv u❤_


                🔮🔮🔮🔮
*```Page 68```*
A hnkli tayi saurin janye jikinta daga nashi ta zauna kan bed.
  Shima ya bita kan bed d'in ya zauna yana mae kallon ta sae fmn share hawayen fuskarta take yace"me aka miki ne?
  Komai bata ce mai ba sae girgiza kanta tayi alamar ba komai yace"to mene ne?
  Murya can ciki tace"ba komai"
  Tana gama fad'ar haka taji inna na qwala mata kira ta miqe had'e da fad'in "na'am inna"
  Mohd  ya bita da ido har ta fita ya sauke numfashi snn ya tashi ya fito d'akin ,
Amir dake zaune a falo yace"yauwa dama kai nake jira ka fito ka maida ni gida"
  Makulli kawae man ya miqa masa yace"je maida kanka ni ta matata nake tukun"
  Amir yayi dariya yace"hm abubuwan da angwaye keyi ne kaima ka soma"
  Mohd yace"Amir knn nidae ungo kar6i makullin ni ko a kabubu ne zan koma"
  Amir yace"ikon Allah lallai ka tsunduma da yawa a mota naga sae kallon yrnyr nn kake tayi hk a qauye da suka fita duk ka rasa natsuwarka yanzu mun dawo sae fmn bibiyar ta kake idan wata gare ka naga ai kana da mata sae kaje  ka rage qishirwar ka a can ko kafin ka sami wnn"
  Mohd dake kallon sa d'auke da murmushi ya girgiza kansa yace"kasan cewa idan kana jin qishin ruwa babu wani  abu da zaka sha ya kore ma wnn qishin gabad'aya har sae idan ka sami ruwan tukun,kuma ai malika da kake wani  zancenta kasan still basu dawo ba,kuma bibiyar Ryynt da nakeyi kai baka fhmci damuwar da take ciki bane dan Allah tun a mota"
  Amir yace"kewa ce fa ka sani ba wani  abu ba sbd dole ne ta tuna da rayuwar ta da tayi a baya musamman mutuwar mahaifinta"
  Jiki sanyaye Mohd yace"hkne shiyasa take ban tausayi wlh har bana son ganinta cikin damuwa komai qanqantar ta kuwa"
  Amir bai ce komai ba sae kalar tausayi da ya nuna a fuskar sa yayin da man yace"muje to muyiwa inna sallama sae mu tafi ko"
  Nan Amir ya tashi suka tafi d'akin inna wacce suka samu ta tsiyaya wa Ryynt fura a cup tace"ungo kar6i kisha idan kin gama sae kije ki d'an watsa ruwa ko jikin naki zai d'an sake miki.
  Ryynt ta kar6i fura ta fara sha sbd har da yunwa na damunta don bata wani ci abinci sosai a qauyen ba.
  Man dake kallonta ya maida dubansa gun inna yace "inna mu zamu tafi sae anjima idan na dawo"
  Inna tace"to en albarka Allah hutar da gajiya"
  Suka ce"Amin"snn suka fita.

Guraren qarfe tara na dare sae ga mohd ya koma dawowa gidan, d'akin inna ya fara zuwa ya samu tana bathroom yayinda Ryynt ke kwance kan  bed kmr wata mara  lafiya sanye da kayan baccin ta riga da wando,
 sae da ya ajiye ledar da ke hannun shi snn yaje gab da ita ya zauna had'e da riqo hannun ta yana mae kallon fuskarta,ta kalle sa sau d'aya ta kauda idonta snn ta zare hannunta a hnkli tare da juya mai baya ya kalle ta kawae snn ya kalli inna wacce ta fito daga bathroom knn ya gaida ta ta amsa ba yabo ba fallasa snn yace"ya gajiyar hanya tace "Alhmdlh ai ba wata gajiya yanzu sae bacci ita Ryynt kaga har ta samu tayi baccin ma"
  Nan Mohd ya kalli Ryynt da kulawa snn yace"idonta biyu fa inna maybe dai baccin take ji "
  Inna tace"au to shine kazo kayi zaune ka sata a gaba kana kallo awa wanda ke shirin had'iye ta"
 Mohd yayi murmushi  kawae had'e da d'aga wayar sa da ta shiga ruri bayan ya gama wayar ne yace"inna ni zan tafi nayi baqo a gida ne"
  Tace"to sae da safe d'an albarka Allah kiyaye hanya"
 Yace"Amin"
snn ya fita ba tare da ya d'auki ledar da ya ajiye ba don dama fruits ne ya siyo musu.

Washe gari tun da safe Ryynt ce ke harhard'a en kayanta da zata je dasu gidan su Saliha sbd umman saliha ce ta nemi inna da tana son Ryynt taje mata kafin su tashi tafiya.
  Bayan ta kammala komai da qarfe goma nasir yazo ya d'auke ta ya kaita.
 Da 11 sae ga mohd yazo gidan inna don shi bae san da zancen zata je gun umman saliha d'in ba sae a bakin inna yaji.

Tunda Ryynt taje gidan su saliha aikin komai bata yi sae gyaran jiki da umman saliha keyi mata taci wnn tasha wnn ta shafa wnn sae duk nn take jikinta ya fara nuna sauyi don wani  irin haske ta qara tana sheqi kmr wata amarya duk fatar ta ta canza gabad'aya cikin en kwanakin da basu wuce uku ba wanda a cikin kwanakin sosai mohd yaso ganin Ryynt kmr me amma umman saliha bata barshi ba don tasan duk ta yarda yaga Ryynt ba lalle bane ya iya haqurin barinta kan irin gyaran da tasha ita kuwa tafi so sae sunyi tafiyar ko komai zai wankana.
    A cikin en kwanakin sae duk mohd ya soma ramewa sbd kawai rashin ganin Ryynt da yaji kmr ya kwashe wasu shekaru ne bai ganta ba.
  Next day ne tafiyar su India shiyasa da dare umman saliha ta tasa Ryynt gaba tana mata en nasifofi snn ta bata turarukkan mata masu qamshi kusan kala biyar da zata riqa amfani dasu idan tayi wanka zata shiga bacci.
  Sosai Rynt ta mata godiya dmn taji dad'i har ranta duk da cewa har yanzu jikinta mace yake na rashin son komawarta gidan man.
    Nasir ne yazo ya maida ta gidan inna ita da saliha sbd saliha so take ta kwana gidan inna dmn gobe da safe tana son taga tafiyar su Ryynt.

   Washe gari tun da  safe suka tafi.
 Cikin jirgi Ryynt sae kuka take tayi man kuwa duk ya sukuikui ce yana faman rarrashin ta da qyar ya samu tayi bacci ,
Ya kafe ta da ido sae kallon yanda ta kame sosai a jikin sa yake don ko da ya jirgin ya tashi a tsorace take sbd bata ta6a shiga jirgi ba ko a mafarki wnn ne karo na farko.
  Koina tsit sae ajiyar zuciyarta ke fita a hnkli kan kukan da tasha man kuwa baya da aiki sae na kallonta har baya son qiftawa sbd gabad'aya ta canza mae da mugun kyaun da tayi sae wani  murza ftr hannunta yake tayi a hnkli kan laushin da yaji a tare da ita har baya son dainawa wanda nn gurin da yake ya jure ne kawai dan shi kad'ai yasan irin abinda yakeji.
  Shidai Amir yana can nasa gefe shida matar sa da d'ansa dan tare yazo dasu.

Bayan sun isa da dare  sunje masauki har ma sunci abinci Ryynt na kwance inda tayi sallah tana sauke gajiyar zaman jirgi man kuwa kayan jikin sa ne yake ragewa zai watsa ruwa ,
da ya gama cire kayan ne ya fad'a bathroom koda ya fito Ryynt tayi bacci abinta,ko kad'an bai so tashin ta ba  amma yana son ta d'an watsa ruwa ko zata fi jin dad'in baccin.
  Nn ya durqusa gab da ita ya shiga kiran sunanta a natse ta bud'e idonta cikin yanayin jin bacci ta kalle sa,
 ba shiri ta kauda idonta da sauri sbd farin boxer ne kad'ai a jikin sa  bai riga yasa farar singlet din da ke hannun shi ba .
 Sae da ya saka singlet d'in snn yace"tashi kije kiyi wanka sae kizo kici gaba da baccin ko"
  Ba musu ta tashi ta nufi bathroom ya bita da ido har ta 6ace ma ganin sa ,ya lumshe ido had'e da fitar da numfashi a hnkli snn yaje ya shafa mai ya feshe jikin sa kaf da turare ya kwanta yana mae jiran fitowar ta.
  Yana nn kwance  ya fara jin saukar ruwan sama kad'an kad'an har suka soma yawa Ryynt dake bathroom duk ta tsorace sae sauri take ta gama wankan dan sae walqiya ake tayi da iska sosai dake kad'awa.
  Ai kuwa tana gama wankan ta nufi towel rack da sauri zata jawo towel sae kawai wuta ta d'auke duhu ya bayyana had'e da wata irin tsawa da akayi mai firgitarwa.
     Lokaci d'aya ta fasa wani irin Ihu cikin jin tsoro wacce sae jin tayi man ya cicci6eta,
ta wani qanqame shi sosai sbd wata irin tsawa da aka sake yi da tasa ta fashe da kuka cikin mugun tsorata har sae da man dake d'auke da ita ya shiga mata addu'a yaje da ita kan bed  yana qoqarin saisai ta ta ta hanyar rarrashi  bata iya shiru ba don har lokacin ba haske ko kad'an kuma sae tsawa ake tayi had'e da walqiya da wani  irin iska mai qarfi,
Nn ya had'e bakin su dmn samun natsuwarta yayinda take manne a qirjin sa sae rawar tsoro take  yana faman shafa bayan ta alamar rarrashi ,
Da sauri ta zare bakinta gabanta sae dukan uku uku yake tana kame kame sbd kayan da tasan babu a jikinta murya can qasa mai d'auke da jin tsoro tace"ka kunna mana haske ina jin tsoro"
 Bai ce komai ba sae jikinsa da ya nemi janye daga nata tayi saurin riqo shi ta saddà kantà qasà cikin jin kunya kmr yana ganinta tace"ba kaya a jikina ka bani abu na rufa jikina tukun"
  Kasa komai yayi don sae ta saukar mai da wata irin kasala nn ya jawota kawai ya rungume had'e da lumshe ido yayin da baka jin qarar komai sae saukar ruwan sama ,Ryynt da duk ta kasa sake jikinta tace"meye hk ka tashi dan Allah kar a maida wuta gashi ba kaya a jikina.....gabanta ne yayi mugun fad'uwa sbd hannun sa da taji kan qirjinta yana shafawa kafin ta iya cewa komai se bakin shi taji a cikin nata nn fa jikinta ya kwashi rawa tana neman qwace kanta amma ta kasa sbd irin riqonda yayi mata.
 Kisin d'inta kawae yake lokaci d'aya taji bakinsa a qirjinta,ta sakar masa kuka a tsorace tana faman turashi amma mohd yaqi kyaleta sae abubuwa yake mata masu rikitarwa da yasan kai tsaye zasu kashe mata jiki, take kuwa yayi nasarar kashe mata jiki sae  narke mai da tayi yaci gaba da romancin d'inta son ranshi ,
 yana gab da cimma burinsa ne ta soma yin kuka tana turashi tana fad'in bata so,bata so, da qyar cikin kasalalliyar murya can ciki yace"plz Rynt ki taimaka min wlh bazan iya haqura ba"
  Kuka ta shiga yi tana girgiza kanta had'e da yunqurin miqewa nn ya shiga rarrashinta sosai yana bata haquri akan ta barshi yayi amma sam taqi ,
ganin haka yasa ya danne ta ya soma aikin sa yayinda take ta kuka tana faman kokowa dashi amma sam bai saurara mata ba har sae da yaji he is totally satisfied snn ya jawota ya qanqame ta sosai a qirjinsa ya lumshe ido yana jin wani irin mugun sonta na fizgar shi.




Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮?🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮















                🔮🔮🔮🔮
*```Page 69```*
Hawayenta ne yaji suna sauka a hnkli kan qirjinsa ya kira sunanta a hnkli bata tanka shi ba ta qyale shi sbd wahalar da take ciki ko magana ma bata son yi don sae taji kmr yaune ta soma sanin d'a namiji a rayuwarta don wani  irin mugun zafi take ji a qasanta  har bata son tayi wani  motsin kirki.
  Mohd kuwa sae kallon ta yake cike da tausayi don shi kan shi yasan ya bata wahala ba kad'an ba.
   Ya sake kiran sunanta a karo na biyu bata tanka shi ba sae kuka da ta soma yi cikin dasassiyar muryar ta da tasha kuka.
    Wacce duk ta tattara zanin gadon ta rufe jikinta dashi sbd wutar da aka jima da maidawa bcs dama ba wutar gari ce aka d'auke ba daga laifin mitar gidan ce.
Man yakai hannu ya rage hasken d'akin snn ya nemi cire mata zanin gadon amma ta kama ta rirriqe ta hana shi cire zanin bai takurata ba sae d'aukar ta da yayi ya nufi bathroom da ita wacce tasha kuka ba kad'an ba don wanka ya mata kan dole ya kuma gasa mata jikinta sosai snn ya fito da ita ya kwantar kan bed sae kuka take marar sauti har tayi bacci.
  Mohd dake zaune can gefe guri d'aya ya sauke numfashi had'e da matsowa gab da ita ya kwanta tare da jawo ta zuwa qirjinsa ya rungume yana ta kallon fuskarta dake masa mugun kyau idan tana bacci,
 a hnkli ya d'aura lips d'insa kan goshinta ya mata kiss yana mae ci gaba da kallonta cike da so  daga haka ne shima bacci ya kwashe sa sae safe.


Washe gari mohd ya riga Ryynt tashi yaje bathroom ya d'auro arwala yazo ya sameta ta farka amma bata tashi daga kwancen da take ba sae hannun ta da take d'an moving dashi kan bed ,
ya durqusa gab da ita had'e da riqo hannunta yana mai kallonta cike da tausayi bata kalle sa ba sae hannun ta da ta  janye taje zuwa share qwallar da suka zubo mata ya riqe hannun ya kai nasa hannu ya share mata qwallar had'e da fad'in "yi hqr tashi kije kiyi arwala kizo muyi sallah kinji"
   Shaye da toka ta kalle sa kawae ba tare da ta iya ce masa komai ba don  kanta ke mata masifar ciwo a gurin ga zuciyar ta dake ta faman tashi,ba'a fi minti d'aya ba ta miqe lokaci d'aya ta tafi da gudu zuwa bathroom tana kwara amai ta samu da qyar aman ya tsaya mata mohd dake riqe da ita shi ya taimaka mata ta wanke bakinta ta d'auro arwala snn suka je sukayi sallah ko shi a daddafe tayi sllr wacce tana idarwa sae kwanciya tayi kan darduma mohd dake addu'a kallonta kawae yayi yaci gaba da addu'ar sa da ya gama ya tashi yaje ya bud'e fridge ya d'auko gasasshiyar kaza yaje ya mata warming sae gashi ya dawo d'auke da fresh milk a cup da kuma naman kazar da ya saka a cikin plate.
  Yazo ya durqusa gab da ita yana kiran sunanta a hnkli bata tanka shi ba don har bacci ya kwashe ta a lokacin shi kuwa bae kula da hakan ba sae zama da yayi tare da janyo ta zuwa jikin sa ya cire mata hijab nn ta soma kuka dan sae a lokacin ta farka ya kira sunanta a natse yana ta6a jikinta da yaji ya soma yin zafi bai ji dad'in zafin jikin ba dan sae yaji damuwa a ransa.
   Ryynt dake kan jikin sa sae qoqarin zamewa take ta kwanta kan darduma bai barta ba sae qara kwantar da ita yayi kan qirjinsa ya d'ebo naman kaza zae bata tayi saurin girgixa kanta alamar bata so ya ajiye naman ya shiga rarrashinta kan tasha ko fresh milk ce nn ma taqi kan dole ya barta ta koma kan darduma tayi kwanciyar ta bata jima ba bacci ya koma d'aukar ta.
Baccin qwarai tayi dan ba ita ta farka ba har sae da akayi sllr zuhur ta tashi a daddafe dan har lokacin bata jin dad'in jikinta taje tayi wanka ta fito ta nemi er doguwar riga ta saka snn ta sanya hijab tayi sallah a nn gurin tayi kwanciyar tana d'an jin tashin zuciya nn ta lumshe idanunta a hnkli
sae ga man ya shigo d'akin tana jinsa tayi kmr bata san da shigowar sa ba shi kuma yayi tsaye yana kallon ta d'auke da kular abincin da ya kar6o a gurin su Amir dan duk cikin gida d'aya suke kowa dae da nasa 6angare.
 Kan dining yaje ya ajiye abincin snn ya d'auki breakfast d'inta dake ajiye tun d'azun ya fita dashi dan yasan yanzu kam lokacin cinsa ya wuce sae dae kuma lunch.
   Bai wani  jima ba ya dawo ya same ta kmr yanda ya barta wanda duk a tunanin sa bacci take.
Ita kuwa tana nn kwance cikin jin jiki har akayi sllr la'asar,yayinda man ke zaune sae kula yake da duk wani  motsi nata.
Ganin anyi sllr la'asar ne yasa yaje yayo sllr ya dawo ya sameta itama tayi sllr tana zaune  kan darduma ta had'e kai da guiwa tana fama da kanta dake mata masifar ciwo.
   Yazo gab da ita ya durqusa ya shiga kiran sunanta a natse tayi kmr bata ji sa ba don ko magana bata son a mata.
   Nan ya tashi ya d'ebo mata abinci ya kawo gabanta ya ajiye yace cikin muryar rarrashi "yi haquri kici abinci dan Allah kinga tun safe komai baki ci ba kinji"
  Rynt kam qamshin abincin soma damunta ma yayi nn take taji cikinta ya hautsine ta soma yunqurin amae bai bar ta tashi ba ya riqe ta dan yasan ko taje wahala kawae zata yi dan ba wani  abu taci ba,nn ya kwantar da ita kan qirjinsa yakai hannu yana shafa bayanta yayinda ta cusa fuskarta gabad'ya cikin qirjinsa tana shaqar qamshin turarensa da ya soma kwantar mata da zuciya daga haka ne bacci ya kwashe ta sae kallon ta yake cike da tausayi dan yasan dole tana jin yunwa gashi jikinta har yanxu yana d'auke da zafi.

  Yana nn zaune abinshi rungume da ita sae bacci take ya soma jin zafin jikin nata sae qaruwa yake musamman kan goshinta nn ya d'auke ta yaje ya kwantar kan bed ya jawo wayar sa ya kira Amir ya gaya masa irin magungunan da yake buqata.
  Ba jimawa yaji knocking yaje ya bud'e qofa,
Amir dake tsaye a bakin qofar yace"inace  dae jikin da sauqi koh?
  Mohd yace"to jikin nata sae zafi yake tayi tun safe har yanzun wlh gashi tana fama da yunwa don tun safe komai bata ci ba yanzu da na kawo mata abinci ko qamshin sa ma bata son ji bare ta iya cin sa.

  Amir ya nisa tare da fad'in"bari naje to nasa my wife ta mata farfesun kifi ko zata iya cin sa"

 Mohd yace"olryt tnks"
snn ya kar6i ledar magungunan da Amir ya miqa masa ya maida qofa ya rufe yaje ya ajiye ledar magungunan kan bedside drawer  ya zauna jiki sanyaye kusa da Ryynt yana kallonta cikin tsabar tausayinta da yake ji don kallo d'aya zakayi mata kasan cewa tana jin jiki.
  Bata wani jima da baccin ba ta farka sae juyi take tana neman fad'owa kan gadon mohd da ya fito daga bathroom yaxo da gudu ya tarbota,
 ta dafe  kanta dake mata masifar ciwo har bata son bud'e idonta sae hawaye kawae dake fitowa a idanun nata.
     Fuskar sa d'auke da tausayi yakai  hannu yana share mata hawaye snn ya jawo farfesun kifin da mtr Amir ta kawo mata tana bacci.
 yana bud'e kular farfesun kifin knn,
 taji tashin zuciya sosai bakinta ya cika tap da yawu ta tashi aguje ta nufi bathroom tana kwara amae mai wahalar gske dmn amman kumallo ne kawae,
 tana gama amman ta samu da qyar ta wanke bakinta sbd wani irin jiri da ke d'ibar ta ga ciwon kai kuma.
  Mohd ya riqo ta zae taimaka mata su fito bathroom d'in ta zame jikinta a hnkli ta zauna qasan tiles d'in bathroom d'in ta had'e kai da guiwa sae numfashi take fitarwa a wahale.
  Mohd dake durqushe gabanta yana kallonta kmr ya cire ciwon yake ji ya maida jikin sa.
  Cikin damuwa kmr zae yi kuka yace"Ryynt yi hqr tashi muje ki d'an ci wani abu sae kisha magani kinji"
  Da qyar murya can ciki tace"um um bazan iya cin wnn farfesun kifin ba ka fita dashi dan Allah"
   Mohd yace"shike nn idan na fitar me kike son a kawo maki kici to"
   Cikin muryar kuka tace"nima ban sani ba kawai kaje ka fita da farfesun kifin tukun"
 Nan ya kalleta snn ya tashi yaje ya d'auki farfesun kifin ya fita dashi wanda ya d'an jima kafin yake dawowa d'auke da ledar snacks a hannun sa yaga still bata fito daga bathroom ba yaje ya sameta kwance  qasan tiles har ta koma yin wani bacci kuma,
ya d'auko ta ya fito da ita ya kwantar kan bed.
  Yayi zaune gefen gadon had'e da dafe kansa don ko kad'an bae so ta koma yin baccin ba har sae ta d'an samu abinda taci ta kuma sha magani tukun.

 Ba ita ta tashi daga baccin ba sae bayan isha'i ta tashi cikin kukan wahala  dan wata irin yunwar masifa take ji ga jikinta da mugun zafi har ita kanta bata son ta6a jikin nata.
 Mohd dake zaune tun d'azu zaman jiran farkawarta ya janyo ta a hnkli zuwa jikin sa yana share mata qwallah had'e da rarrashinta,
 ta qara narkewa sosai a qirjinsa murya can ciki tace"zanci abinci"
 Jikin sa na rawa ya jawo kular abincin su da aka kawo musu na dare ya d'ibar mata abincin a plate ya d'ebo a spoon zae kai bakinta ta kalli abincin kawae ta kauda kai,snn ta kalle sa qwalla tap a idonta kmr zasu zubo tace"kayi hqr dan Allah ni bazan iya cin wnn abincin ba idan da abun sha ka bani"
   Jiki sanyaye ya maida abinci ya ajiye snn ya jawo pillow ya kwantar da ita don ya fhmci ko zama bata iya yi.
  Ya tashi yaje ya bud'e fridge ya tsiyayo mata fresh milk ya kawo mata had'e da snacks d'in da ya siyo mata a d'azun ya shiga bata da kanshi ta d'anci ba sosai ba sae fresh milk da ta d'an sha rabin d'an qaramin cup tace zatayi sallah ya bata magunguna tasha snn ya ja hannunta zuwa bathroom ya taimaka mata har wanka tayi snn tayi arwala suka fito .
Tayi sallolin da ke kanta wacce da qyar taga ta kammala sallolin sbd har lokacin kanta kamar zae tsage take ji  amma ta fara jin qarfin jiki dae dae gwargwado sae dae a kwance tayi addu'a dmn in ta kwanta ciwon kan na d'an
mata sauqi.
   Mohd yazo ya sameta gurin ta kammala addu'a ya riqo hannunta tare da fad'in"zo muje to na kaiki kan bed ki kwanta koh"
   Komai bata iya ce masa ba har ya tallabeta cak sae kallon sa take tayi har yaje da ita kan bed ya kwantar.


Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮















                🔮🔮🔮🔮
*```Page 70```*
 Washe gari mohd ne ya tashi daga bacci ya kalli Ryynt dake kwance kusa dashi tana bacci yakai hannu ya yaye farin handkerchief d'inda ke kan goshin ta ya d'aura tafin hannun sa akai yaji still akwai zafi a goshin nata,ya lumshe ido cike da damuwa yana tunanin dole sae ya mata allura knn dan jiya cikin dare sosai ciwon kan ya dame ta sae kuka take ta kasa  bacci har sae da ya koma bata magani ya kuma yi zaune da farin handkerchief d'in sa yana tsomawa a ruwa idan ya matse snn ya d'aura mata kan goshinta yana rage mata zafin kan har ya samu tayi bacci.
  Jiki sanyaye ya sauka kan gadon yana mae kallonta snn ya nufi bathroom koda ya fito ya same ta zaune kan bed ta had'e kai da guiwa yaje ya zauna gab da ita ya d'ago kanta ya ta6a goshinta yana kallon fuskarta yace"har yanzu kan bae daina maki ciwo ba ko"
  Cikin sanyin murya tace"um um ya daina min"
   Ya sauke ajiyar zuciya yace"to ya naji jikin naki da zafi ko wani  abu ke maki ciwo ne?
   Ta girgiza kanta tace"ba komai"
  To muje na kai ki bathroom kiyi arwala ko,
  Ta kalle sa tace"zan iya zuwa da kaina"
  Nan ya barta ta tashi sae kallon ta yake har ta shige bathroom snn ya tashi ya fita.
  Koda ya dawo ta idar da sallah tana kwance  kan darduma tana bacci yaje a hnkli ya cire mata hijab ya maida ta kan bed.

Sae guraren qarfe goma ta tashi koshi wayar da man keyi ne ya tashe ta,
Ya katse wayar ya kalli Ryynt da ta tashi zaune cikin jin bacci yace"sorry Ryynt na tashe ki ko"
  Bata ce komai ba sae sauka taje zuwa yi kan gadon da sauri, ya riqo ta yace"amae"
 Ta sadda kanta qasa cikin jin kunya tace"Aa zanyi fitsari ne"
  Yace"to jeki"
 Nan ta tashi ta wuce bathroom bayan tayi fitsari ta cire tufafin jikinta tayi wanka ta jawo towel ta d'aura taxo tayi tsaye riqe da kayan da ta cire a hannunta ta kasa fitowa sbd hijab d'inda bata tare dashi.
  Tana tsaye kusan minti biyar taji an turo qofar bathroom d'in sukayi ido hud'u da man tayi saurin sadda kanta qasa shi kuma yayi murmushi had'e da kar6ar kayan da ke hannunta yace"me kike so ne da kika kasa fitowa?
 Ba tare da ta d'ago ta kalle sa ba tace"hijab nake so"
  Ba musu ya juya yaje ya d'auko mata hijabin ya kawo mata ta saka hijabin snn ta fito shi kuma ya fita ya bar mata d'akin domin ta shirya.

 Sae da ya tabbatar ta kammala shiri snn ya dawo ya sameta riqe da wayarta a hannunta tana neman gurin saka caji ya kar6i wayar yaje ya saka mata caji snn yaja hannun ta zuwa kan dining ya ja mata kujera ya zaunar da ita snn shima ya zauna kusa da kujerar da take zaune ya zuba musu abinci a plate da'ya wato arish, plantain da kuma soyayyen qwai sae ruwan zafin tea da man ya zuba a cups ya had'a musu snn ya kalli Ryynt da kallon sa kawae take yana aikin.
   Ya d'ebo arish a fork spoon zae kai bakinta ta kalle sa had'e da kar6ar fork d'in ta shiga ciyadda kanta shima ya shiga ci sae yi yake yana kallonta sbd yaji dad'in ganin bata ji amae ba don tun lokacinda ya bud'e kula yake ta Allah Allah kar tace zatayi amae.

Bayan sun kammala cin abincin ne sae ga matar Amir ta shigo gaida Ryynt da jiki a nn Ryynt ke tambayar ta sadiq tace wlh sun fita shida Abban shi nn suka zauna shiru sae jefi jefi suke magana sbd ba wani  sabawa akayi da juna ba man kuwa tun lokacinda ta shigo suka gaisa ya fita ya basu guri wanda ya jima kafin yake dawowa ya samu matar Amir tuni ta koma 6angaren su sae Ryynt kad'ai ya samu kan bed kwance lamo kamar mai bacci yaje gab da ita ya durqusa ta d'ago ido ta kalle sa kmr zata yi kuka dan duk ta soma jin kanta a kad'ai ci.
    A hnkli ya shafo gefen fuskarta yace"mene ne?
    Cikin yanayin kukan da take d'auke da shi ta janye hannun sa dake kan fuskarta tace"ni ka kira min inna"
  Sae da ya tada ta zaune snn ya ciro wayar sa a aljihu ya kira mata inna ,ya miqa mata wayar ta kar6i wayar da hanzarinta ta kara wayar a kunenn ta cikin amsa sallama dan lokacin har inna ta d'auka.
   Washe da baki inna tace"Ryynh kece"
 Ryynt tace"eh inna ina wuni"
  Tace"lfy lau Ryynh ai ni duk kun tashi hankali na ko na kira ba'a samun wayar ko d'ayanku sae ata min wani  banzan turanci can "
 Ryynt tace"eh inna ni wayata ba caji a kashe take"
 Inna tace"ayyo haka kuwa nasiru ya gaya min cewa wayoyin naku duk a kashe suke wae lokacinda na kira baku sauka a jirgi ba amma yayi waya da Amir bayan saukar ku yace masa kun isa lafiya har ma kuna masauki,
inace kuna zaune qalau dae ko"
  Ryynt tace"eh inna"
   Inna tace"to ya nake jin muryar ki kmr marar lafiya"
  Sae da ta kalli man ta gefen ido snn tace"lafiya ta qalau inna ba komai"
  Inna tace"to muhammadu fa"
  Ryynt tace"gashi"had'e da miqa masa wayar ya kar6a d'auke da murmushi ya kara wayar a kunnen sa suka gaisa daga haka ya soma yin dariya yana ta ba inna haquri,Ryynt sae kallon sa take dan kmr bata ta6a ganin dariyar sa ba sae yau.
    Yana gama wayar ne ya kalleta d'auke da sauran dariyar da ke kan fuskar sa yace"wae kinji inna sae fad'a take ta min wae ban kirata nace mun iso lafiya ba shine nake bata haquri"
    Ryynt dae bata ce komai ba sae d'an murmushi da tayi a fuskarta man dake kallonta d'auke da nashi murmushi ya tashi yaje ya d'auko wayarta da ya saka mata caji ya saka mata sabon layin da ya siyo mata ya bata wanda ya cire yace"ki ajiye wnn sae idan mun koma zaki ci gaba da aiki dashi,
 a nn kuma wanda na saka miki d'in nn ynx shi zaki riqa amfani dashi kinji"

 Ta gyad'a masa kai  had'e da kar6ar wayarta da ya bata koda ta duba har copying numbers yayi mata don duk ta sami numbobinta a ciki.
  Sai da ya d'an fita snn ta kira umman saliha wacce tana ganin numbar waje ta san cewa Ryynt ce tana d'aga wyr kuwa taji muryar Ryynt nn suka gaisa fuskar kowannen su d'auke da murmushi sae waya suke lokaci mai tsayo cike da nishad'i dan har saliha da mami duk sae da tayi waya dasu ai kuwa duk wani kad'ai cin da ta soma ji taji ya tafi.


Da yamma man ne cikin shirin sa zai fita sbd wasu kayan amfani da yake son siyo musu yayiwa Ryynt sallama ya kama hanya zae fita har yakai hannu zae bud'e qofa sae kuma ya juyo,
Ryynt dake kallon sa tayi saurin sadda kanta qasa yazo gab da ita ya d'ago fuskarta yana kallon manyan idanuwanta da suka ciko da qwalla yace"mene ne ko kina zuwa muje?
  Da sauri ta gyad'a masa kai, yaje ya d'auko mata hijab ya saka mata da kanshi yaja hannunta suka fita.

Kan hanya Ryynt sae kallon gurare take tayi da suka mugun bata sha'awa har suka isa wani makeken mall,
nn fa ta shiga ba ido haqqinsa don gurin ya had'u iya had'uwa kmr wata aljannar duniya yayinda man ke janye da ita yana musu siyayya ya tafi da ita gurin rigunan bacci ya ciro kusan kala biyar masu shegen kyau da baza su wuce iya cinya ba ita dae Ryynt sau d'aya ta kalli kayan ta kauda fuskarta dan jin tayi kmr ta nitse don kunya dan taga tsiraicin kayan sosai wacce duk a tunanin ta malika ya siyawa dan ita taga tana saka irin su.
   Bayan sun dawo gida har anyi sllr magrib da isha'i Ryynt na kwance kan darduma lumshe da ido tana jin bacci mae dad'i na son fizgarta,
 bata ji shigowar man ba sae qamshin turaren sa da taji gab da ita nn ta bud'e idanunta a hnkli ta ware su akanshi ya dafa goshinta tare da fad'in"jikin ne?
Tace"um um bacci nake ji"
  Yace"to muje muci abinci sae ayi wanka koh?
  Ba musu ta tashi suka je kan dining sae dae bata wani ci abincin sosai ba sbd baccin da ya mata yawa a ido ta ture plate d'in gabanta zata tashi man ya riqo ta yace"ba dae amae ba?
  Kallon sa tayi snn tace"um um wanka zanyi nayi bacci"
  Yace"indae wanka ne zan miki zauna ki qarasa cin abincin ki tukun"
  Tace"um um ya ishe ni fa"
 Yace"yi haquri dae ki qara ko kad'an ne kinji"
   Ta girgiza kanta alamar a'a bae kula ta ba sae jawo plate d'inta da ta ture  yayi zae ci gaba da ciyadda  ita,cikin yanayin jin bacci d'auke da shagwa6a ta fashe mai da kuka,
da sauri ya ture plate d'in yace"yi haquri muje ayi wankan to"
  Tace"um um nida kaina zanyi"
   Yace"to tashi kije ki cire kayan jikin ki kafin na had'a maki ruwan wanka"
  Nan ta tashi taje zuwa cire kaya shi kuma ya nufi bathroom  ya had'a mata ruwan d'umi ya fito snn taje  ta shiga.

Koda ta fito ta samu ya ajiye mata d'aya daga cikin rigunan baccin da taga ya siyo ai kuwa ta zaro ido tana kallon rigar snn tayi murmushin mamaki wae ita ya siyo ma kayan knn ashe kuwa zasu tabbata ba'a sa ba.
  Nan ta wuce abinta ta bar rigar taje ta ciro turarukkan da umman saliha ta bata ta shafa.
   Bayan ta gama shafa turarukkan ne ta bud'e wardrobe ta nemi kayan baccin ta sama da qasa bata gansu ba     nn tasan cewa mohd ne ya d'auke su don  kawae tasa waccan rigar da ya ajiye mata.
  Rai 6ace cikin kukan shagwa6a taje tayi kwanciyar ta kan bed ta soma yin baccinta sanye da hijab da  towel d'in da ta fito wanka dasu.

Mohd ya shigo yayi tsaye yana kallonta d'auke da murmushi snn ya kalli rigar baccin da ya ajiye mata da ta ture gefe.
  Ya tafi kawae ya cire kayan jikin sa ya fad'a bathroom yayi wanka ya fito snn yaje yayi shirin bacci ya dawo gun Ryynt da har baccinta ya soma nisa ya jawota a hnkli zuwa jikinsa ya cire mata hijab nn yaji wani irin kamshin dad'i yana fita a jikin ta ya rungume ta had'e da lumshe ido yana shaqar qamshin ,
ba  abinda ya fad'o masa a rai a lokacin sae daren rnr da suka zo yana mae tuna kaf abinda ya faru tsakanin sa da ita dan daren ya masa dad'i ba kad'an har baya jin zae iya manta shi a rayuwa.
  A kasale ya d'ago ta zae cire mata towel ta farka firgigit had'e da riqe towel d'in gam ta kalle sa cike da shagwa6a tace"meye haka?
   Yace"rigar bacci zan saka miki"
  Ta ware manyan idanun ta tace"wace rigar?
  Yace"wacce kika samu na ajiye miki kan bed"
  Ta maqale kafad'ar ta cikin muryar shagwa6a tace"Allah ni bazan iya saka wnn abin kunyar ba,kawae ka bani kayan bacci na da ka d'auke min"
  Mohd dake kallon yanayin shagwa6ar ta abin sha'awa yayi dariya yace"yi haquri ki saka kinji"
  Tace"um um ban so"
Nan kawae yayi murmushi tare da kwantar da ita kan qirjinsa yana shafa bayanta yace"shike nn yi bacci tunda ba kya so".




Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮















                🔮🔮🔮🔮
*```Page 71```*
Kasa d'agowa tayi daga kan qirjinsa ta lafe abinta tana shaqar kamshin turaren sa mae saka natsuwa daga nn fa bacci yayi awon gaba da ita.
   Mohd sae kallonta yake har sae da ya tabbatar baccinta yayi nisa snn ya soma zare mata towel sannu a hnkli har ya zare sa gabad'aya ya d'auko rigar bacci zae saka mata yayi tsaye yana kallon albarkatattun qirjin ta dake matuqar bashi sha'awa kan cikar su da kuma yanda suke tsaye a jikin su.
  A hnkli ya sauke idanun sa kan cikin ta da ya d'aura hannun sa akai yana shafawa yayinda yake fata a ransa Allah ya nuna masa abinda ke ciki ya fito lafiya.
 Daga haka ne ya saka mata rigar bacci ya kwantar da ita d'auke da murmushi a fuskar yana mae kallon yanda rigar baccin tayi d'as a jikinta ta kuma yi mata kyau sosai.
 yasa blanket ya rufa mata jikinta snn ya d'auke hijab da towel yaje ya kaisu inda ya dace ya dawo ya kwanta tare da kashe musu wutar d'akin.

Washe gari ya fito daga bathroom Ryynt dake zaune kan bed ta had'e kai da guiwa ta d'ago fuskarta tana kallon sa cikin fushi.
  Murmushi yayi dan yasan laifinsa ya qarasa gurinta tare da janyo ta zuwa jikin sa yana fad'in "yi haquri ba kya son riga na saka miki ko"
  A shagwa6e ta ture sa daga jikinta  tana kallon sa idonta tap da qwallah le6ace da baki kmr er qaramar yarinya zata yi kuka.
  Hakan ba qaramin birge sa yayi ba don sosai yake son shagwa6a a rayuwar sa.
 Shiyasa duk ya sukui sukui ce ya soma lallashinta har ta fasa kukunda tayi niyya.
  Yakai  hannu zai yaye blanket d'inda ta rufe jikinta dashi har wuya,tayi saurin kama blanket d'in ta rirriqe had'e da dalla masa harara dan rigar komai nata ana gani,
 da murmushi ya saki blanket d'in yace"to ni zanje masallaci kema ki tashi kije kiyi arwala kiyi sallah kinji"
 Daga nn bai jira me zata ce ba ya fita dn sauri yake ko zae sami jam'i ,
koda ya dawo tana zaune kan darduma ta idar da sallah tana addu'a yaje ya zauna kusa da ita suka tofa addu'ar a tare ,
ta tashi zata bar gurin ya jawota ya zaunar tare da fad'in"zauna muyi magana"
 Cikin fushi ta fizge hannunta ta miqe ya sake janyota ya zaunar yana mae kallon fuskar ta yace" hln dae kin manta mgnr da na gaya miki a rnr, ta kalle sa tana son tuna wace magana ce yace"ina wnn mgnr da na gaya miki a kunne gidan innaa,
 kin tuna"
  maqale kafad'a tayi tana kallon sa tace"ai nasan ma baza ka min ba ka fad'a ne kawae"
  Yace"waya gaya miki kawae dae ki daina musa min kiga ni kuwa zan maki abinda nace"
  Tace"ba wani nn wayo kake min nasani amma shi yaya nasir nasan da gaske zae yi min"
  Kallon ta yayi dan tabbas wayo yake mata d'in don ko giyar wake yasha ba zae zubar mata da ciki ba, ya fad'a ne kawae don ya sami natsuwar ta a rnr,don a rnr bayan kalaman rarrashi da ya gaya mata ce mata  yayi duk ta daina musa mae akan komai shi kuwa yayi alqawarin da kanshi zae zubar mata da ciki tunda bata so kuma ba zae sake takura ta akan komai ba.
   Kuma ko nasir yasan wayo kawae yake yi mata,amma kuma wata qil da gske yake mata tun da duk haushin sa suke ji a lokacin sae yanzu ne da komai ya dawo normal.
  Ya kalle ta yace"meyasa kike tunanin da gaske Nasir yakeyi?
  Tace"shifa har asibiti muka je akace cikin bai isa zubàrwa ba sae ya qara watanni amma kai tun daga rnr ko mgnr ma baka sake yi min ba"
   Ta qarashe mgnr had'e da turo baki tana kallon sa shaye da toka shi kuwa ya fashe da dariya don ya fhmci duk dae wayon ne ake yi mata,
 yace"inafa zan miki zancen Ryynt hnkli a tashe amma kinga yanzu Alhmdlh sae ki daina musa min akan komai ni kuma sae na miki abinda kike so sae ma ki samu kiyi karatun ki cikin natsuwa dan nasan shine abinda yafi damunki ko"
Ta gyad'a masa kai kawae tana kallon shi don har yanzu bata yarda da gske yake ba.
  Shima dae ya fhmci haka yace"in tambayeki Ryynt wae meyasa kike son 6arar min da cikin nn ne dan Allah,shin baki san irin sonda nake masa bane"
 Tace"shi cikin da aka samu ta dalilin abinda ka kira a qaddara"
  Kallon ta yayi jiki sanyaye cikin rashin jin dad'in mgnr duk da dae yasan cewa laifin sa ne yace"wace irin magana ce wnn Ryynt,shin idan kin 6arar da cikin nn ba kya gudun had'uwa da fushin ubangiji ko kin manta cewa rayuwa ce zaki hallaka ko rayuwa kuwa ta d'an adam wanda bai ji ba bai gani ba,i beg u idan akan wnn maganar da na gaya miki ne kike son 6arar da cikin nn dan girman Allah kiyi haquri kar ki zubar min dashi wlh ina son sa,
 Ya qarasa mgnr ne kmr zae yi kuka dan har idon sa sun canza launi.
  Itama kmr zatayi kuka ta kalle sa tace"to ai cikin ne ba zae bar ni nayi karatu ba gashi har ya fara min girma idan ban 6arar ba ya kake so na koma school to"
   A hnlkli ya riqo kumatun ta yace"um um Ryynt in dae karatu ne zan san dabarar da zan miki idan kin haifu sae kici gaba ba ma sae kin koma secondary school ba high school kawae zaki d'aura"
  Tace"kamar ya?
 yace"jarrabawa zakiyi waec n neco ba sae kinyi ss2 n 3 ba"
  Girgiza kanta tayi tace"wane irin abu ne hk ko Ss one d'in ma ban kammala ba fa kasani"
  Sae da ya share mata en silallan qwallar da suka xubo mata snn yace"na sani Ryynt amma kinada basira sosai ta yanda inshaa Allah zaki iya yin hk d'in bata tare da an sami wata matsala a karatun naki ba,kawae kice kin yarda dan Allah i beg u"
   Shiru kawae tayi tana kallon sa kmr yanda shima yake kallon ta dmn jin me zata ce.
   Murya can ciki mae d'auke da jin kuka sosai tace"to naji amma kuma ai kasan nayi qanqanta da haifuwa wata qil ma mutuwa kawai zanyi"
   Tana kaiwa nn ta fashe mishi da kuka yayi saurin rungumota yanaji kmr ya taya ta kukan dan haka kawae yaji ta bashi tausayi dan tayi qanqanta d'in kmr yanda ta fad'a"
   Rarrashin ta ya shiga yi sosai yana fad'in ta kwantar da hankalin ta inshaa Allah lafiya lau zata haifu ba abinda zae sameta nn ya samu har ta daina kukan yayinda still yake rungume da ita quite 4 a while some time kmr ba kowa a cikin d'akin sae can mohd ya d'ago fuskar ta yana kallon manyan idanuwan ta dake d'auke da jin bacci yace"bacci" ta gyad'a masa kai ya tashi rungume da ita a jikin sa suka je kan bed ta kwanta nn wayar sa dake kan bedside drawer ta shiga ring,
 malika ce mae kiran bae d'aga wayar ba sae da ya fita dan baya son yayi disturb in Ryynt.

Bai wani jima sosai d'in nn ba ya dawo ya samu har Ryynt tayi baccinta.

 Yayi zaune gefen gado ya jawo stool ya d'aura laptop akai yana wani  aiki wanda har yayi nisa da aikin ne wayar sa ta shiga ring still dae malika ce,
sae da yayi tsaki kafin yake d'aga wayar cikin fad'a yace"wae malika sau nawa zance miki Aa nace ba sae kin zo ba kawai kibi ummanki ku koma ai nima  ina nn dawowa,oho koma yaushe ne dae"
  Yana gama fad'ar haka ya katse kiran yaci gaba da aikin sa.
  Har guraren qarfe goma snn ya rufe laptop d'insa ya tashi ya nufi bathroom yayi wanka ya fito.
  Bayan ya gama shiri ne yayi tsaye akan Ryynt dake ta faman juyi ya hau kan gadon a hnkli ya janyo ta zuwa jikin sa yace"Ryynt mene ne?
  Da qyar tana yarfi da hannu tace"cikina"
    Kai tsaye  yakai  hannu ya cire mata hijab ya kuma kwance  zanin da ta d'aura kan rigar baccinta ya yaye rigar yana duba cikin yace"nuna min daga ina yake maki ciwo"
 Murya can ciki mae d'auke da son yi kuka tace"mird'a min yake yi gabad'aya"
   A hnkli ya maida ta ya kwantar yaje ya tsiyayo fresh milk a cup yazo da magani ya tashe ta ya bata sae yi yake yana shafa cikin yayinda take rungume a jikin sa idanun ta a rufe kmr mai yin bacci man sae kallon goshin ta yake da yayi zufa zufa duk irin sanyin Ac da ke cikin d'akin kuwa nn ya ciro handkerchief ya share mata zufar ta bud'e idanun ta a hnkli tana kallon sa shima kallonta yake yayinda yakai hannu kan santala santalan cinyoyinta yana shafawa da sauri ta kai idonta akai snn tayi saurin janyo hijab ta rufe cinyoyin ta tafi dashi har izuwa qirjinta duk ta rufe don sae lokacin ta tuna cewa ya cire mata hijab da zani kuma sam ta manta yanayin rigar da ke jikinta.
   Kallon ta kawae mohd yayi bae ce komai ba sae hannun sa yakai ya d'ago fuskarta yana kallonta yace"cikin ya daina maki ciwo?
  Kai ta gyad'a masa ta saka hijab zata miqe tsaye yace"ina zuwa?
 Tace"wanka zanyi"
   Yace"to muje na tayaki wankan ko"
  Ta maqale kafad'a had'e da fad'in"ni kunya nake ji kawae kayi zamanka"
  Yace"Aa sae dae ki za6i d'aya da na tayaki wanka da na shirya miki idan kin fito wanne kike so"
  Tace"bari idan na fito ka shirya min"
   Ta fad'i hkne kawae don ta samu ta tafi kafin aman da takeji ya kufce mata.
  Shi kuwa har ransa yaji dad'in ganin ta d'an fara sakewa dashi yace"shike nn jeki"
   Nan ta nufi bathroom wacce koda ta fito bata same shi a d'akin ba sae gado da ta samu an gyare tsaf.
   Dad'i taji har ranta ganin baya d'akin don ita ko shiri bata iya yi a gabansa bare zancen yace shi zae shirya mata nn ta nufi wardrobe da hanzarin ta dmn ta samu ta shirya kafin ya dawo sae dae koda ta bud'e wardrobe duk ya cire kayan da tazo dasu ya saka mata wasu qananin kaya kala kala,kafin ta iya komai sae jin mutum tayi a bayanta ya rungume ta a hnkli tare da fad'in "ya kika ga kayan suna da kyau?
  Komai bata iya ce masa ba sae hannu yakai ya zaro kala d'aya daga cikin kayan yaja hannun ta yakai kayan kan bed ya ajiye ita kuma ya tafi da ita gun dressing mirror ya zaunar wacce tana ji tana gani ya cire mata hijab ya fara shafa mata mae bata iya hanashi ba don ko magana ma da taje zuwa yi hanata yayi kawae dae ya rage hasken d'akin zuwa dim light.
  Tsaf ya shafa mata mae kmr wata er baby don ko towel d'in jikinta bae bar ta dashi ba ya kuma shafa mata duk wasu turarukkan sa da yake amfani dasu yayinda kanta ke qasa cike da jin kunya ta kasa hana shi komai har ya d'auke ta ya tafi da ita kan bed ya saka mata  tufafin da ya d'auko wato riga da wandon da sukayi matuqar kyau a jikinta ita kanta ta yaba da kayan sbd kayan basu da tsirai ci ko kad'an dmn kayan irin na Indiyawa ne er duguwar riga mai guntun hannu da aka d'an matse body d'in rigar se tunda daga kan qugu aka baje ta har zuwa guiwa yayinda wandon ya kasance skin tight.
  Mohd sae kallon Ryynt yake tayi wacce har yanzu ta kasa d'ago ido ta kalle sa duk da ba wani haske ne a d'akin ba.
   Ya kira sunan ta a natse had'e da d'ago fuskarta suka kalli juna ta cikin ido nn man ya qara jin wata irin kasala ta saukar mae wacce tun lokacinda yake shafa mata mae ya soma jinta ,
a hnkli ya matso fuskar sa gab da tata ya d'aura tsinin hancin sa akan nata Ryynt da ta fahimci abinda yake son yi ta kauda fuskarta gefe ,
bae ce komai ba sae hannunta yaja suka je kan dining,sae dae Ryynt ta kasa cin komai sbd zuciyar ta dake fmn tashi hkn yasa shima mohd ya kasa cin komai sae kwantar da ita yayi kan qirjin sa ya shiga shafa bayanta yana tambayar mene ne,
 Shiru kawae Ryynt tayi don ba abinda take jin so irin agwalima wacce tasan da kmr wuya samunta a nn,
Mohd dake shafa  bayanta a natse yace"gaya min me kike so kinji"
  Ta d'ago fuskarta kmr zata yi kuka tace"agwalima nake so kuma nasan a nn babu ko?
   Cikin damuwa yace"No Ryynt da kmr wuya amma kina son fruits?
  Da sauri ta gyad'a masa kai yace"to muci abinci sae muje a siyo ko"
 Tace"um um kawae kai kaci sae muje"
  Ya girgiza kansa yace"um um kema kici ko kad'an ne kinji i beg u"
Ya fad'i hkne yana mae kallonta cikin nuna damuwar son taci abincin.
Hakan yasa ta kasa musa mae duk da tana ji kmr idan taci zatayi amai amma hkn ta dake ya fara bata abincin tana ci sae Allah Allah take kar amai yazo mata yayinda take ta kallon shi bae ci abincin ba sae bata da yake,
Mohd ya kalleta ganin ya d'ebo abinci a spoon yakai bakinta taqi bud'e baki taci sae kar6ar spoon d'in tayi ta kai bakin shi ,
da kmr mamaki ya bud'e bakinsa a hnkli ta sakà mishi yana mai kallonta cike da jin dad'i a ransa.
 Inda cikin ikon Allah Ryynt kuwa taci gaba da ciyadda dashi yana ciyadda ita har suka kammala cin abincin.
  Man dake ta kallon Ryynt cikin so da jin dad'i ya zaro tissue ya goge mata d'an qaramin bakinta snn  yaja hannunta d'auke da murmushi a fuskar sà ya tafi da ita gun wardrobe d'in ta ya ciro black after dress da ya siyo mata tsadadda mai kyau ya saka mata snn ya ja hannunta suka fita.



Billy giro😊
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮















                🔮🔮🔮🔮
*```Page 72```*
  Sun d'an jima kafin suke dawowa dan sae da suka d'an zaga gari kmr yanda Ryynt ta buqata.
Koda suka shigo mohd ne riqe da wata babbar leda da aka ciko tap da 'ya'yan fruits kala kala har wad'an da ma bata saba gani ba.
   Haka ma Ryynt na riqe da wata leda mae d'auke da ice cream taje ta saka a fridge shi kuwa mohd kitchen ya tafi da ledar fruits d'inda ke hannun sa,bai jima sosai ba ya dawo d'auke da fruits d'inda ya gyara a cikin fruit bowl yazo yaja hannun Ryynt da ta cire after dress ta mayar a wardrobe yaje da ita kan sofa ya zaunar ya kunna musu TV suna kallo yana bata fruits a baki tana ci kmr wata er baby kan yanda ya rungume abar sa a gefen qirjinsa sa ita dae Ryynt ta zamo speechless sae kallon  sa kawae take don abubuwan nasa har mamaki suke bata don komai sae  yace baza tayi da kanta ba sae shi ze yi mata wacce ko ledar ice cream da ta shigo riqe da ita sae da tayi da gaske snn ya barta ta riqo ledar.
  Haka yaci gaba da bata fruits in sae da tace ya isheta snn ya cinye sauran.

2 dayz later
Ryynt ce zaune kan kan bed sae waya take da mutan gida wato su inna da su umman saliha,saliha, mami har ma da qawar ta Sarah.   Wacce tana gama wayar ne sae ga mohd ya shigo d'akin nn take ce masa tana son zata je 6angaren su mtr Amir bai musa mata ba ya jata suka tafi 6angaren suka sami Amir zaune a falo shida d'an shi saddiq da mtr sa suna kallo abinsu.
   Cikin sakin fuska suka gaisa da juna mtr Amir taja Ryynt suka je daga ciki ,
a nn man ya kalli Amir yace"shin wae kai ka dawo ke nn ko kuwa?
  Sae da Amir ya nisa snn yace"Aa nifa ajiye aikin ma nake ganin zanyi na koma Nigeria na gaji da zama qasar wasu ina masu aiki bayan qasata na buqata"
  Mohd yace"au ka fara kishin qasar taku knn"
 Amir yace"ka jika idan banyi kishin qasar mu ba tawa zanyi kawae dae wlh kmr kar mu jima gida karon nn naji ina sha'wan ci gaba da zama cikin en uwa haka my wife da taji zamu dawo har kuka sae da tamin ita gida bae isheta ba ,
sae da na mata bayani snn hankalinta ya kwanta.
  Mohd yace"knn itama tana son komarwa ka aiki Nigeria?
  Eh to tana so amma ba don komai ba sae don ganin Khadija na gida ynx sae duk taji nn d'in ya fita ranta,mohd yace"ni kuwa Amir har kaima d'in baka da labarin inda Aamil yaje wae?
  Amir yace"inafa zan sani man kuma abin tausayi ya tafi ya bar Khadija da sabon ciki mae matuqar bata wahala da komai bata iya yi sae an mata  bayan baqin cikin da ya tafi ya bar ta dashi"
  Mohd ya nisa kawae ba tare da ya iya cewa komai ba sae wayar sa da ke ring a cikin aljihu ya ciro ya d'aga.

Ryynt kuwa da mtr Amir ta jata zuwa ciki sosai ta sake da Ryynt don sae jan ta take da fira  hkn yasa Ryynt ta sake itama sae fira suke abinsu bayan kayan motsa baki da ta jerawa Ryynt a gabanta.

9:00pm
Tuni suka dawo 6angaren su har sunci abinci suna zaune a falo suna shan ice cream yayinda Ryynt ice cream d'inta har ya soma narkewa kan yanda take faman danne danne a wayarta d'auke da er damuwa a fuskarta ta d'ago ta kalli man dake kallon labarai a TV amma duk wani  motsi nata yana kule dashi shiyasa da ta kalle sa ya sauko kan doguwar kujerar da yake zaune dan ita zaune take a qasa ta jingina bayanta a jikin doguwar kujerar.
  Bayan ya zauna kusa da ita ne yace"ya akayi ne Ryynt?
   Ryynt dake kallon sa tace"so nake dan Allah ka bud'e min whatsApp Saliha ke son mu riqa chat "
   Ba musu ya kar6i wayar ta ya tura mata watsApp a wayar shi ya kuma saita mata har yana nuna mata yanda ake chat d'in dan ya fhmci she is innocent.
  Cikin jin dad'i ta masa godiya sae dae koda ta duba Saliha bata online bata hau ba sae wata numba taga ta turo mata text ta kalli man dan kai tsaye ta gane numbar sa ce, smile ya sakar mata snn ta duba me yace, ta d'ago ta kalle sa d'auke da d'an murmhshi a fuskarta snn ta shiga bashi amsa yana karanta amsar yayi smile ya mata reply tana karantawa ta saka tsayanta a baki tana thinking snn can ta mae reply cike da murmushi ya bata amsa ita kuwa tana karantawa bata iya bashi amsa ba sae kallon sa tayi a shagwa6e had'e da girgiza masa kai yace"To shike nn zan turo wasu numbers sae ki sake picking tace"to turo"
  Yana turo mata wasu numbers ta za6a
da ta turo mae wacce ta za6a ya mata reply tana dubawa ta kalle sa had'e da maqale kafad'a tace"wlh um um wayo ka min"
 Mohd ya fashe da dariya yace"naji sake za6a amma ki sani wnn shine karo na qarshe kin yarda tace"eh na yarda"
  Nan ya turo mata  numbers ta xa6a snn ya tura amsoshin tana duba amsar lambar da ta za6a ta tashi cikin kukan shagwa6a har tana doddoka qafafun ta a qasa tace"wlh Allah ban yarda ba a sake"
  Mohd ya tashi ya jawota jikin sa sae dariya yake yace"Allah ba ruwana kin riga kin za6a daga haka yaje zuwa cire mata riga tayi saurin riqe rigar tace"Aa yi haquri zanyi first choice d'ina amma fa sae ka rufe idonka"
  Ba musu ya rufe idonsa tare da fad'in "to yi min"
    A maimakon yaji saukar kiss sae jin yayi ta qwace kanta tayi ciki da gudu ya bita da sauri can ya samu ya damqe ta suka fad'a kan bed sae dariya take tana bashi hqr yace"ai kin rigada kin ja ma kanki last choice d'in nn da ba kya so"
  Tace "Aa yi haquri zan maka firts choice wlh"
   Bai kulata ba sae kayan jikinta ya shiga cirewa bata iya hanashi ba dan sae cakulkuli yake mata had'e da cire mata kayan yayinda take ta zille zille tana dariya tana bashi haquri bae haqura ba sae dariya da yake shima har ya cire mata kayan sae inna wears kad'ai da ya bari a jikinta ya d'auke ta sae zuwa bathroom.
   Wanda sae da suka jima kafin suke fitowa kowannen su d'aure da towel sae murmushi suke fmn yiwa junan su.
 Bayan sun shafa mae mohd ya d'auko musu  kayan bacci ,ya ba Ryynt er ficikar rigar baccin da ya d'auko mata wacce yasan da kmr wuya ta yarda tasa dan kullum sae tayi bacci yake samu ya sakata mata rigar sae dae idan ta tashi da safe tayi ta fmn fushi dashi.
Haka ko akayi don ko kar6ar rigar taqi tayi sae shagwa6a ta ajiye mae kan bazata sa ba.
Ya shiga lallashinta taqi yace"shikenan idan baza ki saka rigar ba sae mu kwana a haka ya fad'i hakane tare da cire towel d'in jikin sa ya yar had'e da hawa kan gadon wata irin kunya Ryynt taji tayi saurin cusa fuskarta gabad'aya cikin cinyoyiñta bata an kara ba sae jin tayi itama ya cire mata nata towel ya yar cike da jin kunya ta cumui muye shi tana neman jawo blanket ta rufa jikinta ture blanket d'in yayi ya fad'i can qasa ya kuma kashe wutar d'akin tace"wayyo yi hqr wlh na yarda zàñ saka rigar......bakinta taji ya had'e da nashi sae can  ya zare yana kissing d'in jikinta ta koina yana mata abubuwa a jiki masu tsabar kashe jiki da yasa ta kasa yin komai sae zame jiki tayi ta kwanta ya bita yana kissing d'in  wuyanta har yaje kan qirjinta yana mata wani  irin salon da yasa ta kama masa suka shiga romancing d'in juna kmr zasu kashe kansu da qarar komai ba ka ji sae sautin numfashin su dake fita a hnkli har suka je tsundum a cikin duniyar ma'aurata wacce Ryynt ta sami kanta cikin yanayin da bata ta6a tsintar kanta a ciki ba don wnn karon a hnkli ya bita.
 
Washe gari ta riga shi farkawa ta ganta ya wani rungume ta sosai  a qirjinsa kmr wanda aka ce za'a qwacewa ita,ta d'ago tana kallon kyakkyawar fuskar sa mae d'auke da sajen da suka masa mugun kyau snn ta kalli dogon hancin sa da ya tafi kmr biro ga d'an maidaidaicin bakin sa dake d'auke da red lips kmr mace,
 A hnkli ta kalli hannunta dake kan faffad'an qirjin sa da gashin qirjin nasa ya kwanta luf abin sha'awa nn ta shiga shafa gashin qirjin nasa a hnkli
sae kawae taji ya riqo hannun ta da take shafa qirjin nasa nn ta kalli  fuskar sa da sauri sukayi ido had'u
 ya sakar mata murmushi had'e da d'aura mata kiss kan goshi snn yace"ina sonki Ryynt"



Billy giro😊
🔮```BAXAN BARSHI BA!🔮```















              🔮🔮🔮🔮
*page  73*
Ina kuma roqon Allah ya qara maki.....ya qarasa zancen a cikin kunnen ta cike da jin kunya ta 6oye fuskarta gabad'aya cikin qirjin sa ,
sosai ya fad'ad'a murmushin sa yana mae shafa gefen fuskarta yace"meye na jin kunya nifa mijinki ne is gud na yaba irin ni'imar da Allah ya maki dmn wlh ke ta daban ce Ryynt ina alfahari dake ako yaushe then......ya qarasa zancen cikin kunnen ta tayi zumbur zata miqe tana dariya ya janyo ta ya maida kan qirjinsa ya kwantar yace"kin san me Ryynt?
 Ta kalle sa tare da fad'in"um um sae ka fad'a"
  A natse yace"plz ki daina motsi mae qarfi masamman gudu idan ba so kike babyn mu ya sami matsala ba kinji"
  Ya fad'i hakane yayinda yake shafar cikinta ita kuma tace"inshaa Allah zan kiyaye "
yace"nagode to tashi muje muyi arwala muyi sallah ko"
ba musu ta tashi sanye da er fincikar rigar baccin da ke jikinta suka je bathroom sukayi arwala.

Bayan sun ida sallah da d'an jimawa mohd ya kira umman sa suna gaisawa a nn Ryynt dake kan jikin sa taje zuwa tashi ya maida ta had'e da fad'in"zo ga umma na son ku gaisa"
 Ta kalle sa jiki sanyaye snn ta kar6i wayar ta kara a kunnenta muryar ta can ciki tana rawa tace"umma ina kwana"
  Cikin sakin murya umma tace"lafiya lau Ryynt kina lafiya?
  Tace" lafiya lau umma"
  Umma tace"to ya can d'in?
Ryynt tace"lafiya qalau"
Daga haka ta bawa mohd waya kmr yanda ummar ta buqata.
  Mohd ya kar6i wayar d'auke da murmushi a fuskar sa.
  Bayan sun gama wayar ne Ryynt dake kwance kan qirjinsa ta d'ago tana kallon sa tace"Abba fa naga bana samun layin sa idan na kira?
    Mohd dake kallonta yace"koh to ya akayi ni ko jiya fa nayi waya da Abba har ma yace yana gaida ki kuma ko yanzu shi na fara kira sae bae d'aga ba,amma bari na sake kiran sa idan ya d'aga  sae na baki shi ku gaisa"
  Nan ya shiga dialling number d'in Abba aka yi sa'a kuwa ring da'ya,biyu ya d'aga byn ya gama gaisawa dashi ne snn ya ba Ryynt wacce tana gama gaisawa dashi taje kan bed ta kwanta sae bacci.

Sae guraren qarfe goma ta farka sae sharara ruwan sama ake ta ganta rungume a jikin mohd daga ita sae er rigar baccinta ya cire mata hijab da zanin da tayi sallah dasu ga hannun sa tsundum cikin rigar ta ya d'aura hannun kan cikinta wanda da alama shafa cikin yake har yayi bacci ,
a hnkli ta zare hannun sa ta sauka kan gadon ta nufi bathroom tayi wanka ta fito knn taji knocking da sauri ta nufi wardrobe ta zuba hijab d'inta har qasa snn taje ta bud'e qofar.
  Matar Amir ce tsaye a bakin qofar riqe da basket d'in abinci cikin sakin fuska suka gaisa snn Ryynt ta kar6i basket d'in had'e da mata godiya.
  Ta wuce ita kuma Ryynt ta rufe qofa ,
nn taji man ya rungumota a hnkli ta baya ta juyo tana kallon sa sae wani  kallon so yake mata mae d'auke da murmushi ,
 ta sadda kanta qasa tace"ka tashi"
    Bai ce mata komai ba sae basket d'in hannunta ya kar6a ya tafi rungume da ita gun dining ya ajiye basket d'in ya shiga cire kulas yana jerawa Ryynt dake kallon sa tace"hln yaushe zamu koma Nigeria?
  Cak ya tsaya da abinda yake ya kalleta da kulawa snn yace"ya akayi ne Ryynt ko kin gaji da zama nn ne"
  Girgiza kanta tayi tare da fad'in"Aa ina dae son naji yaushe zamu koma"
  Yace"next week inshaa Allah amma sae munje Germany tukun"
Tace"to me zae hana ka d'an siyo kayan abinci na riqa mana ko wahalar zae ragewa maman saddiq"
  Yayi murmushi had'e da lakato hancinta yace"naqi d'in salon kije ki qonewa mutane gida ki bani aiki nida bako d'an qasa ba"
 Tayi er dariya tace"um um ba abinda zae faru inshaa Allah ka siyo kawae"
Yace"No gsky bazaki wahala ba na hutar dake"
A shagwa6e ta janye jikinta dagà nashi tace"to ita sae tayi ta faman wahala kenan"
  Yace"wa ya gaya miki tana wahala ne wae itafa ta saba da aikin abinci ba kmr keba"
 Zata yi magana knn  ya janyo ta zuwa jikin sa had'e da cire mata hijab ya tsaya yana kallon gashin kanta dake jiqe ya sauko har kan kafad'unta yakai  hannu ya riqo jelar gashin
Yace"kinyi wanka ne?
Tace"eh fitowa ta knn akayi knocking"
Yace"shine baki tashe ni ba muyi wankan tare to muje ki min"
  Ta maqale kafad'a
Yace"ni ko"
 Ta gyad'a masa kai tana murmushi dan sae yanayin mgnr sa yayi mata kmr wani qaramin yaro har dae yanayin fushin da ya nuna a fuskar sa tana kallo ya wuce har sea da taga shigar sa bathroom snn taje tayi zaune kan dressing mirror ta shafa mae tayi kwalliya abinta kmr wacce zata fita ga gashin kanta da yàsha gyara ta sake abiñta ba tare da tasa ribbon ba snn ta tashi zuwa saka tufafi sae dai yau ta rasa kayan sawa don duk babu na kirki a ciki ta saye masu d'an damar.
  Tana cikin hakane sae ga man ya fito sanye da white bathrobe ya nufi dressing mirror ya d'auki Vaseline ya tafi dashi kan bed ya zauñà zae shafa ta kalle sa taga dgske still fushi yake a nn kawae taji tana son faranta mae ta d'auki kala uku a cikin kayan da ta kasa sawa ta kai masa a cewar ya za6a mata d'aya daga ciki.
  Ko kallon gefen ta bai yi ba sae Vaseline da ya soma qoqarin shafawa,
 jiki sanyaye ta zauna kusa dashi ta d'auki vaseliñe zata taya shi shafawa ya kar6e Vaseline d'inda ta d'auka yana kallon ta cikin fushi"
 tace"yi haqauri bari na shafa ma kaji"
  Shaye da toka yace"bana so kuma ki tashi kusa dani in daina gànin ki"
   Kai tsaye taji idonta sun ciko tap da qwalla tayi saurin d'aukar tufafinta zata bar gurin mohd ya janyota da sauri, yace"Ryynt wae kuka zakiyi daga kawae wasa"
   Bata iya cewa komai ba sae kukan ta fashe dashi dan ya riga da yazo mata nn ya rungumeta yanà shafa gashin kantà dake shimfid'e a bayañta yàna mae fad'in"oh no Ryynt wlh am just kidding yi haquri daina kuka kinji"
Nan yaci gaba da lallashinta har ya samu ta daina kukan sae ma dariya da ta koma yi sbd lallashi irin nasa da yake had'awa da barkwanci,
d'auke da murmushi ya d'ago fuskarta yana mae qara share mata hawaye don har lokacin akwai hawaye a fuskarta.
 yace"bani kayan to na za6a miki"
 Tace"bari na tayaka shafa mae tukun,amma ya naji jikin naka da zafi ko baka da lafiya ne?
 Da murmushi yaja hancinta yace"ni qalau nike gardamar ki dae ke son samin ciwo"
   Tayi murmushi kawae ba tare da tace komai ba ta cire masa bathrobe ta shiga shafa masa mai sae kunya take d'anji duk da cewa akwai farin boxer a jikin sa.

Bayan ta ida shafa masa mae ne yaja hannunta suka nufi wardrobe d'inshi yasa ta za6o mishi kayan sawa ya kuma sa ta shirya mishi da kanta.
  Snn itama ya shirya mata cikin wata er  farar doguwar riga handless iya guiwa da qasan gefe d'aya yafi d'aya tsayi kuma gabad'aya rabin banta a waje yake haka ma gaban rigar duk ana ganin rabin mammanta amma ta kama jikin Ryynt d'as tayi mata shegeñ kyau  don har photo sae da mohd ya musu shida ita snn yajata sae zuba qamshi suke suka je kan dining zuwa break fast yayinda sukà shiga ciyadda junan su cike da nishad'i.

Nigeria
At 5:00pm
Malika ce  taje gidan qawar ta fa'iza wacce ta tarbe ta da murna bayan sun zauna fa'iza ke cewa"ashe man d'in ki ya dawo shine baki gaya min ba"
  Malika tace"wa ya gaya miki?
  Fa'ixa tace"au to wa na ganki dashi yanzu ya sauke ki a mota"
  Malika ta le6ace baki tace"Switat ne fa"
  Fa'iza tace"ke mutuniya ba dae har yanzu kina wnn harakar bar ba,inace kin daina tun kafin aurenki"
  Malika tace"eh mana sanin kanki ne baxan iya had'a my man da kowanne d'a namiji ba dmn shi na dabanne kuma son sa nakeyi da gaske shiyasa ma na  aure sa amma kuma sae yazo ya 6ata komai don 6acin randa yake samin ne yasa na koma tsundum a ruwa"
  Fa'iza tace"haba malika ke fa yanzu matar aure ce..... N so what!kin fa san halina ni banada jimirin rashin namiji a kusa dani.....ba wani nn duk kan desire tablet d'inda kike sha ne kin sani,idan zaki daina sha to"
  Malika tace"hm fa'iza knn baza ki gane bane wlh da kin soma shan desire tablet baza ki iya ta6a dainawa ba kuma ki gwada ki gani sae ma kinfi jin dad'in rayuwarki a haka"
  Fa'iza tace"hm Allah sauwake min ko yaushe cikin buqatuwa kema da kike sha Allah ya yaye miki"
  Malika tayi er dariya tace"ke matsalar ki knn rashin fahimta shiyasa ko a class ke ke cije bindi"
  Fa'iza ta fashe da dariya had'e da kai mata duka snn tace"ban son sharri malika"
  malika tace"au sharri na miki knn in banda rashin fahimta wae ace har kin yarda kin kwashi ciki tun baki gama holewa ba wlh je zuwa zubarwa dan ina gaya miki da kin yarda kin fara haife haifen nn tsufa zakiyi ako zuba ki a kwandon shara dan kina ji kina gani zai d'auko miki yarinya d'anya sharaf suna soye a gabanki sae dae ki zama er kallo wlh dan ba yanda zakiyi kin riga ki 6arar da ajinki"
  Fa'iza tace"hm a gsky malika bazan iya 6arar da cikin nn ba dmn hubby na son cikin nn sosai kuma nima ina son abuna wlh.
  Malika dake kallonta ta yatsine fuska had'e da le6ace baki tace"ke kika sani nidae bani ruwa nasha"
  Nan fa'iza taje ta kawo mata lemu da abin motsa baki tayi zaune suka soma wata firar.

 6angaren su Ryynt kuwa da dare guraren qarfe tara Ryynt ce kan bed cikin shirinta na bacci tana kwance kan cinyoyin mohd tayi pillow dasu sae chat take da saliha da kuma qawar ta sarah shi kuwa mohd hankalin sa na kan TV yana kallon labarae sae can ya kashe TV a nn zaunen da yake,
 ya jawo wayar sa ya shiga chat jim kad'an Ryynt ta kalle sa tare da maqale kafad'a tace"banyi ka min wayo sae dae idan ni zan baka options kana za6a"
  Yace"to naji gareki"
 Nan suka soma yin game d'in karo na farko Ryynt ta tashi sae dariya take mishi yaja hancinta shima yana dariya yace"wae ke wayo ko zan kama ki ne yarinya"
  Nan ya sauka kan gadon ya duqa kai tsaye Ryynt ta d'ale bayan sa sae murna take tana jin dad'i ya d'aga da ita cak  sukaje yana zagayawa da ita cikin d'akin har zuwa falo snn suka dawo ya sauke ta kan bed sae sauke numfashi yake wae nauyi ne da ita har yana fad'in wnn cikin gobe sae munje anyi scanning inga meye a ciki da yasa kikayi nauyi haka,
 tayi dariya kawae don da wasa yake mata zancen ba wani  nauyinta da yaji.
  Nan suka je zasu ci gaba da yin wasar su wayar mohd da ta shiga ring ce ta katse su,tare suka kalli mae kiran wato Malika wanda kafin ya d'aga wayar sae da yace da Ryynt"sorry Ryynt bari na d'anyi waya kinji"
da qyar ta iya qirqiro murmushi ta gyad'a masa kai don haka kawae taji wani irin kishi ya turniqeta nn kawae ta rage hasken d'akin tayi kwanciyar ta.





 Billy giro😊
🔮```BAXAN BARSHI BA!🔮```















              🔮🔮🔮🔮
*page  74*
Mohd na gama waya ya matsa gab da Ryynt yana kiran sunanta a hnkli.
  Yaji shiru ba amsa wacce tana ji ya kwanta yaja musu blanket ya rufa musu jikin su ya rungume abar sa suka shiga bacci.

Washe gari bayan sunyi sallah har sunyi wanka sunyi break fast suna zaune falo kan doguwar kujera mohd na riqe da laptop yana nunawa Ryynt kayan yaran da yake son siyowa a Germany yayinda Ryynt ke d'auke da murmushi a fuskarta don kayan sun mata kyau sosai.
    Sae da ya gama nuna mata komai snn ya rufe laptop yaja hannunta ya tafi da ita kan bed sukayi kwance abinsu sae fira suke can mohd ya d'an mirgino kan jikin Ryynt yana kallon rigar jikinta er simple maroon in colour silky mae d'an siririn hannu tsayinta iya cinya da ko dogon motsi Ryynt tayi ana hango d'an bum short d'in jikinta kalar rigar.
A hnkli yakai hannu kan wuyanta yana shafa wuyan cikin tafiyar tsutsa har ya tafi da hannun kan d'an siririn hannun rigar ta ya kama ya tafi dashi kmr zae zare Ryynt dake kallon abinda yake shirin yi ta katse shi da d'aura tafin hannunta kan gefen fuskar sa tayi shiru tana ta kallon kyakkywar fuskar sa long time kmr mae neman wani abu a jikin fuskar tasa,
 Mohd ya d'aga girar sa had'e da lakato hancinta yace kallon fa"
Cikin yanayin jin kunya tayi murmushi tare da kauda fuskarta gefe tasa hannu ta rufe fuskarta,
Hkn da tayi ya birge mohd sosai se  murmushi yayi had'e da kai mata kiss kan gefen wuyanta snn ya janye hannuwanta a hnkli yana kallon kyakkywar fuskarta da ta rufe idanun ta masu d'auke da long eyelashes,
 Yakai hannun sa a hnkli ya soma zare mata hannuwan rigar ta dan kawae ko zata bud'e idonta bata bud'e idanun nata ba sae hannu takai kan qirjinta ta dafe gaban rigar ,shikuwa ya kai bakin sa a hnkli ya d'aura mata kiss kan goshi had'e da fiddo tsinin halshen sa ya tafi dashi a hnkli sae kan tsinin hancinta ya gantsara mata d'an qaramin cijo,
 Ryynt ta bud'e idonta da sauri ta kalle sa a shagwa6e tare da kama tsinin hancinta tana yarfi da hannu ta le6ace baki kmr zatayi kuka,
D'auke da murmushi ya d'aura tsinin hancin sa akan nata ya goga had'e da fad'in "sorry"
 A shawa6a ta ture shi daga kan jikinta ya tashi sae dariya yake rungume da ita yana bata haquri.
  Bata haqura ba sae tsinin hancinsa take son kamowa cikin kukan shagwa6a wae ita sae ta rama shi kuma bae barta ba sae dariya yake har ya kwantar da ita tare da had'e bakin su gam ya kuma sa6ule rigar jikinta ta ya shiga wasa da albarkatattun qirjinta dan rigar kawae ce a jikinta ba bra.
Sae da yayi  romancing d'in ta son ranshi snn ya janyo ta ya rungume yana shafa bayanta yayinda ita kuma take shafa sumar qirjinsa a hankali sae kallon juna suke d'auke da d'an murmushi a fuskar su .
Ryynt ta tashi riqe da rigarta ta juya mae baya zata saka rigar, sae jin tayi ya rungume ta ta baya tare da zagayo hannuwan sa kan qirjinta yana yawo dasu a hnkli har yaje kan cikinta yana  shafawa Ryynt dake kallon hannuwansa d'auke da murmushi ta karkatar da wuyanta a hnkli had'e da lumshe ido tana sauraren yanda yake ta kisin d'in wuyanta,
nn takai d'ayan hannunta tana shafo gefen fuskar sa  yayinda d'ayan hannunta ke riqe da rigarta ta d'aura kan qirjinta da yake faman shafawa bayan d'ayan hannun sa da yake shafa cikinta dashi.
   Tana ji ya sa6ule rigar hannunta ya zagayo ya zauna kusa da ita tare da shafo gefen fuskarta ta d'ago tana kallon sa yace"muje a saka wasu kayan fita nake son muyi kinji"
  Ta gyad'a masa kai yaja hannun ta ya shirya mata snn suka fita.


Bayan en wasu awanni da fitar su ne suka dawo Ryynt ce ta fara shigowa rae 6ace cikin fushi taje kan bed ta kwanta had'e da fashewa da kuka mohd ya shigo d'akin shima cikin 6acin rae yazo kan Ryynt yace"oya tashi bani zoben nawa tunda ba kyaso"
 Jiki sanyaye ta tashi tana kallon sa cikin share qwalla tace"nifa ba wae bana son zoben bane so nake ka bani wanda ka cire min ina son abuna wlh"
  Shaye da toka ya miqa mata zoben ta na azurfa da marigayi anwar ya bata yace"gashi ciro nawa ki bani"
  Zatayi magana knn yace"shiiiii! ban son jin komai wlh kawae ki bani abuna"
  Qwalla tap a idonta ta kalle sa snn ta kalli zoben diamond mae kyau dake jikin yatsarta ta ciro zoben ta miqa masa shi kuma ya bata nata ta kar6i zoben yayinda hawaye ke silalowa a hnkli kan kumatun ta.
  Mohd kuwa yana kar6ar zoben ya juya ya fita ya bar gidan gabad'aya.
  A nn Ryynt dake riqe da zoben ta ta koma kan bed ta kwanta ta soma wani  kukan.

Sae guraren qarfe tara na dare snn mohd ya dawo gidan ya sami Ryynt zaune kan bed cikin shirinta na bacci ta had'e kai da guiwa, jin shigowar sa ne  yasa ta d'ago tana kallon sa da manyan idanunta da suka sha kuka ya kalle ta sau d'aya ya wuce bathroom yayi wanka ya fito tana kallo yayi shirin sa na bacci yazo yayi kwance had'e da juya mata baya ya kuma kashe wutar d'akin,
a hnkli ta shiga yi masa magana yayi banza da ita hkn yasa itama tayi kwanciyar ta ta juya masa baya had'e da jan blanket ta rufe jikinta.

Washe gari da safe koda Ryynt ta farka bata sami man ba ya tashi har ya tafi masallaci itama taje ta d'auro arwala tazo tayi sallah bayan ta idar da sallah tayi addu'a lokaci mae tsawo snn ta kwanta  nn kan darduma bacci ya kwasheta sae goma da rabi ta farka taje tayi wanka ta shirya cikin en guntayen rigunan da ta fara sabawa dasu taje kan dining ta sami komai a jere tayi break fast d'inta ba tare da ta jira mohd ba sbd taga alamar yayi break fast kuma cikin baccinta taji lokacinda ya shigo yayi wanka ya fita.

Bayan ta kammala break fast ne ta zauna falo ta kunna kallo had'e da jawo wayarta ta kira inna sae waya suke cike da nishad'i kmr wad'an da ke zaune guri d'aya kan yanda suka jima suna wayar.
  Suna gama wayar ne sae ga mohd ya shigo wanda kai tsaye ciki ya nufa nn Ryynt ta tashi ta bishi  ta samu ya jawo laptop yayi zaune kan bed zae soma wani  aiki,
Tayi zaune gefen gadon wacce cikin sassanyar murya ta soma magana tana bashi haquri,
Nan mohd ya lumshe ido d'auke da damuwa ya rufe laptop d'in sa yana kallonta kafin yake kallon yatsar ta da tuni ta maida zoben azurfar ta akai sosai yaji ransa ya 6aci nn  ya miqe  rae 6ace zae fita Ryynt tayi saurin tashi tasha gaban shi tana bashi haquri yace"wae meye matsalarki zobe ne dae ba kyaso na kar6e abuna na baki naki da kike ra'ayi sae kuma kizo kina takurani akan nayi haquri for what!
  Cikin muryar kuka Ryynt tace"nifa wlh bance maka bana so ba zoben azurfa nane bazan iya rabuwa dashi ba kmr yanda kace ,fisabilillah kan me baza ka barni da abuna ba tunda ba yatsa d'aya nake dashi ba inada wasu yatsun  da zan saka naka akae,kuma nayi maka bayanin yanda zoben nn yake ko don haka ya kamata ka tausaya ka barni da abuna dan Allah"
  Mohd dake kallonta yace"kina hauka ne da kullum na kalli yatsun ki sae naga xoben wani a jikin yatsar ki"
 Ryynt tace"nafa gaya maka mutumin nn baya raye ka sani"
 Mohd yace"ko baya raye Ryynt ae still kina sonsa na gani tunda har kika kasa rabuwa da zoben sa,why can't u remove it n throw it away!
Da sauri Ryynt ta girgiza kanta tace"A gsky bazan iya ba nayi masa alqawari ba kuma zan karya ba"
 Idanun Mohd ne suka kad'a sukayi jajur ya riqo kafad'unta yace"knn kinfi son naci gaba da riqe nawa zoben sbd ba kya sona ko,shin me wancan  mataccen mutum yafi ni dashi ne da har zaki fifita abunsa akan nawa why Rynt ki gaya min!
Kuka kawae Ryynt ta fashe dashi tana kallon sa ta fizge jikinta daga riqon da ya mata ta tafi da gudu kan bed ta kwanta tana kuka tasan tuni ta fad'a son mohd amma bata iya rabuwa da zoben anwar.

  Mohd kuwa idanun sa ne suka qara yin jajur suka ciko tap da qwalla nn ya fita da sauri ya bar d'akin.

Tun daga ranar mohd fushi yake da Ryynt har ya kwashe kusan kwana biyu ba ruwan shi da ita gashi taso ta fahimtar dashi kmr me amma yaqi bata fuska hakan yasa itama ta d'auki fushin dashi har ta ajiye mae rigima kan sae ya maida ta Nigeria gun inna.
Nan fa ya susuce ya shiga damuwa sosai ya kuma so ya rarrashe ta amma fir taqi saurarar shi sae ma kayanta da ta shirya ta fake,hkn ya qara sa shi shiga damuwa amma babbar damuwar sa itace  rashin cin abincinta don tunda tayi break fast bata sake cin wani abinci ba har dare,
gashi kwata kwata ya kasa shawo kanta.


Guraren qarfe goma na dare Ryynt na cikin bacci ta soma jin ana shafar fuskar ta,ta bud'e idonta a hankali ta sauke su akan mohd tana kallon sa cikin fushi,
 shi kuwa ya wani  maraerae ce fuska cikin muryar rarrashi yace"plz Ryynt i beg u,i beg u 4 d sake of our baby ki tashi dan Allah na roqeki kici abinci ko kad'an ne kar ki jama kanki wani ciwon kinga har jikin ki ya soma zafi ,pls i beg u Ryynt dan Allah ki tashi kinji"
 Ryynt bata iya ce masa komai ba sae tashi tayi ta rungume shi tare da fashe masa da kuka,
mohd  ya qara rungumeta sosai a qirjinsa yana rarrashinta.






Billy Giro😊
[3/21/2017]


```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```














             🔮🔮🔮🔮
*page 75*
Har ya samu tayi shiru, ya d'ago fuskarta ya share mata hawaye, nn Ryynt ta ciro zoben azurfar ta ta kamo hannun sa tasa a tafin hannun sa tace"gashi na amince ka yar sae ka saka min naka"
  Tayi maganar ne cikin muryar kuka had'e da sadda kanta qasa.
 Mohd ya d'ago fuskarta yana kallon manyan idanuwanta da suka ciko tap da qwallah kmr zasu zubo, yace"ina sonki Ryynt, zan kuma so abinda kike so koma mene ne indae bana sa6on Allah bane don haka na amince kici gaba da zama da zoben ki har abada dmn ina son ki kasance mae cika alqawari"
  Nan ya kamo yatsar ta zae maida mata zoben Ryynt dake kallon sa tace"Aa ka fara samin naka tukun"
 D'auke da murmushi mohd ya ciro zobe a aljihunsa ya kama yatsarta ya saka mata snn ya maida mata nata da ta cire.
  Nan Ryynt ta rungume sa d'auke da murmushi had'e da fad'in "nagode"
 Mohd ya d'ago ta yana murmushi yace"ni ba godiya kad'ai nake so ba"
  Ta kalle sa tace"To me kake so"
Nan mohd yakai  bakinsa saitin kunnen ta ya rad'a mata magana,Ryynt bata iya kallon sa ba ta sadda kanta qasa cikin murmushin jin kunya tana wasa da zoben diamond d'inda ya saka mata.
 Mohd dake kallonta ya riqo yatsunta ya sarqe da nashi yace"ko baza kimin bane?
 Ryynt wacce still kanta yana a qasa tace"zan maka amma sae ka rufe idonka tukun"
 Ba musu mohd ya rufe
Idon sa a hnkli yace"to na rufe"
 Nan Ryynt taje a hnkli kan kumatun sa ta d'aura masa kiss ta kowane gefe ,mohd ya bud'e idonsa cike da jin dad'i ya sauke su akan Ryynt wacce tayi saurin sa tafukan hannayenta ta rufe fuskarta.
 D'auke da murmushi ya girgiza kansa snn ya janye hannuwanta da ta rufe fuskarta ya kama kumatun ta yaja yace"iyayen kunya to bud'e idanun naki"
 Ryynt bata bud'e idanun ta ba sae murmushi ta sakar mae tare da kwantar da kanta a qirjinsa tana wasa da buttons d'in rigar sa, ya d'ago fuskarta had'e da d'aura mata kiss gefen fuska snn ya tashi tare da fad'in"u have to eat, ina zuwa ko"
 Ta gyad'a masa kai ta kwanta dan duk yunwa ta cinye mata d'an qarfinta.
 Jim kad'an sae ga mohd ya dawo d'auke da abinci ya jawo stool ya d'aura akai snn ya tada Ryynt zaune ya rungume abar sa yana bata abinci har sae da tace ya ishe ta snn ya bata ruwa tasha ya zaro tissue ya goge mata bakinta yayinda Ryynt ta qara lafewa a qirjinsa sbd wani  irin bacci da take jin yana fizgarta.
  Mohd ya shiga shafa bayanta har tayi bacci sae kallon ta yake har sae da baccin nata yayi nisa snn ya shimfid'e ta,ya zagaya ya kwanta tare da rungume ta ya rufa musu blanket snn ya kashe bedside lamp.

Washe gari bayan sunyi sallah suka koma bacci.
 Kamar a mafarki mohd ya jiyo ihun Ryynt ya tashi firgigit yana lalubar inda take bata nn ba shiri ya yaye blanket d'in jikin sa ya tafi bathroom bae sameta ba sae kukanta da ya shiga jiyowa kad'an kad'an ya kuma kasa gane inda sautin kukan ke fitowa gashi sae tafka ruwan sama ake.
  Cikin sauri mae kmr gudu mohd ya fita yana qwalawa Ryynt kira jim kad'an sae gashi ya dawo d'auke da ita sae kuka take dafe da ciki,
 Mohd dake d'auke da ita duk ya rud'e ya shiga damuwa yakai  ta kan bed ,da sauri ta zame kan gadon had'e da fasa ihu dafe da ciki tana yarfi da hannu.
  Nan gabad'aya mohd ya rasa natsuwar sa ya janyo ya Ryynt zuwa jikin sa yana fad'in"plz Ryynt nace ki gaya min me ya faru dake?
 Da qyar cikin kuka tace"wanka naje inayi a cikin ruwan sama shine santsin ruwa ya jani na fad'i akan cikina"
   Kmr zae yi kuka yace"haba Ryynt me ya kai ki zuwa wanka a cikin ruwan sama dan Allah"
  Ryynt kam bata iya bashi amsa ba sae ihu take tana juyi.
  Nan mohd ya tashi a agurguje ya canza mata kaya ya kwashe ta sae zuwa asibiti.

Bayan wasu awanni da fitar su ne,mohd ya dawo d'auke da Ryynt dake bacci yaje kan bed ya kawantar da ita ,ya qure d'an tulun cikinta da kallo yana shafawa d'auke da murmushi a fuskar  sa.
 Nan yaji knocking ya tashi yaje ya bud'e qofar.
 Amir ne tsaye a bakin qofar ,
mohd ya fad'ad'a murmushin sa yace"yanzun nn kuwa nake shirin zuwa gurinka dmn na snr da kae wani babban albishir d'inda ya sameni a safiyar yau"
 Amir dake kallon sa ya saki murmushi snn yace"Au haba na qaraso daga ciki knn"
  " Aa muje daga waje dae"
 Cewar mohd wanda yaja hannun Amir suka fito suka je can gurin shan iska suka zauna kan resting chairs snn mohd ya kalli Amir d'auke da murmushi a fuskar sa yace"wae ka san me, Ryynt triplet take d'auke da su"
 Amir ya fiddo ido yace"what! triplet fa kace?
 Mohd ya lumshe ido ya ware su d'auke da murmushi yace"wlh kuwa baka ji irin tsabar dad'in da nake ji a raina ba har ma na rasa ta yanda zan godewa ubangiji na"
 Amir ya nisa yace"wlh wnn ba qaramin abun farin ciki bane amma Ryynt she is too young  ta yaya zata iya renon su"
 Mohd yace"Uhm Amir knn ae Allah baya d'aurawa bawa abinda yafi qarfin sa, mu ba gamu ba da taimakon sa mun taso cikin qoshin lafiya da samun kyakkyawar kulawa ba tare da umma ta gaza damu ba,kawae abinda nake tsoro shine bana son Ryynt taji dmn idan taji zata tashi hankalinta sosai shiyasa bayan kai bana son don Allah kowa yaji har sae idan ta haifu"
  Amir yace"inshaa Allah but wlh am still really pity her with dis triplet siblings how can she feed them all"
  Mohd yace"common sae kace ba Dr ba u know ko twins ne sae an had'a da madara bare triplet,kuma indae har ina raye wlh inshaa Allah Ryynt bazata wahala da d'awainiyar su ba,iyakar ta dasu shayarwa idan sun buqata fatana Allah yasa yaran basa da wata rigima don banida wani  buri da ya wuce naga Ryynt cikin hutu, kwanciyar hnkli da kuma jin dad'i, kuma ina roqon Allah yasa ta haife min yarana rayayyu cikin qoshin lafiya da ita har su"
 Amir yace"Amin amin"
Snn yace"ashe asibiti kuka ce knn dan my wife tace min taje kai muku break fast ta samu ba kwana"
  Mohd yace"eh wlh asibiti muka je a rud'e shiyasa ma ban samu na snr daku ba"
 Amir yace"subhanallah me ya faru?
 Mohd yace"Uhm wae Ryynt ta fito wasa cikin ruwan sama sae santsin ruwa ya jata ta fad'i kan cikinta shine ina cikin bacci naji ihunta koda na tashi naga bata kan bed don tare nake da ita muna bacci, na tashi na duba bathroom na duba ban ganta ba sae sautin kukan ta da nake jiyowa a wani  gun shine koda na fito na same ta kwance dafe da ciki sae kuka take na d'auke ta naje da ita ciki a can take gaya min abinda ya faru ,ba shiri na kwashe ta mukaje asibiti, Allah da ikon sa har ta fara bleeding wlh akayi nasara shawo kan matsalar kuma da aka duba yarana ba abinda ya same su suna kwance qalau abinsu.
  Amir ya nisa yace"Allah to ya qara tsare gaba"
 Mohd yace "amin"tare da fad'in"bari na koma daga ciki kar Ryynt ta tashi bata ganni ba"
 Amir yace"ok to"
 Nan mohd ya yunqura zae tashi sae kuma ya koma ya zaune tare da fad'in"sorry plz na manta baka gaya min abinda yazo da kae ba har zan tafi"
 Amir yace"no ba wani  abu bane it's just about fitar da kukayi ne kuma ka gaya min"
  Mohd yace"olryt"snn ya tashi ya koma daga ciki.
  Koda ya shiga kuwa ya sami Ryynt ta tashi sae juyi take,ya qarasa gurinta da sauri ya zauna gefen ta tare da shafo fuskarta yace"mene ne Ryynt?
 Bata iya ce masa komai ba sae qwallar da suka ciko tap a idonta, a hnkli ya tada ta zaune ya kwantar da kanta a qirjinsa yana shafa bayanta yayinda yake kallonta ta kulawa yace"gaya min mene ne kinji, ko still marar ki bata daina miki ciwo bane?
 Ta girgiza kanta had'e da fad'in"um um"
Yace"to mene ne gaya min wani  abu kk so?
 Ta girgiza masa kai,
Yace"to ko inda aka miki allura ne yake miki zafi?
  Nan ta gyad'a masa kai shi kuma yakai hannu yana murza mata bayanta a hnkli.
  Can yaji alamar zata yi bacci ya d'ago fuskarta yace"kar kiyi bacci kinji Ryynt bari idan munyi wanka munci abinci ko"
 Ba tare da ya tsaya jin me zata ce ba ya shiga rage mata kayan jikinta snn shima ya rage kayan jikin sa ya tafi da ita bathroom.

Bayan sun fito har sun shirya sunci abinci har Ryynt ta koma bacci, man dake rungume da ita sae kallonta yake d'auke da murmushi yakai  bakin sa a hnkli kan goshinta ya d'aura mata kiss snn ya qara rungume ta had'e da lumshe ido yana shafa cikin ta kmr wani  mae shafa qwai, yayinda yake jin wani  irin farin ciki fal a ransa kmr wanda akayiwa busharà da gidan aljannah.

Wayar sa da ke cikin aljihun wandon sa ce ta shiga ring yayi saurin ciro wayar ya sakata a silent ya zare jikin sa a hnkli ya fita.



Srry plz jiya har na gama muku typing wlh komai  ya goge min gabad'aya😰😪.



Billy Giro😊
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```

















             🔮🔮🔮🔮
*page 76*
Malika ce ta kirashi wacce tana gama waya dashi ta kalli qawar ta faiza dake tsaye kusa da ita a bakin gate ta rakota, tace"kinji my man a cikin kwanakin nn zae dawo amma wae sae yaje Germany tukun"
  Faiza tace"yin me kuma?
 Malika tace"mtsw ni bansan uwar me zae je yi ba wlh yanda na matsun nn ya dawo har ji nake kmr nayi tsuntsuwa naje na same shi amma shi na fahimci kmr ma sam ba missing d'ina a tare dashi sae harakar gaban sa da yake"
  Fa'iza tace" haba ae kinsan dole yana cikin missing d'inki tunda shi ba qarfe bane,amma keda kike tare da switat d'inki yana d'an d'ebe maki kewa meye na damuwa"
   Malika ta dalla mata harara  snn tace"kinji ki nifa manage kawae nake dashi wlh don baza a ko ta6a had'a my man da shi ba, dmn my man qarshe ne gurin iya sarrafa mace samun irinsa a cikin maza sae an tona, shiyasa ko a mafarki bana fatan ganin rabuwa ta dashi.
 Faiza tace"hm ae kuwa tunda kika koma a ruwa kina cikin had'ari dan duk rnr da man yasan kina tare da wani  d'a namiji bayan shi sunanki sorry"
  Malika tace"hm fa'iza knn hkn ma ba zae ta6a faruwa ba,don bazan ta6a sakacin barin sa har ya gano ni ba,dan haka kima daina min baki"
  Fa'iza tace"hm ni ba baki na miki ba idan dae zaki daina to walillahi hamdu ni kinga tafiya ta sae gobe idan kin shigo, kuma dan Allah karki 6ata mana lokaci don nasan halinki da baqin African time kmr akan ki aka fara.
  Malika tace"to naji"
Daga haka ta juya ta koma daga ciki yayinda fa'iza taja motar mijinta da tazo da ita ta bar layin.

 Man kuwa yana gama waya da malika ya koma daga ciki yayi tsaye yana kallon Rynt sae ci gaba take da baccin ta.

Guraren qarfe biyar tuni Ryynt ta tashi suna zaune gefen gado ita da man wanda ke rungume da ita yana ciyadda da gasasshiyar kaza da fresh milk.
  Ryynt bata wani  ci sosai ba tace ya isheta.
 man yace"No Ryynt ki d'an qara ko kad'an ne kinji"
  Tace"um um ya isheni sae anjima ko zan qara"
   Bae ce mata komai ba sae sauran fresh milk d'inda ke cikin cup ya qarasa shinyewa ya ajiye cup yana mai kallon yanda ta d'aura hannunta kan cikin ta nn shima ya d'aura hannun sa akan cikin nata yana mae kallon fuskarta da kulawa yace"mene ne?
  Murya can ciki tace"ba komai motsi kawae yake min"
  Mohd ya shafi cikin yace"motsin ae ba zafi koh?
  Tace"um um babu zafi akwae damuwa dae"
 Yace"shi motsin?
Tace"eh mana ni ban so"
 Mohd yayi d'an nurmushi yana kallon Ryynt wacce ta qarashe zancen ne cikin shagwa6a.
    Bae ce mata komai ba sae shafa cikinta da ya ci gaba dayi ita kuma ta lafe kmr mae bacci tana shaqar daddad'an qamshin turaren sa.
  Sukayi shiru tsawon lokaci abinsu d'akin yayi tsit kmr ba kowa sae can mohd yaje zuwa janye jikin sa a hnkli Ryynt ta d'ago ta kallesa tace"fita zakayi?
  Yace"eh zan fita ne me kike so?
 Tace"zan bika"
 Yace" yi haquri bari idan jikin ki yayi sauqi sosai sae mu fita koh"
   Ba musu ta gyad'a masa kai shi kuma ya d'aura mata kiss kan goshi ya tashi tare da fad'in sae na dawo"
     Ryynt tace"Allah ya tsare min kai"
  Mohd ya tsaya cak ya dawo ya zauna yana kallon ta d'auke da murmushi yace"dan Allah maimai ta min me kika ce"
  Ryynt ta sadda kanta qasa d'auke da murmushin jin kunya tana wasa da zoben yatsar ta wacce cikin murya can ciki mae dad'in sauraro tace"nace Allah ya tsare min kae"
  Mohd dake kallonta sae yaji ya qara sonta cikin jin dad'i ya d'ago fuskarta d'auke da murmushi ya d'aura mata kiss kan lips yace"Amin my Ryynt ina sonki Allah ya bar min ke"
D'auke da murmushi tace"Amin"
Ta bisa da ido har ya fita snn ta kwanta tare da janyo pillow ta rungume a hnkli had'e da lumshe ido tana murmushi.


Sae da ya d'an jima kafin yake dawowa ya sameta zaune falo ita da mtr Amir sae fira suke abin su suna kallo,
 Ryynt ce ta fara ganin sa,
 ya sakar mata murmushi ta mayar masa yayinda take kallon ledodin da ke hannun sa tana son tashi ta tarbo sa amma kuma tana jin kunyar matar Amir wacce ta shiga gaisawa dashi,suna gama gaisawa da ita ya shiga daga ciki ita kuma ta kalli Ryynt wacce ke zaune abinta ba alamar zata tashi,ta saki baki tace"Ryynt ya haka mijinki ya dawo ba sannu da zuwa kuma ba alamar zaki je ki tarbe sa kika bar sa da kaya a hannun sa har ya shige"
  Ryynt tayi murmushi kawae ta sadda kanta qasa, mtr Amir ma tayi murmushi had'e da girgiza kanta ta miqe tsaye d'auke da Sadiq da yayi bacci tace"in dan nice nikam kinga ma tafiya ta"
  Ryynt tace"Aa dan Allah yi zamanki"
  Matar Amir tace"kinji ki da wani zancen kedai sae anjima Allah ya baki lafiya ya kuma tsare gaba"
  Ryynt tace"Amin"
Matar Amir ta fita ita kuma ta shiga daga ciki.
 Man dake tsaye jikin wardrobe sae jin yayi ta rungumo sa a hnkli ta baya tace"sannu da zuwa"
  Ya juyo d'auke da murmushi ya shafo fuskarta yace" sannu my Ryynt ya jikin naki"
  Tace"Alhmdlh bana jin komai sae zafin allurar da ka matse ni aka min"
 Tayi mgnr ne tana kallon sa d'auke da yanayin shagwa6a a fuskarta.
shi kuma ya lakato hancin ta yace"to ai kece kika qi tsayi sae kuka da kike tayi kina qoqarin guduwa sae kace kinga mae d'aukar rae"
  Ta turo baki a shagwa6e tace"to ai  zafi ne da allura gashi har yanzu sae zafi take tamin"
 Yace"to yi hqr bari na qara murza miki sae ta daina miki ciwo koh"
ya fad'i hkne yayinda ya qara janyo ta zuwa jikin snn yakai hannun sa a bayanta yana murza mata gurin ta yanda gurin zae yi saurin watsewa.
 Ryynt tace"wash"tare da qara qanqame shi snn tace"uhm uhm ciwo kamin a hankali"
 Ya qara rungume ta yace"sorry kar kiyi kuka kinji hkn zae fi saurin watsewa"
Nan yaci gaba da murza mata gurin ita kuma sae wash take fad'i tana qara shigewa jikin sa har ta fara masa kuka.
  Kan dole mohd ya barta ya d'ago fuskar ta sae rarrashinta yake yana share mata hawaye yace"is ok kukan ya isa haka muje na nuna miki wani abu da na siyo miki.

Nan yaja hannun ta sae jin dad'i take taga mene ne.
 Kan bed ya fara zaunar da ita snn ya jawo ledodin da ya shigo dasu ya ciro wata er qaramar leda  mae d'an akwatiñ sarqa a ciki ya bud'e
ya ciro wata dakakkiyar sarqar diamond simple  design mai matuqar kyau iri d'aya  da zoben da ya saya mata.
   Wani  irin dad'i Ryynt taji har ranta ta qar6i sarqar tare da qanqame sa tana  masa godiya yayinda man ke kallonta d'auke da murmushi
tace"ya naga iri d'aya da zobe na?
Yace"wlh nima haka kawai yau ina komawa shagon da muka siyo zoben nagan su wae ashe kowane zobe idan kana ra'ayi akwai sarqar su har ma da abun hannu, rigimar ki ce bata bar na fahimta ba"
  Ya qarashe mgnr ne cikin zolaya tare da kai hannu a cikin aljihun wandon sa ya zaro bracelet yace"kinga abun hannun har dashi na siyo maki"
 wani irin dad'i Ryynt taji fiye da na farko ta kar6i bracelet d'in tare da qara qanqame shi tana zuba mishi godiya man kuwa sae kallonta yake cike da so yana murmushi dmn yanzu bashi da wani  burin da ya wuce yaga Ryynt cikin farin ciki ako yaushe.
  Da kanshi ya saka mata sarqa da en kunne da kuma abun hanun ya jata sukaje gun mirror a nn fa ta kasa rufe bakinta dan sarqar ta mata kyau ba kad'an ba har ma ta rasa ta yanda xata qara gode mishi sae hugging d'in sa da ta qara yi tare da masa peck ,
shi kuma ya d'auke ta cak yana juyi da ita kmr wata er baby sae qyalqyatar dariya take har ya kaita kan bed ya sauke.

Washe gari da dare bayan sunyi shirin bacci suna zaune kan bed manne da juna suna cin popcorn suna kallo cike da nishad'i ,
man ya kalli Ryynt wacce ta kwantar da kanta a kafad'ar sa,yace"gobe kad'ai fa muke a garin nn inshaa Allah don haka gobe da safe sae ki shirya muje ki siyo en tsaraba"
  Ryynt ta d'ago fuskarta tana  kallon sa tace"to Allah kaimu goben,su maman Sadiq fa yaushe zasu koma ko a nn zamu bar su?
  Yace"No ae Amir ya kammala abinda yazo yi tare zamu koma har  ma Germany duk tare zamu je muyi kwana biyu sae mu wuce Nigeria.
  Daga haka sukayi shiru Ryynt ta jawo wayarta ta soma chart man dake kallon ta ya kar6e wayar yace"baki san cewa idan ana tare da mai gida ba ba'a yin chat lokaci ne da zaki bashi kulawa"
  Ya qarashe mgnr ne yana murmushi ita ma tayi murmushi tace"yi haquri ganin nayi wae  ba ma yin komai sae kallo kuma ni na gaji da yin kallon"
  Sae da ya kashe TV snn yaja hancinta yace" to ai nima na gaji da yin kallon sae kimin fira mae dad'i inji"
  Tace"uhm sae dae idan kai zaka bani labari"
  Yace"ke ba kiyi labari ba sae ni Ryynt"
 Tace"To ni ina zan sami labari nida ba fita nake ba"
  Yace"to ae ba dole sae labari zaki bani ba"
 Nan takai hannu a hankali ta shafo cikin sa tace"ni kuwa me zan baka naga dae baka jin yunwa"
  Yace"ae ba abinci kad'ai ne abinda mata zata bawa mijinta ba"
   Tace"to ni kuwa me nake da shi da zan baka?
A hnkli ya shafo cikinta tare da fad'in"to tunda ba kya da abinda zaki bani ni inada abinda zan baki wanda zan qarawa babyna qwari"
  Tace"uhm kmr y......bata qarasa fad'a ba kawae taji bakin sa a cikin nata yayinda yakai hannu ya kashe musu wutar d'akin.







Billy Giro😊
[3/25, 11:15 PM] ‪+234 703 962 5239‬: [3/25/2017]

 ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```

















             🔮🔮🔮🔮
*page 77*
Washe gari da asuba mohd ne ya fara tashi ya kalli Ryynt dake bacci abinta lafe cikin qirjin sa.
 Sae da ya yaye blanket d'in jikin su snn ya shiga shafa bayanta a hnkli yana kiran sunan ta.
   Amma shiru ba alamar zata tashi gashi lokacin sallah yana gab da qurewa hkn yasa ya tashi zaune rungume da ita a jikin sa yana ci gaba da tashin ta kmr farko.
  Da qyar ya samu ta shiga motsawa cikin muryar kuka irinta shahwa6a tace"uhm uhm mene ne"
 Mohd yace"sorry tashi muyi sallah sae ki koma baccin kinji"
  Tace"to"
Ta tashi tare da janyo blanket ta rufe jikinta tana lalubar rigar baccin ta kasancewar d'akin ba haske sosai sae mohd ne ya kunna wuta ya nemo mata rigar ya saka mata  suka tashi suka nufi bathroom sukayi brush da arwalla suka fito.

Bayan sunyi sallah har sun koma kwanciya Ryynt ta kasa bacci sae juyi da ta soma yi da qarshe ma kwanciyar ta gagare ta sae tashi tayi zaune ta had'e kai da guiwa takai d'ayan hannunta kan cikinta ta dafe.
  Cikin fargaba mohd ya tashi zaune yana kallon ta ya janyo ta zuwa jikin sa tare da d'aura hannu sa akan cikin ta yace"Ryynt me yake faruwa?
   Murya can ciki tace"bazan iya bacci ba yunwa nake ji"
  Ajiyar zuciya ya sauke a natse snn yace"olryt ina zuwa"
 Nan ya tashi ya nufi kitchen ya bud'e fridge ya ciro gasasshiyar kaza da ya siyo jiya suka ci d'aya suka bar d'aya yasa a microwave yayi warming bayan tayi ya fitar ya saka a plate ya had'o da fresh milk da cup ya fito.
 Ya same ta zaune kmr yanda ya bar ta.
  Ya jawo stool ya d'aura akai snn ya zauna yayinda Ryynt ta matso gab dashi ta zagaya da hannun ta kan waist d'in sa tare da kwantar da kanta a qirjinsa ya fara ciyadda ita har sae da tace ya ishe ta snn ya bata fresh milk tasha ya zaro tissue ya goge mata bakinta ta lumshe ido tare da qara lafewa a qirjin sa ya shiga shafa bayanta sannu a hnkli har tayi bacci ya maida ta ya kwantar snn shima ya kwanta tare da rufa musu blanket ,yayinda take manne a jikin sa sae shafa cikinta yake har yayi bacci.

Basu suka tashi ba sae guraren qarfe goma ,
kai tsaye suka shiga bathroom sukayi wanka suka fito kowanen su sanye da white bathrobe suna tafe d'auke da murmushi a fuskar su  rungume da juna kmr wasu couples.
Ryynt ce ta fara janye jikinta daga na mohd taje zuwa gyaran bed shi kuma yaje gun dressing mirror ya shiga shafa Vaseline bayan ya gama ya kalli Ryynt wacce har ta gama gyara gadon tsaf, ta nufo shi sae kallon d'an tulun cikin ta yake da ya tura bathrobe ,
tana qarasowa ya riqo hannunta ya zaunar da ita kan cinyoyin sa suna kallon juna ta jikin mirror ya d'aura hannun sa kan cikinta yace"wae kinga yanda cikin nn ya qara girma kuwa"
  A shagwa6a tace"eh wlh ni har kunya nakeji yanzu kowa ya kalle ni lokaci d'aya yasan akwai ciki a tare da ni"
  man yayi murmushi yace"Ryynt cikin da ba na shege ba meye na jin kunya kuma"
 Tace"akwai kunya mana tunda ba haka kawae cikin ke fitowa ba dole sae da faruwar wani  abu da kowa ya kanga yasan mene ne"
 Ta qarashe mgnr ne had'e da turo baki Mohd dake kallon ta yayi er dariya tare da d'aurawa bakin nata kiss snn ya kafe idonsa a cikin nata yace"mene ne abun ni ban sani ba gaya min wane abu ne akeyi har a sami ciki?
   Ryynt ta kalle sa kawae ta sadda kanta qasa tana murmushi .
  Mohd yace"gaya min mana ina saurarenki ko ba kya son na shiga cikin masana ne nima"
     Tace"uhm nidae muyi mu shirya kasan kace fita zamuyi fa"
 Har Mohd zae yi magana sae kuma yayi shiru yana sauraren yanda cikin ta ke motsawa a hnkli,sbd still hannun sa na kan cikinta,
 ya kalle ta d'auke da murmushi yace"bari to na qarawa babyna kuzari sae mu shirya mu tafi"
  Cike da jin kunya taje zuwa tashi ya maida ta yace"jiya fa kad'an nayi kin sani"
 Ryynt tayi saurin kallon sa don jiya ba qaramar gajiya ya saukar mata ba.
  Ta shagwa6e fuska kmr zatayi kuka ya lakato hancinta yace" da wasa nake miki fa"
  Nan tayi murmushi yaja hannun ta riqe da Vaseline suka je kan bed ya cire mata bathrobe ya kwantar da ita yana shafa mata mae cikin wani salo mae had'e da matsa mata jikinta yana gama shafa mata man ne yayi kwance kusa da ita suna fuskantar juna ,
ya kai hannu a hnkli ya shafo gefen fuskarta tare da d'aura mata kiss kan goshi yace"ko zamu fasa fita ne yau don naga daren jiya na saukar miki da gajiya sosai u have to rest,kina buqatar hutu"
   Ryynt dake yawo da hannun ta kan qirjinsa cikin lallausar murya tace"ba gobe ne kace zamu tafi Germany ba?
  Eh amma sae mu fasa har zuwa jibi don bana son jigilar ta miki yawa.
  Tace"um um in dae gajiya ce ae tabi gado"
 Ta fad'i hkne tare da saurin rufe fuskarta, mohd yayi murmushi tare da kai hannu kan qirjinta yana shafawa yace"to amma shine da nace zan qarawa babyna kuzari kika tsorata ko kina jin zafin abun sosai ne wae?
   Ta girgiza kanta tare da tashi zata bar gurin ya janyo ta yace"gaya min da bakin ki inji kina jin zafi sosai ne?
  Yafad'i hkne tare da janye hannuwanta da ta rufe fuskarta,a nn tayi saurin cusa fuskarta gabad'aya  cikin qirjinsa tace"plz Mk ka canza wani zancen dan Allah kunya nake ji wlh"
 Mohd ya d'ago fuskarta d'auke da alamar tambaya yana kallonta yace"Mk kuma me kenan kike nufi?
 Ryynt tayi murmushi tace"kai da sunan ka kuma,to yi nazari ko zaka gano"

Mohd yayi shiru yana nazari cikin 3 scnds yace"mohd kabeer kike nufi koh?
 Tayi murmushi tare da gyad'a masa kai,
 Shima yayi murmushi tare da lakato hancinta yace"kin ganki wace irin kwanya ce Allah ya maki wae"
 Tace"Uhm ai kaine mai kwanyar kaida ka gano cikin d'an qanqanin lokaci,inace ba wanda ya ta6a kiran ka da sunan dae ko?
 Yace"ko d'aya kece first person amma meyasa kika yi nazarin had'a sunan nn?
 Tace"sbd nafi so na kiraka da sunan da ba wanda ya ta6a  kiran ka dashi sae ni kad'ai"
 Yayi fari da ido Yace"ko meyasa to?
Tayi murmushi kawai ta riqo en yatsun sa tana wasa dasu tace"in tambaye ka meyasa kake bearing da mohd Aminullah Nasir baka bearing da sunan Abba?
  Yace"Mohd Aminullah shine sunan da aka zana min,Nasir kuma sunan kakan mu ne nake bearing dashi.
 Tace"to ya kaji Mk kana ra'ayin na riqa kiran ka dashi?
  Yace"Ni kuwa nake so my Ryynt dmn sunan ya min dad'i sosai uwa uba kuma ke had'a shi amma kuma zan so nasan dalilin da yasa ba kya son kirana da sunan da kowa ke kirana da shi.
  Shajen fuskar sa ta shafo tana murmushi tace"sbd a gurina kai na daban ne da zan so na ke6ace komai naka a daban dana kowa"
 man dake kallonta d'auke da murmushi yace"idan na fahimce ki kina nufin nayi gurbi a cikin zuciyarki knn?
   Ryynt tayi murmushi tare da sadda idanun ta qasa tace"eh hkne d'in ka fahimce ni "
 Farin cikin da Mohd yaji a ransa ya kasa barin sa a kwance hkn yasa ya tashi zaune tare da tada Ryynt itama ,
ya d'aura tafukan hannuwan sa kan kumatun ta yana mae kallon cikin idanunta snn yace"my Ryynt samun gurbi a cikin zuciyar ki yana nufin kina sona koh?
  Sae da Ryynt tayi qasa da kanta cikin jin kunya tace"eh haqiqa ina sonka bazan 6oye maka ba, ba kuma  zan kasa furta maka ba dmn ka cancanci fiye da haka a gurina sae dae ina tsoro kar sae na sakankance da soyayyar ka kazo ka juya min baya.
  Ta qarashe mgnr ne cikin muryar kuka.
  Mohd da ya tsinci kansa cikin wani  irin farin ciki kan jin kalamanta,
ya d'ago fuskar ta yana kallon idanuwanta da suka ciko tap da qwallah yace"No my Ryynt ta yaya kike tunanin zan iya juya miki baya duk da irin sonda nake miki ko a ganin ki duk yaudara ce ba wae da gaske nake sonki ba"
  Tace"Aa ba haka bane ina tsoron kar sae mun koma wnn matar taka ta qwace min kai ta yanda bazan sake samun kulawar ka ba"
  Mohd yace"To kuma ke sae kiyi sake da baki ki barta har ta qwace miki ni"
 A shagwa6e ta kalle sa tace"to ae kaine in ta gaya maka abu kake yarda kana biye mata kan duk abinda tace har ma baka yin bincike.
  Ta qarashe mgnr ne cikin kuka,
 mohd yayi saurin rungume ta yana shafa bayanta yace"no Ryynt wlh wnn kuskure ne da rashin sani amma nayi miki alqawari inshaa Allah bazan qara kuskure makamancin sa ba,I beg u kiyi haquri kinji kuma ki cire a ranki cewa zan iya juya miki baya wlh ko a mafarki hkn ba zai ta6a faruwa ba inshaa Allah,yi haquri daina kuka kinji.
   Nan ta d'ago  tana share hawayen fuskar ta mohd dake taya ta yace"kin haqura ko?
 Ta gyad'a kai masa yace"to idan kin haqura yi min......
ya qarashe mgnr a cikin kunnen ta,
da sauri ta maqale kafad'a tana dariya zata bar gurin ya janyo ta da sauri yana dariya shima yace"sae fa kin min idan ba haka ba yau  ba inda zamuje ko kuma na tafi ni kad'ai abuna bada ke ba gashi su maman sadiq ma duk fita zasuyi"
 A shagwa6e tace"um um gsky bazan iya ba kunya nake ji ka fad'i wani  abu dae"
 Yace"shi d'in dae nake so idan kuma baza ki min ba shike nn bari na tashi na shirya na fita abuna ni kad'ai"
 Yana gama fad'ar haka yaje zuwa tashi,tayi saurin riqo hannun sa tace"um um to zan maka d'in amma sae ka rufe idonka"
 ba musu ya rufe idonsa Ryynt takai bakinta a hnkli ta had'e da nashi tana tsutsar lips d'in sa da harshen sa cikin wani salo kmr ta sami alawa,after a while taje zuwa zare bakin nata a hnkli,
 man bae barta ba ya koma had'e bakin su ya soma yi mata nashi salon ,
bayan hannun sa dake kan qirjinta yana wasa dashi a nn Ryynt ta kasa in ma kanta sae kwanciya tayi ya bita tare da xare bakinsa ya maida kan qirjinta yana kissing d'in jikinta ta koina Ryynt bata iya hana shi ba sae kama masa tayi suka shiga romancing d'in juna.
 Basu su suka iya barin junan su ba har sae da suka gamsar da juna.

Sukayi shiru rungume da juna sae numfashi da suke fitarwa a hnkli.
  Man dake shafa bayan Ryynt ya shafo fuskar ta tare da d'aura mata kiss kan goshi yace"yau dae ba zancen fita kin gaji da yawa koh"
Tace"um um MK wlh nasa raina a fitar nn dan Allah muje"
  Yace"ae tunda kina so za'a je d'in,tashi muje to muyi wanka sae mu shirya mu tafi"
  Tare suka tashi zaune Ryynt ta rungumo sa tare da shafo cikin sa tace"cikin ka kmr kana jin yunwa"
  Yace"wlh kuwa yunwa nakeji sosai kema nasan kina jin yunwar koh?
  Tace"um um ba sosai ba kasan kafin mu koma bacci naci nmn kaza  bari na kawo maka kaima kaci sae muyi wanka koh"
  No kawo min fresh milk kawae nasha idan muka fito wanka sae muyi breakfast gabad'aya.
  Nan ta tashi ta jawo bathrobe ta saka snn taje ta tsiyayo masa fresh milk a cup ta dawo ta same shi shima ya saka bathrobe d'in sa yana zaune akan bed yana duba missed calls d'in da ya gani a wayar sa don tun zasu  koma bacci ya saka ta a silent.
Yana ganin ta dawo ya ajiyar wayar ,
ta zauna a kusa dashi ta bashi fresh milk d'in da kanta har sae da ya shanye snn suka je zuwa wanka basu wani  jima sosai ba suka fito suka shirya snn sukayi break fast suka fita.

Da dare mohd ne zaune a falo kan doguwar kujera yana sanye da farar singlet n boxer yana kallon labarai yayinda Ryynt ke kwance kan qafafuwan sa tana sanye da farar rigar baccinta silk mae d'an siririn hannu da tsayinta ba zae wuce iya cinya ba ,wacce tuni tayi bacci sbd gajiya dmn yau yawo sukayi sosai a cikin garin mumbae wato gurare daban daban na bud'e ido da kuma gurin shaqatawa sukaje kuma duk inda sukaje sae da mohd yasa aka musu photo shida ita snn sukayi dasu Amir da matar sa da kuma d'an d'ansu sadiq dan duk tare suka fita shiyasa basu dawo ba sae yamma da kaya niqi niqi na en  tsarabar da Ryynt ta siyo.
  Da ya gama kallon labaran sa ne ya kashe TV ya d'auki Ryynt ya shiga ciki da ita.

Washe gari ne suka je Germany kwanan su biyu a can suka kammala abinda suka je yi suka tafi dubai sukayi kwana biyu dmn hutawa inda a germany har dubai sae da man yaja Ryynt suka zaga gari dmn ta bud'e ido.
 Bayan sunyi kwana biyu a dubae ne washe gari suka kama hanyar dawowa Nigeria.

6anaren malika kuwa safiyar yau sae murna take tayi dan man ya kirata ya snr da ita yana hanya har ma ya snr da ita lokacinda jirgin nasu zae yi landing ai kuwa tasa aka shirya masa hadaddiyar liyafa wacce tana ganin lokacin saukar jirgin su ya kusa taje tayi wanka ta tsala ado taja motar ta sae Airpot dmn tarbon mohd wacce kwata kwata bata san cewa tare da Ryynt yake ba dan har yanzu bata da labarin komai  asalima shaf ta shafe babin Ryynt a cikin rayuwar ta.




Billy giro😊
[3/26, 11:27 PM] ‪+234 703 962 5239‬: ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```

















             🔮🔮🔮🔮
*page 78*
Da isar ta ne jirgin nasu ya sauko mutane suka fara firfitowa kan farin ciki bakin ta baya ko rufuwa sae rarraba ido take ta inda zata hango mohd.
 Kai tsaye duk wani farin cikin nata a take ya tafi numfashinta ya nemi ya d'auke,
 ganin mohd tafe cikin baqar suit maqale da Ryynt a jikin sa tana sanye da arabian gown baqa tayi rolling da black top kmr wata balarabia dan gabad'aya ta canza mata ta qara kyau da haske da ita har mohd d'in sae sheqi suke ga wani murmushi da suke da ya qara musu kyau suna tako cikin natsuwa.
 Sam malika ta kasa gazgata abinda take gani musamman hannun mohd da ta hango ya zagayo dashi ta kunkunmin Ryynt yazo dashi har izuwa kan tulun cikinta da ya fito 6aro 6aro da cikin ne abinda yafi matuqar bata mamaki don har suka qaraso ta kasa gazgata abun wae kodai mafarki ne ba gske ba gashi ko qaramin yatsanta tama kasa motsawa sae dasqarewa da tayi a guri d'aya ta kafe su da ido tana kallo Nasir  yaje ya tarbe su cike da murna.
 Yayin da su saliha da mami dake tare dashi suka qanqame Ryynt cike da murnar ganin ta kafin suke zuwa gun matar Amir itama suka tarbe ta.

D'auke da murmushi mohd ke kallon malika dake qarasowa gurin su wacce tana isowa cikin tsananin 6acin rae ta damqo suit jacket d'in mohd da hannuwanta duka biyu ta jijjiga shi tace"gaya min shin mafarki nakeyi ko kuwa da gaske ne dae wnn abar ce nake gani a tare da kai!
  Da qarfi mohd ya buge hannuwanta ya jawo Ryynt zuwa jikin sa yace"kin ganta gata ba mafarki kikeyi ba dagaske ne kuma wlh kar ki kuskura ki sake kiranta da wnn abar idan ba haka ba wlh zanyi mugun sa6a miki very stupid!
  Nan kawae malika tayi kukan kura zata shaqo wuyan Ryynt man yayi saurin ture ta gefe
snn ya nuna ta da yatsa yace" Ryynt she is my wife n my life bazan ta6a yarda kici zarafinta ina tsaye ba and idan har kinsan tashin hankali ya kawo ki maza bar gurin nn in daina ganin ki ko kuma wlh na miki dukan tsiya a nn!
  Tsaf tasan zae iya aikata abinda yace ta kalli Ryynt ta qyasta yatsunta tare da nuna ta tace"wlh wlh yau sae na zamo ajalinki"
  Daga haka ta wuce fuuu a fusace.
  Mohd dake kallonta ya buga tsaki dan shi a shirme ma ya d'auki zancen nata ya kalli Ryynt wacce still tana a jikin sa yace"Ryynt are u ok bata ta6a ki ba dae ko?
   Ryynt ta girgiza kanta tana qoqarin maida hawayen da suka cika mata ido ba wae don ta tsorata da jin furucin malika ba sae don ko kad'an bata ji dad'in abinda ya faru ba har dae yanda gabad'aya gurin idon kowa ya tsaya a kansu har ma wasu na nuna su suna magana.
 Nasir da Amir ne suka ce da mohd "wae me yake faruwa ne?
  Mohd ya buga tsaki yace"da Allah ku fita batun mahaukaciya kuzo mu tafi"
   Daga haka suka wuce ba wanda ya sake cewa komai.

Amir da matar sa da d'ansa motar su suka shiga da driven su yazo da ita yaja su zuwa family houshe.

Mohd da Ryynt kuwa motar Nasir suka shiga dasu har su saliha wanda basu zarce koina ba sae gidan inna wacce tana ganin Ryynt ta washe baki cikin tsananin murna suka rungume juna inna ta d'ago riqe da baki sae kallon Ryynt take cikin jin dad'i ganin yanda kallo da'ya zaka yiwa Ryynt kasan cewa tana samun matuqar kulawa da jin dad'i musamman yanda fatar ta tayi smooth da haske tayi fresh da laushi kmr ftr sabon jinjiri sae sheqi take tana qyalli.
   Washe da baki inna ta qwalawa baaba hurera kira baaba hurare taxo da murna ta musu sannu da zuwa wacce itama ta kasa rufe baki sae kallon yanda Ryynt ta canza take.
Washe da baki inna tace"kema kinga yanda Rayyanah ta dawo ko awa wata balarabiyar saudia ai  Alhamdulillahi ba abinda zance da kae Muhammadu sae nace Allah shiyi maka albarka dmn ba makawa Ryynt ta sami sauyi da kulawa a gurinka haqiqa naji dad'i wlh ubangiji Allah sarkin halitta shi qara yi maka  albarka.
  Mohd yace"Amin Amin inna"
yayinda yake kallon Ryynt dake murmushi tana fmn 6oyon tulun cikinta da take jin kunyar a gani.
   Kai tsaye taga mohd ya d'aura hannun sa akan cikin nata yace"inna kalli d'an jikanki ki fa yanda ya taso"
   Wata irin kunya Ryynt taji kmr ta nutse tayi saurin ture hannun sa zata bar gurin mohd ya janyota zuwa jikin sa yana dariya,a shagwa6e ta fashe masa da kuka ta qwace kanta ta koma jikin inna ta 6oye fuskarta a qirjinta tana ci gaba da kukan da ta soma maida shi da gaske don rugumar da ya mata yasa ta qara shiga wata kunyar.
  Ya riqo hannunta yace"zo ni na 6oye ki a nawa qirjin tunda kunya kike ji.
  Da sauri Ryynt ta fizge hannun ta yayinda inna ta girgiza kanta d'auke da murmushi tace"Allah ya shirye ka muhammadu snn ta shafo bayan Ryynt tace"qyalesa Ryynh yi shiru daina kuka ae yau ya jawa kansa don baza ki koma gidan sa ba
sae ya zo biko"
  Mohd yayi saurin kama kunnen sa yace"Aa inna amin afuwa  bazan sake ba na tuba"
 Inna tace"kaja kunnen ka ma yafi na zomo tsayi bazan haqura ba  sae kazo biko tunda har kasa min ita kuka.
   Mohd ya shagwa6e fuska kmr qaramin yaro yace"inna nine fa"
  Tace"kaiwa daga ina"
 Mohd yace"mai gidan naki kuma inna Baaba hurera  kinaji fa"
 Baaba hurera dake kallon su ita da su Nasir suna murmushi ta girgiza kanta d'auke da murmushi taje da sauri dmn kawo musu abinci da lemu da ruwan sha kmr yanda inna ta umarce ta.

A nn tsakiyar falon aka shimfid'a qatuwar darduma Baaba hurare ta jera kulolin abinci akai da ruwa da lemu wanda dama musamman dan su aka had'a.

 Zasu fara cin abinci  knn wayar mohd ta shiga ring koda ya duba mae kula da harkokin gidan sa ne ya kirashi yake snr dashi irin 6arnar da malika ke aikatawa a gidan shi don sae farfasa abubuwa take.
  A natse ya kalli Nasir yace"plz bani makullin motar ka"
   Ba musu Nasir ya miqa masa makullin yace"lafiya dae ko"
  Yace"ba wani  abu bane yanzu zan dawo inshaa Allah"
Daga haka ya fita Ryynt ta bisa da ido sae ga inna ta fito daga ciki d'auke da fruits salad mai sanyi da ta ciro a cikin fridge taga bata ga mohd ba tace"Aa ina kuma muhamnadu ya tafi"
  Tayi mgnr ne tana mai kallon Ryynt wacce bata iya cewa komai ba sae Nasir ne yace"an kira sa ne ya d'an fita ya dawo"
  Inna tace"ayyo"
tare da ajiye fruit salad d'inda ke hannun ta.

Mohd kuwa yana isa gida yayi tsaye a cikin falo hannuwan sa cikin aljihu yana kallon yanda gun dining duk yayi  kaca kaca malika duk ta watsar da liyafar da tasa aka shirya mae ta kuma farfasa duk sabbin kayan da yasa aka zuba a falon na gyaran gidan da yasa akayi gabad'aya duk wani  abin fashewa bata bar shi ba har TV kuwa.
  Yana tsaye sae gata ta fito kitchen riqe da wuqa sabuwa dal zir sae qyalli take.
  Tayi kmr ma bata ganshi ba ga mamakin sa sae sauri take ta fita yayi hanzarin fizgota yace"ke ina kuma zaki je da wuqa"
  Bata masa magana ba sae qwatar kanta da take qoqarin yi ya qara damqar ta had'e da daka mata tsawa yace"ina zaki tafi nace!
  Ta fizge kanta tace"so kake kaji to gurin wnn abar zan tafi don wlh yau bazan barta da rai ba sae na hallaka ta na kuma hallaka abinda ke cikin cikin.....bata qarasa fad'a ba taji saukar wani irin gawurtaccen mari ya kuma ja hannun ta ya tafi da ita sae fizge fizge take har ya kaita d'akin ta ya jefar ya fito ya rufe d'akin ya xare key ya saka a aljihun sa ya fita yana mamakin hauka da baqin kishi irin nata.

 Gidan inna ya koma Nasir ya kar6i makullin motor sa ya fita zuwa aiken da inna ta mai wacce tana bashi saqon ta koma daga ciki sbd wayar ta da taji tana ring.
  Ya kasance falon ba kowa don mohd yana fita Ryynt taja su saliha suka tafi d'akinta da inna tasa aka share tun jiya da taji zasu dawo.
  Ya nufi d'akin kai tsaye ya same su zaune su uku suna cin abinci a mazubi d'aya sae firar  bayan rabuwa suke cike da nishad'i.
  Ba tare da yace musu komai ba ya riqo hannun Ryynt ya fito da ita zuwa falo suka zauna kan darduma da abincin sa ke ajiye da aka sa d'ayan plate aka rufe ya bud'e abincin yace"muci wnn sae ki bar musu wancan suci gaba da ci"
  Tace"meyasa abincin fa yana da yawa baza su iya cinye sa ba na mu uku ne muka d'iba"
  Yace"eh ki bar musu kawae"
  Ya fad'i hakane tare da d'ebo abinci a spoon zae kai bakinta tace"mk nifa ina jin kunyar inna tazo ta same mu muna cin abinci a tare"
  Nan kawae ya tashi yaja hannun ta riqe da abinci suka tafi d'akinta da niyar suci a can ,
gashi ita ko a gaban su saliha d'in bata iya cin abinci a tare dashi,
 tace"plz Mk tafi kawae kaci abinka ni sae na ci gaba da ci tare da su saliha kaji.
 Man da har ya zauna kan sofa ya kalleta kawae bae ce mata komai ba ya tashi ya fita d'auke da alamar fushi a fuskar sa.
  Jiki sanyaye Ryynt ta zauna dmn ci gaba da cin abinci tare da su saliha.
    Saliha dake kallonta tace"is better ki tashi kije ki bashi haquri kici abincin dashi dmn ga dukkan alama fushi yayi"
  Ryynt da qwallah suka taru a idon ta tace"Saliha kunya nakeji da dae mu kad'ai ne zan iya"
  Saliha tace"olryt bari to mu koma falo nida mami sae ku dawo a nn kuci"
   Saliha ba haka nake nufi ba ,saliha da ta fhmce ta tace"to ai sae ki zauna mijinki na fushi dake mala'ikun Allah na tsine maki"
  Ryynt ta kalli saliha ,mami tace"kije mana Anti meye abin kunya dan kinci abinci da yaya nima fa da muna gidan sa a tare muke cin abinci kin sani"
  Ryynt tayi d'an guntun murmushi tana kallon mami snn ta tashi taje falo ta samu mohd ya mayarda abincin ya rufe zae fita don har ma yakai  bakin qofa.
  Ryynt ta kira sunan sa a hnkli.
Ya tsaya kawae ba tare da ya juyo ba.

 Taje ta riqo hannun sa ya juyo yana kallon ta tace"MK ina zuwa kuma baka ci abinci ba?
  Yace"zanje inda za'a bani ba tare da na roqa ba"
  A nn tayi saurin sadda kanta qasa d'auke da hawayen da suka cika mata ido don sae taji wani  irin kishi duk da taga yanda suka kwashe shida malika a airpot.
  Murya can ciki tace"yi haquri muje na baka"
   Yace"tafi kawae kici inda kike son ci d'in ni ki barni na tafi abuna"
   Hawayen da suka cika mata ido ne suka silalo a hnkli ta share hawayen jiki sanyaye ta juya zata bar gurin,
Jiki sanyaye mohd ya riqo ta yace"meye na kuka kuma Ryynt inace kinfi ra'ayin kici abincin a tare da su shiyasa nace ki tafi"
 Ryynt tace"Allah ba wani nn fushi kayi "
  Ya janyo ta zuwa jikin sa yace"to yi haquri kuma ni ba fushi nayi ba dama na gwada ki ne kawai inga ko kina son mijinki da gaske sae naga ashe ke dad'i miji ce da ba kya son ganin fushin sa.
Da wasa ta sha toka tace"me kake nufi?
 Ya d'aura mata kiss kan lips yace"abinda kika fahimta shi nake nufi"
A shagwa6e ta maqale kafad'a tana doka qafafun ta qasa tace"wlh Aa ni ba dad'i miji bace"
  Ya lakato hancinta tare da fad'in"ba wani  nn na gano ki ae"
   Kuka ta fashe dashi ta shiga kai masa duka irinta ta shagwa6a tana fad'in"wlh Aa ni ba dad'i miji bace"
 A nn Mohd ya shiga kare dukan sae dariya yake ita kuma sae ci gaba da dukan sa take tana fad'in ita ba dad'i miji bace shidai ne haka ba ita ba nn ya kama yatsan ta ya gantsara mata d'an qaramin cizo ya gudu ya barta sae kukan shagwa6a take tana yarfi da hannu yaje kan darduma ya zauna tabi shi ta kama yatsan sa ta rama ya shiga yarfi da hannu sae dariya take masa dan da gaske ta cije shi, ganin zae kama hannun ta ya rama ta tashi da sauri ya biyota dai dai inna ta fito taje bayan inna ta la6e sae gwalo take masa tañà dariya.



Sorry 4 dis one

Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```

















             🔮🔮🔮🔮
*page 79*
Nan mohd ya shiga qoqarin ganin ya janyota inna bata barshi ba sae fad'in take wae muhammadu lafiyarka?
  Yace"Inna cizo na fa tayi"
Ryynt tace"wlh inna shine ya fara ni kuma na rama"
 Ta qarashe mgnr tare da yi masa gwalo bata ankara ba sae ganin tayi ya jawota tace"wayyo Allah yi haquri inna zae rama dan Allah ce yayi haquri bazan sake ba wlh"
  Inna taje zuwa qwace ta mohd yace"inna wlh ba abinda zan mata abinci zamu ci"
    Ryynt tace"inna ba wani nn ramawa zae yi"
Ta fad'i hkne yayin da take yunqurin komawa ga inna amma bata iya ba dan man sae d'aukar ta yayi cak tana wuntsil wuntsil da qafafu har yaje da ita kan darduma nn inna tayi murmushi had'e da girgiza kanta ta tafi ta basu guri dan ta fhmci mohd ba kunya ne da shi ba.
    Ryynt kuwa cikin fushi ta kalle sa tace"wae meyasa kake min abubuwan da kake sa ina jin kunya dan Allah ban so ka daina"
  Ta qarashe mgnr cikin muryar kuka mohd ya d'aura mata kiss kan lips yace"to naji yi hqr muci abinci"
    Ta tashi tare da fad'in"banci"
   Mohd ya riqo ta ta buge masa hannu yayi saurin kama hannun nasa had'e da fad'in "Ash!
 ya yaye hannun rigar sa wata irin babbar yankuwa ta bayyana yayinda hannun farar rigar sa ta ciki duk ta lalace da jini.
  Da sauri Ryynt ta koma ta zauna ta riqo hannun sa tana kallon gurin ta kalle sa idon ta tap da qwallah tace"mk me ya same ka haka?
   Bae ce mata komai ba sae kallon yankuwar yake yana tuna lokacinda yaja malika zae kaita d'aki ne wuqar hannunta ta yanke sa garin fizge fizgen ta.
   Ya kalli Ryynt wacce duk ta rud'e tana basa haquri had'e da tambayar me ya same shi .
ya shafo fuskarta yace"d'an wani tsautsayi ne ya same ni d'azun da na fita amma kar ki damu kinji"
  Ryynt da hawaye suka silalo kan fuskarta ta kalle sa tace"wnn ne d'an jifa yanda yankuwar tayi babba sosai warkewar ta ma zae yi wuya"
   Ta qarshe mgnr ne cike da son fashewa da kuka.
  Mohd da saurin kukanta ke bashi mamaki gashi baya son ganin kukan nata ko kad'an ya janyo ta zuwa jikin sa yace"don't cry mana Ryynt jikina baya da matsala take naji sauqi kar ki damu kinji"
  Ryynt ta d'ago tare da share hawayen ta ta tashi tare da fad'in "to ina zuwa"
  Ya maida ta yace"no yi zamanki bana so inna ta sani"
  Tace"ba gaya mata zanyi ba first aid case  zan d'auko"
  Yace"yi zamanki kawae idan na fita zanyi dressing d'in gurin don idan inna taga kin d'auko first aid kit d'in dole zata nemi dalili"
  Ryynt ta gyad'a masa kai tana kallon yankuwar da ya maida hannun rigar sa ya rufe.
 Ya sakar mata murmushi yace"to muci abinci koh"
  Fuskar ta cikin damuwa ta bud'e plate suka fara cin abincin tana bashi yana bata har suka kammala cin abincin.
mohd ya tashi zuwa sllr magrib.
  Ita kuma ryynt sharp sharp ta kwashe kwanikan abincin ta kai kitchen snn ta tafi d'akinta ta sami su saliha tuni sun kammala cin abincin su,
Saliha na bathroom gurin yin arwala mami kuwa sae fmn game take da game tap d'in ta.
   Ryynt ta kar6e game tap d'in ta kashe tace"mami  ana yin kirayen kirayen sallah kina yin game ki daina ba kyau kinji"
  Mami ta washe baki tace"to Aunty na daina amma yaushe zamu koma gidan yaya"
   Ryynt tace" idan kun koma gida ki gaya ma umma a had'a maki kayanki idan zan koma sae mu koma kinji"
   Mami ta daka tsalle ta rungume Ryynt tace"da gaske Aunty?
  Ryynt tayi murmushi tare da gyad'a mata kai.
  Sae ga saliha ta fito daga bathroom Ryynt ta tashi ta shiga.

Sae da suka ida  sllr magrib da d'an jimawa Nasir yazo ya kwashe su ya maida su gida.
  Ryynt kuwa d'akin inna taje sae firar bayan rabuwa suke cike da nishad'i.

Mohd kuwa tunda ya fita sllr magrib ba shi ya dawo ba sae bayan isha'i.
  Kai tsaye d'akin inna ya nufa ya gaida inna dake jikin wardrobe ta saka dardumar sallah ta amsa gaisuwar yayinda man ya saki baki yana kallon Ryynt wacce zata shiga bathroom sanye da zani d'aura gaba da hijabi har guiwa riqe da brush a hannunta
yace"keda nazo muje gida kuma wankan me zakiyi"
  Tayi murmushi tace"nifa a nn zan kwana"
  Yace"hm da wasa kike kema yi sauri je yi wankan ina jiranki kizo mu tafi"
  Inna tace"kai dae keyin wasa muhammadu ae Ryynh ba inda zata je sae ta min kwana biyu tukun"
  Mohd yace"dan Allah inna daina zancen nn"
  Inna tace"yo muhammadu kmr ya na daina zancen nn ,kwanaki da yawa bana tare da Ryynt su en kwana biyun da zata min na rage kewar ta kuma kace a'a"
 Inna ba haka bane indai Ryynt ce gobe sae na kawo maki ita,
  Inna tace"to muhammdu nuna min ka fini iko da ita.
  Fuskar sa d'auke da damuwa yace"ba haka bane inna ina laifin dae ko kwana d'aya"
 Inna tace"Aifa sae ka d'auke ta ku tafi ban hanaka ba"
 Ba yanda mohd ya iya yace"Aa inna yanda kike so haka za'ayi"
  Nan ya tashi cikin damuwa had'e da kallon Ryynt wacce kanta ke qasa yace"idan kinyi wankan ki sameni falo muyi sallama"
  Ta gyad'a masa kai snn ta bisa da kallo har ya fita taje cikin murna ta qanqame inna tace"inna na gode nsn da nice ma ba zae bar ni ba"
  Inna tace"inafa koni ai dan nasha masa toka ne amma ke kuma Ryynh meyasa baza ki bisa ku tafi ba naga fa kmr ya shiga damuwa sosai"
  Ryynt tayi shiru ita kanta tana son bin sa amma kuma tasan idan ta bishi zata kwana cikin quncin rashin sa a kusa da ita dmn in ga adalci gun malika ya kamata ace ya kwana,shiyasa take son ta kwana biyu tukun in yaso idan ta koma sae ta fara koyon sa ma kanta haquri.
  Tace"inna ni nafi so kawae na kwana a nn"
 Inna tace"to shike nn ae tunda yana da wata mtr ba matsala bane jeki abinki kiyi wanka amma fa kar ki jima kinsan fa yace yana jiranki"
  Nan Ryynt ta wuce bathroom tayi wanka sharp sharp ta fito ta shirya cikin riga da wando na bacci ta saka hijab ta fito tayi tsaye jiki sanyaye ganin mohd baya falon knn ya gaji da jiranta ya tafi ko kad'an bata ji dad'i ba amma hakan ta juya zata koma ciki sae ga mohd ya shigo ta sauke ajiyar zuciya a hnkli tana kallon sa tare da sakar masa murmushi tace"ae na d'auka ko ka gaji da jirana ka tafi har banji dad'i ba"
  Sae da mohd yaja hannunta suka zauna kan doguwar kujera snn ya kalle ta yace"dan na tafi ae ba damuwar ki bane farin cikin ki ne tunda har kika yarda zaki kwana biyu ba tare da ni ba"
   Tace"yi haquri kwana biyu ae kmr yanzu ne in ga rae da lafiya da kuma yardar ubangiji"
 Yace"a gurin ki ba amma ni a gurina tamkar shekaru biyu ne"
  Tace"uhm bacci ne fa kawae baza mu riqa yi a tare ba dan nasan zaka shigo gobe ae ko?
 Yace"um um bazan shigo ba"
  Tace"meyasa ko ka manta da zancen zuwan mu family house"
  Ban manta ba driver zan turo maki tunda ni kin gaji da gani na.
    A shagwa6e tace"wlh Aa  ba haka bane sae dae in kaine ka gaji da gani na"
   Yace"ta yaya Ryynt nida na shiga damuwa jin zaki kwana har biyu ba tare dani ba amma ke ko a skin har ma Allah Allah kike kar nace ban yarda ba"
  Ryynt ta marairaece fuska tace"Mk ba wae ban damu bane dole zan damu ae kasani,kuma kayi haquri kar ka turo min driver kazo muje tare kaji,sae dae kuma kmr mun shiga haqqin mtr ka ko?
  Kallon ta mohd yayi dan shi ya ma manta da wata malika yace"hm nifa wasa nake miki da kaina zan zo muje bari naga baby na tafi dare nayi"
    Nan ya kai hannu zae yaye mata hijab ta riqo hannun tare da fad'in"in ga"
Nan ta yaye hannun rigar sa a hnkli taga har yayi dressing d'in gurin da ya yanke ta kalle sa da damuwa tace"sannu"
  Ya lumshe ido tare da gyad'a mata kai sae kuma ya saki murmushi yana kallonta kmr wanda zae ce wani  abu sae kiss ya d'aura mata kan lips yace"ina sonki Ryynt"
  Ryynt tayi lallausan murmushi tare da sadda kanta qasa shi kuma yakai  hannu ya yaye hijabin ta har rigar ta ya shafi cikin ya duqa ya d'aura masa kiss ya d'ago ya kalli Ryynt dake kallon sa d'auke da murmushi ya shafo gefen fuskarta tare da d'aura mata kiss kan kumatu yace"sae da safe koh"
  Nan suka tashi a tare mohd ya nufi qofa Ryynt ta bisa da ido har yasa qafa zae fita ta kira sunan sa a hnkli ya juyo a natse yana kallonta taje kmr mae jin kunya ta d'aura masa kiss gefen fuska snn ta sadda kai tace"Allah ya tsare min kae"
  Mohd da har ransa yaji dad'i ya shafo fuskarta d'auke da murmushi yace"Amin my Ryynt nagode"
  Snn ya fita had'e da yi mata bye bye ta juya jiki sanyaye ta shiga ciki.

 Man kuwa yana isa gida d'akin malika ya nufa ya bud'e d'akin ya same ta tana  waya da fa'iza yayinda take cewa"wlh kuwa da gaske nake gaya miki fa'iza duk makircin da na qulla mata a banza ya maida auren wae har ma tana d'auke da ciki tulele dashi ,
Shine d'an baqin son haifuwa ya wani kwasheta suka tafi waje abinsu suna holewa ashe shine dalilin da yasa yace min kar inje.
  Fa'iza tace"wlh duk kuskuren ki ne malika in banda wauta irin taki ta yaya zaki gayawa qanwar sa pretty yanda komai ya faru, ae kin san dole ta gaya masa kin ma ci sa'a da yaji bae sake ki ba ya fita harakar ki kawae.
 Malika tace" faiza ba haka bane pretty sam bata snr dashi ba dan  na kirata tayi min bayanin komai abinda ya faru da bana nn ashe er banzar tun kafin ya sake ta ne ta sami cikin nice kawai ya maida er iska yana nuna min sam bata gaban sa bayan komai yana wankana a tsakanin su.
  Fa'iza tace"lallai ya kamata ki d'auki babban mataki don wlh yaci zarafinki da yawa.
Malika tace"Hm bari kawae fa'iza wlh sae tayi nadamar sanin my man a rayuwarta don sae nayi ajalinta da ita har abinda ke cikinta kuwa"
  Fa'iza tace"hm ni wlh man har mamaki ya ban da har ya iya kula wnn abar har ya bar wani  abu ya shiga tsakanin sa da ita .
  Malika tace"fa'iza yarinyar ce akwai diri da kyaun jiki shiyasa tun farkon ganinta nayi qoqarin ganin na raba ta dashi dmn nsn yau da gobe zata iya janye masa hnkli na dawo er kallo.
   Fa'iza tace"ita wnn abar er qauye baqa da ita ma"
  Malika tace"itafa kallon tsaf ne baki mata ba,dan idan ma kika ganta yanzu to wlh sae kin raina kanki.
   Fa'iza tace"hm ta raina kanta dae don wlh in nice tun a airport sae dae wata ba ita ba kai har shi d'in ma in ya matsa sae na had'a dashi don nafi gwammace mu rasa gabad'ayan mu.
   Malika tace"kinsan ina son my man ba kad'an ba baxan iya masa haka ba kawai dae ita zan hallaka wlh don ba'ayi macen da zata ra6e sa na barta ba.
  Fa'iza tace"hm aini duk rnr da mijina yamin irin haka to kuwa na barsa har abada duk sonda nake masa wlh ki tsaya nn garin kallon ruwa kwad'o ya maki qafa,baqin cikin d'a namiji ya kashe ki a banza yanxu gashi ya rufe ki a d'aki ya barki ya tafi abinshi da ace lokacinda ya same ki kin fara ta kanshi ai da tuni itama kin gama da ita.
  Malika tace"hm fa'iza bazaki gane irin son da nakeyiwa my man bane kuma shima yana matuqar sona ta yaya zan cuci kawunan mu akan wnn abar kawae dae yanzu jiransa nake yazo ya bud'e ni,
 to kuwa ko ta halin qaqa daren yau bazan bar barta ba wlh........qarar wayar man ce ta katse ta don sam bata ji shigowar sa ba duk mgnr nn da suka jima suna yi kuwa.
  A tsorace tayi saurin katse wayar tana kallon man dake zaune kan sofa ya jingina bayan sa ya d'aura qafa kan qafa yayinda ya bar wayar sa naci gaba da ring a cikin aljihun sa ba alamar zae ciro ya d'aga sae malika da yake kallo.
   Ya tashi cikin tako d'ai d'ai har ya qaraso gurin ta yana mata wani  irin kallo ita kuma gabad'aya tasha toka dan kar ma yaga damar ta.
  A natse cikin deep voice yace"qarya kike ba kya sona malika babu wata soyayya ta a tare dake, kina sona zaki hallaka min abinda nayi matuqar qwallafa raina akan shi don kawae biyan wata banzar buqatar ki,to bari kiji wlh ni duk kin fita a raina sakin ki a gurina ba komai bane  kuma idan kikayi gigin wani abu ya sami Ryynt kin san sauran amma dan Allah ki fara gwadawa tukun ki gani shege ka fasa kije tana can gidan inna kin dad'e baki hallaka ta ba.
 Daga haka ya kama hanya ya fita.
 Malika ta bi sa d'auke da idanun ta da suka kad'a sukayi jajur suka ciko tap ta qwallah.
Aguje hawayen suka  fito suna sauka akan kumatun ta ,ta share hawayen da takaici tace"wlh in kasan wata baka san wata ba.

Washe gari guraren qarfe goma man ne ya fito cikin shirin sa na farar suit sae zuba qamshi yake yaje ya shiga farar motar sa da aka wanke masa aka goge yaja ya fita ya bar gidan.
  Malika dake tsaye a balcony tana kallo koda ya fita snn ta juyawar ta ta koma ciki.
  Man kuwa kai tsaye gidan inna ya nufa bai sami kowa a falon ba haka ma d'akin inna nn ya tafi d'akin Ryynt ya sameta kwance taci kwalliya abinta cikin wani dakakken less black mai d'auke da  pink big flowers tana riqe da waya a hannun ta  tana chat yayinda d'an qaramin bakinta mae d'auke da pink lipstick ke d'an motsawa a hnkli alamar tana cin wani  abu.
  Qamshin turaren sa ne yasa ta d'ago ta kalli bakin qofa ta ganshi jingine  jikin qofar hannuwansa a cikin aljihu yana kallonta d'auke da murmushi sbd ba qaramin kyau yaga tayi mishi ba itama sosai taga ya mata kyau ta sakar masa murmushi kafin take tasowa ta rungume sa a hnkli tana mishi sannu da zuwa.
  Mohd ya shafo bayanta a hnkli yace"mun tashi lafiya?
 Tace"lafiya lau"
   Ya d'ago ta ya shafa cikin ta yace"to ya babyna"
  Tace"shima qalau"
A nn ya kalli d'an qaramin bakinta dake motsi yace"me kike ci?
 Tace"chewing gum ne"
 Yace"da safen nn Ryynt kinyi breakfast ne?
  Tace"eh"
 ok inna fa naje d'akin ta ban sameta ba?
 Tana bathroom wanka take,ya hannun naka kaji sauqi?ya gyad'a mata kai tare da fad'in Alhmdlh.
  Tace"muje inga"
 Nan taja hannun sa suka je kan bed suka zauna ta yaye hannun rigar sa tana kallon gurin da ya sake mishi sabon dressing ta maida hannun rigar ta  d'ago ta kallesa a hnkli tace"wae mk me ya same ka ne?
  Ya lumshe ido tare da kwantar da kanta a qirjin sa yace"My Ryynt ba wani  abu bane tsautsayi ne"
  Ta d'ago ta kalle sa kawae bata ce komai ba ta sake maida kanta tana wasa da buttons d'in rigar sa yace"me zan samu naci banyi break fast ba na fito sae yunwa nake ta ji"
  Ryynt ta d'ago tana kallon sa tace"Arish mukayi da soyayyen qwai sae farfesun kaza ,kuma akwai ruwan zafin tea a flacks,na kawo maka"
  Yace"eh kawo min"
 Sae da ta shifid'a qatuwar darduma a nn qasa kusa da gefen gadon snn ta fita ta dawo d'auke da kayan break fast d'in gabad'aya cikin tray ta ajiye kan darduma snn ta koma fita taje d'akin inna ta d'auko masa fresh milk da ruwa ta kawo kan darduma ta jera ,
man dake zaune har ya fara zuba ma kansa ya kalle ta washe da baki yace"wae nida wa wad'an nn kayan haka?
  Tace"uhm kai kad'ai mana"
Yace "so kike na kasa tashi knn"
  Tace"Aa so dae nake nayi fata fata da yunwar cikin ka"
Yace"to ae sae ki zauna ki bani da kanki dmn zanfi ci sosai"
 Nan ta zauna ta qarasa zuba abincin a plate ta d'ebo a fork spoon zata fara bashi  yace"Aa da yatsun ki nake son ki ciyadda ni yau"
   Murmushi tayi ba tare da ta musa ba ta ajiye fork d'in tasa yatsunta ta soma ciyadda shi.
 Sae can bayan har ya kusa qoshi ,ya d'ibi arish da qwai zae kai bakinta tace"um um nifa a qoshe nake"
 Yace"wae kar kice sae ci nake ban taya miki ba"
  Tace"uhm bayan duk dae kuma kaida kazo kwaraka ma"
  yace"ai kece ogar kwarakar da kika kwana gidan mutane kika bar mijinki cikin kewa"
  Tace"uhm gidan innan ne na mutane?
Yace"to na aljanu ne"
   Tace"hm gidan ka ne na aljanu ae da ake kwasar mutum a yar"
  Ya kalleta had'e da er dariya yaja hancinta yace"ni gidana ba aljanu kece dae da baqin tsoron ki sae kace farar kura"
 A shagwa6e ta turo baki tace"ba wani nn kawai kai dae ba ka so a fad'a"
  Zae ce wani  abu knn suka ji inna na qwala ma Ryynt kira tayi saurin zaro tissue ta share hannun ta ta fita.
   Koda taje d'akin inna fitowar ta daga bathroom knn tana zaune kan bed tana shafa mai.
 Inna tace"sae naji kmr muhammadu ya shigo ko,dan naji kmr sallamar sa da ina bayi.
  Ryynt tace"eh ya shigo"
Inna tace"yanzu zaku tafi can gidan nasu ko kuwa?
Ban tambaye sa ba tukun yana cin abinci ne.
  To shike nn jeki.
Nan Ryynt ta juya ta koma d'akinta.
 Ta sami man na waya yana ganin ta yace da wanda yake waya bari zan kiraka anjima daga nn ya tsinke wayar ya maida aljihu.
  Ryynt tace"meyasa baka bar kun qarasa wayar ba?
   yaja hannunta ya zaunar da ita kusa dashi tare da fad'in"ina tare da mata ta ina zanyi lokacin wani can"
  Ryynt dake kallon sa tayi murmushi tare da kwantar da kanta kan kafad'ar ta sa ta shafo cikin sa tace"a qara maka abincin ko ya ishe ka?
  Yace"ya isheni zuba min fresh milk kawae nasha"
 Nan ta tashi daga kan kafad'ar sa ta zuba masa ta bashi yasha snn yasha ruwa ya zaro tissue ya share bakin sa da hannun sa Ryynt kuwa ta kwashe kwanika ta fitar dasu.
  Koda ta dawo ta same shi zae fita daga d'akin yace"ki shirya idan na dawo daga gun gaida inna sae mu tafi kinga 11 har ta gota ya fad'i hakane tare da kallon wristwatch d'in hannun sa,Ryynt tace"to"snn ya fita taje ta zaro gyale kalar kayan jikinta ta yafa tasa takalmi ta jawo jaka da wayar ta taje ta same can d'akin inna.
Ba jimawa sae gashi sun fito shida ita sae kallon ta yake tayi wacce ta fhmci tunda ta shiga d'akin inna yake kallon ta har sukayiwa inna sallama suka fito.
Har zatayi magana knn taga yaja hannun ta ya tafi da ita d'akin ta yana qoqarin cire mata mayafi tace"mk lafiya"
 Yace"har kya tambaya bayan kinga irin tsabar kyaun da kikayi, ae idan na barki kika fita kin nemi wani  ya qwace min ke,don haka nemo wasu kayan a canza shirin nn"
  D'auke da d'an murmushi a fuskarta tace"hm kaima dae da wasa kake don kasan duk duniyar nn ba wanda ya isa ya qwace maka ni sae mutuwa"
  Mohd yace"to so kike wani  ya kalla min ke ya shammace ni ,wae ma dae ya akayi keda ba kya saka gyale sae gashi kin saka yau?
   Tace"saliha ce wlh jiya ta za6ar min kaya da taji ina tunanin kayan sawa shine ta ciro min su a cikin akwatinan lefe"
Yace"to nemo hijab d'in su don gsky baza ki fita da gyalen nn ba"
  Tace"to ae babu hijab gyalen ne kawai koni da ta ciro min kayan nace bana son gyale ta duba min hijab koda ta duba babu klr kayan"
  Yace"to nemo wasu  kayan da keda hijab"
A shagwa6e tace"oh oh mk wlh ni baxan iya canje canjen nn ba kayi haquri dan Allah"
  Man yayi tsaye riqe da waist d'inshi yana qare ma fuskarta kallo.
  Nan kawae taga ya jawota zuwa jikin sa ya had'e bakin su sae tsutsar lips d'in ta yake  sae can ya janye bakin nasa yana kallon lips d'inta yakai babban yatsan sa ya shafo lips d'in nata ya duba yatsan sa yaga ba komai yayi murmushi had'e da girgiza kansa yana kallonta yace"wae ke wane irin lipstick ne haka kika sa da baya fita kanshi ne fa kawai na tsotsi lips d'inki ko xae fita don na fhmci ba qaramin kyau ya miki ba,
dmn wnn ba na fita bane sae wa ni kad'ai ya kamata ace kinyi wa kwalliya dashi.
  Ryynt tayi er dariya mae kmr murmushi tace"ai gwanda da bai fitan ba don da ka 6ata min er kwalliya ta"
  Nan Man ya harare ta da wasa yace"koh? yayi yanzun kuwa zan tsotse shi tas"
  Yana gama fad'ar haka yaje zae kai bakin sa a nata,cikin dariya tayi saurin cusa fuskarta a qirjinsa tana fad'in"yi haquri dan Allah idan ba so kake lips d'ina su kumbura ba don wlh baya da saurin fita"
  Ya d'ago fuskarta tare da jan hancinta yace"shike nan naji na barki amma yau kad'ai"
  Tayi murmushi tare da gyad'a masa kai yaja hannunta suka fito daga cikin gidan.
  Wushil man yaga kmr mutum ya fito daga  qarqashin motar shi ya wuce da sauri.
 Ya kalli Ryynt kmr zae ce wani abu sae kuma ya basar ya tafi da ita suka shiga motar ya tashi motar suka bar layin.




Billy giro😊
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```

















             🔮🔮🔮🔮
*page 80*
Basu kai koina ba sae gashi sun dawo Ryynt ta fito da sauri ta shiga cikin gida  jim kad'an ta fito riqe da wayar ta a hannun ta wacce ta manta da ita a d'akin inna.
 Taje zata bud'e gambun mota knn sae saukar ball taji tim a kan cikin ta, a tsorace ta fasa ihu ,yayinda mohd ya fito motar a fusace ya nufi yaron da ya jefo ball d'in cike da niyar kai masa mari Ryynt tayi saurin zuwa ta riqe masa hannu tace"Mk dan Allah kayi haquri yaro ne fa"
  Yace"dan ubansa ko yaro ne kan me zae jefo ball akan cikin ki ko kuma shi abinda ke cikin ki ba rayuwa bane!
  Yi haquri dae dan Allah tun da kaga bada gayya bane.
 Mohd dake kallon yaron rae 6ace yace"oya duqa ciro ball d'inka a qarqashin mota ta ko kuma wlh na taka ta na wuce"
  A tsorace yaron ya duqa ya ciro ball d'in sa zae wuce man ya bisa da ido yace"kae xo nn"
Jiki sanyaye yaron ya juya,
 mohd yace"wa na gani ya fito a qarqashin mota ta d'azun?
  Yaron ya sadda kansa qasa yace"nine"
  Mohd yace"uban me kamin a qarqashin motar to?
  Yaron yace"ball d'ina ne da ya gangara na d'akko"
  Mohd ya kalli Ryynt yace"u see kince bada gayya bane bayan wnn ne karo na biyu koma fiye dmn muna fitowa naga lokacinda ya fito a qarqashin motar da sauri ya fice shiyasa sam ban cika son barin mota na a waje ba dan irin yaran nn marassa ji sae su maka 6arna a banza,bari kaji idan na qara ganin kana ball a guraren gidan nn wlh sae nayi maganin ka,oya tafi in daina ganin ka a nn very stupid!
  Sim sim yaron ya bar gurin.
Ryynt ta kalli man tace"dan Allah ka rage yawan fad'an nn bana so wlh"
  Mohd yace"Ryynt nasan yaron  baya ji wlh ko kad'an,
 musamman yake da filin ball a cikin gidan su  banga uban me yasa ya fito yana ball a waje ba har yake qoqarin hallaka min ke da babyna ,
wlh gwara ma ace motar ce ya daka glass d'in motar ya fashe kan ya doka min ke .
 Tace" to yi haquri dae dan Allah ya wuce.
  Yayi murmushi had'e da jan hancinta yace"ni a gurina bae wuce ba sae naga lafiyar babyna tukun"
 Tayi murmushi yayinda yaja hannunta suka shiga mota yakai  hannu ya yaye rigarta yana shafa cikin yace"ya kika ji a lokacinda qwallor ta dake ki?
  Tace"naji zafin saukar ball d'in ba sosai ba na kuma tsorata don har sae da abinda ke ciki ya motsa.
 yace"da qarfi sosai ya motsa ko kuwa?
  Tace"da qarfi ba sosai ba"
  Man yayi shiru yana kallon ta can yace"Ryynt ya zama dole muje asibiti nayi scanning dmn naga lafiyar babyna"
  Ryynt tace"plz Mk ba sae ka duba ba inshaa Allah ba wata matsala"
  A natse ya girgiza kansa yace"No Ryynt abinda zaki d'auka ba matsala ba shi zae zo ya zama matsala kuma hankalina zae fi kwanciya idan na duba kiyi haquri muje kinji baza mu wani  jima ba"
  Ta gyad'a masa kai  snn yaja motor suka tafi sae asibitin shi.

Kan hanyar su ta dawowa daga asibitin ne Ryynt ke kallon man wacce gabad'aya jikinta a sanyaye tace"mk nifa na tsorata don sae naga kmr yara har uku a cikina"
  Saurin kallon ta yayi don sae da fa yace ta rufe idonta ashe ta bud'e bae sani ba,bae dai ce mata komai ba yayi d'an guntun murmushi yace"Ryynt knn kije ina da yara har uku photon ne kawae ya rarrabu"
  Ajiyar zuciya ta sauke tace"ai ni har na soma shiga tension wlh"
  Yace"tension name dan Allah ya baki babbar kyauta.
 Tace"um um wlh ni ko biyu ne bazan iya ba bare uku"
  Yace"to idan Allah ya baki fa sae kiyi yaya?
  Tace"hm nima ban sani ba amma na tabbatar cikin da kanshi zae zube kan tsananin tashin  hankalin da zan shiga"
 Mohd yayi murmushi kawae ba tare da yace komai ba yaci gaba da jan mota.

Suna isa family house basu zarce koina ba sae 6angaren iyayen sa.
   Basu sami kowa a falon ba mohd ya umarce Ryynt da ta zauna bayan ta zauna ya haura sama jim kad'an sae gashi ya fito shida mahaifiyar sa da suka qaraso Ryynt ta zame kan kujera ta russuna cike da ladabi tana gaida ta.
  Ba yabo ba fallasa mahaifiyar sa ta amsa mata har tana tamvayar ta ya hanya tace"Alhmdllh"
  Mohd yace"Abba fa ko har yayi tafiyar dan jiya da na shigo gaida shi naji yana waya kan cewa zae je abuja"
 Tace" Aa bae tafi ba tukun sae gobe yanzu haka yana d'akin shi bari naje na dubo maku shi.
 Nan ta tafi zuwa sama mohd ya kalli Ryynt wacce ke durqushe still bata koma kan kujera ta zauna ba sae zama tayi a takure nn qasa gun gefen kujera.
  Yace"Ryynt koma mana kan kujera ki zauna kin wani  takura kanki haka sae kace kinxo baqon guri"
  Tace"um um barni a nn kawai ya isa"
  Bai ce komai ba sae  hannun ta ya riqo zae maida ta kan kujera tayi saurin qwace hannun cike da jin kunya sbd Abba da ta hango tafe shida umma.
 Mohd da bai gansu ba yaje zae sake riqo hannunta tayi mai wani  kallo na alamar ga fa su Abba nn tafe suna kallon mu.
  Nan ya juya had'e da d'an sosa bayan kansa alamar jin kunya suna qarasowa ya durqusa cike da ladabi yana gaida Abba,Abba ya amsa snn ya kalli Ryynt wacce tayi qasa da kanta tana gaida shi ya amsa d'auke da murmushi a fuskar sa  yana tamvayar ta ya hanya tace"Alhmdlh"
   Bayan sun gama gaisawar ne Abba ya koma daga ciki umma ta kira mai aikin ta ta kawo musu ruwa da lemu da kuma abun motsa baki.
  Umma da kanta ta zubawa Ryynt lemu a cup ta bata ta kar6a ta samu da qyar ta kur6a kad'an ta ajiye  don gabad'aya kunyar hjyr take ji gashi sae kallon ta take.
  Kuma su biyu ne kawae zaune a falon sbd mohd ana kawo masu ruwa da lemu aka kirasa a waya ya fita.
 Hjyr mohd kuwa tana  kallon Ryynt ne sbd ganin yanda Ryynt ta canza tayi kyau klr ta ta koma kmr tashin er abuja ga natsuwa sae duk taji ta soma son Ryynt sosai a ranta,nn ta tsinkayo muryar Ryynt na tambayar Ameera fa.
  Allah sarki taga dae ko kad'an Ameera bata ta6a nuna mata so ba amma kuma har take tamvayar ta ai kuwa sae taji ta qara sonta,
 ta sakar mata murmushi tace"Ae Ameera na can gidan pretty,pretty taje da ita dmn ta samu ta riqa rage mata wani  aikin kafin hutun makarantar su ya qare.
  Ryynt da kanta ke qasa tayi d'an guntun murmushi tace"Allah sarki"
daga hk tayi shiru bata sake cewa komai ba .
  Sae ga mohd ya dawo yace"umma bari muje other parts mu gaida su"
 Tace"to sae kun dawo"
 Nan Ryynt ta tashi suka tafi.
 Sae da suka tafi d'ayan 6angaren snn suka je 6angaren su saliha.

Da murna sosai umman saliha ta tarbe su  yayinda man da Ryynt suka gaida ta ta amsa musu cikin sakin fuska tana tambayar su ya hanya suka ce Alhmdlh nn Ryynt ta wuce d'akin saliha ta bar mohd suna qara gaisawa da umman saliha.

Ryynt na shiga d'akin saliha tayi tsaye tana kallon saliha dake chat tana qyalqyatar dariya.
  Ryynt ta girgiza kanta taje ta zauna  kusa da ita tana fad'in"keda waye haka?
  Da sauri saliha ta kalli Ryynt tace"yaushe kika shigo har kika zauna ban ko ji ba?
  Ryynt tace"hm inafa zaki ji hankalin ki na gun chat.
  Saliha ta tashi zaune tare da fad'in"wlh kedai wata qawata ce er ban dariya keta sani dariya har cikina yayi ciwo wlh.
  Ryynt tayi murmushi tare da ajiye jakar hannun ta saliha da ta kafe ta da ido tace"waih  barikallah yau sae kika qara yin kyau sosai wlh har dae pink lipstick d'in nn da kika shafa kan d'an mitsilin bakin nn naki mae matuqar kyau kmr na qwace maki shi na gudu.
  Da wasa Ryynt ta harare ta had'e da turo baki tace"kin fara koh saliha?
  Saliha tace"to ae gsky na fad'a ina kika samo kalo d'in nn da na jima ina neman irinta bana samu daga dark sae mae haske sosai nake samu,
  Ryynt tace"wlh a dubai kedai na siyo wata er kit ta cosmetics ciki sae ki samu komai da kike so,kema taki na nn na siyo miki ae"
  Ihun murna saliha tayi tare da rungume Ryynt tace"kai amma wlh naji dad'i na kuma gode"
   "oyoyo Aunty!
cewar mami wacce ta shigo da gudu, Ryynt ta d'auke ta cike da murna ta d'aura ta kan qafafunta.
  Umman saliha da suka shigo tare da mami tace"Ah sauketa kar ta zunguren min d'an jika"
  Sosai Ryynt taji kunya tayi saurin sadda kanta qasa tana murmushi .
  Umman saliha da ita ma murmushin take taje zuwa sauke mami,mami ta qanqame Ryynt tace"um um mama nifa ba inda zanje tare zamu koma nida Aunty idan zata tafi"
  Umman saliha tace" mami nafa gaya miki baza ki koma ba gwanda tun wuri ki fidda ranki"
  Ryynt ta d'ago ta kalli umman saliha tace"meyasa mama?
  Umman saliha tace"Ryynt takuraku kawae zata yi dan yanzu ba d'aya bane da wancan lokacin kawae dae zan riqa barin ta tana zuwar miki ko weekend ne.
 cikin fushi mami tace"wlh mama ban so"nn ta sauka kan jikin Ryynt ta fita daga d'akin cikin kukan shagwa6a.
  Umman saliha ta bita da ido d'auke da dariya a fuskarta,Ryynt kuwa ta qwala mata kira a cewar tazo umma wasa take mata amma mami taqi dawowa.
   umman saliha ta kalli saliha da ke bin mami da kira itama, tace"kinga tashi je kawo ma Ryynt lemu da ruwa ae kinsan mami in ta fara fushi ba rarrashi take ji ba dan kanta zata sauko ta dawo.
  Ba musu saliha ta tashi ta fita umman saliha ta kalli Ryynt tace" gobe ne zaki koma koh?
  Ryynt tace"eh inshaa Allah mama"
 Umman saliha tace"dama wasu turarukka ne nasa aka sake had'a miki  dan nasan wad'an can sun isa qarewa koh?
 Tace"Aa mama akwae saura,
 Tace" to indae kin tashi zan baki ki tafi dasu .
  Cike da jin dad'i Ryynt ta mata godiya don sosai take son turarukkan har dae yanda ta fahimci  mohd na jin dad'in qamshin turarukkan ba kad'an ba.


8:30pm
Sae a lokacin zasu koma.
 Mohd ya kalli Ryynt wacce ta shigo mota fuskar ta d'auke da damuwa yayi shiru yana kallonta shidai a sanin sa hjyr sa ta fara sake mata bare yayi tunanin ko ita ce ta mata wani  abu bare kuma duk yinin nn a 6angaren su saliha tayi shi.
  Hannun ta ya riqo ta kalle sa yace"me aka miki?
 Cikin muryar kuka tace"umman saliha ce tace wae baza ta bar mami ta koma gurina ba sae dae kawae ta riqa zuwar min weekend da farko na d'auka wasa take ashe da gske take yi yanzu haka mami na can sae kuka take"
  Mohd yace"to ae sae gobe ne ko zaki koma koh?
  Tace"eh shine da zan fito nace gobe a shirya wa mami kayanta idan zan koma zan biyo mu d'auke ta a nn take gazgata min cewa itafa da gaske  ne mami bazata koma ba"
  Yace"meyasa ko kin ta6a yiwa mami wani  abu ne da bata ji dad'in sa ba?
 Tace"Aa ba haka bane wae zata takura mu idan ta koma"
  Man yace "wace irin takurawa kuma?
 sae kuma yayi shiru yana nazari can yace"haka ne Ryynt tayi tunani kuma"
  Da sauri Ryynt ta kalle sa tace"kmr ya nifa banga wani  takurawa ba tunda ba d'aki d'aya muke zaune da kai ba"
  Yace"to ae rnr dutyn ki ne magana dmn dole a d'akina zaki kwana,
 Kinga ba zae yiyu ki barta ita kad'ai a d'akin ki ta kwana ba koh.
  Ryynt tace"to ae sae naje da ita mu kwana a d'akin naka mana"
   Hm Ryynt knn wa ya gaya miki ana zuwa turakar miji da yaro.
  Idon ta tap da qwallah tace"ba wani  nn kai ma dae baka so ta koma d'in na fhmce ka"
  Ryynt ba haka bane ki fhmce ni.....haka ne mana.
  Ta qarashe mgnr ne cike da son fashewa da kuka hkn yasa yayi shiru bae sake ce mata komai ba yaja motar suka tafi.

  Suna isowa gidan inna cikin fushi Ryynt ta fita mota ta wuce wacce bata zarce koina ba sae d'akin ta.
  Mohd kuwa d'akin inna ya nufa d'auke da sallama abakin shi inna ta amsa sallama washe da baki tace"kun dawo?
  Yace"eh inna mun dawo"
  Nan ya nemi guri kan sofa ya zauna inna tace"Ryyh fa?
 Yace"tana d'akinta  rigima take ji yau"
  Inna tace"rigimar me kuma ko so tayi ta kwana a can ka hanata?
  Yace"Aa inna zancen komawar mami gurinta ne nn yayi wa inna bayanin komai wacce tayi shiru snn tace"to muhamnadu gsky fa kasan xama irin gidan ka ba d'an yaron da ke tayaka xama ba dad'i ne dashi ba,tunda kai dae ba zama kakeyi ba snn qarin abun ma kasan Ryynt bata iya bacci ita kad'ae a d'aki tunda kaga ba ita kad'ai ce matar ka ba da za'a ce kullum kuna tare don haka zancen rashin komawar mami a gurinta bae taso ba,
 kawae abinda naga yafi shine zan samar mata er yarinya mae aiki da zata riqa kwana  tare da mami idan ita  tana naka d'akin ko kuwa hakan bai fi ba,don gsky bazan so a takura er marainiyar Allah ba bayan akwae yanda za'ayi.
  Mohd ya nisa yace"hakane inna zan sami umman mami sae muyi magana"
 Inna ta washe baki tace"to shike nn d'an albarka ko me tace sae kazo ka gaya min ni kuma sae nasa baaba hurera ta samo mata er yarinya mae hnkli da natsuwa,dan hk tashi maza je lallaso min ita.
  Mohd ya tashi d'auke da murmushi ya tafi d'akin Ryynt ya same ta zaune kan bed ta had'e kai da guiwa sae kuka take.
  Yaje ya zauna gab da ita tare da janyo ta zuwa jikin sa bata jira me zae ce ba ta zare jikin ta daga nashi  ta sauka kan gadon ta shigewar ta bathroom ta rufe.

Mohd bae bita a bathroom d'in ba ya koma d'akin inna tace"ya naga har ka dawo?
 Yace"inna mutuniyar taki tayi fushi da yawa inaga shiga bata ko tsaya ta saurare ni ba ta shigewar bathroom ta rufe"
  Inna tace"muhammadu nasan halinka wata qil kan hanya fad'a ka mata sosai koh?
  Haba inna meye abin fad'a a ciki sam wlh ni ban mata fad'a ba.
  Inna tace"to jeka abinka ni naje na rarrashe ta"
   Yace"to inna zan tafi d'in amma zan dawo zuwa an jima"
 Tace"to sae ka dawo"
  Daga haka ya tashi ya fita.
Inna kuwa ta tashi ta nufi d'akin Ryynt .
  Ryynt na cikin bathroom zaune ta had'e kai da guiwa tana ci gaba da kukanta taji muryar inna ta kira sunan ta,da sauri ta share hawayen fuskarta tace"Na'am inna"
  Inna tace"yi haquri bud'e qofa fito muyi magana kinji Ryynh"
  Ba musu Ryynt ta tashi ta bud'e qofar ta fito.
  Inna taja hannunta suka je kan bed suka zauna ta kalli Ryynt da kulawa ta dafa kanta tace"kwantar da hankalin ki Ryynh indae mami ce tare zaku koma kinji"
 Ryynt ta gyad'a kanta snn inna tayi mata bayanin duk yanda sukayi da mohd  sosai taji dad'i har ma tayiwa inna godiya.
Nan inna ta tashi ta koma d'akinta Ryynt kuma ta rage kayan jikiñta ta fad'a bathroom zuwa wanka.
  Ta kwashe kusan awa d'aya kafin take fitowa d'aure da towel.
  Bayan ta shafa Vaseline ta d'auko turarukkan ta na jiki ta shafe jikinta dasu tsaf sae zuba qamshi take snn ta nufi wardrobe dmn ciro kayan bacci sae jin tayi an rungumo ta,
 a d'an tsorace ta juya taga mohd ne ta lumshe ido had'e da rungume shi murya can ciki tace"mk kaine har kasa naji tsoro"
  Mohd dake shinshinar qamshin jikin ta ya shafo bayanta a hnkli yace"am sorry"
  Nan ya qara qanqameta a jikin sa yana ci gaba da shaqar qamshin turaren ta kamar yanda itama take shaqar nashi suka jima a haka sae can ya d'ago yakai  hannu a cikin wardrobe ya ciro kayan baccin da yaga zata ciro yaje da ita kan bed suka zauna yakai  hannu zae yaye mata towel d'in jikinta dmn saka mata kayan baccin Ryynt tace"um um Mk kar inna tazo ta same mu bari naje bathroom na shirya"
  Ba musu ya bata kayan taje bathroom ta saka ta fito ta same shi yayi kwance yana fuskantar silin idanuwan sa a rufe kmr mae bacci.
  Taje a hnkli ta zauna kusa dashi nn ya bud'e idanun sa sae kallonta yake tana kallon shi can ya sauke idon sa akan cikinta ya jawota zuwa jikin sa yana shafa cikin.
  A hnkli Ryynt ta tashi daga kan jikin sa ta zauna nn mohd ya tashi zaune yana kallon ta yace"Ryynt wae baki daina fushi dani bane duk da inna ta miki bayani"
  A hankali ta riqo hannun sa tana kallon sa tace"No Mk ba haka bane nifa ina gudun kar inna ta same mu ne"
  Sae da ya janyo ta ya kwantar kan qirjinsa snn yace"inna fa tasan ina d'akin nn bazata shigo haka kawae ba tunda tasan mata da miji ta ajiye"
  Ryynt tace"to ai dare nayi ka tafi gida"
  Yace"korata ma kikeyi to ae ni a nn zan kwana"
  Ryynt ta kalle sa d'auke da murmushi tace"ae nasan da wasa kake"
  Yace"ni da gaske nake dan yau kin tsakaloni da yawa bazan iya bacci ba ke ba"
  Tace"me na maka"
Yace"ba ke bace kika zauna kina shafa turarukka ba towel a jikin ki"
  Tayi saurin rufe fuskarta da tafin hannunta tace"haba MK ya zaka tsaya to kana kallona"
  Yace"to sae kar na kalla nida matata kuma ae laifin ki ne da kika wani sakankance ba kaya a jikin ki kina aikin gabanki"
  Cikin muryar kuka tace"to mutum da d'akin shi kuma har ya rufe qofa uhm uhm,wlh kuma ae ma duk laifin ka ne da ka koya min haka"
  Nan ta d'auki pillow zata doka mai mohd ya riqe pillown yana dariya rungume da ita a jikin sa taje zuwa tashi ya qara rungume ta yace"nifa wlh da wasa nake miki ban ganki ba qamshin turaren ki ne kawai ya nemi rikita ni"
  Tace"to meyasa kace ka ganni?
Yace"sbd na koya maki na kuma san zakiyi"
 A shagwa6e ta bugo qirjin sa tace"shine kasa na tashi yin kuka da gaske"
   Yace"kan me to ni ba mijinki bane dan na ganki sae ya zamo wani  abu"
  Tace"to ai ba dad'i ne mutum yana yin abu bae san ana kallon shi ba"
 Yace"to yi haquri bari inga babyna na tafi"
 Bata ce komai ba sae kallon sa take ya yaye rigar baccinta ya shafo cikin tare da d'aura masa kiss,ya tafi a hnkli kan qirjinta zae yaye rigar tayi saurin hanashi ya kalle ta yace"ayi haka an barni naga baby amma kuma a hanamin ganin abincin baby"
  Ya qarashe mgnr ne d'auke da murmushi a fuskar sa,itama cikin murmushi tace"eh mana ayi sbd baby naka ne abincin baby kuma nawa ne da samun ganin sa sae an yanka ticket"
  Yace"ok ai kuwa yanzun nn zan yanka ticket nn yaje zuwa had'e bakin su tayi saurin tashi tana ja baya tana dariya tace"nidai dan Allah ka tafi dare nayi"
    Mohd da ya miqe tsaye yace"to zo mana muyi sae da safe"
  Tace"me zaka min in nazo?
Yace"zanyi pecking d'inki ne kawae kema sae kimin na tafi"
  Ba musu taje ya janyo ta zuwa jikin sa ya kai bakinsa a hnkli kan lips d'inta ya d'aura mata kiss itama ta mishi snn suka d'ago suna kallon juna ta cikin ido mohd yace"gobe da safe ki shirya xanzo mu koma gidan mu"
  Tace"plz Mk ka bari sae dare dan Allah sbd gobe da safe so nake na cire en tsarabar kowa na aika mishi"
    Yace"To ae ba wani  aiki bane wnn zaki gama shi in time"
Sosai ta marairaice fuska tace"nidae dan Allah ka bari sae dare guraren bayan isha'i haka"
  Yace" to naji Allah ya kaimu"
Ya fad'i hakane tare da d'aura mata kiss kan goshi snn ya mata bye bye ya fita.



Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```

















             🔮🔮🔮🔮
*page 81*
washe gari guraren 11am man ne ya gama shirin sa tsaf na zuwa asibiti riqe da briefcase a hannun sa zae fito sae ga malika ta shigo d'akin cikin shirin ta itama fuskar ta a d'aure ta kalle sa tace"fita nake son nayi"
  "Kifi ruwa gudu"
Shine kawae abinda yace ya ra6a ta gefenta ya wuce ta bisa da kallo har ya 6ace ma ganin ta snn ta fito bayan har ya fita gidan snn itama taja motar ta ta fita.
  Bata zarce koina ba sae gidan fa'iza wacce dama ta san da zuwanta taja hannun malika tace"zo muje daga ciki"
  Bayan sun shiga ciki sun zauna fa'iza ke cewa" malika matsala ta dake ba kya jin shawara wlh da nice ya ma haka ko shi kad'ai ne d'a namiji a duniya na yafe sa har abada amm ke wae ace har ya dubi tsabar idon ki ya gaya miki cewa kin fita a ranshi kuma kikayi sake da baki kika kasa d'aukar wani mataki sbd kawae kina gudun kar ya sake ki,mutumin da ke kad'ai ke haukar son shi,shi ya daina  sonki meye amfanin rayuwa dashi to.
 Malika tace"hm kefa ya fad'a ne kawae sbd zafin zuciya dmn tsawon shekarun da muka kwashe muna soyayya ba zae ta6a iya cire ni a ransa zama d'aya ba ya fad'a kawai dmn yaji dad'in bakin sa amma qarya yake yace na fita a ranshi.
  faiza tace"To in hkne meyasa bazaki bi shawarar da na baki ba.
 Wato fa'iza wlh ina tsoro sbd nasan halin my man yanda ya d'auki son haifuwa ya d'aura a ransa ba kad'an bane da zarar nayi kuskuren ta6a lafiyar wnn abar wlh zae iya sakina komai sonda yake min kuwa.
  Fa'iza tace"hm ai ko in yasan wata bae san wata ba matso kiji"
    Nan fa'iza taje saitin kunnen malika ta rad'a mata magana.
   Daga haka suka kwashe da dariya suka lale malika tace"gud idea shiyasa nake son yin shawara dake wlh"
   Fa'iza tace"hm bari kedai Allah ne ya ceci wnn abar da yasa bani bace ke ".
    Malika tace"ko ni d'in ma ae ba dad'i na take ji ba wlh don ban ta6a d'aga qafa ba.
 
         ****
Da dare bayan isha'i  Ryynt ce cikin kwalliya tayi shirin ta tsaf cikin babbar super Holland riga da rafa zane da sukayi matuqar kyau a jikinta tana sanye da gold sarqa da en kunnen ta masu kyau da aka saka a cikin lefen ta sae zuba qamshi take.
  Ta d'auki jakarta da gyale kalar kayanta ta fito falo ta sami jikar baaba hurera zaune a falon wacce itace  yarinyar da baaba hurera ta samo mata mai suna alawiyya tana zaune qasa kusa da gefen doguwar kujera ga tv kunne amma har ta soma bacci tana gyangyad'i rungume da jakar tufafinta a hannun ta.
 "Allah sarki alawiyya  har kin gaji da jira kin soma bacci"
Cewar Ryynt wacce ta nufi d'akin inna.

Man da tuni yazo yana jiranta tana shiga d'akin ya kafe ta da ido sae kallonta yake don sosai tayi kyau ba kad'an ba.
     Hannun ta yaje riqowa xae zaunar da ita kusa dashi bata barshi ba taje gefen inna ta zauna tare da dalla masa harara da wasa,
 inna dake kallon su tayi murmushi cike da jin dad'in ganin wae yau Muhammadu ne da Ryynh ke shiri haka abin sha'awa.
   Nan ta sasu gaba ta d'anyi musu hud'uba snn suka fito falo aka tashi alawiyya inna ta rako su har mota tana tsaye suka tashi motar snn ta juya ta koma daga ciki.
  Tafe suke amma gabad'aya jikin Ryynt a sanyaye don haka kawae taji kewar inna sosai.
  Dukkan su suka yi shiru kmr ba kowa har suka isa family house suka d'auko mami.

 Da suka iso gidan mohd tun daga kan harabar gidan Ryynt tasan cewa an qara qaya ta gidan sbd gabad'aya kujerun zama na shan iska an canza ba wad'an da ta sani bane haka da suka zo kan falo kaf komai yasa an sake sauya wa akan wad'anda malika ta farfasa kmr ma ba wata 6arna da ta ta6a faruwa a falon don an tsarashi matuqa Ryynt sae kallon falon take abin sha'awa kmr wata aljànnar duniya komai fari tas sae qawar da akayi da gold .
Da suka je d'akinta ma hakane Fari n gold duk an canza komai kmr d'akin turawa.
  Dama tun da rana man yazo da kayanta kuma ta samu ya tsara mata komai sae akwatin mami ta kar6a dake hannun sa tasa a wardrobe ya bata makullin d'akin da ke kusa da ita wato inda alawiyya zata zauna wanda dama d'akin don baqi akayi shi.
  Sae da ta kar6i makullin yace"idan kin kaita d'akin kizo falo ina son zanyi magana da kune keda malika"
  Ryynt tace"to"
Snn ya fita ita kuma taje takai alawiyya a masaukinta ta d'an nuna mata yanda zatayi amfani da abubuwa ta fito taje downstairs ta samu har ya kiro malika taje tayi zaune ya soma yi musu bayanin tsari da kuma irin zaman lafiyan da yake so ayi a gidan shi baya son wani tashin hankali ko wani makirci da qulle qulle byn nn ya raba musu kwana wato two two days da kowace zata riqa yi a nata duty snn yace idan da akwae mai magana a cikin su sae tayi.
    kowaccen su tayi shiru sae can Ryynt dake zaune qasa kusa da gefen kujera tace ita dae bata da abin cewa dmn tsarin da yayi dae dae ne a gurinta nn ya kalli malika dake zaune kan kujera kusa da shi wacce kmr ma bada su yake zancen ba ta wani  d'aura qafa kan qafa tana chat yayinda take tauna chewing gum a bakinta.
  Yace"kefa?
  Ba tare da ta kalle sa ba tace"bani da abin cewa"
 Daga haka ta tashi ta bar gurin ba tare da taji me zae ce ba.
  Bae damu ba sae kallon Ryynt yayi d'auke da murmushi a fuskar sa ya sauko kan kujera ya zauna qasa kusa da ita yakai  hannu ya tallabo fuskarta yana kallonta yace"kin san dae cewa dutyn ki ne yau don haka je ki sallami alawiyya da mami   kizo ina jiranki a d'aki"
   Ryynt tayi d'an guntun murmushi tare da gyad'a masa kai.
  Nan suka tashi mohd ya nufi 6angaren d'akin sa itama haka.
  Koda taje ta sami mami kwance akan bed tayi bacci.
  Ta nufi wardrobe ta bud'e ta ciro farar rigar baccin ta irin wad'an da take sawa a mumbae sae dai wnn tana da er sama da zata rufe mata jikinta har qasa.
  Bayan ta cire kayan jikinta sae da ta qara shafe koina na jikinta da turare snn ta saka kayan baccinta ,
ta cire wa mami kayan jikinta ta saka mata na bacci ta d'auke ta ta kaita d'akin alawiyya ta rufo musu d'akin ta fito.

 koda tazo zata shiga d'akin mohd sae ga malika itama zata shiga da mamaki ta kalli Ryynt tace"jarababbiya me kuma zaki shiga yi a d'akin shi ke  bada duty ba ko kuma nn d'akin uwarki ne da kike shiga duk lokacinda kika ga dama"

  Man dake cikin d'akin shi yana kallon su ta ta camera setting a jikin TV ya fito a fusace yana kallon malika yace"wace irin magana ce wnn ke har  kinada bakin kirama wani  jarababbe wlh mind ur tongue kar na qara jin kin zage ta idan har ba so kike na sa6a miki ba and 6ace a nn in daina ganin ki da wani  shirmen zancen ki can"
  Malika tace"wlh ba inda zanje sae naji dan ubanta kan me zata fara duty kafin ni"
  Yace"bana son raini su kwana biyun da kikayi kina duty fa!
  Tace"yaushe ne ka raba mana duty da har na kwana biyu ina yi,ko kuma kwana biyun da suka wuce kulawar ka ka bani da har za kace nayi nawa duty.
  wani irin mugun kallo ya mata zae yi magana Ryynt ta katse  shi da cewa"No barta she is ryt"
  Daga haka ta juya ta bar gurin malika ta bita da kallo le6ace da baki ita yaushe ne ta fara bokon da zata wani  fara sako turanci a zancenta.
  Tana qisa hkne a cikin ranta mohd kuwa  6acin rae bae bar ya tsaya ba ya koma daga ciki kafin malika ke binsa daga baya.
  Ryynt kuwa d'akin alawiyya taje ta d'auko mami ta maida ta d'akinta tayi zaune kan bed tare da share qwallar da suka zubo mata sbd sosai taji ciwon zagin iyayenta da malika tayi had'i da jarababbiyar da ta kirata dashi.
  Nan tayi addu'a ta kwanta had'e da kashe musu wutar d'akin.

Guraren qarfe goma sha biyu sae ga man ya shigo d'akin ya sami Ryynt duk tayi zufa sbd d'akin d'if ba AC nan ya kunna musu Ac snn yaje a hnkli ya cire mata er samar rigar baccinta sae kallon fuskar ta yake dake matuqar bashi sha'awa idan tana bacci yayinda yake ta faman shafa cikinta  yaje a hnkli kan goshinta ya d'aura mata kiss snn ya tashi ya fita ya bar d'akin wanda koda ya fita idon Ryynt na kansa sbd taji lokacinda ya shigo sae tayi kmr bata ji sa ba.


Washe gari tun da asuba sae da yaje ya tashe ta snn ya wuce masallaci ita kuma bayan ta tashi tayi arwala taje ta tashi alawiyya.

 Guraren qarfe goma ya sami Ryynt cikin kwalliyar ta sae zuba qamshi take kmr wacce zata fita anguwa.
   Yayi tsaye jingine a bakin qofa sae kallonta yake cike da so ,
Ryynt dake zaune gun dressing mirror tana qara gyara fuskarta ta hango shi ta jikin mirror tana kallo ya qaraso ya kwanta kan bayanta a hnkli ya rungume ta tare da d'aura mata peck gefen fuska suna masu kallon junan d'auke da murmushi ta jikin mirror yace"kinyi kyau sosai my Ryynt"
   A hnkli ta furta "nagode"
 Snn ta mishi ina kwana byn ya amsa gaisuwar ne yace"ya  akayi bayan kinsan jiya na gaya muku a tare za'a riqa cin abinci amma sae kika sa kuku ya kawo maki naki kika iza mami ita kad'ai.
  Tace"Aa ae alawiyya nasa ya kaiwa abincin rashin fitowa na kuma ban kammala shiryawa bane sae yanzun"
   Yace"oh sorry ae na d'auka ko kinyi fishi dani ne har na fara tunanin yanda zan bada haquri"
    Tace"kan me zanyi fushi da kai?
 Yace"abar zancen kawai tashi muje kar yunwa ta illata min ke da babyna nn ta tashi suka fito suna tafe mohd ke cewa"hln dae tsarin gidan nn da aka sauya bai maki ba?
  Ta kalle sa tace"Allah yayi min kyau sosai me ka gani?
  Yace"gani nayi tun jiya baki ce komai ba har yau"
  Tace"hm ae tsarin kyawon sa ne ma yasa na kasa cewa komai amma cikin zuciyata wlh sae yaba tsarin gidan nake sae dae nace Allah ya qara maka bud'i"
  Mohd yace"Amin"
Dai dae sun qaraso gun dining kowanen su yaja kujera ya zauna suka soma cin abinci malika dake kusa da man taje kan jikin sa ta zauna sae wani iyayi take tana ciyadda shi don kawae Ryynt ta gani taji haushi ,Ryynt kuwa yi tayi tamkar ma bata san da zamanta a gurin ba sae cin abincin ta take haushin ta d'aya mami dake gurin tana fuskantar su wacce bae kamata tana kallon irin abubuwan nn ba.

Sry 4 dis one banji dad'i bane da qyar ma nayi wnn.

Billy giro😊
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```

















             🔮🔮🔮🔮
*page 82*
 Cikin hikima da dabara mohd ya janye malika daga kan jikin sa ya soma ciyadda kanshi sbd ya fahimci tana yi ne kawae don ta 6ata ran Ryynt wacce yaji dad'in ganin yanda ta nuna ko oho duk da yasan dole a ranta xata ji wani  abu.
  Suna kammala cin abincin Mohd yakai hannu zae d'auki briefcase d'insa dake ajiye gefe malika ta rigashi d'auka ta rataya jakar ta tafi dashi rungume a jikin ta sae kwarkwasa take still Ryynt bata bi ta kanta ba sae hannun mami taja suka tafi d'aki.


Da dare bayan isha'i Ryynt ce zaune a d'akin ta tana koyarda su Alawiyya da mami karatun qur'ani yanda ake fitar da harafi da komai su kuma suna saurarenta idan ta gama su karanto inda duk sukayi kuren fitar da harafi ta gyara musu.
   Tsawon lokaci Man na tsaye a bakin qofar d'akin yana sauraren yanda qira'ar Ryynt ke  shiga kunnen sa mai dad'i sae duk ya qara jin sonta a ransa yana kuma jin shi kam ya gama yin sa'ar uwar 'ya'yansa a duniya.
    Gyaran murya yayi had'e da yin sallama Ryynt ta kai aya snn ta amsa masa sallama tana mai kallon sa sae murmushi yake mata har ya qaraso gurin su yazo gab da ita ya zauna nn qasa kan dardaumar sallah inda take zaune akai nn mami da alawiyya suka gaida shi, ya amsa musu yayinda  alawiyya taja hannun mami suka fita.
  Ryynt ta gaida shi cikin sakin fuska,
Shima fuskar sa a sake ya amsa mata had'e da riqo hannun ta yana mae kallon fuskarta yace"karatun ki da dad'i Ryynt?
    Ryynt tayi murmushi tace"uhm zolaya koh?
A hnkli yaja hancinta yace"ba wani nn aikin san gaskiya na fad'a,don haka yau sae kin koya min qira'ar nn taki mae dad'i.
    Ya fad'i hakane tare da janyo ta zuwa jikinsa ya d'auki qur'anin da ke ajiye kusa da ita ya bud'e,
 Yace"oya karanta min ina jin ki"
  Tace"hm Mk knn ni bance ka koya min taka qira'ar ba sae kai"

  Yace"yaushe kika ta6a jin karatuna da zaki ce haka"
  Tace"a mumbae mana idan muna sllr asuba"
  Yayi murmushi kawae dmn haqiqanin gaskiya shi kaina yasan karatun sa nada dad'i sosai amma na Ryynt dabanne da zaka ji kmr kar ta daina idan tana yi dmn har wata irin natsuwa mutum ke jin kansa a ciki.
 Yace"karanta min to ko aya biyar ne inji kinji"
   Tasan da gaske yake zancen hkn yasa bata sa wasa ba ta kalli qur'ani ta fara karanta wa mohd yayi tsit had'e da lumshe ido yana saurarenta har sae da yaji ta tsaya snn ya bud'e ido, Ryynt tace"bacci kake ji?
Mohd dake kallon ta cike da so yace"bacci jin dad'in karatun ki ba"
 Ya fad'i hakane tare da rufe qur'ani ya ajiye ya riqo hannun ta yace"ya naji jikin naki da kamar zafi?
  Ryynt tayi shiru dan ita kanta bata san me ke damunta ba kawae dae taji jikin nata nayin zafi.
 Mohd yace"kinyi shiru gaya min baki da lafiya ne"
  Tace"lafiyata qalau"
  ya shafo cikinta yace"babyna fa?
 Tace"shima haka"
   Yace"that's gud bari naje na d'an watsa ruwa bcs dawowa ta knn nace bari nazo na ganki tukun"

 Tace"ba dae tun fitar ka ta safe ba"
  Yace"eh wlh aiki ne ya riqe ni"
  Tace"eyyah sannu ni na d'auka ko ka dawo ba kai dae sami fitowa bane"
  yace"inafa aiki bae bar na dawo ba yanzu gabad'aya jikina ma sae ciwo yake min ga kuma bacci da nake ji sosai"
  Ryynt tace"idan ka watsa ruwa mana sae kasha magani koda zaka tashi jikin naka ya sake maka ae koh"
  Hakane my ryynt bari na tashi  naje.
  Nan ya tashi ya fita Ryynt ta bisa da kallo har ya fita snn taje ta kirawo mami da alawiyya suka ci gaba da karatun su.

 Bayan sun gama karatun ne alawiyya ta tafi d'akinta Ryynt kuwa tayi wa mami wanka ta mata shirin bacci snn itama taje tayi wanka wacce koda ta fito tuni mami tayi bacci hkn yasa tana gama shirinta na bacci itama ta kwanta tare da kashe musu wutar d'akin.

Bayan har bacci ya kwashi Ryynt mohd ya shigo d'akin wanda yana ta6a jikinta yaji ya qara zafi fiye da yanda yaji sa a d'azun.
  A hnkli ya zauna kan bedside drawer yana shafa goshin ta da yaji yafi koina zafi a jikinta sae kallonta yake yana ji kmr ya ta she ta ya bata magani sae dae kuma baya son farkadda ita hkn yasa ya tashi ya fita.

Guraren 11 sae gashi kuma ya kasa haquri ya dawo riqe da ledar magunguna a hannun shi da kuma gorar ruwa had'e da glass cup.
 A nn tsayen da yake ya ajiye magungunan kan bedside drawer ya bud'e gorar ruwa ya soma tsiyaya ruwa a glass cup yana cikin hakane yaji kmr motsi tafe a bayan shi juyawar da zae yi ne glass cup ya qwace mai ya fad'i ya fashe ,qarar fashewar glass cup d'in ne yasa Ryynt ta tashi a firgice zata fasa ihu mohd yayi saurin rufe mata baki ya janyota zuwa jikin sa sae duk ta qara rud'ewa tana qoqarin qwatar kanta nn mohd yaje saitin kunnen ta yace"am sorry Ryynt nine"
  Ajiyar zuciya ta fitar mae qarfi tare da qara qanqame shi sae faman sauke numfashi take kmr wacce tayi gudu sosai.
  Mohd kuwa sae shafa bayanta yake a hnkli nn kawae ya soma jin saukar hawayen ta a qirjinsa yayi saurin d'ago fuskarta yana share mata hawayen yana fad'in "yi haquri na tsorata ki da yawa koh"
  A hnkli ta koma kan qirjin sa ta kwanta murya can qasa tace" kaina ke ciwo kuma abu ya shige min a qafa"
   Nan ya kai hannu ya kunna wutar d'akin ya riqo qafar ta zae cire mata glass d'in da ta taka tayi saurin riqe masa hannu cikin murya mae kama da ta kuka tace"zan cire da kaina"
  Yace"yi haquri bari na cire maki kinji bana son kije baki cire da kyau ba ki bar saura a jikin ki"
   Ba yanda ta iya ta gyada masa kai had'e da 6oye fuskarta a qirjin sa shi kuma ya kai hannu cikin hikima da dabara ya cire mata glass d'in a hnkli ba tare da ya karye a jikinta ba snn ya zaro farin handkerchief d'insa ya d'aure mata qafar sbd jinin da ke fitowa.
   Sae a snn Ryynt ta d'ago daga kan qirjin sa tana share hawayen da ke kan fuskarta sbd kuka tayi a lokacin da yake cire mata glass.
    Mohd ya sake maida ta kan qirjin nasa yakai hannu yana shafa bayanta had'e da yi mata sannu ita kuma ta lafe sosai tana qoqarin komawa bacci ya d'ago ta  yace"kar kiyi bacci bari kisha magani tukun kinji"
  Ba musu ta gyad'a masa kai shi kuma ya jawo ledar magunguna ya 6alla mata ya bata tasha daga nn ta koma abinta kan bed ta kwanta mohd kuwa na durqushe kan guiwoyinsa a gefen gadon yana shafa goshinta tana kallon sa yace"daga kanki ba inda ke maki ciwo dae koh ?
  Tace"eh"
Yace"to yunwa fa ba kya ji?
Tace"um um"
Ta fad'i hakane tare da rufe idanun ta a hnkli
Shi kuma daga haka bae sake cewa komai ba sae hannun sa da ya kai kan cikinta yana shafawa har tayi bacci snn ya tashi daga durqushen da yake ya gyarawa mami kwanciyarta yasa blanket ya rufa musu jikin su.
  Ya kwashe glass cup d'in da ya fashe yasa a dustbin ya goge gurin snn ya kashe musu wutar d'akin ya fita yaje d'akin sa wanda da shigar sa yayi tsaye idonsa akan malika da yaga kmr yanzu ta kwanta don ba ma yanda ya barta ba ya ganta nn dae ya basar ya kwanta had'e da kashe bedside lamp.


washe gari tun da asuba sae da yaje d'akin Ryynt ya tashe ta ta miqe tana d'an d'ingishi ta nufi bathroom mohd dake kallonta sae duk bae ji dad'i ba haka dae ya fita ya tafi zuwa masallaci.


Yana dawowa daga masallaci bae zarce koina ba sae d'akin Ryynt ya same ta zaune kan darduma riqe da qur'ani a hannun ta ta bud'e zata fara karatu.
  Tana ganin sa ta rufe qur'ani tace"barka da asuba ka tashi lafiya?
  Yace"lafiya lau my Ryynt ya kan naki ya daina maki ciwo?
  Tace"Alhmdlh  gabad'aya ya daina min ciwo"
 Yace"mashaa Allah amma kuma qafar ki na damun ki sosai koh, dan naga har ba iya taka ta da kyau"
  Tace"eh amma ba wani  zafi sosai kmr kar nayi arwala ma sae naji ta sake min ba kmr lokacinda ka tashe ni ba"
  Tana mgnr ne yayinda mohd ya riqo kafarta yana dubawa ya tashi tare da fad'in "ina zuwa"
  Ya fita bae wani  jima ba ya dawo riqe da wani  magani ya shafa mata a qafa snn yace"bari na barki kiyi karatun ki koh"
    Bata ce komai ba sae d'an guntun murmushi da tayi ta bishi da ido har ya fita.

 Da dare guraren qarfe tara da rabi Ryynt ce d'aure da towel iya cinya tana neman kayan baccin da zata saka sae ga mohd ya shigo d'akin d'auke da sallama a bakin sa Ryynt ta kalle sa snn ta amsa sallamar bae qaraso ba yayi tsaye kmr mae fushi yana kallonta tace"yi haquri yanzun nn gani nn zowa kayan bacci kawae zan saka.
 Bae ce komai ba har sae da ya qarosa gurinta ya rungumo ta ta baya bakin sa saitin kunnen ta yace"na qagu da yawa Ryynt amma kuma ke sae jamin aji kike kmr nayi miki wani  laifin "
  Tace" ni baka min laifin komai ba"
   To amma shine kika bar ni tun d'azun inata faman jiranki.
  Tace"yi haquri to za6a min kayan baccin da zan saka sae mu tafi"
   Nan ya ciro mata wata er fincikar riga pink mae kyau wacce ita ta siyo abar ta da suka je dubai,
 ya kai hannu zae zare mata towel tayi saurin  riqewa ta kar6i rigar sae wani  murmushi take tana kallon sa tace "bari naje bathroom na shirya"
   Mohd yace"hm jeki yau naga qarewar 6oye min jiki da kike don yau bazan ma kashe wutar d'akina ba"
  Tayi er dariya tace"da wasa kake kaima nn ta wuce bathroom ta sako rigar ta fito a yangace ta kama gefen rigar ta tsaya tace"ya ka gani?
 Mohd da ya qaraso gurinta ya rungumota tare da d'aura mata kiss kan goshi yace"sosai my Ryynt kinyi kyau"
  Kamar da shagwa6a ta kalle sa tace"uhm to rigar fa baka ce na iya za6e ba"
  Sae da yaja hancinta d'auke da damurmshi yace"sosai kin iya za6e my Ryynt kuma rigar tayi miki kyau sosai"
    Tace"um um fa"
Yace"Allah kuwa"
 Tace"nagode bari na saka hijab to"
  Yace "kema dae da wasa kike"
Nan ya d'auke ta cak zae fito da ita malika da tun d'azun take la6e a bakin qofa tana kallon su tayi saurin barin gurin.
Ryynt tace"wlh aa da gske nake rigar bata fita ka sani har dae da safe idan zan fito"
  Ya sauke ta tare da fad'in "to naji je sako hijabin muje"
  Nan taje ta saka hijabin suka fito mohd na rungume da ita a jikin sa har suka isa d'akin shi.

 Washe gari guraren qarfe goma na safe Ryynt ce taci kwalliya abinta cikin wata atamfa riga da skirt da sukayi d'as a jikinta tayi d'aurin d'an kwalinta mae kyau tana rataye da briefcase d'in mohd dake rungume da ita a jikin sa yana sanye da milk suit dukkan sunyi kyau sae zuba qamshi suke sun fito daga d'akin shi suka wuce malika dake zaune a falo.
 Suna kaiwa qofar fita falon mohd yayi tsaye cike da murmushi yana kallon Ryynt yace"my ryynt ba sae kin fita har waje ba dmn bana so ki wahala kawo jakar koma abinki kije ki kwanta ki huta kinji"
  Ryynt ta lumshe ido had'e da sakar masa lallausan murmushi ta miqa masa jakar ya kar6a tare da d'aura mata kiss kan goshi snn kuma yaje  kan cikinta ya mata ya d'ago tare da fad'in"sae na dawo"
bye ta mishi snn tace"Allah ya tsare min kai"
 Sae da yace"amin"snn ya fita Ryynt ta
juya zata tafi d'akinta sae malika ta gani tsaye a gabanta".


Billy giro😊
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```

















             🔮🔮🔮🔮
*page 83*
Ta tsare ta da mugun kallo tace"ina umartar ki da kiyi gaggawar fita rayuwata da my man idan ba haka ba wlh sae na illata ki nasa kinyi babbar nadamar sanin my man a rayuwar ki dmn ba'ayi wata macen da zata ra6e sa ba na barta ba wlh bare bagidajiya er matsiyata irin ki da ko kashe ki nayi na kashe ki a banza ba abinda xa'a iya min"
Qyar Ryynt ke kallon ta wacce ta le6ace baki ta ra6a ta gefen ta wuce.
  Malika ta bita da ido tana jin kmr taje ta fizgota amma kuma tana gudun had'uwarta da man,wacce ba abinda yafi qona mata rae irin yanda taga mohd yafi zumud'in Ryynt a kanta bayan ita ya jima baya tare da ita amma wae Ryynt da yayi tafiya da ita yake marmari ba ita ba,nn dae ta juya ta bar gurin cike da tunàni
 kala kala a ranta na hanyar da zàta bi tasa Ryynt ta bar gidàn da qafafunta kuma ta tafi knn har abada.

 Ryyñt kuwa tana shiga d'aki sae ga mami ta shigo aguje sae dariya take taje bayan Ryynt ta 6uya tace"Anti 6oye ni muna wasan 6uya ne nida alawiyya"
 Kafin Ryynt tace komai sae ga alawiyya ta shigo d'akin  nn mami ta fita aguje ta bar d'akin alawiyya ta bita sae sautin dariyar su kake ji,
D'auke da murmushi Ryynt ta girgiza kanta tace"aifah an had'u da an dace"
  Taje ta zauna kan bed tare da jawo wayarta da ke ajiye kan bedside drawer ta kira duk wani  nata da ta sani ta musu gaisuwar juma'a.
  Bayan ta gama wayar ne ta soma jin bacci na fizgar ta nn ta d'an kwanta ba jimawa bacci ya kwashe ta.

Ta jima abinta tana bacci snn ta tashi wacce da tashinta ta cire kayan jikinta ta fad'a bathroom tayi wanka ta fito tayi shirin ta cikin wata doguwar riga ta material less mai d'an qyal qyali light brown ga rigar ta kama jikinta sae ta mata kyau sosai  har dae d'aurin d'an kwalin da tayi sae ya qara fito da ita ,ita kanta har mamakin ganin yanda ta iya d'aurin d'an kwali take bayan gani kawae take a kan mutane ba koya tayi ba.
    Mami ce ta shigo d'akin ta kalli Ryynt dake feshe jikinta da turarukka tace"Anti kinyi kyau fiye da kwalliyar d'azun hln fita zakiyi?
  Ryynt tace"ba abinda zanje mami"
  To amma kuma shine kikayi wani  wankan har da canza kaya, uhm mami knn cewar Ryynt wacce taja hannun mami suka je downstairs gun dining ta samu kuku ya gama jera komai na abinci wacce dama tazo ta duba ne kar sae mohd ya dawo ba'a kammala jera komai ba gashi yau juma'a yana gab da shigowa.
  Nan suka juya zasu koma upstairs suka ji qarar bud'e gate mami tace"eh!  yaya ya dawo"
 Daga haka bata jira me Ryynt zata ce ba ta fita da gudu jim kad'an sae gashi sun shigo ita da mohd yana riqe da hannun ta yayinda d'ayan hannun sa ke riqe da briefcase d'auke da murmushi Ryynt ta kar6i briefcase d'in tana mishi sannu da zuwa.
  "Yauwa my Rynt"cewar mohd wanda shima yake d'auke da murmushi a fuskar sa,mami ta kar6i briefcase a hannun Ryynt tare da fad'in"Anti kawo na kai masa a d'aki"
   Ryynt tace"zaki iya?
Eh anti zan iya,to ki riqa da kyau nn mami ta rataya briefcase d'in ta wuce.
Kamar jira mohd keyi ya janyo Ryynt zuwa jikin sa yace"Ryynt wnn kwalliya haka so kike na kasa zuwa masallaci"
  Tace"uhm Mk knn abinci zaka fara ci ko kuma sae kayi wanka?
  Muje na fara cin abinci tukun, ya fad'i hakane tare da jan hannunta suka je kan dining suka zauna sae ga mami ta dawo mohd yace"mami je gayawa Antinki malika tazo aci abinci"
  Tace"to"ta tafi da gudu ba jimawa sae gata ta dawo taja gujera ta zauna.
  Bayan malika ta fito har sun fara cin abinci Mohd sae kallon Ryynt yake d'auke da murmushi a fuskar sa ita ma sae kallon sa take tana murmushi sbd qafar sa da yakai  kan tata yana shafawa har itama ta soma ramawa wanda duk abinda suke idon malika na kansu tana ganin yanda suke wasa da qafafuwan su ta under table.
    Da qyar taga sun kammala cin abincin ta tashi zata bar gurin sae kuma ta juyo tana kallon mohd da ya zari tissue yana share hannun sa tace"ina so zanje gida"
   Yace"sae kin dawo"
 Daga haka yaja hannun Ryynt suka bar gurin ba tare da ya jira ko malika zata ce wani  abu ba mami kuwa dama suna kammala cin abinci ta bar gurin.

Suna shiga d'aki man ya soma cire kayan jikin sa Ryynt na taya shi yasa bathrobe yaja hannun Ryynt suka nufi bathroom ta taya shi wanka suka fito ya zauna yana shafa mae Ryynt taje ta ciro masa kayan juma'a wani  tsadadden farin yadi mae kyau da akayi wa aiki da light brown ta ciro masa hula mae klr aikin da kuma takalmi suma klr wato light brown bayan ya gama shafa mae ta taya shi ya shirya tana fesa masa turare sae kallon sa take dan ba qaramin kyau yayi ba,ya kar6i turaren ya fesa mata a wuya ta lumshe idonta a hnkli yace"wnn kallon fa my Ryynt?
Sae da taje kan qirjin sa ta kwanta snn tace"kyau kamin"
  Ya shafo bayanta  yace"ae kin fini yin kyau don yau da qyar ma ne zan tafi masallaci"
    Ryynt ta d'ago d'auke da murmushi tana kallon sa tace"hm mk ka cika zolaya"
    Yace"hm zolaya ko ai zakiyi bayani ne in na dawo daga masallaci"
  A shagwa6e ta kalle sa tace"um um dan Allah yi haquri ni kwad'ayin fita ma nakeji amma sae ka dawo tukun sae mu tafi yawo"
  Mohd yayi murmushi tare da jan hannunta suka fito ta rakashi har mota snn ta dawo wacce bata zarce koina ba sae d'akin ta.

Koda mohd ya dawo daga masallaci ya sami Ryynt ta ida sallah tana linke hijab  yaje yayi kwance  rigingine kan bed ya maida hannayen sa baya yayi pillow dasu had'e da lumshe idanun sa.
  Ryynt tazo ta zauna a hankali kusa da shi tare da d'aura hannunta akan sajen fuskar sa,cike da kasala ya bud'e idonsa ya riqo hannun ta da ta d'aura akan sajen fuskar sa yana kallon ta kafin yake sauke idonsa akan cikin ta ya tashi zaune ya janyota zuwa jikin sa yana shafa cikin snn ya kalle ta yace"ya naga kmr babyna ya rage girma yau?
  Tace"rigar ce ta 6oye girman shiyasa naji dad'inta wlh"
     Mohd yace"ashe sae nasa a qara d'inka maki irin ta da yawa kafin ki haifu sae ki sami na sawa koh"
  Ryynt tace"kayan ae zasuyi yawa tunda ko na lefe yaushe yaushe ne na fara saka su"
   Mohd yace"um um ai doguwar riga tafi dad'in sawa ga mai ciki har dae irin ta jikin ki d'in nn kuma kayan lefen da kike magana idan cikin ya tsufa sae kiga kin nemi na sawa kin rasa duk sunyi kad'an sae dae ko bayan kin haifu.
  Tace"to ae sae idan cikin yayi qatoto ne,ni kuma nafi so ma ya tsaya a haka ba sae ya qara girma ba"
  Mohd ya kalle ta ba tare da yace komai ba don yasan cikin ba qaramin girma zae yi ba shiyasa take bashi tausayi yanda zatayi kayan cikin idan ya tsufa.
  Ryynt tace"amma a d'inka min ko kala uku ne a cikin zannuwan lefen da naga ba'a d'inke ba"
   Mohd ya gyad'a mata kai d'auke da idanun sa da suka soma canza kala,
Ryynt dake kallon sa tace"bacci kake ji?
Yace"eh tashi muje d'akina"
  A shagwa6e tace"Mk yawon da nace maka fa"
  Ryynt wane yawon ba inda za'a je ki huta abinki kawae.
  Tace"um um ni yawo nake so"
Yace"to bari idan na tashi daga bacci zuwa bayan la'asar sae ki shirya na zagaya dake cikin gidan nn kiga guraren da baki je kin gani ba"
  Kmr zatayi kuka tace"uhm uhm ni na d'auka ma ko cikin gari zamu je"
   Mohd ya goga tsinin hancinta akan nashi yace"kar ki min kuka wasa nake miki bari idan na tashi daga bacci koina kike so za'a je"
  Da sauri tace"har da gidan inna"
   Yace"har ma da gidan gwaggo"
 D'an kuka shagwa6a ta fashe masa da shi  don ta fhmci knn zancen fitar ma da kmr wasa yake mata.
   Mohd yayi er dariya yaja hannunta suka fito sae kukan shagwa6a take tana roqon sa ,
shi kuma yana janye da ita har suka je d'akin shi.
    Da kanshi ya rage kayan jikin sa tayi zamanta tana kallon shi ya dawo daga shi sae singlet n boxer yazo ya xauna kusa da ita yana shan ruwan gora masu sanyi da ya ciro a fridge ya bata tace"um um tare da  marairaice fuska tace"mk dan Allah dae wlh ban san me yasa ba kwad'ayin fita nake ji yau"
  Yace"Ryynt ae da gske nake miki zamu fita d'in amma banda gidan inna don nasan fad'a kawae zata miki kin dawo da kwana biyu har kin fara fita,ki bari zuwa sati biyu haka sae na kaiki gidan inna kinji"         Tayi murmushi tare da rungume shi tace"na gode"
   Nan taji hannun mohd akan zip d'in rigarta yana zugewa ta d'ago tana kallon sa tace"bacci fa kace zakayi"
 Idanun sa masu cike da sha'awa ya kalle ta da su yace"hm wae ke ba kya banbance sha'awa da jin bacci ne"
Sosai ta shagwa6e fuska tana kallon sa kafin tace komai sae bakin sa taji a cikin nata tare da kai hannu a cikin rigarta yana wasa da dukiyar fulaninta.


Sorry dan Allah wlh ina fama ne da rashin son typing gashi na matsu na kammala muku shi na huta amma kuma da zarar na d'auki waya sae naji gabad'aya typing ya fita raina kwata kwata shiyasa duk yanda naso nayi mae yawa nake kasawa.






Billy giro😊
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```

















             🔮🔮🔮🔮
*page 84*
  Bayan sllr la'asar sae gasu sun fito bathroom  mohd na sanye da white bathrobe  Ryynt  na sanye da baby pink sae dariya take had'e da d'an gudun ta bata so mohd dake biye da ita ya kama ta bata kai koina ba ya cafko ta zuwa jikin sa yaje da ita kan bed ya kwantar had'e da yi mata rumfa zae kai bakin sa a nata ta kauda fuskarta tace"Mk lokacin sallah fa na tafiye ka sani"
  Yace"to ae kece bana gajiyawa dake kin sani"
    Ryynt tace"uhm mk meyasa ka fiye son zolaya ne wae"
   Yace"au so kike  wnn karon ma na nuna miki ba zolaya nake ba"
    Ya fad'i hakane yayinda ya kai hannu zae zare mata bathrobe tayi saurin cewa"Aa yi haquri dan Allah wlh na gaji "
   Yace "to tashi muje muyi sallah"
  Tace"banda abin sallah d'akin nn"
 Yace to muje na raka ki ki d'akko nn ta miqa masa hannun ta ya kama ta suka fito yayinda Ryynt ke rungume a ajikinsa suna tafe sae shafa cikinta yake suna magana suna dariya ba tare da sun kula da malika dake zaune a falo ba ita da qawar ta fa'iza sae kallon su suke har suka 6ace ma ganin su.

 Fa'iza da still ta kasa d'auke idonta ta jinjina kanta had'e da fad'in cabd'i! lailai samun guri"
 Malika da duk kishi ya gama cikata taja hannun fa'iza tace"zo muje da Allah bana son ganin dawowar su"
  Suna isa d'akin nata tayi zaune tare da dafe kanta fa'iza tace"meye kuma abin damuwa bayan kin san makomar er banza wnn abun da take duk na d'an lokaci ne dan da ganin wnn cikin nata duk dad'ewar sa bazae wuce nn da 3months ba ta haife shi.
  Malika tace"ga dukkan alama hkne  shiyasa naji dad'in shawarar da kika bani dmn itace mafi sauqi da zan rabashi da ita har abinda ta haifa ko ma nace abinda ke cikin ta dmn kafin ta haifu zan aiwatar da komai kawai fatana na san lokacinda ta fara naquda har zuwan su asibiti to da na sami hakan buqata ta biya kuma duk wani  baqinci nayi sallama dashi a rnr har abada amma kuma tun ba'a je koina ba haquri na yana so ya qare kan abubuwan da ke faruwa tsakanin shi da ita musamman irin zumud'in da yake yi akanta ya soma kaini maqura ba kad'an ba, kiji fa wanka suka fito yanzun wanda na tabbatar wani  abu ne ya faru tsakanin shi da ita.
   Fa'iza tace"calm down my dear ki barta lokacin ta ne tayi abinta lokacin ki zae zo da zaki rabata dashi har ma kowa nata"
   Hakane fa'iza i knew but abin ne da ciwo kawai daga sama wata banza can taxo  tana qoqarin qwace maka miji wae har ace ko rnr girki na yafi lokacin ta akaina don rnr yana dawowa daga aiki gurinta ya fara zuwa kafin ni kuma har cikin dare fa tashi yake yaje d'akinta haka kawai......what!cewar faiza,malika tace"hm bari kawai ke dae ai har calendar na ajiye dmn na fara soke kwanan watan lokacin cin ubanta wato na ganin cewa na rabata dashi har abada ynx so kawai nake rnr girki na ta zagayo na tambaye sa hln cikin ta wata nawa ne dmn zanfi jin dad'in ci gaba qirgar watannin"
  Fa'iza tace"hln zae gaya miki ne?
  Hm ina mace kuma bare kuma yanda yake son cikin nasan zae ji dad'i  idan yaji na d'auko zancen sa don duk qarin haukar son nn da yake mata bae wuce cikin da ke jikinta ba.
  Fa'iza tace"hkne kam shiyasa nake son ki ajiye banzar aqidar ki kema ki sami cikin nn"
  Malika tace"ae samun ciki mae sauqi ne aqida ta kuma dole na ajiye ta na samar masa baby sbd ina son na dawo da duk wata soyayyar da yake min a baya ina kuma son na  goge laifin zubar masa ciki da nayi kuma ko ba komai hkn zae sa ya manta da wnn abar kwata kwata a rayuwar sa.
   Fa'iza tace"da yafi miki ,ni zan tafi  kinsan sauri nake zanje gida sae munyi waya.
  Malika tace"to ai nima kinsan fita zanyi shigowar ki ne ya tsaida ni bari na jawo veil d'ina muje"
  Nan malika ta ciro mayafin ta taja key d'in motar ta suka fita.

Washe gari da guraren qarfe biyar na yamma Ryynt ce riqe da hannun mami ta rako saliha wacce taxo mata yini tun safe.
 Suna tsaye a bakin gate yayinda Ryynt ke cewa" yanzu saliha gobe idan kun koma shikenan kuma sae idan anyi hutu ko zamu sake had'uwa"
  Saliha tace"inafa ai kinsan na gaya miki wnn karon ban d'auke maki kowane visiting ba kuma wlh idan baki zo ba munyi fad'a"
  Ryynt tace"saliha ina kike son naje da wnn  cikin ko kuma so kike a filin visiting d'in idon kowa ya koma kaina ne"
Hm kinjii ki da wani zancen wnn cikin ae baiyi girman da zae hana miki shiga mutane ba kawai kedai kice baza kije ba shikenan Allah bamu alheri kinga tafiya ta
  Ta qarashe mgnr ne d'auke da fushi a fuskarta zata bar gurin
 Ryynt tayi saurin riqo ta tace" Haba saliha  kin san ba haka bane wlh kunyar shiga jama'a nakeji da cikin nn bare kuma lokacin nasan ya qara girma amma inshaa Allah zan zo ko visiting d'in farko ne kawae dae Allah yasa yayanki ya barni"
   D'auke da murmushi saliha tace amin Allah yasa, ni zan tafi.
   Ryynt tace"to Allah ya kiyaye hanya ki cewa umma na gode sosai"
   Saliha tace"to"kafin take fita Ryynt kuwa ta juya riqe da hannun mami suka  koma daga ciki.

Guraren qarfe tara da rabi na dare sae ga man ya shigo d'akin Ryynt  ya same ta sae waya take tana qyalqyatar dariya tana fad'in"ni bazan rantse maki ba sae dae kinzo ki ganewa idonki ko zaki fi yarda"

 Man yayi tsaye kawae yana kallonta wacce bata lura dashi ba har sae da ta gama wayar ,
da sauran murmushi a fuskarta ta gaida shi ya amsa had'e da qarosowa inda take ya zauna kan bedside drawer yace"da waye  kike  waya haka sae  faman dariya kike?
  Tace"hm qawata ce Sarah ke mamakin jin cewa ni matar aure ce har ma taqi ta yarda wae sae na rantse mata"
   Mohd yace"a bakin wa taji ne to?
  A guna taji da na gaya mata wnn karon bazan koma school ba shine ta nemi jin dalili na gaya mata,kuma qarin mamakin ta jin cewa kaine mijina wacce duk a tunanin ta kai yayana ne ban kuma gaya mata ainihin dalilin da ya hana ni komawa ba  kawae dae nace oga ya hana.
  Mohd yace"ashe idan ta ganki d'auke da babyna sae mamakin yafi haka"
 Tace"ae kam har laifina ma sae ta gani ko ma tayi fushi dani don ita fa komai nata bata 6oye min,in tazo ban ma san ta inda zan fara ba.
  Mohd bae ce komai ba sae hugging d'inta da yayi tare da kai hannu yana shafa cikinta snn yace"ae ko don albarkacin babyna zata miki haquri"
  Uhm ko ta qara yin fushi ba kawae dae sauqin abun tana da sauqin kae wanda idan na mata bayanin yanda abun yake zata fhmce ni.
  Mohd dake rungume da ita ya d'aura mata kiss snn ya miqe yace"sae da safe my Ryynt yau bacci nake ji sosai"
  Tace"to sae da safe"
 Nan ya fita ita kuma ta d'auki wayarta ta soma chat.

Bayan wasu en kwanaki da faruwar haka Ryynt ce zaune a a falo alawiyya na mata kitso sbd anjima da yamma ita ce zata kar6i girki.
  Kallo suke abinsu suna kitso sae ga malika ta fito tayi tsaye riqe da qugu tana kallon Ryynt tace"cabd'i amma lallai yarinyar nn ba er iska irinki ko an gaya miki cewa kowa qazami ne irinki da zaki zauna ana maki kitso a main falo sbd gidadanci irin naki bari kiji wlh maza
ku tashi a nn ki koma can side d'inki ki barbad'a qazantaccen gashin ki a can"
 Tana gama fad'ar haka alawiyya taje zuwa miqewa Ryynt tace"ke zauna qarasa min ba inda zamu je wlh"
  Malika tace"hm lallai yarinyar nn dani kike zancen zaki gane kuren ki ne idan man ya dawo wlh"
   Daga haka ta wuce fuuuu!Ryynt ta bita da kallo le6ace da baki tace"in yazo ki gaya masa har ma abinda ba'ayi ba inga ko kashe ni zae yi ki huta da gani na"
  Alwiyya tace"um um anti dan Allah tashi muje ko d'akin da nake zama ne sae mu qarasa a can"
  Hm ba inda zanje alawiyya nn nake ra'ayin zama kuma a nn za'a qarasa kitson.

 Alawiyya bata sake cewa komai ba suka ci gaba da yin kitson su basu jima ba suka kammala dan dama sunyi jima da farawa.
  Da suka gama Ryynt ta kwashi kayan kitso ta koma d'aki alawiyya kuwa ta tsaya zata share falon.

Da shigar Ryynt d'aki wayar ta da ke hannunta ta shiga ring Sarah ce mae kiran ta d'aga wayar cikin murna tace"da gaske to shikenn gani nn zowa na shigo dake.
  Nan ta jawo qaton hijab d'inta mae kai mata har qasa tasa ta fita jim kad'an sae gashi sun shigo ita da qawar ta sarah da duk ta cika da mamaki dan kan aje koina ta gama yarda Ryynt matar aure ce sbd cikin da ta gani bayyane a jikinta sae duk ta kasa cewa komai sae bin Ryynt take da kallo tana binta kmr raqumi da akala har suka je d'aki.
  Bayan ta zauna ryynt taje ta bud'e frigde ta kawo mata lemu da ruwa snn ta kira kuku a landline a cewar ya kawo abinci.
  Bayan kuku ya kawo abincin ne Ryynt ta kalli sarah tare da murgud'a mata baki tace"kallon fa"
  Sarah ta nisa tare da fad'in "hm lallai Ryynt kin nuna min ba kowa nake a gurin ki ba gwara ma na tashi na bar gidan nn tun wuri kafin na qara had'uwa da wani takaicin kuma"
  Daga haka Sarah ta tashi zata fita Ryynt ta sha gabanta tace"dan Allah Sarah ki tsaya ki saurareni wlh yanda kike tunani ba haka bane yi haquri muje ki zauna kinji dan Allah"
  Ba yanda Sarah ta iya ta koma ta zauna Ryynt ta mata bayanin komai koma nace ta bata labarin ta komai bata rage mata ba.
   Sosai Sarah ta tausaya mata matuqa tace"Allah sarki Ryynt labarin ki abin tausayi"
  Ryynt tace"ae Alhmdlh yanzu komai ya wuce"
 Sarah tace"shi Aamil daga rnr da ya tafi har yau bae dawo ba?
  Ryynt tace"bae dawo ba ni matar sa ma tausayi take ban dan rnr da mukaje family house a 6angaren su na ganta gabad'aya ta canza ta rame sosai sbd damuwa da kuma sabon cikin da ya tafi ya barta dashi.
  "Toh Allah ya kyauta"
 Cewar Sarah, Ryynt tace"amin"snn ta bud'e lemu ta tsiyaya mata a cup ta bata.
 Bayan har taci abinci Ryynt tace"bari na kira maki mk yazo ku gaisa"
  Tace"to"
Ryynt kuma ta jawo wayar ta ta kira mohd ring d'aya biyu ya d'aga ,bayan ta gaida shi take gaya masa Sarah tazo.
  Yace"to kinsan bana gida fa amma idan na tsaigaita aikin da nake a asibiti zan shigo mu gaisa"
  Tace"to shike nn sae ka shigo"
 ta kashe wayar tana mai kallon Sarah tace"yana asibiti amma yace"idan ya kammala aikinda yake zae shigo ku gaisa d'in"
  Tace"ok"
Snn ta d'aura da cewa"ni kuwa Ryynt  idan zaki yi waec n neco a school d'in mu zakiyi ko kuma zauna miki za'ayi?
   Aa ni nafi son na rubuta da kaina don koshi haka yace kawae fatana Allah yasa a lokacin na haifu.
 Sarah tace"kai ae har ma abinda kika haifa ya soma wayo dan kinsan akwai sauran lokaci kawae fatana  Allah yasa ki haifa mana baby boy"
  Ryynt ta kalle ta d'auke da d'an guntun murnushi ,
Sarah tace"ko kinfi son ki haifo mana baby girl?
Tace"um um Allah dae ya bani mae albarka "
  Sarah tace"wlh kinyi magana amma dae cire qaton hijabi d'in nn haka kisha iska kin wani  qunshe mana baby wae ke ba kya so a gani"
  Ryynt tace"uhm Sarah knn ae ko baki ce ba da niyyar cirewa nake sbd kitso aka min da zafin shi ko iska bae sha ba sae ga kiranki kinxo.

  Sarah tace"muga kitson"
  Nan Ryynt ta cire hijab d'in ta ta nuna mata
Sarah tace"wayyo Allah wa ya miki wnn shuku mae kyau haka wlh tayi kyau ba kad'an ba don ina mugun son side weaving hln saloon kika je?
  Ryynt tace"um um wlh wata yarinya ce tamin alawiyya"
  Sarah tace"er maqotan ku ce?
 Aa yarinyar da aka samar min ce.
  Sarah tace"kai amma dae gaskiya ta iya kitso wlh da nice na iya kitson nn haka saloon kawai zan bud'e"
  Ryynt tayi er dariya tace"kai sarah Allah ya shirye ki shi zanen lallen da kika iya ae banga kin maida shi sana'a ba"
    Sarah tace"hm wlh da ace Abba da umma sun barni da tuni na maida shi sana'a don ina sha'awar sana'ar hannu fiye da yanda ba kya tsammani dmn har kuka sae da nayi da aka hana min en gidan mu kawae nake yiwa idan sun buqata"
  Ryynt tace"Allah Sarah sae naji kin qara birge ni sosai sbd rashin girman kanki ina sha'awar naga mutum haka wlh"
  Murmushi kawae sarah tayi don ta fhmci inda Ryynt ta dosa wato na ganin ita er mae kud'i ce amma kuma sam bata kai kanta a wata ba tace"hm Ryynt knn"
  Ryynt tace"me nayi ae gaskiya na fad'a"
  Ae bance kinyi qarya ba na gaida ke ne kawai.
   Ryynt tace"to na amsa kyauta,amma kuma ina neman wata alfarma"
  Ta me knn?
So nake ki zana min lalle d'an simple mae kyau sbd yau nike da oga.
  Ta qarashe mgnr ne tare da saurin rufe fuskarta da tafukan hannyen ta.
   Sarah tace"hm yau kuma ni kike kunya nida rnr kikace da kiji kunya ta gwara kinyi kunyar desk d'inda muke zaune"
  Ryynt tace"nidae zaki min ko kuwa sae kin tsaya dawo da abinda ya wuce"
  Tace"tashi d'auko kayan lalle idan kina da"
  Kai tsaye Ryynt ta tashi ta d'auko kayan lalle suka fara.

6:00pm
Ryynt ce ta fito raka Sarah da zata koma gida dan tuni ta gama mata lallen har ma ta wanke.
  A bakin gate suka tsaya Ryynt tace"kiyi hqr Sarah inaga mk aiki ya masa yawa shiyasa bae samu yazo kun gaisa ba"
  Tace"Allah ba komai amma mami fa ba kince min gurinki take ba?
  Eh bata nn ne taje yini a gidan yaya nasir.
  Tace"olryt ni na tafi nagode sosai sae munyi waya"
  Ryynt tace"nima nagode Sarah ki gaida su umma"
  Tace"zasu ji"
  Nan ta wuce Ryynt ta koma daga ciki"



Bayan isha'i zaune suke gabad'ayan su zasu fara cin abinci Ryynt na  tsaye cikin kwalliyar ta mae kyau kmr wata amarya ta jawo kula zata  zubawa mohd abinci tana bud'e kular tayi tsaye turus tana kallon abincin, mohd yace"lafiya"
 Ya fad'i hakane yayinda ya kai idon sa a kan abincin,rae 6ace yace"what! me zan  gani suma a cikin abinci garin ya haka,nn ya soma qwalawa kuku kira cikin d'aga murya.
  Malika tace"ba laifin kuku a ciki laifin ta ne ta sani don zaune tayi a nn falon ana mata kitso da na mata magana tace ba inda zasu je har ma ta nemi ta zageni"
  Mohd ya kalli Ryynt yace"wae hakane?
  Ryynt bata ce komai ba sae zaro gashin tayi tana kallo don bae koyi kalar sumar ta ba gashin kanti ne tsintsa wanda tasan ba makawa malika ce tayi aikin.
  Tace"ae wnn ba.......no Ryynt bana son jin wani  surutu gaya min eh ko a'a.
   Maurya can ciki tace"eh amma....kinga bana so kar a sake,
  Tace"shike nn kayi haquri inshaa Allah baza a sake ba.
  Bae ce komai ba sae tashi yayi ya bar gurin itama taja hannun mami zasu bar gurin malika tasha gabanta tana mata shu'umin murmushi wacce ba haka taso abin ya kasance ba sosai taso mohd yayiwa Ryynt fad'a amma ko hkn ya mata dad'i kafin tace komai Ryynt ta ra6a ta gefen ta ta wuce sbd tasan ko minti d'aya ta qara a gurin baza ayi ta da kyau ba gashi bata son ta fara biye mata.



Guraren qarfe goma mohd ya shigo d'akin Ryynt dmn yayi kiranta a waya har ya gaji taqi d'agawa.
  Tana kwance  abinta kan bed sanye da kayan bacci riga da wando da ya tsaya mata iya guiwa yayinda mami ke kwance  gefen ta sae sharar baccinta take.
 Yace gab da ita ya zauna yana kallo ta juya masa baya bae ce komai ba sae kallon kitson ta da yake  had'e da zanen lallen da aka mata mae kyau
Yakai hannu yana shafa kitson snn yace"tashi muje d'akina kinji"
tace"ka tafi kawae ni a nn zanyi bacci na"
yace"haba Ryynt don kinyi laifi an miki magana kuma sae ki d'auki fushi da mutum bayan kinsan abinda kikayi ba dae dae bane"
  Cikin muryar kuka tace"to ai kaine kaqi ka saurare ni sae fad'a da da kake ta min"
  Kafin yace komai sae  da ya tada ta zaune  had'e da rungume ta a jikin sa yana mae shafa bayanta a hnkli snn yace"Ryynt ba fad'a bane magana ce"
  Tace"fad'a ne mana tunda har ma baka bari na qarasa zanje na"
  Yace"to yi haquri raina ne ya 6aci sbd na tsani ganin gashi a cikin abinci amma yi haquri kinji"
 Idon ta tap da qwallah ta d'ago tana kallon sa tace"to meyasa baka zo kun gaisa da Sarah ba har ta tafi kuma har kiranka na sake yi amma kaqi d'aga waya"
  Wlh Ryynt har zan zo aka kirani za'ayi family meeting amma kiyi haquri da kaina zan d'auke ki muje har gidan su ki kai mata ziyara kinji"
   Ta gyad'a masa kai tare da komawa kan qirjinsa ta kwanta.


Sorry plz munyi biki ne kwana biyu shiyasa kuka jini shiru.




Billy giro😊
```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```

















             🔮🔮🔮🔮
*page 85*
 Ya riqo hannunta yana duba zanen lallen da aka mata yace"wa ya miki lalle da kitso ?
  Tace"alawiyya ta min kitso Sarah kuma ta zana min lalle"
  Yace"dama mutanen qauye sun iya kitso haka"
  Tace"hm MK knn me ka maida mutanen qauye ne wae"
  Yace"um um fa kar ki canza min manufa ganin nayi kitson yayi kyau sosai"
  Tace"hkne kam nima nayi mamaki sae dai kuma kitso sana'ar ta ne shiyasa ta qware sosai don ba kalar kitson da bata iyaba ba a yanda ta gaya min sbd ban ma san ta iya  kitso ba jin tayi ina magana kan ina son zanje kitso tace ae in zo ta min ta iya shine nayi zaune ta tsantsara min abuna don haka duk wanda ya kalli kitson sae ya biya kud'in kallo har ma da na lalle"
  Yace"har da wanda akayi domin shi?
  Eh mana ae shi ma yafi cancanta ya biya kud'in.
     Yayi murmushi yace"naji zan biya kud'in har ma da kud'in wanda za'a sake min dan dae yau kam wnn zae sha ruwa"
   Murmushi tayi mae d'auke da jin kunya tace"to ae kitso ne ba zae lallace zama d'aya ba"
  Yace"a cikin kwana biyun nn kin san iya shan ruwan da zae yi ne to"
  Kallon sa tayi tace"Ae kana da tausayi na sani baza ka wahalladda ni ba"
   Kinji an wayo ,wae dae tukun me kika bawa Sarah da tazo?
  En tsarabarta na bata kayan bacci, turare da kuma makeup kit.
  Yace"banji dad'i ba naso ace nazo mun gaisa"
 Nima banji dad'i ba amma da ka min bayani na fahimta kuma ae kace zamu je koh?
 Yace"eh zamuje my Ryynt amma se next  weekend sbd kinga an koma school"
   Tace"wlh kuwa duk sae naji ina son komawa amma babyn ka ya hana min"
  Ta qàrashe mgnr ne had'e da turo baki.
 Mohd ya kalle ta tare da shafo cikinta yace"afwan ae da kin haifu zakiyi boko har ki gode Allah"
 Tace"to Allah yasa muna da rae da lafiya"
Yace"amin"
Wanda ya fad'i hakane tare da yaye rigarta yana kallon cikin ta da ke ta faman motsi yakai hannun sa sae shafa cikin yake yana murmushi tace"yunwa nakeji Mk muje d'akin ka in da akwai abinda xanci"
   Ya d'ago ya kalle ta yace"tun d'azun kiranda nake ta miki knn kixo ki sami abinda kika ci ,
ki kaiwa su mami nasu amma kika qi d'aga wayar wae ke fushi  gashi kinsa sunyi bacci da yunwa "
 Tace"ae basuyi bacci ba sae da suka sha tea"
  Yace"to muje ke ki sami abinda kikaci"
  Tace"hln mene zaka ban naci?
  Sae da ya d'auki mami snn Yace" kaza ce da hollandia yogurt ,amma ke da fresh milk zaki had'a dan ban cika son kina shan zaqi ba"
  Tace"um um gaskiya ban so"
Yace"to naji muje"
  Nan malika dake la6e tayi saurin barin gurin su kuma suka fito suka kai mami d'akin alawiyya snn suka tafi d'akin mohd.

 Washe gari malika ce tsaye a balcony tana kallon Ryynt da man da suka fito harabar gidan kowanen su cikin shiri sunyi kyau sosai sae zuba qamshi suke tana rataye da briefcase d'in shi,shi kuma yana rungume da ita a jikin sa suna tafiya har suka isa gun motar sa ya kar6i briefcase d'in tare da d'aura mata kiss kan goshi snn yaje a hankali kan cikinta ya d'aura mata ya shiga mota yana mata bye bye haka itama, bata daina masa bye bye ba har sae da motar sa ta fita gate d'in gidan snn ta juya ta koma daga ciki.
    Malika ta koma ta zauna cike da baqin ciki dan ita ko ta rako man bae wuce ya kar6i briefcase dinsa ya shige mota ya tafiyar sa, ba wani zancen ya mata kiss bare shi bye bye.

Da dare Ryynt ce zaune a falo tana sanye da riga da wando rigar milk ce handless iya cinya da aka d'an tsage gefe gefen ta yayinda wandon jikinta ya kasance maroon da ya kama jikinta dae dae,tana d'auke da er simple makeup a fuskarta amma sae tayi kyau sosai gashi ba d'ankwali a kanta sae qaton ribbon maroon da ta d'aure shukur ta dashi yayinda jelar shukur keta reto a bayanta tana riqe da waya sae chat take abinta can ta gaji da chat d'in ta ajiye wayar ta kunna TV tana kallo wacce kallon kawae take amma hankalinta na gun man da tun fitar sa da safe har yanxu bae dawo ba haka dae taci gaba da yin kallon ba wae don tana jin dad'i ba tana cikin hakane sae ga malika ta fito wacce kai tsaye ta d'auki remote ta canza tasha tayi zaune tare da d'aura qafa kan qafa tana kallo Ryynt ta kalle ta zata yi magana knn ta jiyo sallamar mohd ya shigo cike da murna ta tashi cikin sauri mae kmr gudu taje tayi hugging d'insa tare da fad'in"oyoyo my Mk i really missed u"
   Sae da ya d'aura mata kiss kan goshi snn yace"me too my Ryynt i really missed u aiki nake amma sae faman tunanin ki nake keda babyna"
     Ya qarashe maganar ne yayinda ya shafi cikinta snn ya zauna kan one seater Ryynt kuma ta durqusa kan guiwoyinta tana cire masa takalmi da socks, yayinda hannun sa ke kan jelar shukur ta yana wasa dashi tana gama cire masa takalimi da socks ya janyo ta ya zaunar kan cinyoyin sa sae shafa cikinta yake yace"ya lafiyar babyna kinji motsin sa a yau"
  Ryynt dake cire masa buttons d'in rigar sa ta gyad'a masa kai yace"to me kika masa da ya motsa?
  Me kake so na masa nikam?
D'auke da murmushi a fuskar sa yaja hancin ta a hnkli yace"ki shafa min shi mana a hnkli kamar yanda  kika ga inayi idan ya motsa miki.
  Tace"uhm to naji"snn ta shafo cikin sa tace"cikin ka ya lafe sosai muje kaci abinci ko wanka zaka fara yi tukun?
  Eh  wanka zanyi amma sae na fara bawa matata goron kwaliyya tukun,kafin Ryynt tace komai sae jin lips d'insa tayi a goshin ta ya d'aura mata kiss snn yaje kan kumatun ta ta kowane gefe ya mata ya kuma je a hankali zae kai bakin sa a nata
 Malika dake kallon su ta buga uban tsaki had'e da tashi ta bar gurin Ryynt da sam ta manta  da zamanta a falon ta kalle ta kawae ta maida dubanta gun man da bae ma san da zaman malikar ba gabad'aya sae tsakinta da yaji ya kalle ta kawae ya maida duban sa gun Ryynt yakai bakinsa a nata ya d'aura mata kiss ta sakar masa murmushi had'e da riqo hannun sa tace"muje kayi wankan koh"
  Nan ya tashi rungume da ita a jikin sa suka tafi d'akin shi da taimakonta ya cire kayan jikin sa suka nufi bathroom ta taya shi wanka suka fito.
  Bayan ya shirya yaci abinci suna zaune kan bed sae shan fruit suke abinsu suna kallo mohd yace" wae mami tayi bacci ne?
  Ryynt tace"inafa suna can sae wasa suke ita da alawiyya an gamu da an dace dan alawiyya akwai son wasa kmr wata er shekara biyar"
   Mohd yace"ko ke da kika girme mata ae naga biyewa mami kike kuna ta yin wasar"
  Ta kalle sa d'auke da murmushi tace"ae wnn daa ne ka sani"
  Yace"ba wani  nn ko yanzu kika sami dama nasan zakiyi babyna ne kawae bae barki ba"
    Tace"nikam  babynka bae hana min ba kawae dae na bar wasar ne"
 Mohd ya kai hannu yana shafa cikinta yace"kina nufin har yanxu babyna bae fara miki nauyi ba"
  Tace"ya fara mana kawae dae bana jin wahalar yin komai don ko wasan tsera zan iya"

 Mohd dake kallonta yayi er dariya yace"kinji ki sae kace da gaske keda ko abun nn kuka kike min wae kin gaji bare wasan tsera"
  Tace"uhm to ae ba d'aya bane da wasan tsera ka sani "
  Yace"to ae ke zan gaya wa haka dan wasan tsera ya fishi wahala kin sani"
  Tace"ba wani  nn"
  Ta fad'i hkne tare da tashi zata bar gurin ya riqo hannun ta yace"ina zuwa?
  Tace"ina son zanje na d'an watsa ruwa ne nayi shirin bacci"
   yace"tun ban gama ganin kwalliyar da aka min ba"
   Tace"wlh yau bacci nakeji sosai"
  Yace"to muje bathroom d'ina na taya ki wankan koh"
 Tace"kayan bacci na fa na d'aki"
  Yace"muje dae ayi wankan tukun"
    Tace"to"yayinda ya d'auke ta cak suka nufi bathroom.

2 weeks later
Sae a lolacin mohd ya sami damar kai Ryynt gidan su sarah bayan sun baro gidan ne ya kaita gidan inna sae dare bayan isha'i snn yaje ya d'auke ta suka je family house to 9 suka fito zasu koma har ma sun shiga mota Ryynt tace"Mk ba mu fa je d'ayan 6angaren ba kuma ya kamata naje na duba maman ilham da jiki.
    Ba musu mohd ya fito suka tafi suna shiga 6angaren suka had'u da mahaifiyar maman ilham ta sauko daga upstairs knn riqe da tray mae d'auke da kulas akai zata kai kitchen wacce tana ganin su ta saki fuska cike da fa'ara tana amsa gaisuwar da suke mata had'i da tambayar ta ya mae jiki tace"Alhmdlh ku shiga tana daga ciki"
  Kai tsaye suka nufi d'akin da maman ilham take sae dae kafin su qarasa wayar mohd ta shiga ring koda ya duba kiran Abba ne hakan yasa ya fita ya bar Ryynt ta qarasa wacce tana bud'e qofar d'akin tayi tsaye cak tana kallon Aamil dake durqushe kan guiwoyin sa yana tada maman ilham dake kwance  kan bed tana bacci wacce ta bud'e idon ta da qyar tana kallon mae tashin ta cikin mugun mamaki ta miqe zumbur har tana qoqarin fad'uwa sbd bata da wani  qarfi a jikinta duk ciwo ya cinye.
  Aamil ya riqota da sauri ya tafi da ita zuwa jikin sa yana kallon fuskarta cike da qwallah tap a idon sa ganin yanda ta rame sosai yayinda ita ma take kallon fuskar sa da duk ta cika da qasumba ga baqar ramar da yayi takai hannu kmr da tsoro ta riqo kumatunsa da qyar muryar ta na rawa tace"Abban ilham kaine ko kuma mafarkin da na saba yi ne?
  Qwallar da suka cika masa ido ne suka gangaro kan fuskar sa yana kallon ta cike da tausayi yace"nine my wife ba mafarki kike ba"
  Nan kawae ta fashe da kuka sosai tare da fad'awa kan qirjin sa ta qanqame shi tace"Abban ilham meyasa ka tafi lokaci mae tsawo kabar ni cikin damuwa"
   Aamil da hawaye ke ci gaba da gangarowa kan fuskar sa ya qara rungume ta a jikin sa yace"am sorry my wife ban tafi a son raina ba sae don ya zama dole,ko yanzu nazo ne kawae dmn na ganki na koma"
  Da sauri ta d'ago fuskarta hawaye sha6e sha6e tana girgiza masa kae tace"no Abban ilham dan Allah kar ka sake tafiya ka barni wlh bazan iya jurewa ba"
  Yace"ya zanyi my wife ae ya zama dole na tafi dmn bazan iya had'a ido dasu Abba ba musamman Ryynt kiyi haquri dan Allah na miki alqawari zan riqa zowa a 6oye ina ganin ki kinji"
   Kallon sa take ba tare da ta iya cewa komai ba sae wani  sabon kuka da ta fashe masa dashi ta riqo hannun sa ta d'aura kan cikinta tace"Abban ilham in ka tafi ya kake so nayi da wahalar sabon babynka da komai bana iyayi ga kuma damuwar rashin ka a tare dani"
   Da sauri ya kalli cikinta yace"dagaske my wife ciki ne dake?
  Ta gyad'a masa kai tace"da gaske nake maka Abban ilham dan Allah kar ka tafi ka tsaya mu reani babynmu kmr yanda muka raeni cikin ilham kaji"
Aamil bae iya cewa komai ba sae shafa cikinta da yake qwallah na zuba a idon sa yace"no way my wife gaya min ina ilham take in ganta"
  Cikiñ muryar kuka tace"tana d'akin umma tana bacci bari na d'auko maka ita.
  Yace"no kawae ki shafa min kanta kinji ni zan tafi.
   Bae jira me zata ce ba ya janye jikin sa daga nata ya kama hanya zae fita ta riqe sa sae kuka take sosai  tana roqon sa kar ya tafi.
  Ba yanda Aamil ya iya don kuka yake ji sosai amma hakan ya dake ya janye hannunta daga riqonda ta masa ya nufi qofa da sauri zae fita ba shiri ya tsaye cak yana kallon Ryynt da ya gani tsaye a gabansà  d'auke da hawaye a fuskarta tanà kallon sa




Billy giro😊

```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```

















             🔮🔮🔮🔮
*page 86*
kafin Ryynt tace komai sae ga mohd ya shigo d'akin yana kallon Aamil ba tare da ya nuna mamakin ganin sa ba sbd tun d'azun yake tsaye a bakin qofa yana kallon duk abinda ke faruwa.
     Ya qarasa gurin Aamil tare da dafa kafad'ar sa yace"Aamil ka dawo knn ba inda zaka je,duk da cewa naji dalilin ka na son komàwa amma wnn ba hujja bace dmn matar ka da er ka suna buqatar kulawar ka kuma wacce kayiwa laifin tuni ta yafe maka kan me to zaka je kaci gaba da azabtar da kanka a bisa laifin da aka riga aka yafe ma.
  Aamil da tun d'azun kansa ke qasa ya d'ago yana kallon mohd d'auke da qwallah tap a idonsa cikin muryar kuka yace "No Man dole zan koma inda na fito sbd ban cancanci yafiya a gurin Ryynt ba dmn wlh na cuce ta ba kad'an ba ta yanda ni kaina bazan iya yafewa kaina ba snn ta yaya kake tunanin zan iya tunkarar su Abba da wane ido zan kalle su bayan na 6ata duk wata tarbiyar da suka min na aikata babban kuskuren da har mutuwa baza a ta6a manta shi ba,nn kawae ya fashe da kuka yace"tell me ta yaya zan kalle su,ta yaya zanci gaba da kallon Ryynt wacce duk lokacin da ta ganni sae ta tuna da mummunan abinda na mata na kàshe matà màhaifi da nàyi.
 Ya qàrashe mgnr ne cikin kuka sosai hakama a gurin Ryynt kukan ta soma yi.
 Mohd ya riqotà ya d'an tafi da ita zuwa jikin sa yanà shafa bayàñta snn yace"Aamil Ryynt ta yafe maka bazata kalle ka da hakan ba,amma in kace ka sake tafiya hakan zae sa kowane lokaci aka tuna da kae a tuna dalilin tafiyar ka amma idan kayi zamanka sannu sannu yau  da gobe sae ka ga an manta komai kmr ba abinda ya faru....... No Man ba irin wnn mummunan aikin da na aikata ake iya mantawa dashi ba never,
 kawae ka barni na tafi abuna dàn Allah.
  Mohd yayi shiru yana kallon sa kafin yake cewa"Aamil magana d'aya zanyi itace idan har kace sae ka tafi tofa lallai sae ka bawa khadija takardar ta dmn bazata zauna da aurenka akanta ba"
   Da sauri Aamil ya girgiza kansa yace"haba man wlh bazan iya sakin khadija ba ka sani ina sonta"
  Mohd yace"kana sonta amma kuma ka za6i taci gaba da cutuwa har iya lokacin da ba'a san iyakar sa ba sàm hkn ba zae yiyu ba kawae ka bata takardar ta idan har kace a'a tofa lallai baza ka je koina ba wlh.
  Aamil ya girgiza kansa qwallah na faman sauka kan fuskar sa kafin yace komai sae ga mahaifiyar maman ilham tazo tace"Aamil gaskiyar mohd ne dole ka za6i d'aya kuma naga abinda ka aikata kayi nadama tun rnr da ka aikata haka kuma Ryynt ta yafe maka abinda kawae ya rage kaje ka sami Abbanku ka qara bashi haquri wanda na tabbatar shima zae haqura ya yafe maka.
  Aamil ya kalle ta yace"ina tsoro umma kmr Abba bazae yafe min ba"
Ta girgiza kanta tare da kai hannu tana share masa hawaye tace"kuje kaida mohd inshaa Allah zakayi nasara kaji"
   Aamil bae iya cewa komai ba sae mohd ne yaja hannun sa suka fita basu zarce koina ba sae 6angaren su,suka samu Abba na zaune yana kallon labarai umma na zaune kusa dashi riqe da nail cutter tana cire masa qunbar yatsun hannun sa wacce tana ganin su ta saki nail cutter ta miqe zumbur tace"Aamil!
 Aamil dake tsaye yayi saurin sadda kansa qasa sae ga Abba ya qaraso gurin sa a fusace yana kallon sa yace"me ya dawo da kai maza fita a nn in daina ganin ka shashan yaro kawae"
  Hawaye masu zafi ne suka gangaro kan fuskar Aamil yayinda  mohd yace"Abba haqiqa Aamil yayi kuskure amma dan Allah kayi haquri ka saurare mu wlh yazo qara baka haquri ne akan abinda ya faru"
  Komai Abba bae ce ba sae komawa yayi ya zauna itama umma ta zauna mohd yaja hannun Aamil suka je suka zauna qasa kusa da gefen doguwar kujerar da Abba ke zaune.
Aamil da kansa ke qasa ya samu da qyar ya bud'e bakinsa sae haquri yake ta bawa Abba cikin nuna matuqar nadama akan abinda ya aikata.
  A nn mohd shima yasa bakin sa yana bawa Abba haquri byn nn itama umma tasa bakinta cikin rarrashi tana qara bashi haquri.
  Can Abba ya nisa ya kalli Aamil yace"Naji na haqura na kuma janye hukuncin da nayi niyyar sa ayi maka amma ka sani sae na tara kaf  familyn gidan ka basu haquri haka ma Ryynt sae ka same ta ka qara bata haquri bayan haka sanin kanka ne azumi sittin na kanka duk sae ka yi su ba tare da ka tsallake ko rana d'aya ba.
  Aamil yace"hakane Abba har ma nayi azumin a inda naje"
  Abba yace"shike nn mohd tashi je kowane 6angaren ka snr da kowa a had'u a main falo snn ka kira Amir da Nasir a wayà kace duk su zo.
  Mohd yace"to"
snn ya tashi ya fita.
  Bayan mohd yaje ya sanar dasu kowa ya hallara Aamil ya basu haquri kmr yanda Abba yace .
kowanen su ba wanda bae yafe masa ba asali ma sunji dad'in dawowar sa ba dan komai ba sae dan cike suke da tausayin mtr sa Khadija da ya tafi ya bari.
 Da su Ryynt zasu koma gida ne Nasir,Amir and Aamil sun rakosu zasu shiga mota Aamil ya qara ba Ryynt haquri da neman yafiya a gurinta wacce ta nuna masa ita har ga Allah tuni ta yafe masa kuma komai ya wuce a gurinta dmn ta d'auki abun a matsayin qaddara fatan ta kawae Allah yaji qan Baffanta da Rahama Amin.

Bayan sun koma gida ne Ryynt na kwance d'aure da towel a jikin ta ga dukkan alama wanka ta fito bata samu tayi shirin bacci ba tayi kwance  kmr wata marar lafiya don haka kawai abubuwan da suka faru a yau ta shiga jin kewar baffanta sosai.
   Nan mohd ya shigo d'akin cikin shirin sa na bacci sae zuba qamshi yake yaje kusa da ita ya zauna ta tashi a hnkli taje zuwa jikin sa tare da kwantar da kanta a qirjinsa tana shaqar qamshin turaren sa mohd ya d'ago fuskarta yana kallon idanun ta dake son fitar da qwalla yace"kar kiyi kuka gaya min mene ne kinji"
  Sae da ta maida kanta a qirjinsa ta kwantar snn tace"ba komai"
  shiru yayi bae sake ce mata komai ba dan ya fahimci damuwar  baffanta ce a tare da ita ,
 yasan da ya matsa mata zata iya fashe masa da kuka shi kuma ba son kukan nata yake ba.
   Nan yakai  hannu sa a hankali yana shafa bayanta d'akin yayi tsit kmr ba kowa sae can mohd yace"tashi muje d'akina kinji"
  Nan ta janye jikinta daga nashi zata tashi dmn d'auko kayan bacci mohd yace"yi zamanki bari na d'auko maki "
  Nan ya tashi ya ciro mata rigar bacci a cikin wardrobe yaje ya sa mata rigar da kanshi snn yaja ta suka tafi d'akin shi.

  washe gari Ryynt ce rungume a jikin man sun fito bathroom sae kuka take tana yarfi da hannu tana d'ingishi man dake janye da ita duk ya damu sae faman rarrashin ta yake har suka je kan bed ya zaunar da ita ta jawo blanket ta rufe jikinta sbd ba komai a jikin nata haka ma man wanda bae damu da ya rufa jikin nasa ba sae qafar ta ya riqo yana dubawa wacce ta fad'i kan qafar ne a bathroom ,
yakai  hannu a hnkli yana ja mata qafar amma hakan bae hana ta fasa ihu ta qanqame shi sosai tana kuka duk sae mohd ya qara shiga damuwa amma hkn ya dake yaci gaba da ja mata qafar sae kuka take tana roqon ya daina bae daina ba sae da ya tabbatar yaja qafar yanda ya dace snn ya tashi ya d'auko wani  magani ya shafa mata a nn fa Ryynt ta soma wani  kukan dan maganin ba qaramin zafi ne dashi ba mohd ya rungume ta a jikin sa sae rarrashinta yake yana shafa mata qafar har zafin maganin ya rage ta daina kuka sae
lafewa tayi sosai a jikin sa tana shafa sumar qirjin sa a hankali.
  Mohd ya d'ago fuskarta yasa bayan hannun sa yana share mata hawaye kasancewar baya son saka mata yajin maganin da ya shafa mata a qafa.
   Yace"sannu ina zuwa kinji"
 Ta gyad'a masa kai yayinda ya tashi ya nemo boxer yasa snn ya saka jallabiya ya nufi bathroom ya wanke hannun sa ya fita.
  Bae zarce koina ba sae d'akinta ya nemo mata kayan sawa ya fito riqe dasu a hannun shi sae ga malika ta fito daga 6angarenta ta bisa da ido le6ace da baki tana kallon sa har ya wuce taje ta zauna kan kujerar dining sae wani abu take ji a ranta na baqin ciki wae yau man ne ke kula wnn abar ba ita ba har ma kayan sawa shike d'auko mata abinda bae ta6a mata ba ko lokacinda sukayi soyayyar su ta amarci nn kawae taji qwallah sun ciko tap a idonta bata bar sun fito ba ta had'iye su takai hannu tana shafa cikinta cike da shu'umin murmushi kafin take zubawa kanta abincin breakfasts ta soma ci jim kad'an da fara cin abincin nata sae ga man ya fito tana kallo ya d'ibar musu abincin breakfast shida Ryynt ya koma daga ciki ba tare ta iya ce masa komai ba sae binsa da kallo tayi tace"hm aikin banza"
   Nan taci gaba da breakfast d'inta ita kad'ae sbd mami dae tana school alawiyya kuwa har d'aki kuku ke kai mata nata.
 Cikin qunci sosai take breakfast d'in dan da qyar ma abincin ke wuce mata qarshe ma kasa ida cin abincin tayi ta tashi cike da tunanin bata jin zata iya ci gaba da ganin wnn baqin cikin ya zama dole tasa qiyaya tsakanin Ryynt da man yayinda man zae dinga tsanàr Ryynt har zuwa lokacin haifuwar ta wato lokacin da ita kuma zata samu ta cika burinta ba tare da ta sake ganin wani baqin cikin ba tayi sallama dashi har abada.
    2 weeks later tun a washe garin rnr kuwa malika tayi nasarar had'a qiyaya tsakanin man da Ryynt ta hanyar sawa man garin magani a abinci wanda taje ta kar6o wani qauye gurin boka ita da qawar ta fa'iza.
 yanzu ya kasance kwata kwata man ba ruwansa da Ryynt sae tsana mae qarfi da ta shiga tsakanin sa da ita dashi kansa bae san dalilin tsanar ba,bare ita Ryynt da kullum cikin kuka take tana roqon ya gaya mata idan wani laifi ta masa ta bashi haquri amma komai baya ce mata sae muguwar tsawa da yake korarta da ita wani  lokacin ma har dukan ta sae da ya tashi yi shiyasa tun da daga rnr bata sake tunkarar sa ba,kuma bata snr da kowa halin da take ciki ba sae ubangiji ta barwa komai ta duqufa ba dare ba rana tana kai kukanta a gurin ubangiji tana roqon ya kawo mata sauqi a cikin gaggawa dmn sati biyun nn da man ya kwashe yana nuna mata tsana sae taji tmkr shekara biyu ne shiyasa duk ta rame ta zama abin tausayi don kullum bata da aiki sae na kuka ga wani  irin girma da cikinta ke ci gaba da yi da kuma nauyi.
  A gurin malika kuwa duk da cewa still man bae damu da ita ba wani irin farin ciki take ciki sosae na ganin tayi nasara har ma ji take yanzu bata da wani sauran baqin ciki a rayuwar ta don ganin take shikenan tayi nasara man ba zae sake kula ryynt ba har ta kai ga cika burin ta.



Billy giro😊
```🔮BAZAN BARSHI BA🔮```














                    🔮🔮🔮
*page 87*
Haka Ryynt taci gaba da rayuwa a cikin gidan har aka sake kwashe sati d'aya bata fita koina daga d'akinta sae d'akinta har abinci bata fita ci sae dae tasa kuku ya kawo mata dan ita tsoron mohd ma take ji yanzu bata ko son had'uwa da shi don ko da kuskure ta kalle sa sae ya watsa mata mugun kallo.
  Washe gari ta tashi da wani  irin zazza6i mae qarfi ta yini haka komai bata iyayi sae alawiyya ce ke d'an kula da ita wacce taso a snr da mohd Ryynt tace a'a dan ta fahimci alwiyya bata san abinda ake ciki ba.
  Kwanan ta biyu tana fama da rashin lafiya a na ukun ne taji sauqi sosai dan komai tana iya yiwa kanta qarfin jikinta ne kawae bae gama dawo mata ba.
  Da yamma bayan la'asar tana zaune kan darduma riqe da qur'ani tana karatu sae ga mami ta shigo d'akin aguje tace"Anti yaya Nasir na kira ku gaisa"
  Ryynt ta tashi riqe da hannun mami suka fito   Nasir na zaune shida mohd kan doguwar kujera yayinda mohd ke riqe da laptop yana wani  aiki wanda yana ganin Ryynt ya tashi ya bar gurin byn yace da Nasir idan kaje ka gaida inna.
  Nasir yace "za taji"
Yayinda Ryynt tayi qoqarin had'iye hawayen  dake son fito mata ta shiga gaida nasir, nasir ya amsa gaisuwar yana kallon ta da kulawa dan ya fahimci da kmr akwai damuwa a tattare da ita har dae yanda yaga ta rame nn ya bawa mami makullin motar sa yace je d'auko ice cream a mota mami ta kar6i key ta tafi aguje sae murna take tana tsalle a natse nasir dake kallon Ryynt yace"me yake damunki ne Ryynt?
 Ryynt tayi saurin girgiza kanta tace"ba komai"
  Yace"amma kuma kika rame da yawa haka ko dae ba kya son gaya min abinda ke faruwa ne"
  Ryynt tayi d'an guntun murmushi tace"ba haka bane nayi zazza6i ne kwana biyu"
  Yace"Eyyah Allah sarki to ya jikin?
  Tace" Alhmdlh ae naji sauqi sosai"
  Ta qarashe mgnr ne yayinda mami ta dawo riqe da ledar ice cream,Nasir ya kar6i makullin motar sa yace"to ni na tafi Allah ya bida lafiya tace"Amin"
snn ya tafi ita kuma taja mami suka koma daga ciki suna shiga mami ta bata  d'ayar robar ice cream dan guda biyu ne Ryynt tace"Aa kaiwa alawiyya dae idan zata sha .
Mami na fita Ryynt ta zauna tare da d'aura hannun ta akan cikin ta sae kallon cikin take tana shafa shi  a hankali tana sauraren yanda cikin ke motsi yayinda hawaye ke silalowa a hnkli kan fuskarta dan tayi kewar kulawar mohd ba kad'an ba.
  Bayan kwana biyu da faruwar haka guraren  qarfe goma sha biyu na dare Ryynt na kwance tana bacci kan darduma riqe da littafin addu'o'i a hannunta,
 a cikin baccin nata ne ta soma jin daddad'an qamshin turaren mohd yana shiga  hancin ta nn ta soma bud'e idanun ta a hankali har ta sauke su akan mohd dake durqushe a gabanta d'auke da qwallah tap a idon sa sae kallon yanda ta rame yake.
A d'an tsorace ta tashi zaune tana kallon sa sae ganin tayi ya tafi da ita zuwa jikin sa ya rungume ta sosai a jikin sa sae kuka ya fashe dashi yana bata haquri kan abubuwan da ya mata dashi kansa baisan dalili ba Ryynt dae bata ce komai ba sae kuka ta fashe dashi itama yana ta rarrashinta har ya samu tayi shiru ya cire mata hijab tare da d'aura hannun sa akan tulun cikinta yana kallon yanda cikin nata ya qara girma bae ce komai ba sae kallon yanda ta rame yake cike da tausayi don har sae da idanun sa suka ciko da qwallah yace"my Ryynt dan Allah ki yafe min wlh bansan ya akayi ba haka kawae naji na tsane ki amma bayin kaina bane wlh i don't know why"
 Ya qarashe mgnr ne yayinda hawaye suka gangaro kan fuskar sa.
  Ryynt da bata kawo zargin kowa a ranta ba tasa hannu ta share masa hawaye snn ta kwantar da kansa a qirjin ta tace"ba komai Mk sharrin shaitan ne da baya son ganin ma'aurata cikin shiri kuma inshaa Allah ba zae sake yin galaba akan mu ba.
    Nan mohd ya maida ta kan qirjin sa ya kwantar ya lumshe idanun sa sae shafa bayanta yake haka itama idanun ta a lumshe suke tana shafa sumar qijinsa a hankali sbd rigar da ke jikin sa a bud'e take.
   Haka suka kwana abinsu har safe baccin da Ryynt taji kmr kar ta farka sbd ta jima batayi bacci mae dad'i irin sa ba.

 Guraren qarfe tara na safiyar rnr Ryynt ce ta shigo d'akin mohd cikin doguwar rigar ta mae kyau ta atamfa ta sami mohd d'aure da towel ya fito daga wanka knn yayi tsaye sae kallonta yake tayi dan sosai tayi kyau duk da ramar da take d'auke da ita kuwa.
  Bata iya qarasawa ba sae sadda kanta tayi qasa dan haka kawae taji tana jin kunyar sa sae mohd d'in ne ya qaraso da kanshi gurinta ya kai lips d'insa a hnkli kan goshinta ya d'aura mata kiss,a nn ta mishi ina kwana ya amsa tare da jan hannunta suka je kan bed suka zauna yakai hannu sae shafa cikinta yake yana kallonta yace"babyna yana lafiya?
  Ta gyad'a masa kai tare da kwanciya kan qirjin sa takai hannu tana shafa sumar qirjinsa da ta kwanta luf abin sha'awa.
  Mohd kuwa d'ankwalin kanta ya ture yana shafa  gashin kanta da yasha gyara har ma yana fitar da wani daddad'an qamshin da kai tsaye mohd ya soma jin kansa a kasala ya lumshe ido sae shaqar qamshin yake yana ci gaba da shafa sumar a hankali,  Ryynt na jinsa har ya soma wuce gun dan zip d'in rigarta ya zuge sae shafa jikinta yake ta koina yana kissin d'inta bata hana shi ba ta bada kai suka shiga romancing d'in juna kamar zasu kashe kansu har suka lula duniyar ma'aurata wacce suka ji dad'inta ba kad'an ba.

Tun daga rnr wata irin tsabar kulawa da soyayya mohd ke nunawa Ryynt wacce tafi ta farko ma dan duk rnr girkinta zaka gansu harabar gidan gurin shan iska manne da juna sae soye wa suke tayi abinsu kmr wasu Luv birds.
Malika kuwa tun da ta fahimci sun dawo da shirin su ba yanda batayi ba na ganin ta wargaza shirin ta hanyar sake zubawa man garin magani a abinci amma abu ya faskara sbd still Ryynt batayi sake da nafilfili da addu'o'in da takeyi ba dare da rana.
   Kan dole malika ta gaji ta daina zuba masa maganin cike da nadamar ina ma tun farko bata soma ba dan gashi yanzu shirin da sukeyi ma yafi na daa yayinda ita kuma ta qara dawowa kwandon shara.

Sannu sannu lokaci keta tafiya dmn yanzu cikin Ryynt ya shigo cikin wata na tara yayinda cikinta yayi wani  irin girman gaske da duk wanda ya ganta sae ya tausaya mata don ta ma daina fita koina ko downstairs ma sae da taimakon mohd take iya saukowa wanda yanzu kwata kwata mohd bashi da wani  aiki sae na kula da ita  hatta office ma ya daina zuwa ya barwa Amir da Aamil ragamar kula da asibitin dan shi yanzu ta Ryynt yake wacce duk safe da yamma sae ya fita da ita a cikin harabar gidan ya sata su zagoya gidan kaf duk fad'in sa kuwa.
  Hakan duk yafi qona ran malika dan duk tulun cikin da ke gaban Ryynt bae hana man ya d'auki abar sa idan ta gaji da zagayawar ya tafi da ita gun resting chairs ya zaunar kan kujera ya kuma tsiyaya mata fresh milk mae sanyi a cup ya bata tana sha shi kuma ya shimfid'a handkerchief a qasa ya zauna ya kama qafafunta ya d'aura kan jikinsa yana matsa mata su cike da so da kulawa.

Ranar lahadi da dare guraren qarfe tara mohd ne jikin wardrobe yana ciro tufafi sae ga Ryynt ta shigo d'akin cikin shirin ta na bacci mohd yazo da saurin sa yaja hannunta yaje da ita kan bed ya zaunar da ita ya ciro farin handkerchief yana share mata zufar da ya gani a kan goshinta d'auke da damuwa a fuskar sa yace"Ryynt meyasa kika fito da kanki baki kirani a waya nazo ba"
   Tace"na kira wayar ka ban samu ba kuma gashi ina son in fito"
  Kallon ta mohd yayi cike da tausayi dan yasan da qyar ne ta iya saukowa don gashi sae numfashi ma take ta fitarwa sae duk yaji kamar ya cire cikin ya maida a jikin sa amma ba yanda zae yi tunda abune da bazae yiyu ba hkn ya tashi ya tsiyayo mata ruwa masu sanyi a glass cup ya zauna ya bata tasha snn yasa ruwan a handkerchief ya d'an jiqa shi yana share mata goshinta,fuskarta har zuwa qirjinta.
   Ryynt dake kallon sa tace"ina zaka tafi da daren nn naga kana ciro kaya?
    Yace"tafiya ce ta kamani Ryynt"
  Kmr zata yi kuka tace"zuwa ina?
  Yace"Abuja zan tafi"
 Tace"zan bika"
  Cikin muryar rarrashi yace"my Ryynt kinsan ba zae yiyu ba kiyi haquri ae kwana biyu kawae zanyi kinji"
  Tace"to ka kaini gidan inna in ka dawo sae ka d'auko ni"
   Yace"No my Ryynt ga alawiyya ae zata riqa taimaka maki da wasu abubuwan kinji yi haquri"
   Kallon sa tayi qwallah tap a idonta yayi saurin girgiza kansa yace"yi haquri dan Allah kar kiyi kuka kinji ba jimawa zanyi ba 2dayz ne fa kawae"
    Da qyar Ryynt ta iya had'iye hawayen ta snn ta gyad'a masa kae.
  Mohd ya rungume ta a jikin sa yana qara rarrashinta.

Washe gari tun da safe mohd ya tafi ya bar Ryynt sae kuka take wanda ba irin rarrashin da bae mata ba amma taqi shiru hkn ya tafi ba a son ransa ba wanda ba don tafiyar ta zamar masa dole ba da ya fasa.
  Malika kuwa ba kad'an ba taji dad'in tafiyar sa sbd wani tunanin da ya fad'o mata a rae da zata samu tacika burinta kafin ya dawo shiyasa yana barin gidan tasa qafa ta fita.
    Bata wani  jima sosai ba ta dawo bata zarce koina ba sae d'akin Ryynt bata shiga ba ta la6e tana jiyo sautin kukan Ryynt a hankali dan har lokacin bata daina kuka ba.
  Le6ace da baki malika ta baro qofar tana mae fad'in"wae ke miji dad'i zaki ci ubanki an jima don wlh sae kinyi naqudar baki shirya ba"

 Da dare ta sake dawowa ta samu Ryynt na bathroom tana wanka mami kuwa har tayi bacci.
  Kai tsaye ta nufi fridge har zata bud'e ta hango ruwa da cup a ajiye kan bedside drawer nn taje da sauri ta bud'e gorar ruwan ta saka wani tablet qwara biyu a ciki ta shiga jijjiga gorar ruwan har maganin ya narke tsaf snn ta ajiye ta fita ta la6e a bakin qofar d'akin ta jira har sae da Ryynt ta fito daga wanka tana kallo Ryynt ta tafi kae tsaye gun bedside drawer ta tsiyaya ruwa a cup tasha snn ta nufi dressing mirror ta zauna tana shafa Vaseline.

Nan Malika ta bar qofar d'akin cike da murna ta kira fa'iza tace"tayani murna fa'iza wnn abar dae tasha maganin"
Fa'iza tace"dagaske?
 Malika tace"wlh kuwa a gaban idona ina kallo tasha nasan ko ta kira kafin dae azo a tafi da ita asibiti abinda ke ciki ya gama hallakewa ita kuma kin san sauran"
  Nan fa'iza ta fashe da dariya tace"aikin ki na kyau malika kika ce dae gobe akwai labari mae dad'i"
  Malika tace"hm bari kawae kedai zan kiraki goben"
  Daga nan ta katse wayar.


Ryynt kuwa lafiya lau ta gama shirinta na bacci mohd ya kirata a waya suka jima suna waya bayan sun gama wayar ne snn ta kwanta bacci a cikin baccinta ne wani irin ciwon baya ya farkadda ita wacce tun tana jin abun sannu sannu har abun ya soma yawa sae juyi take ta kasa komawa bacci.
  A gurin mohd ma haka ta kasance don yana cikin baccin sa  haka kawae yaga ya farka ya kuma rasa me ke masa dad'i sae tuñanin Ryynt da yake.
  Nan kawae ya jawo wayar sa ya kira ta ba tare da ya damu da ganin ko qarfe nawa na dare ba shidae yaji lafiyar ta.
  Ryynt da har ta zame kan bed tana durqushe kan guiwoyinta cikin matsanancin hali taji wayarta ta soma ring ganin mohd ne mea  kiran yasa ta iya d'aga kiran amma kuma ta kasa cewa komai sae mohd ne keta magana bata iya bashi amsa.






Billy giro😊
```🔮BAZAN BARSHI BA🔮```














                    🔮🔮🔮
*page 88*
 Sae can Ryynt ta samu da qyar tace"Mk bana jin dad'i ka bari da safe mayi waya"
Daga haka bata jira me zae ce ba ta katse kiran ta ajiye waya ta soma kuka a hnkli sbd zafin ciyon abinda take ji ya soma kaita maqura.
  Mohd kuwa duk ya rud'e sae kiranta yake tayi amma bata d'aga ba nn kawai ya kira Nasir da inna ya sanar dasu halin da ake ciki.
   A cikin daren Nasir  ya tashi ya shirya yaje ya d'auko inna suka zo gidan.
 Kai tsaye suka nufi d'akin Ryynt Nasir ya tsaya a bakin qofa inna ta shiga daga ciki ta sami Ryynt kwance  cikin jini duk ta galabaita sae kuka take a wahal ce tana juyi a qasan tiles d'in d'akin.
 A rud'e Inna ta qwalawa Nasir kira ya shigo d'akin wanda bae tsaya wata wata ba ya kama Ryynt inna ta kama masa suka fito da ita suka saka ta a mota ,
inna ta zauna baya tare da ita Nasir yaja motor a gaggauce suka bar gidan.
Nan itama malika ta fito ta shiga motar ta ta bisu dan tun shigowar su gidan tana sane asali ma ita da kanta ta bud'e musu qofa a lokacinda taji suna knocking.
  Man hospital suka nufa ta parker motar ta tayi zamanta a ciki tana kallo aka shiga da Ryynt ta saki shu'umin murmushi d'auke da chewing gum a bakinta tana taunawa ta d'auki wayarta ta kira fa'iza ring d'aya biyu sae ga fa'iza ta d'aga ,
malika tace"au bakiyi bacci ba knn"
  Fa'iza tace" inafa hubby bae barni ba kinsan yau ya dawo daga tafiya da qyar ma na samu ya saurara min yanzu haka ma yana bathroom yana wanka sae dae kuma ke ya akayi bakiyi bacci ba har yanzu?
  Hm lallai fa'iza har kya tambaya ae yau banga ta bacci ba sae komai ya gama faruwa a gaban idona tukun don yanzu har wnn abar ta kira wnn tsofuwar da ake kira inna sun zo ita da Nasir suka kawo ta asibiti shine na biyosu sae kallon su kawae nake dan na tabbatar ba abinda likitawan zasu iya mata don kafin ma su iya yin komai abinda ke ciki ya riga ya gama hallakewa haka itama  zafin aikin maganin da wahalar naquda bazai bar ma ta rayu ba don kan aje koina ma har ta fara bleeding"
Fa'iza tace"Au haba?
 Malika tace"Wlh kuwa ae overdose na had'a mata maganin ynx jira kawae nake in ga an fito da gawar er banza.
    Fa'iza tace"kae kinyi dae dae wlh,
 ashe koni banga ta bacci ba yau sae dae najira kiran wayarki dmn naji kyakkyawan labari"
  Malika tace"lallai
dae kam ki saurari kirana ko yaushe don yau kan farin ciki ma har sadaka sae nayi abinda ban ta6a yi ba a rayuwata kuwa"
 Fa'iza tayi er dariya tace"kinga bye sae kin kirani dan naji alamar hubby zae fito daga bathroom baccin qarya nake so zanyi dan nasan halinsa in yaga ban koma bacci ba ko yayi wanka wlh zai iya sake nemana a second round"
 Malika tayi er dariya tace"ae kima yi baccinki dan koni idan naga zasu 6ata min time gida zan koma dole dae da safe zanji labari don mutuwa dae ba 6oyuwa take ba kawae dae ki saurari kirana"
  Fa'iza ta fashe da dariya tace"kae malika bakida dama wlh"
 Malika tace"uhm kedai sae anijma"
 nn suka katse wayar.
  Daga nn ma kawai malika taja motar ta ta koma gida.

Ryynt kuwa har washe gari ba kanta sae wahala da take ta faman yi ita bata haifu ba ga jinin yaqi tsayi duk da irin taimakon da nurses keta bata kuwa.
  Guraren qarfe goma sae ga mohd ya diro asibitin da kallo d'aya zakayi masa kasan hankalin sa a tashe yake.
Ya sami inna da Nasir still su kad'ai ne a asibitin ba wani  wanda yazo dan ba'a sanar da kowa ba tukun sae anga yanda abun ya kasance.
  Yace dasu"ya ake ciki ne dan Allah ina Ryynt d'in take in ganta?
  Kafin suce komai sae ga wata likita ta fito tana ganin mohd tace"yauwa Dr ur wife tana cikin wani  yanayi gabad'aya ta galabaita sam bata iya pushing any more da kamar sae an mata aiki"
  A rud'e Mohd yace"muje in ganta"
 Nan suka tafi kai tsaye se d'akin da Ryynt take wacce ke kwance kan gadon haifuwa abin tausayi duk ta wahala mohd ya nufi gurinta kmr zae yi kuka yana kallon yanda take bleeding a fusace ya kalli nurses d'inda da ke kan Ryynt yace"wane irin abune haka kun bar min ita sae bleeding take kuma kun kasa fitar min da babies d'ina so kuke su mutu ne ko yaya!
 Likitar da suka shigo tare da shi tace"Sory Dr wlh it's not our fault haka aka kawo mana ita kuma munyi iya qoqarin mu amma abu ya faskara kawae abinda na fahimta ba time d'in haifuwar ta bane da akwai maganin da tasha da ya mata qarfi har ya tashi naqudar shiyasa ta wahala har ma abinda ke ciki duk ya galaibata baya iya yunqurin fitowa"
  Kwalla tap a idonsa ya kalli ryynt wacce ke kallon sa ta kama hannun sa ta riqe gam a cikin nata cikin muryar kuka tace"Mk zan mutu"
 Da sauri ya girgiza kansa yana mae share mata zufar goshinta da d'ayan hannun sa yace"Baza ki mutu ba my  Ryynt ki nisa inshaa Allah yanzun zaki haifu kinji"
  Ryynt da ko numfashin kirki bata iya yi muryar ta na rawa tace"Mk bazan iya ba mutuwa ma zanyi na sani"
  Girgiza kansa yayi had'e da saurin kai hannu yana share mata hawayen da ke sauka kan fuskarta yace"um um my ryynt inshaa Allah baza ki mutu ba ki daina fad'ar haka dan Allah"
  Tace"uhm uhm mk nayi qanqanta da haifuwa ka sani  kuma wnn qaton cikin bansan ma ya zan iya haifo abinda ke ciki ba"
Yace"my Ryynt Allah zae taimake ki kawae rufe idonki ki nisa kinji dan Allah"
  Ba musu ta rufe idanunta a hnkli tayi iya qoqarin ta na ganin ta nisa amma ta kasa sae kuka ta fashe masa dashi muryar ta na rawa tace"bazan iya ba mk dan Allah kiramin inna in ganta dan Allah"
   Nan mohd yasa aka kira mata inna tazo Ryynt ta kama hannun inna sae kuka take tana roqon inna ta yafe mata mutuwa zatayi inna ta shiga rarrashinta tana mata  addu'a tana tofa mata man kuwa duk yabi ya rud'e komai ya kasa yi sae shafar goshin Ryynt yake yana ta rarrashin ta wacce ta soma salati tana qoqarin miqewa sbd wata irin azaba da ta soma ji ta koma da qarfi ta saki hannun inna ta kama hannun mohd sae kuka take tana roqon ya yafe mata ga kuma salatin da take ta faman yi a bakinta yayinda take ta faman qoqarin miqewa man yana maida ta sae addu'a yake ta mata dan ya fahimci haifuwar tazo mata gab.
Da qarfin tsiya Ryynt ta qara riqe masa hannu sbd wani irin nishi mae qarfi da yazo mata a nn man yayi qoqarin cire hannun sa daga nata yaje da sauri yana bata taimako ta hanyar sa hannun sa ya soma ciro 'ya'yan sa d'aya bayan d'aya santala santala dasu biyu maza mace d'aya kuma kowanen su cikin qoshin lafiya.


Plz sorry 4 diz one

Billy giro😊```🔮BAZAN BARSHI BA🔮```














                    🔮🔮🔮
*page 89*
A take nurses suka kar6i yaran dmn zuwa gyara su.
  Cikin tsananin murna inna ta fita ta snr da Nasir abinda aka haifa.
  Mohd kuwa ya kama Ryynt sae kissing d'inta yake yana mata sannu ita kuwa sae kallon sa kawae take qwalla tap a idonta.
  Mohd da kanshi ya gyarawa Ryynt jikinta snn aka tafi da ita d'akin hutawa.
  Nasir kuwa a lokacinda inna ta snr dashi ba qaramin farin ciki yaji ba wanda a nn take ya ciro wayar sa ya kira family house ya snr dasu.
  Snn suka tafi d'akin da aka kae Ryynt sae barka suke mata  shida inna suna mata sannu ,da aka shirya yaran aka kawo musu inna ta kar6i yaran d'aya bayan d'aya sae rawa take tana murna tana godewa ubangiji.
  Haka ma Nasir bae yi rawa ba dae ya kar6i yaran cikin tsananin murna yana ta kallon su snn ya bawa mohd wanda bakin sa har kunne sae kallon kya wawan yaran sa yake da sak mazan shi suka biyo macen kuwa kamar an tsaga kara ita da Ryynt sae dae hasken duk na mohd ne.
  Cike da so mohd ke kallon Ryynt yana nuna mata 'ya'yan su Ryyñt ta kalle su kawae bata ce komai ba shi kuma yayi zaune yana wa yaran sa addu'a.
  A nn cikin asibitin mohd yasa aka had'awa Ryynt tea mae kauri tasha.
  Basu bar asibitin ba sae ga mahaifiyar mohd tazo it da umman saliha.
   Murna a gurin su ba'a cewa komai musamman mahaifiyar mohd da wani  tsabar son Ryynt ya qara shiga ranta da duk motsi idan Ryynt tayi sae tace ya akayi ne Ryynt ba abinda ke maki ciwo dae ko, ko kina buqatar wani abu ne a kawo maki.
   Ryynt kuwa kae kawae take girgiza mata d'auke da jin dad'in yau itace ke samun kulawa haka sosai a gun mahaifiyar mohd duk da cewa tuni ta fara samun kulawa a gurinta amma yau kulawar ta daban ce da kowa na cikin d'akin sae da yaji dad'in hakan musamman mohd wanda sae kiran wayar sa ake ana masa barka dan ba family ba har en uwa da abokan arziki duk an sanar dasu.

Sae da Ryynt ta sami hutu aka kuma tabbatar she is ok ba wata matsala snn suka nufi gida.
  Gidan man suka nufa kmr yanda ya buqata snn ko za'a tafi gidan inna daga baya.
   Suna shiga gidan da gud'a inna ta fito mota tana taka rawa dan farin cikin da take ciki ya ma wuce misali kuma irin tsafin nn ne da basa iya 6oye farin cikin su a koina.

  Malika ta fito daga kitchen knn riqe da plate da abinci akai yayinda d'ayan hannun ta ke riqe da glass cup da ruwan lemu a ciki.
  Ta tsaya cak tana sauraren ina ne gud'a ke fitowa.
  Kafin ta iya yin komai sae gasu sun shigo falon ba shiri ta saki plate da glass cup d'inda ke hannun ta tayi saurin dafe mararta da taji ta wani  irin tsinka mata sae ga jini agurguje yana fitowa ta qafafunta yàyindà ta saki ido tana kallon Ryynt da suka fara shigowa ita da man tsaye a qafafuwanta lafiyar ta qalau ga kuma jarirae uku da ta gani a hannun su umma da inna wacce still sae gud'a take ci gaba dayi shiyasa da kmr ba wanda ya lura da malika a cikin su bare zancen jin qarar fashewar glass cup da plate d'inda ta yar har suka haura sama zuwa d'akin Ryynt.
   Malika kuwa kmr wata zautatta ta nufi hanyar d'akinta ba tare da ta lura da jinin dake ci gaba da fita a jikinta ba har ta isa d'aki ta d'auki wayar ta kai tsaye ta kira fa'iza muryar ta na rawa tace"Wayyo Allah fa'iza na shiga uku wlh wnn abar bata mutu ba haka ma abinda ke cikinta da ta haifo har su uku"
  Da qarfi fai'za tace"what! she is still a live fa kikace! kuma ta haifo en uku hm never ga dukkan alama tashin ki knn daga bacci kinyi mafarki shine kika zo kina gaya"
 Malika tace"wlh maganar gaskiya nake gaya miki fa'iza yanzun nn suka shigo da ita har da yaran"
  Hm!plan ne kawai suka had'a maki malika dan inaga akwai wanda ya ganki a lokacin da zaki saka mata wnn maganin"
 No fa'iza na tabbatar wlh ba wanda ya ganni a lokacin da nake saka mata maganin dan duk yaran da take tare dasu sunyi bacci  kuma man baya ko gari kin sani.
  Faiza tace"malika ki yarda da zance na wnn maganin qarfin tsiya ne dashi kuma kince kin had'a mata overdose snn young girl like her ace ta haifi yara har uku haba ae hankali hanji ne wa ita nn"
 Hm fa'iza na gaya miki fa a gaban idona wlh ina la6e ina kallo tasha ruwan da na saka mata maganin a ciki snn girman cikinta kad'ae ya isa na yarda cewa ita ta haifi yaran, at all yanzu nasan shike nn ta gama saye min miji"
  Ta qarashe mgnr ne cike da qwallah tap a idonta.
 Fa'iza tace"ae wlh bata isa ba tayi kad'an"
 Qwalar da suka taru a idonta ne suka zubo cikin muryar ta mae d'auke da rawar kuka tace"to yanzu fa'iza me kike ganin zanyi wanda zanci riba a kanta kuma, na farko na xubar da ciki na a banza wanda da yanzu qila ma nice na haifa masa yaran,na biyu maganin da muka kar6o a qauye gurin boka na sawa man a abinci dmn ya tsaneta har ya fara aiki yazo ya karye kuma tun daga lokacin maganin bae sake ci ba yanzu na sa mata maganin da nake ganin da ita har abinda ke cikinta ba wanda zae yi survive amma sae gashi she is still a live an dawo da ita lafiya qalau da ita har yaran,known fa'iza how can i do, me kuma ya rage da zan mata yanzu .
  Fa'ixa tace"wlh baza mu barta ba sae kin dawo da mijinki hannun ki ,ki shirya yanzu yanzu nn kizo gidana muje wani qauye gurin wani shaharren boka aikin sa kmr yanka wuqa yau yau d'in nn sae a neme ta a rasa da ita har 'ya'yan kuwa kuma sae a lafira ko za'a ganta ta wlh dan nasan wacce tasa akayiwa kishiyarta haka kuma har yau mgnr da ake shekara uku da suka wuce ba ita ba labarinta har iyayenta sun haqura da nema.
  Malika tayi saurin share hawayenta tace"shikenan gani nn zuwa yanzun.
    Nan ta tsinke wayar had'e da juyowa cikin hanzari sae kawae ta tsaya cak ko tako d'aya ta kasa yi tana kallon man dake tsaye a bakin qofa ga kuma jinin da ta hango tun daga wajen qofar har zuwa inda take tsaye a lokacin suma ne kawae bata yi ba ta dasqare guri d'aya dan tasan tata ta qare man ya gama jin komai dan jikin sa har rawa yake kan tsananin 6acin rae ga wani irin mugun kallo da yake mata har ya qaraso gareta wanda kae tsaya ya kai hannu kan qugun sa ya zaro belt d'in wandon sa a nn malika tayi saurin durqusawa kan guiwoyinta ta kama qafafunsa sae girgiza kanta take tana fad'in"my man dan girmañ Allah kayi haquri wlh kasan duk abinda nakeyi a dalilin sonda nake maka ne dan Allah kayi adalci akan hukuncin da zaka min na roqeka"

 Da qarfin tsiya man ya ture ta ba tare da yace mata komai ba sae zabgar ta da ya fara yi ta shiga ihu tana roqon yayi haquri amma ina kmr ma ziga shi take qara yi dan sae dukanta yake ci gaba dayi ta koina baji ba gani ita kuma bata fasa ihu tana bashi haquri ba.
Ganin yana neman hallaka ta yasa ta fito d'akin aguje yana biye da ita yana duka har suka sauko downstairs zuwa falo aguje ta nufi hanyar fita ya fizgota yana ci gaba da dukanta sae ihu take sosai tana bashi haquri.
  Sae gasu umma sun fito gabad'ayan su suna tambayar sa lafiya me yake faruwa bae basu amsa ba sae aikin ci gaba da dukan ta yake nn Nasir da shigowar sa knn ya samu da qyar ya riqe mohd wanda sae faman huci yake yana kallon malika da duk ya farfasa mata jiki,cikin 6aciñ randa yake d'auke dashi ya nunata da yatsa yace"kije na sake saki uku kuma yanzun yanzun nn fita a nn in daina ganin wlh"
   Subuhanalillah!
Shine abinda su umma da nasir suka fad'a inna kuwa sae salati ta soma yi,
 Ryynt bata iya cewa komai ba sae kallon malika take da ta d'oro hannu akae ta fashe da wani irin matsanancin kuka mae cike da nadamar abubuwan da ta aikata"
   Tazo gabanta tana kuka sosai ta kama qafafuwan ta tace"Dan Allah Ryynt ki roqa min shi ya janye sakin wlh bazan sake yunqurin cutar da ke ba na rantse"
 Ryynt bata iya cewa komai ba sae mohd ne yazo yaja malika ya tafi da ita qiiiiiii kmr kayan banza ya tura ta waje ya rufe qofa sae kuka take tana dukan qofar tana bashi haquri  da qarshe ta gaji ta zame jikin qofar tana ci gaba da matsanan cin kukan da take tunanin shike nn rayuwarta ta lalace ta rasa mohd a rnr da take tunanin rnr farin ciki ce a gurinta amma ta zamo mata rnr baqin ciki mafi soyuwa da komai ya ca6e mata har d'an cikin da take kurin ta samu wata biyu da suka wuce taqi snr dashi akan sae burinta ya gama cika ko zata snr dashi gashi ya 6are,burin bae cika ba,ga saki uku  ga kuma irin dukan da tasha, cikin ma bae ji d'aya daga cikin mugayen ayukkan da take aikatawa ba tukun.
 Rayuwa knn shiyasa aka ce idan zaka gina ramin mugunta to ka gina shi kad'an dmn wata rana zaka iya fad'awa ciki.
  Allah dae ya shirye mu yasa mu dace amin.

Mohd kuwa tun da ya fitar da malika ya rufe qofa su umma sukayo kanshi cike da son  tambayar sa abinda ke faruwa bae bar sun kae ga tambayarsa ba yayi saurin barin gurin   ya tafi zuwa d'akin sa.

  Ba yanda suka iya nan suma suka juya suka koma daga ciki amma mafaiyar mohd da Nasir fita sukayi dan dama ta kirashi ne dmn ya maida ta gida tana so zata d'an shiryawa Ryynt abincin da masu biqi ke ci.

  Bayan har inna tayi wa yaran wanka an shirya musu ita ma Ryynt umman saliha ta had'a mata ruwan zafi tayi wanka ta shirya.
  Mohd ya shigo d'akin ba tare da yace da kowa komai ba yaja hannun Ryynt ya tafi da ita d'akin shi sae kallonsa kawae ryynt keyi har ya zaunar da ita a hankali kan bed snn shima ya zauna yana kallonta ,a natse yace"still ba abinda ke maki ciwo koh?
 Ta gyad'a masa kae yace"to wa ya miki wanka?
 Murya can ciki tace"ni nayi da kaina"
 Yace"kin tabbatar kin gasa jikiñ ki da kyau kuwa?
 Ta gyad'a masa kae yace"ryt to yarana fa sun sha mamma ko har yanzu mamman bae kawo ba?
  Kallon sa tayi kmr zata yi kuka tace"ko ya kawo ya kake son na shayar dasu har su uku"
Mohd ya girgiza kansa dan tun asibiti ya fahimci fushi take tun a lokacin da ya nuna mata yaran.
  Ya d'an janyo ta zuwa jikin sa yace"yanzu Ryynt dan Allah ya azirtamu da yara har uku a lokaci d'aya shine ba kya so ga wasu sae nema suke ko d'ayan ma su samu"
  Tace"ni ba haka bane wlh d'awainiyar shayar war su ne bansan ya zanyi ba"
  Zaki iya my Ryynt kawae ki d'auki abun da sauqi kinji ae Allah ba zae d'aurawa bawa abinda yafi qarfin sa ba koh.
  Ta gyad'a masa kai tare da kwanciya kan qirjinsa tanà shafa qirjiñ nasa a hnkli snn tace"kayi haquri zan tambaye ka"
  Yace"ina jinki my Ryynt"
 Tace"me yayi zafi tsakanin ka da mtr ka da har ka mata saki uku a lokaci d'aya abinda Allah baya so"
  Yace"ki barta kawae my Ryynt so take taga bayan ki keda yarana kuma Allah ya fi ta,ni a ma daina zancen ta bana so kinji, gaya min a nn kike son zama ko gidan inna?
  Ryynt wacce tayi shiru murya can qasa tace"gidan inna mana ka sani"
 Yace"ni kuma gashi a nn nake son ki zauna shiyasa ma nayi wayon cewa a fara zowa nn gidan mu d'auki wasu kayan dan kawae na samu na lalla6i inna dmn ta zauna nn tare da mu"
  Tace"ni gaskiya um um gidan inna nake so"
  Yace"to shike nn my Ryynt amma kisani nima zan d'au jakata na bi ku sae ki la6ani a d'akin ki nida yarana"
  Ta d'ago fuskarta d'auke da d'an murmushi tana kallon sa tace"kai ma dae da wasa kake ka sani dan inna ma bazata barka  ba da kae har jakar ka  zata koro ka ne"
  Yace"to ke kuma kina kallo har ta koro ni baki ce komai ba"
    Da wasa tasha toka  tace"eh bazan hana ba sbd ni fushi ma nake da kae"
  Yace"ni d'in nn kan me to?
 Tace"sbd ka 6oye min ko yarana nawa ne a ciki na bayan rnr na gani kace min wae photon ne ya rarrabu"
   Yayi murmushi tare da jan hancin ta yace"ae halin ki na sani zaki iya hargitse min idan na gaya miki amma kinga yanxu ba yanda zakiyi"
  Tace"koh,ni koh nake da yanda zanyi dan yau ruwa kawae yaranka zasuyi ta sha bazan ba su mamma ba. 
Yace"ae kuwa dana tsulaleki da zariyar wandona dan kinsan ban had'a komai da yarana ba don haka muje ma ki basu idan kina son zaman lafiya.
 Ryynt dake kallon sa tayi murnushi tare da girgiza kanta tace"nifa kunyar su inna nake ji kuma yaran ma ana gama musu wanka sukayi bacci.
  Yace"ba wani nn ko bacci suke sae kin basu kar yunwa tayiwa yarana illa"
  Daga haka ya tashi ya fita Ryynt tabi sa da kallo d'auke da murmushi jim kad'an sae gashi ya dawo da yaransa duka uku cikin keken jarirai da ake turawa mae d'an fad'i kmr bed.
   Ryynt ta kalli yaran sae wuntsil wuntsil suke kmr zasuyi kuka tace"har sun tashi daga baccin knn"
 Mohd yace"inafa zasuyi bacci mae tsawo kin bar min su da yunwa tunda aka haife su gashi har kuka suke son su fara"
  Ryynt tace"ae ba laifi na bane mamman ne bae kawo ba kai da kanka ka sani"
   Yace"to naji ungo dae fara ba macen dan nafi ji da ita sbd kmr da kukeyi duk da dae hasken nawa ne"
  Ryynt tayi murmushi tasa hannu biyu ta kar6i jaririyar ta d'aura ta kan cinyarta yayinda d'ayan hannun ta ke tallabe da kan jaririyar d'ayan kuma yana kan mammanta na gefen dama tana qoqarin fitarwa ta qasan rigar ta,da ta fitar mohd yasa tafin hannun sa ya share mamman snn Ryynt tayi bisimillah tare da sakawa jaririyar a baki ta soma sha dan lokacin ruwan mamman ya kawo.

 Bayan sun gama shan mamman ne suka kwasa zuwa gidan inna har dasu alawiyya  da mami.
Da suka je gidan inna mutane sae zuwa barka suke tayi dan su Aamil da matan su har da pretty mtr Nasir duk sun tafi haka ma Sarah qawar Ryynt taje ita da mahaifiyar ta sbd Ryynt ta kira ta a waya ta snr da ita.


 
 Billy Giro😊
```🔮BAZAN BARSHI BA🔮```














                    🔮🔮🔮
*page 90*
Da dare Ryynt na d'akin inna ta gama shayarda yara sunyi bacci tana zaune tana shan farfesun naman kaza yayinda mohd ke zaune kan sofa yana sauraren inna dake tambayar sa abinda ya had'a sa da malika har ta kai ga saki uku.
  Nan Mohd ya gaya mata komai bae 6oye mata ba har ma zubar da cikinta da tayi ta laqawa Ryynt.
  Inna ta jinjina kae tace"cabd'i lallai wnn ba matar zama bace ja'ira gwanda da ka sake ta dan dama tun farko ni bata kwanta min a rae ba ashe kuwa da mugun nufi take ,Allah kuwa ya fita dan inshaa Allah bazata ta6a yin nasara ba har abadah.
   Mohd yace"ae har umma da Abba sun so ganin laifina akan saki ukun da na mata zama d'aya amma dana musu bayani suka fahimta har ma Abba ya bani wasu addu'oin tsari yace mu riqa yi nida Ryynt har ma da yaran mu.
 Inna tace"lallai ba'ayi sake ba Allah dae ya qara tsarewa"
  "Amin"cewar mohd wanda ya miqe tsaye yaje gun 'ya'yansa sae kallon su yake sunata sharar bacci abinsu cikin d'an qaramin gadon su da kowannen su ke kwance cikin wali.
   Sae da mohd ya gama kallon 'ya'yan sa snn ya musu sae da safe ya fita.
  Inna ta kalli Ryynt dake ci gaba da shan farfesu abinta ba alamar zata raka shi
 tace"yo ryynt ke har yanzu baki san hausar ki raka miji ba idan zae fita ae kya tashi kije ki masa sae da safe koh"
   Ryynt tayi murmushi ba tare da tace da inna komai ba ta zari tissue ta goge hannunta da bakinta ta fito ta samu mohd har ya kae qofar fita falon ya juyo yana kallonta dan yaji motsin fitowar ta,ta qaroso gurinsa yana kallon ta yace"ae har zanyi fushi dan na d'auka baza ki fito muyi sae da safe ba"
 Tace"uhm ni kuwa naga kmr ma baka ci abinci ba gashi har zaka tafi"
  Yace"to ba ke bace kikayi zaune kina shan farfesun ki baki koh taya min ba"
  Tace"eyyah ban d'auka zaka ci ba bari na d'auko maka akwai wani a kula amma na qassan naman rago ne"
 Yace"um um da wasa nake miki ni naci abinci kawae dae zan kwana da kewar ki keda yarana"
  Tace"uhm su yaran da aka haifa yau yau"
  Yace"baki san yanda nake jinsu a raina bane Ryynt da bazaki fad'i haka ba inaga ma da anyi biki zan d'auke ku ne mu koma dan bazan iya baqura ba har ayi arba'in"
  Tace"uhm kaima dae da wasa kake nida komawa gidanka sae nayi wata biyar"
   Mohd yayi er dariya tare da jan hancinta yace"da wasa kike kema dan kina wuce arba'in baki koma ba kayan mu kawae zan kwaso mana gabad'aya sae mu dawo nn da zama"
 Tace"shike nn ko inna ta sami abokan zama"
Yace"to lallai dae kam sae ki gaya mata ta tanadar min gurin da zan zauna nida matata da yarana inda zan sakata na wala ba wani wanda zae je ya takura mu"
  Tace"Aa aiko d'akinta kad'ai ya ishemu mu dukkan mu har ita sae ma ka sakata ka wala ba wanda zae hanaka"
  Mohd ya girgiza kansa d'auke da murmushi yace "kin ganki koh muyi sae da safe dan naga alamar tsokanar ki ba qarewa zatayi ba"
  Ryynt tayi murmushi yayinda mohd yakai lips d'insa kan goshinta ya d'aura mata kiss snn ya d'ago yana kallonta yace"ki shafa min kan yarana ki masu addu'a kafin ki kwanta bacci kinji"
  Ta gyad'a masa kae tare da fad'in"inshaa Allah,Allah ya tsare min kae sae da safe"
  Yace"Amin my Ryynt"
snn ya fita.
  Ita kuma ta juya ta koma daga ciki.

Washe gari fa'iza ce taje gidan su malika dmn jajanta mata abinda ya faru,ubanta baya gari sae mahaifiyar ta kad'ae da abin yayi mata zafi sosai har tana ikirarin sae tasa mohd qara kan irin dukan da yayiwa malika na fitar arziki.
 malika bata barta ba tace ta barshi kawae don ita ta jawo komai har abin yakae ga haka,kan dole  mahaifiyar ta ta bar zancen amma ba don taso ba dan ganin take ba qaramin cin zarafi akayiwa erta ba duka da saki uku a lokaci d'aya duk da cewa sane tasan abinda malika ke aikatawa na mugun nufinta akan Ryynt amma bata ga laifin ta ba sae laifin mohd da ta gani.
  Malika na kwance  sanye da drip a hannun ta fa'iza na zaune gefen ta tana mata sannu d'uke da alamar tausayawa a fuskarta tana kallon malika dake kallonta tana fitar da qwallah a idonta wacce ta bud'e bakinta a hankali tace"fa'iza wlh ina matuqar son my man bana jin zan iya rayuwa bashi amma gashi ya sake ni har saki uku ba wani  gyaran da za'ayi na koma gareshi,shike nn yanzu gabad'aya rayuwata ta lalace ko ma nace na lalata rayuwata da kaina dmn nice na janyo faruwar komai.
Ta qarashe maganar ne cikin muryar kuka sosai.
  Fa'iza ta nisa tace"malika ni kaina na tausaya miki dmn ban d'auka haka abun zae kasance ba duk a tunani na mune zamuyi nasara sae gashi Allah ya nuna mana ikon sa akan mu amma abinda nake tunani shine tunda man bae ta6a sanin kina tarayya da wani  bayan shi ba zaki iya koma masa"
  Da sauri malika tace"ta yaya fa'iza bayan saki uku ya min"
  Fa'iza tace"ta hanyar auren d'ibar wuta"
  Ni kuwa wa zan aura fa'iza?
 Sweetat d'inki mana amma kar ki yarda yasan auren d'ibar wuta zakiyi dashi kinga idan anyi auren sae ki samu hanyar da kika bi ki fito masa sae ki koma ga man d'inki.
  No fa'iza ko nayi hakan nasan my man ba zae maida ni ba ya riga da ya tsane ni.
  Hm kawai kedae kiyi abinda nace sae dai ko idan kina shakku ko sweetat d'in naki ba zae yarda ya aure ki ba koh?
  No fa'iza nasan ma zae aure ni sbd ba kad'an ba yana matuqar son kasancewa dani a ko yaushe kinga kuwa kae tsaye zae amince da aure na,matsalata d'aya shine man dana nasan ko nayi aure na fito ba zae maida ni ba.
  Fa'iza tace"kedai ki gama idda kiyi auren ki fito ni nn zan gaya miki hanyar da zaki bi har ki samu ya maida ki ba boka ba malam.
  Malika tace"nagode fa'iza da wnn shawara taki da tasa naji sanyi a raina domin bani da wani  burin da ya wuce naga cewa na koma ga my man na kuma haifa masa yara kmr yanda yake so kuma har abadah bazan sake tarayya da wani  d'a namiji ba face shi sbd bana son mu sake samun sa6ani nida shi bare zancen rabuwa.
  Fa'iza tace"that's gud tun daga yanzun ma kar ki sake bari wani  abu ya shiga tsakanin ki da sweetat d'inki har sae kunyi aure"
  Malika tace"zan kiyaye"

6angaren Ryynt kuwa kullum man na zuwa gidan kuma sosai take samun kulawa a gun inna ita da yaran ta,ga yaran sam basa da rigima kwata kwata dan ko suna farke sam basa kukan banza sae dae idan sunji yunwa suke d'anyin kuka da kuma ta basu mamma aka had'a musu da madara shike nn suyi bacci abinsu kuma suna jimawa kafin suke farkawa.
   Koda rnr biki ta matso su saliha sunyi hutu ae kuwa ba qaramin dad'i Ryynt taji ba duk da dae saliha tafi ta jin dad'in haka ma Ameera taji dad'i dan yanzu ta fara sakewa da Ryynt ba kmr daa ba ,don ko preety ma yanzu alhmdlh bata nuna tsana ga Ryynt sae ma wani janta take a jiki.
  Ranar suna sosai akayi biki shagali da mohd ya darje yasa aka yankawa 'ya'yansa kowannen su
Sa da Rago biyu yayinda yaran suka ci suna.
  Muhammad Ammar, Muhammad Anwar,and Aishatu Razeenah.



Billy giro😊```🔮BAZAN BARSHI BA🔮```














                    🔮🔮🔮🔮
*page 91*
 Bayan sati d'aya da yin biki Ryynt ce zaune a d'akinta tana shayar da Razeenah sae ga saliha ta shigo d'akin da sallamar ta,Ryynt ta amsa mata sallamar d'auke da murmushi a fuskarta,saliha ta zauna tana fad'in"maman yara kina nn sae shayarwa kike tayi ina Ammar da Anwar?
 Ryynt tace"Ammar na gun Baaba hurera ta goya min shi hakama Anwar na a bayan alawiyya ta goya shi"
  Saliha tace"ok dana shigo gidan sae naji tsit kamar ba kowa"
  Suna baya suna shan iska ni kuma muna nn muna bacci nida Razeenah shine ta farka nake bata mamma.
 Saliha tace"zakiyi fama kam idan kuka koma sauqin ki d'aya yaran basa da rigima"
 Ryynt tace"wlh kuwa  kuma naji ma mk yace idan mun koma en reno zae samar musu had'i da alawiyya"
  Saliha tace"da yafi kam nama ji umma na fad'in wnn kàron mami bazata koma ba"
  Ryynt tace"ae banji dad'i ba umma ce wae d'awainiyar zata yi yawa"
 Saliha tace"ai kam abun zae yi yawa wlh"
 Ryynt tace" haka dae kuke gani ya ita umma da mami suna lafiya?
 Lafiya qalau suke umma ta ma ce in gaida ki keda yaranki ga ma wnn tace na baki sae ta kiraki a waya zata miki bayani.
  Rryynt ta kar6i ledar da saliha ta bata tayi godiya had'e da jawo bedside drawer ta saka a ciki.
   Saliha tace"tun yanzu an fara yiwa yaya gyara"
  Hm saliha knn bafa kayan da kike nufi bane.
 Ba wani nn kan me to za'a ce sae an kiraki a waya snn za'a miki bayani ni ba amin bayanin ba na miki.
   Ryynt tayi murmushi
tace"ina jin kunyarki saliha a daina zancen nn kuma in banda abinki idan ba'a fara gyaran tun yanzu ba yaushe za'ayi?
  To Ryynt ina na sani na d'auka wani  abun sae kana tare da miji kake sha.
  Eh akwai abinda dole sae kana tare da miji amma wnn basu bane na gyaran jiki ne tukun dan kinga tun rnr da na haifu na soma tsalki da ruwan bagaruwa sbd tana saurin warke miki ,
take kuma take matse mutum,sae dae kinyi aure zaki fi fahimta dan wani abun ma in kika sha shi sae kin qwaci kanki wlh.
  Saliha tace"cabd'i da wahala knn?
  Uhm kedai sae kinyi auren koma mene ne kyaji da kanki ba sae kin sami labari a bakin kowa ba.
Saliha tace"wlh Allah Ryynt ni har ko yaushe mamakin aure nakeji da bana ganin mata da miji na jin kunyar junan su wae ace rnr da aka kae amarya ko sakewa basu fara yi da junan su ba sae kiga abu ya shiga tsakanin su inyi mamakin ta yaya ma zan barka nikam.
  Ryynt tace"hm saliha knn duk da dae ba haka nawa yazo ba amma wlh mazan ne da shegen wayo sae kiga suna miki laf laf sae lalla6aki suke suna kashe ki da dad'in baki har su kae ga cimma burin su kawae  da safe ke ya bari da jin kunya dan dae shi ba jin kunyar zae yi ba.
  Saliha tace"kae bazae ji kunya ba fa kika ce"
  Ryynt tace"inafa namiji kuma ae sae dae ma yayi ta sa ki qara jin kunya dan wani ma sae ya tsinto abubuwan da kikayi fad'a a cikin faruwar abun yana fad'a miki kin jima baki nutse a cikin qasa ba shi ina ruwan sa.
 Dan haka wata da muka had'u a chat da aka mata aure a kwanaki take gaya min wae ashe haka maza suke basu da kunya  rnr da aka kaita ya neme ta taci kuka tana kiran umma da Abba da gari ya waye sunyi wanka sunci kwalliya suna zaune a d'aki suna breakfast kanta qasa ko kallon sa bata iya yi daga rad'a ya mata a kunne yace ni'ima mene ne ko zamu je gun umma da Abba ne naga daren jiya sae kuka kike kina kiran su,nayi dariya nace to ke me kika ce masa tace"inafa ji tayi kmr ta nutse anyi sa'a baqi sunyi sallama tayi saurin fita ta bashi guri,kuma kiji fa ni'iman ba sunan ta bane Aysha ne sunanta kawae dan yaji ta yanda yake so shike nn ya maida ta ni'ima kuma a gaban kowa kiranta yake da sunan da duk lokacin da ya fad'a sae taji kunya tunda tasan dalilin da yasa yake kira mata sunan tayi tayi ya daina yaqi ta gaji ta barshi.
  Saliha tace"hm lallai maza ba kunya"
  Ryynt tace"uhm kedai bari kawae"
  Nan suka bar zancen saliha ta kar6i Razeenah da ta gama shan mamma sae kallonta take cike da sha'awa tace"gaskiya Ryynt mamman ki yana da kyau ji yanda yaran nn suka qara yin 6ul 6ul kamar ba en sati biyu ba wlh"
 Ryynt tayi d'an guntun murmushi tace"ae dole wnn kunun hakukuwa na gyaran nono da inna keta d'ura min wani lokacin ma idan suka jima suna bacci mamman har zuba yake.
  Saliha tace"to kuma shine ake had'a musu da madara"
 Ryynt tace"eh mana nonon baya fa isar su har su uku dole sae an had'a musu da madara"
  Saliha tace"kina ma qoqari wlh, ko d'aya ya aka qarasa dashi bare uku"
   Ryynt tace"ae bari rnr da akayi suna da dare bayan isha'i ina cikin baccin gajiya da ya d'auko dad'i kawae naji Mk na tashi na wae in tashi in ba yaransa mamma sun tashi ae bansan lokacinda na fashe masa da kuka ba a take ya shiga rarrashina yana bani haquri,snn ya had'awa yaransa madara ya basu ni kuma tuni na koma bacci ban san ma lokacin da ya tafi ba.
 Saliha tayi murmushi dan rayuwar mohd da Ryynt na matuqar birge ta bata dae ce komai ba sae tashi tayi tare da d'aura Razeenah a kafad'ar ta ta kwantar tana fad'in "bari naje na gaida su inna na dawo"
  Ryynt tace"to"
Kafin saliha ke fita daga d'akin.
  Da dare Ryynt ta fito daga gurin wanka ta sami mk kwance akan gadon ta idanuwan sa a lumshe kamar mae bacci sae shafa bayan Ammar yake dake kwance kan qirjinsa yana bacci,
Ryynt tazo ta zauna kan gadon tana kallon Mk da ya bud'e idon sa yana kallonta tace"Anwar fa da Razeenah ko sunyi bacci ne?
Yace"Eh suna can d'akin inna sunyi bacci  amma shi ammar ya kasa baccin sae kuka da yake da alama yunwa yake ji shine nazo ina ta jiran fitowar ki amma naji shiru hkn yasa na had'a masa madara na bashi yasha yayi baccin"
 Ryynt ta kae hannun ta a hankali ta shafo kan Ammar tace"Allah sarki na manta d'azun yana bacci koda aka basu madara da kuma ya tashi ba'a bashi ba shiyasa"
 Mohd bae ce komai ba sae kallon jikin Ryynt yake wacce ke d'aure da towel iya guiwa tayi haske sosai ta qara kyau ga cikinta da ya koma tsaf kamar ba itace tayi kayan cikin en uku ba.
  Yace"my ryynt kinyi kyau kuma jikin ki ya qara fresh me inna ke baki haka dani ta barni duk na rame"
 Ryynt ta kalli jikinta d'auke da murmushi snn ta kalli nasa jikin lumui lumui kmr jikin zomo sbd laushin fata irin nasa da baka babance shida Ryynt wa yafi wani  laushin jiki.
Tace"ni kuwa Mk banga wata rama da kayi ba"
  Yace"Allah koh ni kuma ji nake kamar na rame"
  Tace"um um gaskiya baka rame ba kana nn yanda kake,me ma zai sa ka rame to"
  Yace"kewarki mana kwata kwata wlh tunda kika bar gidan baya min dad'i so lonely gashi nasan inna bazata barki ki koma ba sae kunyi arba'in"
   Yana maganar ne kmr wani qaramin yaron da ke cikin damuwa.
  Ryynt tace"kana fad'in arba'in nifa sae munyi wata ko uku ne"
  Mohd yayi murmushi yace"ae ke nasan idan aka barki ko shekara d'aya zaki iya yi babu ruwanki da damuwar da zan shiga"
   Tace"uhm Mk knn  idan ban damu da damuwarka ba damuwar wa kake so na damu da ita?
  Yace"to gashi kina fad'in sae kunyi wata uku bayan yanzu yanzun nn na gama gaya miki irin damuwar da nake ciki"
  Tace"ka fahimce ni mana ba wae ban damu da damuwar ka bane"
 Yace"ba wani nn ae na gano ki"
  Ya fad'i hakane yayinda ya tashi zaune sannu a hankali rungume da Ammar a jikin sa ya tafi dashi zuwa kafad'ar sa snn ya tashi yaje ya kae shi d'akin inna ya dawo.
  Ryynt na jikin wardrobe tana ciro kayan bacci yaje sukayi sae da safe kmr yanda suka saba snn ya wuce.


Sannu sannu lokaci keta tafiya wanda tuni su saliha hutun su ya qare sun koma school Ryynt kuwa har tayi arba'in.
  Su Ammar sun qara yin 6ul 6ul da kyau  abin sha'awa don duk wanda ya gansu sae yaji yana son d'aukar su har dae yanda sukayi saurin wayo dan idan ba'a gaya maka arba'in kawae akayi ba zaka d'auka  ko en wata uku ne.

 Da dare guraren bayan isha'i mohd ne tafe  cikin mota shida Ryynt  yaransu na baya tare da allawiya.

 Mohd dake driven bae zarce koina ba sae gidan sa wanda tun lokacin da ya shigo gate d'in gidan Ryynt ke kallon sa da mamaki har ya parker mota kafin tace komai wayar sa tayi qara ya d'aga wayar ya fito mota ya zagaya ta gefenta ya bud'e mata yaja hannun ta suka shiga ciki suka tsaya a falo sae kallon sa take yana waya.
 Yana gama wayar  tace"Mk kai da kace min family house zamu je ya kuma kazo damu nn"
 Yayi murmushi yace"wayon manya na miki ba wani family house da zamu je nn nake nufin zamu zo"
 Tace"to meyasa?
 Yace"har kya tambaya ko kin manta na gaya miki cewa da kinyi arba'in zaki dawo ne"
  Tace"uhm kaima dae da wasa kake Mk abu sae kace tulin wanki haka kawae ba shiri ka kwaso mu kace mun dawo knn,da akwai dae abinda ka shigo d'auka je ka d'auko mu tafi kasan mun bar alawiyya da yara a mota"
  Yace"Allah da gaske nake miki mun dawo knn ba wani  abunda nazo d'auka"
  Tace"Mk bana son irin wasar nn dan Allah ka maida mu gida dan wlh ni ban shiryi dawowa ba"
  Yace"Ryynt wane irin shiri kuma idan kayane gobe zanje da kaina gidan inna na kwaso maku komai"
  Haba mk haka kawai zan dawo banje nayiwa kowa sallama ba nida nake son har qauyen mu sae naje.
  Gaskiya Ryynt ni bazan iya harakar al'ada d'in nn ba wae ace don mutum yayi arba'in sae yaje yawo gidajen mutane kiyi haquri bana so ba kuma zakiyi ba amma zuwa qauyen ku bazan hanaki ba ko gobe kike so zan kaiki.
  Ryynt ta girgiza kanta tace"gaskiya ni kawae ka maida ni bazan iya wnn abin kunyar ba ae sae ace da had'in bakina tunda ko inna bata sani ba"
  Da mamaki yace"abin kunya kuma Ryynt kina mata ta dan na maida ki shine ya zamo abun kunya"
 Tace"eh mana yau yau fa da yin arba'in se aji kawae na dawo haba gaskiya ni ka maidani"
Yace"wlh bari kiji ba inda zan maida ki kin dawo knn"
  Cikin muryar kuka tace"wlh ni kuma bazan zauna ba sae na koma"
 Rae 6ace mohd yace"shike nn gaki ga hanya jeki bazan hanà ki ba amma wlh kar ki kuskura kice zaki je min da yara ,kiga idan baza mu rayu ba dan ba ke"
  A fusace ta fita tana fad'in ae dama bance da yaran naka zan tafi ba.
 Cikin 6acin randa tafito d'auke dashi taje taja alawiyya zasu bar gidan ,
Alawiyya tace"Anti ina zamuje munbar su Ammar a mota?
 Ryynt tace"ki barsu ubansu zae ji dasu"
  Daga haka alawiyya bata sake cewa komai ba har suka fita suka tari napep suka wuce sae gidan inna.



Billy giro😊[4/24, 10:12 PM] ‪+234 703 962 5239‬: ```🔮BAZAN BARSHI BA🔮```














                    🔮🔮🔮
*page 92*
Suna shiga gida suka sami inna zaune a falo tana kallo wacce tana ganin su tace"Aa lafiya jim kad'an da fitar ku sae gashi har kun dawo?
  Ryynt bata iya ce mata komai ba sbd kukan da take ji sosai tayi sauri ta shiga d'akin ta ta zauna gefen gado tare da fashewa da kuka.
 Sae ga inna ta shigo d'akin ta zauna a kusa da ita ta dafa kanta tana fad'in subuhanalillahi lafiya Ryynt me yake faruwa?
    Cikin kuka Ryynt ta shiga yiwa inna bayanin abinda ya faru tsakaninta da mohd.
  Inna ta jinjina kae tace"cabd'i! lallai muhammadu ba d'an rainin wayo irin sa daga cewa zaku tafi wancan gidan shine zae d'auke ku ya tafi daku gidan sa a cewar kun koma knn ba tare da ya ko snr dani ba bare zancen shiri,kinga yi shiru daina kuka zae zo ya same ni shasha shan yaro marar kunya fitsararre ae gwanda da kika masa haka ina nn zae zo ya sameni  sae naji in ubansa kabiru ne ya turo sa yayi hakan.
  Tana kaiwa nn sae ga allawiya ta shigo d'akin da sallamar ta mohd ya aiko ta a cewar yana da magana da inna ,inna ta tashi tana fad'in shashasha dama nace ina nn zae zo ya sameni bari inje inji da wane shashan cin kuma yazo min dashi.
 Ta fita bata ganshi a falo ba sae d'akinta ta same shi sae safa da marwa yake yaransa na ajiye gefe cikin keken su na turawa sae da inna ta zauna snn ya zauna suna fuskantar juna.
  Cikin fad'a inna tace"shasha sha wane kuma shashancin ka zo min dashi ne iye fad'i ina jinka"
  Mohd dake kallonta yace"haba inna ni  gaskiya abinda Ryynt ta min sam banji dad'i ba amma kuma kinxo kina ganin laifina"
  Inna ta dunqule yatsunta biyar ta watsa masa tace"ungo nn dan uwarka idan banga laifin ka ba laifin wa zan gani ne iye shashashà marar kunya ace yarinya yau yau da yin arba'in haka kawae zaka wani d'auke ta ka maida ba wani shiri ba tare da kuma ka sanar dani ba sbd ban isa da kai ba bani na haife ka ba koh!

Ni inna kinsan ba haka bane harakar al'ada d'in nn ne na zuwa yawon sallama gidajen mutane ne bazan iyaba shiyasa kawae ban sanar da ke ba.
  Inna tace"yo lallai muhamnadu abu tun kakannin kakannin kace kae baka yarda dashi ba to bari kaji ba inda Ryynt zata koma sae taje tayi sallama da mutane kuma har qauyen su sae taje  kaji in gaya ma.
  Rae 6ace mohd yace"gaskiya inna ina buqatar matata ta koma bazan iya haquri har tayi wnn yawance yawance ba ta bari in taje can tayi"
  Inna tace"dan uwarka a ina ka ta6a ganin anyi haka kuma da kace baka iya haqurin jiranta tayi wnn yawace yawacen ae duk dad'ewar dae ba zae wuce kwana uku ko hud'u ba idan anyi ququwa sati d'aya a cikin na biyu.......haba habà inna gaskiya ni bazan iyaba, na gaji da kad'aicin da nake d'auke dashi a bani matata  kawae mu koma idan baso ake na shiga wani  hali ba.
  Inna tace"yo ka jima baka shiga wani halin ba shasha shan yaro marar kunya ba inda Ryynt zata je kumà maza fita a nn in daina ganin ka"
   A fusace mohd ya tashi zae bar d'akin inna tace"wa kuma ka bar ma yaran naka ne iye?
  Mohd ya juyo ya kalli yaransa snn ya kalleta cikin marairaice fuska yace"inna ya zanyi ne idan na tafi dasu bayan Ryynt bata can kuma kince bazata koma ba"
  Tace"yo ae sae ka tambayi kanka daa da kace ta bar maka yaran ya kake tunanin zakayi dasu ne iye"
 Shiru mohd yayi dan shi kansa yasan a lokacin zafin zuciya ne ya d'ebe sa ya kaisa ga cewa hakan.
  Inna tace"kana jina kayi min shiru"
 Yace"inna wnn zafin zuciya ne dmn bana da nufin zaluntar su na raba su da mahaifiyar su da ita kad'ai ce zata iya kula dasu yanda ya dace"
  Inna tayi shiru tana kallon sa  tace"matsalar ka knn muhammadu zafin zuciya abinda sam bayada anfani,yana da kyau mutum ya riqa tausasa zuciyar sa kafin ya fad'i magana dan kaga yanzu ba wata riba kuma sanin kanka ne yanda ka 6ata ran Ryynt ba lallai bane ta kar6i yaran nn kai tsaye sae kayi kamar kanayi.
 Mohd yayi shiru kafin yake cewa"inna kiyi haquri dan Allah na barsu a hannun ki nasan idan kika lalla6a min ita zata haqura ta kar6e su dan yanzu nasan ni ko naje ba zata saurare ni ba"
   Inna tace"Aa ni baxa ka bar min yaranka ba,ba kuma zanje na lallashi Ryynh ba kaje da kanka ae da zaka maida ta gidan ka bakayi shawara dani ba sae ma qarya da kamin sbd ka maida ni shasha sha"
 Mohd yace"inna dan Allah kiyi haquri naji nayi kuskure zan kuma bi duk yanda kuke so koma yaushe ne zan haqura,kawae bana son fad'an da mukayi da ita ya shafi yarana dan Allah inna kije ki rarrasheta.
 Inna ta nisa snn tace"naji zanje na rarrashe ta d'in"
 Mohd ya mata godiya  snn ya fita a cewar zae tafi ya dawo.
 Inna tayi zaune shiru  dan sae duk taji mohd ya bata tausayi amma bata jin zata iya bashi Ryynt su koma yau d'in nn dan ko ba komai tana son qara gyara ta da kyau.
 Nan ta tashi ta nufi d'akin Ryynt dmn rarrashinta.

Bayan awa d'aya da fitar mohd sae gashi ya dawo,kae tsaye d'akin Ryynt ya nufa ya sameta zaune kan bed d'aure da towel ta fito daga wanka tana shafa vaseline ya zauna kusa da ita sae kallonta yake yasan ta ganshi amma sae tayi kmr bata ganshi ba tana ci gaba da shafa Vaseline d'inta dan har lokacin ranta a 6ace yake duk da cewa sosai inna ta rarrasheta abinda bae mata dad'i ba shine jin cewa a cikin kwanakin nn zata koma.
  Mohd dake kallonta ya kira sunan ta a hankali bata amsa ba sae tashi tayi zata bar gurin ,a hnkli ya maida ta ya zaunar, qwallah tap a idonta ta kae hannu tana son cire hannun sa daga riqon da ya mata mohd ya sakar mata hannu tare da kwantar da ita kan qirjinsa sae rarrashinta yake yana bata haquri cikin kalamae dake saurin sanyaya rae,da yasa ta lafe a qirjin sa tana fitar da qwallah had'e da sautin kukanta da ke fita a hankali,mohd ya d'ago ta yana share mata hawaye yace"am sorry bazan sake ba kinji ban kyauta ba is ok daina kuka"
   Bata ce komai ba sae komawa tayi kan qirjin sa ta kwanta d'auke da wasu qwallah a idonta cikin muryar kuka tace"haba Mk wane irin rashin haquri ne da baza ka barni ba na qara samun hutawa ko na wata d'aya ne dan Allah"
 Jiki sanyaye Mohd ya d'ago ta yana kallon ta yace"Ryynt har wata d'aya fa kika ce kin san fa kafin ki haifu na jima rabona dake sbd naga abun na maki wahala sosai kuma bana son takura ki shiyasa na barki har kika haifu yanzu kinyi arba'in kuma kice na qara miki har wata d'aya,am sorry plz kiyi haquri zan dae iya qara miki sati biyu dmn wata d'aya ta min yawa kinji"
  Ta gyad'a masa kae yayinda ya kae hannu yana share mata hawayen fuskarta snn ya maida ta kan qirjinsa ya kwantar yana shafa bayanta a hankali.
  Sukayi shiru d'akin yayi tsit kmr ba kowa mohd ya katse shirun da cewa"yarana fa suna d'akin inna still suna bacci ko sun tashi?
  Tace"eh sun tashi"
Yace"Mamma fa sunsha ko madara aka basu?
 Tace"duka sun sha"
   Yace"Nagode my Ryynt bari na tashi naje na gansu nayi sallama da inna na tafi yau bacci nakeji da wuri"
  Nan sukayi sae da safe kamar yadda suka saba snn ya tafi d'akin inna. A nn Ryynt ta tashi tayi shirin bacci koda ta gama taje d'akin inna tuni mohd yayi musu sae da safe ya wuce.

Tun a washe garin rnr inna ta soma gyaran Ryynt da kayan mata kala kala masu inganci da umman saliha ta aiko sbd taji Ryynt zata koma dan a cikin satin nn mohd ya kaita gidajen kowa wato gidan nasir da gidan Amir da kuma Aamil dmn tuni matar sa Khadija ta koma ta kuma ji sauqi sosai don har ma cikin nata ya fara fita.
 family house shine farkon inda suka fara zuwa har ma mahaifiyar mohd taba Ryynt turarukkan mata kala kàla masu dad'in qamshi  tsadaddi bayan wad'anda ummam saliha ta bata.
  Snn gida na qarshe da suka je shine gidan su Sarah qawar Ryynt.

  A cikin sati na biyu suka tafi qauye aka musu tarba mae kyau  matan mae gari sae barikalli suke ta fad'i ganin su Anwar sun yi wayo sun qara yin 6ul 6ul abin sha'awa sbd da Ryynt ta haifu an sanar dasu har ma suna sae da suka zo.

Da zasu koma matan mae gari suka basu cimakar qauye na kayan marmari da kuma abubuwan  kayan miya qwarya qwarya kmr su busasshiyar ku6ewa, ,tafarnuwa ,man shanu da dae sauran dmn ba kad'an ba sunjin dad'in alherin da Ryynt taje musu dashi wacce mohd ne ya bata yace ta basu a matsayin ita ce ta bayar.
Da itama a gurinta sosai taji dad'in yanda mohd ya mata.

3 dayz later
Yau ce rnr da Ryynt zata koma tana zaune gefen gado cikin shirin ta tsaf kanta qasa tana sauraren inna dake zaune gefen ta tana bata shawarwari akan yanda zata kula da kanta da kuma yaranta ta gefen tsafta da kuma tarbiya mae kyau da zata taso ma yaranta dasu snn tace"kuma kar ki ta6a sake da musu addu'a safe da yamma da kuma idan zaku shiga bacci,haka kema kanki kar kiyi sake da addu'a"
  Tace"inshaa Allah inna zan kiyaye"
 Nan inna ta riqa hannun ta tace"to tashi muje kinsan muhammadu na can na jiranki a falo tun d'azu.
  Kmr mae jin kunya Ryynt ta tashi suka fito inna ta rakasu har mota taga wucewar su snn ta koma daga ciki.
  Tafe suke cikin mota yaran su na baya tare da alawiyya ,
Mohd kuwa na gaba shida Ryynt wanda tuqi yake amma duk rabin hankalin sa na gun Ryynt sae kallon yanda tayi kyau yake sabon kitson ta ya qara haskaka fuskarta an mata zanen lalle mai kyau ga kuma wani  daddad'an qamshin turare da yake jin yana fita a jikinta yayinda ita kuma kanta ke qasa kmr mae jin kunyar sa dan ko wani  dogon motsi bata yi hkn yasa mohd ya riqa  jin kansa kmr wani  sabon ango.


Billy giro😊
[4/26, 6:52 AM] Bili Giro Author: ```🔮BAZAN BARSHI BA🔮```














                    🔮🔮🔮
*page 93*
 Bayan sun isa gidan ne mohd ya tafi da yaransa d'akin sa Ryynt kuwa taje d'akinta haka ma alawiyya.
  Da shigar Ryynt d'aki ta soma cire kayan jikinta dmn shirin bacci.
Duk da cewa jikinta baya buqatar wani  wanka amma haka ta fad'a Bathroom ta sake wani  wanka ta fito tayi zaune tabi koina na jikinta duk ta shafa turarukka masu daddad'an qamshi ta d'anyi er simple make up ta shiga bacci snn ta tashi taje jikin wardrobe ta nemo farar rigar bacci wacce sae da ta feshe ta da turare snn ta saka,
 rigar er fincika ce sosai iya cinya gashi komai na jikinta ana hangowa dan ita kanta ma sae da taji kunyar kanta a lokacin da tana kallon jikinta ta jikin mirror.
   Ta jawo farar er samar rigar baccin da tsayinta iya guiwa zata saka kawae ta hango man jikin qofa cikin shirin sa na bacci yana zuba qamshi sae kallon ta yake yana qarosawa sannu a hankali har ya qaroso gurinta yana kallon yanda ta sadda kanta qasa taqi yarda su had'a ido.
  Man da duk qamshin turarenta ya soma rikitashi yakai lallausan hannun sa a kasale ya d'ago fuskarta yana bin fuskarta zuwa surar jikinta da kallo cikin wani irin kallon  sha'awa,
murya can ciki mae d'auke da kasala yace"my Ryynt yau ni kuma kike jin kunya"
  Ryynt bata iya ce masa komai ba sae wani d'an murmushi tayi mae natsuwa da janhankali da yasa man yayi tsaye ya kafe ta da ido cikin wani yanayi da yake jin kansa na kasalar da ta qara saukar mae,ya kar6i er samar rigar da ke hannunta cike da kasala ya saka mata snn ya d'auke ta cak suka tafi d'akin shi.
  D'akin ba haske sosai sae dim light da kuma wani daddad'an qamshi da ke fita a d'akin ga sanyin splt.
  A hankali mohd ya sauke Ryynt tare da kai hannu ya cire mata er rigar sama ya yar,
 ya kama d'ayar rigar itama yana cire ta sannu a hankali har ya cire ta gabad'aya sae bin jikinta yake da kallo kamar yau ne ya soma ganin sa snn ya lumshe idon sa a hankali ya janyota zuwa jikin sa had'e da kae hannu kan mammanta yana shafawa ya kalli yaransa dake kwance cikin d'an bed d'insu suna bacci snn ya maida dubansa gun Ryynt a natse murya can qasa yace"hope  yarana sun sha sun qoshi dmn daren yau namune mu kad'ai bana son su tashi su takura mu"
   Ryynt tayi murmushi tare da gyad'a masa kae.
 Tana kallo ya rage kayan jikinsa snn ya d'auke ta cak yaje da ita kan bed ya kwantar  had'e da zira harshen sa a cikin bakin ta lokaci mae tsawo snn ya zare sae shafa jikin ta yake yana kissing d'inta ta koina har ta soma maida masa martani suka shiga romancing d'in juna har suka je ga duniyar ma'aurata da gabad'aya man ya fita hayyacin sa sae sambatu yake yiwa Ryynt da yaji tamkar yau ne ya soma 6are ta a leda.

Washe gari da asuba mohd ne ya fara tashi sae kallon Ryynt yake da ke rungume a qirjin sa tana ta sharar bacci abinta sannu a hankali ya zare jikin sa daga nata ya tashi ya nufi bathroom yayi arwala ya fito.
  Yaje yayi zaune kusa da ita yana shafa gefen fuskarta a nn ta shiga bud'e idanun ta a hankali har ta sauke su a nashi,
d'auke da d'an murmushi cikin jin kunya tayi qasa da idonta dan sae ta tuna komai da ya faru tsakanin su jiya.
  Mohd dake kallon ta
yayi murmushi tare da kai lips d'insa a hankali kan goshinta ya d'aura mata kiss snn yace"asuba tayi tashi kiyi sallah kinji"
  Ba musu ta tashi ya bita da kallo har ta shige bathroom snn ya tashi ya nufi masallaci.

Guraren qarfe goma zaune suke kan dining kowannen su cikin ado sunyi kyau sae zuba qamshi suke suna ciyadda junan su a natse,
Suna cikin cin abinci Ryynt ta kai spoon zuwa bakin mohd bae kar6a ba sae tagumi yayi yana ta kallonta  wanda ba abinda yake tariyo wa face daren su na jiya da yake jin kamar ya sake tsintar kansa a lokacin.
  Ryynt dake kallon sa taje a natse ta hura masa iskan bakinta ya lumshe idanun sa d'auke da murmushi snn ya koma ware su a kanta,
 Cikin shagwa6e ta kalle sa tace"ya ina baka abinci kaqi  kar6a sae kallona kake"
  Mohd bae ce komai ba sae kar6ar spoon d'in yayi ya ajiye ya janyota zuwa jikin sa sae kallon ta yake cike da so snn yace"my Ryynt ina sonki kuma har ko yaushe ina mae gaya miki cewa keta daban ce da sauran mata, hm shin kinji irin farin cikin da kika tsunduma ni a daren jiya kuwa"
Ryynt dake kallon sa tayi murmushi tare da saurin sadda kanta qasa mohd ya d'ago ta yace"uhm my ryynt knn meye na jin kunya kuma bayan duk burin mace ta gari shine taga cewa ako yaushe ta faranta ran mijinta,ni mijinki ne kin faranta min dole na nuna miki farin ciki na a fili dmn fiye da tunanin ki kin faranta min ba kad'an ba da har ma kikaci babbar kyauta a gurina da sae kin fara karatun ki snn ko zan baki amma yanzu gaya min bayan karatun ki meye kuma burin ki na gaba a rayuwa da kike son cikawa?
  Cikin sassanyar murya mae d'auke da farin ciki tace"burina na gaba shine ina son idan na kammala karatuna ka bar ni nayi aiki"
 Yace"kin samu my Ryynt sae kuma me kike so?
  Tayi murmushi tace"kai nake so da kuma gangar jikin ka gabad'aya yayinda zan kasance taka ni kad'ae"
 Yace"wnn kin jima da samun sa my ryynt sae kuma me?
 Tace"um um bana tunanin yanzu akwai wani  abu da nake so da dae baffana zae dawo da ina so"
 Mohd dake kallonta yayi murmushi dan itama d'auke da murmushi tayi maganar amma kuma sae yaji tausayinta yace"Allah yaji qan baffa da Rahama"
 Tace"Amin"
Snn ta d'auki spoon ta kae bakin sa taci gaba da ciyadda shi shima yana ciyadda ita har suka kammala cin abincin.
  Yaja hannunta ya tafi da ita d'akin yaransa  yana nuna mata yanda yasa aka tsara d'akin sae yaba d'akin take tayi dan an tsara d'akin sosai kmr ba a cikin Nigeria ba.

Bayan sati biyu da faruwar haka sosai su Ammar ke samun kulawa a gurin en renon su shiyasa sam Ryynt bata wani  wahalar d'awainiya dasu sae dai shayarwa.

 6angaren Malika kuwa zaune take gurin wani gurin shan iska lemuna a gaban su suna sha suna magana ita da sweetat d'inta wacce ke kallon sa tana fad'in"Aa wlh ba wani  laifi da ka min,na hana maka kaina ne sbd wani dalili......wane irin dalili ne haka da kika hana min kanki har na tsawon watanni?
  Tace"Aah me kake yiwa sauri ae dalilin ba wani  abu bane sae wani  babban albishir dana 6oye maka nace sae nayi idda tukun snn ko zan gaya maka dan nasan idan na gaya maka kafin na kammala zaka qosa ka ga na jima ban kammala iddar ba,Albishir d'in kuwa shine aure nake so zamuyi nida kae dmn zamu fi jin dad'in rayuwar mu ko  ya kace"
Wani irin murmushi yayi da jin zancen nata banbara kwae yace"kema dae da wasa kike malika in banda abinki ina  zancen aure a tsakanin mu"
Tace"kan me zaka ce haka saki uku fa man ya min kuma har na kammala idda me kuma ya rage"
  Yace"Hm dan Allah ke yanzu idan nace zan aure ki zaki yarda"
  Tace"why not zan yarda mana sbd nasan bakada wani  burin da ya wuce mu kasance tare ako yaushe"
  Yace"u are wrong ni sam baki fahimce ni ba dmn ni bani da burin da ya wuce na sami yarinya saliha kamila sabuwa fil a leda ba irinki da kika zubar da mutuncinki a titi ba da har kikayi aure baki daina yawon iskancin ki ba snn har kike tunanin wae zan aure ki tir"
 Cikin tsananin mamaki tace"Rasheed ni kake gayawa haka bayan kaine mutum na farko daka fara sani na a 'ya mace kaine ka 6are ni a  leda"
 Cikin d'aga kafad'a yace"And so what ni nace ki bani kanki ko kuma na miki dole ne  ko kuma ni kaid'ai naji dad'in bada ke ba"
   Tace"kaga Rasheed idan har tunanin kake idan munyi aure zan iya kula wani bayan kae sam ka cire hakan a ranka dmn sanin kanka ne tun lokacinda muka fara sanin juna bana kula kowane d'a namiji bayan kae har nayi aure kuwa"
  Yace"hm nifa ba sakaran namiji bane da kike tunanin zan yarda dake keda duk son da kike yiwa man bai hana kin cutar dashi ba kina yawon bin maza a titi"
Ran malika ne yayi mugun 6aci tace"kaga Rasheed mu daina wnn wasar dan ni har raina ya so6a 6aci wlh,gaya min yaushe zaka turo magabatan ka?
  Yace"hm totally u have gone mad! na tura magaba ta na wa auren ki  tuf! Allah sauwaqe na auri mace irinki wlh never"
 Yana gama fad'ar haka ya tashi zae bar gurin ta miqe a fusace ta kama kwalar rigar sa tace"wlh baka isa ba Rasheed dan ubanka sae ka aure ni ko kuma na had'a maka tuggun da bazaka ta6a fita ba wlh"
  Tana kaiwa nn yasa qarfin sa ya ture ta tare da kife ta da mari ya nunata da yatsa yace"kin sanni wlh na fiki zama tataccen d'an iska duk wani abu da zakiyi sae dae na juyar dashi zuwa kanki amma idan kina musu ki gwada ki gani shege ka fasa"
  Yana gama fad'ar haka ya tafi ya barta dafe da kunce hawaye masu zafi na sauka kan fuskar ta dan tasan tabbas ba abinda zata iya masa da zata ci riba ya riga ya gama da ita.



Billy Giro😊```🔮BAZAN BARSHI BA🔮```











*LAST  PAGE*


                    🔮🔮🔮
*page 94*
Duk da cewa lalura ce kawae tasa taso ta  aure shi amma sosai taji ciwon cin mutuncin da ya mata dmn bata ta6a tsammanin zae mata haka ba.
  Amma ba komai tunda bashi kad'ai ne d'a namiji a duniya ba da akwai su birjik da kyaun ta kad'ai ya isa ta sami mae aurenta cikin lokaci yayinda zatayi gaggawar yakice wnn auren dmn taga cewa ta koma ga auren man,
 fatar ta kawai Allah yasa har mutuwa kar man ya ta6a jin cewa ta ta6a bin wani namiji a waje dmn tasan koda ta cimma burin koma ma auren sa idan yaji wnn labarin zae sake ta ne ba makawa.
 Tana gama qisa haka  a cikin ranta ta kai hannu zata share hawayen fuskarta sae ta tsaya cak cikin tsananin mamaki tana kallon man da ta gani tsaye a gabanta yana mata mugun kallo kmr wanda zae bugota.
 Kasan yin komai tayi dan ta rasa ta inda ya fito gashi yanayin kallon sa kad'ai ya isa ya fahimtar da ita ya gama jin komai tsakanin ta da Rasheed idan kuwa hakane tata ta qare dan duk wani  burinta na koma ma auren sa ya gama lallacewa nn kawai ta saki jiki sakwaf ta kai qasa durqushe kan guiwoyinta ta had'e tafukan hannayen ta ta soma kuka tana ba mohd haquri a cewar ya yafe mata sharrin shaid'an ne.
  Mohd bae bar ya saurare ta ba ya bar gurin a fusace don ya tabbatar ko minti d'aya ya qara a gurin ba duka ba komai zae iya faruwa.
  Cike da nadama malika ta tashi tana dana sani a rayuwar ta taje ta shiga motar ta bata zarce koina ba sae gidan fa'iza.

Bayan ta isa gidan  cikin kuka ta shiga yiwa fa'iza bayanin abinda ya faru tsakanin ta da Rasheed da kuma ganin man da tayi ba tare da tasan inda ya fito ba don sosai tayi mamakin ganin sa duk da cewa gurin,gurin shan iska ne da kowa kan iya zuwa.
  Fa'iza da ke kallon ta tace"Hm dama ae duk wanda ya sayi rariya yasan zata masa yoyo kuma sanin kanki ne baza ki shuka gero ba ki girbe masara dole duk abinda ka shuka shi zaka girba yanzu ga irin ta nn ya gama amfanuwa dake ya nuna miki halin sa na d'a namiji kuma yanzu shike nan zancen kiyi auren d'ibar wuta bae taso ba tunda man ya riga ya gama jin komai babu wata hanya da zamu iya bi mu shawo kansa
ya maida ki tunda ba sakaran namiji bane shi.
Cikin muryar kuka malika tace"Ae shike
 nn fa'iza nasan tawa ta qare min banida wani sauran farin ciki a rayuwa ta,
ayukka na marassa kyau sun sa na rasa abinda nafi qauna a rayuwata.
 Ta qarashe mgnr ne cikin kuka.
Nan Fa'iza ta shiga rarrashin ta,
 malika bata iya daina kukan ba sae cewa tayi" ya zanyi da rayuwata fa'iza abubuwa goma goma sun tara min zama d'aya,disire tablet d'in da nake sha tuni na daina amma still ko yaushe cikin buqatuwa nake jin kaina musamman da dare dako baccin kirki bana iya yi nabi duk wata hanya da nake tunanin zan daina ji amma abu ya faskara bansan ya zanyi ba fa'iza gashi bana son sake komawa gurguwar hanyar da na fito koda zan mutu kuwa.
 Fa'iza ta nisa tace"u see ba yanda banyi dake ba kan ki daina sha amma fir kika qi saurarata gashi ni yanzu bani da wani  abun da nasan zan iya miki sae dae kici gaba da neman magani har ki dace.
 Shiru malika tayi bata sake cewa komai ba sae hawaye masu zafi dake gangarowa kan fuskarta tana ji ina ma bata zo duniya ba da wnn halin qunci da ta saka kanta a ciki.

 Da dare guraren qarfe goma mohd ne cikin d'akin sa tsaye cikin shirin sa na bacci yana yiwa yaransa addu'a dake kwance cikin bed d'in su suna bacci,
Bayan ya ida masu addu'ar ne sae ga Ryynt ta shigo d'akin cikin shirinta na bacci itama, ta sami mohd  still yana tsaye kan yaran sa sae kallon su yake yana shafa kansu a hnkli.
   Ta qarasa gurin shi tare da rungumo sa ta baya mohd ya juyo yana kallonta kmr wani  marar lafiya,
Ryynt dake kallon fuskar sa da kulawa tace"mk wae lafiya tun lokacinda muka fita a hanyar mu ta dawowa na ganka cikin wani yanayi,bamu ko dawo gida ba kaje damu asibiti sae gwaje gwaje kake mana dana tambaye ka lafiya kace min ba komai bayan da gani akwai abinda ke faruwa ka 6oye min ne kawae don gashi har yanzu akwai sauran damuwa a fuskar ka,plz dan Allah ka gaya min yaran mu ne ba lafiya ko kuma wani ne a cikin mu"
  Mohd da tun lokacinda ta fara magana yake kallonta yaja hannun ta yaje da ita kan bed suka zauna a natse yace"my Ryynt kinsan  fitar da mukayi a d'azun a gurin shan iska inda har mun gama abinda muke zamu tafi sae banga makullin motor ba na koma nema,na sami makullin zan bar gurin knn sae muryar malika naji suna magana ita da wani,ba wanda ya ganni a cikin su haka kuma banyi niyyar tsayi ba amma mgnr da naji sunayi ce tasa dole na tsaya ina sauraren su sbd na razana da jin mummunan abinda malika ke aikatawa a lokacinda muna tare har kafin ma mun kasance tare.
  Nan mohd ya gayawa Ryynt kaf komai abinda yaji tsakanin malika da rasheed wanda shine dalilin da yasa kae tsaye ya tafi dasu asibiti dmn duba lafiyar su idan basa d'auke da wata cuta.
   Ryynt dake kallon sa take idanunta suka ciko tap da qwallah a rud'e muryar ta na rawar kuka tace"innalillahi wa inna ilaihi raji'un Allah yasa bata laqa mana wata cutar ba"
  A hankali Mohd ya janyota zuwa jikin sa ya rungume ta yana fad'in "Haqiqa Allah ya kare mu my ryynt dmn sakamakon gwajin da na mana ya nuna bama d'auke da kowace irin cuta don haka is ok kar kiyi kuka kinji.
 A natse ta sauke ajiyar zuciya ta gyad'a masa kae tare da qara lafewa a qirjinsa tace"Allah ya shirye ta ya qara tsare mu"
  Mohd yace"Amin"
 Daga haka sukayi shiru basu sake cewa komai ba sae shafa bayan ta da yake,
 sae can ya kira sunanta a hankali yaji bata amsa ba koda ya duba har tayi bacci nn ya kashe musu wutar d'akin ya musu addu'a snn ya kwanta rungume da ita a jikin sa.
  Bayan kwana d'aya da faruwar haka guraren qarfe tara na dare man ne zaune a falo kan doguwar kujera yayinda Ryynt ke kwance  kan qafafuwan sa tayi fillow dasu sae wasa yake da gashin kanta suna firar su cike da nishad'i.
  A cikin firar su ne man ke tambayar Ryynt me take son ta karanta tace mishi medicine idan na kammala sae mu riqa zuwa aiki tare da kae amma dai tukun gaya min nawa kake biya ma'aikatan ka?
  Yace"um to tunda kece zan riqa baki 5k a wata"
   Ta kalle sa a shagwa6e d'auke da dariya a fuskar ta tace"wlh da banyi ba"
  Cikin dariya yace"nine fa my Ryynt tace"to ae nima nice"
    Yaja hancinta yace"kin ganki son kud'in ki yayi wa"
   Tace"ba wani nn ae da gaskiyata"
 

Few months later
Tuni Ryynt ta rubutu jarrabawa har ta fara karatun ta yayinda mohd ya cika mata alqawarin bata babbar kyautar da yace sae ta fara karatu zae bata wato mota ya saya mata Accord V6 sabuwa fil wanda tuni ya koya mata don itama ke kai kanta school.
  Yaransu kuwa tuni sun qara wayo abin su don har sun fara rarrafe suna koyon tsayi and still suna nn 6ul 6ul sae qara shawa suke gasu da yawan dariya kuma sam basa da qiyuwa duk wanda ya miqa musu hannu zuwa suke d'auke da dariya a fuskar su koda kuwa basu san wanda zae d'auke su ba.
Idan Ryynt zata tafi school a hannun en renon su take barin su amma mostly gidan inna Mohd ke kaisu sae idan ta dawo snn ake d'auko su ,kuma duk mohd zae je family house dasu yake zuwa.

6angaren malika kuwa damuwa da dana sani  yasa ta rame sosai gabad'aya ta fita kamannin ta duk kyaun da take kuri dashi ya tafi shiyasa har yanzu ba wani wanda ya fito da sunan zae aure ta gashi kullum sae fama da buqatuwa take dmn tayi neman magani har ta gaji amma abu ya faskara shiyasa kullum sae qara yin nadama take don wani  lokacin ma zama take tayi ta kuka.
 Bayan lokaci ya qara tafiya ne ta samu wani  abokin mahaifinta ya aureta,abubuwa suka fara sauqaqa mata ta fara murjewa tana maida jikinta sbd ba kad'an ba akwai daula a gidan da kwanciyar hankali sbd ita kad'ai ce a gidan ba gida d'aya suke da uwargidan sa ba,
sae dai basu fi shekara d'aya cikin ta biyu ba ya saketa sbd ba don komai ya aureta ba sae don samun haifuwa ita kuwa da zarar ta sami ciki yana kae wata uku sae ya zube  baya tsayi kuma duk cikin zae zube wahala take sha sosai kmr bazata rayu ba shiyasa likitawa suka cire mata mahaifar gabad'aya sbd a binciken da sukayi sun gano wani abortion pills tasha mai qarfi da ya 6ata mata mahaifa da sam ciki ba zae ta6a iya rayuwa a cikin mahaifar ta ba sae dae ma yayi yunqurin tafiya da rayuwar ta.
  Tun daga lokacin nadama da quncin rayuwa suka sake dawowa malika ta soma ganin fa'iza ta cuceta dan bata ta6a shan abortion pills ba sae a dalilin shawarar da ta bata na sharrin da ta qullawa Ryynt,gashi yanxu  tana gani tuni fa'iza ta haifi d'anta har ma tana d'auke da wani  cikin amma ita gashi kwata kwata ma ta rasa mahaifar.

Da haka wasu shekarun suka sake tafiya inda da dama abubuwa sun faru dmn Ryynt har ta kammala karatun ta ta fara aiki asibitin man da kullum tare suke zuwa kuma tare suke dawowa.
  Yaran su kuwa tuni sun fara zuwa school.
  Haka ma Saliha,da Sarah har ma da Ameera tuni sunyi aure har ma kowannen ya haifu.


Ranar wata assabar da dare man ne da Ryynt tsaye a gaban mirror yana rungume da ita sae kallon fuskokin su yake kan irin hasken da yaga Ryynt tayi da kad'an ya rage ta kaishi.
  Nan ya kai hannun sa kan cikinta yana shafawa,bakin sa saitin kunen ta yace"gaya min meye sirrin wnn haske haka kodai akwai babyna a tare dake shine baki gaya min ba kike 6oye min"
 Ryynt ta bud'e ido tace"Rufan asiri dan Allah ae su Ammar sun ishe mu"
  Yace"uhm kema dae da wasa kike ae haifuwa yanzun kika soma ba dai da kika kammala karatun ki ba"
 Maqale kafad'a tayi tace"um um ba yanzu ba sae na qara hutawa tukun"
  Yace"kae my Ryynt duk shekarun da kika kwashe kina hutawa"
Tace"wane hutun ina karatu dae samun baby kuma sae na saba da aiki tukun"
  Mohd dake kallonta yace"hm my Ryynt knn babyna kam kin riga da kin samu don wnn hasken kema kinsan na babyna ne"
 Tace"ba wani nn dama inada haske na dan wlh ba za'a kirani baqa ba"
 Nan ya d'aura hannun sa kan qirjinta yace"to naji shi wnn qirjin da ya qara cikowa fa ko kuma shima ba daga babyna bane"
Da wasa ta harare sa tare da ture hannun sa tace"ni babynka bai qara min komai ba don kasan ko bayan na yaye su Ammar aka kalli qirjina ba za'a ta6a cewa na shayar ba suna nn daram tsaye abinsu a cike ko wata budurwa albarka ehe"
  Ta qarashe mgnr ne d'auke da dariya zata bar gurin sbd mohd da ya kama towel d'inta yana son cirewa wae sae ya nuna mata cikar da babynsa ya qarawa qirjinta"
 Bata barshi ba ta kama towel din ta riqe gam sae zille mae take tana dariya har suka je kan bed ya samu da qyar ya cire towel d'in daga nn wasar ta canza salo zuwa wasannin su na ma'aurata.....

Malika kuwa duk shekarun nn da aka kwashe bata samu ta sake wani auren ba sae can da qyar ta samu wani dattijo ya aure ta matan sa uku itace ta hud'u kuma a gida d'aya suke zaune shiyasa sam bata jin dad'in rayuwar gidan tana zaman haquri ne kawai ga masifar matan sa da gorin haifuwa da take sha sosai a gurin su da kullum idan tana zaune shiru sae tayi ta kuka don sosai wani  irin son haifuwa ya shigo ranta.
 Qarin abin ma sun maida ta kamar wata er aiki da duk wani  cefanen gidan ita ke zuwa tayi duk da akwai masu aiki a gidan dmn gidan ba talauci amma kwanciyar hankali da jin dad'i sun gagareta.

 Wata rana taje super maket tana siyen kayan abinci kamar daga sama taga Ryynt tare da su Ammar, Anwar n Razeenah yaran da in ka gansu kamar ka sace sbd kyau da shiga rai shirin su a wayen ce kmr wasu 'ya'yan turawa,Ryynt kuwa ta qara haske sosai tayi fresh d'an cikin ta ya fito abin sha'awa da har yanzu in ka ganta kmr yarinya er 17yrs sae jiki da ta qara kad'an irin na jin dad'i da kwanciyar hankali.
 Malika tayi tsaye sae kallon su Razeenah take cike da sha'awa tana ji kamar ace yaranta ne.
 Ta kuma bi cikin Ryynt da kallo qwallah tap a idonta sae kuma a take tayi saurin had'iye hawayen ta qarasa gurin su Ryynt da suka gama siyayyar su zasu fita ta kira sunanta a hankli,Ryynt ta tsaya tana kallon  malika tana son tuno ina ma tasan fuskar dan gabad'aya malika ta sauya ta dawo kamar wata er qauye.
 Malika da ta fahimci bata gane ta ba tace"baki gane ni ba koh malika ce"
 Sosai Ryynt tayi mamaki kafin take sake mata fuska suka gaisa har malika na tambayar sunan su ammar Ryynt duk ta gaya mata sae ga man ya shigo yana waya da gabad'aya hankalin malika ya koma kanshi sbd tsabar kyaunda taga ya qara wanda da gani kasan baya d'auke da wata damuwa sae kwanciyar hankali da jin dad'i.
 Yana gama wayar malika ta gaida shi ya amsa mata sama sama yaja yaransa suka fita tare da Ryynt da duk tausayin malika ya cikata.

Nan Malika ta bisu da kallo hawaye masu zafi na sauka kan fuskar ta.
 Tana ji ina ma rayuwa zata koma mata baya da bata bar ta aikata marassa kyaun ayukkan da suka kaita ga asara da da na sani ba.

Allah ya kare mu da aikata aikin da na sani da asara Ameen.


ALHAMDULILLAH A NAN NA KAWO QARSHEN WANNAN LITTAFI NAWA INDA NAYI KUSKURE ALLAH YA YAFE MIN AMEEM.

KHALEESA HYDAR MY ADVISER AND EDITA I THANK U SO SO MUCH.
 NA GAIDA ILHAM AND MUJAHEED.

MY LADY (FUTUHATULKHAIR)INA FATAR ALLAH YA BAKU ZAMAN LAFIYA DA ZURI'A D'AYYIBA AMEEN.

LUV U ALL MY FANS ALLAH YA BAR MU TARE.



BILLY GIRO😊

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *