Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Friday, January 11, 2019

boyayyen-alamari-seema-complete-hausa-novel

adsense here
akar>‎khaleesat haiydar hausa novels*....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_Pure Moment Of Life writers_*© ```Written```By*_Seemaluv_*Bismillahir Rahmanir Rahim...Da Sunan Allah Mai Rahma Mai Jin K'ai...*01*A zaune Safna take saman tabarma rik'e da razor a hannun ta tana cire kumban k'afar ta, Sai Umma wacce take ta kara kaina a tsakar gida ' sai kuwa k'an nanta guda biyu Rumaisa da Anisa wad'an da suke wasan guje guje a tsakar gida.Safna ita ce babba a cikin su ' don kuwa zata kai kimanin shekara 20 cir, Rumaisa kuwa shekaran ta 17 Anisa 10.Safna, Rumaisa da Anisa marayu ne ' Mahaifin su yarasu sakamakon rashin lafiyan da yayi mai tsana ni.Hakan yasa karatun Safna ya tsaya cak tunda ta gama secondry school ' bata samu damar zuwa gaba ba, Kasan cewar matsalar rashin kudin da sukefama dashi.Rumaisa da Anisa kuwa ' a makarantar Primary suka tsaya, ba tare da sun cigaba ba ' sai makarantar allon da suke zuwa anan k'ofar gida.Rumaisa ita ke fita k'ofar gida tana suyan wara, A haka har tayi ciniki susami abinda zasuci.Ita kuwa Safna aikatau take zuwa mak'otan su, wani lokaci haka zata gama aikin ranar baza'a bata abinciba.Umma ce keta d'awainiya dasu da dad'i babu dad'i, Hakan baisa tayi wani auren ba ' wani lokuta ma 'yan uwanta ke d'an harhad'a mata kayan abinci."Safna ya kamata ki tashi ' ki tafi wajen aikin ki rana nayi".Inji Umma."Umma ranar ma tayi wallahi ' yanzu ina zuwa fad'a zasu rufeni dashi, Suda basu da uzri"."Baki da wani uzri ai lafinki ne ' bakison zuwa da wuri, Yanzu dai ki tashi ki d'auki hijabin ki ki wuce"."To shikenan Umma".Safna ta fad'i haka tana k'ok'arin tashi."Safna zan biki".Cewar Anisa."A'a kiyi zaman ki gida".Safna na fad'in haka ta mik'e tare da janyo hijab d'inta maroon colour dake saman k'ofa, Ta sanya ta fice.Haka ta kama hanya ' harta isa kusa da gidan ta had'e da k'awar ta tana fitowa ciki."Sumayya ya garin ne".Cewar Safna.Harare hararen da Sumayya takeyi ne ya d'aure ma Safna kai."Lafiya kuwa"."Lafiyar ta kawo haka!"."Tooo! Allah ya baki hak'uri sai anjima".Safna tana fad'in haka ta k'arasa cikin gidan, Kai tsaye ta wuce d'akin hajiya domin su gaisa.Bayan ta shiga ne Safna ta iske suna magana da babban d'anta.Haka ta zuk'unna har k'asa ta gaishe ta, Bayan sun gaisa ne ta tashi zata fita Hajiya ta tsaida ita."Safna tsaya tukunna"."To".Ta fad'a tare da komawa ta zuk'unna, Hajiya bud'e jakarta tayi ta ciro kudi kimanin dubu 2 ' ta mik'awa Safna, Haka Safna ta mik'a hannu ta amsa ba tare da tasan na menene ba."Safna ' wannan kud'in sallama ne, Bakison zuwa dawuri kuma bakison wanke mun kwanoni da kyau ' saboda haka na yanke shawarar cenja ki" ."Subhanallah! Hajiya don Allah kiyi hak'uri ki dawo dani ' wallahi Allah ina miki aiki dakyau, Yaune kawai na makara".Tana fad'in haka hawaye na zubo mata a ido."Nifa ba kuka nace kimun ba, Saboda haka tashi ki fita"."Hajiya kiyi mata afuwa mana".Cewar d'anta."Bana son iskanci kaji ko?"."Allah ya huci zuciyarki".Safna kuwa ganin bata da niyyar hak'ura ne yasa ta tashi ta fita, Harta kama hanyar fita taji motsi a kitchen alamar ana wanke wanke."Bari inga wacce aka cenja".Ta fad'a a zuciyar ta.Tana k'arasawa wajen taga mahaifiyar k'awarta wato sumayya, Mamaki ne ya cika Safna ' hakan yasa ta juya da sauri tabar wajen.Haka Safna ta baro gidan cikin wani hali ' tafiya kawai takeyi tana share k'wallar dake idon ta, Har ta isa gida cike da sallama a bakin ta.Umma ta iske ita kad'ai a tsakar gida tana surfa dawa."Wa'alaiki-salaam Safna, Lafiya kika dawo?".Matso murmushi tayi ta sakar mata ' amma sam fuskarta babu walwala, Tukunna ta k'arasa kusa da Umma wacce tayi kasak'e tana kallon ta."Am... Umma ga wannan inji Hajiya".Safna mik'awa Umma kud'in tayi, Umma ta lura idanun ta cike suke da hawaye."Tooo Kud'in aikin ki aka biyaki da wuri haka?"."A'a Umma, Kud'in sallama ce".Nan gaban Umma ya fad'i tayi sauri ta jinginar da tab'arya jikin bango, Gami da dafe k'irji."Uban me kikayi? Iyi Safna wane laifin kika aikata? Sata kikayi mata?".Jin an abaci sata ne ' yasa Rumaisa fitowa daga d'akin su cikin sauri, Ita kuwa Safna hawaye kawai ke mata zarya a fuska."Haba Umma! Ya za'ai kici taimata sata? Bayan kinsan halayen Yaya Safna kaf...".Idanun Umma ne suka ciko da k'walla, Rumaisa tasahannu ta sharewa Safna hawaye tare da janyo tabarma suka zauna."Yaya Safna meya faru?".Nan Safna ta fad'awa Umma duk abinda ya faru, Umma waje ta samu ta zauna cike da ajiyar zuciya."Yanzu abunda Hajiya zatai mun kenan?"."Umma karki damu ' insha Allah zan fita in nemi aiki,Kuma insha Allah bazamu tagayyara ba"."Rumaisa ina Anisa?".Inji Safna."Tana Bacci".Mik'ewa Safna tayi idon ta akan Umma wacce duk damuwa sun bayyana a fuskar ta."Umma ki bani koda dubu d'aya ne cikin kud'in, Domin zan hau adaidaita sahu ' inshiga cikin gari"."Hm... Yanzu idan kinje ina zaki nufa?".Cewar Umma."Umma manyan kanfanoni(Companies) zan fara bincikawa ' ni koda share share ne su bani"."Hm... Meyasa baki tunanin k'asa da wannan? Meyasa baza kije gidaje ba? Safna ina ganin kamar neman aiki a kanfanoni zaiyi maki wahalar samu".Rumaisa ce tayi saurin kutsa baki cikin maganar."Haba Umma fatan alkairi kawai zamuyi mata"."Hakane Rumaisa".Umma na gama rufe baki ' ta zari dubu ta mik'awa Safna, Ta karb'a sannan tasa kai ta bar gidan cike darashin sanin inda zata fara nufa.Bayan Safna ta fito ne ' tayi sa'a tasami adaidaita ta shiga."Ina muka nufa?"."Cikin gari zamu shiga ' kawai kaita kewaye da wajajen manya manyan ma aikatun nan".Haka mai adaidaita sahu yaja napep d'inshi Safna na ciki, Har suka isa cikin gari.Mai napep zagaye ya dunga yi da ita ' tana k'arewa kowacce ma'aikata kallo kasancewar Garin babban gari ne ba k'arya. Safna wani k'ayataccen company ta hango cikin garege d'inshi motocin ma'aikata ne birjit iyakar ganin ka.Hakan yasa Safna yin saurin tsaida mai adaidaita sahun."Bawan Allah mu tsaya anan, Nawa ne kud'inka?".Tayi tambayar tana k'ok'arin saukowa daga napep d'in."Gaskiya malama bisa adalci ' dubu d'aya zaki bani"."Haba kaikuwa? Har dubu d'aya? Ina laifin d'ari ukku? Kaga fa dubu d'ayan nan ita kenan mun, Kuma wajen nan zan iya kaiwa yamma"."Shikenan kawo d'ari biyar ' gaskiya iyakar abunda zan iya ragewa kenan".Inji mai Napep.Safna mik'a mashi dubu d'ayan nan tayi, Shi kuma ya bata cenjin d'ari biyar sannan ta juya ta doshi cikin company d'in.*DEDICATION..._My Family!_*....*....B'OYAYYEN**AL'AMARI**2-3**_Pure Moment Of Life writers_*© ```Written```By*_Seemaluv_**2-3*Safna tafiya takeyi tana kallon yanayin Company d'in, Har ta isa bakin k'ofar shiga ciki ' jitayi ana."Hey! Hey!!!".Hakan yasa ta tsaya cak ' cike da fargaba, Wasu securities guda biyu sukayo kanta."Madam! How can we help you?".Nan bakin Safna ya hau rawa ' kasan cewar turancinkad'an kad'an take iya maidawa."Am... Sunana Safna ' nazo neman aiki ne a job".Nan securities d'in suka fara dariya tare da k'are mata kallo."Madam, ba'a d'aukan aiki anan, saboda haka ki tafi ki nemi wani wajen".Cewar d'aya daga cikin su."Don Allah koda shara ne zanyi muku ' sai ku rik'a biya don Allah".Tana gama fad'in haka suka rufe security door d'in, Hakan yasa Safna juyawa ta matsa daga wajen ' ta nemi waje ta zauna tana k'arewa motocin da ke wajen kallo.Bata ankara ba taji iskar hadari ta taso ' hakan yasa tabarin wajen cikin hanzari, Ta shige cikin wani garden wanda aka k'ayatar dashi matuk'a.Safna kujera ta samu ta zauna ' tare da d'aura kanta saman table, Haka akaita tsugaga ruwan sama ita kuwa tuni bacci ya kwashe ta a wajen.*35 MINUTES LATER*Safna taji ana buga table d'inda ta d'ora kanta akai, Hakan yasa ta farka daga baccin tare da d'ago kai domin taga waye.Wani Mutum ta gani sanye da suit a jikin shi ' Chocolate colour, Zubin masu kad'i."Who are you?".Nan nefa Safna ta kauda kanta daga kallon da take mashi ' ta koma kallon sama don duban hadari."Ashema angama ruwan!"Shima juyawa yayi ya dubi sama."Oh yes angama, and am advising u, koma wacece ke kibar wajen nan ' kafin nakira securities".Ai nan Safna ta mik'e tsaye gami da zaro ido."Don Allah ka taimaka mun! Wallahi aiki nazo nema ido rufe, Sir koda Shara ne zanyi muku sai ku biyani".Kujera yaja ya zauna, sannan yace."Hope kina da takaddun ki a hannu?"."Eh dasu nazo".Miko mata hannu yayi ta bashi takaddun nata ' ya duba tsaf sannan ya mik'a mata."Kamata yayi kije ki cigaba da karatun ki ' inyaso saiki dawo mu baki aiki"."Sir nidai a taimaka mun insamu da secondry schoolcertificate d'in"."Well... Is ok if that's what you want, Ammm are you good in making Coffee?"."Coffee?"."Yes Ruwan bunu"."Amm.. A'a...".Bata kaiga k'arasawa ba ya katseta da cewa."Then saikije ki koyo ' domin shine zai zama aikin ki dazaki rik'ayi a wannan Company"."OK! Na gode"."Am KAMAL ABUBAKAR ni ne mataimakin mai wannan Company ma'ana (P.A), You can call me Sir Kamal Ok?".Ta d'aga mashi kai alaman To."Sir, Yaushe zan fara aikin?".Murmushi yayi mata ' ganin ta cika sauri."Ai zaki fara ' har saikin gaji"."Hmm"."Yanzu tashi zakiyi ' ki biyoni mu shiga Office d'ina, Domin insamu wasu informations a tsanake.""Har ina ne wajen?".Kamal sauri yayi ya d'ago kai ya kalleta."Office d'ina mana!"."Hmm... Nidai da dai zamu iyayin komai anan"."What!? You are not serious!, Look inada aiki sosai a gaba na ' so ki tattara inaki inaki kibar wajen nan".Kamal tashi yayi cikin b'acin rai zai bar wajen tayi saurin rik'o gefen rigar shi, Gami da zubewa k'asa."Sir Kamal! Am sorry, ka taimakamun don Allah ' na yarda muje cikin office d'in naka amma kuma inaso ka rik'e Allah ya zuciyar ka"."It's Ok".Haka Safna ta bishi suka shige cikin ma'aikatar securities da sauran ma'aikatan kallonta kawai sukeyi, Ita kuwa Safna wurga idanu kawai takeyi tako ina har suka isa cikin Office d'in.Kamal a kujerar shi yaje ya zauna ' gami da zaro takarda, Sannan ya d'auki pen daga desk d'in shi, Zaifara rubutu kenan ya ankara ashe a tsaye take har yanzu."Madam!".Ta d'ago kai ta kalleshi tare da cewa."Sir!"."Zaki iya zama".Safna waje ta samu ta zauna ' sannan ta maida kanta k'asa Kamal ya cigaba da rubutu.Sai da ya kammala ne ya d'ago kai ya kalleta tare damik'a mata takaddan."Am..ansa wannan ' zaki dawo ranar monday! Wannan takaddan itace zaki nunawa securities idan kinzo, Understand?"."Yes"."Good! But before then, Ya kamata inji sunan ki ' infact you have to introduce yourself to me now!"."Ok, Sunana Safna Habib! Ina zaune ne ana k'auyen GATORIYA, Kuma ni marainiya ce mahaifina ya rasu' sai mahaifiya ta wacce take d'awainiya damu..."."Ya Salaam! Allah yaji k'anshi"."Amin"."Insha Allah zaki sami aiki Safna ' Zanyi magana da Ogana kinji?"."Nagode"."Shikenan! Zaki iya tafiya yanzu".Safna tashi tayi rik'e da takaddan ta ahannu, Tabar Office d'in cikin hanzari tana fita suka ci karo da wani har suna bangazar juna.Wani Handsome guy ne ' mai kamala shima cikin suit, Fari ne zubin larabawa ' da bloothode d'in shi sanye a kunne, Matashi ne d'an kimanin shekara 30."Whattaaa!!!".Abunda taji ya furta kenan tajuyo cikin tsoro ta kalleshi."Kayi hak'uri don Allah"."What? Are you blind? Wacece ke? Daga ina? And who gave you the permission to...".Bai k'arasa ba tayi saurin katseshi da cewa."Ha'a bana baka hak'uri ba? Hmm".Tana gama fad'in haka ta juya ta wuce.Mamaki ne ya cikashi ganin yadda ta juya ta wuce without begging."Wace yarinya ce wannan? She don't even have manner, i will surely find out ' mtsww".Yana fad'in haka ya juya tare da sanya hannun shi cikin aljihu ya wuce.*DEDICATED TO MY FAN'S**....B'OYAYYEN**AL'AMARI**4-5**_Pure Moment Of Life writers_*© ```Written```By*_Seemaluv_**4-5*Safna tana fita daga company d'in ta tsaya bakin titi domin samun abun hawa, Bata wani b'ata lokaci ba ta tari mai keke napep tai mashi kwatancen inda zai kaita ' kasancewar K'auyen su da cikin garin bashidanisa.Farin ciki ne cike ranta ' don kuwa ya kasa b'oyuwa afuskarta."Bawan Allah d'anyi sauri mana".Cewar Safna.Haka tasa mai keke-napep ya karawa keken shi gudu, Ita kuwa sai godewa Allah takeyi da k'osawa taga Umman ta.*AROUND 5:00PM*Safna ta isa gida ' nan ta sallami mai keke-napep sannan ta shige gida, Safna shiga tayi d'auke da sallama a bakinta ta iske Rumaisa tana jan ruwa a rijiya.Jin sallamar yasa Rumaisa d'ago kanta ta kalli Safna, Cikin jindad'i da nuna farin ciki Rumaisa ta aje gugar a gefe tayo kanta."Yaya Safna, sannu da dawowa ' Allah dai yasa antaki sa'a".Murmushi kawai Safna tayi gami da cewa."Umm! Ina Umma take?"."Umma tana d'aki tare da Anisa"."Ok".Safna da Rumaisa d'aki suka shige cike da sallama Umma ta amsa."Alhamdulillah Safna ya hanyar?"."Umma hanya lafiya k'alau, yana barku?"."Lafiya k'alau Safna, Allah dai yasa anci nasara!"."Insha Allah Umma".Cewar Safna.Bakin gado ta samu da zauna ' sannan ta cire hijab d'inta ta aje gefe, Tukunna ta cigaba da cewa."Umma! Kinga wannan takaddar?".Tayi mata nuni da takaddar dake hannun ta."Eh k'warai"."To mataimakin Ogan wajen ne yayi mun rubutu aciki ' yace kuma indawo ranar litinin da takaddar tabbas zan samu aiki"."A wane waje kika nema?".Cewar Umma."Umma a babbar ma'aikata ce (Company)"."Kinga Safna banason abunda zaije yajawo matsala?".Rumaisa ce tayi sauri ta shiga maganar."Haba Umma? Insha Allah babu wata matsala!"."To Shikenan! Allah ya shige mana gaba"."Amin"."Umma? Ina abinci na don nadawo da yunwa wallahi".Cewar Safna."Tuwo ne da miya gayacen ' ki d'auko kwano ki d'iba".Tashi Safna tayi gami da cewa To ta nufi wani d'an d'aki wanda anan ne suke aje kwanoni, Nan ta d'aukikwano ta dawo d'aki ta zuba tuwon taci.Bayan ta gama ne Umma tace."Safna?".Ta d'ago kai ta kalleta tare da cewa."Na'am"."Wai wannan ma'aikatar ta mecece?"."Umma ma'aikar tumatirin gwangwani ne"."To Allah yasa adace!".Rumaisa wacce ke gefe tana kallonsu ta amsa da amin.Safna suna cikin haka ne aka kira sallar magrib, Cikin nutsuwa gaba d'ayan su suka tashi sukayo alwala sannan sukayi sallah.Bayan sun idar ne Rumaisa ta tada Anisa domi itama tayi sallar.Atak'aice dai basu kwanta bacci ba saida sukayi sallar isha'i tukunna.Haka rayuwa tacigaba da juyawa ' da dad'i babu dad'i haka Safna da Umma ke fad'i tashi don ganin rayuwarsu ta inganta.*3DAYS LATER...*Yau take lahadi, Safna da Rumaisa tunda sassafe suka tashi suka fara aikin cikin gida ' kamar yadda suka saba, Sannan Umma ta tashi ta had'awa Rumaisa waran da zata sayar a k'ofar gida domin susamu su sami abinda zasu ci.B'angaren Kamal kuwa zaune yake cikin Office d'in shi yana danna laptop kira ya shigo cikin wayar shi, Ganin Oga ne yasa shi yin saurin d'agawa."Sir?"."Yes come to my office right now!"."Am on my way Sir".Kamal yana gama fad'in haka wayar ta yanke hakan yasashi tashi cikin hanzari ya nufi office d'in Oga.Kai tsaye ya shiga ciki ' ya sameshi a zaune saman kujerar shi ya juya baya."Sir, Am here".A hankali ya juyo ya kalli Kamal."Good! Zaka iya zama".Kamal zama yayi cike da ladabi."Kamal, Ina fatan komai suna tafiya yadda akeso?"."Eh sosai kuwa"."Good, there is a lady ' da naga ta fito daga office d'inka kwana biyu da suka wuce!"."Ohh Safna?"."I don't know!!!".Ya fad'i haka cikin fad'a da tsawa, Hakan yasa Kamal jin fargaba a cikin zuciyar shi."What did she think of herself? Who is she to you?!"."Sir am very sorry!"."Sorry for what? Me tazo nema?"."Oga, Aiki tazo nema with secondry certificate ' Sir please a taimaka mata marainiya ce! And is like itake d'awainiya da gidansu...."."So? What does that suppose to mean?"."Sir please ' yarinyar tausayi ta bani, Please koda coffee ne saita rik'a had'a maka ana biyanta sallary"."What??? Coffee? Did you just said Coffee? How? Wannan kucakar yarinyar? No no no! No way!!"."Sir! Bantab'a neman abu wajen ka ba narasa, Yakamata ka duba"."It's ok i will think about it! But mind you idan ma wannan ne ' then it would have to be competitive"."Hmm Okay Sir! Thank you... "."You may leave now! ".Kamal tashi yayi yabar office d'in cike da ladabi."Inhar Sunana *FAUZAN IMRAN!* then i will have to teach that what so called Safna ' a leason!, I will teach her how to respect her elders ' batada ladabi ko kad'an".Yana gama fad'in haka ya d'ora hannun shi saman laptop ya cigaba da advertising products d'in shi".*DEDICATED TO MY FAN'S*B'OYAYYEN* 👒
       👒 *AL'AMARI*

*_Pure Moment Of Life writers_*

© ```Written```     
       By
*_Seemaluv_*👄

                        *6-7*

    Yana cikin hakan ne ' yaji ana knocking k'ofa, Nan take ya bada iznin shigowa.
   Wata mace ce kyakkyawa slimly ajin farko ta shigo d'auke da murmushi a fuskarta, Shima ganinta yasashi sakin wani murmushi.
   K'arasawa tayi ciki taja kujera ta zauna, Sannan ta aje handbag d'inta a saman desk.
   "My Man!".
   "Sweet-Suhailah, Zakizo shine baki kirani a waya ba?".
   "Ehen, Am just missing you shiyasa! Kuma time d'inka kawai nakeso".
  Ta fad'i haka cikin shagwab'a.
   "You see?, Shiyasa naso ki kirani first kafin zuwanki ' and now ina abu mai muhimmanci kingani!".
   "Akwai abu mai muhimmanci da yawuce ni? For God sake Fauzan ' meyasa yanzu nake rasa gane kanka ne?".
   "You know what? Am a little busy now! Kije gida zanzo ind'auke ki mu fita".
   Yana fad'in haka idonshi na kan laptop, Haka ta tashi ta d'auki handbag d'inta ta fice ranta a b'ace.
   Wace ce Suhailah?, 'yace ga Alhaji Muktar. Ita kad'aice wajen mahaifinta, Mahaifiyar ta Allah yayi mata rasuwa tun tana k'arama.
   Hakan yasa Alhaji Muktar shagwab'a ta matuk'a! Kasancewar shid'in mai kud'ine.
   Haka company d'in Mr-Fauzan ya cigaba da yalwata da samun k'arin fasaha.
   Mr-Fauzan saida ya tabbatar yayi announcing cewa ' zaiyi k'arin ma'aikata wad'anda suka kware a fannin had'a coffee.
   Yana gama hakan ya rufe laptop d'inshi, Sannan ya d'auki wayarshi k'irar iphone7 da car-key d'inshi ya fito daga office d'inshi ' da alama gida zai koma.
   Yana cikin tafiya cikin isa ' suka had'e da P.A Kamal shima yana fitowa daga nashi office d'in, Nan ya dakata cikin ladabi irin nasu na workers.
   "Sir are you leaving?".
   "Yes of cause ' yanzu nakeso in koma gida".
   "Ok sir."
 Nan Mr Fauzan ya juya ya fita daga company d'in.
   Bayan fitarshi ne ya bud'e motarshi yashiga tukunna yaja cikin class ya nufi gida.
   *Wane ne Mr-Fauzan?*, Mr-Fauzan mutum ne mai kud'i! Kuma mutum ne maison iyayen sa, Ya kasance d'an gata kuma shid'in kyakkyawa ne hakan yasa 'yan mata keson shi duk inda yaje, Amma saidai kash Mr-Fauzan mutum ne mai wulak'anci musamman akan mace.
   Mr-Fauzan d'ane ga Alhaji Imran ' haka zalika d'ane ga Hajiya Saratu, Alhaji Imran da Hajiya Saratu 'ya'ya biyu suka mallaka arayuwarsu ' Mr-Fauzan da Khairat wacce take da shekara 19, Hakan yasa suka sami gata da duk wani abunda suke buk'ata na rayuwa!.
  Kasancewar Alhaji Imran mai kud'ine cikin garin Kaduna yana cikin jerin mutanen da ake kwatance dasu, Amma saida Hajiya Saratu macece wacce bata k'aunar talaka ' batason talaka ya tab'e ta sam.
   Mr-Fauzan yana yin packing ya fito cike da kuzari ya shige cikin gida,  Da Mummy ya fara had'a ido wacce ke zaune a babban parlor saman kujera ' sai Khairat dake kwance ta  d'ora kanta bisa cinyar Mummy.
   Mr-Fauzan sallama yayi suka amsa tukunna ya sami waje ya zauna tare da sauke ajiyar zuciya.
   "Son da alamun kasha aiki a office d'in nan yau Right?."
  Inji Mummy.
   "Eh Mummy sosai kuwa."
  Nan ya kalli Khairat wacce hankalinta ke kan wayarta k'irar iphone6+ ' tana chatting abunta.
   "Ke bakisan kice sannu da dawowa bako?."
  Cikin k'unk'uni tace.
   "Sannu da dawo...."
 Ta k'arashe maganar cike da zunb'uro baki.
   Abunne ya bashi haushi ya zaburo zaikai hannu ' tare da cewa.
   "Ke ni kikema k'unk'uni?."
  Mummy ce tayi saurin shiga maganar da cewa.
   "A'a banason haka! Karka sake! Daga dawowar ka?, Tashi ka wuce part d'inka Mairo tana nan zata kawo maka abincin ka."
  Mr-Fauzan tashi yayi gami da cewa.
   "Mum! Zaki jawa yarinyar nan tasha wahala a banza."
  Harya kai bakin steps Mummy ta dakatar dashi.
   "Son?."
  Cak ya tsaya ya juyo ya kalleta.
   "Na'am."
   "Dawo inason magana dakai."
 Dawowa yayi ya zauna a gajiye ' sannan Mummy taci gaba da cewa.
   "Suhailah bata dad'e da barin nan ba! And tazomun da complain akanka, Son meyasa kakeyin haka?."
   "Ohh Mummy k'arata ta kawo maki kenan?."
   "Look Son! Banason haka ' kuma inaso ka gane Suhailah iyayenta suna da kud'i, Wace yarinya zaka kawo wacce zata fita? To bari kaji ingaya maka ' gwara tunda wuri kaje ku shirya da ita, Domin ni zuciyata ta ruga ta aminta da ita."
   "Haba Mum, Nifa ba k'aramin yaro bane i know what am doing!..."
   Yana fad'in haka ya tashi yayi tafiyar shi.
   "Ohh haka zaka fad'amun? To bari Daddynku ya dawo zaka maimaita ai."
   Mr-Fauzan yana shiga part d'in shi ya wuce bedroom d'inshi direct ya fad'a saman gado, Abubuwa iri iri sukaita fad'o mashi arai ' da ranar da suka bangaji juna da Safna da kalmarta ta k'arshi data furta, Inda tace.
   "Ha'a bana baka hak'uri ba? Hmm."
   Zaki yaja gamida tashi zaune, A zuciyar shi yace.
   "Yarinyar nan! Zaina zame mata leason arayuwar ta, Zan bata aikin kodan in bak'anta mata."
   Yana gama ayyana haka ne ' yaji ana knocking k'ofa.
   "Waye ne?."
   "Mairo ce abincin na kawo maka, Kayi hak'uri banson ka dawo bane sai yan...."
  Bata k'arasa ba ya katseta da cewa.
   "Naji!! Ya isa haka, Ki shigo ki ajemun a parlor saman saman table d'ina."
  Haka Mairo tayi taje ta aje sannan ta bar part d'in.
   Mr-Fauzan saida ya cire kayan shi ya ragemai daga shi sai boxer da singlet ' sannan yaje ya zauna yaci abincin.
    Yana gamawa ya shige bathroom yayo wanka, Sannan ya shirya cikin manyan kaya shadda fara ' ya d'auki car-key d'in shi ya fita.





*DEDICATED TO MY FAN'S*
❤❤❤👄👄*....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_Pure Moment Of Life writers_*© ```Written```By*_Seemaluv_**8-9*Tunda Mr-Fauzan yasa kai ya fita ' bai tsaya ko ina ba sai a wani k'ayataccen restaurant wanda wajen ya zame mashi jiki kusan kullun sai yazo wajen, Kasancewar akwai wajen hutawa kala kala.Nan wajen yake had'uwa da abokanshi 'ya'yan manya kamarshi.B'angaren Safna kuwa ' a zaune suke a tsakar gida kamar kullun, Anisa nayiwa Umma tausa a k'afarta ita kuma Safna da Rumaisa hirarsu kawai sukeyi."Umma wallahi duk na k'osa gobe tazo."Cewar Safna."Saboda me?.""Hm! Umma, Kin manta gobe akace inkoma za'a bani aiki?.""Oh! Hakane fa, Sam na mance ' Safna Allah ya kaimu goben lafiya.""Ameen."Safna k'arar loud-speaker taji na masallaci alamar za'a kira Sallar magrib, Hakan yasa ta juya ta kalli murhu taga babu komai akanshi."Umma?."Umma d'ago kai tayi ta kalleta, Tare da cewa."Na'am!.""Umma me za'a d'ora ne? Don naga magriba tayi."Abunda Safna ta fad'ane yasa Umma sauke ajiyar zuciya."Hmm... Kema dai kamar kikan mance ne ko? Safna inda akwai abun sarrafawa aida baki ganmu haka zaune ba!.""A'a akwai d'ari a waje na ' cenjin da yarage na cefane, Bari inbawa Anisa koda lipton sai a siyo musha.""To, amma kinada kud'in da zaki bawa mai keke napep ne gobe?"Inji Umma."Eh Umma akwai d'ari biyu."Kai kawai Umma ta d'aga sannan Safna ta mik'e ta nufi d'aki ta d'aga pillow, Ta d'auki d'ari tukunna ta fito ta mik'awa Anisa."Ani, Gashi kije shagon malam kice ya baki lipton na d'ari."Anisa ansa tayi cikin hanzari ' ta janyo hijabin ta dake saman igiya ta sanya ta fita a guje, Kasancewar tanajin yunwa.Cikin 'yan lokuta k'alilan Anisa ta dawo, Nan Safna ta karb'a sak'on sannan ta d'ora ruwan zafi a murhu, Tukunna dukkansu sukayo alwala suka shige d'aki domin sallah.Saida suka idar, Sannan Safna ta tashi ta zubo ruwan zafin a kwano ' ta kawo d'aki."Rumaisa tashi kije ki d'auko kofuna, da abunda zan juya ruwan lipton d'in."Cikin hanzari Rumaisa ta tashi ' bata wani b'ata lokaci ba ta dawo da 3cups da spoon a hannunta."Akwai siga a k'ark'ashin gado, Anisa sa hannu ki d'auko."Cewar Umma.Anisa hannu tasa ta janyo sugar kamar yadda Umma tace , Ta mik'awa Safna ta zuba gamida jujjuyawa.Saida ta kammala tsaf ' sannan ta zubawa kowa a cup suka fara sha."Aiko gobe insha Allah ' Rumaisa ke da Anisa zan aikeku gidanmu wajen baba, Idan yanada dubu uku ya baku."Nan Safna ta had'e rai tare da ajiye cup d'in da ke hannun ta."Haba Umma? Meyasa kikeson tambayarsa kud'i? Bayan kinsan fanninshi bakomai kike samuba.""Bana son iskancin banza da rashin kunya! ' aiko ba komai inada hak'k'i akansa, Kuma ya zama dole in tambayeshi, Idan har ban tambayeshi ba suwa kikeso in tambaya? Ko kinada abunda zaki bada ne?.""A'a Umma kiyi hak'uri, Insha Allah ' Allah bazai barmu haka ba ai! Allah zai bani abunda zan kula daku, Amma Umma ko 'yan uwa ai zaki iya tambayarsu."Nan Umma taja tsaki tacigaba da kurb'ar ruwan lipton d'in ta.*AROUND 9:00PM*Mr-Fauzan ya dawo ' sai da yayi packing motarshi, Tukunna ya fito ya nufi cikin gida.Mr-Fauzan iske Mummy da Daddy yayi zaune a parlor suna tattaunawa."Yawwa Alhaji, Gashi ai ya dawo."Abunda yaji Mummy ta furta kenan ' hakan yasashi k'arasawa cikin parlon d'auke da sallama Daddy ya amsa.Mr-Fauzan zama yayi saman kujera ' cike da ladabi, Sannan Daddy yace."Am!!... Fauzan my Son, Hope ka dawo cikin k'oshin lafiya?.""Lafiya k'alau Daddy.""Good!."Daddy gyaran murya yayi ' ya cigaba da cewa."D'azu na dawo Mum d'inku ke fad'amun wata magana, Akan Yarinyar da takeso ka aura.""Ohhh! Come on... Mummy how many times zamuyi wannan maganar? Daddy am not a kid ' nasan abunda nakeyi fa! For godsake Mummy meyasa kikeson maida zance baya?.."Mummy zatayi magana kenan ' Mr-Fauzan ya tashi fuuuu! Ya wuce part d'inshi."Ka gani ko? Kaga abunda nake fad'a maka ai, Kwata kwata Fauzan ya gama raina ni ' to shikenan na barshi yaje ya nemi duk wacce taimashi, Amma karya sake ya kawomun talauci cikin gida!!!."Mummy na gama fad'in haka ta tashi ta haura part d'insu, Daddy kuwa mamaki ne ya cikashi yasa saidai ya girgiza kai kawai ' ya cigaba da kallon news.Daddy *around 10:30pm* ya tafi taje ya kwanta, Mr-Fauzan tunda ya wuce d'aki yayi wanka ya komaya kwanra ' daga nan bacci yayi awon gaba dashi.*** *** *** *** *** *** ***Washe gari...*AROUND 6:00AM*Safna ta tashi ' bayan tayi sallah ta fito ta fara kinkintsa gida, Tana cikin shara ne Umma ta fito daga d'aki nan Safna ta zuk'unna har k'asa ta gaisheta, Sannan ta mik'e tsaye."A'a bar sharar nan ' kije kija ruwa a rijiya kiyi wankadon ki tafi da wuri, Sai Rumaisa tayi sharan.""Uhum."Aje tsintsiyar tayi, Sannan taje taja ruwa ta nufi bayi dashi.Koda ta fito daga wanka ta iske Umma tana shirin dama koko ' haka Safna ta wuce d'aki ta hau shafa mai da powder cikin sauri.Bayan ta gama ne ta d'auko hijab d'inta pink color daatamfa mai ratsin pink, Duk da kayan sun kod'e hakan bai hanata yin shiga ta mutunci ba.Safna tsakar gida ta fito ' ta nufi wajen Umma ' Umma ta zuba mata koko, Sannan ta karb'a ta shanye ba tareda ansa sugar ba."To Umma nizan wuce.""Allah ya tsare ' Allah kuma yasa asami abunda akaje nema."Amin Safna tace, Sannan tasa takalminta ta fice.*DEDICATED TO MY LOVELY FAN'S**....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_Pure Moment Of Life writers_*© ```Written```By*_Seemaluv_**8-9*Tunda Mr-Fauzan yasa kai ya fita ' bai tsaya ko ina ba sai a wani k'ayataccen restaurant wanda wajen ya zame mashi jiki kusan kullun sai yazo wajen, Kasancewar akwai wajen hutawa kala kala.Nan wajen yake had'uwa da abokanshi 'ya'yan manya kamarshi.B'angaren Safna kuwa ' a zaune suke a tsakar gida kamar kullun, Anisa nayiwa Umma tausa a k'afarta ita kuma Safna da Rumaisa hirarsu kawai sukeyi."Umma wallahi duk na k'osa gobe tazo."Cewar Safna."Saboda me?.""Hm! Umma, Kin manta gobe akace inkoma za'a bani aiki?.""Oh! Hakane fa, Sam na mance ' Safna Allah ya kaimu goben lafiya.""Ameen."Safna k'arar loud-speaker taji na masallaci alamar za'a kira Sallar magrib, Hakan yasa ta juya ta kalli murhu taga babu komai akanshi."Umma?."Umma d'ago kai tayi ta kalleta, Tare da cewa."Na'am!.""Umma me za'a d'ora ne? Don naga magriba tayi."Abunda Safna ta fad'ane yasa Umma sauke ajiyar zuciya."Hmm... Kema dai kamar kikan mance ne ko? Safna inda akwai abun sarrafawa aida baki ganmu haka zaune ba!.""A'a akwai d'ari a waje na ' cenjin da yarage na cefane, Bari inbawa Anisa koda lipton sai a siyo musha.""To, amma kinada kud'in da zaki bawa mai keke napep ne gobe?"Inji Umma."Eh Umma akwai d'ari biyu."Kai kawai Umma ta d'aga sannan Safna ta mik'e ta nufi d'aki ta d'aga pillow, Ta d'auki d'ari tukunna ta fito ta mik'awa Anisa."Ani, Gashi kije shagon malam kice ya baki lipton na d'ari."Anisa ansa tayi cikin hanzari ' ta janyo hijabin ta dake saman igiya ta sanya ta fita a guje, Kasancewar tanajin yunwa.Cikin 'yan lokuta k'alilan Anisa ta dawo, Nan Safna ta karb'a sak'on sannan ta d'ora ruwan zafi a murhu, Tukunna dukkansu sukayo alwala suka shige d'aki domin sallah.Saida suka idar, Sannan Safna ta tashi ta zubo ruwan zafin a kwano ' ta kawo d'aki."Rumaisa tashi kije ki d'auko kofuna, da abunda zan juya ruwan lipton d'in."Cikin hanzari Rumaisa ta tashi ' bata wani b'ata lokaci ba ta dawo da 3cups da spoon a hannunta."Akwai siga a k'ark'ashin gado, Anisa sa hannu ki d'auko."Cewar Umma.Anisa hannu tasa ta janyo sugar kamar yadda Umma tace , Ta mik'awa Safna ta zuba gamida jujjuyawa.Saida ta kammala tsaf ' sannan ta zubawa kowa a cup suka fara sha."Aiko gobe insha Allah ' Rumaisa ke da Anisa zan aikeku gidanmu wajen baba, Idan yanada dubu uku ya baku."Nan Safna ta had'e rai tare da ajiye cup d'in da ke hannun ta."Haba Umma? Meyasa kikeson tambayarsa kud'i? Bayan kinsan fanninshi bakomai kike samuba.""Bana son iskancin banza da rashin kunya! ' aiko ba komai inada hak'k'i akansa, Kuma ya zama dole in tambayeshi, Idan har ban tambayeshi ba suwa kikeso in tambaya? Ko kinada abunda zaki bada ne?.""A'a Umma kiyi hak'uri, Insha Allah ' Allah bazai barmu haka ba ai! Allah zai bani abunda zan kula daku, Amma Umma ko 'yan uwa ai zaki iya tambayarsu."Nan Umma taja tsaki tacigaba da kurb'ar ruwan lipton d'in ta.*AROUND 9:00PM*Mr-Fauzan ya dawo ' sai da yayi packing motarshi, Tukunna ya fito ya nufi cikin gida.Mr-Fauzan iske Mummy da Daddy yayi zaune a parlor suna tattaunawa."Yawwa Alhaji, Gashi ai ya dawo."Abunda yaji Mummy ta furta kenan ' hakan yasashi k'arasawa cikin parlon d'auke da sallama Daddy ya amsa.Mr-Fauzan zama yayi saman kujera ' cike da ladabi, Sannan Daddy yace."Am!!... Fauzan my Son, Hope ka dawo cikin k'oshin lafiya?.""Lafiya k'alau Daddy.""Good!."Daddy gyaran murya yayi ' ya cigaba da cewa."D'azu na dawo Mum d'inku ke fad'amun wata magana, Akan Yarinyar da takeso ka aura.""Ohhh! Come on... Mummy how many times zamuyi wannan maganar? Daddy am not a kid ' nasan abunda nakeyi fa! For godsake Mummy meyasa kikeson maida zance baya?.."Mummy zatayi magana kenan ' Mr-Fauzan ya tashi fuuuu! Ya wuce part d'inshi."Ka gani ko? Kaga abunda nake fad'a maka ai, Kwata kwata Fauzan ya gama raina ni ' to shikenan na barshi yaje ya nemi duk wacce taimashi, Amma karya sake ya kawomun talauci cikin gida!!!."Mummy na gama fad'in haka ta tashi ta haura part d'insu, Daddy kuwa mamaki ne ya cikashi yasa saidai ya girgiza kai kawai ' ya cigaba da kallon news.Daddy *around 10:30pm* ya tafi taje ya kwanta, Mr-Fauzan tunda ya wuce d'aki yayi wanka ya komaya kwanra ' daga nan bacci yayi awon gaba dashi.*** *** *** *** *** *** ***Washe gari...*AROUND 6:00AM*Safna ta tashi ' bayan tayi sallah ta fito ta fara kinkintsa gida, Tana cikin shara ne Umma ta fito daga d'aki nan Safna ta zuk'unna har k'asa ta gaisheta, Sannan ta mik'e tsaye."A'a bar sharar nan ' kije kija ruwa a rijiya kiyi wankadon ki tafi da wuri, Sai Rumaisa tayi sharan.""Uhum."Aje tsintsiyar tayi, Sannan taje taja ruwa ta nufi bayi dashi.Koda ta fito daga wanka ta iske Umma tana shirin dama koko ' haka Safna ta wuce d'aki ta hau shafa mai da powder cikin sauri.Bayan ta gama ne ta d'auko hijab d'inta pink color daatamfa mai ratsin pink, Duk da kayan sun kod'e hakan bai hanata yin shiga ta mutunci ba.Safna tsakar gida ta fito ' ta nufi wajen Umma ' Umma ta zuba mata koko, Sannan ta karb'a ta shanye ba tareda ansa sugar ba."To Umma nizan wuce.""Allah ya tsare ' Allah kuma yasa asami abunda akaje nema."Amin Safna tace, Sannan tasa takalminta ta fice.*DEDICATED TO MY LOVELY FAN'S**....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_Pure Moment Of Life writers_*© ```Written```By*_Seemaluv_**_@Kamar yadda nasami k'orafin readers da dama akan rashin k'arashe B'OYAYYEN AL'AMARI da banyi ba, To Alhamdulillah yanzu dai na aje wancen na kuma cigaba da wannan...._**10-11*Safna na fita bata wani wasting time ba ' ta tari mai keke-napep ta shiga, Tukunna taimashin kwatancen inda zai kaita.Bata isa company d'in ba sai wajen k'arfe *8:00am*, Haka ta mik'awa mai keke-napep kud'insa ya wuce ' ita kuma ta shige cikin company d'in da takaddar ta Kamal yace ta dawo da ita a hannu.Dai dai bakin k'ofar shiga security ya tsare ta."Kina da buk'atar taimako ne?."Ya fad'a cikin harshen turanci."Yes."Nan Safna ta mik'a masa Application letter d'in ya karance ta tsaf."Sir Kamal ya baki ko?.""Eh.""Ok barima inkaiki har Office d'in nasa."Haka Safna tabi bayan security man d'in, Har saida ya shigar da ita office d'in tukunna ya juya yayi tafiyarsa.A zaune Safna ta iske Kamal ' tare da laptop a gabanshi.Jayo attention d'inshi tayi da cewa."Good morning, Sir!."A hankali Kamal ya d'ago kai ya kalleta da manyan idanun shi, Ganin itace yasa shi rufe laptop d'in gamida calming hands d'in shi."Have a seat!."Abunda yacewa Safna kenan ' ta sami waje ta zauna, Tukunna ya kafeta da ido."I have been expecting you!."Nan tad'an sunkuyar da kai alaman ladabi.Nan ya d'aga waya ya kira messenger d'inshi.Cikin hanzari messenger ya shigo cikin office ' cike da ladabi."Sir! Gani.""Yes, Inaso ka kaita inda ake screening coffee makers.""Ok."Haka Safna ta tashi jiki a sanyaye tabi bayan messenger d'in, Har sunkai bakin k'ofa ya tsaidai ita da cewa."Be praying."Uhum, Kawai Safna tace suka fice daga wajen ' waniwaje suka shiga an k'ayatashi da kujeru yadda kasan parlor komai pink colour yayi kyau sosai, Ita dai kalle kallenta kawai takeyi bata ankara ba taji ance."Madam, Ki sami waje ki zauna."Inji Messenger.Saida ya tabbatar ta zauna ' sannan ya juya yabar wajen.Bayan ta zauna ne ta ankara da mutanen da ke zazzaune a wajen, Mata ne dukkansu ' sunci kwalliya sunci gyale wasuma babu ko gyalen a jikinsu, Daka gansu kaga 'ya'yan manya.Cikin 'yan lokuta k'alilan aka kawowa kowanen su cup&spoon da ingredients d'in da zasuyi amfani dashi wajen making coffe d'in.Nan Safna taji wata murya tace "start!".Kasancewar bata tab'a had'awa ba hakan yasa ta fara kallon yadda ta kusa da ita keyi, Cikin hikima Safna ta fara making coffee har ta gama ' sannan tajiansake cewa."Your time is off! Young ladies."Mr-Fauzan yayi maganar in slangs.Nan ne Safna ta d'ago kanta domin taga inda maganar ke fitowa, Hakan yayi daidai da juyowar Mr-Fauzan wanda yake zaune a saman kujerar shi ' nan sukayi ido hudu da Safna."Subhanallahi! Wannan bashine wanda nabige shi ' abisa rashin sani ba?."Tayi tamabayar a cikin zuciyar ta.Nan take zufa ta fara karyo mata.Shi kuwa Mr-Fauzan tunda ya fahimci Safna cike take da tsoro yasaki wani irin murmushin da baikai zuci ba.Nan ya umarce su ' da kowaccen su ta kawo mashi coffee d'inda ta had'a yayi tasting, Haka sukaita tashi suna kaiwa yana tasting kuma yana rubuta masu score.Safna ganin an kusa kaiwa kanta ne yasa ' ta fara addu'o'i, Tana gama rufe baki line d'in ya kawo kanta' nan ta tashi cikin sauri rik'e da cup d'inta ta nufi wajen shi.Mr-Fauzan ko kallon ta beyiba ya karb'a yayi tasting ya rubuta mata score d'inta, Sannan ta juya ta koma ta zauna.*After some minutes* ya tashi ya koma office d'inshi,messenger na biye dashi, Bayan Mr-Fauzan ya zauna ne messenger yace."Sir, akwai wani aike ne?.""A'a babu, Zaka iya fita."Bayan fitar shine ' Mr-Fauzan ya d'aga waya ya kira P.A Kamal, Ringing d'aya zuwa biyu tayi ya d'auka."Sir?.""Kamal, Kazo yanzu.""Ok."Abunda Kamal ya fad'a kenan Mr-Fauzan ya kashe wayar.Cikin 'yan lokuta k'alilan Kamal ya shigo cikin Office d'in Mr-Fauzan, Bayan ya zauna ne Mr-Fauzan ya mik'o mashi paper tare da cewa."Kamal, inaso kaje kasa a nuna ma Safna Habib and Muneeba Imran yanayin aikinsu ' sauran kuma a sallamesu because they are not qualified.""Ok."Abunda Kamal yace kenan ' sannan ya juya yabar wajen, Jin sunan Safna a ciki abun yasa shi farinciki matuk'a.Kamal hole d'in ya shiga da kansa, Nan yayi calling attention d'in ko wacce a wajen.Kamal ' hak'uri ya fara bama wad'anda basu sami aikin ba, Ita kuwa Safna babu abinda gabanta keyi inba fad'uwa ba.Bayan ya gama dogon bayanin shine ' ya kira sunan Safna da Muneeba tare da cewa."Safna Habib da Muneeba Imran, Su kad'ai ne aka d'auka amatsayin Coffee makers."Safna mik'ewa tayi cikin jin dad'i tana murmushi, Don kuwa samun aikinta shine burinta na farko dayafara cika.Kamal ganin yadda hole d'in ya hargitse ne ' yasa shikomawa Office tare da kiran messenger d'inshi a waya cewa."Kaje cikin hole d'in nan, Ka zomun da Safna Habib da kuma Muneeba Imran."To kawai d'an aiken(messenger) yace, Sannan Kamal ya kashe wayar shi.B'angaren Safna kuwa! Ai baki har kunne, Nan take ta fara neman Muneeba gami da kwala mata kira."Muneeba Habib!."Muneeba kuwa jin yadda aketa kiran sunan tane yasata juyowa a tsorace' cikin sa'a kuwa sukayi ido biyu."Lafiya kiketa kiran sunana?.""Lafiya kalau ' Muneeba nice Safna Habib, Ina fata zamu had'a kanmu domin muyi aiki tare."Muneeba tab'e baki tayi cike da downgrading ta juya tacigaba da harkar gabanta, Ba tare da tacewa Safna komai ba.Safna ganin haka ne yasa ta koma ta zauna ' jiki a sanyaye taci gaba da k'arewa mutanen da ke wajen kallo.©Seemaluv_Novels*....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_Pure Moment Of Life writers_*® ```Written```By*_Seemaluv_**_Ina dai sake bama Fan's d'ina hak'uri , Masu bin Novel d'ina ' Ayyuka ne sukai yawa..._**12-13*Suna cikin haka ne Messenger yazo cikin hole d'in yakira sunayen su kamar yadda Sir-Kamal ya umurce shi, Safna jin ankira sunan ta yasa tayi saurin mik'ewa tsaye tare da k'arasawa wajen shi.Ita kuwa Muneeba saida aka kira sunan ta ' kusan sau uku tukunna taje inda ake kiranta, Nan Messenger ya juya zuwa office d'in Sir-Kamal su kuma suna biye dashi a baya.Bayan sun isa bakin office d'inne yayi musu nuni da yatsa alaman su shiga, Bayan shigar sune ya juya yayi tafiyarsa.Safna shiga tayi tare da yin sallama ' Muneeba na binta abaya.Sir-Kamal ansa sallamar yayi ' ba tare daya d'ago kai ya kallesu ba har saida ya kammala danna laptop d'inshi."Ku zauna."Ya fad'a haka yana musu nuni da kujerar dake gefensu.Bayan sun zauna ne yace."Hope kun shirya ma aikin nan?.""Insha Allah."Suka fad'a a tare."Good! So yanzu zan fad'a muku yadda aikin yake."Sai da yad'an d'auki lokaci yana kallonsu, Sannan yace."Ko waccen ku za'a rik'a biyanta salary akan naira 100,000(dubu d'ari) ' kuma idan har kika tsaya kan aikin ki, To salary d'inki zai ruk'a increasing."Muneeba smiling tayi tare da gyara zama, Sannan Sir-Kamal ya cigaba da cewa."Early morning *7:00am* idan kukazo aiki ' zaku had'a coffee ku kaima workers, Sannan After that zaku bi kowane Office ku kai."Sir-Kamal, Bayan ya gama musu bayani ne ' ya mik'e tsaye tare da cewa."Ku tashi muje in kaiku Store."Safna da Muneeba tashi sukayi suka bi bayan shi zuwa store, Suna isa wajen yasa hannu ya murd'a handle d'in k'ofar ya bud'e suka shige ciki.Nan ya nuna musu komai da komai, Wanda zasuyi amfani dashi fannin aikinsu.Sir-Kamal, Bayan ya gama introducing masu komai ne ' harya juya zai koma office sai kuma ya tsaya gami da juyowa ya kalli Safna wacce hankalin ta kekan cups d'inda ke wajen."Safna Habib!."Jin kiran sunanta da yayi ne ' yasa tayi saurin juyowa ya kalleshi, Tare da cewa."Yes Sir?.""Ki biyoni zuwa Office."Ok tace ' sannan ta bishi suka wuce, Muneeba ganin haka yasa ta tab'e baki tare da calming hands d'inta zuciyarta cike da sak'e sak'e.Safna bayan isarsu cikin office d'in ne, Yayi mata iznin zama ' tukunna shima ya zauna."Am.. Safna i need to discus something with you!.""Ok Sir.""You see!, Nan Company ne mai son tsafta da gayu ' da k'yale k'yale you know! Da dai sauransu."Nan ta fara duban jikin ta ' tana mamaki."No, Bawai bakida tsafta bane ' what i mean is that, Ki k'ara because matsalan ba daga ni bane ' understand?."Kai Safna ta d'aga mashi alaman Eh."Anyway! Koma yayane dai ' a hankali zaki fahimta.""Insha Allah! Zan gyara."Cewar Safna."Good! Zaki iya tafiya."Safna tashi tayi tabar office d'in, Harta nufi side d'insu sai kuma ta tsaya ' a zuciyarta tace."Ina d'aya daga cikin ma'aikatan company d'in nan, Ya kamata in kewaya inga ko ina."Bayan ta ayyana haka a ranta ne ' ta saki murmushi, Tare da juyawa ta nufi wani b'angaren da yake tsit! Tamkar babu mutane.A hankalin Safna ke tafiya ' kasancewar yadda wajen yake ba hayaniya, Wata k'ofa ta hango and'an bud'eta kad'an.Safna k'arasawa wajen tayi ta bud'e k'ofar. Guess-room ne k'ayatacce, Komai na cikinsa designer ne ' ganin haka yasa ta shigewa ciki domin ta bama idonta abinci.Tana shiga ta sami waje ta zauna a bakin gado ' tana tab'a drowers d'in dake gefen gadon."Rayuwa kenan! Idan da ranka zakasha kallo."Ta fad'i haka tana murmushi.B'angaren Mr-Fauzan, Zaune yake tare da ma'aikatan shi a chamber inda suke had'uwa suna meeting ciki kuwa harda Sir-Kamal.Meeting d'in bai wani d'auki lokaci ba suka kammala, Kowa tashi yayi ya koma kan aikin shi ' Sir-Kamal office ya koma yayi zaman shi.Mr-Fauzan kuwa yana fitowa daga chamber ' kai tsaye ya nufi guess-room d'inshi domin ya kwanta ya huta.Koda ya doshi wajen gani yayi k'ofar a bud'e, Hakan yasa shi k'arasawa wajen da izza tare da cewa."Is like ' wani ya shiga ya barta a bud'e, To waye kuma meyasa?."Safna jin ana magana sama sama ne ' yasa tayi hanzarin b'oyewa bayan labule cike da tsoro.Mr-Fauzan koda ya shigo ciki ' baiga kowa ba illa takalmi daya gani a bakin k'ofa, Hakan ya k'ara tabbatar mashi da cewa akwai mutum a ciki.Nan ya fara dube dube ' shine har under bed da k'ark'ashin kujera, Amma baiga komai ba.Safna kuwa jikinta rawa kawai yakeyi."Ya Rabb! Ya kafitar dani lafiya."Ta fad'i haka a cikin zuciyarta.Mr-Fauzan bakin gado ya samu ya zauna, Safna gumi kawai take had'awa bata ankara ba taga kenkyaso a saman hijabin ta.A 360 Safna ta fito daga bayan labule ' sam ta mantada mutum cikin d'akin, Cikin rawar jiki da tsoro ta yaye hijabin dake jikinta ta yarfar dashi gefe, Sannanta koma jikin bango ta jingina tare da rufe idonta tana maida numfashi.Mr-Fauzan kuwa abun dariya ya bashi ' amma sam bai bari ta fito fili ba, A zuciyar shi yace."Oh God! Ji yadda take sakin ajiyar zuciya, Tamkar taga wani mugun abu."Mr-Fauzan tsayawa yayi yana k'arewa halittar jikinta kallo.Kasancewar Safna rigar dake jikinta tad'an matseta kad'an duk da dai kayan duk sun kod'e, Don akwai inda yad'an fara yagewa, Sannan ga gashin kanta yazubo har izuwa k'asan k'irjin ta.kasancewar kitson dake kanta all-back ne, Uhm abunka da bafullatana ' abun dai ba'a cewa komai.Har izuwa yanzu Safna runtse take da idonta ' tana ajiyar zuciya, Mr-Fauzan kuwa murmushin mugunta ya sakar mata."Lallai yanzu zaki dawo hayyacinki kuwa!."Ya fad'i haka a zuciyar shi, Tare da mik'ewa tsaye."What!!! You?."Ya furta hakan cikin tsawa, A razane Safna ta bud'e idonta ' sai a wannan lokacin ne ta tuna cewa akwai mutum a d'akin.Safna koda suka had'a ido da Mr-Fauzan saida cikinta ya murd'a, Ganin babu hijab a jikin tane ' yasa tayi saurin kare jikinta da hannayen ta.Yunk'urawa tayi zata d'auki hijabin ta yayi saurin take hijabin da k'afarshi tare dayin calming hands."First! What are you doing in my guess-room."Safna sunkuyar da kanta tayi ' ba tare da tace komai ba."Bakiji ba?.""Sir, please am sorry ' kayi hak'uri wallah..."Bata k'arasa maganar ba ya daka mata tsawa, Da cewa."Answer me!!!, What are you doing in my guess-room!.""No answer right? Dama matsalan ku talakawa kenan!, Sata kikazo yi dama?."Zaro ido Safna tayi ' tare da girgiza mashi kai alaman a'a."Then what? Ki fad'amun idan ba sata ya shigo dake ba to meye?."Safna k'walla ce cike a idonta k'iris ya rage hawaye su zubo."I wil expose you infront of everyone, Gobe bazaki k'ara shiga wani waje da sunan sata ba."Jin haka yasa Safna tayi saurin zubewa k'asa tana kuka."Sir!, Don Allah kayi hak'uri ka yafeni ' wallahi ba sata ya shigo dani ba, Wajen ne ya burg..."Bata kaiga k'arasawa ba ya fizgo hannunta, Tare da janta suka fito daga guess-room d'in.Safna hawaye kawai ke zuba a fuskarta ' ganin suna gab da shiga inda mutane suke ne, Yasa tayi saurin kare jikinta da hannu d'aya.Mr-Fauzan kuwa, Fizgarta kawai yakeyi.*_©Seemaluv Novels…_*[10:29PM, 8/19/2017] Hannatu: *....B'OYAYYEN* 👒
       👒 *AL'AMARI*

*_Pure Moment Of Life writers_*

® ```Written```     
       By
*_Seemaluv_*👄

    *_Assalamu Alaikum, Nasan k'ila hak'urin ku ya k'are, Ko dayake nima balaifina bane ' kunsan al'amarin yadda ciwo yake!, To a yanzu dai na sami sauki.... ( Always in my heart ' baby!..S2😘.)_*

                     *14-15*

   Mr-Fauzan tunda yaja Safna bai tsaya ba saida ya tabbatar sun shiga cikin mutane, Sannan ya tunkud'ata tsakiyar su, Hakan yasa gaba d'ayansu suka juyo suna kallon shi.
   Sir-Kamal ya fito kenan rik'e da files a hannunshi zai shiga Office d'in Mr-Fauzan, Yaji surutai ' hakan yasa shi juyawa ya nufi wajen.
  Bayan isarshi wajen ne ' ya lura da yanayin da Safna ke ciki, Sir-Kamal harya bud'e baki zaiyi magana yaji Mr-Fauzan yace.
   "Attention please!!,  Musamman securities ' muddin bazaku rik'a kula da properties na company d'in nan ba to tabbas zan cenja ku in nemi wasu, Look at her."
   Ya nuna Safna da yatsa, Hakan yasa dukkansu suka maida kallonsu akan Safna ' wacce hawaye kawai ke zubowa a fuskarta a sunkuye.
   "Ta shiga guess-room d'ina da niyyar sata ' domin kuwa aciki na kamata, Shi dama tsiyar talaka kenan! Bai iya samun waje ba, let me warn everyone of you here! Especially securities ' dole ne ku zama masu lura, Idan kuma ba haka ba ' to lallai zan d'auki mummunar mataki.
    Muneeba dake tsaye a wajen ne zuciyar ta cike da farin ciki.
    "So disgusting!, Nan gaba korar ki za'ayi ma."
  Ta furta hakan in murmured.
  Mutanen da ke wajen ' daga mai cewa aida ganinta zata iya sai masu suratai kala kala, Safna kuka takeyi sosai ' tana girgiza kai. 
   Mr-Fauzan nuna Safna da yatsa yayi yace.
   "And let me tell you something Ki tsaya ' a matsayin ki kawai zaifi, If not! To kina tattare da wahala arayuwarki ' k'azama kawai."
  Yana gama fad'in haka ya juya ya koma office, Safna kam kasa motsawa tayi ko nan da cen saboda kunyar data sha.
   Sir-Kamal, Wanda ya dad'e tsaye a wajen ranshi a b'ace cike da tausayawa ne, Ya k'arasa wajenta tare da maida kallon shi akan mutanen da sukayi carko carko awajen.
   "Ina son kowa ya koma kan aikin shi ' yanzun nan!!!."
   Ya fad'a a tsawace, Hakan yasa kowa ya juya ya koma kan aikin shi.
   Sir-Kamal, Files d'in dake hannun shi ya aje gefe ' sannan ya cire Suit d'inshi ta saman ' ya rufema Safna jikinta dashi tare da cewa.
   "Kije office d'ina ki jira ni."
  Haka Safna ta juya ta nufi office d'inshi a gaban idon shi, Tukunna shi kuma ya wuce office d'in Mr-Fauzan.
  Bayan ya kammala duk wani aiki ne ' ya dawo cikin office d'in shi, Ya iske Safna a zaune tana kuka.
  Kai kawai ya girgiza ' sannan ya k'arasa ciki ya zauna, Gami da yin gyaran murya.
   Safna kai ta d'ago ta kalleshi da rinannun idanun ta.
   "Inason ki daina kukan nan haka, Ki fad'amun gaskiyar abunda ya faru."
   "Sir, Wallahi babu abunda nayi ' babu abunda na d'auka, Kawai wajen ne..."
  Safna k'arashe maganar tayi cikin kuka, Kuka mai tsuma zuciya.
   Sir-Kamal runtse ido yayi domin kuwa kukan har cikin ranshi yake jinsa.
   "Calm down Safna! Is ok, Na fahimci cewa ya yanke hukunci ne abisa rashin sanin gaskiyar lamarin, But it's ok."
   "Sir, Nidai kawai ina ganin ban shigo company d'in nan da sa'a ba, Ina ganin zan aje aikin kawai..."
   "What!!! Don't you ever say that again!."
  Sir-Kamal ya fad'a cikin fad'a.
   "Yau yau da baki aiki ' sannan kice zaki aje? For what reason?  Kinsan yadda aiki yake da wuyar samu kuwa? Ko don kinga kin samu cikin sauk'i?."
  Safna lura tayi ranshi ya b'aci, Hakan yasa ta sunkuyar dakai ' tare da cewa.
   " Sir!, idan abunda na fad'a ya b'ata maka rai kayi hak'uri..."
  Ajiyar zuciya kawai yayi ' sannan yace.
   "Idan lokacin tashi yayi ' karki tafi ki tsaya ki jirani, Ina hijab d'inki?."
   "Yana a d'akin nashi."
   "D'aki kuma? Uhm! Guess-room ake cewa."
  Sir-Kamal wayar shi ya d'aga wacce ake amfani da ita cikin company d'in, Ya umarci security da su binciko hijab d'in Safna cikin guess-room d'in Mr-Fauzan.
   Haka ko akayi ' cikin lokuta k'alilan security man d'in nan ya shigo da hijab d'in Safna cikwikwiye a hannun shi, Tare da cewa.
   "Sir, here it is."
   "What!!! Haka kaga ya dace ka kawomin shi? Because bakasan darajar hijabi ba ko?."
   "Am sorry Sir."
  Security man d'in ya fad'i haka, Sannan ya ninke hijabin ya mik'a mashi.
   "Ita zaka bawa, Ba niba."
 Sir-Kamal ya furta hakan cikin isa.
  Safna hannu ta mik'a ta karb'a hijab d'in nata ta sanya a jikin ta, Sannan security man d'in ya juya ya fice.
   "Yanzu ki tashi ' ki kawomin coffee."
   Safna tashi tayi cikin hanzari ta nufi store ta had'a mashi coffee d'in cikin d'an k'an k'anin lokaci, Sannan ta dawo office d'in ba tare da tayi knocking k'ofar ba ta fad'a.
   Safna sallama tayi Sir-Kamal ya amsa, Tukunna ta k'arasa ciki ta aje mashi coffe d'in gami da cewa.
   "Sir, Gashi."
  Sir-Kamal d'ago kai yayi ya kalleta, yace.
   "Sami waje ki zauna!."
 Babu musu ta sami waje ta zauna.
  Nan yayi gyarar murya yace.
   "Safna Habib!."
  Ta d'ago kai ta kalleshi.
   "Ki kasance mace mai nutsuwa, And in tambayeki?."
  Ta d'aga mashi kai alaman Eh.
   "Kinaso ki shirya da Ogana?."
   "Eh Sir, Inhar hakan mai yuwuwa ce."
   "Good!."
  Ya furta ' sannan ya d'auki coffee yakurb'a, Tukunna ya cigaba da cewa.
   "This your dressing! Dole saikin cenja shi."
  Cikin mamaki ta kalleshi.
   "Yes! Zaki daina sanya wannan kayan na jikin ki, da wannan hijab d'in."
   "Sir! Bangane abinda kake nufi ba."
   "Very soon! Zaki gane, Yanzu ki koma kan aikin ki ' After closing karki tafi ki tsaya ki jirani, Ok?."
   "Ok."
  Tana fad'in haka ta tashi ta bar office d'in ta wuce cikin ma'aikata, Safna koda taje wajen mutane kallonta kawai sukeyi suna zund'en ta. Ganin haka ne yasa ta juyo ta dawo bakin store taja kujera ta zauna.
 
 
 
 
 



*SEEMALUV NOVEL'S GROUP*
  📚📚📚
[10:29PM, 8/19/2017] Hannatu: *....B'OYAYYEN* 👒
       👒 *AL'AMARI*

*_Pure Moment Of Life writers_*

® ```Written```     
       By
*_Seemaluv_*👄

Follow me on wattpad  @Seemaluv1

                      *16-17*

  Bayan ta zauna ne da 'yan lokuta k'alilan, Muneeba ta iso wajen cike da shan k'anshi taja kujera ta zauna tare da cewa.
   "Safna?."
  Safna d'ago kai tayi ta kalleta ' ba tare da tace komai ba, Sannan Muneeba tace.
   "Ko zaki fad'amun gaskiyar abunda ya faru?."
  Cikin mamaki Safna tace.
   "Bangane ba!."
   "Ina nufin kinyi satar ko bakiyi ba? Kamar yadda Oga ya kamaki, Kuma da yadda naji mutane na fad'a don kuwa kaf workers d'in da ke cikin company d'in nan sun yarda cewa kinyi sata.
   Safna nan take idonta ya cika da k'walla tace.
   "Muneeba, ni nasan cewa ba sata nayi ba ' kawai dai k'addara ce."
   "Well. Ban yadda dake ba Safna, Because dama irin ku sai a hankali."
   "Me kike nufi?."
 Ya tsine baki Muneeba tayi ' ta tashi tabar wajen, Ba tare da tace komai ba.
  Safna girgiza kai kawai tayi cike da damuwa, Tana cikin haka ne lokacin tashi yayi *2:00pm* hakan yasa ta tashi gamida kakkab'e jikinta zata wuce suka had'e da Muneeba ta dawo d'aukar hand-bag d'inta domin wuce gida.
   Safna fita daga company d'in tayi taje ta tsaya bakin gata, Harta tsaida mai keke-napep kenan ta tuna da abunda Sir-Kamal yace mata.
   "Ohh Sam! Na manta zan tsaya injira wani, Bawan Allah kayi hak'uri ka tafi kawai."
   Abunda ta cewa mai keke-napep kenan ta koma k'ark'ashin  bishiya ta tsaya jiran Sir-Kamal.
  Safna bata dad'e a tsaye ba Sir-Kamal ya fito cikin company rik'e da wasu documents tare da Ogan shi Mr-Fauzan,  Sir-Kamal sai da ya tabbatar Mr-Fauzan ya shige cikin motar shi ' sannan ya mik'a mashi documents d'in gami da rufe mashi mota.
   Ganin haka yasa Safna k'arasawa inda yake tare da cewa.
   "Sir?."
  Sir-Kamal jin ankira shine yasashi juyowa a uzurce, Ganin Safna ce yasa shi sakin smiling.
   "Yes! I keep you waiting koh?."
  Safna girgiza mashi kai tayi ' tukunna yace.
   "Alright, Muje toh."
  Sir-Kamal k'arasawa wajen motar shi yayi, Sannan ya umarci Safna ta bud'e motar ta shiga.
  Babu musu Safna ta bud'e ta shiga ' tukunna shima ya shige, Bayan shigar shine yace.
   "Safna, Nasan hankalin ki yana gida ko?."
   "Eh."
   "Inason in kaiki gida ' da kaina."
   "No Sir, da kabarshi ma wallahi."
   "Meyasa?."
  Yayi tambayar yana kallon fuskarta.
   "Gani nayi bazaka rasa aiki ba sosai, Kuma...".
   "No ni nasa kaina ai, So just let me."
  Zatayi magana kenan yayiwa motar key ' yaja suka wuce, Safna kwatancen k'auyen nasu taimashi, Sir-Kamal mamaki ne ya cika shi jin inda Safna ke zaune.
   "Kai!!! Tun daga cen kike zuwa?."
  Ta d'aga mashi kai alaman Eh.
   "Okay! Insha Allah za'a nemi mafita."
  Jin haka yasa Safna ta d'ago kai ta kalleshi, Shi kuwa tuk'in shi kawai yakeyi.
  A haka har suka isa cikin k'auyen ' tukunna suka shiga cikin unguwar har k'ofar gidan su Safna.
   "Na gode."
  Abunda ta furta kenan ' ta juya zata bud'e motar, Sir-Kamal ya tsaida ita.
   "Saurin me kikeyi?."
   "Am... Babu komai."
   "Good! Well, Yanzu kije kawai we will talk tomorrow Ok?."
  Kai ta d'aga mashi tare da cewa.
   "Na gode sosai."
  Safna bud'e motar tayi ta fita ' ta shige gida, Sannan shi kuma yaja motar shi ya wuce.
   *WANENE Sir-Kamal?*, A tak'aice Sir-Kamal mutum ne mai kyautatawa iyayen sa ' shi kad'ai ne wajen mahaifiyarsa,  Mahaifinsa kuwa Allah yai masa rayuwa...
   Sir-Kamal bayan ya koma gida ne, Yayi packing motar shi a packing space ' tukunna ya shige ciki ya iske mahaifiyarsa a zaune tana kallo, Hakan yasa yashiga ciki d'auke da sallama a bakinshi.
   Bayan ta amsa sallamar ne Sir-Kamal ya nemi waje ya zauna, Sannan yace.
   "Ammi, Yana sameki?."
   "Lafiya kalau Kamal, Ya aikin naku?."
   "Lafiya Ammi..."
 Ya fad'a tare da sauke ajiyar zuciya.
   "Kamal ' yau da farin ciki ka shigo, Meke faruwa?."
   "Uhm! Ammi kenan, Ai dama kullun haka nake shigowa."
   "A'a, ba kamar na yau ba dai."
  Murmushi mai k'arfi Sir-Kamal yayi, Sannan ya mik'e tsaye tare da cewa.
   "Uhm! Ammi kenan idan tayi wari zakiji ' yanzu dai kice ma mai aiki ta kawomin abinci na."
  Yana fad'in haka ya juya ya haye sama ya wuce d'akin shi.
 
 *AROUND 3:00PM*

 B'angaren Mr-Fauzan, Zaune yake a d'akin shi rik'e da pen a hannun shi, Yana duba documents.
  Bayan ya kammala ne ya tashi ya wuce garden ' inda yake hutawa ya same waje ya zauna, Yana nazarin ayyukan dake k'unshe cikin company d'inshi.
  Yana cikin haka ne Safna ta fad'o mashi a rai, Yana tuna da irin wulak'ancin da yayi mata.
   "But i see passion in her eyes!, Tana k'unshe da wasu abubuwa ' dana kasa gane meye su!."
  Abunda Mr-Fauzan ya furta kenan a fili, Sam baisan Mummy na tsaye a bayan shiba ' sai ji yayi tace.
   "Son?."
  A razane ya juyo ya kalleta, sannan ta sami waje ta zauna d'auke da murmushi a fuskarta.
   "Son! Wacece wannan wacce naji kana maganar ta?."
   "Mummy wa kikaji ina maganar ta?."
   "Yakamata ka kawo man ita ' ta gaisheni."
   "Mummy ' nifa bakiji da kyau bane."
  Mummy b'ata rai tayi tare da nuna fushin ta fili.
   "Fauzan! Karka sake ka k'ure ni, Don kuwa inhar ka bari raina ya b'aci game da maganar nan to tabbas zan aura maka wacce baka so!!!."
  Mummy na gama fad'in haka ta tashi ta koma cikin gida, Shi kuwa Mr-Fauzan in ranshi yayi dubu ya b'aci, Don kuwa babu abinda ya tsana irin auren had'i.
   "I really have to do something!, Dole in nemi mafita."
  Abunda yace kenan ' ya tashi ya wuce part d'in shi shima.










*SEEMALUV NOVELS GROUP*📚
*FACEBOOK @SEEMALUV HAUSA NOVELS*
[10:36PM, 8/19/2017] Hannatu: *....B'OYAYYEN* 👒
       👒 *AL'AMARI*

*_Pure Moment Of Life writers_*

® ```Written```     
       By
*_Seemaluv_*👄

Follow me on wattpad  @Seemaluv1

                     *18-19*

   Safna kuwa tunda ta dawo ta shige d'aki, Sam babu walwala a tattare da ita ' Umma ta lura da haka, Hakan yasa ta tashi tabi Safna d'aki ta iske ta a kwance saman gado tayi ruf da ciki.
   "Safna?."
  Jin ankira sunanta ne yasa ta tashi ta zauna ' tare da cewa.
   "Na'am Umma!."
 Umma bakin gado ta zauna ' daidai saitin Safna.
   "Na lura dake tunda kika dawo ' sam babu walwala a fuskar ki, Kuma baki fad'amun komai game da aikin kiba ' ince dai babu wata matsala ko?."
   "Eh babu komai Umma, Aiki kuma Alhamdulillah nasamu."
  Safna na gama fad'in haka ta koma ta kwanta.
   "Ha'a ya ina magana kin koma kin kwanta, Safna akwai abunda ke damunki fa."
   Safna sake tashi tayi ta zauna cike da damuwa, Tace.
   "Umma karki damu ' kawai wasu 'yan matsala dana fuskanta yau, Amma babu komai."
   "To Allah ya k'ara tsarewa."
   "Amin."
  Har Umma ta tashi zata fita Safna ta tsaida ita ' da cewa.
   "Umma abinci na fa? Yunwa nakeji wallahi."
   "Abincin ki ' gayacen a kwano ki d'auka."
  Umma taiwa Safna nuni da wani kwano ' dake a k'asa a gefen gado tukunna ta fice, Cikin sanyi jiki Safna ta sauko daga saman gadon ta d'auki abincin ta fara ci da sauri.
   Bayan ta gama ne ta fito daga d'akin ta iske Rumaisa da Anisa zaune saman ta barma Umma kuma na zaune a saman turmi tana gyara shinkafa.
   Safna bakin rijiya ta nufa ta wanke hannunta ' Sannan ta dawo ta zauna cikin su Rumaisa. 
   "Umma, Me za'a dafa ne da yamman nan?."
   "Gashi kuwa ina gyarawa shinkafa!."
   "Yauma shinkafa da mai da yaji?."
   "Eh."
 Ajiyar zuciya kawai Safna tayi, Sannan ta tashi ta nufi bakin murhu ta hau had'a wuta domin d'aura ruwan zafi.
 
  *AROUND 6:00PM*

 Mr-Fauzan na zaune a babban parlor Khairat ta sauko daga saman steps ' tazo ta zauna a parlon  rik'e da popcorn a hannunta tana ci.
   "Ehen! Bani pop-corn d'in nan inci."
   "Haba Yaya don Allah! Bafa shida yawa."
  Ta fad'a tana turo baki, Ganin haka yasa shi fizge ledar popcorn d'in gaba d'aya tare da cewa.
   "Ni kike turowa baki ko? To aisai kici ingani."
   "To nida abuna?."
   "Yes!!! Ke da abun naki ' na hanaki."
  Khairat ganin baida niyyar bata ne ' yasa ta barin parlon cikin gunguni.
   Mr-Fauzan kuwa cin pop-corn yakeyi yana kallon news, Yana cikin haka ne maganar Mummy ta fad'o mashi a rai ' hakan yasa shiyin zambur ya mik'e tsaye tare da dailing number d'in babban abokin shi mai suna Hafiz.
  Ringing d'aya zuwa biyu wayar tayi Hafiz ya d'auka.
   "Hello Hafiz?."
   "Babban mutum! Ya akayi ne?."
   "Where are you?."
   "Am at home now."
   "Good! Hafiz i really need your help, Ya za'ayi inganka?."
  Cewar Mr-Fauzan.
   "Kazo gida kawai ' sai muyi magana."
  OK kawai Mr-Fauzan yace, Sannan ya kashe wayar ya fita zuwa garege ' ya shiga motar shi, Ganin haka yasa mai gadi yin saurin bud'e gate tukunna Mr-Fauzan yaja motar shi ya fice.
   Hafiz kuwa tunda suka gama waya da Mr-Fauzan ' yaje part d'in hajiya wato mahaifiyar sa ya sanar mata da cewa babban abokin shi zaizo, Hakan yasa Aleeza wato k'anwarsa yin saurin shiga kitchen ita da 'yar aiki suka fara preparing abinci.
   "Wayyo Allah! Dama yace yana sona."
  Cewar Aleeza.
   "Amma wai daman bak'on kine ko kuwa bak'on Yayan ki?."
  Inji 'yar aiki.
   "Nidai banason surutu! Kiyi abunda na saki."
  Aleeza barin kitchen d'in tayi ta wuce parlor inda Hafiz ke zaune, Ta zauna.
   "Yaya Hafiz, Haryanzu abokin naka bai iso bane?."
  Hafiz d'aure fuska yayi, Tare da cewa.
   "Kinada sak'on da zaki bashi ne?."
   "A'a kawai dai na matsune ingansa, Saboda inajin labarin sa ' Allah Yaya guy d'in..."
  Bata kaiga k'arasawa ba Hafiz ya daka mata tsawa da cewa.
   "Ke! Don Allah kin isheni da surutu, Inma sonsa kikeyi gwara kin cireshi a ranki ' don ba ajinki bane."
  Aleeza tashi tayi ta wuce part d'in hajiya tana gunguni.
 Aleeza kyakkyawar yarinyace 'yar shekara 19 tana, Cikin wannan year d'in zata gama school d'inta na fannin jami'a.
  Hafiz na cikin danna wayar shine yaji tsayawar mota ' a cikin garege, Hakan ya tabbatar mashi da cewa Mr-Fauzan ne.
   Hafiz tashi yayi taje ya shigo dashi cikin gidan ' tare da yimashi maraba, Sannan Mr-Fauzan ya nemi waje ya zauna.
   "First bari in kira hajiyata ku gaisa, Tunda ka dad'e rabonka da gidan nan."
  Cewar Hafiz.
 Hafiz wuce part d'in hajiya yayi ya sanar da ita cewa abokin nasa ya iso, Saboda haka ta fito su gaisa.
  Hafiza da hajiya tare suka fito zuwa parlor sai kuma Aleeza dake binsu a baya, Koda suka isa parlor Aleeza bata k'arasa wajen ba ' saidai ta rakub'e jikin bango tana lek'en Mr-Fauzan har suka gama gaisawa da Hajiya ta koma part d'inta.
   "Wayyo... Allah na! Jibeshi cikin fararen kaya, Wallahi guy d'in nan ya riga ya lashe zuciyata inason shi."
  Abunda Aleeza ta fad'a kenan tare da dafe k'irjinta tana sauke ajiyar zuciya, Tukunna ta juya ta nufi kitchen ta iske 'yar aikin sai kai da komowa takeyi.
   "Oh my God! Yanzu baki gama abincin ba?."
   "Eh, Kiyi hak'uri kinsan halin shinkafa."
  Girgiza kai kawai tayi gamida jan tsaki, Sannan ta d'auri trey ta bud'e fridge ta had'a drinks kala kala, Sannan ta d'auka ta nufo parlor d'in dashi a hannu.
  Koda Aleeza ta doso parlon idonta na kanshi, Haka ta k'arasa ciki da sallama a bakinta ' dukkansu suka amsa, Sannan Aleeza ta ajiye trey d'in a k'asa daidai saitin Mr-Fauzan.
   "Sannu da isowa!."
   "Yawwa."
  Abunda ya fad'a kenan ba tare da ya d'ago kai ya kalleta, Hakan yasa ran Aleeza ya b'aci ta juya ta wuce tamkar zatayi kuka.
  Bayan wucewar tane Mr-Fauzan yace.
   "Ehem! Hafiz nazo wajenka akan wata magana ne."
   "Fad'amun inajinka."
  Nan Mr-Fauzan ya gyara zama, Tare da yin gyaran murya.
   "Wato Mummy ce ' take nema ta huramun wuta! Akan lallai saina kawo mata wacce zan aure."
   "Fauzan, To meye aciki? Ai kawai malam kayi aure musha biki."
   "No please! Ka daina zaulaya! This is a serious issue, Babu matar ne ai."
   "Kamarya? Kana nufin duk 'yan matan dake sonka babu wacce taimaka?."
  Mr-Fauzan d'an k'aramin tsaki yaja.
   "Is ok! I understand your pain, Ya kamata mu sami lokaci mu fitane ' domin kaga wacce taimaka."
  Nan Mr-Fauzan yayi saurin taron numfashin Hafiz, Da cewa.
   "Ehen! And ita Mummy ta nace dole sai 'yar gidan masu kud'i, And to tell you the truth? Ni gaskiya bazan auri yarinya tazo tana raina ni ba, Su suna da raini ne."
   "Eh kwarai haka ne ' suna da wannan, Yanzu dai you know what?."
  Mr-Fauzan ya girgiza kai alaman a'a.
   "Insha Allah zan zauna ' inyi tunani domin muyi finding solution, Gobe kuma zanzo company d'inka sai a tsayar da magana."
  Mr-Fauzan dad'i yaji sosai, Sannan ya mik'awa Hafiz hannu alaman gaisuwa.
   "Gaskiya na gode sosai Abokina da time d'inka."
  Cewar Mr-Fauzan.
 Haka suka tashi ' Mr-Fauzan yayiwa Hafiza sallama, Sannan ya fita ya shige motar shi yaja ya wuce.







*SEEMALUV NOVELS GROUPS*📚*....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_Pure Moment Of Life writers_*® ```Written```By*_Seemaluv_*Follow me on wattpad @Seemaluv1*_Kuyi hak'uri jina da kukayi shuru! Na d'anyi fama da ciwon kai ne shiyasa INASON KU MASOYA NA, i love you too JAMEESHA Wannan page d'in naki ne ke kad'ai..._**20-21*Bayan Mr-Fauzan ya dawo gida ne, Yayi packing motar shi tukunna ya shige cikin gida ' kasancewar bai sami kowa a parlor bane yasa shi wucewa kitchen kai tsaye domin ya zuba abinci.Koda Mr-Fauzan ya shiga kitchen d'in 'yar aiki ya iske tana ta k'okarin kammala abincin."Haba! Me akeyi since ' ba'a gama ba?."Cewar Mr-Fauzan."Kayi hak'uri an kusa gama wa."'Yar aikin ta fad'a tana k'okarin duk'awa k'asa.Mr-Fauzan juyawa yayi ya wuce part d'in, Yayi wanka tukunna yayo alwala kasancewar baiyi sallar isha'i ba.Bayan ya fito daga bathroom ne ya bud'e wardrop d'in kayan shi, Ya ciro jallabiya ya sanya ' sannan yashinfid'a dadduma yayi sallar sa.*AROUND 9:00PM*Safna na kwance a d'aki saman tabarma, Umma da Anisa da Rumaisa kuma suna saman gado suna ' kowannen su yayi shuru yana tunanin zuci."Yaya Safna? Ranar bikin ki ba k'aramin casu za'ayi ba."Inji Rumaisa."Hmm... Lallai Rumaisa zuciyar ki tana fad'a miki k'arya, To Allah dai ya hore mana."Amin dukkan su sukace ' sannan Umma tayi gyaran murya, Tace."Yaro yaro ne ' inbanda abunku, Ai walima tafi rufin asiri ' Allah dai ya baku mazaje na gari."Amin Safna da Rumaisa suka ce."Umma halan Anisa bacci tayi ne, Najita tsit ne."Cewar Safna."Tab wannan ai tunda taji cikin ta ya d'auka shikenan!."Haka su Safna sukaita fira har bacci yayi awon gabadasu.*** *** *** *** *** *** ***Washe gari da sassafe ' wajen k'arfe *7:00am* Umma ta tada Safna daga bacci."Tashi mana! Kinfa makara, Yanzu bakwai tayi fa."Safna najin haka tayi wuf ta tashi cikin hanzari ' ta fito daga d'akin ta nufi wajen rijiya taja ruwa a buta, Sannan ta shige bayi.Bayan fitowar tane ' ta iske Rumaisa a bakin rijiyar zataja ruwa itama."Yawwa Rumaisa jamun ruwan wanka ' don inayin sallah zan shiga wanka.""Da ruwan sanyi?.""Eh mana! To dame kikeso inyi bayan na makara."Nan wajen Safna ta zuk'unna tayi alwala a gurguje ta shige d'aki tayo sallah, Sannan ta fito ta.Safna ruwan wankanta ta d'auka ta nufi bayin, Cikin 'yan lokuta k'alilan ta fito.Tana fitowa ta iske Umma na dama koko, Hakan yasa Safna shigewa d'aki a tsanake ta shirya ' sannan ta kalli agogo taga wajen k'arfe *7:30am*."Ya salaam! Lallai na makara da yawa."Safna waje ta fito ' ta nufi wajen Umma ta zuk'unna, Umma ta zuba mata kokon ta fara sha ko sugar babu don kuwa idan da sabo aita saba.Tana kammala wa ta mik'e tsaye tare da cewa."Umma ni zan wuce wajen aiki.""To Safna Allah ubangiji ya tsare."Amin Safna tace, Sannan ta zarce d'aki ta d'auki hijab ta sanya ta fice, Tana fita ne taga mai keke-napep a tsaye jingine a jikin napep d'inshi a k'ofar gida."Bawan Allah lafiya?."Cewar Safna."Kece Safna habib ko?."Ta d'aga mashi kai gami da cewa."Eh.""Yawwa cewa akayi inzo inruk'a d'aukan ki kullun idan zaki tafi wajen aiki."Abun ne ya ba Safna mamaki tace."Bawan Allah injiwa?.""Yace in fad'a miki Ogan ki Kamal."Abun d'aure mata kai yayi, Sai dai tayi murmushi tace."To shikenan muje."Safna shiga tayi shima mai keke-napep d'in ya shigayaja suka tafi.*AROUND 8:00AM* Safna ta isa cikin company d'in, tana sauka ta ciro d'ari biyu daga cikin 'yar k'aramar jakarta ta mik'a mashi."A'a ai shine zai rik'a biyana duk k'arshen wata."Safna dafe kai tayi alaman mantuwa, Tace."Ya salaam! Kayi hak'uri na manta ne."Nan ta maida kud'inta ta juya ta nufi cikin company d'in, Koda ta shiga a tsaitsaye ta iske mutanen dake ciki ' Mr-Fauzan sai zabga bala'i yakeyi akan ba'ason zuwa akan lokaci.Jin haka yasa Safna yin ajiyar zuciya ' acikin zuciyarta tace."Uhp ashe ma bani kad'ai bace ta makara d'in."Safna hango Muneeba tayi ' hakan yasa ta k'arasa kusa da ita."Muneeba wai meke faruwa ne?."Cewar Safna."Hmm. Kinsan halinsa ai ' fad'a yake akan wad'anda basa son zuwa in time, Kuma saida ya tambaye ni ina abokiyar aikina."Nan take gaban Safna ya fad'a, Tace."To me kika ce masa?.""Ha'a me kuwa zance masa? Zanyi masa k'arya ne saboda in faranta miki?, Ce masa nayi baki ruga kin iso ba."Nan fa Safna tsoro da fargaba suka bayyana a fuskarta, Mr-Fauzan kuwa ashe ya riga yaga shigowar Safna wajen."Where is Safna Habib?."Mr-Fauzan ya tambaya yana kallon side d'inda take.Safna salati kawai takeyi a cikin ranta."She is here Sir."Cewar Muneeba.Safna k'arasawa tayi gabansa tare da cewa."Gani.""Baki karanta rules d'in aikin ki bane?."Mr-Fauzan yayi maganar cikin tak'ama."Na karanta.""Good! So baki shirya ma aikin bane?.""Ba haka bane, Wallahi nauyin bac...""What?? Nauyin bacci? You are not serious Safna.""Take it easy Sir."Cewar Sir-Kamal..Sai a wannan lokacin ne Safna ta lura da Sir-Kamal a wajen, Ganin sa yasa tayi ajiyar zuciya ' tasan koba komai bazata wulak'anta ba."Zaki bama duk wani ma'aikaci dake cikin wannan company d'in Coffee for good 2weeks ba tare da taimakon abokiyar aikin ki ba, Wannan shine punishment d'inki."Mr-Fauzan ya fad'i haka d'auke da murmushin mugunta, Sannan ya k'ara da cewa."Idan kinso zaki iya cigaba dayin nauyin bacci, Zaku iya komawa kan aikin ku."Ya umarce su, Nan Safna ta juya kowa ya watse ya cigaba da harkar gabansa.Safna direct store ta nufa ' ta fara had'a coffee tana zubawa a cups tanayi tana kaiwa ma'aikatan dake wajen, Saida ta kammala tukunna ta fara kaiwa office.Safna office d'in Sir-Kamal nufa, Knocking tayi ya bata iznin shiga ' sannan ta bud'e k'ofar ta shige d'auke da sallama.Bayan ta aje mashi coffee d'in saman table d'inshi nesuka gaisa, Sannan tace."Sir?."Ya d'ago kai ya kalleta."Naga Abun arzik'i naji dad'i kuma nagode, Allah ya saka da alkairi.""Ki sami waje ki zauna ' first."Safna zama tayi suna facing juna, Sannan Sir-Kamalyace."No need of thanking me Safna, Saboda wannan ai yiwa kaine."Murmushi tayi ta sunkuyar da kanta."Yanzu kije ki cigaba da aikin ki, Idan kin gama saikizo i have a surprise for you."Ok Safna tace ' ta mik'e d'auke da murmushi a fuskarta, Sannan ta d'auki ragowar Coffee d'in ta nufiOffice d'in Mr-Fauzan dashi.Nan suka had'e da Hafiz abokin Mr-Fauzan yana k'okari shiga cikin Office d'in, Safna tsayawa tayi caktare da cewa."You are welcome."Hafiz kallonta yayi daga sama har k'asa, Sannan yace."Thank you!."Hafiz bud'e office d'in yayi ya shige tukunna Safna tabiyo shi a baya.Haka ta shiga da sallama a bakin ta jikin ta na d'ar d'ar.Bayan Mr-Fauzan da Hafiz sun gaisa ne Safna ta ajemusu Coffee two cups a wajen, Ganin yayi bak'o ne yasa ta juyawa zata wuce ba tare data gaishe shi ba ' saboda kar tayi interrupting d'in shi.Harta kai bakin k'ofa ya daka mata tsawa da cewa."Where did you think you're going to?."Cikin fargaba ta juyo ta kalleshi a sanyaye."Sorry Sir.""Wane irin Sorry Sir, Come on zo nan."Safna dawowa tayi ' tayi tsaye wajen desk d'inshi, Shi kuwa Hafiz kallon su kawai yakeyi yana murmushi."First, Kin kawomin Coffee without sayin anything, Second ' kin juya zaki tafi without greetings, Tarbiyyar da aka koya miki kenan daga gidan ku?."Nan take hawaye suka zubo daga fuskarta."Am sorry Sir!..."Ta furta cikin rawar murya."Calm down mana!, Hak'uri akeyi and she even apologized."Tsaki Mr-Fauzan yaja cikin b'acin rai yace."Leave my office."A tsawace yayi magana, Hakan yasa Safna juyawa cikin hanzari ta bar Office d'in tana hawaye."Haba aboki! Kacika zafin rai da fad'in hash-words."Cewar Hafiz."Yarinyar sam batada alk'ibula ne, P.A nane ya matsa saina d'auke ta aiki ' ita gata k'azama."Mr-Fauzan ya fad'i haka cikin izza, Hafiz murmushi kawai yayi yad'an tsaya k'are mashi kallo nad'an lokaci."Meye haka, Kana kallo na kana smilling.""Kuma yarinyar nan daga ganinta talakace ko.""Ehen now!."Nan Hafiz ya gyara zama ' gamida duba wristwatch d'in hannun shi."Ina ganin ' yanzu komai zaizo mana da sauki.""What do you mean?."Mr-Fauzan yayi tambayar."Ina nufin ita tafi dacewa da kai Abo....."Hafiz bai kaiga k'arasa maganar sa ba, Mr-Fauzan ya dakatar dashi."No please ' karma ka k'arasa please, Hafiz wace irinmagana kake fad'amin? Yau kuma da wannan k'azamar zaka had'ani?.""Ka daiyi tunani akai Fauzan! Ni abokin kane, Kuma bazan tab'a baka gurguwar shawara ba, Batun rashin tsafta kuma ai kaine zaka gyara ta.""No no no... Mubar maganar nan don bazata sami shiga ba.""Ok! Then, Ni bara in tafi, Idan kayi tunani akai ' saika nemeni."Nan Mr-Fauzan da Hafiz sukayi sallama da junan su, Bayan fitar Hafiz ne Mr-Fauzan ya bud'e laptop d'inshi ya fara aiki.*©SEEMALUV NOVELS GROUP*21*....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_Pure Moment Of Life writers_*® ```Written```By*_Seemaluv_*Follow me on wattpad @Seemaluv1*_Dedicated to Momyn-Sultan and Sadnaf,..._**22-23*B'angaren Safna kuwa ' a zaune take a wajen zamansu babu abinda takeyi inba kuka ba, Muneeba ce tsaye a kanta tana tambayar abunda ya faru."Wai don Allah meye ne? Nifa na fara gajiya da wannan koke koken naki, Don karki samun ciwon kai.""Don Allah Muneeba ki kyaleni! Ki barni inji da d'aya mana ' ku baku tab'a damuwa da damuwar wasu saidai taku kuka sani, Na rok'eki ki barni inji da wulak'ancin da mutumin nan kemin."Tab'e baki Muneeba tayi, Ta koma taja kujera ta zauna ta cigaba da danna wayarta.Safna sai da tasha kuka har kanta ya fara ciwo, Tukunna tayi shuru ta fawwalama Allah komai.Saida ta dad'e a zaune, Sannan ta tashi ta nufi toilet d'in mata ta wanke fuskarta, Tukunna ta fito ta wuce office d'in Sir-Kamal kai tsaye.Tana isa wajen ta bud'e k'ofar ba tare data jira anbata izni ba, Sakamakon ciwon kanda take fama dashi.Safna kai tsaye ta shige ciki ta samu waje ta zauna agajiye, Sannan tace."Sir, Na dawo."Sir-Kamal lura yayi da yadda idonta ya kunbura ' yasan cewa babu makawa Safna kuka tayi."Safna Akwai abunda ke damunki ne?."Ta girgiza mai kai, Alaman a'a."No you better tell the truth!, Because daga ganin idonki kinyi kuka.""Sir-, Koma menene ya riga ya wuce ' maimaita maganar batada wani amfani."Girgiza kai kawai yayi ' sannan ya mik'e tsaye yaje d'auko wata leda dake cike da kaya a jikinta ya mik'awa Safna, Tare da cewa."Ansa ki bud'e ki duba ki gani, Idan sunyi miki saiki sanar dani."Safna karb'ar ledar tayi cike da son ganin abunda ke ciki, Bayan ta bud'e ne ta fara d'aga kayan tana dubawa cikin jin dad'i.Abayas ne masu kyau ' kuma masu tsada, Ko wannen design d'inshi dabam zasu kai kala goma.Safna murmushi kawai ke bayyana daga lips d'inta, Cikin nutsuwa tace."Sunyi kyau! Gaskiya kayan nada kyau sosai."Sir-Kamal komawa yayi ya zauna ' zuciyar shi cike da farin ciki, Yace."Alhamdulillah!Wannan kayan nakine na baki kyauta!, daga yau inason ki ruk'a sanya su, Banason insake ganinki cikin wannan kayan na jikin ki."Cikin fara'a Safna tace."Nagode.""And, Ki duba takalman dake ciki idan sunyi miki ' ki sanar dani."Cikin zumud'i Safna ta fara d'aga takalman tana gwadawa, Cikin sa'a kuwa duk sunyi mata kasancewar su flat-shoes ne."Sunyi."Ta furta, Kanta a sunkuye."Good!, Ki d'auka ki tafi dasu wannan shine gift d'ina na farko.""Na gode ' na gode Sir, Allah ya saka da alkairi."Safna tashi tayi tabar Office d'in nashi cikin jin dad'i, Ta wuce side d'insu sam ta manta da ciwon kanda take fama dashi ' ai tuni taji ta warke.Bayan ta isa bakin store ne taja kujera ta zauna ' gamida ajiye ledar kayan nata ta fara tunane tunane kala kala a zuciyarta."Meyasa yakeson farantamun rai a kullun? Gaskiya Sir-Kamal yana da kirki, Ni duk na k'osa in nunawa Umma wannan kayan."Tana cikin wannan tunanin ne Muneeba tazo wajen.."Lafiya daiko? Kika zauna ke kad'ai kina murmushi.""Uhm! Lafiya k'alau Muneeba."Muneeba kallon ledar dake gaban Safna tayi."Meye a cikin wannan ledar kuma? Don naga dai bada ita kikazo ba."Safna cikin fara'a tace."Kyauta Sir-Kamal yaimun."Nan Muneeba ta had'e rai ta sami waje ta zauna, Tukunna tace."Kyautar menene?."Nan Safna ta fad'a ma Muneeba komai da duk irin halaccin da yake mata."Wow! Ashe dama akwai irin ku a duniya? Marasa wayau?.""Ban gane abunda kike nufi ba!.""Yes da sannu zaki fahimta ai, To bari kiji Safna you have to shine your eyes! So yake kawai yaja ra'ayinkida irin wad'an nan abubuwan domin at the end kingaidan ya buk'aci wani abu daga gareki bazaki k'i basaba.""Yes niko insha Allah ' inhar Sir-Kamal zai buk'aci abu a wajena zan bashi, Muddin inada shi."Muneeba tab'e baki tayi gamida jan tsaki, Tace."Koda kuwa jikin ki ya buk'ata?."Nan Safna ta had'e rai tare da mik'ewa tsaye cike da tunani."A'a, Gaskiya Sir-Kamal bazai taba kasancewa hakaba Muneeba, Kinyi masa mummunar fahimta ' kuma ina rok'onki da kibar fad'amin haka domin kuwa alhakinsa kawai zaki d'auki."Tsaki Muneeba taja, A zuciyarta tace."Ai wallahi baki isa ki fini da komai ba Safna, Talaka dake ma!."Muneeba na gama ayyana hakan ta tashi fuuuu ta bar wajen.Wucewar Muneeba ne Safna ta shige cikin store ' ta duba agogon wajen taga *1:30pm*, Hakan yasa ta fara preparing had'a coffee donta bawa mutanen wajen.B'angaren Mr-Fauzan ' zaune yake da laptop a gaban shi, Amma sam hankalin shi baya kanta ' maganar Hafiz kawai ke dawo masa a rai."Hmm how can i even start this rubbishness? Yarinyar nan according to her Education bawani nisan karatu tayi ba!, So ta ina zan fara? Don ban taba jin sonta ba kokad'an."Yana cikin wannan maganar ne yaji ana knocking k'ofar."Come in!."Abinda Mr-Fauzan yace kenan, Tukunna ya maida kallonshi ga laptop d'in gaban shi.Safna ce ta shigo tare da yin sallama, Hakan yasa shi amsawa ba tare daya d'ago kai ya kalleta ba, K'arasawa ciki tayi ta aje mashi coffee d'in bisa deskgamida cewa."Gashi coffee d'in."Harta juya zata wuce ya tsaida ita da cewa."Banason insake ganin ki da wannan hijab d'in daga yau, Don zaki iya korar customers dake ziyartar company d'in nan, And ni karan kaina ma hijab d'in kyama yake bani! Muddin kinason aikin ki ya zama dole ki cenja dressing!."Safna shuru kawai tayi idonta na kallon k'asa, Sannan Mr-Fauzan ya k'ara da cewa."And look! Idan kud'in siyan kayan sawa ne bakida shi, Why not ki rok'a abaki."Jin wannan maganar ya k'ara b'atawa Safna rai batuk'a, A zuciyarta tace."Hm bana tunani zan juri wulak'ancin mutumin nan, Zan iya jure duk wani abu amma banda wulak'anci.""Ke!!."Ya kirata cikin tsawa, Hakan yasa tayi saurin d'ago kai ta kalleshi."Ok, Na fahimci matsalarki.Abunda Mr-Fauzan yace kenan, Ya mik'e tsaye ya ciro wallet d'inshi ya zaro kud'i 'yan dubu dubu ya watsoma Safna dake tsaye tana kallon shi."Ko ba kud'i kike nema ba?."Nan take idanun Safna suka ciko da hawaye, Kasa cewa komai tayi ta juya a guje ta bar office d'in tana matsanacin kuka.Safna direct ta shige store ' saida tasha kukanta ma'ishi, Sannan ta fito ta d'auki gift d'inda Sir-Kamalya bata, Harta nufi hanyar fita sai kuma ta dawo ta zarce Office d'in Sir-Kamal.Knocking tayi sau d'aya aka bata uznin shigowa, Safna ta shiga ciki ' cikin sanyin jiki ta nemi waje ta zauna."I hope dai lafiya!."Cewar Sir-Kamal."Nazo ne inyi maka sallama ' kuma inyi maka godiyada irin hallacin daka nunamun, Domin daga yau nabar aiki a k'ark'ashin wannan company d'in.""Meyasa? Akwai wanda yai maki laifi ne ko wani abu?.""Sir, Zan iya jure komai amma banda wulak'anci ' ni kuma gaskiya na gaji da wulak'ancin da mai wannanwajen kemin, Shiyasa na yanke wannan shawarar.""To! Da kika yanke wannan hukuncin ' kina da inda zaki cigaba da aiki ne?."Nan ta sunkuyar dakai ' tace."A'a banda shi, Amma zan nema aikatau inyi ' don shine daidai dani dama."Abunda Safna ta fad'a ne yayiwa Sir-Kamal ciwo sosai hakan yasa ya runtse idonshi, Domin har cikin zuciyar shi ' ya tsani mace yarinya tayi aikatau."No Safna ' karkiyi aikatau please..."Yayi maganar cikin sanyin murya.Ita kanta tayi mamaki yadda taji muryar shi ta cenja 'cikin k'ank'anin lokaci."Safna ki bari ' ni zan nema maki aiki mai nagarta, Amma kafin nan akwai school d'inda nakeson insaka ki kinji?.""Sir, Dama kabarshi amm..."Bata k'arasa ba Sir-Kamal ya tsaida ita da cewa."Shhhh… bake kika sani ba! Ninasa kaina so just let me, Yanzu idan kin tafi gida ' *Around 4:00pm* zanzo inyi magana da Mahaifiyar ki."Safna kai kawai ta d'aga mashi alaman to, Sannan ta tashi ta fita daga Office d'in.Bayan fitar ta daga company d'in ne ta sake ganin mai keke-napep d'in nan a tsaye, Hakan yasa ta k'arasa wajen."Bawan Allah! Koda yaushe kana nan ne dama?.""Eh hajiya! Ai dama aikina kenan in d'auke ki daga gida zuwa wajen aiki, Haka zalika daga wajen aiki zuwa gida.""Duk shi Ogan nawa yasaka yin haka?."Ta fad'a tana murmushi."K'warai dagaske hajiya! Yanzu ina zan kaiki?."Cewar mai na-pep."Uhm! Gida zaka kaini."Haka Safna ta shige ciki ' shima ya shiga ya tada na-pep d'in suka wuce.*®SEEMALUV NOVELS GROUP*....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_Pure Moment Of Life writers_*® ```Written```By*_Seemaluv_**24-25*Bayan tafiyar Safna ne da 'yan lokuta, Sir-Kamal ya baro Office d'inshi zuwa Office d'in Mr-Fauzan.Sir-Kamal bai kaiga k'arasawa ba ' suka had'e dashi yana fitowa daga Office d'in nasa ranshi a b'ace."Sir i want to have a conversation with you."Cewar Sir-Kamal."I don't have time now!."Mr-Fauzan ya fad'a yana k'ok'arin wucewa."Sir, It's about this lady Safna."Jin haka yasa Mr-Fauzan juyowa ya fuskanci Sir-Kamal."Ok! What is it?.""Tazo mun ne da cewa ' wai ta aje aiki, Am confuse and worried about her Sir ' Yarinyar abun a taimaka mata ne.""Confused?."Mr-Fauzan yayi tambayar, Sannan ya cigaba da cewa."Worried about her? Thank God data aje aikin, Don koda bata aje ba nizan koreta! Besides ' wannan k'azamar? Duk inda taje bazata sami aiki ba."Mr-Fauzan yana gama fad'in haka ya gyara bottles d'in suit d'inshi ya wuce.Sir-Kamal girgiza kai kawai yayi, Sannan ya juya cikin company d'in yana zagaye.*After Closing...*Sir-Kamal ya koma gida, Bayan yaci abinci ne yayi wanka ' yadawo parlor ya zauna tare da Ammi suna fira."Ammm... Ammi wallahi akwai wata yarinya da taketa fad'i tashin neman na kanta, Kuma Ammi basu da shine ' amma kuma Ammi kinsan menene?.""A'a saika fad'a.""Ammi wallahi babu wani abu tsakanina da ita ' so nake kawai na taimaka mata with all my efforts, Don ni a matsayin k'anwata na d'auke ta.A tak'aice Sir-Kamal ya fad'ama Ammi duk abunda ya faru da Safna a company."Lallai wannan yarinya abun a tausaya mata ne, To yanzu a ina zaka nema mata aikin?.""Akwai wani restaurant da nake tunanun zata iya samun aiki a wajen because akwai d'an connection da nake dashi a wajen, Amma kafin nan akwai school d'inda nakeson insaka ta mai suna *GYARA KANKI* kinsan suna wayar da 'yanmata musammanirinta, Kuma kinsan restaurant irin wannan saida wayewa ' 2weeks kawai zatayi a wannan school."Inji Sir-Kamal."Kwarai haka ne, To yanzu dai Allah ya bada sa'a kuma duk abunda ya shige maka gaba ka sanar dani.""Insha Allah Ammi, Yanzuma nakeso intashi inje gidansu domin innemi iznin yin komai wajen mahaifiyar ta.""To shikenan Kamal ' saika dawo."Sir-Kamal tashi yayi rik'e da key d'in motar shi a hannu ya fice.*** *** *** *** *** *** ***Tun lokacin da Mr-Fauzan ya dawo gida ya zarce d'akin shi kai tsaye, kasancewar babu kowa a parlor.Bayan ya watsa ruwan d'umi ne ya fito parlor daga shi sai boxer sai singlet a jikin shi.Mr-Fauzan waje ya samu yayi zamanshi gamida d'aukar remote ya kunna TV ya fara kallon news.Yana cikin kallo ne yaga wata bak'uwar fuska tazo ta zauna rik'e da cup d'in youghurt a hannun ta tana sha.Ganin sun had'a ido ne yasa ta tasowa tazo gabanshi ' tare da mik'a mashi hannu tace."Hey! Am Nafeesat but you can call me Nafee.""Who are you?."Mr-Fauzan ya tambaya ' ba tare da ya bata hannu ba.Ganin haka yasa Nafee komawa ta zauna ' gamida aje cup d'inda ke hannun ta a side table, Tace."Well, Am your wife to be! Fauzan.""What!!!?.""Yes, Fauzan."*Wacece Nafee?* Nafee kyakkyawar macece ' fara ce slimly in structure, Ta gama karatunta na jami'a since last year!.Mr-Fauzan harya tashi zaije wajen Mummy ' ya had'e da ita tana saukowa zata k'araso parlon."A'a koma ka zauna, Dama kai nake jira."Cewar Mummy.Mr-Fauzan komawa yayi ya zauna ' tukunna Mummy itama ta zauna."Nasan zakaita tambayar kanka wacece wannan!."Tayi mashi nuni da Nafee, Sannan Mummy tacigaba da cewa.."Sunanta Nafeesat, 'yar k'awata ce musamman nacea kawomin ita tazo taimin 2weeks, Saboda ku fahimci junan ku.""But Mummy na fad'a miki fa!.""Look! Wannan ita ce shawarar dana yanke , kuma ko kanaso ko baka so auren nan sai anyi shi."Cewar Mummy."Mummy please nifa ba yaro bane! Yakamata a barni inzab'a wacce nakeso.""Da sannu zaka fara sonta!."Mr-Fauzan tashi yayi yabar parlon zuwa garden d'inshi, Nan ya tsaya yana dogon tunani."Ina ganin shawarar Hafiz zanbi ' koma ta yayane dai ni bazan auri wannan yarinyar mai kama da second hand ba."Abinda Mr-Fauzan ya fad'a kenan ya juya ya koma cikin gida domin kiran Hafiz a waya.Harya shige parlor suka had'e da khairat ta dawo daga school, Mr-Fauzan wristwatch d'in hannun shi ya kalla yaga *4:00pm*."Ke sai yanzu ne kike dawowa?.""Eh Yaya Fauzan ' lectures!."Ta fad'a a tak'aice sannan ta k'arasa ciki a gajiye ' shima yabi bayanta, Mr-Fauzan part d'inshi ya wuce ita kuma Khairat ta zauna nan a parlor domin su gaisa da Nafee.Bayan shigar Mr-Fauzan d'akin shine ya d'aga wayar shi ya kira Hafiz, Saida yayi mashi two missed calls tukunna ya d'auka."Hello dude! Ina ka shiga ne ina kiran wayarka naji shuru?.""Babban mutum! Bana kusa da wayar ne ai."Cewar Hafiz.""Ok! Akan maganar nan ne dai na kira ka.""Wace magana?.""Oh come on! Maganar yarinyar daka ce in nema mana!, Yanzu dai na yarda da shawarar ka Hafiz ' amma saidai tabar company d'ina yanzu haka.""Shit! What happen?.""Well. Ba wannan ya kamata ka tambayeni ba yanzu ' Inda zamu sameta ya dace ka tambaya!."Cewar Mr-Fauzan."Yeah!.""But wannan ma bazai bada wahala ba! Zan umurci P.A d'ina Kamal, Domin naga yafi kusanci da ita.""Amma Fauzan kana tunanin zata yarda dakai kuwa?."Mr-Fauzan hannun shi ya damtse tare da cijewa, Yace."Duk abunda na nema ' to saina same shi, Ballema irin wannan mutanen kud'i kad'ai ya isa nasayi soyayyarta duk da ba sonta nakeyi ba!!."Kalaman da Mr-Fauzan yayi ne yasa Hafiz sakin ajiyar zuciya, Yace."Alright then, Idan ansami address d'in nata sai ka sanar dani."Abunda Hafiz yace kenan ' Mr-Fauzan ya kashe wayar shi.Bayan Hafiz ya aje wayar ne ' Aleeza tazo ta zauna kusa dashi tare da cewa."Yaya Hafiz! Please aramun phone d'inka in kira wata friend d'ina.""Ke me naki phone d'in keyi?.""Well. Ina cikin wayane credit d'in suka k'are."Hafiz tsaki yaja ' sannan ya d'auki wayar ya mik'a mata, Tare da cewa."25 minutes na baki.""Ok."Abunda Aleeza ta fad'a kenan ta tashi ta wuce d'akinta, Nan ta duba number d'in Mr-Fauzan kasancewar tasan dashi suka gama waya, Aleeza saida ta tabbatar tayi copying number d'in to her phone sannan ta mayar wa Hafiz wayar shi gami da cewa."Thanks bro."Sannan ta koma part d'in hajiya.B'angaren Safna kuwa a zaune take a tsakar gida saman tabarma tana kuka, Umma tayi juyun duniyarnan ta fad'a mata abunda ke faruwa amma Safna tak'i, Saboda tsabar k'uncin dake zuciyarta ne ko abinci bata nema ba.Tana cikin wannan yanayin ne aka aiko yaro ' cikin gidan cewar ana sallama da Safna.Jin haka yasa Safna tashi tsaye ' ta janyo hijab d'intadake saman igiyar shanya ta sanya, Sannan ta fita.Safna koda ta fita Sir-Kamal ta iske jingine jikin motar shi yana shafa waya, Hakan yasa taimashi sallama ' Sir-Kamal ya d'ago kai ya kalleta tare da amsa sallamar.Bayan sun gaisa ne ' Yace."Safna nazo akan maganar da mukayi ne ' ina fatan babu matsala.""Eh babu matsala ' bari inshiga in fad'ama Umma zuwanka tukunna."Ok Sir-Kamal yace, Sannan Safna ta juya ta shige gida ' tana shiga ta cewa su Rumaisa su tashi su koma ciki ' bata wani b'ata lokaci ba ta fito gamida cewa."Ka shigo."Sir-Kamal bin bayanta yayi har suka isa cikin gidan, Nan Safna ta bashi kujera ya zauna ' tukunna Sir-Kamal ya gaishe da Umma.Bayan sun gaisa ne ' Sir-Kamal ya sanar ma Umma duk abinda ke faruwa da Safna, Da duk irin k'alubalen data samu a rayuwa.Umma ajiyar zuciya tayi ' ta maida kallon ta kan Safna."Amma Safna shine kika kasa fad'amun?."Nan idanun Umma suka ciko da k'walla ' ganin haka yasa Sir-Kamal cewa."Ayi hak'uri Umma, Ai Insha Allah komai yazo k'arshe, Domin kuwa iznin ki nazo nema don insamama Safna aiki ' aikin da babu mai takura mata."Ajiyar zuciya Umma tayi ' ta maida hawayenta dake shirin zubowa, Tace."Yaro, Ni babu abinda zance maka sai godiya! Kumana amince kuma na yarje maka ' inhar kanada halin yin hakan to kayi.""Alhamdulillah!Na gode da naji haka."Nan Sir-Kamal ya cire kud'i daga aljihun shi 'yan d'ari biyar rabin bandir ya aje a saman tabarman da Umma ke zaune."Umma ga wannan! Kud'anyi amfani dashi nad'an wani lokaci."Godiya Umma taimashi, Sannan ya fita Safna ta bishi a baya.Bayan fitarsu ne ' sukayi sallama, Sir-Kamal ya shige motar shi ' tukunna Safna ta shige gida._we don't just entertain and educated, But we also touch the hearts of the readers_*Follow me on wattpad @Seemaluv*....*....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_Pure Moment Of Life writers_*® ```Written```By*_Seemaluv_**_Seemaluv is back again!!!..._**26-27*Bayan komawar Sir-Kamal gida ne yaga shigowar kiran Mr-Fauzan, Cikin sauri yayi receiving."Hello Sir!.""Kamal, Inason ka turomin da address d'in wannan yarinyar."Mr-Fauzan ya fad'a a tak'aice."Wace Yarinya kenan?.""Ha'a karka cemun baka gane abunda nake magana ba! That k'azama wacce tabar company na.""Oh! Safna?.""Whatever her name is! Nidai ka turomun address d'in gidan right away.""OK."Abunda Sir-Kamal yace kenan, Mr-Fauzan ya kashe wayar.Sir-Kamal, Mamaki ne yacika shi ' ganin yadda Mr-Fauzan ke neman address d'in gidan su Safna."Ha'a to meyafaru haka? Me kuma ya k'ara had'ata dashi?."Sir-Kamal bai wani b'ata lokaci ba, Yayima Mr-Fauzan sending address d'in gidan ' sannan ya fice zuwa masallaci, Kasancewar lokacin sallar magrib yayi.*AROUND 8...PM*Bayan Mr-Fauzan ya dawo daga mosque ne ' ya sami waje ya zauna a parlor ya fara duba wayar shi 'ya ga text d'in Sir-Kamal, Hakan yasa shi dubawa ' ganin abunda ya buk'atane yasa shi dialing number d'in Hafiz, Ringing d'aya zuwa biyu ya d'aga."Babban mutum, Ya akayi ne?."Cewar Hafiz."Lafiya k'alau, Nasami address d'in gidan su fa... Soboda haka Hafiz ' kai zakaje ka fara yi mata magana.""Oh come on! Kai d'in fa? Tare ya dace muje ai.""Hafiz, kaje kawai! Please inda hali ma ni kawai akawomin ita gidana as my wife ' ba tareda nayi wasting time d'ina ba."Cewar Mr-Fauzan."Ha'a haba Aboki? Wace irin magana ce haka?.""To shikenan, Yanzu dai ka fara zuwa tukunna ' and you know what?."Sai ka fad'a."Cewar Hafiz."We have to meet ' kafin kaje wajen ta, Zan baka kud'inda zakayi spending mata ' because kasan irin su saida haka.""Alright, Shikenan ' Gobe Around *12:00pm* zanzo inansa sai inwuce gidan nasu.""To shikenan."Sallama sukayi ' sannan Mr-Fauzan ya kashe wayar shi, Ya Cigaba da kallo.Mr-Fauzan na cikin kallo ne ' Daddy ya dawo daga wajen aiki d'auke da sallama ya shigo cikin parlor, Mr-Fauzan amsa sallamar yayi gamida yi mashi sannu da dawowa.Bayan Daddy ya wuce ne ' Mr-Fauzan yace."I don't think ' Daddy yasan abunda Mummy ke shirin yi."A zuciyar shi ya furta hakan.Tashi yayi ' ya koma d'akin shi ya zauna a kujerar sofa tare da janyo laptop d'inshi zai hau aiki.Mr-Fauzan yana cikin hakan yaji wayarshi ta fara k'ara alaman kira, D'auka yayi ya duba ' ganin Number ce yasa shi tab'e baki gami da cewa."What a trashy!"Ya fad'a gami da maida kallon shi zuwa kan laptop ba tare da yayi receiving call d'in ba.B'angaren Aleeza kuwa zaune take a d'akinta rik'e dawayarta a hannu tana kiran number d'in Mr-Fauzan, amma baya d'agawa."Meyasa bazakayi picking ba? Please pick up my call Fauzan..."Abunda Aleeza taita nanatawa kenan a zuciyar ta, Gami da sake dialing number d'in ' ganin baiyi receiving bane yasa tayin wurgi da wayan saman gado cikin zafin rai.Aleeza kwalla ne suka ciko Idonta ' tayi saurin mayarda hawayen."Wallahi inason shi..."Abunda ta furta kenan, ta bud'e wadrope ta ciro nightgown ta sanya ' sannan ta haye gado taja blanket.*** *** *** *** *** *** *** ****Washe gari...*Da assussuba Safna ta tashi ' ta tada su Rumaisa daUmma, Sukayi Sallah ' sannan Umma ta koma bacci kasancewar ta tashi da zazzab'i.Safna Umarni ta bawa Rumaisa dataje ta fara wankewanke, Ita kuma sai tayi shara daga nan ta d'aura ruwan zafi a murhu domin dama koko.Misalin k'arfe *6:00am*, Su Safna suka kammala aikin gidan ' Safna d'aki ta nufa ta tada Anisa daga bacci."Jeki wajen Rumaisa ta zuba maki koko kisha, Ki kuma wanke baki tukunna."To kawai Anisa tace ' ta wuce, Sannan Safna ta fara yiwa Umma magana cikin siga ta tausayawa."Umma?."Umma d'an motsawa tayi tare da sakin ajiyar zuciya."Umma, Ki tashi kisha koko ' daga nan sai inje chemist in anso maki magani."Umma tashi zaune tayi ' tana shivering, Safna ta fita cikin hanzari ta d'iboma Umma kokon a cup ta kawo mata."Gashi Umma! Ki daure ki shanye ' kinga ko suga bansa ba, Ni bari inje chemist d'in insiyo maka magani.""Toh."Abunda Umma ta iya furtawa kenan ' Safna ta d'aukihijabin ta ta sanya ta bar d'akin, Harta kama hanyar fita sai kuma ta dawo."Rumaisa! Ku tashi ku koma d'aki wajen Umma, Donbatajin dad'i."Rumaisa da Anisa, Tashi sukayi suka koma d'aki wajen Umma ' Sannan Safna ta fice.Kai tsaye Safna ta nufi chemist aka harhad'o mata magun guna kala kala sannan ta juyo ta kama hanyar dawowa gida.Cikin sauri take tafiya ' daka ganta kasan a uzurce take.Bayan ta dawo gida ne ' ta kaima Umma magun gunan had'e da ruwa tasha.Haka Umma ta ansa tasha maganin ' tukunna ta koma ta kwanta, Safna dasu Rumaisa sannu kawai suke mata tana ansawa agajiye.Safna kwantawa tayi k'asa saman tabarma ' tare da cewa."Rumaisa bari ind'an runtsa, Nad'an lokaci."To kawai Rumaisa tace, Sannan Safna ta fara bccinta cikin kwanciyar hankali.*AROUND 11:30AM*Hafiz yazo gidansu Mr-Fauzan tare dayin packing motar shi a packing space, Sannan ya ciro waya yayidialing number d'inshi.Mr-Fauzan na zaune a garden d'inshi yaga shigowarkiran Hafiz cikin wayar shi, Nan yayi receiving call gamida karawa a kunne."Ya! Kaifa gani na k'araso cikin gidanku yanzu.""OK, just give me 5minutes ' gani nan fitowa."Mr-Fauzan cikin gida ya shiga ' direct ya wuce d'akinshi ya bud'e side drower ya d'auko bandir d'in y'an dubu sababbi fil, Ya fito wajen dashi a hannu.Bayan ya isa wajen Hafiz ne suka gaisa ' tukunna ya mik'a mashi kud'in tare da cewa."Behave well!.""OK."Abunda Hafiz yace kenan, Ya shige motar shi yaja ' ya wuce, Sannan Mr-Fauzan ya juya ya koma gida.Koda ya shiga gida kai tsaye ya wuce part d'insu Mummy, Bayan sun gaisa ne Mummy tace."Son? Kunfara magana da Nafee kuwa?.""Oh Mummy come on! Nifa bazan auri wannan ' mara tarbiyar ba."Cewar Mr-Fauzan.Mummy zaro ido tayi cike da mamaki and at the same time tare da nuna b'acin ranta."What!!! Son? Yarinyar k'awar tawa ce mara tarbiyya?."Mr-Fauzan sunkuyar dakai yayi ' gami da nuna ko a jikinsa."OK! Lallai zan sanar ma Daddynku bari ya tashi bacci, Tunda ni bakajin magana ta yanzu."Mr-Fauzan tashi yayi yawuce ' Mummy ta bishi da kallo, Kai tsaye ya nufi kitchen ya bud'e fridge ya d'auki yoghurt domin kuwa yunwa yakeji ' kasancewar baiyi breakfast ba.Mr-Fauzan harya d'auko ya juyo zai bari kitchen d'in suka had'e da Nafee itama zata shigo kitchen d'in.Wata fitinanniyar rigar bacci ne a jikinta ' wacce takeiyakarta gwiwa gata armless, Mr-Fauzan tunda ya kalleta sau d'aya ya d'auke kanshi daga kallonta zai wuce ' ta tsaida da cewa."Good morning ' Sweetheart.""Morning."Ya fad'a yana tafiya bata tare daya juyo ya kalleta.Ganin haka yasa Nafee yin smiling gamida girgiza ' tace."Zakazo hannu."Abunda tace kenan ' ta k'arasa cikin kitchen d'in itama ta d'auki yoghurt ta nufi bedroom d'in Mr-Fauzan dashi.Nafee shiga tayi ba tare da tayi knocking ko sallama ba, A zaune ta iske Mr-Fauzan rik'e da yoghurt hannu d'ayan hannun kuma yana danna laptop dashi.Mr-Fauzan tsayawa yayi yana kallon ta ' daga bisanikuma ya kauda kanshi, Tare da cewa."Get out of my room! Now."Ya fad'a a uzulce."Why?."Tayi tambayar tana k'arasowa tsakiyar d'akin.Ganin haka yasa Mr-fauzan mik'ewa tsaye cikin b'acin rai."Don't you dare come near me!.""Meyasa bazaka bi umurnin Mummy ba? Meye aibuna?."Mr-fauzan ganin zata b'ata mashi lokaci ne yasa shi fizgota suka nufi bakin k'ofar."Get out! And be out of my life forever."Yana gama fad'in haka ya bud'e kofar ya tunkud'a ta waje, Sannan ya rufe k'ofar shi ya koma ya zauna.Nafee juyawa tayi ta koma d'aki tana dannan hannun ta inda ya rik'eta, Ba k'aramin zafi wajen ke mata ba."Dole sai na gasa wajen."Abunda nafi tace kenan ' ta tashi ta cire rigar baccin jikin ta ta d'aura towel, Sannan ta shige bathroom._we don't just entertain and educated, But we also touch the hearts of the readers_*Follow me on wattpad *....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_Pure Moment Of Life writers_*® ```Written```By*_Seemaluv_**28-29*B'angaren Safna kuwa ' baccinta kawai takesha, Rumaisa da Anisa suna cikin yima Umma tausane sukaji ana sallama ' hakan yasa suka amsa.Rumaisa ce ta tashi tare da sanya hijabin ta ' ta fita.Hafiz ne tsaye a k'ofar gidan, Yayi calming hands d'in shi."Ina wuni."Hafiz jin maganar yayi kamar daga sama kasancewar baiga zuwan ta ba, Hafiz kallon Rumaisa yayi cike da tausayawa yace."Y'an mata ya kike? Ya mama?.""Lafiya lau.""Nan ne gidan su Safna ko?."Yayi tambayar yana kallon cikin idon Rumaisa."Eh nan ne! Yaya tace ma, Bari in kirata."Rumaisa juyawa tayi ta shige ciki ' Hafiz ya girgiza kai alaman tausayawa.Bayan Rumaisa ta shige gida ne ' ta fad'a cikin d'aki jikinta na rawa."Yaya Safna! Ki tashi wani mutum yazo wajen ki ' mai mota."Safna cikin magagin bacci ta tsinci maganar, Hakan yasa tayi firgigit ta farka cike da mik'a."Wai meye? Waye shi?."Cewar Safna."Wallahi wanine dai ' kuma ba wanda yazo jiya bane."Rumaisa ta fad'i haka with full of excitement.Safna mik'ewa tayi ta fito tsakar gida ' ta wanke fuskarta, Tukunna ta dawo d'aki ta sanya hijabi ta fita domin duba wanda ke kiranta.Safna koda ta fita a tsaye ta iske Hafiz jingine jikin bangon gidansu ' yana kallon mutanen da ke wucewa, Hakan yasa tayi mashi sallama ' shima ya amsa tare da juyowa ya fuskance ta.Bayan sun gaisa ne ' Hafiz yace."Nasan dai baki sanni ba ko?."Ta d'aga mashi kai alaman Eh, Sannan Hafiz ya cigaba da cewa."Sunana Hafiz Khalif, In short dai ni Abokin Mr-fauzan ne wanda kika tab'ayin aiki a k'ark'ashin Company d'insa."Sunkuyar da kai tayi ' domin sam batason ta tuna darayuwar da tayi awajen."Safna! Maganan da nakeso muyi dake ' inason ki natsu kuma ki fahimceni.""Insha Allah."Ta fad'a a natse."Abokina ne ' yace inzo wajenki domin neman wata alfarma.""Alfarma?.""K'warai kuwa!."Ajiyar zuciya tayi ' sannan tace."Wace irin Alfarma?.""Good! Alfarma ce ta yagani yana so kuma yana so ku daidai ' domin ayi maganar aure."Safna still tayi a wajen ta tana kallon shi ' domin kuwa makamanciyar wannan ranar take jira."Ko kad'an banga laifin ka ba, Domin kuwa kai abokinsa ne ' kuma shi yasan cewa bazan saurare shiba shiyasa ya turo ka kai."Dogon numfashi Hafiz yaja ' yace."Ki kasance mai yafiya Safna... Kasancewar bazai iya had'a ido dake bane yasa shi ya turo ni.""Mutumin da baisan darajar mutane ba? Mutumin dayake kyamatan talaka?."Cewar Safna."Kiyi hakuri ki amince masa Safna, Kuma ki gwada ki gani..."Tunda kafin ya k'arasa rufe baki, Tace."Bazan tab'a iya saka sonshi a zuciyata ba, Balle harna auresa ' domin kuwa tsanarsa ce cike a cikin raina.""Is OK! Na fahimce ki."Ya fad'a tare da saka hannun shi cikin aljihu, Ya ciro bandir d'in kud'in da Mr-Fauzan ya bashi ' ya mik'a mashi tare da cewa."Ga wannan, Ko zaki sai wani abun."Safna kud'in ta kalla ta had'iye miyau don kuwa sunacikin buk'atar su, Lokaci d'aya kuma ta kauda kanta tare da cewa."Ka barshi na gode.""A'a ki karb'a ni da zuciya d'aya na baki."Safna k'in ansa tayi ' shi kuwa ya nace, Suna cikin haka ne Rumaisa ta fito a guje tana haki ' cikin tashin hankali Safna ta rik'ota."Ke lafiya?."Cikin rawar baki Rumaisa tace."Yaya Safna, Umma ne ke aman jini.""Innalillahi!."Hafiz ya fad'i haka, Ganin yadda Safna ta shige gida a rud'e ne yasa shi bin bayanta.D'aki Safna ta fad'a cikin rawar jiki taga Umma rigingine a k'asa tana aman jini, Hafiz d'akin ya shiga shima."Subhanallah this is a critical condition."Safna kuwa hawaye kawai ke zuba daga idonta ' Rumaisa da Anisa ma kuka kawai sukeyi."We have to rush to the hospital, Safna ku kamata asata a mota ' akaita hospital.""To."Ta fad'a, Sannan ita da Rumaisa suka d'aga suka fito waje Hafiz ya bud'e mata motar suka saka ta a back seat."Rumaisa keda Anisa ku tsaya gida ' kafin indawo."Safna ta fad'i haka tana share hawayen fuskarta."Haba, Ya zakice su tsaya gida su kad'ai? Su shiga mu tafi kawai.Cewar Hafiz.Haka kuwa akayi ' Rumaisa ita da Anisa suka zauna a back seat kusa da Umma, Sannan Safna ta shiga front ta zauna.Hafiz zama yayi cikin motar ' yayi saurin tadawa suka tafi, Kai tsaye ya wuce dasu wani babban private hospital ' yayi packing motar shi a ciki tukunna ya bud'e suka fito.Safna ce ta bud'e inda Rumaisa ke ciki suka fito da Umma tukunna Hafiz yayi musu jagora zuwa cikin hospital d'in.Bayan shigar sune ' Nurses suka zo cikin hanzari suka anshi Umma daga hannun su Safna."Please kuyi admitting d'inta kuma kuyi duk abinda ya dace, Kafin inga Doctor d'in."Hafiz ya fad'i haka yana k'ok'arin ciro waya daga aljihun shi, Safna ta tsaida shi tayi da cewa."Bawan Allah na gode da k'ok'ari."Ta fad'a cikin rawar murya ' idanu ciccike da hawaye."Karki damu babu komai, Yanzu dai kije ki sami wajeki zauna ' kafin inga doctor d'in."Safna hannun Anisa ta kama Rumaisa na biye da ita suka sami waje suka zauna a wajen.Hafiz kuwa dialing number d'in Mr-Fauzan yayi ' ringing biyu tayi yayi receiving."Hello! Aboki?."Cewar Hafiz."Na'am Hafiz how far? Ya ake ciki?.""Aiba k'aramar matsala aka samu ba ' in fact madai bata amince da maganar ka ba, And you know what?.""Kai nake saurare ai.""Muna hospital yanzu ' Mum d'inta is in critical condition, Yakamata inbaka Safna kuyi magana.""No! No need of that."Mr-Fauzan ya fad'i haka cikin gadara."Wai meyasa kake haka ne?.""Hm Hafiz raini ne bana so!!! You know me very well,Kunyi magana da Doctor d'inne?."Mr-Fauzan yayi tambayar."A'a, akwai patients d'inda yake dubawa ne, Idan ya gama zamu sameshi.""OK then, Duk yadda kukayi dashi ' you let me know.""OK."Abunda Hafiz yace kenan ' Mr-Fauzan ya kashe wayar, Cikin sa'a saiga doctor d'in ya fito daga wani Ward.Nan ya tsaya suka gaisa da Hafiz ' tukunna Safna ta taso tazo inda doctor d'in ke tsaye, Nan ta fara mashi bayanin condition d'in Umma.Doctor juyawa yayi ' ya nufi ward d'inda aka kwantarda Umma, Hafiz dasu Safna suna biye dashi a baya.Bayan ya shiga ne ya fara yima Umma y'an dube dube ajikin ta, Sannan yace."Za'a dib'i jinin ta yanzu, Akwai blood test da za'ayi mata da Scanning kafin a tantance abunda ke damun ta."To kawai Hafiz yace ' sannan Doctor d'in ya fita, Hafiz ya sami waje ya zauna kasancewar ba k'aramar gajiya yayi ba.Safna kuwa idon ta na kan Umma wacce take unconscious ' batama san inda take ba, Bata ankara ba taji wasu zafafan hawaye suna sauko mata."Yaya Safna, Ki daina kuka ' ai Umma zata warke ko?."Cewar Anisa.Safna jin abunda Anisa ta fad'ane yasa tayi saurin goge hawayen, Tare da cewa."Anisa ba kuka nakeyi ba ' karki damu."Suna cikin haka ' aka shigo aka d'ibi jinin Umma, Sannan akayi settling scanning machine ' cikin y'an lokuta k'alilan aka kammala komai aka fitar da duk wani abunda ke damun Umma.Hakan yasa Doctor ya kirasu ita da Hafiz ' sukaje Office d'inshi suka sameshi.Bayan sun zauna ne Doctor ya fara yi masu bayani ' yadda zasu fahimta, Sannan ya k'ara da cewa."Ba komai ke damunta illa hunhunta da kitse ya rufe."Nan gaban Safna ya fad'i, Cikin rawar baki tace."Likita ban gane ba!.""OK!, Ina nufin kitse ya shiga cikin hunhunta, Yayi causing problems da dama ' Sannan kuma aka bata maganin da bai dace da wajen ba tasha! Wanda hakan shine yasa ta fara aman jini.""Yanzu Doctor meye abunyi?."Hafiz yayi tambayar."Well, Aiki za'ayi mata idan kun amince, Wannan shine kawai solution d'in inba haka ba kuma zata iyarasa ranta ' Kuma wannan aikin yanada buk'atar kimanin kud'i har miliyan d'aya! (1 million)."Safna zaro jajayen idonta tayi wanda suka rune saboda kuka, Tace."Likita ka taimakeni ' ka kuma rufamun asiri, Wallahi ita kad'ai ta tarage mana gashi kuma ba muda kud'i don... "Bata k'arasa ba Hafiz ya dakatar da ita da cewa."Karki damu ' wannan aiba wasu kud'i bane masu yawa."Safna baki ta saki ' tana kallonshi cikin mamaki, Sannan Hafiz ya maida kallonshi kan doctor."Doctor, wannan bazai zama matsala ba ' yanzu dai a d'aurata akan magunguna kafin kud'in su samu.""Alright, To shikenan ' yanzu na baku nan da sati d'aya ku kawo kud'in."Cewar Doctor.Safna da Hafiz tashi sukayi suka bar Office d'in zuwa ward d'in da Umma tace, Safna ta tsaida shi da cewa."Amma a ina zaka sami wad'an nan kud'i?."Ta furta haka cikin sanyin jiki"Safna kenan! Ai kinada inda zakije ki nemo kud'in.""Wallahi babu inda zanje abani wad'an nan kud'in masu yawa.""Akwai!."Hafiz ya fad'i haka, Hakan yasa ta juyo ta kalleshi ' taga fuskar shi babu wasa aciki."Ina kenan?.""Wajen wanda kika tsana ' kika k'i yarda da abunda ya nema a wajenki, Tabbas zaki sami kud'in wajen Abokina Fauzan."Ajiyar zuciya ta saki mai k'arfi, Sannan ta fara tuna halin da Umma ke ciki ' da kuma bayanin da Doctor yayi masu.Cikin Muryar kuka ' tace."Amma kana ganin zai bani kud'in?.""Why not?, Karki damu zanyi mashi bayani ' kuma am very sure zai baki, Yanzu ki koma wajen Ummanki ' zanje indawo."Abunda yace kenan! Ya juya bar Hospital d'in, Sannan itama ta wuce wajen Umma.*** *** *** *** *** *** *** *** ****AROUND 1:00PM*Bayan Hafiz ya koma gida ' yayi wanka yaci abinci, Tukunna ya kira Mr-Fauzan awaya ' bayan ya sanar dashi komai da duk damuwar da Safna ke ciki a yanzu, Mr-Fauzan yace."Zanyi amfani da wannan damar ' in tursasa mata dole sai ta aure ko tana so ko bata so.""Hmm... Aboki kenan bakada dama ' kamar kana sonyarinyar nan fa!.""Oh Come on! Sam babu sonta a raina ' me zanyi da wannan k'azamar? Kawai zan aureta ne don banason Mummy na ta auramun wanda banaso, You know me very well Hafiz."Murmushi kawai Hafiz yayi ' yana jinjina maganar Mr-Fauzan."Yanzu a wane hospital suke?."Cewar Mr-Fauzan."Suna private hospital girmi, And please ka aika akai musu abinda zasuci ' because basuci komai ba.""Alright, Zan tura P.A Kamal, Hafiz inason Monday ka kawo ta Office d'ina."Ya fad'i haka agadarance."OK I will do that."Nan sukayi sallama da junan su ' Mr-Fauzan ya kashe wayar, Sannan yace."Duk abunda ' na buk'ata saina sameshi!!!, Zaki aureni ko kinaso ko bakyaso ' That's Fauzan."Yana gama fad'in haka ya fito daga d'akin shi zuwa garden._we don't just entertain and educated, But we also touch the hearts of the readers_*Follow me on wattpad @Seemaluv1**....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_Pure Moment Of Life writers_*® ```Written```By*_Seemaluv_**_@My Bestie~Jameesha..., Wannan page d'in naki ne ' kuma zanyi amfani dashi domin Nuna how muchI care about you! You're just different Besty, You're different indeed... Bari dai inyi shuru saboda sa'idawa!, In short! I love you... _**30-31*Bayan ya zauna ne ' Mr-Fauzan ya d'aga wayar shi ya kira Sir-Kamal, Ringing d'aya tayi ya d'aga."Hello Sir.""Amm... Kamal ' what are you doing now?.""Nothing Sir.""Good!, Inason kaje private Hospital Girmi ' yanzun nan, Wannan yarinyar na nan Mummyn ta batada lafiya, So I want you to go there! Ka siya musu abunda zasuci ' Ok?.""Ok Sir!."Cewar Sir-Kamal."And if you guys need something ' you let me know.""Ok Sir."Abunda Sir-Kamal yace kenan, Mr-Fauzan ya kashe wayar shi.Sir-Kamal mamaki ne ya cika shi ' zuciyar shi na rayamai wani abun daban.Tashi yayi ' ya fito daga gida ya shige motar shi gateman ya bud'e gate, Sannan ya fice a guje.B'angaren Mr-Fauzan zaune yake a garden tunda suka gama waya da Sir-Kamal, Tsuntsaye da furanni kawai yake kallo.Yana cikin hakan yaga Nafee tazo wajen taja kujera ta zauna ' tunda ya kalleta sau d'aya bai sake kallon taba, Nafee gyarar murya tayi zatayi magana ya d'aga mata hannu alaman dakatarwa."Meyasa kika zamo tamkar karya ' wacce batada zuciya?."Kalmar daya fad'i ne ta bugi zuciyar Nafee, Don kuwa abunda tayi hating arayuwarta shine akira ta da karya."Ko ce miki akayi ana so dole? Mum tana deceiving d'inki ne kawai ' amma babu yadda za'ayi na aura wacce bana so."Cewar Mr-Fauzan.Nan Nafee ta sunkuyar da kai ' hawaye na shirin zubo mata, Tace."Fauzan! Inason ka! Kuma nid'in mai k'aunar kace, Ka zageni ka kuma muzantani iya muzantawa ' amma inason ka sani cewa a yau d'in nan zan bar gidan nan naku... Kuma tabbas zan dawo domin saina rama abunda kaimun."Hawayen idonta ne suka zubo ' tayi sauri ta share, Sannan ta tashi tabar wajen.Mr-Fauzan karan kanshi yasan she is hurt, Amma sam baiyi nadamar abunda ya fad'a ba.Haka ya tashi yabi bayanta domin ya tabbar ko dagaske takeyi, Mr-fauzan koda ya shiga parlor a zaune ya iske Mummy da Daddy suna fira, Nan ya sami waje ya zauna shima.*After 5minutes...* Nafee ta fito along with her trolley' Khairat nabiye da ita abaya sai faman bata hakuri takeyi, Ganin haka yasa Mr-fauzan yatsine baki tare da nuna halin ko inkula.Mummy ne da Daddy suka mik'e tsaye cike da mamaki."Nafee lafiya?."Cewar Mummy."Mum! Ina d'aki fa naga tashigo tana kuka, Sannan tace mun ita gida zata wuce yau she will no longer stay with us again."Khairat ta fad'i haka cikin damuwa."Nafee? Lafiya? Ko mun maki wani abun ne?."Inji Mummy."No ni bakuyi mun komai ba, Nidai kawai inason in tafi gida yau am tired."Nan Daddy ya shiga cikin maganar."Nafeesat, Zo zo ki zauna nan muyi magana."Nafee sakin trolley d'in nata tayi ta sami waje ta zauna, Sannan suma suka zauna."Inason ki fad'amun dalilinki nacewa zaki wuce gida yau!.""No reason! Ni dai kawai I just want to go home, And please don't stop me."Daddy ajiyar zuciya yayi ' tare da girgiza kai."Shikenan Nafee bari insa driver ya kaiki."Mummy ta fad'i haka tana k'ok'arin mik'ewa tsaye, Nafee ta tsaida ita da cewa."Na riga na kira driver d'in gidanmu and am sure thathe's on his way now, Nagode da hallaccin da kika nunamin."Nafee na gama fad'in haka ta mik'e tsaye tare da jan trolley d'inta ta fice, Nafee cen wajen gate ta nufa ta bud'e, Sannan ta fice ' nan ta tsaya tana jiran driver d'in gidansu.B'angaren Mummy kuwa tunda Nafee ta fice ' take kallon Mr-fauzan, Tasan cewa duk yadda akayi he isresponsible."Son?."Mr-fauzan kai ya d'ago ya kalleta ' idon shi kawai ta kalla taga rashin gaskiya k'arara."Me kaiwa Nafee?.""Mum! Ta fad'a miki naimata wani abune?.""Son! Nasan abunda zaka iya da abunda bazaka iya ba, Haka nan kawai Nafee bazata ce zata wuce ba.""Mum, Kawai fa na fad'a mata gaskiya ne ' cewa bana sonta, Nothing else."Mr-fauzan ya fad'i haka tare da maida kallon shi akan TV."What!!!?."Daddy ya furta haka cikin mamaki."Haba Yaya Fauzan ' wallahi tana sonka sosai."Cewar Khairat."Ke ni abokin wasan kine ko? Sai na kakkaryaki awajen nan ' muddin kika sake sako bakin ki cikin maganar nan."Zumb'uro baki Khairat tayi ' taje kusa da Mummy ta zauna."Wane irin rashin hankali ne wannan? Yarinya tabaro gidansu duk saboda kai!, Sannan kayi wasa da feelings d'inta haka?."Nan Mr-fauzan ya d'an nutsu, Don ko kad'an bayason yaga ya b'atawa Daddy rai."To bari kaji in fad'a maka, Tunda har ka wulak'anta yarinyar nan haka! Na baka nan da 2weeks ka kawomin wacce zaka aura, Idan kuma ba haka ba! To kasa aranka tamkar Nafeesat taga gama matar kace."Nan hankalin Mr-fauzan ya tashi, Sunkuyar da kai kawai yayi ' sannan yace."Daddy ' karka biyema Mum mana, Kuma... "Bai k'arasa abunda yake shirin fad'a ba Daddy ya dakatar dashi ' ta hanyar yimasa tsawa."Fauzan!!, Zaka b'acemun da gani ko saina sab'a maka?."Mr-fauzan tashi yayi ya wuce d'akin shi sumumu tamkar wanda yai k'arya.Bayan wucewar Mr-fauzan ne Daddy yace."Kinji mun ja'iri? Please ki tabbatar kin kira mahaifiyar yarinyar nan.""Insha Allah."Daddy tashi yayi ya wuce part d'inshi, Mummy da Khairat kuma suka cigaba da kallo.B'angaren Mr-fauzan, Yana shiga d'akin shi ya zauna a kujerar sofa tare da jinginar da kanshi yana sauke ajiyar zuciya, Wayarshi ya d'auka datake gefensa ya kira number d'in Sir-Kamal.Sir-Kamal yana restaurant tare da Safna da k'annan ta, Yaga shigowar kiran Mr-fauzan ' d'agawa yayi cikin sauri."Hello Sir?.""Kamal! Ina fatan kayi abunda nasaka.""Eh nayi ' gamu nan ma tare dasu a restaurant, Yanzu zan maidasu Hospital d'in.""Ok ' ka tabbatar kayi abunda ya dace.""Ok Sir."Abunda Mr-fauzan ya furta haka ya kashe wayar shi,Nan Sir-Kamal dasu Safna suka fito daga restaurantd'in gami da rik'oma Umma nata abincin ' domin ta samu taci bayan ta dawo conscious.Bayan sun shiga cikin mota ne ' Sir-Kamal yace."Kinga wannan Restaurant d'in?."Safna ta d'aga mashi kai alaman Eh, Sannan yace."To anan na sama miki aiki ' kuma anriga anyi settling komai, Sunci inhar kin shirya zaki iya zuwa Ranar monday!."Safna wani dad'i taji har cikin ranta, Batama son lokacin data bud'e motar ta fito ta tsaya tana kallon restaurant d'inba don kuwa babban restaurant ne.Safna saida ta kai 5minutes a tsaye a wajen ' tukunna ta koma cikin mota."Na gode!, Na gode sosai ' Insha bazan yi maka butulci ba, To amma ya maganar school d'in da kacezaka sani?.""Wannan duk ba matsala bace ' sunce zaki iya zuwa haka nan."Safna juyawa tayi ta kalli su Rumaisa ' da farinciki ya bayyana a fuskarsu, Tace."Rumaisa kuyi masa godiya."Rumaisa da Anisa godiya sukayi mashi tare da nunafarin cikin su a fili, Sannan Sir-Kamal ya tada motar shi yaja suka d'auki hanyar komawa Hospital.Bayan sun isa cikin hospital d'in ne ' yayi packing a gefe, Sannan yace ."Amm... Safna akwai maganar da nakeso muyi dake,Amma ba yanzu ba tukunna ' sai Umma ta sami lafiya .""To."Tace cikin nutsuwa, Sannan sukayi sallama ' ta fito daga motar, Suma su rumaisa suka fito.Sir-Kamal saida yaga shigewar su ciki tukunna yaja motarshi ya wuce.*_Fan's d'ina kuyi hak'uri da wannan!, kuma kuyi hkr da rashin yin posting in time ' duk da dai dama banyimuku alk'awarin zaku ruk'a samu kullun ba kasancewar nima inada abunyi!!! And then Aisha Inaso ki gane cewa bazan mayar miki da martani ba har saikin je kin koyi yadda ake magana tukunna..._*_we don't just entertain and educated, But we also touch the hearts of the readers_*Follow me on wattpad @Seemaluv1**....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_Pure Moment Of Life writers_*® ```Written```By*_Seemaluv_**_@Been in love ' is something special, Ever since I meet you Samra ' my heart keeps telling me that you are the right person to be with,You are my Sweetheart' my lollipopty. This page is yours kawai..._*_And for you my Besty(Jameesha), Am very sorry, you know I heart you, so inasonku both._*32-33*Bayan shigarsu Safna cikin hospital d'inne ' suka zarce ward d'in da Umma take, Suna shiga suka iskeUmma zaune ita da wata nurse ' tana mata settling drip.Safna dasu Rumaisa waje suka samu suka zauna, Sannan Safna tace."Umma ya jikin?.""Da sauki."Rumaisa da Anisa sannu sukabi Umma dashi, Bayan nurse d'in ta gama ne ta juyo ta fuskanci Safna gamida cewa."Yanzu ansa mata ruwa, Ki tabbatar taci abinci domin akwai wasu magungunan da zanzo inbata."To kawai Safna tace, Sannan Nurse d'in ta juya ta fita.Bayan fitar tane ' Safna ta bud'e ledar da suka shigo da ita, Ta d'aukowa Umma take away na abincin ta ' ta bata gamida cewa."Umma ga abinci ki ' tuwon shinkafa ne, Ki daure kici."Ansa Umma tayi ta aje agefenta ' tace."Safna ina aka sami kud'i haka?"Nan Safna ta bawa Umma labarin duk abinda ya faru ' da yadda sukayi da doctor.Umma ajiyar zuciya tayi ' tare da girgiza kai alaman damuwa."Yanzu a ina zamu sami wannan mak'udan kud'in?.""Umma karki damu, Abokin Oga na yace ' babu matsala inhar taje na tambayeshi zai bani."Safna ta fad'i haka cikin walwala, Umma kuwa ajiyarzuciya kawai tayi ' ta fara cin abincin ta.Haka rayuwa ta cigaba da juyi dasu Safna ' Hafiz abokin Mr-Fauzan shi ke zuwa yana maidasu gida, Ita kuma Umma nurses na kula da condition d'inta.*** *** *** *** *** *** *** ****Yau take Monday...*Da sassafe Safna ta tashi daga bacci, Ta had'a musu koko suka sha ' sannan suka yi wanka.Bayan sun gama shiri ne ' sukaji ana sallama."Wannan muryar Abokin Oga ne."Safna ta fad'i haka tare da sanya hijabinta ta fita domin dubawa.A tsaye ta ganshi, Nan taimashi sallama suka gaisa tukunna yace."Amm.. Kundai shirya ko?.""Eh mun shirya.""To ku fito inkaiku hospital d'in, Daga nan sai muje wajen Abokin nawa."Safna juyawa tayi ta koma ciki domin su fito ta kulle gidan, Cikin 'yan k'ank'anin lokaci suka fito gaba d'ayansu Rumaisa na rik'e da kwanon kokon Umma wanda zata karya dashi.Dukkansu mota suka shige ' shima Hafiz ya shiga yatada motar, Sannan yaja suka wuce.Bayan *2hours*, Suka isa hospital d'in, Bayan yayi packing ne yace."Safna, Kije kiyiwa Ummanki bayanin inda zakije ' kuma sannan kice inai mata sannu.""To."Abunda tace kenan ta bud'e k'ofar ta bar motar, Rumaisa da Anisa na biye da ita.Safna sai da tad'an jima, Sannan ta fito daga hospital d'in.Hafiz kuwa wak'a ya saka a motar ya k'ure sauti, Yana facing left side d'inshi.Haka Safna ta iso wajen motar ta dunga sallam ' amma sam baiji ba, Sai da ta bud'e motar ta shiga tarufo k'ofar da k'arfi tukunna ya juyo da sauri ya kalleta tare da rage volume d'in sautin, Sannan ya tada motar suka wuce.Hafiz gudu kawai yakeyi babu abinda ya dameshi, Cikin 'yan lokuta k'alilan suka isa company d'in.Hafiz packing yayi, Sannan suka fito suka shiga ciki, Safna kallon mutanen da ke ciki taitayi kasancewar kallon komai takeyi sabo, Domin ko kad'an bataga idon sani ba.Hafiz tafiya kawai yakeyi zuwa office d'in Mr-FauzanSafna na binshi abaya.Bayan sun kai bakin office d'inne Hafiz yace."Ki jira anan ' tukunna."Yana fad'in haka ya bud'e office d'in ya shige.Safna dai tsaye take tana ta baza ido tako ina, Don batasan abinda suke tattaunawa ba.Hafiz bai wani b'ata lokaci ba ya fito gami da cewa."Ki shiga kuyi magana, In kinfito ina mota."Kai ta d'aga mashi kawai ' zuciyar ta na bugawa, Don kuwa bazata mance wanene Mr-Fauzan ba.Bayan wucewar Hafiz ne Safna ta bud'e office d'in ahankali tamkar wacce tai k'arya.Sallam tayi sannan ta k'arasa ciki, Koda ta shiga ta iske shi a zaune amma ya juya bayan sa."Ki nemi wajen zama."Abunda taji yace kenan, Taje ta zauna tana kallon bayansa."Hafiz ya fad'amun cewa Mum d'inki bata da lafiya."Murmushi tayi tace."Eh ashema yayi maka bayani, Wallahi bata da lafiya' tun a gida ta fara rashin lafiyan to shine...."Bata k'arasa ba Mr-Fauzan ya dakatar da ita da cewa."Idan surutu zakimun ' tun wuri ki tashi ki fita."Ya fad'i haka tare da juyowa.Safna sunkuyar da kanta kawai tayi, Don kokad'an batason suna had'a ido."Amm... Dama taimako nazo nema wajenka, Sir please ka taimakamun da kud'in da zan bada aima Umma ta aiki, Likita yace idan ban nemo kud'in ba zata iya rasa ranta.""Are you afraid to loose her?."Safna saurin d'ago kai tayi ta kalleshi ' da hawaye cike da ido, Ita dama abun kuka baya mata wuya."Ita kad'ai ce ta ragemun sai kuma 'yan k'annai na, Kuma likita yace miliyan d'aya suke buk'ata, Sir don Allah ka taimaka mun."Safna ta fad'a haka tana share hawaye."Zan baki kud'in da sukafi haka muddin kika amince da abinda zan fad'a miki yanzu.""Sir, Indai akan infanshi ran Umma na ne ' to nai maka alk'awari zan amince da duk abinda kace."Safna sam ta manta tayin da Mr-Fauzan yayi mata.Mr-Fauzan murmushi yayi ' sannan yayi calming hands d'inshi yana kallon ta."Zan kaiki gidanmu In gabatar dake amatsayin wacce zan aura."Zaro ido Safna tayi tana mamakin abunda Mr-Fauzan ke fad'a."Yes! And after that zan aure ki! Ba don komai sai don banason Mummyna ta aura mun wata, If not ' kema kinsan babu abinda zanyi dake amatsayin mata."Sunkuyar da kai tayi ' idanunta cike da k'walla, A zuciyarta tace."Nasan dama saina fuskanci wulak'anci awajen mutumin nan, Amma babu komai...""Taimaka miki zanyi kawai ' amma ba don inasonki ba, Kuma cikin wannan satin nakeso ayi auren!, Za'a cigaba da kula da Ummanki a hospital har ranar aure kin cika alk'awarin da kika d'auka sannan zanbaki kud'in."Safna saurin kallon shi tayi tana girgiza kai."Sir, Kada kaimun haka don Allah ' likita yace zata iya rasa rayuwarta a kowane irin lokaci, Ka taimaka mun.""Ke zaki taimaka ma kanki ' kibi duk abinda nace, Muddin kika kwantar da hankalinki to babu abinda zai sami Ummanki."Dogon numfashi Safna taja ' sannan tayi shuru nad'an lokaci tace."Kana ganin baza'a sami matsala ba?.""Bana buk'atar tambayoyi daga gareki, And mind you ' koda na Aure ki kada kiyi kuskuren sakani aranki because zakisha wahala a banza."Safna kuwa k'asa kawai take kallo don kuwa hawayen ma sunk'afe, Zuciyarta a bushe take ' tsantsar tsanace ke d'awainiya da ita."Gobe, *Around 11:00am* zan turo P.A Kamal ya d'auko ki, And make sure kin fad'ama Ummanki."Safna harzata tashi da niyyar wucewa ' ya dakatar da ita."Ki sanarma Ummanki ' cewar mun dad'e tare so mun riga mun fahimci juna, If not zaki iya rasa ta inhar aka sami delay!!!."Safna kai kawai ta d'aga mashi, Sannan ta tashi ta fita cikin sanyin jiki.Tafiya kawai takeyi amma hankalinta baya jikin ta ' Safna condition d'in Umma kawai take tunawa.Inda Hafiz ya tsaya ta nufa ' tana isa ta bud'e motar ta shiga, Hafiz bacci ma ya fara jin anrufo motarne yashi yin firgigit ' ya bud'e ido.Ganin Safna yayi cikin wani yanayi ' yanayi na damuwa."Safna lafiya kuwa?."Shuru tayi bata bashi amsa ba ' hakan yashi sake tambaya."Ko ya hanaki kud'in ne?.""Ka kaini wajen Umma na ' ita kawai nakeson gani."Hafiz tab'e baki yayi gamida nuna halin ko'ajikin shi, Tukunna yaja motar zuwa hospital._we don't just entertain and educated, But we also touch the hearts of the readers_*Follow me on wattpad @Seemaluv1*
@Seemaluv1*B'OYAYYEN**AL'AMARI**_Pure Moment Of Life writers_*® ```Written```By*_Seemaluv_**_I proudly dedicated this page to you my sweetest and lovely Samra, Am so much proud of Baby..._**34-35*Bayan sun isa hospital d'inne Hafiz ya ajeta, Sannan ya juya ya wuce.Haka Safna ta k'arasa cikin hospital d'in sukuku jikinta babu k'wari, D'akin da Umma tace ta nufa ' bayan shigarta ne ta sami waje ta zauna, Sannan tace."Umma ya k'arfin jikin naki?.""Toh 'yan nan da dadi sauk'i, Amma nikam ji nake kamar ciwon k'aruwa yake."Umma ta fad'a haka tana kwance, Safna kai kawai tagirgiza tace."Umma dama akwai maganar da nakeso muyi dake.""To inajinki."Safna wasa da 'yan yatsunta ta farayi fuskarta na kallon k'asa tace."Umma dama Oga nane ' ya dameni yanason ya turomagabatansa domin ayi maganar aure.""Ogan ki kuma? Safna?.""Eh Umma!.""Inace shine wanda kike bani labarinsa!.""A'a Umma bashi bane ' wannan wanine daban, Kuma yace cikin wannan satin nan yakeso a d'aura wai saboda iyayensa sun matsu."Umma shiru tayi tana nazari akan maganar."Kuma Safna ayi biki ina kwance a asibiti?, Amma idan yazo kice masa inason ganinshi."Doguwar ajiyar zuciya ta saki, Sannan tace to ' tare da kallon su Rumaisa da suke kwance saman tabarma a k'asa suna bacci.*AROUND 2:00PM*Safna da Umma suna cikin fira ' Sir Kamal ya shigo tare da yi musu sallama rik'e da ledar a hannun shi, Alamun abinci ne ya kawo musu.Sir Kamal ciki ya k'arasa Safna ta tashi ta bashi wajen zama ya zauna, Sannan ya gaishe da Umma da jikinta."Dama Oga nane yace inkawo muku wannan."Sir Kamal ya fad'a tare da mik'awa Safna ledar take away d'in."Amma ai jikin da sauki ko?.""Eh da sauk'i Alhamdulillah."Cewar Safna."To shikenan, Ni bari intafi.""Har zaka wuce? To nagode kace mashi mungode."Cewar Umma.Sir-Kamal tashi yayi ya fita Safna na binshi a baya, Bayan sun isa wajen mota ne yace."Oh God! Na manta Oga yace inbaki waya kuyi magana, Amma kafin nan dai bari infara fad'a maki abinda ke cikin raina Safna ' kinsan nace miki akwai maganar da zamuyi."Kai Safna ta d'aga mashi alaman Eh, Sannan ya cigaba da cewa."Safnaaa... Na kasa hak'uri da abinda zuciya ta take fad'amun a koda yaushe, Ya zama dole yau in bayyana maki."Ita dai Safna kam k'asa kawai take kallo, Tana sauraron shi."In fact! Ina sonki Safnaaa..."Gabanta ne yayi mugun fad'uwa tayi saurin d'ago kanta ta kalleshi cike da mamaki da d'aurewar kai."Yes Safnaaa... Ina sonki ' kuma so na gaskiya, Inason inga na mallakeki a matsayin mata ta."Safna bata san lokacinda hawaye suka zubo mata ba ' tayi sauri ta share."Why are you crying Safnaaa, Meyasa kike kuka?."Cikin kuka tace."Babu komai, Bakace zamuyi magana da Oganka ba?."Kai ya d'aga mata, Sannan ya ciro wayar a aljihun shi gami da dialing Number d'in Mr-Fauzan tukunna ya bata."Kisa a kunne ' idan ya d'auka sai kice kece."Ringing uku tayi Mr-Fauzan yayi picking tare da karawa a kunne."Assalamu alaikum!, Safna ce."Jin haka yasa Mr-Fauzan lumshe idanu ' sannan yace."Nasan zaki nemi ni shiyasa nace abaki wayar.""Amm.. Dama Umma ne tace tana son kazo.""Ok, Kice mata zanzo zuwa anjima *Around 9:00pm*."Abunda yace kenan ya kashe wayar ' jin haka yasa ta mik'awa Sir-Kamal wayar shi ta juya zata wuce yayi saurin tsaida ita."Meyasa zaki tafi bayan bamu gama magana ba?."Safna juyowa tayi ta kalleshi cike a tausayawa tace."Saboda maganar batada wani amfani a halin yanzu."Waro ido yayi yana mamakin furucin Safna."Safna wannan maganar itace mafi amfani awajena, Ki tsaya ki saurareni please..."Yayi maganar ta wata muryar data kasa tantance soyayyace ko kuwa damuwa!.Nan take hawaye suka fara yimata zarya a fuskarta, Sir-Kamal yayi sauri matsawa kusa da ita tare da cewa."Please inhar abunda na fad'ine ya saki kuka ' to kiyi hak'uri bazan sake ba.""Kayimun komai a rayuwa ta ' haka zalika ka taimakeni a lokacinda nake da buk'atar taimako, Amma a halin yanzu kazomin da abinda bazan iya taimaka maka da shiba ' kayi hak'uri ka cireni a cikinranka."Ta gama rufe baki ta juya ta wuce ' saida takai bakink'ofar shiga hospital d'inne taji tada motar shi, Nan ta tsaya cak gami da dafe kanta."Ya salaam! Mena aikata?."Juyawa tayi da sauri taga harya wuce, Nan ta sami bango ta jingina hawaye kawai ke fita daga idon ta tana cewa."Nima ina sonka! Ina sonka."Safna ji tayi ance."Baiwar Allah idan kina son shi ' to ki fad'a mashi zaifi."Jin abinda akace ne yasa Safna saurin kollon side d'inta taga Nurse ce a yatsaye kusa da ita."Bazai sameni ba.""Meyasa? Ba kince kina sonsa ba? Then, ki fad'a masa kawai."Safna kai kawai ta girgiza gamida cewa."Bazaki tab'a fahimtar komai ba."Abinda Safna ta fad'a kenan ta wuce cikin hospital d'in, Saida ta tabbatar ta share hawayenta sannan tak'arasa cikin ward d'in da Umma take.*** *** *** *** *** *** *** ***B'angaren Hafiz ' tunda ya koma gida yaketa aikin akan computer d'inshi kasancewar he's a business man.Hajiya ce ta fito tsakar parlor ta iske 'yar aiki na gogegogen inda yad'anyi k'ura, Nan ta sami waje ta zauna gami da cewa."Wai ina Aleeza take ne?.""Hajiya tana d'akin ta."Cewar 'yar aiki."Je kikira min ita."'Yar aikin aje tsunman tayi ta tafi d'akin Aleeza ta isar da sak'on Umma tukunna ta baro d'akin.Aleeza tashi tayi daga kwanciyar da tayi tahau gyarakanta ' gaban mirror taje ta tsaya ta shafa powder, Sannan ta gyara d'aurin kanta gamida d'aukan gyaleta yafa bisa kafad'anta gefe d'aya, Tukunna ta fito parlor ta zauna kusa da Hajiya."Hajiya gani.""Na fito ne banji motsin ki ba! Shine nace aje akira mun auta."Murmushi Aleeza tayi cikin shagwaba tace."Yawwa Hajiya ki d'an bani key d'in motarki inje wani waje.""Ina kuma zakije?."Langwab'ar da kai Aleeza tayi tace."Gidan k'awata.""Toh amma dai kar a dad'e kinsan dai halin Yayanki."Kai kawai Aleeza ta d'aga, Sannan Hajiya tayi mata nuni da saman kujera gamida cewa."Ga key d'in cen."Aleeza tashi tayi ta d'auki key d'in ta fice, Tana fita taumarci mai gadi daya bud'e mata gate.Cikin hanzari ta bud'e motar ta shiga taja ta wuce.Company d'in Mr-Fauzan ta nufa, Cikin mintoci ta isa wajen.Aleeza gefe ta samu tayu parking sannan ta fito ta k'arasa ciki, Bayan shigarta ciki ne security suka taretare da 'yan tambayoyi."Mtsw look! Banazo wajen nan domin ku rufeni da questions bane, Office d'in Mr-Fauzan nakeson ku kaini."Nan ma wani dogon surutun suka tsareta dashi, Hakan yasa Aleeza yin magana cikin fad'a."Hey!! Kun san wacece ni? Ni matarsa ce, Saboda haka ku kaini inda yake."Jin abinda ta fad'ane yasa suka sunkuyar dakai gamida bata hak'uri, Sannan d'aya daga cikinsu yayimata jagora zuwa Office d'in.Saida ya tabbatar ya kaita bakin office d'in tukunna ya juya ya tafi.Aleeza dogon numfashi ta saki tare huro iskar bakinta waje, Sannan ta bud'e ta shiga ciki.Koda ta shiga iske shi tayi yana aiki bisa laptop d'in shi tare da cike wasu documents.Sallama tayi mashi ' hakan yasa shi d'ago kai ya kalleta tukunna ya amsa sallamar ya cigaba da aikinshi, Aleeza waje ta samu ta zauna sannan tace."Fauzan...""Can you please introduce yourself?."Mr-Fauzan ya fad'i haka ba tare daya kalleta ba."Am Aleeza ' ni kanwar abokin ka Hafiz ne.""Can I help?."Ajiyar zuciya tayi mai k'arfi wanda har saida ya juyo ya kalleta."Fauzan... Bansan yadda zan furta maka ba ' but koma ta yayane inason ka fahimce ni.""Go ahead!.""Tun lokacin da kazo gidan mu naji inasonka a cikin raina ' kuma naga dakai na dace."Wani mugun kallo Mr-Fauzan yayi mata hakan yasa ta kauda kanta, Domin kuwa babu abinda zai hanatafad'in abunda ke ranta."Wallahi inasonka ' ina sonka Fauzan..., Inason ka bani dama so that I can prove it to you please...""So! Aleeza haka kika lalace da son maza ko? I will definitely tell your bro, Now ki tashi kibarmun office ' tunkafin in b'ata miki rai.""Fauzan, Ka so mai sonka ' wallahi zan iya shiga wani hali muddin bansame kaba.""Get out of my office I said!!!."Tsawar da yayi mata ne yasa ta razana ' tayi saurin mik'ewa, Hakan yasa ta turgud'e ta fad'i.Mr-Fauzan tab'e baki yayi gamida nuna halin ko inkula da ita, Aleeza kuwa dakyar ta iya jan k'afarta ta bar Office d'in.Bayan fitar tane Mr-fauzan ya girgiza kai tare da cewa."Ladies of nowadays ' sam basu da kunyar fad'ama namiji suna sonshi, Amma yaushe Aleeza ta fara hauka haka?."Tsaki yaja sannan ya cigaba da aikin shi.B'angaren Aleeza kuwa ' tunda ta samu takai kanta cikin mota take hawaye, Damuwa ce sosai ta bayyana a fuskarta.Ganin kukan bazai amfana mata komai bane yasa tabud'e dose lock box d'inta dake cikin motar ta ciro wasu k'wayoyi tasa abakinta ta tsotse, Sannan ta tada motar ta wuce.Tana cikin driving ne ' taji wani dizziness na d'ibanta,Hakan yasa ta fare k'ok'arin samun wajen packing amma ina! Abun yaci k'arfinta, Ji kake kararaf!!!._we don't just entertain and educated, But we also touch the hearts of the readers_*Follow me on wattpad @Seemaluv1*
*....B'OYAYYEN* 👒
       👒 *AL'AMARI*

*_Real Pure Moment Of Life writers_*

® ```Written```     
       By
*_Seemaluv👄_*

      *_@ Dedicated This page to you Samra, Because I choose you. and i'll choose you, over and over. without pause, without a doubt, in a heartbeat, i'll keep choosing you,I love you. _*

                       *36-37*

 Tun daga nan Aleeza bata sake samun kanta ba ' sai dai ta farka ta ganta a gadon asibiti, Sam bata lura da wanda yake zaune a gefenta ba ' hakan yasa ta yunk'ura zata tashi sai jitayi ance.
   "A'a, Ki kwanta abunki ' kin d'anji rauni dayawa."
  Da sauri Aleeza ta juyo ta kalli mai magana tare da dafe kanta tace.
   "Naji rauni? Rauni?  How?."
   "Amm... Sunana Dr Khalil Muhammad!, Nine wanda mukayi karo da junanmu ' amma ni banji komai ba Allah ya tsare, Kema d'in bakiji ciwo sosai ba saidai buguwa da kikayi."
  Aleeza tsayawa tayi tana kallon shi ' shima d'in kallonta yakeyi yana smiling, Hakan yasa tayi sauri ta d'auke kanta tare da cewa.
   "Bani phone d'inka inkira Yaya na!."
  Khalil ciro wayar shi yayi k'arar IPhone8 ya mik'a mata gamida cewa.
   "Meyasa bazaki kira Mum ba?."
   "A'a,  Banason hankalinta ya tashi ne."
  Murmushi yayi tare da girgiza kai yace.
   "Ita ya dace ki kira not your brother."
  Aleeza ba tare da taimashi gardama ba tayi dialing number d'in Hajiya, Cikin sa'a kuwa ringing d'aya tayi ta d'auka, Aleeza tayi gyarar murya tace.
   "Hello Hajiya!."
   "Na'am Aleeza ' wannan number d'in waye."
  Aleeza kallon Khalil tayi tace.
   "Meye sunan wajen nan?."
   "Private Hospital Girmi."
  Nan ta maida wayar a kunnenta tace.
   "Hajiya ina private Hospital Girmi,  Kuzo."
   "What! Subhanallah ' meyafaru dake Auta?."
  Umma ta fad'i haka tare da mik'ewa tsaye.
   "Hajiya please ki kwantar da hankalinki ' accident ne but banwani ji ciwo ba."
   "Shikenan gamu nan zuwa da yayanki."
  Abunda Hajiya tace kenan ' ta shiga kiran Hafiz, Bayan ya fito tsakar parlor ne Hajiya ta sanar dashi komai, Hakan yasa shi matsawa kusa da ita ya zaunar da ita sannan yace.
   "Hajiya ki kwantar da hankalin ki, Ki sanya hijab ' ni bara inje intada mota."
  Hajiya sawa tayi 'yar aiki ta d'auko mata hijab, Sannan shi kuma Hafiz ya fita harabar garage ya umurci gate man ya bud'e masa gate.
  Bayan shigarsa mota ne Hajiya ta fito ta shiga motar suka wuce.
  B'angaren Aleeza kuwa tunda ta gama wayar ' taketa juya wayar a hannunta, Shi kuwa Khalil smiling kawai yake sakar mata.
   "Tai maki kyau ne?."
 Taji tambayar kamar daga sama, Hakan yasa ta juyo ta kalleshi ' sannan ta maida kallonta kan wayar tare da mik'a mashi.
   "Idan kinaso ' to nabaki halak malak."
  Had'e rai tayi ta wurga mashi wayar shi tace.
   "Cemaka akayi banda waya? Kokuwa fad'a maka akayi inada buk'atar wayarka?."
   "Allah ya baki hak'uri! Amma meyasa kike yawan tunani?."
   "Bangane ba."
   "Yes dear, Kina cikin damuwa ko! Hakan yasa kikasha maganin da yafi k'arfin jinin ki which is very bad, Karki sake shan magani irin haka kinji ko?."
  Kai ta d'aga mashi cike da shagwab'a idanuwanta duk sun cicciko da hawaye.
   "Nima d'in badason raina nasha ba, Hasalima niba ma'abociyar shan kwaya bane."
   "To meye dalilin da yasa kika sha."
   "Wani nakeso and shi kuma baya sona, Shiyasa kullun nake shiga damuwa."
   "It's OK! I can understand how you feel, Amma kibar damuwa aibazaki rasa masoya ba ' ballema ke d'in kyakkyawa ce."
  Murmushi kawai Aleeza tayi mai kama da kuka, Sannan yace.
   "Can I have your number?."
  Ganin bata bashi amsa bane yasa shi dank'a mata wayar a hannunta, Nan Aleeza ta rubuta mashi ta mik'a mashi.
   "Thank you dear."
   "You're welcome."
   "Da wane sunan zanyi saving?."
Yayi tambayar yana kallon fuskarta.
   "Aleeza."
   "Nice name."
Suna cikin haka ne su Hajiya suka shigo cikin hospital, Nan suka tambayi nurse aka nuna musu ward d'inda take.
  Bayan sun shiga ne Hajiya ta zauna kusa a Aleeza ' shi kuma Hafiz ya mik'a ma Dr Khalil Hannu suka gaisa.
   "Hajiya ina mai baku hak'uri da abinda ya faru, Nayi k'ok'arin kauce mata abinda yak'i ' kunsan tsautsayi baya wuce ranar sa, To amma Alhamdulillah bataji rauni da yawa ba."
   Cewar Dr Khalil.
  Hamdala Hajiya tayi ' sannan Dr Khalil yayi musu bayanin abinda yayi causing accident d'in.
  "Bari in rubuta maku antibiotics wanda zata ruk'a sha."
 Ya fad'i haka yana k'ok'arin ciro paper da pen daga cikin aljihun shi, Aleeza tace.
   "Dama a Hospital d'in nan kake aiki?."
   Kai kawai ya d'aga  mata ya fara rubuta mata magunguna. 
  Bayan ya gama ne ya mik'awa Hafiz paper d'in,  Tare da basu iznin tafiya gida.
  Cikin kamala Dr Khalil yayiwa su Hajiya rakiya har inda sukayi packing motar su, Sannan ya juya ya koma ciki.
  Bayan shigarsu mota ne kiran Mr-Fauzan ya shigo cikin wayar Hafiz, Hafiz ciro wayar yayi daga aljihun shi yayi receiving gamida da karawa a kunne.
   "Hello Babban mutum ya'akayi ne?."
   "Aboki so nake kazo muje wajen yarinyar nan ' Mum d'inta keson ganina."
   Cewar Mr-Fauzan.
   "To yanzu dai ina hospital d'inma amma zan koma gida yanzu in aje su Hajiya, Sai inzo mutafi."
   "Hajiya ce ba lafiya?."
   "A'a Aleeza ce k'anwa ta, Bari dai idan naje gida zan kira ka."
  OK kawai Mr-Fauzan yace ya kashe wayarshi.
  Mr-Fauzan aikinshi ya cigaba dayi a office hankalinshi kwance.
 
*AROUND 5:00PM*

 Mr-Fauzan ganin haryanzu Hafiz bai iso bane yasa shi sake kiranshi a waya, Cikin d'an k'ank'anin lokaci Hafiz ya d'aga wayar.
   "Haba Hafiz! Kaifa naketa jira since, Wallahi na k'osa inbar company d'in nan inbarwa P.A aiki."
   "Ohhh so sorry Aboki, Sam na manta wallahi ' gani nan zuwa yanzu."
  Abinda Hafiz yace kenan ya kashe wayar ya fito daga cikin gida ' ya shiga mota yaja zuwa Company d'in Mr-Fauzan.
  Mr-Fauzan kuwa bayan sun gama waya da hafiz ne ya kira Sir-Kamal ya dank'a mashi wasu documents akan ya cigaba da aiki sai *9:00pm* zai bar office.
   Mr-Fauzan bayan ya kammala harhad'a komai ne ya fito waje zuwa inda yake hutawa, A nan ya zauna.
  Zaman shi keda wuya yaji hone, Hakan yasa shi juyawa domin yaga waye.
   Hafiz ne ya fito daga cikin motar ' ganin shine yasa Mr-fauzan yin saurin tashi tare da k'arasawa wajen shi suka gaisa.
   "Muje ko?."
  Cewar Mr-fauzan.
   "Eh."
 Hafiz ya bashi ansa.
  Mr-Fauzan shiga cikin motar Hafiz yayi suka tafi.
  Cikin 'yan mintoci suka isa cikin hospital d'in, Cikin sa'a sunayin parking ana kiran sallar magrib.
  Saida sukayi sallah tukunna suka k'arasa ciki.
  Direct ward d'inda Umma take suka nufa, Cike da sallama suka shiga ciki Safna ta amsa.
  Ganin sune yasa ta fara kintsa wajen da kauda kwalin takeaways da sukaci abinci dashi.
  Hafiz zuk'unnawa yayi ya gaishe da Umma da jiki ' Sannan shima Mr-Fauzan ya d'an sunkuya ya gaisheta.
   "Amm Rumaisa ku d'agamin tabarman nan in shinfid'a musu."
  Cewar Safna.
 Har su Rumaisa sun tashi Mr-Fauzan ya dakatar dasu ' cike da nuna k'yamata.
   "A'a kuma barshi we are OK here!."
 Ya fad'a yana yatsine baki tamkar mace.
   Ita dai Safna kanta a sunkuye yake ' zuciyar ta babu abinda takeyi in banda suya, Wurin ne yayi tsit nad'an lokaci ' sannan Safna ta d'ago kai ta kalli Umma wacce take kwance don ita tama mance zatayi bak'o.
   "Umma ' gafa bak'in nan sunzo."
   "Wane irin bak'i kuma 'yan nan?."
   "Umma maganar da mukayi dake d'azun mana."
  Nan Umma ta yunk'ura cike da ninshi ta zauna.
   "Oh Allah sarki ' anyi haka kuwa, To Alhamdulillah sannun ku da zuwa."
   "Yawwa sannu Umma."
  Cewar Hafiz.
 Umma gyaran murya tayi ' ta fara fad'awa Mr-Fauzan tarihhin Safna da yadda danginsu suka juya musu baya Tare da cewa.
   "Ba muda gata ' sai Allah, Kuma yaro na amince maka na kuma baka auren Safna ' idan za'a d'aura auren aje masallaci ayi."
   "Amm... Wannan duk ba abin damuwa bace ' gobe insha Allah zanzo da mahaifina domin ayi maganar auren, Don ni nafison nan da next week ayi bikin."
  Cewar Mr-Fauzan.
 Umma ajiyar zuciya tayi cike da jinjinawa al'amarin, Tace.
   "To shikenan ba matsala."
   "And then, Insha Allah bayan bikin za'ayi miki aikin ciwon dake damunki."
  Umma zaro ido tayi tare da nuna jindad'in ta, Gamida cewa.
   "Yaro na gode, Alhamdulillah! Allah ya sanya alkairi."
  Nan sukayiwa Umma Sallama ' Mr-Fauzan ya sanya hannu a aljihu ya ciro band'ir d'in 'yan dubu ya ajiyewa Umma bisa gadon da take, Suka juya suka fita.
   "A'a'a'a... Yaro harda wahala haka? To angode."
  Abinda Umma tace kenan ta koma ta kwanta, Sannan Safna tabi bayansu.
  Bayan sun fita daga cikin hospital d'in Safna na biye dasu, Hafiz yace.
   "Fauzan bari inshiga mota injira ka, Ka tsaya ku gaisa ko?."
  Hafiz ba tare daya tsaya yaji abinda Mr-Fauzan zaice ba ya shige mota ya barsu nan tsaye.
  Mr-Fauzan da Safna, Shuru sukayi nad'an lokaci sannan Safna tace.
   "Amm... Na gode da duk alkairin da kaimun."
   "Don't Mention."
 Ya fad'a yana k'ok'arin wucewa, Cikin k'arfin hali tace.
   "Harzaka tafi?."
Jin abinda tace yasashi juyowa ya kalleta, Hakan yasa ta sunkuyar da kai.
   "Yes, Wucewa zanyi don banga amfanin tsayuwa anan ba! Besides '   taimakon ki nayi nazo wajen nan, Kamata yayi ki kwana kinamin godiya ' zan taimaki Umman ki ' ni a yanzu haka inajine tamkar infasa aurenki but I will not do that because ' banason zab'in wasu zab'in kaina nakeso."
  Safna had'e rai tayi kanta na sunkuye hawaye na mata zarya a fuska, Mr-Fauzan yazo daf da ita suna facing juna yace.
   "And let me remind you Safna, Zan aure ki ne kawai don na ajeki cikin gida na ' har sai lokacin da naga wacce taimun, Sannan na aure ta ' ke kuma na sake ki."
  Abinda Mr-Fauzan yace kenan ya juya zai wuce ' Safna cikin kukan da bashida sauti da radad'i ta tsaida shi da cewa.
   "Naji dad'i tunda akwai saki aciki, Kuma ina k'ara yi maka godiya."
  Tana gama fad'in haka ta juya aguje cikin kuka ta shige cikin hospital d'in. 
  Mr-Fauzan wucewar shi yayi ' tare da nuna halin ko'inkula ya shige mota, Hafiz yaja suka wuce.

*AROUND 8:00PM*

Hafiz ya aje Mr-Fauzan gida, Sannan shima ya koma gida.
  Mr-Fauzan koda ya shiga cikin gida ' a harabar parlor ya tsaya ganinsu Mummy da Daddy zaune suna kallo.
  Mr-Fauzan sallama yayi Daddy ya amsa ' sannan ya k'arasa wajensu ya sami waje ya zauna, Tukunna yace.
   "Daddy, Na sami wacce zan aura ' kuma mahaifiyar ta tace inturo zuwa gobe."
  Daddy maida kallon shi yayi kan Mr-Fauzan yace.
   "To Alhamdulillah, A ina suke?."
 Nan Mr-Fauzan ya fad'awa Daddy komai da duk abinda abinda ya k'unshi rayuwar da suke ciki, Sannan ya k'ara da cewa.
   "Amma Daddy Mahaifiyar ta tana hospital a yanzu haka, Kuma tace babu damuwa zama a iyayin bikin tana kwance."
   "Subhanallah! Meke damunta kuma?."
   "Eh aiki dai za'ai mata, But nina d'auki nauyin aikin ' bayan biki I mean next week za'ayi mata aikin."
  Maganar Mr-Fauzan ne yabawa Daddy dariya, Hakan yasa yace.
   "Wato dai Son, Kana nunfin next week za'ayi auren kenan?."
   "Eh Daddy, Saboda abunda na riga na tsara kenan."
   "Very Good!, To Allah ya kaimu goben sai muje hospital d'in, Allah kuma ya maka albarka."
  Ameen Mr-Fauzan yace ' ya tashi zai wuce Mummy tace.
   "Fauzan?."
  Juyowa yayi ya kalleta with cares.
   "Na'am Mum."
   "Ina fatan dai ba dangin talaka zaka kawo mana ba!."
  Har Mr-Fauzan ya bud'e baki zaiyi magana Daddy yayi saurin cewa.
   "Yi tafiyar ka Son."
Mr-Fauzan part d'inshi ya nufa, Sannan Daddy yace.
   "Wai kekam meyasa kike haka? Haba! Su talakawan ba mutane bane?."
   "Mutane ne amma..."
   "Amma what!?."
 Mummy tashi tayi ta haura sama cikin k'unk'uni, Tukunna shima yabi bayanta.
  B'angaren Mr-Fauzan kuwa, Yana shiga bedroom d'inshi ya cire kayan  jikin shi ' ya bari daga shi sai boxer ya fad'a bathroom domin yin wanka.
  Mr-Fauzan yana jikin wanka ne ' maganganun daya fad'awa Safna sukaita fad'o mashi a rai, Nan tausayin ta ya kamashi ' sam yasan cewa bai kyauta. 
   "She's hurt! She is really hurt."
  Abunda ya dunga furtawa kenan harya gama wanka, Sannan yayo alwala ya fito.
   Mr-Fauzan wardrobe d'inshi ya bud'e ya ciro jallabiya ash color ya sanya, Sannan ya fara sallar isha'i.
  Bayan idarwarsa ne ' ya fito daga d'aki ya nufi kitchen ya had'a Coffee ya koma bedroom d'insa.
  Mr-Fauzan a bakin gado ya zauna ' ya shanye coffee d'in tass, Sannan ya haye gado tare da kamo pillow ya rungume.
   "Is like I miss something!."
 Ya fad'a yana sauke ajiyar zuciya, Nan bacci yayi awon gaba dashi.

 


 

 

 
_we don't just entertain and educated, But we also touch the hearts of the readers_

*Follow me on wattpad @Seemaluv1**....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_UNIQUE WRITERS ASSOCIATION_*® ```Written```By*_Seemaluv_*https://www.facebook.com/groups/1649808818646464/*_@I Dedicated This Page To My Love Ones, Thank You For Support And Cares..._**38-39**_Washe gari_**AROUND 8:00AM*Mr-Fauzan ya tashi bacci, Bathroom ya shige yayi taking bath d'inshi gamida d'auro alwala sannan ya fito.Mr-Fauzan shinfid'a praying mat yayi ' yayi sallarsa, Bayan ya idar ne ya tashi ya shirya cikin black suite da takalmin shi black built sannan Mr-Fauzan ya dawo gaban mirror ya tsaya.Fauzper perfume ya fesa kamar kullun sannan ya d'auki wayarshi ya rik'e.Mr-Fauzan parlor ya fito ya iske Mummy da Daddy zaune a dinning tareda Khairat suna breakfast.Mr-Fauzan k'arasawa wajen yayi yayi joining d'insu, Nan ya gaishesu suka amsa sannan Daddy yace."Son kenan! Harka shirya kenan.""Yes Dad."Mr-Fauzan ya fad'a tare da tsiyaya tea a cup."Fauzan?."Cewar Mummy.Mr-Fauzan d'ago kai yayi ya kalleta with cares tare da cewa."Na'am Mummy.""Fauzan karka kawomin dangin talakawa am repeating myself."Mr-Fauzan aje cup d'in hannun shi yayi zaiyi magana Daddy ya dakatar dashi da cewa."Haba! Meyasa kikeyin haka? Why? Shi talakan ba Allah ne yayi shiba?.""Ainasan Allah ne yayi shi but ni kawai banaso, Akanme?."Mummy ta fad'i haka."Wow, Za'aje ganin auntyn mune? Daddy zan biku."Cewar Khairat."Yes, Tare dake ya dace aje ai ' ki gano min kalarta."Umma ta fad'i haka.Mr-Fauzan ne yayi saurin shiga maganar da cewa."No ' no need, Karma kisa ran zaki bimu, Besides ba school zaki tafi ba?."Khairat zunb'uro baki tayi tare da cewa."Ai wannan ba problem bane.""Na dai fad'a miki bazaki bimu ba, Hole I make myself clear."Mr-Fauzan ya fad'i haka tare da mik'ewa tsaye gami da cewa."Daddy bara in jira ka cikin motor.""Son, Harka gama breakfast d'in kenan?.""Yes Dad, I just lost my appetite that is it."Ok kawai Daddy yace sannan Mr-Fauzan ya juya ya fita."Haba! Why are you doing this iye? Ki bar fad'in irin wad'an nan magan maganun gaban su fa am warning you."Daddy ya fad'i haka."A'a allow me, Kuma idan har bai kawo min ita na gani ba ' to bazan tab'a karb'ar ta a matsayin suruku ba Alhaji."Daddy girgiza kai kawai yayi gami da cewa."Duk ma haka bata taso ba, Bara muje mu dawo."Mr-Fauzan yana fita direct ya nufi wajen mota, Mr-Fauzan key yasa a jikin motar k'irar Mercedes yabud'e tukunna ya shiga driver seat ya zauna.Mr-Fauzan dialing number d'in Hafiz yayi, Ringing d'aya Hafiz ya d'aga wayar."Ya! Babban mutum."Cewar Hafiz."Hafiz do you know what? Yanzu zamuje Private Hospital Girmi nida Dad fa.""Kai! Aboki da sauri sauri haka? Kanason yarinyar nan fa.""Oh come on! I just wanted to help her kawai, Me zanyi da k'azama irin ta? Kaima kasan she's not my type."'Yar dariya Hafiz yayi gami da cewa."Hm! Kada dai reshe ya juye da mujiya, Fauzan ka rik'a sassauci fa.""Don't change my mode, I will hang up now ' we will talk later."Abinda Mr-Fauzan yace kenan ya kashe wayar shi, Daddy ne ya bud'e motar ya shiga front seat ya zauna sannan ya rufe."Let me just assign driver to drive us."Daddy harya bud'e motar zai kira driver Mr-Fauzan yace."No Dad, Bara nayi driving d'in kawai."Ok kawai Daddy yace tukunna Mr-Fauzan ya tada motar gate man yayi hanzarin bud'e gate, Mr-Fauzan yaja motar suka nufi Private Hospital Girmi.B'angaren su Safna kuwa tunda ta tashi daga bacci tayi sallah sannan tayi wanka.Safna saida ta gama kintsa Umma tukunna Rumaisada Anisa suka shirya.Safna fita tayi daga cikin hospital d'in ta tsaya bakin titi tasiyo musu kunun gyad'a, Sannan ta dawo cikin hospital suka karya.Bayan sun karya ne Safna ta tashi tare da sanya hijab d'inta gami da cewa."Umma, Zanje in d'auko muku kayan da zaku cenja ke dasu Rumaisa, Daga nan nima incenja."To Umma tace, Safna har ta juya zata fita ward d'in Umma ta tsaida ita da cewa."Kud'in wajen ki zasu isheki ne?.""Eh Umma zasu isa har su rage."Umma d'aga kai tayi alaman gamsuwa sannan Safna ta juya ta fice.Safna a bakin titi ta tsaya ta tari mai keke-napep ta shiga ta wuce.Bayan wucewar tane Mr-Fauzan da Daddy suka iso cikin hospital d'in.Mr-Fauzan parking yayi a gefe tukunna suka fito daga motar, Mr-Fauzan jagaba yayiwa Daddy zuwa ward d'inda Umma take.Sallama sukayi sannan suka shiga ciki, Umma ganinsune yasa ta tashi zaune suka gaisa.Rumaisa da Anisa gaishesu sukayi Mr-Fauzan ya amsa a yatsine."Ke tashi ki shifid'a mashi tabarma ya zauna mana."Cewar Umma."A'a tama barshi, Am okay here."Mr-Fauzan ya fad'i haka cike da nuna kyamata.Daddy gyaran murya yayi ' yayi introducing kanshi ma Umma, Sannan ya fad'a mata dalilin zuwanshi.Umma nuna farin ciki tayi matuk'a tare da yima Daddy godiya."Kinsan halin yaran yanzu, So shiyasa mukeson ayi bikin nan da wuri."Cewar Daddy."A'a ba damuwa, Wannan ba wani abu bane ai."Umma ta fad'i haka."To mu ta fanninmu bamu son auren ya wuce nan danext week wato nan da wani sati kenan."Umma aminta tayi da abinda mahaifin Mr-Fauzan ya fad'a, Domin ita duk ta k'osa taga auren Safna.Umma kwatance tayiwa Daddy, Inda dangin uban suSafna suke, Domin kuwa sune zasu gindaya yadda sadakin zai kasance.Daddy nuna gamsuwa yayi sannan ya tashi gamida ciro bandir d'in duba d'aya ya aje ma Umma saman gadon da take zaune."Ga wannan.""Alhaji harda d'awainiya haka?.""Bakomai."Cewar Daddy.Nan sukayi sallama Daddy da Mr-Fauzan suka bar ward d'in.Bayan sun fito cikin hospital d'inne Daddy ya tsaida Mr-Fauzan da cewa."Fauzan, Amma ya abun nan zai kasance haka?.""Daddy meke nan?.""Lafiyar ita mahaifiyar yarinyar nan, Menene? Me take buk'ata ne?.""Never mind Dad, Na riga na d'auki nauyin komai a hannu na' Bayan aure za'ayi mata aiki."Ok Daddy yace sannan suka k'arasa wajen mota, Shiga Daddy yayi tukunna Mr-Fauzan ya zagaya ya shiga ya tada motar suka nufi unguwan da dangin mahaifin su Safna suke.B'angaren su Aleeza, Zaune take a parlor da bucket of warm water a gabanta Hajia na gaggasa mata inda yayi mata tsami Hafiz na gefe tare da laptop yana dannawa bisa cinyarsa."Auta ya kamata kiyi taka tsantsan fa! Wannan yawon banzan ki rage shi."Hajia ta fad'i haka tana dannawa Aleeza goshinta dad'an k'aramin towel.Wayar Aleeza ce ta fara ringing alaman kira, Hakan yasa ta d'an juya ta fuskanci wayar.Wata new number ce wacce batasan da ita ba, Hakan yasa tayi ignoring call d'in.Aleeza k'ara ta saki sakamakon Hajia ta tab'a mata inda ke mata ciwo sosai."Hajia a kwai zafi fa."Aleeza tayi maganar a shagwab'e.Suna cikin haka ne kira ya sake shigowa cikin wayarAleeza.Aleeza picking call d'in tayi gami da tashi ta wuce d'aki.Bayan ta zauna saman gado ne tace."Aleeza speaking.""It's Dr Khalil Muhammad.""Oh!."Aleeza ta furta."Are you surprise?.""Surprise of what?.""Nothing, Well ' yaya jikin naki? Ko sai nazo?."Yayi maganar cikin zolaya."Naji sauk'i ma, Ana d'an min warming d'in wajen ciwon ne ma ka kira.""Ok then, Aje acigaba da warming up, Inason ki kasance cikin lafiya I will call later.""Ok thanks for your cares."Nan Aleeza tayi hanging up d'in kiran, Barin phone d'in tayi saman gado ta koma parlor ta zauna Hajia ta cigaba da duba lafiyar ta.B'angaren su Mr-Fauzan, Cikin unguwan da aka yi musu kwatance suka shiga.Tambaya sukayi aka kaisu har gidan, Bayan sun shiga zauren gidanne sukayi sallama wata mata wacce ta manyanta ta fito sanye da zani ta lullub'e jikinta.Bayan sun gaisa ne suka sake tabbatarwa ko nanne gidan da Mahaifiyat Safna tayi musu kwatance, Matar amsawa tayi da cewa."Eh k'warai nan ne, Amma Allah yasa dai lafiya."Nan Mr-Fauzan ya fad'a mata dalilin zuwansu, Jin haka yasa ta koma cikin gida ta d'auko tabarma ta shinfid'a musu.Mr-Fauzan a zuciyar sa yace."Oh God! Tabarma tabarma dai, Meyasa sukeson tabarma? So irritating."Abinda Mr-Fauzan ya fad'a cikin ranshi kenan, Ganin Daddy ya zauna ne yasa shima ya zauna tare da tank'washe k'afa.Nan suka tsaida magana Daddy ya ciro 50 thousandya ajiye kamar yadda matar nan ta ambata a matsayin sadakin Safna.Ganin hakan yasa ta tashi ta shiga cikin gida ta kira sauran dangi dukda cewar basu da wani yawa.Dukkansu sanya albarka sukayi, Ciki kuwa harda masu bak'in ciki.Nan aka tsaida gamsas-shiyar magana akan next week ne za'a d'aura aure a cikin babban masallacin juma'a.Daddy da Mr-Fauzan sallama suka yiwa mutanen wajen sannan suka juya suka nufi wajen mota.Bayan sun shiga mota ne Mr-Fauzan yayi ajiyar zuciya cike da nuna gajiya, Sannan ya tada motar suka bar wajen.Mr-Fauzan yana cikin driving ne kiran Sir-Kamal ya shigo ta wayar shi, Kasancewar akwai Bluetooth ear set a kunnen shi, Hakan yasa shi amsa calling d'in kai tsaye."Hello Sir.""Yes Kamal, Any problem?.""Sir, Akwai meeting d'in da zakayi attending around 12:00pm."Sir-Kamal ya fad'i haka yana cikin office d'in shi zaune.Mr-Fauzan wristwatch d'in hannun sa ya duba ganinit's almost 12 ne yasa shi cewa."And kuma sai yanzu ne zaka fad'amin ina da meeting da zanyi attending?.""Am sorry Sir, Abubuwa ne suka shigemin gaba.""I can't attend that meeting, Just cancel it."Ya fad'i haka yana driving."But Sir, You have to ' because it's very important.""Kamal you had what I said, Right?.""Yes Sir, And then wasu sunzo suma kai suke jira.""Kamal, Just handle everything, I need to rest today."OK Sir-Kamal yace sannan Mr-Fauzan ya danna Bluetooth ear set yayi ending call d'in.Daddy ne ya kalli Mr-Fauzan yace."Son, You have to go and check what's going on ' on that company.""Okay Dad, But ba wani abu bane fa, Just lazy P.A gareni baya son yin abinda ya kamata."Mr-Fauzan ya fad'i haka yana driving.B'angaren Safna kuwa har taje gida ta dawo cikin hospital d'in.Umma fad'awa Safna tayi yadda sukayi da mahaifin Mr-Fauzan.Ganin Safna bata nuna jin dad'in ta bane, Yasa Umma cewa."Safna?."Safna d'ago kai tayi ta kalli Umma kamar zatayi kuka."Na'am Umma."" 'Yan nan idan har akwai wata matsala wanda bansan da itaba ki fad'amun tunda wuri, Farin cikin ku kawai nakeso na gani."Safna mik'ewa tsaye tayi tare da juya baya tace."A'a Umma babu wata matsala, Ni kaina farin cikinkinake buk'ata, Don duk na k'osa ki sami lafiya Umma.Nan hawaye suka zubo Safna a fuska tayi sauri tasa hannu ta share."Karku damu idan harni mai rayuwa ce ' zan rayu, Kuma bakiji likita yace za'aimun aiki nan da sati uku ba?."Safna juyowa tayi ta kalli Umma gami da d'aga matakai alaman Eh, Sannan ta maida kallon ta kan Anisah dake kwance saman tabarma tana bacci.39
*40-41**AROUND 2:00PM*Bayan Mr-Fauzan ya ajiye Daddy wajen business d'in shine ya kama hanyar komawa gida.Mr-Fauzan a bakin gate ya tsaya gate man ya bud'e mashi sannan ya shigo.Bayan yayi parking ne ya bud'e motar ya fito ya k'arasa ciki, Mr-Fauzan koda ya shiga parlor a zaune ya iske Mummy rik'e da remote a hannunta sanye da medicated glass a idonta.Mr-Fauzan sallama yayi tukunna ya k'arasa cikin harabar parlor.Bayan ya zauna ne Mummy ta kalle shi tace."Son?.""Mom."Ya furta a gajiye."Inaso gobe ka kawo min ita domin mu gaisa, Inasonnaga surukata.""To Allah ya kaimu."Ameen Mummy tace, Sannan Mr-Fauzan ya tashi yawuce part d'in shi.Bayan ya shiga bedroom d'in shi ne ya cire suit d'in jikin shi tare da takalmin shi built, Sannan ya haye gado ya kwanta.Mr-Fauzan janyo wayar shi yayi ' yayi dialing number d'in Sir-Kamal, Ringing d'aya zuwa biyu yayireceiving."Kaje GIRMI hospital kuwa yau?."Cewar Mr-Fauzan."No Sir.""OK then, Kaje yanzu! ka siya musu abinda zasuci, I will transfer 10k into your account now!."Dogon numfashi Sir-Kamal yaja, Sannan yace."OK."Nan Mr-Fauzan yayi ending call d'in.Mr-Fauzan transfer yayiwa Sir-Kamal through mobile bank.Nan ya ajiye wayar saman side drower ya koma ya kwanta tare da rungume pillow.B'angaren Sir-Kamal, Fitowa yayi daga company ya nufi inda yayi parking motar shi cikin hanzari.Shiga yayi gami da yiwa motar key ' yaja ya nufi restaurant.Sir-Kamal abinci ya siyowa su Safna, Sannan ya shiga motar shi ya nufi Girmi-Hospital.Bayan isarsa cikin hospital d'in ne ya fito daga motarcikin sauri rik'e da ledar takeaways a hannun shi.Cikin hospital d'in ya shiga ya nufi ward d'in da Umma take.Sir-Kamal shiga yayi cike da sallama a bakin shi.Safna ce tayi saurin mik'ewa tsaye tare da amsa sallamar, Nan su Rumaisa suka gaishe shi ya amsa, Sannan ya mik'awa Safna sak'on da aka bashi.Sir-Kamal maida kallon shi yayi akan Umma yaga bacci takeyi."Yaya jikin Umma?.""Da sauk'i."Cewar Safna."Am.. Abinci ne a ciki inji Oga."Sir-Kamal ya fad'i haka fuskar shi babu annuri atattare da ita.Safna karb'a tayi tare da cewa."Gashima har na siyo mana abinci munci ' wannan sai dai anjima da yamma."Sir-Kamal juyawa yayi zai wuce, Safna tayi saurin tsaida shi da cewa."Kamal?."Sir-Kamal tsayawa yayi cak ba tare daya juyo ya kalleta ba yace."Safna.""Kamal, Zan iya magana da kai don Allah?.""Eh."Ya fad'a a tak'aice, Hakan yasa Safna ta mik'awa Rumaisa ledar takeaways d'in, Sannan tabi bayan Sir-Kamal suka fito bakin hospital d'in."Am...Kamal...,Nasan zaka d'auke ni a matsayin butulu wacce tak'i karb'ar soyayyar ka ko?."Safna ta fad'i haka tana kallon gefen fuskar shi kamar zatayi kuka.Sir-kamal smiling d'in k'arfin hali yayiwa Safna gamida cewa."Ko kad'an, Ai nasan kina da dalilin yin hakan.""Kamal, Yin hakan shine alkairi a gareni, Banaso na amshi soyayyar ka daga k'arshe kaga kamar na yaudare ka."Na fahimce ki Safna, Amma inaso ki sani bazan daina sonki a cikin zuciya ta ba."Safna girgiza kai tayi tare da sunkuyar da kanta k'asa idanuwan tane suka cicciko da kwalla."Kamal, Ka cewa Ogan ka nagode ' kuma don Allah inaso ka cire zancen sona a ranka, Mu zama abokai."Safna na gama fad'in haka ta juya ta koma ciki, Sir-kamal right hand d'in shi ya dunk'ule zuciyar shi na mashi k'una.Sir-Kamal wajen motar ya nufa cikin hanzari ya tadamotar ya bar hospital d'in.Sir-Kamal gida ya wuce direct, Bayan yayi parking motar shi a compound ne ya fito ya shige cikin gida.Kasancewar bai sami kowa a parlor bane yasa shi shigewa bedroom d'in shi kai tsaye.Sir-Kamal kayan jikin shi ya cire ya ya shige bathroom, Koda ya shiga shower ya kunna ya tsaya tsakiya ruwa na ratsa jikin shi.Takaicin maganganun Safna kawai ke fad'o mashi a rai."Meyasa baza kice kina sona ba? Why? Didn't I deserve to be loved?."Abinda Sir-Kamal ya rik'a fad'a a cikin zuciyar shi kenan, Nan ya rufe shower d'in gami da d'aura towel a k'ugunshi tukunna ya fito.Sir-Kamal koda ya fito k'ana nan kaya ya ciro ya sanya sannan ya fito daga d'akin.Ta parlor ya biyo zai fita suka had'e da Ammi tana shigowa cikin parlon."Kamal?.""Na'am Ammi.""Ina zuwa kuma ' ka dawo ko hutawa baka yi ba?."Ammi ta fad'i haka tare da zaunawa saman kujera."So nake inje ziyarar wani friend d'ina.""Kamal dawo ka zauna na tambaye ka."Jin hakan yasa Sir-Kamal dawowa harabar parlor ya zauna a k'asan kujerar da Ammi ke zaune."Ammi gani.""Kamal, Kana cikin damuwa ko?."Cewar Ammi.Sir-Kamal 'yar dariyar k'arfin hali yayi yace."Ammi kenan, Ni banda wata damuwa please karki d'aga hankalin ki.""Ka tabbata?.""Eh Ammi."Sir-Kamal ya fad'i haka tare da duba wristwatch d'in hannun shi yace."Ammi, Bara inje."To Ammi tace sannan Sir-Kamal ya tashi ya fice.*** *** *** *** *** *** *** *** ****AROUND 4:00PM*Mr-Fauzan ya tashi yayi daga baccin da yakeyi gamida sakin doguwar mik'a tare da yin salati.Mr-Fauzan d'aga kanshi yayi ya kalli a gogon d'akin,Yaga *4:00pm*."Oh God!."Ya furta, Sannan ya sauko daga saman gadon gami da cire wandon suit d'in da ke jikin shi ya dawo dagashi sai singlet.Mr-Fauzan d'aura towel yayi a jikin shi sannan ya shige bathroom don yin wanka.Bayan ya fito ne ya shirya cikin jeans and white shirt mai tambarin polo.Mr-Fauzan wristwatch ya d'auko ya sanya a right hand d'in shi mai k'irar gold sannan ya sanya sun glass.Mr-Fauzan takalmin sa ya sanya ' gami da d'aukan car key.Fitowa yayi daga d'akin shi ya shigo cikin parlor zai fita ya had'e da Khairat tana shigowa da alaman daga school ta dawo.Mr-Fauzan harya kama hanyar fita Khairat ta tsaida shi da cewa."Yaya Fauzan?."Nan Mr-Fauzan ya juyo ya kalle ta tare da cewa."Any problem?."Cikin shagwab'a Khairat tace."Bro, Kud'ina ne suka kusa k'arewa.""So?.""Yaya Fauzan, Kad'an bani one hundred thousand nad'an si..."Bata kaiga k'arasa maganar ba Mr-Fauzan ya tsaidaita da cewa."Naji, Basai kinmin dogon surutu ba ' kiyimin sending account number d'inki, I will send more than that."Abinda Mr-Fauzan ya fad'a kenan ya juya ya fice, Nan Khairat ta k'arasa d'akin ta cike da murna.Mr-Fauzan wajen motar shi yaje ya bud'e ya shiga ya zauna, Sauke ajiyar zuciya yayi yace."What am I going to do now? Nasan halin Mom, Ana iya samun matsala idan na kawo mata wannan yarinyar a yanayin da take."Mr-Fauzan jinginar da kanshi yayi a jikin seat d'in mota, A zuciyar shi yace."Or should I take her out for shopping? To idan tak'i yarda fa? Oh no!...."Mr-Fauzan d'an k'aramin tsuki yaja, Sannan ya tada motar shi tare da cewa."Dolenta ma ta yarda ' Whether she like it or not."Abinda ya fad'a cikin ranshi kenan, Gate man ya bud'e mashi gate ya fice.Mr-Fauzan GIRMI hospital ya nufa, Bayan ya isa cikin hospital d'inne yayi parking motar shi sannan ya fito.Mr-Fauzan ciki ya k'arasa, Nan yaga wata attender tana goge goge.Mr-Fauzan aika attender d'in yayi taje ta kira mashi Safna gami da fad'a mata ward d'in da suke.Ba'a wani wasting time ba attender d'in ta dawo wajen tare da Safna.Safna ganin shine yasa mode d'in ta ya cenja, K'arasawa wajen shi tayi ta tsaya tare da sunkuyar da kanta.Jin shurun yayi yawa ne yasa ta d'ago kai ta kalle shi taga wayar shi kawai yake dannawa."Kazo lafiya?."Cewar Safna.Mr-Fauzan maida kallon shi yayi akan ta yace."Lafiya.. Akwai maganar da nakeso muyi but bazan iya yinta anan ba."Safna kwalalo mashi Ido tayi tace."To sai a ina kenan?.""Ki biyoni cikin mota na."Abinda Mr-Fauzan ya fad'a kenan ya juya ya wuce wajen motar shi, Mr-Fauzan bud'e motar yayi ya shige Safna na tsaye tana kallon shi."In biyo ka cikin mota kuma?."Safna girgiza kai kawai tayi cike da takaice ta nufi wajen motar tashi.Safna tsaye tayi a wajen tana tunanin ta shiga ne ko karta shiga?.Tana cikin haka ne Mr-Fauzan ya danna mata hone, Hakan yasa ta razana tayi saurin bud'e motar ta shiga."Wace magana za muyi?, Don Allah kar kace ka cenja shawara ' Umma na tana buk'atar taimako."Cewar Safna.Mr-Fauzan tab'e pink lips d'in shi yayi gami da sakinshu'umin smiling."Inaso in kaiki wajen Mom d'ina ta ganki."Nan Safna ta zaro ido tare da rufe bakin ta cike da kunya, Hakan yasa Mr-Fauzan ya tsaya yana kallon ta nad'an lokaci tukunna yace."And I can't take you to her ' cikin k'azanta, The way you are now."Nan take Safna ta dubi jikin ta, Girgiza kai kawai tayicike da tausayawa kanta tace."To ko zaka bari naje gida na cenja kaya?.""No need of that, Zan siya miki kayan sawa ina kud'i kuma na tarasu I got a lot of money, Babu abinda zaimin wahalar samu a duniya."Safna, Jin abin ya fad'a yasa ta fahimci inda ya dosa."Ka barshi ba saika siyamun ba, Inada kayan sawa."Ta fad'a a tak'aice tare da calming hands d'in ta tanakallon waje.Mr-Fauzan juyowa yayi ranshi a b'ace ya kalle ta, Tare da cewa"Ke..? Harni zance zan siya miki abu kice bakyaso?.""Kayi hak'uri, Kamar yadda kake k'yamatar talaka haka nima nake k'yamatar duk wani abinda zai fito daga wajen ka, Taimakon da zakaiwa Umma na kad'ai ya isa."Safna ta fad'i haka ba tare da ta kalle shi ba.Mr-Fauzan cije pink lips d'inshi yayi ' yayiwa motar key, Da sauri Safna ta juyo ta kalle shi.Mr-Fauzan figar motar yayi a 360 suka bar cikin hospital d'in."Ina zaka kaini?."Ta fad'i haka idanun ta cike da k'walla.Mr-Fauzan shiru yayi ya kyaleta gudu kawai ya tafkawa."Meyasa ka kasance mugu a gareni?."Ta fad'i haka cikin shauk'i na kuka, Mr-Fauzan kuwako a jikin shi driving d'in shi kawai ya keyi."Na tsane ka Fauzan Na tsane ka! Ka maida ni inda ka d'auko ni."Mr-Fauzan dogon burki yaja ya tsaya.*_FACEBOOK@SEEMALUV HAUSA NOVELS_*
*42-43*Mr-Fauzan juyowa yayi ya kalli Safna tare da cewa."Muje.""Ni babu inda zanje, Don Allah ka maida ni inda ka d'auko ni.""I don't want to argue with you Safna, Don't forget akwai yarjejeniya tsakanin mu, Kar kuma ki manta da Mahaifiyar ki dake hospital ba lafiya."Safna sunkuyar da kanta tayi tana nazari, Sannan Mr-Fauzan ya cigaba da cewa."Sabida haka ya zama dole kibi abinda nace, Because I can change my mind at any time.""Saboda kana azzalumi? Meyasa ku masu kud'i bakwayin abu tsakani da Allah?."Safna maganar cikin rawar murya."Daki aure ni Mahaifiyar ki ta warke, Da kik'i amincewa kuma ta mutu wane kika zab'a?."Mr-Fauzan ya fad'i haka ba tare da ya kalle ta ba."Wai kai wane irin azzalumi ne? Wane irin mugu ne kai? Meyasa bakwa taimako tsakani da Allah?.""Why? I thought ke kina da tarbiyyar da zaki iya sadaukawar Mahaifiyar ki farin cikin ki."Mr-Fauzan ya fad'i haka tare da jan tsuki, Sannan yak'ara da cewa."Let me just call the doctor ' na fad'a mashi cewa nina cire hannuna game da mahaifiyar ki."Ya fad'a tare da d'aga wayar shi zaiyi dialing numberd'in Doctor, Safna saurin dakatar dashi tayi da cewa."A'a Don Allah... Kar kayi haka...Kayi hak'uri naji na amince zanbi duk abinda tace."Ta fad'i haka hawaye na gangaro mata saman fuskar.Mr-Fauzan handkerchief ya mik'a ma Safna domin ta share hawayen dake fuskar ta, Haka ta karb'a ta share cike da takaici."Kuma as from today ' inaso ki adana hawayen ki, Because am not bullying you."Abinda Mr-Fauzan ya fad'a kenan ya bud'e mota ya fita.Safna itama budewa tayi ta fito, Wani babban shop suka shiga wanda ya k'unshi komai da komai.Bayan shigar sune Mr-Fauzan ya nufi b'angaren Abayas Safna na biye dashi a baya.Safna tsayawa tayi wajen wata Abaya mai kyau, Ganin haka yasa Mr-Fauzan tsayawa ya duba kud'inAbayan da Safna ke kallo."So cheap."Ya fad'a gami da kamo hannun ta yaja ta suka k'arasa ciki.Mr-Fauzan bai tsaya ko ina ba sai a wajen wasu Abayas masu kyau wanda daka gansu kaga kud'i.Safna k'ok'arin raba hannun ta take da nashi amma ta kasa.Mr-Fauzan kuwa Abayas kawai yake jida, Yana sakawa cikin basket.Suna cikin hakanne Suhailah ta shigo cikin shop d'in,Itama wajen Abayas d'in taje tana zab'ar wanda yai mata.Suhaila hango Mr-Fauzan tayi rik'e da hannun Safnayasa ta aje basket d'in nan wajen ta nufi inda yake.Mr-Fauzan kuwa tunda suka had'a ido da Suhailah yasa ke rik'e hannun Safna sosai."Fauzan?."Suhailah ta ambaci sunan shi cikin mamaki.Mr-Fauzan juyowa yayi ya kalle ta, Safna kuwa k'ok'arin ta shine taga ta raba hannun ta da nashi."Who is she?."Tayi tambayar tana yi mashi nuni da Safna."She's my wife to be."Ya furta with proud.Suhailah zaro ido tayi gami da k'arewa Safna kallo, Ganin haka yasa Safna sunkuyar da kai.Nan Suhailah ta matsa kusa da Safna tare da fincikar hijab d'in gami da cewa."Wannan abun ce kakeso ka aura Fauzan? Dame ta fini?."Mr-Fauzan kab'ewa Suhailah hannu yayi tare da yi mata kasheda yace."Don't try something stupid here Suhailah, And i advise you to leave us alone...!!' kafin ki raina kanki awajen nan!.""Fauzan abinda zakace kenan? Ni kake fad'awa haka akan wannan k'azamar?."Suhailah ta fad'i haka cike da tsirawa Safna hannu.Mr-Fauzan tsuki yaja suka bar wajen."What! Ni Fauzan zaima haka? Ni zai yaudara? Ni zai ciwa fuska sabida wannan abin? Lallai zan nuna mishi kad'an daga cikin aikin Suhailah."Abinda Suhailah ta fad'a kenan tare da karkad'a kanta ta koma wajen inda take zab'an Abayas.A wajen mai karb'ar kud'i Mr-Fauzan ya tsaya, Ciro wallet d'in shi yayi ya zari ATM card d'in shi ya mika musu domin su cire kud'in su.Tunda suka tsaya wajen Safna ke kallon Mr-Fauzan jikin ta a sanyaye."Sona kake da gaske ko kuwa?."Ta fad'i haka cikin ranta.Tana cikin wannan tunanin ne taji ya jata sun nufi wajen k'ofar fita.Fita sukayi daga cikin shop d'in, Mr-Fauzan saida suka isa wajen mota tukunna ya sakar mata hannu.Key ya sanya ya bud'e motar, Sannan ya saka kayancikin bode ya koma cikin mota ya zauna, Tukunna itama ta bud'e front seat ta shiga ta zauna.Mr-Fauzan tada motar yayi suka nufi hospital dominmaida ta.Mr-Fauzan driving d'in shi kawai yakeyi Safna na satar kallon shi.Tabbas Mr-Fauzan kyakkyawa ne kuma ya cancanciduk wata mace ta kalle shi ta yaba.Cikin 'yan mintoci suka isa cikin hospital d'in, Bayan yayi parking ne ya danna wani waje cikin motar hakan yasa bode ya bud'e."Kije ki cire kayan ki."Ya fad'a cike da tak'ama ba tare da ya kalle ta ba."Na gode."Safna ta fad'a, Sannan ta bud'e motar ta fito.Safna wajen bode ta zagaya ta d'aga ' ta d'auki ledarkayan, Sannan ta rufe bode d'in.Nan Mr-Fauzan yaja motarshi ya wuce.Safna koda ta shiga cikin hospital d'in cikin ward ta wuce kai tsaye.'Yan uwan su Umma ta iske a ciki hakan yasa gabanta ya fad'i.Da sauri Safna ta k'arasa ciki, Ganin yadda su Rumaisa ke kuka ne yasa nan take k'afafun Safna suka fara rawa.Anisah ce ta taso ta rungume Safna cikin kuka tace."Aunty Safna, Likita yace wai Umma ta rasu..."Raras gaban Safna ya sake fad'uwa, Nan take idanuwanta suka ciko da hawaye.Safna maida kallon ta tayi ga mutanen da ke tsaye a wajen, Ganin yadda suke girgiza kai alaman tausayawa ne yasa Safna ta matsa wajen gadon Umma.Safna ganin an rufe Umma da farin k'yalle ne yasa tazubewa k'asa, Cikin kuka take cewa."Umma don Allah ki tashi...karki mana haka... Ummaki tashi don Allah."Safna ta k'arashe maganar cikin kuka.Rumaisa tasowa tayi tazo kusa da Safna ta tsaya gami da dafa kafad'an ta.Hakan yasa Safna d'ago kai ta kalle ta."Rumaisa meyafaru da Umma haka?.".Tayi maganar cikin disashewar murya.Rumaisa share hawayen da ke mata zarya tayi tace."Lokacin da kika fitane ciwon ta ya tashi harta kaiga yin kashin jini, Shine na fita na kira likita, Koda yazo ya duba ta sai kawai naga ya rufe mata fuska yace in kira 'yan uwanmu, Shine na d'auki kud'i naje na kira su Goggo mariya."Da sauri Safna ta rungume Rumaisa cikin matsanancin kuka.Goggo Mariya ce ta taso tazo inda Safna take."Kiyi hak'uri Safna ki kuma d'auki k'addara."Cewar Goggo Mariya.Goggo Mariya k'anwa ce ga Umma.Wani ne ya shigo ya cikin ward d'in tare a cewa."Ga motar cen an kawo."Abinda ya fad'a kenan ya shigo ciki tare da Nurses guda biyu suka d'auki gawar Umma suka d'aura ta atrolley chair, Suka nufi wajen mota da ita.Safna dasu Rumaisa kuka kawai sukeyi har suka shiga cikin mota, Aka sanya gawar Umma a baya.'Yan uwan Umma suma shiga suka yi cikin motar, Kasancewar boss ce motar shiyasa ta d'auke su gaba d'aya..*_@Dedicated to SEEMALUV NOVELS GROUP & B'OYAYYEN AL'AMARI FANS GROUP,,,,,,,,,Masoya na ina ganin sak'on nin ku ' Seemaluv really appreciate it._**44-45*Koda su Safna suka isa gida kafin kace kwabo gidanya cika da mutane, K'ofar gidan kuwa cike yake da maza.Bayan anyiwa gawar wanka ne, Safna tana ji tana gani aka d'auki gawar aka fita a ita domin yi mata sallah, Daga nan akaita masaukin ta.“Wayyo Allah na shiga uku... Ni yanzu yazan kasance da k'annai na?.”Safna dake zaune cikin hijab ta fad'i haka cikin matsanancin kuka.Goggo Mariya ce, Ta taso tazo inda Safna take tace.“Haba Safna meyasa bazakiyi tawakkali ba? Meyasa? Karfa ki manta duk mai rai mamaci ne, Kuma ai Allah yana tare daku.”Haka duk mutanen dake wajen suka dunga lallashin Safna.*** *** *** *** *** *** *** *** *** ****AROUND 5:00PM*Bayan ankaita andawo ne, Mutane suka fara watsewa ya rage daga su Safna sai Goggo Mariya.“To Safna ki daiyi hak'uri kuma ki cigaba dayi mata addu'a kawai, Kuma kinga irin rayuwar da muke ciki ' yanzu tashi zakiyi da sana'a saboda ki samu ku kare mutuncin kanku.”Cewar Goggo Mariya.“Yanzu Goggo Mariya, Bazamu sami tallafi daga wajen ku ba kenan?.”Safna ta fad'i haka.Goggo Mariya ajiyar zuciya tayi tare da girgiza kai cike da nuna tausayawa tace.“Safna kenan! Yanzu wa kike ganin zai baku wani tallafi? Toh ni d'innan kinga nima ba wani hali gareniba ' sai mijina ya nemo ya kawo, Gani kuma da 'ya'ya ' kuma yanzu masu kud'in nan ba taimako sukeyi ba.”Safna wasu zafafan hawaye suke kwaranyo mata, Kallon Rumaisa tayi taga babu abinda takeyi sai kuka.Nan ta maida kallon ta kan Anisah ta ganta rakub'e jikin bango tayi shuru.“Bakomai Goggo Mariya, Nagode sosai da shawararki kuma insha Allah zan nemi aikin yi.”Nan Goggo Mariya ta tashi sukayi sallama sannan ta wuce.Bayan anya sallar isha'i ne, Safna da su Rumaisa suna zaune a tsakar gida wani yaro ya shigo tare da yin sallama.Bayan an amsa masa ne yace.“Wai ance ana sallama da Safna.”“Kace gata nan zuwa.”Cewar Safna.Yaron juya wa yayi ya fita, Sannan Safna ta tashi ta fita domin duba wanda ke kiran ta.Safna koda ta fita Ganin Sir-Kamal tayi tsaye, Hakanyasa ta k'arasa inda yake jingine jikin motarshi.Bayan sun gaisa ne Sir-Kamal yace.“Safna naje hospital d'in akace min an sallame ku, To yaya jikin Mahaifiyar taki? Anyi mata aikin ne?.”Safna d'ago kai tayi ta kalli Sir-Kamal tare da cewa.“Umma Allah yai mata rasuwa d'azu.”“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un...”Cewar Sir-Kamal.Shuru sukayi na d'an lokacin, Sannan Sir-Kamal ya lura da kukan da Safna keyi.“Kiyi hak'uri Safna, Allah ya gafarta mata Allah kumayasa hutun kenan.”“Amin na gode.”Ta fad'a da disash-shiyar murya.“To yanzu waye ke zaune daku?.”“Ba kowa.”“Toh... Insha Allah idan akayi sadakan uku, Zan dawo domin akwai maganar da nakeso muyi.”To Safna tace, Sannan Sir-Kamal ya bud'e mota ya ciro abincin da Mr-Fauzan ya umurce shi daya siya masu as usual.Sir-Kamal mik'awa Safna yayi ta amsa, Sannan yace.“Inji Mr-Fauzan, Oga na kenan ' yace inkawo muku wannan, Baima san da rasuwar ba shiyasa but zan fad'a mashi idan na koma.”Nan Safna ta mayar mashi ledar gami da cewa.“Ka mayar mashi da abincin shi, Domin bama buk'ata.”“Ha'a Safna meye dalilin yin hakan?.”“Kamal... Abubuwa da dama sun faru ba tare da saninka ba, Saboda haka kawai abarni inji da mutuwar rasuwar Umma na kad'ai ta ishe ni.”Ta fad'i haka gami da share hawayen ta.“Insha Allah Safna komai zaizo maki da sauk'i, Kuma as far as am alive ni zanyi maki komai, Yanzu kuna da abinda zaku ci ne?.”Kai Safna ta girgiza mashi alaman a'a, Tukunna yace.“To, Kiyi hak'uri ki ansa wannan kuci, Saboda kada ku kwanta da yunwa.”“Kada ka damu Kamal, Zan nema mana abinda zamu ci don akwai sauran kud'i a waje na.”OK kawai Sir-Kamal yace sannan ya maida ledar takeaways d'in cikin mota.Sir-Kamal dawo wa yayi ya tsaya tare da sanya hannun shi cikin aljihu ya ciro 10k ya mik'awa Safna gami da cewa.“Kiyi amfani da wannan, Kafin na sake dawo wa.”Nan Safna ta fashe da kuka, Cike da cewa.“ hak'uri, Amma ni kunyar ansan kud'in ka nakeyi yanzu, Sabida na kasa karb'ar soyayyar ka.”Murmushin takaici Sir-Kamal yayi tare da cewa.“Karki damu Safna, A yau koda ace ban furta miki kalmar so ba ' to zan cigaba da kasancewa inuwa a gareki.”Safna d'ago kai tayi ta kalle shi cikin shauk'in kuka da sautin shagwab'a tace.“Da gaske kakeyi?.”“Uhm.. Da gaske nake mana! Idan har kika bani dama.”“Na gode.”Ta fad'a tare da sunkuyar da kanta, Nan sukayi sallama Sir-Kamal ya shige motar shi yaja ya wuce sannan Safna ta shige gida.Bayan shigar ta gida ne ta iske har Anisah tayi bacci.“A'a Rumaisa tada Anisah, Babu wanda zaiyi bacci baici abinci ba.”Safna ta fad'i haka gami da cire hijab d'in jikin ta.Bayan Rumaisa ta tada Anisah ne Safna tace.“Indomie zaki je ki siyo mana dafaffa wajen mai shayin cen.”To Rumaisa tace sannan Safna ta cire d'ari biyar ta mik'a mata tace.“Kice uku zai dafa maki.”Kai Rumaisa ta d'aga alaman to, Sannan ta sanya hijab d'inta ta fita.B'angaren Sir-Kamal, Bayan ya koma gida ne yayi shirin bacci ya kwanta ya d'auki wayar shi yayi dialing number d'in Mr-Fauzan.Ringing tai tayi bai d'aga ba har sai da Sir-Kamal yayi four missed calls sannan Mr-Fauzan yayi receiving call d'in.“Good evening Sir.”“Evening, Any problem?.”“Well, Yes Sir, Mahaifiyar Safna ce Allah yayi mata rasuwa d'azu.”Mr-Fauzan a kwance yake amma jin haka yasa shi yin saurin tashi zaune.“What!! Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Why didn't you tell me earlier??.. Meyasa sai yanzu kake fad'amin?.”“Am sorry Sir, Nima bansani ba sai da naje kai musuabinda zasuci ne ake fad'amun an sallame su shine nabi ta gidan nasu.”“Ya salaam!...”Mr-Fauzan ya furta tare da dafe goshin shi.Mr-Fauzan ending call d'in yayi ya jefar da phone d'in saman gado, Ya fito yana kwala wa Mummy kira.“Mom! Dad!.”Mummy da Daddy kwance suke suna bacci, Jin yadda kiran yayi yawa ne yasa Mummy tayi firgigit ta farka.Parlor ta sauko cikin sauri tana cewa.“Son what's wrong? Meyafaru?.”Mr-Fauzan dafe kanshi yayi, Gami da cewa.“Mom, Yanzu ake fad'amin Mahaifiyar Safna ta rasu.”“Wacece Safna?.”“Ita ce wacce zan kawo miki ita gobe, Surukan ki Mom.”Mummy rufe baki tayi tare da girgiza kai alaman tausayawa.“Ya salaam!... Allah ya jik'anta.”Amin Mr-Fauzan yace gamida dafa saman kujera.“Shit!!.”Ya furta tare da bugun kujerar.“Calm down Son, Yanzu kaje ka kwanta gobe sai ayi mata ta'aziyya.”“I can't sleep at this time Mom... I can't, I know that Safna will never forgive me...”Mummy tsayawa tayi tana kallon shi cikin mamaki.“Meyasa? Me kai mata?.”Mr-Fauzan shuru yayi na d'an lokaci Sannan Mummy tace.“Kaje dai ka kwanta, Saboda abinda safiya batayi badare bazai yi shiba.”Mr-Fauzan juyawa yayi ya wuce part d'in shi, Mummy girgiza kai kawai tayi itama ta koma b'angaren su ta kwanta.Mr-Fauzan koda ya kwanta, D'aga kanshi yayi ya duba clock yaga *10:00pm*.“Huh! Lemme call Hafiz.”Abinda Mr-Fauzan ya fad'a kenan, Yayi dialing number en Hafiz.B'angaren Hafiz kuwa kwance yake a d'akin shi ya kwanta harya fara bacci wayar shi ta fara ringing.Jikin shi a mace ya tashi gami da d'aukar wayar ya duba yaga Mr-Fauzan me ke kiran shi.“At this time!!??.”Ya fad'i haka tare da picking call d'in.“Babban Mutum! Ya akayi ne?.”Cewar Hafiz.“Hafiz, Ba lafia ba fa!.”“What is the problem?.”“Wallahi Hafiz an yanka ta tashi.”Hafiz wata doguwar hamma ya saki gami da cewa.“What does that means?.”“Please idan ma zaka aje bacci agefe ka aje, Mahaifiyar Safna ce ta rasu yau.”Jin hakan yasa Hafiz ya saki salati, Sannan Mr-Fauzan yace.“Hafiz I don't think zan iya bacci seriously, Yarinyar nan tana iya cewa bazata yarda na aure ta ba ' nasan ta taurin kaine da ita, And she can even blameme for her mother's death!.”“Ai kaga abinda nake guje maka, Shiyasa tuntuni nakeso abi komai a hankali.”“Oh come on! Yanzu meye nayi wanda ba daidai ba a ciki? Kawai son nake na taimaka mata na aure ta that is it.”Mr-Fauzan ya fad'i haka a gadarance.“You fall for her didn't you?.”Hafiz yayi tambayar cike da zolaya.“Haba dai!...”“Oh har yanzu bazaka bada kaiba ko? Aboki kabi a hankali fa.”“Yanzu dai what's the solution?.”Cewar Mr-Fauzan.“Kawai ka bari sai gobe, We will find a way out.”OK Mr-Fauzan yace sannan suka yi sallama ya kashe wayar shi, Ya kwanta.Mr-Fauzan koda ya kwanta tunani iri iri kawai suke zuwa mashi a rai har bacci yayi awon gaba dashi.*FACEBOOK@SEEMALUV HAUSA NOVELS.44*46-47*Washe gari misalin k'arfe *7:00am* Mr-Fauzan ya tashi, Bathroom ya shiga yayi wanka tare da d'auro alwala sannan yayi sallah.Mr-Fauzan shiryawa yayi kamar yadda ya saba cikin suit sky blue colour, Komai nashi matching color ne.Mr-Fauzan perfume ya fesa Sannan ya fito zuwa parlor, Ko da ya isa parlor iskewa yayi har house girl ta gama shirya breakfast su Mummy sun zauna suna karyawa.Mr-Fauzan k'arasawa wajen dinning table d'in yayi ' yayi joining d'insu ya zauna.Mr-Fauzan Daddy da Mummy ya gaisar sannan Khairat da ke gefe tace."Yaya Good morning.""Ehem, Morning Khairat.Cewar Mr-Fauzan.Mr-Fauzan tsiyaya tea yayi cikin cup at fara sha."Fauzan, Yau da safe Hajia ke fad'amin cewar Safna tayi rashin mahaifiyar ta, Allah ubangiji ya gafar ta mata."Mr-Fauzan cikin nutsuwa ya aje cup d'in hannun sa tare da cewa."Amin Dad.""Idan ka tashi zuwa wajen ta'aziyyar, Zaka tafi da Khairat ' ita ce zata wakilce mu nida Alhaji."Mummy ta fad'i haka."OK, Aima yanzu zan tafi ' because inaso in lek'a office yau."Abinda Mr-Fauzan yace kenan ya cigaba da sipping tea d'in shi.*Some minutes later...*Bayan sun gama breakfast ne Daddy ya tashi ya wuce wajen aiki, Mr-Fauzan shima mik'ewa yayi gami da gyara necktie d'in shi yace."Ki same ni cikin motor."Ya fad'awa Khairat haka, Jin haka yasa Khairat ta ajiye cup d'in tea d'inta ta wuce d'akin ta cikin hanzari.Gele ta yafa a k'irjin ta ' ta d'auki side back d'in ta ta fito, Khairat parlor ta dawo ta sallami Mummy tukunna ta fita.Koda ta fito cikin motor ta sami Mr-Fauzan zaune, Hakan yasa ta bud'e front seat ta shiga ta zauna tareda cewa."Yaya, Na shirya."Nan take Mr-Fauzan yayi dialing number d'in Hafiz.Ringing d'aya tayi Hafiz yayi receiving."Babban Mutum!."Cewar Hafiz."Hafiz, Am on my way coming to your house now ' kashirya tare zamu je ta'aziyyar.""Shit!... OK to sai ka iso."Nan Mr-Fauzan yayi ending call d'in ya tada motor suka nufi gidan su Hafiz.B'angaren Hafiz, Bayan ya gama waya day Mr-Fauzan ne ya tashi ya fad'a bathroom yayi wanka, Sannan ya shirya cikin milk d'in yadi mai tsada.Hafiz shiryawa yayi tsaf ' ya fito parlor yayi breakfasta tsaitsaye, Hajia na lura da hakan.Hafiz harya kama hanyar fita ne Hajia ta dakatar dashi da cewa."Hafiz lafiya kuwa? Ina zuwa haka?."Hafiz juyowa yayi ya fuskanci Hajia tare da cewa."Akwai inda zamuje ne nida Fauzan, Banaso yazo ban gama shiryawa bane."Aleeza dake gefen Hajia a zauna gaban ta ya fad'i dasauri ta juyo ta kalli Hafiz."Oh shine yasa kake ta abu baga baga kamar zaka tashi sama?."Hafiz juyawa yayi ya fice cikin walwala tare da cewa."Eh mana."Aleeza tashi tayi zata wuce kitchen Hajia ta tsai da ita da cewa."Ina kuma zakije Auta?.""Hajia, Kitchen zanje zan yiwa mai aiki magana ne."To kawai Hajia tace, Sannan Aleeza ta wuce kitchen, Iske 'yar aiki tayi tana goge goge."Yawwa, Don Allah inason kimin wani abu ne."Cewar Aleeza."To.""Kije harabar garage ki tsaya, Akwai wani abokin yaya Hafiz da zaizo ' da zarar yazo please kizo ki fad'amin."To kawai 'yar aikin tace ta cigaba da gogen ta, Hakan yasa Aleeza tayi saurin ansar tsumman tare da cewa."No! Kije kawai, Bara na cigaba kafin ki dawo."Haka 'yar aikin ta wuce harabar garage ta tsaya wajen flowers, Shi kuwa Hafiz na zaune k'ark'ashin rumfa rik'e da wayar shi yana jiran zuwa Mr-Fauzan.Aleeza jefar da tsumman tayi nan wajen ta dawo parlor ta fara safa da marwa.Hajia na zaune gefe tana kallon ta, Aleeza tana cikin haka wayar ta dake saman three seater ta fara ringing ' hakan yasa tayi sauri ta je ta d'auka.Ganin Dr Khalil ne yasa tayi receiving cikin fara'a, Bayan sun gaisa ne kamar kullun ' Dr Khalil yace."I hope kin shirya ma zuwa ko?.""Insha Allah."Nan suka cigaba da hirar su, Hafiz na zaune yaji hone hakan yasa shi yin saurin mik'ewa tsaye tare da cewa."Yawwa, Bud'e gate d'in da sauri."Hafiz ya fad'awa gate man haka.Bayan gate man ya bud'e gate ne kamar yadda aka umurce shi, Mr-Fauzan ya shigo da motar shi ciki.Bayan yayi parking motar shine ya fito, Cikin fara'a Mr-Fauzan da Hafiz sukai hands shake.Ganin haka yasa 'yar aikin ta juya ta koma da sauri.Aleeza na cikin wayan ne 'yar aikin ta shigo cikin parlor gami da cewa."Gaya cen ya zo."Jin Hakan yasa Aleeza tayi saurin cewa Dr Khalil."We will talk later, Babye."Abinda tace kenan tayi ending call.Aleeza wajen window ta koma tana lek'en su Mr-Fauzan."Wa kike lek'e ne wajen?."Cewar Hajia."Ohhhhhh! Hajia bafa kowa! Naji kamar tsayawar mota ne shine fa nake dubawa."Aleeza ta fad'i haka cikin shagwab'a."To ai shikenan, Ba sai naji duka ba kuma."Aleeza murmushi tayi tare da karkad'a kai ta koma ta zauna kusa da Hajia.B'angaren Mr-Fauzan bayan sun gama gaisawa da Hafiz ne yace."Hajia na nan ko?.""Eh tana nan, Kuma na fad'a mata zuwan ka.""To bari Khairat taje su gaisa.""Oh! Dama tare da Khairat kuke? Shine ta lafe cikin motor?."Hafiz ya fad'i haka, Sannan yace."Bari naje nayi mata magana da kaina toh."Haka Hafiz ya zarce wajen motar ya bud'e, Da sauri Khairat ta d'ago kai ta kalle shi tare da sakar mashi smiling."Ina kwana?.""Kina nufin da bazaki je ku gaisa da Hajia ba kenan?."Khairat kunya ce ta rufe ta yasa sunkuyar da kai gamida cewa."A'a dama ina da niyyar yin haka."Abinda ta fad'a kenan ta fito daga cikin motar, Hafiz ya nuna mata hanyar shiga ta wuce ' Hafiz binta yayida kallo harta shige ciki Sannan ya koma wajen Mr-Fauzan.Bayan sun zauna ne Hafiz ya fara tsarawa Mr-Fauzan yadda suyi."Aini matsala ta da kai shegen girman kai."Cewar Hafiz."Hafiz, You know me very well ' bani son raini at all...and you know that.""Just admit it ' kana son yarinyar nan... Meye a ciki? Ni banga abin raini a ciki ba ai...""Shikenan... Naji I love her and I admit that... Yanzu meye abin yi? What if tak'i yarda dani?."Hafiz dogon numfashi yaja, Sannan yace."Idan tak'i yarda da kai sai ka barta kawai don ba'a so dole, Although nasan Safna na sonka ' sai dai idan kak'i bata hak'uri.""Oh come on... Meya kawo maganar bada hak'uri? Hafiz babu abinda yake bani wahala irin in bud'e baki in bada haku'ri, Musamman ga mace!.""You see your life? Aiko hak'uri ya zama dole ka bata, Because ita mace 'yar tarairaya ce."Mr-Fauzan nuna gamsuwar shi yayi game da maganganun Hafiz, Nan suka tashi suka nufi mota."Af! Wannan taje ta shantake, Let me go and call her."Hafiz ya fad'i haka, Sannan ya nufi cikin gida domin kiran Khairat.Mr-Fauzan kuwa cikin motor ya shiga yayi zaman shi.Hafiz koda ya shiga ciki a parlor ya iske Khairat tare da su Hajia suna fira."Toh, Ke muke jira fa."Hafiz ya fad'i haka.Jin haka yasa Khairat ta mik'e tayi sallama da su Aleeza, Hafiz fita yayi yaje ya shige motor.Aleeza rakiya taiwa Khairat har wajen motor, Sannan sukayi exchanging number tukunna Khairat ta bud'e back seat ta shige.Aleeza harta juya zata wuce taji ance."Madam babu gaisuwa ne?."Aleeza wani farrrrrr taji cikin ranta, Cikin sanyin jiki ta juya ' Ganin Mr-Fauzan tayi yana kallon ta a cikin mirror d'in jikin motor.Hakan yasa Aleeza k'arasawa side d'in da yake tace."Ina kwana?."Mr-Fauzan kasa ansawa yayi, Sakamakon ganin bandage d'in da ke forehead nata."Meya faru dake haka?."Yayi tambayar with cares."Oh! Wai goshi na? I had an accident.""How comes?.""Well... Bayan na bar Company d'in ka abin ya faru dani.""Hafiz kaga irin ta ko? Shiyasa banaso ana barin k'ananan yara suna driving by their selves, I don't like that at all..."Aleeza tsuki taja Mara sauti cikin ranta tace."Ji rainin hankali don Allah! K'aramar yarinya ma yake d'auka ta kenan mtsw."Nan Aleeza ta juya ta wuce rai a b'ace.Mr-Fauzan kallon wucewar ta yayi ta glass sannan ya tab'e baki ya tada mota suka wuce.```MY FACEBOOK FANS, NA GODE SOSAI DA ADDUAR KU GARE NI THANK YOU SO MUCH, YOU GUYS MEAN A LOT TO ME.```*FACEBOOK@SEEMALUV HAUSA NOVELS.*46roups/1649808818646464/*_FAN'S KUYI HAK'URI DA JINA SHURU DA KUKAYI, BANJIN DAD'I NE..._**48-49*K'auyen su Safna suka nufa ' kasancewar tsakanin k'auyen da cikin gari akwai d'an nisa hakan yasa suka b'ata *2hours* kamar kusan kullun.Bayan sun isa cikin unguwar ne, Mr-Fauzan yayi parking daidai k'ofar gidan su Safna."Khairat you get in first, Sai ku gaisa tukunna ki fad'amata zuwan mu.""Okay."Khairat tace, Sannan ta bud'e motor ta fito, Ganin yanayin gidan nasu yasa jikin ta yayi sanyi ta shige cikin gidan."Huh! Ni tausayin yarinyar nan nakeji....Just take a look at the house she is living in!..."Mr-Fauzan ya fad'i haka with sound of sympathy.Bayan shigan Khairat cikin gidan ne ta iske su zaunea tsakar gida saman tabarma.Khairat sallama tayi Safna ta juyo ta kalle ta gamida ansa sallamar.Khairat k'arasa tayi ciki Safna ta bata kujera ta zauna, Sannan suka gaisa Khairat tayi mata ta'aziyya."Sai dai ban gane wacece ke ba."Khairat murmushi tayi ta numfasa, Sannan ta fad'awa Safna wacece ita.Safna ajiyar zuciya tayi ' ta tashi ta d'ebowa Khairat ruwan rijiya ta bata.Khairat kurb'a d'aya tayi ta ajiye ruwan."Ku kad'ai kuke zama ne?."Khairat tayi tambayan cikin tausayawa."Eh mu kad'ai muke zama yanzu, To wama muke dashi da zaizo ya zauna damu? Kinga kuwa dole na tsaya na kula da k'annai na.""To, Kina da wata sana'a ne da kike yi Aunty?."Uhum! A'a bana yin komai, 'Yan kud'in da muka d'an samu ne wajen jinyar Umma kafin rasuwar ta shine nake amfani dashi kafin in nemi aikin yi."Khairat hawaye ne suka zubo mata, Safna tayi saurin share mata hawayen."Haba... Ke kuwa! Idan kina mana kuka ai zakisa na karaya, Kuma a hakan ma aimu munajin dad'i, Idan kikayi la'akari da yanayin da ake ciki."Safna ta fad'i haka cike da bama zuciyar ta k'warin gwiwa.Khairat hannu tasa ta share hawayen ta, Ta maida kallon ta akan Rumaisa dake zaune tare Anisah suna kallon ta."Haka ne..., Bai kamata na zubar maku da hawaye ba, Sai dai tare da Yaya Fauzan nake suna k'ofar gida suna jiran ki."Safna bata rai tayi tare da mik'ewa tsaye, Ganin haka yasa Khairat itama ta tashi tsaye tana kallon Safna."Auntyn mu, Lafiya?.""Kiyi hak'uri Khairat, Bazan iya ganin Yayan ki ba.""Haba Auntyn mu, Ko yayi laifi ne?."Nan take idanun Safna suka ciko da hawaye, Tayi saurin juyawa don kada Khairat ta lura da hakan.Safna d'aki ta shige ta d'auki hijab d'inta ba tare da ta cewa Khairat komai ba, Ta fito ta sanya zata fita Rumaisa tayi saurin cewa."Yawwa, Aunty Safna kafin Umma ta rasu tace kiyi k'ok'ari ki cika mata burin ta."Da sauri Safna ta juyo ta kalli Rumaisa sannan ta kalli Khairat, Safna dawowa tayi ta zauna kusa da Rumaisa."Wane irin buri ne wannan Rumaisa?."Cewar Safna"Tace don Allah ki tabbatar auren nan ya yuwu."Safna saurin kallon Khairat tayi ganin sun had'a ido ne yasa ta d'an sakar mata murmushin k'arfin hali, Sannan ta tashi ta wuce.Safna a zaure ta tsaya ' jikin bango ta jinginar da kanta tana tunanin yadda komai ya juya mata."Insha Allah zan kasance mai biyayya a gare ki ko a bayan ranki ne."Safna ta fad'i haka.Nan ta fita ta k'arasa inda motar su take ta tsaya."Here she comes... Bari na baku guri, And please Aboki kayi abinda ya dace.""Oh come on... You can't tell me what to do!."Cewar Mr-Fauzan."Daga baya kenan dai!."Hafiz ya fad'i haka tare da bud'e motar ya fita, Nan yayiwa Safna ta'aziyya sannan ta zagaya ta bud'e front seat ta zaune gamida ta rufe motar."Ina kwana?."Cewar Safna."Lafiya! Ya k'arin hak'uri?.""Alhamdulillah.""Allah yai mata gafara."Ameen Safna tace, Sannan sukayi shuru na d'an lokaci."Am... Safna...Am..."Safna ita dai ido kawai ta zuba mashi, Tana jiran abinsa zai fito daga bakin shi."Am here to apologize... Safna..."Safna sunkuyar da kai tayi tana sauraron shi."Inason ki manta da duk wani abu da ya faru mara dad'i tsakanin mu."D'ago manyan idanun ta tayi wad'an da sukayi ja ta kalleshi, Hawaye cike a idanun, Phalanges d'inta d'aya kan d'aya."I know that I hurts you several times with my words..."Mr-Fauzan ya fad'i haka in a husky voice."I really regret what I did to you..."Ya fad'i haka With sounds of sympathy tare da dunk'ule hannun shi.Safna d'agowa tayi ta jinginar da kanta jikin seat d'ingami da share hawayen fuskar ba tare da tace mashik'ala ba.Mr-Fauzan harya kai hannun shi zai janyo nata hannun ' sai kuma ya fasa."You totally changed everything in me Safna... Nasanmeye tausayi duk ta dalilinki."Safna juyowa tayi cikin mamaki take kallon cikin idanun shi, A zuciyar ta tace."Anya wannan shine Fauzan d'in da na sani kuwa?.""Surprise right? Yes Safna... Ni d'inne dai Fauzan."Ya fad'i haka tare da janyo hannun ta ya dunk'ule cikin nashi."Please Safna... Will you marry me? Zaki aure ni?."Mr-Fauzan ya fad'i haka.Safna sunkuyar da kai tayi bakin ta yayi mata nauyi, Kasa cewa komai tayi ta tsaya tana kallon hannun shi dake saman nata."Bazan ta kura ki ba, Kuma bazan matsa miki ba, Amma inaso ki amince muyi auren nan Safna... Da yardar ki za'ayi komai.""Babu abinda zai cenja akan maganar auren, Na amince."Cewar Safna."Alhamdulillah,And I promise you that ' zan baka duk wani abinda kike buk'ata na rayuwa."Mr-Fauzan ya furta haka da murmushi akan lips d'inshi.Safna zame hannun ta tayi gamida cewa."Ni zan koma cikin gida.""No wait... Ai ban gama magana ba, Inason ki fad'awa Khairat k'anwata duk abinda kike buk'ata a yanzu."Cewar Mr-Fauzan."A'a, Babu abinda nake buk'ata.""Okay then..."Ya fad'a tare da d'aga wani abu ya ciro kud'i masu yawa ya mik'a mata."Take this, Ki d'an fara rage abinda kike buk'ata na biki.""A'a don Allah ka barshi, Ni a yanzu bana buk'atar komai illa kwanciyan hankali.""Yes, I know that... But ki daure ki ansa wannan, Don't you think zaku buk'aci kud'i na hidiman biki?."Cewar Mr-Fauzan.Safna hannu tasa ta ansa kud'in tare da yimashi godiya, Sannan ta bud'e motar ta fita.Bayan wucewar tane Hafiz ya nufi wajen Fauzan.Hafiz motar ya bud'e ya shiga, Ganin fuskar Mr-Fauzan cikin fara'a ne yasa Hafiz cewa."Tofa! Allah yasa dai bakayi abinda zai dagula komai ba, Don nasan halinka.""I totally changed, Hafiz ' duk ta cenja ni wallahi... I truly love Safna with all my heart, Bansani ba ko asiritaimun cikin k'ank'anin lokaci.""Alhamdulillah,And did you tell her that you love her?.""I haven't... But na nuna mata hakan da baki na... Hafiz bansan nayi iya tausasa murya ba sai yau."Hafiz tsayawa yayi yana kallon shi at the same time yana dariya."Fauzan please be a man mana! Duk kabi ka wani rud'e... Mu dai ka saisaita kanka don driving zakayi yanzu."Nan dukkansu suka hau dariya cike da farinciki.B'angaren Safna, Shigar ta cikin gida ta iske Khairat zaune a inda ta barta tana hira dasu Rumaisa.Safna waje ta samu ta zauna, Ta sauke ajiyar zuciya."Auntyn mu har kin gama?."Cewar Khairat."Eh, Na gama ke kawai suke jira.""To amma Auntyn mu, Zaman nan naku ku d'ai is very risk fa akwai had'ari, Don Allah ku koma wajen 'yan uwa mana."Khairat ta fad'i haka cike da nuna damuwa."To ai Khairat jibi ne fa auren dududu bai wuce mu k'ara kwana d'aya anan ba, Su kuma k'an naina wajen dangin Baba zasu koma."Khairat numfasawa tayi ta mik'e tare da cewa."Indai akwai matsala kawai ki fad'a mana, Babu abinda zai gagara kinji Auntyn mu."Safna kai kawai ta d'aga ma Khairat, Sannan ta tashita raka ta har k'ofar gida tukunna ta koma cikin gida.*FACEBOOK@SEEMALUV HAUSA NOVEL.**50-51**Around 4:00pm*Bayan Mr-Fauzan ya maida Hafiz gidane ' tukunna ya koma gida ya aje Khairat, Sannan ya juya zuwa company.Khairat ko data shiga ciki, Iske Mummy tayi a main parlor zaune sanye da medicated glass a idanun ta tana filling out wasu takaddu.Da sallama Khairat ta k'arasa inda Mummy take ta zauna."Har kun dawo?."Cewar Mummy."Eh wallahi Mom.""Ina shi Fauzan d'in?."Mummy tayi tambayar kanta akan takaddun da take filling."Aje ni kawai yayi ya juya wai he got many things to do."To kawai Mummy tace, Sannan Khairat ta tashi zata wuce side d'in ta Mummy ta tsaida ita."Khairat?."Cewar Mummy.Khairat dawowa tayi ta zauna tare da cewa."Na'am.""Ya ita yarinyar?.""Oh Aunty Safna? Lafiyar ta k'alau, Amma saidai Mummy suna da buk'atar taimako sosai ' gaskiya natausaya musu."Jin hakan yasa Mummy cire glass d'in da ke idon ta."Kar dai Fauzan dangin talakawa ya nemo!."Cewar Mummy."Haba Mummy don Allah."Khairat ta fad'i haka.Khairat tashi tayi gami da bubbuga k'afa da gunguni ta wuce side d'inta.Mummy k'wafa tayi ta cigaba da abinda takeyi.B'angaren Hafiz, Tunda ya koma gida ya kwanta yake bacci abinshi.Aleeza kuwa safa da marwa kawai takeyi bata d'aki bata parlor.Hajia ce ta shigo cikin parlon ta iske Aleeza tsaye tamkar wacce ke jiran tsammani, Kwalliya kuwa tamkar wata amarya ' fannin ado kam ba'a magana."Auta?."Cewar Hajia.Aleeza dake fuskantar window, Juyowa tayi ta kalli Hajia."Na'am.""Akwai wanda kike jira ne?."Hajiya tayi tambayar.Aleeza waje ta samu ta zauna, Sannan tace."Hajiya dama, Wannan Doctor d'inne yace zaizo mu gaisa, Shine naji shi shuru."Ta fad'a tare da nuna damuwa."Wane Doctor kenan?.""Hajia, Doctor Khalil mana... Wanda ya duba ni.""Ohwoo... Allah sarki, To ki sake bashi lokaci mana, K'ila akwai abinda ya tsayar dashi ne."Abinda Hajia tace kenan ta mik'e zata koma part d'inta Aleeza taji k'arar bud'e gate.Hakan yasa tayi saurin tashi taje wajen window domin dubawa."Shine..."Aleeza ta fad'i haka tare da kama hanya zata fita, Hajia tayi saurin dakatar da ita."Ke Auta! Meye haka? Bazaki aji ba?.""Hajia zanje na taroshi ne fa."Hajiya zaunar da Aleeza tayi ta fad'a mata yadda akeyi, Sannan Hajiya ta wuce part d'inta.Koda Dr-Khalil yayi parking motar shi ya fito, Sai da yayi 5minutes a tsaye a wajen banda missed calls da ya dunga yiwa Aleeza.Aleeza saida taja aji tukunna ta fito garage ta nufi inda Dr-Khalil ya tsaya jiranta.Aleeza sanye take da wata had'ad'd'iyar gown blue ' kanta kuwa rufe yake da blue tie sai kuma high hill bak'i a k'afar ta.Bayan ta isa gare shine taimashi sallama, Dr-Khalil d'ago kai yayi ya kalle ta."Ya Salaam!."Abinda Dr-Khalil ya furta kenan yana k'arewa surar jikin Aleeza kallo."Baza ka ansa sallamar tawa ba?."Cewar Aleeza.Nan Dr-Khalil ya amsa sallamar but still idanun shi na kan fuskarta."Mu shiga daga ciki ko?."Aleeza ta fad'i haka.Haka suka nufi cikin gida suna taku.Bayan shigar su parlor ne, Aleeza ta umurce shi daya zauna ita kuma ta wuce kitchen ta d'auko drinks ta kawo mashi, Sannan ta koma ta zauna.Haka suka sha firar su Dr-khalil yana yi yana kora drink a baki.*35minutes later...*Bayan sun gama hirar tasu ne Dr-khalil ya tashi domin yin haramar komawa, Haka Aleeza ta tashi itama suka fito harabar garage suka tsaya inda yayi parking motar."Let's get in ' ko?."Cewar Dr-Khalil."Okay."Aleeza ta fad'a sannan suka shige cikin mota.Bayan shigar sune Dr-Khalil yaja dogon numfashi yace."Na gode da tarba mai kyau Aleeza.""Anytime..."Ta furta a tak'aice cikin fara'a.Nan Dr-Khalil yasa hannu a aljihu ya ciro d'an k'aramin box ya mik'a mata."Please take it."Aleeza kai ta girgiza mashi alaman a'a."I said please... Ba don ni ba."Ya fad'i haka with sounds of pleading.Aleeza karb'a tayi ta tsaya tana kallon box d'in."Open it."Dr-Khalil ya fad'a.Aleeza bud'ewa tayi taga necklace fari mai hasken diamond."Wow..."Ta furta a hankali."I love you Aleeza..."Jin maganar tayi ta doshi cikin k'wak'walwar ta tayi saurin kallon shi."Yes Aleeza, Ki amince dani."Aleeza harta bud'e baki zata yi magana sai kuma ta tuna da maganar Hajia, Cewan ta dunga jan aji."Thank you for the splendid visit..."Abinda ta fad'i kenan ta bud'e motar ta koma cikin gida cikin sauri.Dr-Khalil ajiyar zuciya yayi tare da yin k'wafa yace."Zaki shigo hannu."Nan ya tada motar shi ya wuce.Aleeza tana tsaye wajen window tana kallon shi wucewar, Ganin ya tafi ne yasa ta buga uban tsalle cike da farin ciki ' ta fara rawa."Rawa da girgiza... Zanyi gaban ka in jujjuya! Zanyi maka albishir kayi dace da mai tarbiyy..."Bata kaiga k'arasa wak'ar ba taji kamar motsin Hafizzai shigo cikin parlon.Hakan yasa Aleeza tayi saurin hayewa sama ta nufi d'akin ta.Aleeza koda ta isa cikin d'akin k'arar shigowar text taji cikin wayar ta.Hakan yasa tayi saurin d'aukar wayar ta duba, GaninDr-Khalil ne yasa tayi smiling."Ina sonki Aleeza, Ki amince da soyayya ta ' ke kad'ai nake buk'ata a halin yanzu."Aleeza wurgi tayi da wayar saman gado, Ta haye gadon Tare da rungume pillow tana sakin murmushi mai d'auke da sak'onni iri iri.*** *** *** *** *** *** *** *** *** ****2DAYS LATER...*```YAU TAKE SATURDAY, RANAR BIKI...```Gidan su Safna cike yake da mutane, Gaggo Mariya da dangin Mahaifin su Safna ne keta hidima cikin gidan.Duk da dai dangin mahaifin nata d'aid'aiku ne suka zo, Amma Safna tayi farin ciki matuk'a.Safna zaune take a k'ofar d'aki anayi mata lalle mai kyau.Goggo Mariya ce tazo inda Safna take ta zaune."Ke kuwa mai lalle kiyi sauri fa, Domin nan *1:00pm*za'a d'aura auren kuma yanzu gashi *12:00pm*."Goggo Mariya ta fad'i hakane tana yiwa Safna murmushi.Safna kuwa kunya ce ta rufe ta yasa ta sunkuyar da kanta tana murmushi."Safna?."Cewar Goggo Mariya.Safna kai ta d'ago ta kalle ta tare da cewa."Na'am.""Safna, Na yarda zan rik'e su Rumaisa kinji ko?."Safna waro idanu tayi cike da farin ciki."Alhamdulillah,Goggo Mariya na gode sosai ' gaskiya bamu da kamar ki."Safna ta fad'i haka tamkar zatayi kuka."Haba.... Yo idan ban rik'e ku ba waye zai rik'e ku?."Goggo Mariya ta fad'i haka gamida tashi ta koma wajen girkin da suke yi.Suna cikin hakane wani yaro ya shigo cikin gida."Wai ance ana kiran Safna."Abinda yaron nan yace kenan ya juya yayi gaba abinsa."Kinga bar lallen nan, Bara naje na duba wanene..."Cewar Safna.Safna tashi tayi ta fita, Ganin Sir-Kamal tayi a tsaye jikin motar shi.Haka Safna ta k'arasa wajen shi da d'anyen lalle a hannun ta tare dayin sallama ' ya amsa."Naga kamar kuna hidima ne."Safna murmushi tayi ta sunkuyar da kai."Eh, Kayi hak'uri bansami damar fad'a maka ba...""Me kenan.""Aure zanyi..."Ta fad'a a tak'aice.Sir-Kamal shock yaji at the same time kanshi ya d'aure.Wani irin tafasa zuciyar shi keyi idan da zaku lura dafuskar shi jijiyoyin shi duk sun tashi.Sir-Kamal dakyar ya iya bud'e bakin shi yace."Amma... ina taya ki murna Safna, Wane ne ne Angon?.""Ogan ka Fauzan."Cikin mamaki Sir-Kamal ya tsaya yana kallon ta."Am... Safna dama kawai nazo duba ki da lafiyar ki ne, Ni yanzu zan koma."Ya fad'i haka tare da bud'e motar shi zai shiga."Am... A babban masallacin juma'a za'a d'aura auren, Ina gayyatar ka."Safna ta fad'i haka cike da nuna farin ciki."To! Na gode."Ya fad'i gamida shigewa cikin motar shi yaja ya wuce.Safna komawa gida tayi ta zauna aka idasa lallen, Sannan ta aka kai mata ruwan wankan ta ban d'aki.B'angaren Mr-Fauzan kuwa, Gidan nasu shima mak'il yake da jama'a.Cikin garage kuwa cike yake da Abokan Ango, Da kuma Abokan Daddy.Mr-Fauzan ne ya iso cikin garage d'in cikin manyan kaya ' Hafiz yazo ya tareshi suka k'arasa cikin mutane.Mr-Fauzan farar shadda ce sanye a jikin shi riga da wando da kuma malin malin, Da hular shi black color ' sai wristwatch golden mai tsada.Mr-Fauzan komai na jikin shi to-match ne kuma maitsada.Haka aka shish-shiga motoci masu tsada na gani nafad'a, Suka nufi Babban masallacin juma'a domin d'aura aure.B'angaren Safna kuwa, Har tayi wanka ta shirya tayi kwalliya ta k'ure kwalliya iyakar yinta.Kayan dake jikin ta atampa ce gadagalle sabuwa ' wacce Goggo Mariya ta kawo mata.Haka Safna ta k'unshe d'aki sabida kunya da 'yan k'annanta.*1:00pm dot* aka d'aura auren *Mr-Fauzan&Safna*.Safna na zaune a d'aki ne, d'aya daga cikin wakilen nata ya shigo ya sanar musu cewar Aure ya d'auru.Gaba d'aya gidan hamdala suka shiga yi, Safna kuwa ji tayi tamkar ta nutse sabida kunya."Aunty Safna zan biki cen..."Inji Anisah."Toh Anisah, Karki damu awajen Goggo Mariya zakuzauna ' ni kuma kullun zanzo na rik'a duba ku."To kawai Anisah tace, Goggo Mariya ta shigo d'akin.'Yan nasihohi Goggo Mariya taita yiwa Safna, Yi nayibari na bari da dai sauran su.*FACEBOOK@SEEMALUV HAUSA NOVELS."groups/1649808818646464/*52-53*Suna cikin haka ne, Abokan Ango suka iso k'ofar gidan su Safna da manya manyan motocin su.Saida suka dunga hone, Sannan wata ta fito taimusumagana.Hafiz ne ya fito daga motar shi ya jigina jikin shi."Ni zan d'auki Amarya!."Abinda ya fad'a kenan yayi calming hands d'in shi.Safna kuwa, Koda aka zo aka sanar mata cewar abokan Ango sunzo d'aukan Amare kuka ta fashe dashi.Goggo Mariya ce keta lallashin ta sai kuma wad'an da ba'a rasaba.Haka aka shirya Safna tsaf aka lullub'e mata fuskarta da gyale, Sannan kowa ya sanya hijabin shi.Wasu fita sukayi suka fara shiga mota, Wasu kuma tare da Amaryar zasu fito.Goggo Mariya shirya su Rumaisa tayi ta hanyar mik'a masu hijabansu suka sanya, Domin dasu za'a kai Amarya.Haka da k'yar aka samu Safna ta daina kuka aka fitoda ita aka sata cikin mota.A seat d'in baya aka sanya Safna sai 'yan k'annan ta da take tsakiyar su sai kuma Goggo Mariya data zauna front seat."Aff! Ina zuwa don Allah, Bara na sanya kwad'o (padlock) a gidan."Cewar Goggo Mariya.Goggo Mariya bud'e motar tayi ta fita domin kulle gidan."Amarsu Amarsu... Amarsu ansha k'amshi..."Hafiz ya fad'a cikin zolaya."Nifa har yanzu banji kin fara kuka bane, Don nafiso kiba Ango wahala."Cewar Hafiz."Ai tasha kuka sosai kafin mu fito, Saida aka dunga lallashin ta..."Rumaisa ta fad'i haka."Aww! Lallai yau Abokina sai yayi dagaske kenan, Kafin a kalle shi."Safna da fuskarta take a lullub'e, Shuru kawai tayi batare da tace dashi komai ba.Suna cikin haka ne Goggo Mariya ta dawo, Hakan yasa Hafiz tada mota suka jeru ' motar Amarya na tsakiya, Haka suka d'auki hanyar kai Amarya ' duk tainda suka bi sai an kalle su.B'angaren Sir-Kamal kuwa, Bayan ya kai gidane yayiparking motar shi ya shige ciki ranshi a b'ace.Ammi dake zaune a parlor ne taga yazo zai wuce ba tare da yayi sallama ba talk less of ya gaishe ta."Kamal?."Ammi tayi saurin tsaida shi, Sir-Kamal juyowa yayi ya kalli Ammi idanun nan nashi sunyi ja."Meya faru ka shigo a haka?."Sir-Kamal zuciya ce ta tik'o shi ya juya kawai zai wuce d'aki, Ammi ta dakatar shi."Kamal! Ba tambayar ka nakeyi ba?.""Ammi... Yarinyar da nakeso nake muradin kasancewa tare da ita, Yau na wayi gari Oga na ya aure ta Ammi!."Sir-Kamal yayi maganar yana huci tamkar zaki, Idanun shi kuwa duk sun kawo ruwa.Ganin hakan yasa Ammi tashi taje ta kamo hannun shi suka zauna."Kamal... Wace yarinya ce da har ran maza ya b'aci haka?.""Yarinyar da na dad'e ina baki labarin ta, Ammi bantab'a sanin Safna kwad'ayi keyi da ita ba... Kumaban tab'a sanin Safna hawainiya bace Ammi..."Ammi shuru tayi nad'an lokaci, Sannan tace."Kardai yarinyar da kake cemin ' zaka nemowa aiki kwanakin baya!.""Ammi, Ita ce..."Sir-Kamal yayi maganar ta wata irin murya tamkar zaiyi kuka, Wanda ni kaina Seemaluv saida yayi matuk'ar bani tausayi."Kamal, Hak'uri shine kawai abinyi... Kuma tunda kaga haka to dama Allah baiyi zata zama matar ka ba.""No... No... Ammi! Banason jin wata kalmar hak'uri a halin yanzu Ammi, I must revenge... I must revenge...She betrayed me! Duk irin alkairin da nayi masu??."Sir-Kamal ya furta hakan tare da tashi zai nufi d'akinshi."Kamal, Karka sawa ranka mugun abu fa! Kayi tawakkali mana... Kuma dama ai ba kullun mutun yake nema yake samu ba."Cewar Ammi.Sir-Kamal d'aki ya shige ya kulle ta hanyar sanyamak'ofar key.*** *** *** *** *** *** *** *** *** ****AROUND 3:00PM*Aka isa gidan Amarya, A bakin gate d'in wani d'and'areren gida aka tsaya ' tabbas gidan *BABBANGIDA* ne.Hafiz ne yayi hone gateman ya bud'e gate sannan motocin suka shiga.Bayan shigar sune Goggo Mariya ta tsaya k'arewa gidan kallo, Duk tabi ta k'agara ta shiga ciki.Bayan motocin sunyi parking ne, Aka fito da Amarya ' Dangin Amarya suka dunga gud'a har suka shiga ciki basu daina ba.A parlor suka tsaya kasancewar basu san inda zasu dosa ba, Don gidan lungu lungu ne gashi kuma upstairs.Goggo Mariya ce ta tashi ta haura sama domin dubayanayin gidan.Cikin 'yan mintoci k'alilan ta dawo cikin farin ciki."Yo ku ai ga d'akin amaryar cen na gano.... Nidai tunda nake ban taba shiga irin wannan waje ba!."Goggo Mariya ta fad'i haka tare da kamo hannun Safna suka haura sama.Wasu daga ciki, Lek'e lek'e suka shigayi lungu lungu domin bama idonsu abinci.Bayan Goggo Mariya ta zaunar da Safna saman gado ne ta d'age mata mayafin fuskarta."Kinga yadda Allah ke d'aukaka d'an adam ko? Sabida haka bud'e idon ki kiyi kallo, Wannan d'akin ki ne Safna."Cewar Goggo.Safna d'aga kai tayi ta kalli yanayin d'akin tayi murmushi ta sunkuyar da kanta.Da misalin k'arfe *4:00pm*, B'angaren Mr-Fauzan ' wanka ya sake yi ya shirya cikin milk d'in shadda komai nashi ya tafi daidai.Mr-Fauzan wayar shi ya d'auka yayi dialing number d'in Hafiz, Bayan Hafiz ya d'aga wayar ne Mr-Fauzan yace."Hafiz, Nifa am well ready... Duk na k'osa, Azo a d'auke akai ni gida na.""Ahhh... Kaji mara kunyan Ango, Lallai aboki baka data ido ' to shikenan am on my way."Hafiz ya fad'a.Mr-Fauzan parlor ya fito ya iske mutane kowa na nuna farin cikin shi.Mummy ce tare da Khairat suka shigo cikin parlon hakan yasa Mr-Fauzan k'arasawa inda suke."Bro, Kayi kyau sosai... Ni zanyi maka rakiya har wajen Amarya."Cewar Khairat.Mr-Fauzan murmushi yayi irin na manya yace."Thanks K'anwa ta."Mr-Fauzan maida kallon shi yayi akan Mummy wacce idanun ta suka cika da hawaye."Mum, Nayi kyau?."Cewar Mr-Fauzan."Eh mana Son, Kayi kyau sosai ma..."Mummy tayi maganar cikin sigar kuka ' muryar ta narawa."Oh come on Mum... Please don't cry, Yin aure ba shine cewar na barku kenan ba Mum, Am your son and we will forever be together."Mr-Fauzan ya fad'i haka cikin tausasssar murya.Mummy hannun tasa ta share 'yan hawayen dake shirin zubowa, Tare da cewa."Nidai fata na kada matar ka ta raba ni da kai Fauzan.""Shhhhhh..."Mr-Fauzan ya furta tare da hugging Mummy ta sigarlallashi, Khairat dake gefe hawaye ne suka zubo mata tayi saurin sharewa, Mr-Fauzan yayi hugging d'inta ta d'ayan hannun.Haka Camera man ya dunga d'aukan pictures iri iri, Har su Hafiz suka iso cikin gidan.Mr-Fauzan na cikin lallashin Mummy ne kiran Hafiz ya shigo cikin wayar, Hakan yasa shi d'aga wayar."Babban mutum, Ka fito ' kai kawai muke jira."Cewar Hafiz.Okay kawai Mr-Fauzan yace ya kashe wayar, Sannan ya sanarwa Mummy.Mummy da Khairat ' da sauran mutanen wajen, Rakiya suka yiwa Mr-Fauzan zuwa garage.Nan suka iske Daddy da jama'an shi shima.Haka suka d'unguma suka yiwa Mr-Fauzan rakiya har cikin motor, Saida suka ga wucewar shi sannan suka koma cikin gida.Koda Mr-Fauzan da Hafiz suka isa, Iskewa sukayi har angama kwashe dangin amarya an maida su gida.Goggo Mariya ce kawai dasu Rumaisa suka rage, Suma d'in parlor suka fito zasu fita ' suka had'e da Mr-Fauzan.Nan suka tsaya suka gaisa, Sannan Goggo Mariya tace."Toh... Ga 'yar mu nan amana, Amana muka bar maka ita ' domin kuwa duk wanda yaci amana to amana shima zata ci shi."Mr-Fauzan cikin kamala ya nuna gamsuwar shi game da abinda Goggo Mariya tace.Nan Goggo Mariya ta kama hannun Anisah suka fito domin a maida su gida."To kai, Bari nai maka rakiya wajen Amaryar ko."Cewar Hafiz."A'a! No need ' na hutar da kai... Duk na k'osa naga My Infinity."Mr-Fauzan ya fad'a gami da sanya hannun shi cikin aljihu."Ah! Banda cika baki fa! Don na sanka..."Na sukayi sallama cike da fara'a, Hafiz ya juya ya wuce, Sannan Mr-Fauzan ya juya ya haye sama ' ya nufi d'akin da Safna take.*FACEBOOK@SEEMALUV HAUSA NOVELS."53*....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_UNIQUE WRITERS ASSOCIATION_*® ```Written```By*_Seemaluv_*https://www.facebook.com/groups/1649808818646464/*54-55*Mr-Fauzan, Cikin bedroom d'in ya shiga tare da yin sallama Safna ta amsa.Bayan ya k'arasa bakin gado ne ya zauna while Safna na tsakiyar gadon a zaune.Mr-Fauzan shuru yayi nad'an lokaci sannan yasa hannu ya cire built d'in k'afar shi ya tashi ya bud'e wardrobe ya ciro dadduma ya shinfid'a ya zauna, Sannan ya umurci Safna itama tazo ta zauna.Safna cikin sanyin jiki ta sauko daga gadon ta dawo ta zauna saman dadduma suna facing juna.Mr-Fauzan murmushi yayi yasa hannu ya d'age gyalen dake fuskar ta, Nan yayi hamdala ya mik'a godiyar shi zuwa ga Allah.Sannan Mr-Fauzan ya shiga yiwa Safna tambayoyi kamar yadda musulunci ya tanadar.Duk tambayoyin da Mr-Fauzan yayiwa Safna duk ta amsa ' hakan yasa Mr-Fauzan sauke ajiyar zuciya."Ki tashi kije kiyi wanka, Sannan kiyi Alwala ' ki same a d'aki na.."Mr-Fauzan ya fad'a a tak'aice.Safna shuru tayi kamar bataji abinda yace ba."Okay?."Mr-Fauzan ya fad'i haka.Safna kai ta d'aga mashi alaman toh, Sannan Mr-Fauzan ya tashi ' y wuce.Safna saida tayi 5minutes a zaune a wajen tana tunani iri iri a cikin ranta."Yau ni'ce a gidan Mr-Fauzan a matsayin matarsa? Allah kasa hakan shine mafi alkairi da kwanciyar hankali a gare ni."Safna ta fad'i haka gamida k'arewa d'akin kallo.Komai na d'akin purple ne, Paint d'in d'akin ma purple ne, Hatta globe d'in d'akin purple ne, hakan yasa color d'in d'akin ya koma purple.Safna tashi tayi tayaye mayafin dake kanta, Ta d'agerigar ta taja zanin sama sannan ta cire rigar ta nufi bathroom.Safna hannu tasa ta bud'e bathroom d'in ta shiga, Haske ta gani fauuu... Kasancewar komai na bathroom d'in fari ne.Haka Safna ta shiga ciki ta maida k'ofa ta rufe, Tsayawa tayi tana kallon yanayin bathroom d'in na d'an lokaci."Wannan kuma wane irin bayi ne? To ina ruwan suke?."Safna ta fad'i haka tana waige waige.Juyawa tayi ta fita ' fita tayi daga d'akin ta tsinci kanta a parlor, Parlon ko haske babu sakamakon kashe wutar da akayi.Wani tsoro ne taji ya riske ta lokaci d'aya, Hakan yasa ta juya zata koma d'aki sai jitayi anyi back hugging d'in ta.Safna wani shock taji ya ratsa jikin ta, Cikin tsoro tace."Hasbunallah..."Abinda ya fito daga bakin ta kenan ta runtse idanun ta."My infinity..."Mr-Fauzan ne ya furta haka.Nan ya juyo da ita suna facing juna.Mr-Fauzan hannu yasa ya d'ago fuskar ta suna kallon juna."Har kin shirya ne? Ni kike jira ko?"Kai Safna ta girgiza mashi, Sannan yace."Then, Mene ne?.""Dama... Dama... Ruwan wankan ne babu acen d'in ' shine na fito nema."Cewar Safna.Mr-Fauzan kallon ta yakeyi surprisingly daga bisani ya kamo hannun ta suka nufi d'akin nata.Bathroom d'in suka shiga ya nuna mata yadda zata kunna ruwan da kuma inda zatayi wankan.Nan Mr-Fauzan ya fita daga bathroom d'in tare da rufo mata k'ofa.Kai tsaye ya nufi wardrobe d'in kayan ta ya bud'e side d'aya, Sets d'in rigunan bacci ne a ciki different colours.Mr-Fauzan pink color ya ciro ya ajiye mata saman gado sannan ya fita.Bayan Safna ta fito daga bathroom d'inne taje gefen gado ta zauna ' ga sanyi na ratsa jikin ta."Ya salaam..."Abinda Safna ta furta kenan ta hango Ghana-must-go d'in da aka kawo ta dashi.Safna tashi tayi taje ta bud'e ta ciro riga da zani ' ta sanya sannan taje gaban tangamemen mirror ta tsaya tana k'arewa kanta kallo.Safna perfumes ta gani iri iri had'i dasu humra a saman mirror d'in, Hakan yasa ta d'auka ta feffesa sannan ta nufi d'akin Mr-Fauzan.Safna da k'yar ta iya gano d'akin nashi, Haka ta bud'e ta shiga.Koda ta shiga duhu ta gani don bata iya ganin komai, Safna sallama tayi Mr-Fauzan na zaune saman sofa yana kallon duk moves d'in ta.Mr-Fauzan ganin bata saka rigar baccin bane yasa shi mik'ewa tsaye yaje kusa da ita ba tare da ta sani ba."Meyasa baki sa rigan baccin ba?."Cewar Mr-Fauzan.Safna tsorata tayi ta juya a razane zata fita Mr-Fauzan yayi saurin fizgota ta had'e da faffad'an k'irjin shi, Wanda babu riga daga shi sai boxer."Ki koma akwai rigar bacci, Ki cire na jikinki ' ki saka ki dawo..."Mr-Fauzan ya rad'a mata hakan a kunne.Safna to kawai tace, Sannan ta juya ta wuce d'akin ta.Bayan ta koma d'aki ne ta hangi sleeping gown d'in saman gado.Haka Safna ta taje ta d'auka gamida d'agawa, Ganin irin rigan yasa ta waro idano."Yanzu wannan rigan zan saka yake nufi?."Safna ta fad'i haka tare da sakin ajiyar zuciya.Cire kayan jikin ta tayi ta sanya rigar kamar yadda ya umurce ta.Rigan iyakar ta cinya, Kuma armless ce.Safna hannu tasa ta kare k'irjin ta ta juya ta nufi d'akin Mr-Fauzan.Bayan shigarta ne ' tayi sallama ya amsa, Safna ganin haske tayi fauuu ' Mr-Fauzan ya kunna globe.Hakan yasa ta sake rufe k'irjin ta da hannayen ta.Mr-Fauzan ne ya tako har inda take, Hannu yasa ya tallabo fuskarta yayi pecking d'in ta a goshi.Sannan ya kamo hannun ta suka nufi bakin gado, Mr-Fauzan zaunar da Safna yayi sannan ya d'an zuk'unna gaban ta gami da aje ledar kaza & yoghurt a side d'inta.Mr-Fauzan d'aukar naman yayi zaj bata a baki tayi saurin kauda kai."Mene ne haka? Don't even try that... Kar ki cemin baza kici ba."Cewar Mr-Fauzan."Kayi hak'uri bana jin cin komai ne."Safna ta fad'i haka jikin ta a takure."No, Ban yarda ba, You have to eat this ' kisa wani abu a cikin ki."Mr-Fauzan saida ya matsawa Safna sannan ya samu taci kad'an tasha yoghurt.Mr-Fauzan mik'ewa tsaye yayi ya juya ya nufi bathroom, Haka Safna tabi tsukakken k'ugun shi da kallo har ya shige.Safna kam a takure take da rigar jikin ta, Ga sanyin da takeji kasancewar AC a kunne yake.Bayan Mr-Fauzan ya fito ne ya k'arasa har bakin gadon ya zauna kusa da ita yana shak'ar k'amshin turaren dake jikin ta."Babyna?."Mr-Fauzan ya kira sunanta ta wani irin voice d'inda shima baisan dashi ba.Safna a tsorace ta amsa mashi da. "Na'am." Ba tare da ta kalleshi ba.Mr-Fauzan har ya kai hannun shi zai tab'a ta sai kuma ya fasa, A zuciyar shi yace."What am I doing? I can't beg for that... I have to staycalm... Kada tazo ta raina ni."Mr-Fauzan ya fad'i haka gamida ta tashi tsaye."Babyna... Ya kamata muyi bacci ko?."Cewar Mr-Fauzan.Safna kai ta gyad'a mashi, Sannan Mr-Fauzan ya zagaya ta d'ayan side ya haye ya kwanta.Safna a hankali ta kwanta ita ma tamkar wacce k'wai ya fashewa a jiki, Bayan ta kwanta ne ta runtseidanun ta don kwata kwata jin wani sabon al'amari takeyi.Mr-Fauzan kuwa kallon shapes d'in jikinta kawai yake yi yana yabawa.Mr-Fauzan lura yayi Safna na shivering kad'an, Hakan yasa shi yin saurin lullub'e ta da duvet sannan ya koma ya kwanta.A haka har bacci yayi awon gaba dasu.*** *** *** *** *** *** *** *** *** ****_Washe gari..._*Da sassafe *around 5:00am* Safna ta tashi, Saukowa tayi daga saman gadon ta nufi d'akin ta.Bayan shigar tane ta shige bathroom direct tayi wanka tare dayo alwala, Sannan ta fito.Safna gaban mirror taje ta tsaya ta gyara jikin ta, Sannan ta nufi wajen kayan ta ' har tasa hannu zata bud'e jakar kayan sai kuma ta fasa.Wajen wardrobe ta nufa tasa hannu zata bud'e tare da cewa."Bari na duba wardrobe d'innan naga..."Abinda ta fad'a kenan, Ta bud'e wardrobe d'in.Safna still tayi a wajen sakamakon irin kayan sawan da ta gani jere a ciki.English wears ne dogayen riguna high neck with different colors, Safna murmushi kawai take saki tare da nuna jin dad'in ta a fili."Duk wad'an nan... Na...wa ne???."Tayima kanta tambayar tare da ciro d'aya daga cikindogayen rigunan maroon colour.Safna sake bud'e wani side tayi ta ga duk inner wears ne, Haka ta ciri wanda zata saka ' ta sanya."Allah ka k'ara rufa mana asiri duniya da lahira."Safna ta fad'i haka cike da saka rigar a jikin ta.Safna gaban mirror taje ta tsaya tana kallon yadda rigar tayi mata kyau a jiki tamkar dama don ita akayo su.Hannu tasa ta zame d'an kwalin dake d'aure a kanta tun jiya, Nan dogon gashin ta ya bayya kasancewar babu kitso a kanta.Komawa tayi ta bud'e wardrobe d'in ta ciri gele maroon ta rufe kanta, Sannan ta koma gaban mirror ta zauna.Safna ajiyar zuciya ta saki, Nan tayi kwalliya kamar yadda ta saba, tayi sallah, Sannan ta wuce d'akin Mr-Fauzan.Safna koda ta shiga babu kowa, Hakan ya bata damar gyara gadon.Bayan ta gama ne ta kama hanya zata fita Mr-Fauzan ya fito daga bathroom daga shi sai towela k'ugunsa ' ganin ta yasa shi tsayawa yana kallon dressing d'in dake jikin ta.Hakan yasa Safna tsayawa domin ta gaishe shi."Ina kwana?."Cewar Safna."You looks like a princess Babyna ' perhaps you are..."Mr-Fauzan ya fad'i haka in a slangs way.Safna d'ago fararen idanun ta tayi ta kalleshi, Ganin sun had'a ido ne yasa tayi saurin sunne kanta k'asa.Mr-Fauzan takowa yayi zuwa inda take yayi peckingd'inta."Am so much proud of you."Ya fad'i haka tare da rik'o hannun ta.A bakin gado Mr-Fauzan ya zaunar da Safna gamida cewa."Seat here! Bari in shirya ko?."Ya fad'i haka gamida juyawa ya nufi wardrobe d'in kayan shi."Ka shirya? A gaba na??... Ya salaam."Safna ta fad'i haka a zuciya, Ganin dagaske yakeyi yasa tayi sauri ta mik'e zata fita Mr-Fauzan ya dakatar da ita."Karki je ko ina! Ki dawo ki zauna, Is a command."Cewar Mr-Fauzan.Safna ganin babu wasa a maganar shine ' yasa ta dawo ta zauna tare da sunkuyar da kanta.Mr-Fauzan saida ya gama kintsawa tsaf Cikin singlet da boxer, Sannan suka koma parlor suka zauna.Bayan sun zauna ne da 'yan mintoci Safna tace."Ya kamata kayi breakfast... Me kakeso kaci domin in had'a maka?."Tayi tambayar cikin jin kunya."No... Waye zaisa Babyna shiga kitchen yanzu? Babu!... Khairat zata kawo abinda zamuyi breakfast don't worry okay?."Mr-Fauzan ya fad'i haka.Safna kai kawai ta gyad'a mashi cike da mamakin cenjawan shi cikin 'yan k'ank'anin lokaci.Mr-Fauzan lura yayi da tunanin da takeyi, Yace."I change right? Ba Fauzan da kika sani abaya ba ko?."Safna kai ta gyad'a mashi alaman eh."Don't stress yourself... I will soon tell you the reasonwhy I changed."Ya fad'i haka tare da winking d'in ta.Suna cikin haka ne, Suka ji gateman ya bud'e gate, Nan Mr-Fauzan ya tashi ya lek'a through window ' Khairat cewa ta shigo da motar ta ' tayi parking."Here she comes..."Cewar Mr-Fauzan.Bayan Khairat tayi parking ne ta ciro basket d'auke da flask d'in abinci a back seat.Cikin gidan ta shigo ta same su a parlor, Cikin fara'a Khairat ta k'arasa ciki.Bayan ta zauna ne suka gaisa, Sannan ta tashi rik'e da basket d'in a hannu taje dinning ta aje saman dinning table.Khairat sallama tayi musu cikin hanzari ta tashi zatawuce Safna ta tsaida ita."Haba, Kamar ana tsunkulin ki? Don Allah ki tsaya mana..."Cewar Safna.Khairat dariya tayi tare da cewa."Haba Auntynmu, School zan tafi ' but insha Allah zan dawo anjima."Cikin fara'a Safna tace to, Sannan sukayi sallama Khairat ta juya zata fita sai kuma ta juyo ta kalli Mr-Fauzan tace."Mummy tace ka kira ta."Okay Mr-Fauzan yace, Sannan Khairat ta juya ta wuce.*FACEBOOK@SEEMALUV HAUSA NOVELS**....B'OYAYYEN**AL'AMARI**_UNIQUE WRITERS ASSOCIATION_*® ```Written```By*_Seemaluv_*https://www.facebook.com/groups/1649808818646464/```MASOYA NA DUK NAGA SAK'ON NIN KU KUMA NA GODE MATUK'A, GA MASU COMPLAIN AKAN PAGE 54-55 CEWAR WAYEWAR DA NA SAMA SAFNA TAYI YAWA, TO BARI DAI NA TUNA MUKU ' KAR KU MANTA SAFNA TAYI SECONDARY SCHOOL AKWAI WASU WORDS D'IN DA ZATA IYA FAD'I KUMA AKWAI ABUBUWAN DA ZATA IYA YI, SABODA HAKA BABU YADDA ZA'AYI ACE SAFNA BATASAN KOMAI BA... SABIDA HAKA KU RUK'A TUNA BAYA```*56-57*Bayan wucewar Khairat ne, Mr-Fauzan ya tashi gamida kamo hannun Safna suka nufi dinning.Mr-Fauzan kujera yaja ma Safna ta zauna, Sannan shima ya zauna a side d'in ta.Hannu yasa zai yi serving d'insu Safna tayi hanzarin tsaida shi ta hanyar rik'e mashi hannu."Bari in zuba."Ta fad'i haka tare da mik'ewa tsaye.Mr-Fauzan smiling kawai yayi, Safna tayi serving d'insu, A plate d'aya ta zuba abincin ta koma ta zauna.Mr-Fauzan spoon d'aya yayi ya fara feeding d'in ta, Tun tana kauda kai alaman k'oshi harta hak'ura Mr-Fauzan ya dunga feeding d'inta."Na k'oshi, Kai fa bakaci komai."Safna ta fad'i haka tare da ansan spoon d'in itama tafara feeding nashi.Sai da ya k'oshi sannan ya sha warm water, Ya tashitare da cewa."Ya kamata in kira Mummy, Inji."Mr-Fauzan tashi yayi ya tafi d'aki Safna ta bishi da kallo.Bayan isarshi d'aki ne ya d'auki wayar shi yayi dialing number d'in Mummy.Bayan Mummy ta d'aga wayar ne suka gaisa, Sannan Mummy tace."Son?, Meya hana ka kira na tund'azu?.""Kiyi hak'uri Mummy, Ban..."Mr-Fauzan bai kaiga k'arasa maganar ba Mummy tadakatar dashi da cewa."Come on! yi min shuru! Wato tun yanzu zaka fara zama shanyayye ko Fauzan? Har zaka iya bud'e bakikacemin baka sami lokaci ba ko?.""Mum... You' please take things easy Yanzu na gamabreakfast shiyasa."Cewar Mr-Fauzan."Fauzan... Inason ka kawo min matar ka gobe, Gobe nake son ganin ta."Mummy ta fad'i haka cikin fad'a.Mr-Fauzan shuru yayi nad'an lokaci, Sannan yace."To shikenan Mom, Allah ya kaimu."Ameen Mummy tace ta kashe wayar ta.Nan Mr-Fauzan ya koma saman kujera ya zauna yayi shuru nad'an lokaci, Sannan yayi dialing number d'in Sir-Kamal.Ringing d'aya tayi Sir-Kamal ya d'aga wayar, Bayan sun gaisa ne Mr-Fauzan yace."I hope komai na company yana tafiya yadda ya kamata.""Yes Sir, Komai lafiya lau, Amma Sir lafiya kwana biyu?.""Oh you want to tell me that ' baka san nayi aure ba ko?."Cewar Mr-Fauzan.Sir-Kamal murmushin k'arfin hali yayi gamida cewa."No Sir, Gaskiya ban sani but in any way... Ina taya ka murna.""Thank you Kamal, Insha Allah gobe zan lek'o ai induba komai."Ok Sir-Kamal yace, Sannan Mr-Fauzan ya kashe wayar.Komawa parlor yayi ya iske Safna harta kai plate d'in kitchen ta dawo ta zauna.Mr-Fauzan zuwa yayi ya zauna kusa da ita yana satar kallon ta."Tana da kyau... But ba tada wayewa! Da zata sami wayewa toda babu Wanda zai kaini morewa."Mr-Fauzan ya fad'i haka a zuciyar shi.Safna dai kanta a sunkuye yake cike da kunya.Mr-Fauzan na cikin wannan sak'e sak'en ne wayar shi tai k'ara alaman kira.Dubawa yayi yaga Hajia Salima, Nan yayi saurin d'aga wayar tare da karawa a kunne."Hajia Salima."Cewar Mr-Fauzan."Mr-Fauzan, Ashe ana jinku? Kwana biyu babu motsin ka sam shine nace bari na gwada kiran ka thought ma ka cenja number ne.""Haba Hajia Salima! A'a ko kad'an kawai dai ayyuka ne sukai yawa."Mr-Fauzan ya fad'i haka tare da shafa hannun Safna."Naji ance kayi aure! Shine babu ko gayyata balle ka kawomin amaryar nayi mata gyara na musamman.""Oh Kinsan da yake abinne a gurguje akayi, But this isn't a big deal amarya tana gida anytime ' you're always welcome.""Alright then, Insha Allah gobe zaka ganni ' Saika turomin address d'inka."OK kawai Mr-Fauzan yace, Sannan sukayi sallama ya kashe wayar.Hajia Salima babban mace ce wacce tayi suna wajen gyara rayuwar ma'aurata, Kuma take bata gudunmawa wajen ganin ta wayar da kan ma'aurata.Hajia Salima ta ware babban fage na girke girke domin 'yan mata dama matan aure baki d'aya.Mr-Fauzan da hajia Salima friends ne sosai domin kuwa sunsan junan su tun suna k'anana.Safna hannun ta ' ta janye daga hannun Mr-Fauzan, Domin jin yadda tsigar jikinta ke tashi."Why?."Cewar Mr-Fauzan."Kawai bana so ne.""Baby na, You are not a young girl fa ' you're matured enough, Don't you think zan cutu idan biki barni ba?."Safna sunkuyar da kai tayi gaban ta na fad'uwa.Mr-Fauzan kwanciya yayi saman cinyar ta tare da winking d'in ta, Hakan yasa Safna sa hannu biyu ta rufe fuskarta tana murmushi."So let me make love to you..."Mr-Fauzan hannu yasa ya cire hannayen ta data rufe fuskar, Ya d'an d'ago kad'an yana k'ok'arin pecking d'in ta, Wayar shi tayi k'ara.Mr-Fauzan ajiyar zuciya ya saki gamida tashi zaune ya duba wanda ke kiran shi.Ganin Suhailah ce yasa shi jan tsuki tare da rejectingcall d'in.Sake ganin wani kiran yayi ya shigo hakan yasa shi d'aga wayar a fusace."What is it!."Cewar Mr-Fauzan."Oh just because kayi aure shine zaka rik'a rejecting mun call?.""Me kike buk'ata?."Jin haka yasa Safna d'ago lulu eyes d'inta ta kalle shi."Fauzan kai nake buk'ata... In fact ka fito waje ina bakin gate d'in gidan ka if not zan shigo ciki kawai.""Don't try that trashy! Gani nan fitowa."Abinda ya furta kenan ya kashe wayar tare da jan d'an k'aramin tsuki."Lafiya kuwa?."Cewar Safna."Lafiya lau Baby, Ina zuwa."Ya fad'i haka tare da tashi, Mr-Fauzan fita yayi ya lek'a waje.Hango motar Suhailah yayi tayi parking a gefe tana jiran shi.Mr-Fauzan k'arasawa yayi wajen ya bud'e motar ya shiga rai a b'ace."What is it Suhailah!, Na baki 10 minutes ki fad'i duk abinda ya kawo ki."Mr-Fauzan ya fad'i haka."Divine! Wato don kayi aure shine zakana fad'amin wad'an nan maganganun Right Fauzan? Ko ba komai akwai soyayya tsakanin mu and I still love you...""Enough of this please! Suhailah mata ta ' ta fiye min ke da komai! So is better kisan inda dare yayi miki because I love my wife so much.""K'arya ne! K'arya ne wallahi don ni kad'ai aka yo ka Fauzan, Wannan k'azamar bata isa ba wallahi.... Andam willing to do anything just to have you back."Mr-Fauzan tsaki yaja ya bud'e mota zai fita tayi saurin rik'o mashi hannu."Please Sweetheart don't leave, Ya kamata ka gane bakaimin adalci ba, But is ok akwai wata rana da zaka fahimci cewa wannan k'azamar matar taka kud'in ka kawai take so not you."Mr-Fauzan wani mugun kallo ya watso mata gami da cewa."Karki zama shaid'iya mana Suhailah, Kije kiyi aure that's just the fact because I will not marry Suhailah."Nan yasa kai zai fita ta sake rik'o hannun shi, Mr-Fauzan juyowa yayi ya kalle ta ' ta sakar mashi smiling."Don't worry... Dama gift na kawo maka tunda ka zama ango."Ta fad'i haka tare da sanya hannun ta cikin hand bagd'inta, Perfume ta d'auko ta bud'e ta fesa mashi a jiki."Ha'a are you out of your sense? Meye haka?."Mr-Fauzan ya fad'i haka cikin b'acin rai."Is that a sin? Perfume ne fa nothing else... Inaso kajiko k'amshin yayi maka ne.""Ok then, Thank you."Nan ta mik'a mashi perfume d'in ya ansa ya wuce.Suhailah binshi tayi da kallo har ya b'ille, Wata muguwar dariya ta saki cike da k'yak'yatawa."Wai wani ' ha'a are you out of your sense? Matsoraci kawai Wannan auran daka ke ik'irarin kayishi ' to saina lalata shi, Fauzan bazai yiwu ba! Ni inbanda abin na miji ' me Fauzan ya gani jikin wannan k'azamar?."Suhailah ta fad'i haka tare da jan tsuki ta tada motar ta ta wuce.Bayan shigan Mr-Fauzan gida ne ' ya iske Safna a zaune kamar yadda ya barta tana kallo.Kusa da ita yaje ya zauna gamida cusa fuskar shi jikin wuyanta yana shak'ar k'amshin turaren ta."Baby na...""Na'am.""Ina son inji kina min surutu kina bani labari mai dad'i, Kuma inaso ki fad'amin sunan da zaki ruk'a kira na da shi."Safna murmushi tayi cikin jin kunya, Sannan tace."Zan ruk'a kiran ka da my Man, Yayi?."Tayi tambayar tana janye jikin ta."Uhhh Baby na, Yayi sosai."Pecking d'inta yayi ya tashi ya nufi d'akin shi tare da cewa."Ki same ni d'aki na muyi magana."Abinda yace kenan ya wuce, Safna binshi tayi da kallo daga bisani ta sauke ajiyar zuciya sannan ta tashi ta nuf'i d'akin nashi.Bayan shigan tane d'auke da sallamar ta taji ya rufe k'ofar gamida saka key.Kasancewar d'akin akwai duhu shiyasa ta kasa ganeinda yake."My Man..."Bata kaiga k'arasawa ba taji ya rungumo ta tabaya hakan yasa taji wani tsam ya ratsa jikin ta.Mr-Fauzan juyo ta yayi suna kallon juna, Nan Safna ta lura daga shi sai boxer hakan yasa gaban ta ya fad'i."Inaso in kusanci matata yau, Baby na..."Mr-Fauzan yayi maganar in husky voice.Safna runtse ido tayi jikin ta ya fara rawa, Mr-Fauzan shafata ya farayi yana squeezing d'inta ta ko'ina."Bazan iya danne feelings d'in da nake ji ba Baby..."Yayi maganar yana sakin numfashi mai k'arfi.Mr-Fauzan rungume Safna yayi tsam a jikin shi yanasauke ajiyar zuciya, Hannu yasa ya zuge zip d'in rigar ta.Jin hakan yasa Safna tayi saurin danne rigar jikin k'irjin ta tana girgiza kai k'afafun ta na rawa."Don Allah, Kayi hak'uri...."Safna tayi maganar cikin kuka."No Baby... Please don't... Don't stop me ' in kikayi haka zaki cutar dani.... Please let me."Mr-Fauzan ya fad'i haka gamida d'aukar Safna cak tamkar wata jaririya.Bai tsaya ko ina ba sai a saman faffad'an gadon shi.*FACEBOOK@SEEMALUV HAUSA NOVELS.*57

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *