Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Thursday, May 23, 2019

MUNA TARE complete | Dandalin Hausa Novels

adsense here
MUNA TARE complete | Dandalin Hausa Novels

MUNA TARE complete | Dandalin Hausa Novels

[2/19, 4:49 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
              💝💝
*MUNA* *TARE*

      Na
Hapsat musa


*PERFECT WRITERS  FORUM!.*
          *(PWF)*









*Dasunan* *Allah* *mai* *Rahma* *Mai* *jin* *Kai*

*Ina godiya ga Allah daya bani damar yin wani tsokaci gameda abinda yake faruwa cikin al'ummar mu na yau da kullum.Allah kasa yadda nafara littafin nan lafiya kasa in gama lafiya.*


*Banyi wannan labarin dan cin zarafin wata ko wani ba face kirkirarren labari ne.All the characters in this novel are fictitious and has nothing to do with any living person.*


*Da bazarki muke taka rawa kungiya me albarka wato PERFECT WRITERS FORUM.ina alfahari dake matuka.Har Dama en uwana writers dake ciki.Allah yadada hade kanmu.*

*Gaisuwarki ta dabance shugabar kungiyar mu mai albarka wato perfect writers forum. FATTY AZLAND.Allah ya tayaki riko...*

*All rights reserved!!!*



1-5....

      Sauri k'awai take don ta isa
gida takaima innarta garin tuwo, don ta tuka masu suci domin d'uk yinin ranar babu abinda suka, sai yanzu d'a baban yadawo daga wurin sana'ar facin sa yasamo musu kudin masaran tuwon d'a zasuci.

Sauri k'awai tak'e bataji horn din d'a mota take mata ba,
wata horn din da motar tayi ne ya razana yar budurwar d'ake tafiya tasaki garin dake bisa kanta yafadi yazube, , babu wani saurin moriyar dazaiyi,
Kuka tasaka ta durkusa inda garin yazube,
Cikin ranta Kuwa cewa take Yanzu yazamuyi gashi shikadai ne Abinda Baba ya samo mana?

Alamun motsin mutum taji bayanta yace sannu kinji yan Mata meke damunki, inatayi miki horn bakijiba??

Gashi kinzubar da garin duka babu wani sauran moruwa dazaiyi.

Zaro kudi yayi daga Aljihun wandon shi yayi, yace mata amshi kije kisake wani ko? mikewa tayi cikin Sauri Tace A,a, Inna tahani Amsar kudin wadda bansani ba.

Murmushi yayi yace k'anwata ai ba rokana kikayiba ko? amshi Tace Allah bazan
Amsa ba.

Daukar kwaryarta tayi, shi kam tsaye yayi
Yana kallonta har tashige wani lungun,
Sanna yashiga motar sa yaja.

    "Isarta kenan ta iske Inna Tana Daka kayan miyar daza'ayi tuwo,

Baba kuma yana gefe yana shirin alwalar magariba domin takusa.

Sallama tayi cikin sanyi jiki,
Inna tadago da fuskarta tace Ina garin dakika tafi  Kai nika??

Matsar waye tafara yi, tace  Inna wallahi Ina tafiya wani mai mota ya firgitani har garin yabare,Kiyi Hakuri don Allah,

Inna tace wannan tsoro naki Jidda har ina? Yanzu ya zamuyi to??

Baba dake gefe tun shigowarta beyi magana sai sannan yace kaddarace babu komai, Kinji Jiddar Baba dauki ruwa kiyi alwala.

Yajuyo wajen Inna yace a cigaba d'a aiki Allah bazai hana Abinda za'ayi ba in shaa Allah.

Inna fito sallah zan biyo wajen  Usman mai gari kila yabani bashi, gobe insha Allah nafita kasuwa zan bashi.

Inna tace shikenan malam
Allah yataimaka,
Nima bari nayi alwalar nayi sallah sannan naci gaba, nan yafita itama inna tayi Alwalla tashiga daki.


Bayan Baba yadawo yaci sa'a usman yabashi,Nan Inna ta tuka, sukaci.


    '' Jidda" ce kwance, tunanin  wanda ya tsorata ta har ta barar da Gari take,
Tace masu kudi wasu ashe sunada saukin kai
ba dukane yan wulakanci ba.

Hangoshi tayi sadda yace kanwata  Amshi ba roko na kikayi ba,tana cikin wannan tunanin ne har bacci yadauketa.


*Washe Gari*


      Jitayi Inna nacewa Jidda! Jidda!!

Kina nan kina baccin d'a kika saba ko?
Wanda in kika fara k'amar matatta, bazaki makarantar bane ??

"Zumbur ta mike tunowa tayi sunada test din English kuma
Malamin bashi da mutunchi,He can intentionally not allowed her in."

Inna wallahi inayin sallar Asuba kawai bacci sabo yazo man.

Cikin sauri ta tashi tadauraye fuskarta,tajawo uniform dinta Ash And white,riga da wando da dankawali duk ash
Sai hijabi white ta saka.

Inna tace Jidda wannnan saurin fa? ga tuwon can na dumama ki dibo kici sannan ki tafi ko?tace to inna.

K'itchen ta nufa cikin sauri ta ci sama sama,tace Inna test garemu kuma malamin bashi da kirki shiyasa kikaga inata sau'ri.

''Inna tamikomata wata tsohuwar naira 20 tace Amshi nan babanki yabaki da ita kawai ya kwana''

Jidda ta Amsa cikin tausayin Iyeyenta.

Tace Inna natafi
Inna tace Allah ya kiyaye, kuma ya bada sa'a ameen inna cewar jidda tasa kai ta fice.

    "Tafito Bakin hanya tasamu dan adaidata dazai kaita makaranta ko 30 ne Sbd tanada naira goma cikin jikka.

Tana tsaye bakin titi wata bakar mota ta tsaya gabanta.




_Edited By:_*PERFECT WRITERS FORUM.*
[2/19, 10:40 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
             💝💝
     *MUNA* *TARE*

          Na
Hapsat musa



*PERFECT* *WRITERS* *FORUM*


*(P* *W* *F*)



6_10





 Jidda tana tsaye bakin titi tana jiran motar da zata mikata school, Allah Allah kawai kar malamin English yashigo bata isa ba.

Wata bakar motace sai sheki takeyi tayi parking kusa da ita, zuge glass din motar akayi.

"Kanwata school za'a?"
Jidda tadago fuskarta, sai data tsorata ganin mutumin jiya.

Cikin muryata mai sanyi tace
"Ina kwana?"
Yace
"lafeeya lau, shigo nakaiki school din"
Jidda girgiza Kai tayi
Tace
"A'a Zan hau a daidaita sahu Yanzu"

Bata fuska yayi yace
"Jiya nabaki kudi kin ki Amsa ko? Yanzu kuma nace kishigo na kaiki school Kince A'a, ko kina  tsorona ne?"

Jidda tace
"A,a yazaayi bansakaba kawai sai nashiga motar ka?"

Murmushi kawai yayi yace
"Kedai kina tsoron kar nasaceki ko kanwata?"

Dakyar Jidda tashiga motar nan domin taga time sai tafiya yake, juyowa yayi yace
"wane School ne? Kinsan ni bako ko one year banyi A garinan ba"


Tace masa
" *KATSINA* *COLLEGE* *KATSINA*

Jidda tayi shiru domin wani kwarjini yakemata ga motar ta dume dawani fitanenen kamshi,
Harsuka iso school zaro duba daya yayi yabata, yace banason gardama Amshi kiyi breakfast.
Jidda zaro ido tayi tace
"Don Allah kayi Hakuri ban iya kashe wannnan kudin Anbani Inna zatayi fada"

Yayi dariya yace
"kicema innar yayanki yabaki
Yazuramata idanuwanshi masu firgita tun farkon haduwarsu"
Cikin sanyin jiki ta mika hannu ta Amsa.

Yabude Mata motar yace
"To kanwata Ayi karatu da yawa"

Murmushi kawai tayi ta nufi Section
Na yan science.
Har ta kulle ya binta da Kallo
Komawa yayi  jingine kujera, ya jingina.
Wani yanayi yaji yana
Shiga cikin Ranshi, yace nasamu matar Aure tofa daganin sarki fawa sai miya tayi zaki
Amma muje zuwa
Tadata motar yayi yabar harabar school yana sake sake cikin Ranshi.


Jidda tana isa ta iske malam  Ibrahim bai shigoba.
Wurin zama kawai tanufa ta iske kawayenta,
Rukkayya Hamisu tare da Bil'atu Lawal.
Suna kara duba book din English kafin yashigo.

Itama wurin kawai tasamu ta zauna, 
Can rukkayya hamisu tadago
Fuskarta tace
"sister Ina kikasamu turare mai wannnan kamshin haka?"
Jidda tace
"Kai rukky banason sherri fa"
"Tace wallahi ba sharrin nayi
Tatabo beelatu Lawal data dukufa karatu,
Tace
"Sister beely sinsina Hijab din sis Jidda kinji?"

Beelatu tace
"Kai sister turaren yahadu
Inakika samoshi ne?"
Jidda ta sinsina hijab dinta wani fitatinan kamshi  taji tanayi hijab.
Maganar su ta katse ta sakamon shigowar malam Ibrahim.
Bayan sugaidashi, ya Amsa fuskar nan babu Almar fara'a.

Yarubata test jikin Allo dama kowa yasan dahaka.
Bayan yarubata
Yace minti 30 yabada kowa
Yakammalla
Yadinga zagaye class din domin yaga masu bude book dayakama, sai dai  yaketa  book din yakori mutum waje yagama zaman mashi class.
Minti 30 yana cika yana Amsa.
Yafita nan Aji yakaure da hayaniya,
Rukky hamisu tace
"sister baki fadaman bafa"
Jidda tace
"Kedai baki mantuwa wallahi"
Nan tafadamusu yadda suka hadu.
 Haryanzu dayakowata school
Malamar Islamic ce ta shigo,
Double period gareta daga ita sai break.
Bayan sunfito breakfast ne
Jidda Tace, bazata jeba.
Kan table ta kwantar da kanta
Tana tunanin mutumin jiya wadda batasan sunan shi ba haryanzu.
Jawo hijab dinta tayi takara kanga da hancinta
Wani lumshe ido tayi domin
Kamshi yayimata.


Lokacin tashi school yayi
Suka fito itada Kawayenta, nakusa da ita rukky And beely.

Har harabar makaranta suka fito suka tsaida nepep sukace ma Jidda tazo tashiga
Tace A'a Zan tafi kasa Inna ta Aikeni,
Domin ita har Ga Allah batason doramusu dawainiya.

Tafara tafiyarta har dutsin safe, tagaji sosai tashigo cikin gida.

Cikin sallamarta ta shiga.
Inna tana bakin muguji tana
Shirin sallar Azahar, Jidda daki kawai tashiga tacire uniform dinta tashiga wanka.
Tana fitowa Alwalla kawai tayi tashige daki,
Domin bada farali,

Tana gamawa tayi Addu' a tanufi dakin Inna   tace
"Inna nadawo kuma yunwa nakeji"

Inna tace
"Gashi kuma Jidda Babanki bai dawo ba har yanzu, ko zaki je can bakin Hanyar kisamomana wani abin  dazamuci,
  Nima tuntafiyarki wannnan dumamen na ida ci"

Jidda tace
"to Inna Bari naje"
Zura hijab kawai tayi tafito
Bakin titi inda  Babanta ke faci tayi.
Tana isa ta iske yana facin din wani mashin,
Ga Rana duk gumi ya gauraye masa fuska.

Cike da tausayin kamar tayi kuka tayi sallama

Malam Abdullahi yadago fuskar datayi sharkab da gumi yace 
"Jiddan baba kun jini shiru KO?"
Yanzu Aikin yazo tundazu zaune nake
Yazaro hamsin daga Aljihun shi
Yace
"Gaya nan kuje ku siya
Garin kwaki kafin Anjima muga Abinda Allah zaiyi"

Jidda tace
"To shikenan baba"
Tajuya tatafi cike da tausayi.

Tafara tafiya taje shagon Usman tasiyi gari da sugar.
Gabanta yawani yanke yafadi.


"Tofa meya tsorata Jidda ne?"


*Kubiyo yar mutanen katsinawan dikko kuji komai*




*```EDITED BY; PERFECT WRITERS FORUM```*
[2/20, 2:44 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
            💝💝
          *MUNA* *TARE*
            
             Na
Hapsat musa

*Prefect* *Writes* *forum*



*(P* *W* *F*)
        



11_15






"Jidda" tana  tafiyarta cikin natsuwa, domin, zuwa shagon, Usman  siyo garin kwaki.

Gaban yawani yanke, yafadi
Ganin mutum tayi tsaye, gabanta,
Add'ua tashiga tace wayyo ni Jidda ko nayi gamo
da Aljani ne,?

Kota Ina nabi sai na ganshi
 Ida karasowa yayi inda take,
Fuskar shi dauke, da murmushi, mai Kara masa  kwarjini, A fuska,

"Yace" kanwata   kinfara tsorata  dani ko??

Jidda babu Abinda  tace sai dai dukar  da fuska tayi domin kwarjini yakemata,

Yace inazaki ne??

Jidda "tace  naje. Gurin baba ne,

Yace kanwata kinga  ba mutunchi bane na tsayar dake bakin hanya,

Muje naraki har gida  domin
Inason muzama yan uwa nidake,

"Jidda tadago fuskarta, ta kalleshi, jin maganar, dayayi,

Yace ko bancanci haka bane??

Jidda babu Abinda tace dai yace muje,

Jidda batace komai  har suka isa kofar gidansu,

" Yace"naga gidanmu sai Anjima

Bai tsaya saurerenta yajuya yatafi,

Jidda  har ya kulle tadaina ganinshi sannan ta juya ta koma shagon Usman ta siyo garin sanna tashiga  cikin gida,

Inna  "tace" Jidda sai yanzu kikadawo??

"Tace" inna shagon Usman din, Akwai jira saida mutanen suka  ragene,

Inna "tace" shikenan mai kika samona wajen baban nakine??

Jidda naira hamsi ce yabayar yace  kan Anjima Aga Abinda hali yayi,

Inna " tace" tom Allah ya kyauta Jidda tace Ameen.





Jidda  tatashi ta dauko Kofi suka jika wannnan garin sukaci,

Shigewa Da'ki tayi kwanciya tayi bisa katifar ta tadinga tunani wannnan mutumin,
Wadda har yanzu batasan sunanshi ba,




Can Baba yadawo da marece yasamo musu na Abinchi 

Baba suna zaune suna fira da su jidda Inna kuma ta Dora sanwa tana tankaden garin,

Wani yaro yashigo dan makotansu,

Baba kazo wani dan gayu mai mota yana sallama
Dakai,

Jidda jitayi gabanta ya yanke yafadi Amma Bata nuna ba,

 Baba yazuri takalmishi muje Abbas, yaron daaka Aiko,


Jidda tashiga tunani jitayi Baba nacewa shigo,

Sallama kawai taji tasan wannan mutumin wadda har yanzu batasan sunanshi

Jiddar baba dauko tabarma
A shimfida mashi,
Dasauri Jidda tadauko
Tabarma
Baba yace zauna bawan  Allah,

Samun wurin yayi yazauna
Baba yajuyo wajen sa yace kanason magana Dani  shine nace kashigo ciki muyi
Magana,

Cikin murmushi kodayaushe yace baba nidai sunana.....


Muje zuwa.
[2/20, 11:52 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝                   💝💝
          *MUNA* *TARE*
 💝💝                   💝💝
              Na
    ©Hapsat musa

® *P.W.F*



*16_20*





_Cikin murmushin shi yace "Baba Sunana Abdul    hameed Hamza Naira Banza.!"
 
Baba mikewa yayi cike da razana kafun yace "Alhaji Hqmza naira banza de wanda nake ji
'Cikin Radion.?"

"Yaro mekake b'id'a daga gare mu ne? 'Shin baka ga  yadda muke ba?"

Abdul hameed  yace "Baba kazauna bana b'id'arku da komai b'ace Alkhairi".!

Jin haka yasa baban ya koma  ya zauna kamar yedda ya bukata.

Abdul hameed yachi gaba da fad'in "Baba
Karka damu don kaji wanene maihaifina, Wallahi ni bana la'akari da dukiyar maifina sam".

"Inaso kad'aukeni tamkar d'anka na cikinka baba."

Yakara da cewa "Nahad'u da Jidda ne rana ta farko."
nande yakwashe komai ya fadamishi!

Ya kara da cewa "Baba tun daganan Jidda ta ringa burgeni matuka.
Naji inason nazama yayanta
Nikuma nazamo d'anku,idan har kun amince min da hakan.!"

  Sai asannan Baba ya maida numfashi kafun yasoma mishi magana "Yaro naji zancikanka duka."

    "Kaganni nan.!?"

"Sunana  Malam Abdullahi mai faci,Sana'a ta itace    faci,
Ina zaune da 'yata Jidda sai kuma maifiyarta watau lubah".

"Kaga dai yadda  muke Kullum sai nafita nasamo Abinda zamuci sannan.
Amma kaji kana ra'ayin kazauna damu.?"

Abdul hameed  yace "Baba ai babu wadda yafi wani wurin Allah sai wadda yafishi tsoronshi!"

Baba yace "hakane, Tou Allah yashigemana gaba".
Hameed ya amsa da "Ameen"

Kiraye kirayen sallah ne yasasu tashi suka nufi masallachi.
           
   
  *WAYE* *HAMEED??*


Hameed dane ga Alhaji Hamza Naira Banza;Alhaji hamza yanada dukiya mai tarin yawa wadda shikanshi baisan adadinta ba.Yanada 'ya'yaa ukku,  Hameed shine na farko sa'annan k'annenshi watau
Hanan da Hanifa.

Hameed yayi  karatunshi duka a kasar America. Illah primary kawai da yayi A Ulub-Arab dake nan katsina.
  Suna zaune ne anan unguwar 'kwado'.

Alhaji hamza naira banza ya tsani talaka baya harka da talaka ko kad'an. Domin yace harka da talaka lalurane.
Hameed ya tsani wannan halin na maifinshi
ko maihafiyar hameed Hajiya zainab batason wannan halin na mijinta,
Shiyasa haneefa da hanan suka taso da irin wannan halin na maifinsu sun tsani talaka suma Hajiya zainab na kwatanta musu amma sam basuji,

 Had'uwar Shi da Jidda kuwa sanadiyar zuwan shi  wani gidan gonar maifinshi ne dake anan unguwar su Jiddan, Tun daganan yaji jidda ta kwanta mashi Cikin Ranshi,

Hameee dogo ne k'yakk'yawa ajin karshe afagen had'uwa.wanda turawa ke fad'i aturance da(Handsome Guy)!

Wannan kenan;

Ya tarayyan su zata kasance dasu Jidda..? Gashi Jidda ta yi mishi Amma maihafinshi yatsani talaka.

Hmmn..Kude Biyoni Danjin Yadda Zasu Kasance.!

_Wasa farin girki.._
[2/21, 1:31 PM] Hapsat musa 💝: *💝💝MUNA* *TARE*💝💝
💝💝.                           💝💝

               Na
Hafsat    Musa


® *P*. *W*. *F*




*21*_*25*





       Bayan sati daya
 

Wasa wasa Hameed yazama dan gidan su Jidda baya kwana biyu bai zoba. 

Inna ce zaune yau tana rairaye shinkafa  yar Hausa
Jidda kuma tana  D'aki Domin yau ko school bata jeba zazzabi ya matsamata,
Inna gani tayi Ana shigowa jarkar mai, buhun shinkafa, kwalin taliya,
 
Mikewa tayi tace" bayin Allah nan Akace ko kawo ne ? Naga sai shigowa kuke dasu"
Sukace  Eh wadda yasamu yanan waje
Sallamar Hameed ta katse komai, yace" inna ninace su shigo dasu" zaro kudi yazaro daga Alhjihun ya sallami wadda suka kawo,

Hameed yace" Inna  inazaashigarmiki dasu kinsan lokacin damina kar ruwa ya sakko"?

  Inna tace" nibanma san Abinda zancemaka bane yaro"   Hameed yace" Inna don Allah karkice komai kidauka tamkar  danki don Allah "
Shigar dakayan yayi dakin Baba,

  Inna wai Ina Jidda ne banji motsinta bane?
Inna tace" Jidda tana D'aki zazzabi ya rufemata bakaga yau ko makaranta batajeba"

Shiga D'aki yayi kawai yayi ya isketa lullube da mayafi,
Jidda! Jidda!!    Tashi muje Asibiti, bude Fuska tayi "tace
Yaya Hameed yaushe kazo"??  Yace" yanzu nazo yanzu" tashi muje

Cikin shagwabarta wadda tazamemata jiki "tace Yaya hameed nasha magani"
"Yace Banason Gardama fa"

   Inajiranki  waje fitowa yayi .
Mikewa tayi tafito ta iske Inna zaune tana bakacen shinkafarta
Inna wai kinji Abinda yaya Hameed yace wai nashirya muje Asibiti kuma naji sauki,
Wallahi,
Inna juyowa tayi wajen Hameed da yakame tace "
Tokaji yayan Jidda taji sauki,
Dama tana irin wannan zazzabi lokaci daya yake sauka kuma". Yace" shikenan Inna  Allah yakara Afuwa"

Baba daya dawo yaga kayan da Hameed yakawo  rasa bakin godiya kawai yayi.


               Bayan wata biyu

Karkuso kuga shakuwar da Hameed yayi tsakaninshi da su Inna har tuwon dare yake zuwa ci gidan.
Sun shaku da Jidda sosai Amma bai taba furta Mata wata kalma ta soba

Yauma zaune suke suna karatu domin Exam  su Jidda keyi tafita daga secondary school.
Hameed cikin Ranshi ranar dasu Jidda suka kammala exam Domin kingin biyu su idar ranar zai fadama su Inna burinshi nason Jidda.
 
Bayan sun kammalla karatu ne Hameed yayi bankwana dasu Inna yatafi gida

Yanashiga ya iske Dadyn shi da kannanshi falo
Shima samun wuri shima yayi yazauna,

Dady yajuyo wajen Hameed yace" wai Hameed Ina kake zuwa ne kwana biyu?
Kokasamana surika ne??"
Hameed yace" dady zanfada nan da kwana biyu domin inason Ayi komai  da wuri "

Hanan tayi charaf tace" yaya yar wacece Akasamana"??
Harereta kawai yayi yashige D'akinshi
Hajiya zainab Kuwa murmushi kawai tayi.





KARSHEN TIKA TIK.


Yau su Jidda suka kammala exam din fita daga secondary school suna ta photo na  da yan school dinsu   na bankwana sunata Amsar number juna,


Jidda tashigo gida gajiye turus tayi ganin yaya Hameed tayi ba lokacin zuwanshi ba

Yaya hameed naga ba lokacin zuwanka kazo?
Mikewa yayi   yace"nazo taya kanwata murna ne,"
Murmushi kawai tayi zaro wani Envelope yayi daga Aljihunshi zandawo Anjima,

Inna tafito tace Aaa harkatashi hameed "yace Eh Inna zandawo Anjima   cin tuwo"
Tace" shikenan to saikadawo,

Jidda Kuwa shigewa D'aki tayi domin taga Abinda yayanta yarubuta ta

Can nahango perfect writes forum suna leken Abinda yarubutu😜

Kubiyoni zakuji komai.
[2/21, 4:34 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝    
💝💝💝

💝💝💝💝
            💝💝
            *MUNA* *TARE*
                Na
Hapsat musa
®
 P.W. F.




*26*_*30*





Jidda tana shiga D'aki
Bude Envelope din da Hameed yabata tayi. Wani kamshi ne yabugeta sai data rumtse ido,
Tana budawa taga sakon kamar haka,

_Assalamu_ _Alaikum_ _kanwata_
_inayi_Miki _murna_ _da_ _kamalla_ _Exam_ lafeeya
_Allah_yafiddo _result_ mai _kyau_
_Bayan_haka _kanwata_ _zakiyi_ _Mamakin_ ganin _wani_sako _daga_ _gareni_ _babu_mamaki cikin _magana_ta

_wallahi_ _Jidda_ _tun_lokacin _da_ idanuwana _sukayi_ _Arba_ _da_ kyakyawar fuskar ki
_zuciya_take _kaunarki_
_Ina_jiran Amsa
*ILOVE* *YOU* *MY* *JIDDA*


Jidda linke takardata tayi tadora Akan kirjinta murmushi tayi "tace  yaya Hameed nima tuni zuciyata ta tsunduma cikin kaunarka"
 Samun maboya tayi taboye takarda tafito  tsakar gida taya Inna Aiki

Babane yashigo  Domin yanzu ba kasawaye yake zuwa  wurin Faci ba domin  Hameed yana kuladashi kamar me, tamkar shi ya haifeshi,
Baba "yace Jidda baba Angama  jarabbawa kuma sai Aure KO??"
Jidda " tace Baba Ai nayi karama" dayin Aure "

Baba "yace  gidanku"

Jidda duk yini yau bata fito gudun kar Hameed ya isketa tsakar gida
Can bayan Angama sallar magariba sai gashi kuma
Kamar yadda yasaba zuwa
Amma har yatafi Jidda bata yarda suka hadu sai dai taji firarshi dasu Inna,

Anfi sati Jidda suna wasan boye da Hameed basu haduwa

Kwatsam!!! Ranan batasan ran zuwanshi kamar haka tana waje tayi shimfida tana kwance Inna kuma nadaki batajin dadi,
Sallama taji saida gabanta yafadi dasauri tatashi Yaya Hameed  sannu da zuwa
Harerenta yayi " yace bazan Amsa kingam guduna kamar dodo??"

Sunne fuska tayi "tace  bahakabane yaya Hameed"
"Yace yayane to??"

Jidda "tace kunyar ka nakeji ne shiyasa"
Hameed "yace kunya nidanake fatan kizamo Mata gareni shine zakiji kunyata"
Jidda dai babu Abinda tace dai,
Hameed "yace Jidda babu yaudara Cikin magana ta Wallahi tallahi inasonki
Inakaunarki fatan kizamo Mata ta"
Nan Hameed yakashe Jidda da kalamshi har ta Aminche zata so Hameed kamar yadda yakesonta,


               Bayan wata 1


Su Inna sun fahimci Akwai soyaya tsakanin hameed da Jidda sunyi  murna domin hameed yaro ne nutsase

Hameed yashigo  falon gidansu domin yau yakeson yafadama dadynshi yasamu matar Aure. Yayi sa'a kowa yana falon
Kusada Momyn shi yazauna
Fara Sosa keya yayi
Alhaji hamza naira banza "yace na Lura Akwai magana bakinka my son fadaman"
Hameed " yace  Dady sonake Aika gidansu  yarinyar danakeso ne"
Alhaji hamza naira banza"yace to My son
Yar wacece Acikin Nigeria wanene mahaifinta Acikin Nigeria, meye matsayinshi"

Tofa kunaga ida Alhaji hamza naira banza yaji kowacece Jidda zai Aminche Kuwa?? 

Muje zuwa
Luv you All my fans😘
[2/21, 11:58 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
            💝💝
            *MUNA* *TARE*
                 Na
Hapsat musa
®
P.W.F.





*30*_*34*

    


Hameed  cikin natsuwar shi "yace dady ba yar kowa ce sana'ar maihaifinta Faci yake suna zaune unguwar dakake da gidan gona"

Wani Mari Alhaji hamza naira banza ya watsa Hameed "yace mutumin banza mutumin wofi soyaya da talaka har kace kana son Aika gidansu to tun wurin kafidda zaka Aureta domim bazan taba hada zuriya da talaka ba"

Fuu yafice daga katafaren falon

Hanan "tace kaima yaya karasa wadda zaka Aura sai yar mai faci" dakamata tsawa yayi dagudu sukatashi sukabar falon.
Akabarshi dagashi sai mommy shi,
Hajiya "tace narasa wannnan Dabi'a ta Alhaji wai ta tsanar talaka yasani da mai kudi da talaka duk daya ne wajen Allah sai wadda yafi tsoronshi"

Hameed "yace momy natsani wannnan Hali na dady wallahi"
Hajiya zainab "tace kaita Add'ua kawai Allah yashugimana Gaba"
"Yace Ameen momy"
Yatashi yabar falon yashige D'akin sa





Jidda da Hameed zaune suna fira Inna tashige Cikin D'aki Domin tunda ta Lura Akwai wani Abu tsakanin    Jidda da Hameed dayazo suka gaisa sai tashige D'aki

Hameed " yace my Jidda"
"Take na'am  yayana"
"Yace Inasonki wallahi bazan taba iya yaudaraki ba
Sonki yariga yabi jikina inda har ko sonki da kaunar ki zai fita. Jikina sai Antatse jinin da kejikina da kuma jinin da ke harbawa cikin zuciyata jidda"

Jidda cikin kunya "tace yayana nima inasonka *MUNA* *TARE* ABadan da'iman"

Hameed zaro wani zobe yayi daga hannunshi "yace My Jidda karbi kisa A hannuki" Amsa tayi tasa yayimata masifar kyau.
Hameed "yace My Jidda tamkar zuciyata nabaki  ban iya kallon ko wace mace Dasunan so kamar tayaya Zan furta Kalmar so ma gareta nariga na Mallaka Miki zuciyar"

Jidda itama zaro zoben Azurfar da mamansu belly taje makka takawomata tsaravarshi,
"Tace yayana ga Alkwali nima na mallaka maka nima, tamkar yadda kafada,
*MUNA* *TARE* ruwa ko iska bazai taba rabamu ba"

Hammed "yace zanceki hakkun ne My heart beat
Numfashi tare yake bugawa fuskokin mu daya, haka  ruhinmu, zuciyarmu daya,
Wajen zaman mu daya, Anan Cikin duniya Har ma Acan *MUNA* *TARE"*

Jidda da Hameed sunyi ma Kansu Alkwali duk rintsi duk tsanani  suna  tare.
Saida Baba yadawo suka katse firanan,
Lokacin sallah yayi Hameed da Baba sukayi yadawo yaci Abinchi sannan yatafi badon yagaji da kallon Hasken Ranshi ba.
[2/22, 12:11 AM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
            💝💝
            *MUNA* *TARE*
                 Na
Hapsat musa
®
P.W.F.





*30*_*34*

    


Hameed  cikin natsuwar shi "yace dady ba yar kowa ce sana'ar maihaifinta Faci"

Wani Mari Alhaji hamza naira banza ya watsa Hameed "yace mutumin banza mutumin wofi soyaya da talaka har kace kana son Aika gidansu to tun wurin kafidda zaka Aureta domim bazan taba hada zuriya da talaka ba"

Fuu yafice daga katafaren falon

Hanan "tace kaima yaya karasa wadda zaka Aura sai yar mai faci" dakamata tsawa yayi dagudu sukatashi sukabar falon.
Akabarshi dagashi sai mommy shi,
Hajiya "tace narasa wannnan Dabi'a ta Alhaji wai ta tsanar talaka yasani da mai kudi da talaka duk daya ne wajen Allah sai wadda yafi tsoronshi"

Hameed "yace momy natsani wannnan Hali na dady wallahi"
Hajiya zainab "tace kaita Add'ua kawai Allah yashugimana Gaba"
"Yace Ameen momy"
Yatashi yabar falon yashige D'akin sa





Jidda da Hameed zaune suna fira Inna tashige Cikin D'aki Domin tunda ta Lura Akwai wani Abu tsakanin    Jidda da Hameed dayazo suka gaisa sai tashige D'aki

Hameed " yace my Jidda"
"Take na'am  yayana"
"Yace Inasonki wallahi bazan taba iya yaudaraki ba
Sonki yariga yabi jikina inda har ko sonki da kaunar ki zai fita. Jikina sai Antatse jinin da kejikina da kuma jinin da ke harbawa cikin zuciyata jidda"

Jidda cikin kunya "tace yayana nima inasonka *MUNA* *TARE* ABadan da'iman"

Hameed zaro wani zobe yayi daga hannunshi "yace My Jidda karbi kisa A hannuki" Amsa tayi tasa yayimata masifar kyau.
Hameed "yace My Jidda tamkar zuciyata nabaki  ban iya kallon ko wace mace Dasunan so kamar tayaya Zan furta Kalmar so ma gareta nariga na Mallaka Miki zuciyar"

Jidda itama zaro zoben Azurfar da mamansu belly taje makka takawomata tsaravarshi,
"Tace yayana ga Alkwali nima na mallaka maka nima, tamkar yadda kafada,
*MUNA* *TARE* ruwa ko iska bazai taba rabamu ba"

Hammed "yace zanceki hakkun ne My heart beat
Numfashi tare yake bugawa fuskokin mu daya, haka  ruhinmu, zuciyarmu daya,
Wajen zaman mu daya, Anan Cikin duniya Har ma Acan *MUNA* *TARE"*

Jidda da Hameed sunyi ma Kansu Alkwali duk rintsi duk tsanani  suna  tare.
Saida Baba yadawo suka katse firanan,
Lokacin sallah yayi Hameed da Baba sukayi yadawo yaci Abinchi sannan yatafi badon yagaji da kallon Hasken Ranshi ba.


           After five month


Soyayya Ake zubawa kamar me tsakanin hameed da Jidda duk ranar da Jidda bataga  Hameed batajin dadi cikin ranta ranar wuni zatayi  kamar wadda bata lafeeya,

Yauma zaune take tayi tagumi  Inna kuma tashiga makota Barka,
Sallama Akayi  Akashigo  bataji wake sallamar saida Aka dafata firgit ta razana
Kawayenta konace Amminta
Ruky And Belly tagani Kara tasaki tatashi ta rungumesu,
Murna kawai take, Rukky "tace sister Jidda wannnan tunaninfa?"beelatu "tace
Kedai ganemini Hanya sister"

Jidda "tace kunji komai uwayen tambaya mushiga ciki"
[2/22, 7:26 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
            💝💝
         *MUNA*  *TARE*

                Na

Hapsat musa
®
Perfect writes forum




*36*_*40*





D'aki. Suka shiga Jidda ta debomusu ruwam Randa masu sanyi  suka sha
Beelatu "tace sister shakamana"
Jidda "tace nidai narasa wannnan bin kwakwafi naku wallahi  zanfadamuku yanzu"

Rukky "tace kanfi Fara wai bazaki cigaba da karatu ba ne kinga ni da belly munsamu Admission A ummaru musa yar Aduwa fa"
Jidda "tace  Sainaje dakin mijina shima inyanaso inbayaso shikenan wadda nayi Allah yayi mishi Albarka"

Rukky suka hada bakisukace" lalai yayi Mrs Hameed"
"Tace ganifa ko kuna shakkun hakane"
Sukace A,a yafito mudai musha Biki nan"

Wayar Jidda yar Samsung dinan tayi Kara hameed yakawomata domim su dinga jin muryoyin juna

Dauko tanaga key to my life tayi murmushi mai kayatarwa
Cikin wata murya wadda bansan Jidda tana da ita nidai sai yanzu naji ta,
 Jitayi "tace  _Assalamu__Alaikum nurul kalbee na"
Hameed can daga bangaranshi _walaika_ salam   Sanyi idaniyata" (littafina mai zuwa)

Jidda "tace kabarni inata tunanin ka zuciyata takasamu natsuwa da Rashin ganinka Hanci bayason jin komai sai daddan kamshi turarenka
Idanuwana suna mararin kallonka,
Kunnuwana baso San jin komai sai murya ka"
Hameed yace" nima haka life partner  Amma karki Dani ganinan zuwa yanzu"
"Tace sai kazo  my future"

Rukky da belly Kuwa saki baki sukayi suna kallon ikon
God
Jidda "tace kuyi Hakuri my Aminnai in Ina waya da my Hameed mancewa nake da kowa"
 Rukky "tace Ai munga Alma ne"

Sukacigaba da firarsu ta Aminai har Inna tashigo suka gaisa 
Hameed ne yashigo Cikin sweet voice dinsa   Jidda Cikin murna "tace ga Heart beat dinan yazofa yau zaku ganshi"

Hameed   suka gaisa inna,
Yanufo dakin Jidda sallama yayi yashigo suduka suka Amsa mishi  nandanan kamshi  turenreshi ya gauraye D'aki
Hameed "yace my Jidda koki fadaman kiyi baki karnazo ko? "

Jidda "tace yayana wadannann ba baki bane Aminanai waddda nake fadamaka rukkaya hamisu, tareda beelatu Lawal"
,
Hameed "yace Amianmu sannuku"  sukace yauwa mijin  Aminiyarmu"
Murmushi kawai yayi "yace harnazama kenan "
Rukky "tace
 Meyarage To face Asamuku Rana"
Hameed yayi murmushi "yace ranar zanyi murna my Jidda tazama tawa"
Nan suka cigaba.  Da fira kamar sun Saba ne.

Su rukky suka mike zasu tafi  Hameed yace babu damuwa. Suzo yarage musu hanya.
Har kofar gida Jidda tarakosu,

Kallon Hameed tayi "tace ka kulamar da kanka yayana Allah ya tsareman Kai"
"Yace Ameen my Jidda"
Sukayi bankwana dasu rukky suka tafi  suna mamakin soyayar Hameed da Jidda.

Hameed yasauke kowa gidansu rukky tana yammawa, beely tana  Gafai,



Tafiya tafiya sannu sannu soyaya tsakanin Jidda da Hameed tayi nisa karkuso kuga yadda suke gudanar da soyayar su.

Hameed zaune D'akin shi yana waya waya  da my reality dinshi
 Alhaji hamza naira banza yanufo dakin Hameed Domin yanaso suyi wata magana,ta gagawa  shiysa ya nufo dskinshi

Jiyayi " yace wallahi My  dear *MUNA* *TARE* Abadan Da'iman
Sonake nayi ma Dady magana yanzu (domim befadamata)
Yanzu ma sonake nabudema Baba shago yadaina facinan
Sanna sai A shiga maganar bikinku mu Amma bance kifadamasa ba"

Alhaji hamza naira banza yana tsaye wani bakin ciki yaji yaxomasa  Amma can naga yayi wata dariya Wadda nikaina bansan ma'anarta

Juyawa yayi yakoma falo yatura haneefa takiramashi Hameed din tare suka fito
Samun wuri yayi yazauna "yace gani dady"
Alhaji hamza naira banza "yace my son na Lura tun lokacin damukayi wannan maganar kacanzaman baka shikenan farin cikinka shine nawa na Aminche zaka Auri diyar mai faci
Wane unguwa take ne??"
Hameed cikin murna "yace dady unguwar dakake da gidan gona dutsin safe daganan babu nisa kowa katambaya gidan malam Abdullahi mai faci za'a gwadamaka"
Yace shikenan karkadamu zan Aikeka England zaka wakilce wani sabon company dazan bude
Dakadawo sai hidimar Biki ko gobe zakayi tafiyar"
Hameed yayi mamakin saukowar mahaifinshi Cikin murna "yace nagode dady
Alhaji hamza naira banza yayi dariya dashi kadai yasan ma'anar ta " yace karkadamu kafara shirye shirye gobe jirgin karfe 7:00am zaka bi"
Hameed "yaceshikenan dady"

Mikewa kawai motarshi yazura sai gidansu Jidda
Yana isa ya iske baba nan gaisawa sukayi hameed
Cikin kunya "yace baba dama zanyi wata tafiya zuwan kasar England Dana dawo zaa turo magabata na"
Baba "yace babu damuwa Abdul hameed Allah yakaimu lafeeya yadawo dakai lafeeya yaushe ne tafiyar??"
Hameed "yace gobe insha Allah"
Baba "yace Allah yakaimu lafeeya to"
Yamike "yace nima zanje nan baya diyar wani makocina  tarasu"
Hameed Ayya!!! Allah yajikanta. Baba "yace Ameen"

Hameed yashiga har Cikin  gida suka gaisa da Inna
Wayar shi yazaro yakira Jidda dake cikin D'aki tanajinshi,
"Yace my Jidda fito ganinan"

Inna kuma daman tashige D'aki
 Jidda tafito suka samu wuri suka zauna  Hameed kurama Jidda idanuwa yayi itama Jidda kallon shi tayi
Sun dauki lokacin suna kallon juna Jidda Hawaye kawai taji sun zubomata

Hameed yayi sauri tarba hannushi hawayen suka zubomashi A hannu
"Yace my Jidda inahar Ina rayuwa kuma inatare dake bazantaba barin hawayenki su zuba kasa ba"
Jidda "tace nagode yayana"
Hameed "yace meyafaru ne kike Hawaye"
"Tace nima bansaniba naji sunzobomone"

Hameed "yace Jidda yau munyi magana da dady Akan maganar Auren mu zanyi wata tafiya zuwa kasar England gobe zanyi sati daya Dana dawo sai naturo magabatana"
Jidda tanajin ya Ambaci tafiya gabanta yafadi Amma  ba tuna ba.
Sadda kanta kasa kawai tayi.
Suka cigaba  da firansu ta masoya  har lokacin tafiyarshi yayi yayi ma Inna bankwana.
 Jidda har waje tarakoshi
"Tace yayana ka kula pls kar kaje kaga baturiya ka kyaleni"
Hameed dariya "yace Kai Jidda sarakan kishi Hameed naki kedaya babu Wadda  zata kwacemiki ke Amarya ke uwar gida dake babu Kari"
Jidda murmushi tayi kawai
Hameed yajuyo wajen Jidda
"Yace Jidda  ruwa iska, zafi kireke man Alkawali *MUNA TARE* " Jidda "tace nayi maka Alkawali  Ruwa ko iska babu Abinda zai rabamu"
Sukayi bankwana yatafi har ya shiga mota  Jidda tana kalleshi  wani kuka taji  yazomata (Allah sarki)
Tashige  gida.

Turkashi🤔🤔
Muje zuwa

Lov you my fans😘
[2/23, 2:53 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
             💝💝
                *MUNA* *TARE*
                         Na
            Hapsat musa


®
P.W.F.

_Wannan_page  _na_ _sadaukar_ _dashi_gareki
*Mrs* *Lameedo* *nagode* *da*irin *kaunar* *dakike*man _kinjawo_ni*Ajikinki* *babu* *Abinda* *zance* *miki* *bakina* *baya*_iya_ _furta_*komai* *Allah* *yabarmu* *ke*❤❤
Yakara hadakanmu perfect writes forum.


*41*_*45*




Jidda Kuwa wani kuka kawai taji yazomata tashige gida D'aki kawai tafada tafashe dawani sabon kuka Domin jitake kamar tacema Hameed karyatafi kasar England nan.


Isarshi gida kenan yashiga falo  ya iske momy shi Hajiya zainab zaune su Haneeda kuma suna Da'ki suna ibadarsu chart da friends dinsu, yayan masu shi.
 Hameed samun wuri yayi yazauna "cewa yayi momy  ke kadaice zaune falo??"
Hajiya zainab "tace nikadai" ne Hammed su   Hanan" suna Cikin Da'ki "

Hameed "yace nima Momy Bari namike nafara Shirye Shiryen tafiya kinsa jirgin safe zanbikuma momy wallahi wani Abu nakeji tamkar zai faru Dani"

Hajiya zainab "tace Babu  komai. Hameed ka kwantar da hankalinka kajiko"
"Yace shikenan momy  Bari nashiga ciki"

Yana shiga  ruwa kawai yawatsa ya haye laulasan gadonsa  Kiran  Jidda yayi lokacin  Jidda Kuwa kwance kawai take

Dagawa kawai tayi shiru

Hameed "yace meyafaru ne my dear??" Jidda "tace babu komai kaina ke ciwo ne"
Hameed cikin rudewa "yace kinsha magani? "
Jidda"tace nasha"
Hameed "yace sannu my special kwanta  kisamu bacci  zuwa Anjima Zan kiraki"
Nan sukayi bankwana takashe wayanan

Jidda sake rintse idanuwanta kawai tayi har bacci yadauketa tana tunanin Hameed

Can bayan sallar Isha'I
Hameed yakira Jidda sukayi firar su tamasoya.

               *WASHE GARI*

Jidda tana  bacci Domin yau tana  fashin sallah ko farkawa batayiba can wajen karfe 7 taji wayanta nakara
Tana dubawa taga Hameed ne cikin magagin bacci tadauka.
"Hello my dear"
Hameed "yace my special bacci kike natadaki KO??"
Jidda "tace Wallahi Kuwa  Ina kwana katashi lafeeya"
Hameed "yace lafeeya lau  my Jidda jirginmu ne zai daga nace miki  Bari nakira ki Ina isa zankiraki da layina nacan"
Jidda "tace shikenan my one  Allah yasauke lafeeya *MUNA*TARE   LUV YOU SO MUCH"
"Yace  My Jidda *Muna* *tare*"
Sukayi bankwana.


          Bayan kwana biyu


Jidda ce kwance  tashiga damuwa Domin yau Domin yau kwana biyu da tafiyar Hameed bekirata ba.

Inna ce takwalamata  Kira Jidda!!! Jidda!!!
Cikin  sauri tafito na'am Inna

Inna "tace wai meke damunki ne??"
Jidda "tace Inna babu koma kaina ke ciwo ne"
Inna"tace  to Allah sawkke kigin maganin  ciwon Kai nan kidauka kisha"

Shigowar Malam Abdullahi yakatse maganar dasuke.
Yanayin dayashigo  yasa inna  mikewa"Tace lafiya malam"


Luv you my fans😘😘
[2/24, 4:19 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
            💝💝
             *MUNA* *TARE*
                      Na
         Hapsat musa

 ®
P.W.F



*46*_*50*





Yanayi da malam Abdullahi yashigo yasa mikewa "tace
Malam lafeeya??"
Malam yasamu wuri yazauna "yace Bari luba wai natafo nagamu da kallah maigidan wai danan zaizo sai yagamu Dani  wai yasayar da gidan yabamu kwana daya zuwa biyu mutashi"
Inna tayi salati "Tace yanzu haka zai mana bai fadamaka tunda wuri ba sai yanzu zai ce yabaka kwana biyu  zuwa daya"

Jidda Kuwa babu Abinda Tace shiru take tayi tsaye.
Malam Abdullahi "yace Bari luba Wallahi kuma yanzu kinga bani da kudin Kama wani gidan yanzu sana'ar facin ma tajabaya kinagannin kwana biyu sai dai musha ruwa mu kwanta"

Jidda shigewa daki kawai tayi tana kuka tana tausayin halin dasuka shiga gakuma halin rashin ganin kiran Hameed. (Allah sarki)


Bangaren Hameed kuma ya isa lafeeya kasar England yaje masaukin su domin Alhaji Hamza naira banza yana da gida Acan  Hameed yana isa toilet yashiga yayi wanka yafito don yakira Dadyn shi dakuma heart beat dinshi Jidda.
Amma me kwatsam!! Yafiddo wayar daga Alhjihun wandon shi Amma   yanemi waya yarasa mikewa yayi yakara dubawa Amma yarasa Ina wayar take gashi kuma wayar itace mai number Jidda Cikin. Da itace ma yake Amfani  Abu mai muhimmaci,
Dafe kansa kawai yayi domin yaso jin murya jidda.

Dama yanada Sim din kasar daukowa yayi yasa Cikin gudar waya yakira Dadyn nashi yafadamishi ya iso lafeeya.
Bayan sungama wayar  ne  ya datse wayar komawa yayi yakwanta Cikin takaichin faduwar wayarsa   yanzu sai yayi sati daya baiji muryar
My jidda ba kamar ya runtse idanuwanshi yaganshi gabanta. Tayi mashi wannan murmushin Nata yaji sweet voice dinta.



            _Bayan_kwana biyu




Kallah  don Allah kuyi Hakuri kudaina yimani watsi da kaya don Allah.
  Kallah cikin Fuskar sata marar imani "yace bana fadamaka kwana biyu nabaka ba mai gida yanajiran gidanshi   gobe  yau zasu tare Amma bakada Almun tashi"

Jidda Kuwa da Inna sai kuka suke gwanin tausayi yadda Ake musu watsi da kaya
Saida Aka fiddo komai na gidan domin babu komai sai tabarma sai kayan sawarsu,

Kallah babu tausayi shida Wadda sukazo suka maida gida suka rufe suka juya suka tafi.

Malam Abdullahi "yace kudaina kuka komai yafaru ga bawa daga Allah   badon basai sonshi ba Ahhh jarabawace yakemana yaga zamu cinyeta kutashi muhada kayanan kan mutane sukai dasuna gitto mu"


Jidda da Inna tashi suka hada kayan cikin jikka Domin dama bawasu kayane sosaiba.

            

Malam Abdullahi mutumin jibia shida luba  malam Abdullahi shikadai mahaifiyar shi tahaifa matan maifinshi hudu 
Maihaifiyarshi tarasu da maihaifinshi  danginshi yan uba suka dinga nunamashi tsana suna nuna shi bakowa bane wajensu har ya Auri    luba tataso itama cikin tsangwamar matar uba Domin ita batasan maifiyarta wajen haihuwar kannen luba mahaifiyar tarasu daga ita har Abin data haifa  tataso Cikin maraici narashin Uwa kuma mahaifinta  baya iya magana domin larai ta Asirceshi. Har sukayi Aure da Abdullahi suka haifi Jidda     daganan yadawo Cikin katsina   unguwar dutsin safe  yana  sana'ar shi har Jidda ta girma Akasata makaranta  har ta kammallah.

Yau gashi  gidan dayake haya shekaru wajen 15 Ankoreshi saboda wani yasayi gidan.

Yanzu Ina zai nufa gashi.

Malam Abdullahi yana tafiya shida su Jidda har sukazo daidai wani gidan Anyi komai rufi ne kawai ke baayiba Amma An kamallah komai.

Malam Abdullahi yajuyo wajen su Jidda "yace muyada masaukinan kan muga Abinda Allah yayi"

Shiga kawai sukayi suka zauna da kullin kayansu
Suka zauna.
Malam Abdullahi "yace kuzauna naje Cikin gari nasamona Abinda zamuchi KO"
Jidda " tace  Baba ga wayana kahada kasiyar sai musamu Abinda zamuci"

Baba Cikin tausayi ya Amshi wayar  "yace Allah yayi miki Albarka Jiddah"



           Bayan kwana ukku.


Jidda sunata rayuwarsu cikin wannan kangon gidan dabasun maishiba   lalurarsu data kamasu saidai su nusa can suyi.
Baba kuma yanafita yanasamo musu Abinda zasuci.





Hameed   ne yake sakkowa daga matatakalar bene cike da murmushi ya shaki kamshi kasarshi  zaiga kuma my Jidda domin yayi missing Nata sosai.

Haneefa da Hanan ne sukazo tarbarshi.
Hajiya zainab tayi murna da dawowar danta Alhaji hamza naira banza kuwa bayanan  yaje Abuja wani meeting nasu na yan kasuwa.

Hameed kuwa wanka yashiga  yafito ya iske Anjera mashi  Abinchi Kalah kalah

Sama sama yaci Abinchi yazire key motarshi domin  ko hajiya zainab da haneefa basu San  fitarshi ba.

Mota yaja sai unguwar su jidda...



Luv you my fans❤❤
[2/25, 11:28 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝


💝💝💝💝
           💝💝
             MUNA TARE

                Na
Hapsat musa

®
P.W.F.



*51*_*55*





Cikin nishadi  Hameed kejan motar shi domim yau yana cikin farin ciki zaije yaga rabin Ranshi.

Amma me yana shigowa unguwar su yaji wani faduwar gaba. Baikawo ma Ranshi komai haryazo daidai inda yake parking din motarshi yayi yafito.
Yanufi gidan su Jidda turus yayi ganin gidan kulle da katon kwado.

Tsayawa yayi cike da mamaki "yace to ina su Inna sukatafi harda sa ma gida kwado Abinda bantaba ganina"

Wani yaro yazo shiga gidansu  Hameed kiranshi yayi "yace yaka yaro" yanufi wajen Hameed
Hameed "yace Ina su Jidda sukatafi ne??"

Yaro yace suntashi daga nan unguwar rannan Akai tayimusu watsi da kaya har Jidda da Inna suka Kama kuka"

Maihaifin yaro yafito daga cikin gida  "yace Kai khalipa me kakeyinan"

Wadda Aka Kira khalipa "yace  Abba su Jidda yake tambayata nikuma nace suntashi daganan unguwar KO?"

Abban khalipa "yace suka shiga gida" babu gardama khalipa yashige yana gudun shi na yara.

Malam garba maihaifin  khalipa yajuyo wajen Hameed Wadda yashiga rudani yamikamashi hannu suka gaisa

Malam garba "yace Rannan banan inadawo na iske wannan Al'amarin malam garba yatashi  Kallah me gidan ya saida gidanan na tsakar hanya yadinga yimusi watsi da kaya yayan wannan yaro kefadaman domin dagani har mai dakina bamuma yanzu bamuce maka ga inda malama Abdullahi yakoma da iyalenshi"

Hameed sumar tsaye can ya tsinkayi muryar malam garba yanacemasa sai Anjima shigewa gida yayi


Hameed yayi minti 20 tsaye shi bai tafi shi bai shiga mota ba

Tunani yake Ina Jidda sukatafi wane hali suke ciki yanzu Ina suke zaune da yasan da wannnan Abu zai faru da yasiyar musu gida sun huta haya.

Shiga mota yayi yahada kanshi da sitiyari wasu Hawaye yaji masu radadi suna zubomishi

Yatuna kukan da Jidda keyi Ashe wannan Abu zai faru yanzu Ina zaiga Jidda  inbabu Jidda tamkar  babu shi.

Allah sarki Hameed.


*Kuyi*Hakuri *da* *wannnan* *yau**bamu *samu*nepa ba


Luv you my fans💜💙
[2/26, 10:55 AM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
             💝💝
           MUNA TARE
                 Na
Hapsat musa

®
Perfect writes forum
P.W.F.


 *56*_*60*





Hameed yafi minti 30 bai tuka mota yatafi Domin jiyake bazai iya tafiyaba ikon Allah kawai yakai Hameed gida yanashiga babu kowa falon D'akin shi yashige  yafada bisa gado Domin jiyayi wannnan Azabattan ciwon kirji da ciwon zuciya sun rufeshi bargo yadawo kawai yayi rufa dashi.



Bangaren Jidda kuwa sunata rayuwar su wannnan kangon gidan dabasun mai shiba. Amma da ka kalli Jidda kasan tana cikin damuwa. Domin kusan Kullum sai Jidda tayi kuka Amma bata Bari su Inna su Sani.

Yauma Baba yadawo yasamo musu Abinda zasuci suna zaune sunaci Karar mota sukaji ta tsaya inda suke kuma da Almun mutane sun nufo infa suke.

Baba "yace to luba da Jidda kilakam masu wurinan ne sukazo" Hange mutane sukayi sun nufo cikin kango dasuke ciki sunyi.
Harsuka karaso inda suke Mutanen tsayuwa sukayi
Cike da mamakin haka

Wadda yajiku da nera kuma ya manyanta domim zai Kai 60 years yace" idi wannan kuma wanenene kasamo mansu sune har sun sami wurin zama"
Wadda Aka Kira da idi yace" Wallahi ranka yadade bansan da zamansu ba inaba yanzu ba Domin na kwana biyu ban leko ba sai yau dakaceman zakazo nace Bari sai mutafo tare"

"Yace bayin Allah mekuke Anan ne kuka tsallako Cikin Bari bama gidaba Cikin gidan dako rufe babu??"


Malam Abdullahi ya kalli mutumin yace"  Alhaji zanfadamaka komai daganan duk irin hukunchi daya dace sai kayimana"

Malam Abdullahi yafara bashi labarin shi daga farko haryazuwa yanzu daya riske kanshi haka.


Alhajnan kuwa maida numfashi yayi cike da tausayin Malam Abdullahi "yace Amma wannan kyauta maka ba  sai tasheka Rana daya tasheka daga Cikin gida.Amma Ai wasu mutanen haka suke basu da zuciyar imani Basu tunanim mutum dasuka wulakanta sai masu Rana"


"Yace sunana Alhaji  Ibrahim   Ina zaune garin kano Amma kasuwaci na yafi yawa katsina shine musababin Fara wannan ginin domin  inazo nadinga safka Ina fita kasashen waje  shine yasa naba idi kwangilar wannan gida nawa

Inada yaya biyu Khalil da sameer  

Inhar kuma bazaka damuba zamu tafi garin kano dama maigadina bayanan yatafi garinsu Kai kuma yanzu saika maye gurbinshi".

Malam Abdullahi Cikin murna yace" nagode  Alhaji nagode" 

Alhaji ibarahim "yace babu damuwa dauko kayan Ku mutafi dama nagama Abinda nake daganan Zan aje idi nawuce"

Inna da malam Abdullahi sai murna suke  Jidda kam tana murna zasu samu masauki,
Amma tasan tayi nisa da Hameed
 Mota suka shiga sai birnin kano ta dabo tumbi giwa.



Abangaren Hameed kuwa Hajiya zainab ce tazo falo taga Hameed yadanci Abinci baici dayawa shine tashigo Da'ki taga meyafaru
Turo kyauren tayi da sallamah Amma taji shiru
Har tajuya tadauka Yana toilet sai ta hango Mutum Cikin bargo.

Wurin gadon tanufa tace" Hameed baka lafeeya??" tare da yaye bargon dayayi rufa dashi
Halin dataga Hameed shiya razanata.



Luv my fans💙💜💚
[2/26, 3:45 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
             💝💝
            MUNA TARE
                    Na
            Hapsat musa

®
P.W.F.




*61*_*65*





Halin da Hajiya zainab taga Hameed yarazanata domin jikinkishi wani huchin zafi yake Hajiya zainab Cikin  razana tace
"Hameed!!!Hameed!!!!
Meyasameka dama baka lafiya  ne"
 Cikin sauri tafita tadauki waya takira family doctor dinsu.
Batayi minti 10 dakiranshi sai gashi tare suka shiga
D'akin Hameed 
Nan danan Dr ismeel yafiddo kayan Aikenshi

Yafara duba Hameed dayanajin su sama sama Amma bazai iya magana domin wani nauyi dakanshi yayi.

Bayan Dr ismeel  yagama duba Hameed ne
Yajuyo wajen Hajiya zainab

Yace Hajiya" damuwa ce takamashi farat daya irin ta ce mai sa nandanan ciwon zuciya Yakama mutum"

Hajiya zainab cikin razana tace  "Doctor ciwon zuciya?"
  Doctor ismeel Yace "hajiya bata Riga takamashi   Amma sai dai damuwar datakamashi karaf daya
Amma insha Allah zuwa Anjima zankawo mishi wasu maguguna.
Dasai yi Amfani dasu"
Hajiya zainab tace "shikenan doctor Allah yakaimu."


                *KANO*



su Jidda sun iso  cikin garin kano A unguwar   Sharada phase11
   Jidda dasu malam Baba kuwa sakin baki sukayi ganin gida tangameme wadda tunda suke basu taba ganin shiba tunda suke.
Alhaji Ibrahim yabudemusu mota suka nufa har cikin  gidan
 Tareda sallama suka shiga babu kowa falon
Alhaji Ibrahim yace "ma su Inna su zauna Yana zuwa.

Su Inna samun wuri sukayi suka zauna

Badauki minti 10 saiga Alhaji Ibrahim suna tafowa shida wata mace.

Suka samu wuri suka zauna
Alhaji Ibrahim yajuyo gareta  maman Khalil"
Tace "na'am Abban Khalil"

Yace "wannnan dakike gani naje gidan nake gini na katsina nan yabata labarin komai"
   
Cikin tausayi Hajiya maryam matar Alhaji Ibrahim   tace Alhaji "wasu mutanen basuda imani kallifa Kai tsaye   yadda yace yatashi mashi daga gida.

Tajuyo wajen su Inna tace "karkadamu  damu bayin Allah insha zamu taimaka muku domin duk wadda ya taimaki wani Allah zai taimakeshi"
Alhaji Ibrahim yace "kwarai ko

Yace "malam Abdullahi ga boys quarter's kaga sai kudinga kwana ciki"

Malam Abdullahi da Inna kuwa durkusawa har kasa sukayi suna godiya
Alhaji Ibrahim yace "babu damuwa duk wadda ya taimaki wani Allah   zai taimakeshi nibana cikin wadda insuka samu Abin duniya idanuwa zasu rufe
Dukiyar daza Abarta meyakawo na hamdama
Hajiya maryam

Tace"ma Jidda yakinan yata gaka Alhaji nasamu ya' dama inason diya mace Allah bebaniba" Jidda tashi tayi takoma kusada hajiya maryam   hajiya maryam tace matso kusadani daga yau kidinga kallona tamkar ummanki kinji.

Hajiya maryam tajuyo wajen su Inna tace dafatan zaku barmin ita.

Inna dariya tace "Anbarmiki
Hajiya maryam tace " nagode tajuyo wajen Jidda tace "tom kinji yata  Anbarmin ke daga yanzu kindawo wajena tsakaninki da Inna sai dai kishiga ki gaidatota". Jidda sadda Kai kawai tayi.

Suna zaune saiga wasu samari sunshigo tare da sallama kusada Alhaji Ibrahim suka zauna "dady kadawo ne ?? Amma bakasanar damuba  Alhaji ibarahim yace "dawota kenan
Bakuga bakiba Baku gaishesu gaidasu sukayi
Alhaji Ibrahim
[2/26, 4:16 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
             💝💝
            MUNA TARE
                    Na
            Hapsat musa

®
P.W.F.




*61*_*65*





Halin da Hajiya zainab taga Hameed yarazanata domin jikinkishi wani huchin zafi yake Hajiya zainab Cikin  razana tace
"Hameed!!!Hameed!!!!
Meyasameka dama baka lafiya  ne"
 Cikin sauri tafita tadauki waya takira family doctor dinsu.
Batayi minti 10 dakiranshi sai gashi tare suka shiga
D'akin Hameed 
Nan danan Dr ismeel yafiddo kayan Aikenshi

Yafara duba Hameed dayanajin su sama sama Amma bazai iya magana domin wani nauyi dakanshi yayi.

Bayan Dr ismeel  yagama duba Hameed ne
Yajuyo wajen Hajiya zainab

Yace Hajiya" damuwa ce takamashi farat daya irin ta ce mai sa nandanan ciwon zuciya Yakama mutum"

Hajiya zainab cikin razana tace  "Doctor ciwon zuciya?"
  Doctor ismeel Yace "hajiya bata Riga takamashi   Amma sai dai damuwar datakamashi karaf daya
Amma insha Allah zuwa Anjima zankawo mishi wasu maguguna.
Dasai yi Amfani dasu"
Hajiya zainab tace "shikenan doctor Allah yakaimu."


                *KANO*



su Jidda sun iso  cikin garin kano A unguwar   Sharada phase11
   Jidda dasu malam Baba kuwa sakin baki sukayi ganin gida tangameme wadda tunda suke basu taba ganin shiba tunda suke.
Alhaji Ibrahim yabudemusu mota suka nufa har cikin  gidan
 Tareda sallama suka shiga babu kowa falon
Alhaji Ibrahim yace "ma su Inna su zauna Yana zuwa.

Su Inna samun wuri sukayi suka zauna

Badauki minti 10 saiga Alhaji Ibrahim suna tafowa shida wata mace.

Suka samu wuri suka zauna
Alhaji Ibrahim yajuyo gareta  maman Khalil"
Tace "na'am Abban Khalil"

Yace "wannnan dakike gani naje gidan nake gini na katsina nan yabata labarin komai"
   
Cikin tausayi Hajiya maryam matar Alhaji Ibrahim   tace Alhaji "wasu mutanen basuda imani kallifa Kai tsaye   yadda yace yatashi mashi daga gida.

Tajuyo wajen su Inna tace "karkadamu  damu bayin Allah insha zamu taimaka muku domin duk wadda ya taimaki wani Allah zai taimakeshi"
Alhaji Ibrahim yace "kwarai ko

Yace "malam Abdullahi ga boys quarter's kaga sai kudinga kwana ciki"

Malam Abdullahi da Inna kuwa durkusawa har kasa sukayi suna godiya
Alhaji Ibrahim yace "babu damuwa duk wadda ya taimaki wani Allah   zai taimakeshi nibana cikin wadda insuka samu Abin duniya idanuwa zasu rufe
Dukiyar daza Abarta meyakawo na hamdama
Hajiya maryam

Tace"ma Jidda yakinan yata gaka Alhaji nasamu ya' dama inason diya mace Allah bebaniba" Jidda tashi tayi takoma kusada hajiya maryam   hajiya maryam tace matso kusadani daga yau kidinga kallona tamkar ummanki kinji.

Hajiya maryam tajuyo wajen su Inna tace dafatan zaku barmin ita.

Inna dariya tace "Anbarmiki
Hajiya maryam tace " nagode tajuyo wajen Jidda tace "tom kinji yata  Anbarmin ke daga yanzu kindawo wajena tsakaninki da Inna sai dai kishiga ki gaidatota". Jidda sadda Kai kawai tayi.

Suna zaune saiga wasu samari sunshigo tare da sallama kusada Alhaji Ibrahim suka zauna "dady kadawo ne ?? Amma bakasanar damuba  Alhaji ibarahim yace "dawota kenan
Bakuga bakiba Baku gaishesu gaidasu sukayi
Alhaji Ibrahim yajuyo wajen su Baba yace " malam Abdullahi gaka yayana nan wadda na fadamaka Khalil da sameer twins sukadai Allah yabani  dagasu bankara ba

Malam Abdullahi yace "tom Allah yarayamna zuri'a

Jidda cikin muryar wadda kodayaushe cikin sanyi take

Tace "inayininku" dasauri Khalil yadago fuskar shi yaga wake da wannan sweet   voice din Sameer yace momy "Ina kikasamo yar budurwa?"
Momy tace" Yata ce sunanta jidda kunga in kuka fitarku nasamu mai deveman kewa
Khalil kuwa kallon Jidda kawai yake yanajin wani Abu cikin Ranshi  (tofa😳)
    Tashi Alhaji Ibrahim yayi yagwadama su malam Abdullahi msaukinsu  boys quarter's

Itakam Jidda D'aki guda Hajiya maryam tabata Domin tanajin  wata  kaunar Jidda cikin ranta.
Ta gwadamata duk yadda zatayi Amfani dakomai.

Jidda wanka tashiga tafito
Lokacin sallar Azuhur tayi tabada farali

Kwanciya tayi Domin tagaji kallon zone Hannuta tayi wasu Hawaye taji sun zubomata cikin kuka tace "yayana inazanga iduwana suna son Kallo murmushin ka kunne na yanason jin muryaka kayi man Alkawali bazaka taba barin Hawaye su zuboma yau gasu suna zuba babu kai
Yayana *Muna*tare komai wuya da tsanani
Rushewa tayi dawani irin kuka mai ban tausayi


Shikam Khalil tunda yaga Jidda yakejin yashiga wani yanayi

Tofa wane  irin yanayi yashiga?? Tambaya  gareku masoyan Muna tare
Sai kunjini


Luv my fans💚💜💙
[2/27, 1:11 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
            💝💝
               MUNA TARE
                        Na
                      Hapsat musa
®
Perfect writes forum

P.W.F.




*66*_*70*



Doctor Ismee'l bada jimawa yakawo ma Hameed magani yafada momy duk yadda za'ayi Amfani dashi.
Shiga D'akin Hameed tayi ta iskeshi kwance haryanzu.
Daidai kusadashi taje Hameed!! Hameed!!!

Tashi "ga maguguna Doctor yakawo mezan kawo maka kaci sai kasha magani?"Cikin Almun ciwo  Hameed yatashi 
Yace " momy hadoman coffee kawai"
Tace "shikenan bara nahadomaka"
Fita  tayi  tahadomashi
Hameed kuwa hada kanshi yayi da gado yashiga tunanin Jidda  yake
Kallo zobe hannu shi yayi
Yace "My Jidda Ina kika tafi inazanganki  kece rayuwata kece jinin jikina  zuciyata duk bugawar dazatayi Kaunarki ki karuwa take"   wasu Hawaye masu mugu
Radadi suka zuboma Hameed  wata kaunar Jidda nabin dukkan sasan jikinsa idoshi ya rintse Yana tunani soyayar su.

Hameed!! Hameed!!!
Firgit yadawo daga tunanin
Dayake yashare Hawaye dasuka zubomishi 
Yace "momy harkin dawo"
Momy tace "Hameed meke damunka  tare dasamun wuri tazauna har nashigo bakasan nashigoba kuma naga Hawaye nazuba da idunawanka nasan ba karamin Abu zaisa Hameed kuka ba"

Hameed yace "Babu komai momy"
 
Momy tace "Hameed ni mahaifiyar kace kasan Doctor yafafaman damuwa ce takamaka farat daya  
Menene Hameed fadaman kaji??"

Hameed yace "shikenan  momy nan yafadamata dukkan Haduwarshi  da Jidda  haryazuwa yanzu dayaje Akace suntashi"
Fashewa yayi dawani irin kuka mai ban tausayi yafada jikin Momy yace "Momy inazanga Jidda  itace bugun zuciyata  Momy Jidda tawace munyi Alkawali *MUNA*TARE  Abadan Da'iman"  momy rarrshin Hameed tayi kamar karamin  yaro  "Hameed kayi Hakuri zaga Jidda insha Allah zata zama uwar yayanka kajiko"
Hameed yace "Allah yasa momy na"




                  After 2 month



Jidda suna rayuwarta cikin kwanciyar Hankali   Hajiya maryam tana kula da Jidda tamkar yarta.
Tsakaninta dasu Inna sai dai taje gaishesu.Alhaji ibrahim yanaba Baba Albashinsa kuma duk Abinda zasuci daga gidan Alhaji Ibrahim suke fitowa.


Jidda ce tayi wanka zura doguwar Riga kawai tayi tafito falo   babu wani make up   Hajiya maryam tafita tadawo tazauna 
Zama tayi tashiga sa'naarta wato tunanin Hameed kodayaushe yazamemata Abinchi 

Kan'wanta!!Kanwata!! Firgit tayi tadawo daga tunanin data tafi  Amm Yaya Khalil sannu da  dawowa  yace "tunanin mekeke har nashigo bakisani ba?"
Murmushi tayi tace "Babu komai" yace "shikenan  daukoman Abinchi na"
Mikewa tayi tanufi kitchen  tadauko mashi daukowa tayi Ajewa tayi zata D'aki 
Yace "kuma inazaki?
Dawo kizauna kizuba man "

Dawowa tayi tazuba mishi takure take da tazauna   har yagama ci bata Sani ba

Yace "Jidda"
Tace "Na'am Yaya Khalil"
 Yace "Jidda inason muyi wata Magana dake"
Tace "Yaya Khalil inajinka

Yace " Jidda Iluv you inason mukasance tare har karshen rayuwata.

Zumbur kamar A tsunkulle ta tace "yaya Khalil so na"

Yace "Eh jidda jidda.   tun ranar da  nahada idanuwana dake zuciyata take Ayyana man wani Abu cikin raina".

Jidda wani kuka yataho Mata Dagudu tafita daga Cikin falo boys quarter's kawai tanufa

Inna ta iske tana  girki zarcewa kawai tayi D'aki  tafada bisa  gado  tafara sambatu
" Yaya Hameed kana Ina  kazo gareni katausayaman  sonka zai fasa kirjina kayi Alkwalin Muna tare har Abada  bazamu rabu ba Kai nawa ne nitakace        Yaya hameed wayyo ni Jidda" Kara runkumeme zobe tayi kamar me tafashe da kuka 
Allah sarki Jidda nima fashewa nayi da kuka domin tausayin jidda😭😭


Luv my fans💚💙💜
[2/27, 8:32 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝
     
💝💝💝💝       
              💝💝            
               MUNA TARE
                     Na
              Hapsat musa

®
Perfect writes forum

P.W.F.


_Na__sadaukar _ga_ _wannnan_ _page_ _gareku_ _masoyan_Book _din_MUNA TARE _nagode_ da _kaunar_Ku
Luv you All💙💚






_71__75






Jidda jitayi Anzauna kusa da ita Jidda!!!Jidda!!!
Tashi tayi daga kwanciyar tana goge hawayen tace"Na'am Inna"
 Inna tace "lafiya kika shigo kina kuka??"
Jidda wani sabon kuka yazomata cikin kuka tace "Inna Yaya Hameed natuno shine naga babu inda zanyi  kukana sai nan"

Inna cikin tausayi domin tasan bakaramar shakuwa sukayi da Hameed ba
Tace "kidaina kuka  kinji ko
Kicigaba da Addu'a zaku hadu kunji ko"

Jidda tagoge hawayen idanuwanta tace "shikenan Inna Bari nakoma Momy batanan "
Inna tace "shikenan"


Khalil kuwa ganin  Jidda tafita tana  kuka cike da mamaki yakamashi meyasata kuka
Sameer ne yashigo dakayan
Ball ya iske Khalil haka zama yayi kusadashi
Yace "Brother meke faruwa naganka haka"
Khalil yace "Brother kasan nafadamaka inason Jidda tun ranar danafara ganinta"
Sameer yace "Eh"

Yace "shine  yanzu nafadamat shine tafita tana kuka wadda bansan daliliba"
Sameer yace "tofa ko meyasa kabata wani lokacin kagani saika tuntubeta komeyasa kuka"
Khalil yace "ok"
Tashi sukayi suka nufi cikin D'akinsu.




Bangaren Hameed kuwa Hameed yarame ga wata uwar kasumba dayaje Kullum cikin tunani yake
Alhaji hamza naira banza
Kuwa yayi nadama halin Abinda ya Aikata tofa  meyaka Aikata kuboyini zakuji komai.

Yauma Hameed kwance yake yasa zobe Jidda gaba yana kallon hawaye nazuba daga idanuwansa.
Yanajin wani  son Jidda nabin jikinshi
Tari yasarkayeshi daidai shigowar Dadyn shi tare da momy harda su Haneefa  domin yanzu yadaina zama falo kullum yana cikin D'aki yana tunani.
Dasauri Alhaji hamza naira banza suka iso dady yace "sannu  my son" Amma Hameed tari yake kawai
Dady yajuyo wajen Momy yace " zainab daukomashi  ruwa" dasauri
  Momy tadauko A firjin D'akin  Hameed yana Kaiwa ruwan baki ya Amaidosu hade da jini

Tsananin kaduwa sun kadu
Cikin razana  Hajiya zainab tafashe da kuka  "Hameed   Aman jini kake" ganin Momy  tana kuka yasa Su Haneefa kuka
Alhaji hamza naira banza dauriya yacigabada rarrarshin su
Ganin Hameed wani jini yasake zubomishi ta hanci ta baki yasa Alhaji hamza naira banza rudewa idanuwan Hameed suka juyo yasume.
Hajiya zainab dasu Haneefa Kara fashewa  sukayi da kuka
Alhaji hamza naira banza sabar Hameed yayi sai mota yau kojira direba baiyiba dagudu su Momy suka biyoshi suka shiga mota sai Asibiti.

Gudu kawai yake sharara zuciyarsa cike da nadama danasani.

Alheri clinic suka nufa inda suke da file dama dady yayi waya suna isa Akaturo  gadon marar  lafeeya
Shiga   akayi D'aki guda nan danan  Doctor ismai'lyahau Aiki kan Hameed 

Momy kuwa dasu haneefa sai zarya  suke  sun rasa zaune

Kamar minti30 saiga doctor ismee'l yafito  dasauri Momy suka isa gareshi ",Doctor yajikin nashi"
Doctor ismee'l girgiza kanshi yayi yace ,"kubiyoni office"

 Cikeda faduwar gaba suka bishi office.

Samun wuri sukayi suka zauna  Doctor ismee'l yamaida numfashi yace "Alhaji  Gaskiya  Hameed yana cikin matsanacin hali 
Domin yanzu damuwar harta taba zuciyarsa"
 Alhaji hamza naira banza yace "Doctor yanzu Ake ciki??"

Doctor yace "wannan ciwon ba bangare naneba   bangaren ciwon zuciya
Amma Akwai wani Doctor A kano Dr Khalil yakware  Akan duba zuciya  zanyi masa waya yau gobe sai kufara shirin tafiya"

Alhaji hamza naira banza yace "Doctor kanaganin zai iya? Inahar bazai iya ba nafiddashi waje kawai"

Doctor Ismail' yace "insha Allah shiyasa Zan hadaku dashi
 Alhaji hamza naira banza yace " kayimashi magana gobe sai mufara shiri sai nayi booking jirgin safe"

Doctor ismee'l yace "zan kirashi yanzu"

D'akin Da Akwa kwantar da  Hameed suka nufa  Hameed kamar yakwana yanaciwo fuskar shi tayi fayau.
 Nan Alhaji hamza naira banza yabar momy zaije yayi booking jirgin dazai kaisu Kano gobe.











*NIMA*DAIDAI *NAN* *ZAKU*DAKACENI *SAI*GOBE.


LUV YOU MY FANS💚💙💜
[2/28, 7:56 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝
💝💝💝💝
            💝💝
              MUNA TARE
                      Na
     Hapsat Musa


®
Perfect writes forum
P.W.F


*Nagode*da *kaunarki* *gareni*
*Miss*Aysherh  *marubiyar*(Zahra)
Allah yakara basira da zakin hannu.





_76__80






Jidda ce kwance D'aki  sai rawar sanyi take turo kyauren Akayi Akashigo tare da sallama  cikin sauri Hajiya maryam ta iso wajenta "subhnallah Jidda dama baki lafeeya  baki fadaman ba?"

Cikin rawar Murya Jidda tace "wallahi momy kaina ke wani ciwo ga kuma zazzabi yarufeman jiki "

Hajiya maryam  tace " Allah sawakka Bari nakira sameer ko Khalil yadubaki"

Fita tayi kawai cike da mamaki Jidda cikim ranta tace " dama. Likotaci ne"

Turo kyauren  daakyai ya katsemata tunani  momy ce tare da Khalil suka shigo
Wajen gadon da Jidda ke kwance yanufa kawai

"Kanwata meke damunki"

Jidda cikin muryata mai sanyi wadda ke rikita Khalil
Tace "kwana Biyu ina fama da wani matsanacin ciwon Kai yanzu kuwa harda zazzabi yarufeni"

Kayan Aikinshi daya shigo dashi yahau dubata 
Bayan yagama dubata juyowa yayi wajenta domin hajiya Maryam tafita tahadomata Tea Tasha koshi Tasha

Jidda!! Dagowa tayi domin jitayi yakirata dawani salo na sunan
"Meke damunki har hawan jini na Neman kamaki ne damuwa tayi miki yawa cikin zuciya"

Jidda fashewa tayi da kuka tace "Yaya Khalil  kayi karka damu  halin danake ciki katayani da Addu'a kawai"

Khalil yace "kinaga Hakan shine mafita??"
Gyadamasa Kai kawai tayi

Hajiya maryam ce taruro kyauren dakin tashigo  dauke da cup din tea Kusa da Jidda tazauna  tace "Amshi nan kisha kinji ya'ta

Khalil mikewa yayi  Momy Bari nahadomata maguguna  Amma harda Allura zanayimata"

Jiddasaurin dago fuskatayidomin har ga Allah tun tana karama Akwai tsoron Allura. Har kuka takema Allura.

Cikin hawaye dasuka  fitoma
Tace "Yaya Khalil don Allah karkayiman Allura don Allah"

Khalil yace "di'yar momy bakison Allura?"

Tace "Eh"

Momy tace "Khalil tunda bataso  kabata maguguna kawai"

Cewa yayi "Ok"

Yajuya yafita domin daukomata magugunam"

Dawowo yayi dasu  tsugunawa yayi kusada ita yabalo maguguna yafara bata
Yace "kinsha yanzu sai kuma in Anjima inadawo KO"

Wayarshi tahaukara
Zarowa yayi daga Alhajin wandon shi
Yaganka tareda Sallama
"Assalamu Alaikum kana magana da Dr Khalil Ibrahim"

Dagacan banageren "Akace  Ameen walaika sallman kana magana da Dr ismee'l daga  katsina"

Dr Khalil  yace  "My friend kaboya sai yau katuna Dani"

Dr ismee'l yace "kasan yanayi na Aiku mu fa"

Khalil yace "Hakane fa"
Nan suka gaisa har Dr ismee'l yafadamashi dalilin kiranshi

Dr Khalil yace babu damuwa Abokina katuro man number shi maihaifin yaro inso inso saina turo motar Asibiti tadaukesu"

Dr ismee'l yace "OK"
Sukayi bankwana

Tashi Khalil yayi  yace "Momy natafi office tundazu broos yatafi yanada Aiki ne"
Momy tace "Allah yakiyaye ya tsare"
Yace "Ameen Momy"

Yana fitowa har wajen Baba yaje yagaidashi domin ,yana ganin girmanshi sosai
Sannan yashiga mota sai Asibiti.

Dr Khalil shida sameer cikakun likocine sunyi karatunsu duka A kasar India    primary kawai sukayi A Nigeria domin Alhaji Ibrahim yazauna can

Bayan sun dawo gida Nigeria yabudemasu Asibiti babba maisuna  *K*& *S*  Private hospital
Dr Khalil suna Duba marar lafeeya sosai. Shi Dr Khalil yana bangaren domin har taimako suna badawa dawadda Bashi dashi.


Dr Khalil yanafita hajiya maryam "tacema Jidda takwanta ko jikin yafada
Jamata kofa tayi tafita

Jidda kuwa kallon zoben Hannuta tayi da Kullum yazameta tamkar Hameed take kallo cewa "take yaya Hameed wane hali kake ciki yanzu  jikina yabani Baka lafiya yaya Hameed  wayyo ni Jidda   Yaya Hameed ga hawaye suna zuba da idanuwana zuciyata tanayiman zafi. Nashiga wani hali yaya Hameed rashin ganinka duk yasani sanadin haka"
Jitayi bazata iya kwanciya bama fitowa tayi tanufi bakin get wajen Baba
 Baba Yace "Jidda baba ya Akayi ne??"

Jidda tace "baba  wurinka kawai naji inasonxuwa"
Nan sukayi ta firar 
Baba yace "Jidda nasan kina cikin maraicin wanna yaron Abdul Hameed domin innarki tafadama nima Jidda Abdul Hameed yayiman domin yaron Arziki ne ki cigaba  Add'ua insha Allah zakuga  juna kinji ko"

Jidda wani kuka yazomata tare da son Hameed wani sabo tace "shikenan Baba"

Mikewa tayi  tace Baba Bari nashiga wajen Inna"
Cikeda tausayi yace "to"

Bangaren Inna tanufa kawai tana zuwa ta iske Inna tana bakacen wake kusada ita tazauna takwanta jikinta
Tace  "innata"  inna tace "Jidda yanajikin da zafi"

Jidda tace "inna zazzabi ne Amma yaya Khalil yaban magani naji sauki"

Innace tace "kije ki kwanta to"
Jidda mikewa tayi tace "tom
Inna"

Inna cikeda da tausayin Jidda domim tarame sosai

Jidda cikin gida takoma D'akin ta  kawai tanufa can bargo tayi domin KO barci yadauketa.
Cikeda tunanin Hameed Cikin ranta.


Luv you my fans💚💙💜
[3/1, 10:12 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
            💝💝
              MUNA TARE
                      Na
                  Hapsat Musa


®
Perfect writes forum

P.W.F.






81_85




Dr Khalil yana isa Asibiti parking din mota yanufi cikin Asibiti nan ma'aikata suka Fara gaisheshi  domin Dr Khalil badai mutumchiba
Shida sameer suna ba mutum darajarshi.

Shiyasa kodayaushe Asibitin Kara bunkasa take.

Har ya isa office yazauna yafara ganin patient suna shigowa yanaganinsu

Yanacikin dubasu wayashi tayi New number ce yagani
Tunowa dayayi sunyi magana da Dr ismee'l yaturomashi number beyi saving ba

Dauka yayi tareda Assalamu Alaikum  yace  "Dr Khalil Ibrahim ke magana"

Dagacan bangaren yace "sunana Alhaji hamza naira banza dafatan Dr ismee'l yayi maka bayanin komai"

Dr Khalil yace "Kwarai ko yafadaman Akan kuna tafe da yaronku"
 Alhaji hamza naira banza yace "kwarai kuwa yanzu haka muna filin jirgi zanyi Hayar d mota dazai kawomu Asibitin"

Dr Khalil yace  "basai kayi hayar mota ba gayanan zanturo mota Adaukeku zaku ga Ambulance ce mai dauke tambarin K&S"

Alhaji hamza naira banza yace "Ok"

Suka datse wayar
Fita yayi yayima  wasu nurse magana zasuji filin jirgi    dauko marar lafeeya yanzu suna can suna jiransu
 Tafiya sukayi sukayi ma direba magana  sai  Malam Ameenu kano international  Airport.


Alhaji hamza naira banza   suna tsaye shida Hajiya zainab Hameed kuwa yanacikin keken maras lafeeya.

Motar Asibitin tashigo harabar Airport  ta tsaya dasauri Alhaji hamza naira banza yanufi wajen sai kace ba Alhaji hamza naira ba
Ambulance din yanufa

Yayi musu  magana tuka keken da Hameed yake ciki  Suka shiga Amblumce sai Asibiti.

Suna isa  fitowa sukayi sukuma nurses  suka tura Hameed sai Emergency room.

 Sukafito suka sanar da  Dr Khalil gayacan sun iso Dr Faruq yayima magana Akan yacigabada duba patient sai  ga wani patient Emergency
Domin daga katsina suke.

Fitowa yayi  yanufi D'akin Daa Aka kwantar da  Hameed yayi ya iske Hajiya zainab tare da   Alhaji hamza naira banza suna tsaye sai zarya suke domin nurse sunfadamasu babu maishiga sai  Ma'akaci
Dr Khalil tsayawa yayi yace
"Kune  iyeyensa?"

Alhaji hamza naira banza yace "mune Dr "

Doctor Khalil yace "ok"

Yajuya yanufi ciki
Su kuma su Alhaji hamza naira banza sai zarya yake saikace ba wadda yajiku da naira Cikin Ranshi kuwa tsananin nadama ce tsatsan
Yau gashi kudi babu ranar dasukayi mashi tunda har basu ba danshi wadda yafi soyuwa cikin ranshi lafeeya ba.

Yayi nadama dayaraba danshi da wadda yake so yadauka inyarabasu komai zaizo dasauki. Ashe bahakabane.(tofa🙄)

Tunanin yakatsene momy ce tayi mishi magana Dr yanason ganinsu.

 Office Dr Khalil suka nufa samun masuguni bisa kujera sukayi suka zauna

Dr Khalil yajuyo garesu
Tare da furta yace "gaskiya Alhaji danku yana cikin babbar matsala inhar baasamu mashi Abinda yakesoba damuwa ce tayi mishi yawa A zuciya
Amma zandora shi Akan wasu maguguna zaiji sauki
Amma yazama wajibi kobashi Abinda zuciyar shi keso inhar kuna son lafiyarshi"

Alhaji hamza naira banza  jugum cike danasani nadama.

Yace "shikenan Dr yanzu yamaganar  maguguna"

Dr Khalil yace "baza biya komai har sai yasamu sauki Akan maguguna damuka dorashi.  Sannan saikayi bill kabiya"

Alhaji hamza naira banza yace "shikenan doctor"

Dr Khalil yace yanzu bazaku Ganshi har nan da gobe kozuwa jibi"
 Alhaji hamza naira banza yace "OK babu matsala"

Dr Khalil mikewa yayi yaduba Agogonsa time din tashi yayi  yace "lokacin tashi nayayi sai kuma gobe insha Allah"

Suma Su Alhaji hamza naira banza mikewa sukayi  Hajiya zainab cikin muryan tausayi tace "Doctor don Allah kayi bakin kokarinka da  ilmin da Allah yabaka Akan Hameed"

Dr Khalil yace "karki damu momy insha Allah zai tashi"

Bankwana sukayimashi suka tafi masauki domin sunada gida  A kano Domin. Kowace state Alhaji  hamzanaira banza yanada gida

Shikuma Dr  Khalil shiga yayi yakara duba Hameed cike da tausayin shi Akan yafito yayima Masu Aikin   Lokacin Akan sundiga dubashi sosai.

Mota yashiga sai gida
Yanazuwa Baba yabudemashi get yashiga
Falo yashiga ya iske momy tare da Jidda suna Kallo
Samun wuri yayi yazauna

Juyowa yayi yace "momy yar taki hartaji saukin fitowa falo"
Momy tace "ya'ta taji sauki"

Itadai Jidda batace komai

Juyowa yayi gareta "kanwata   kinsha magani naki dai" Jidda tace "nasha"

Khalil yace "good  yajuyo wajen momy yace " momy nagaji wallahi naga patients dayawa yau gakuma wani patient daakawo daga katsina momy Akan ciwon zuciya  wallahi momy yana cikin matsala"

Ambatar marar lafeeya kawai Jidda taji gabanta yafadi.

Momy tace "yanayin Aiku kune fatana kutaimaka mai nema taimako Akodayaushe"

Khalil mikewa yayi  yace "momy    Bari nashiga ciki broos yadawo??"

Domin wataranan basu haduwa 
Momy tace "A,a"
Shiga ciki yayi  kawai

Itama Jidda mikewa tayi tashiga D'akin ta Domin tunda  Khalil ya Ambaci wannnan marar lafeeya taji kawai takasa sukuni.



Luv you my fans💙💚
[3/2, 8:15 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
             💝💝
                MUNA TARE
                       Na
                  Hapsat Musa

®
Perfect writes forum

P.W.F.



86_90



            Bayan Kwana biyu


Khalil D'akin da Aka kwantar da Hameed yana Kara dubashi juyowa yayi wajensu yace musu "Alhamdullah jiki yayi sauki
Amma gaskiya Asamomasa Abinda yakeso.Momy tace "insha Allahu Dr  zaasamosa"
Dr Khalil yace "hakan zaifi domin inhar Baku samoshi zaku iya rasa rayuwarsa  kodayaushe domin zuciyarsa tadan kumbura"
Cikin razana Momy tace "insha Allah"
Kara dubashi yayi sannan yafita.

Momy kuwa itada dady Kara matsowa sukayi kusada gadon Hameed  Wani kuka yazomata ganin Hameed   yadda cikin kwana biyu yarame. (Allah sarki Allah rabamu da ciwon so)

Dady Cikin rashin kuwa tsantasar nadamace Akan Abinda ya Aikata ma kanshi.yau gashi Muguntarshi Kanshi takare ga danshi kwance.




Dr Khalil yashigo falo dauke da  jakkarshi ta Aiki Jidda ce ya iske zaune falo tayi tagumi har yazauna batasan yazauna ba

Jidda!!! Jidda!!!
Firgita tayi kakaro murmushi tace "yaya Khalil sannu da dawowa"
Yace "yauwa jidda tunanin mekeke??"

Murmushi tasakeyimashi wadda duk wadda yagani yasan nakarfin haline domin rabon da Jidda kaga tana dariya tun ranar da Hameed yabar Nigeria.

Amm "yaya Khalil babu komai"

Khalil yace "shikenan tunda bazaki fadaman ba
Jidda yasake kiran sunanta
Tace "Na'am"

Khalil yace "tunranar danafadamiki wannnan maganar kika fita kina kuka
Nabaki time  Jidda nakasa hakura da sonki Cikin zuciyata yazama wajibi nakara maimaita miki
Jidda ILOVE YOU Wallahi Inasonki    inaso ki kasance uwar yayana"

Mikewa tayi kawai zatabar wurin  dasauri Khalil ya mike yatari gabanta  tare da furta "Wallahi Jidda sai kinfadaman dalilin dayasa kike guduna "

Cikin kuka tace "yaya Khalil bani wuri na wuce"
Yace "bazan bayarba saikin fadaman meye Abun gudu tare Dani"


Shigowar momy falon yabadamar shigewar Jidda D'aki.

Dasauri momy ta iso tace "Ahhh  Khalil meke faruwa ne?? Mekayimata ne take kuka?"

Khalil yace "babu komai"
Momy tace "Fadaman kaidai Khalil  sunkuyar da Kai yayi yace " momy don inasonta ne danayimata magana sai tayi man kuka"

Hajiya maryam wani farin ciki taji yaziryaci zuciyarta domin tanason sameer ko Khalil ya Auri Jidda Domin su hada zuri'a dasu Inna saigashi Khalil yafurta dabakinshi yanasonta

Tace "karkadamu  Khalil kaji ko insha Allah Jidda zata zama matarka dama gobe dadyna Ku zaidawo daga tafiyar dayayi zuwa Egypt.
Kaga sainan sanardashi Bari nashiga wajen Jidda din"

Khalil cikeda murna yatashi yashige D'akin su sameer dake zaune yana duba wasu files. Yaga shigowar shi  cikeda farin ciki da Fuskar shi yace "brother  mekasamu ne naga fuskar ka cikeda farinciki"

Khalil hayewa gado yayi cikeda murna yafadamashi komai sameer yataya Khalil murna jin zai Auri muradin Ranshi.



Momy kuwa D'akin Jidda tashiga tareda sallama dasauri kan momy tagani tashiga share  Hawayen dake Fuskarta takakaro murmushi dole tace "momy"
Hajiya maryam samun wuri tayi tazauna fuskarta dauke  da murmushi tace "Ya'ta
Sannnuki   Ankawo min karki"

Dasauri Jidda tadago fuskarta tace "momy wayakawo miki karata"

Momy tace "karki damu ya'ta Khalil yace man yana sonki Amma kinki bashi hadin Kai  Haba ya'ta  kinsan yadda nakesonki jinake kamar ya'ta  kamar diyar wata kanwata wadda muka fito ciki daya. add'uata Kullum dama nahada Zuri'a dake. Kinji. Ya'ta"

Jidda kuwa wani Abu kawai taji  yanayimata yawo A tsakiyar kanta.

Momy mikewa tayi tace "Bari naje"

Jidda saidai ta waiwaya bata ganta ba.

Kulle D'akin tayi hayewa Gado tayi tare da sakin wani kuka mai raunana zuciyar maiji.Sambatu natafara "yaya Hameed kana Ina kace man MUNA TARE komai wuya da tsanani kace Ruwa. ko iska MUNA TARE wayyo ni Jidda nashiga  tasku Allah gani gareka ka taimakeni

Tashi tayi toilet kawai tashiga tayo Alwalla tayi sallah ra'ka biyu dauko Alquran tayi tafara karantawa nan taji zuciyar tafara sanyi Domin Alquran Haske mai kauda Duhu kowane bawa inhar musulmi
Inhar yashiga damuwa  dauko qur 'ani kaduba zakaji sanyi yana ratsa zuciyarka.

Allah yabarmu cikin musulchi mu mutu Cikin shi Allah yakaramana Son Annabi Muhammad (s.wa)


Jidda tanagamawa tarufe Alquran tayi daga Hannu ta tayj tace " ya ubangijina mahallicin sammai da kassai  Ina roko gareka kasan halin danake ciki ya Allah kabani ikon cinye jarabbawa dakakeman"

Nan tayi Addu'a tashafa.


               Washe gari

Yau Alhaji Ibrahim kedawo daga tafiyar dayayi zuwa kasar Egypt Akan harakar business dinshi.
Hajiya zainab sai girke girke Ake takanas inna tashigo don tayata Aiki  Akan girkin dawowar maigida

Sun kammala komai Anshiraya komai Abisa dinning table

Karar mota sukaji Almar ya iso cikeda da murna Khalil da sameer suka fito tararshi Domin yau sunce bazasu fita office ba sai dady yadawo cikin sauri suka ruga suka rungumeshi

Shima cike da murna
 Yarungumesu

Shima Baba cikeda murna yazo yayima dady sannu dadawo

Alhaji Ibrahim yanashiga  D'akin shi kawai yanufa wanka yayi yafito Dining table yanufa tare da taimakon Momy yaci Abinchi.

Momy tace "dady twins inadauke da wani Albishir"

Dady Aje spoon dayake cin Abinchi yajuyo wajenta menene fadaman
Tace "kaidai ida cin Abinchin
Zan fadamaka"

Khalil  kuwa mikewa yayi  yace "dady natafi office domin inada patients saina dawo"

Sameer yace "nidai bazan fita yau ba sai gobe in Allah yakaimu lafeeya"

Khalil kuwa fitowa yayi yaja motarshi. Sai Asibiti.

               _HOSPITAL_


Isarsa kenan D'akin daakwantar da Hameed Aka kwantar dashi yanufa sallama yayi yagaidasu da dady sannan yaduba Hameed yaga jikin yayi sauki  Amma haryanzu Akwai damuwa tare dashi

Fita yayi yanufi office Domin duba patients dake jiranshi.



Hameed buda idanuwansa yayi wadda  wannan shine nabiyo  tun zuwansu dasauri  momy sukataso suka iso gareshi tareda cewa "Hameed sannu"

Hameed Cikin muryarshi ta marar lafeeya yace "Momy  Jidda tadawo ne Anganta??"

Cike da tausayi   Hajiya zainab "tace Takusa zuwa Hameed  kajiku"

Rintse idanuwanshi yayi kawai.



             BAYAN KWANA BIYU




Alhaji Ibrahim zaune tareda Hajiya  maryam sai Inna da Baba Jidda Khalil sai sameer,

Alhaji Ibrahim yajuyo wajen Baba yace "malam Abdullahi wato dalilin taraku nan  shine Maryam ce tazo man dawata magana wato Khalil yanuna yanason Jidda  nayi farin Cikin haka Amma nace Bari nataraku naji ta bakinku"


Malam Abdullahi yace"Alhaji Wallahi komai kayi wajena daidai ne domin kayiman Abinda bazan taba mancewa ba"


 Alhaji Ibrahim yajuyo wajen Jidda yace "jidda kinason Khalil?"

Jidda jitayi kamar me taji dady yayimata kwarjini  kuma bazata iya kunyata Baba gyada Kai kawai tayi

Alhaji Ibrahim yace "Alhmdlh to"


Jidda tashi tayi kawai yashige D'akin sundauka duk kunyace  yasata haka

Fadawa tayi  Bisa Gado wani matsanacin kuka  yazomata  "yaya Hameed Kai kadai nakeso babu kowa Cikin raina sai Kai  Wallahi banzataba rayuwa da wani namiji ba sai Kai"

Kuka tacigaba dayi kamar me.


             After one month




Hameed sauki sai wurin Allah   Kullum maganarshi
Bata wuce ta Jidda.


Jidda ce D'akin inna zaune inna tana rarrrshinta Domin Jidda takoma kamar ba ita tarame sosai  Kullum cikin kuka take

Inna tace "Jidda ki rungumi kaddara da kinji ko nasan kinason Hameed Amma bekamata  Mu butulcema Alhaji ba"

Jidda goge hawayen tayi tace "shikenan  inna  Bari nakoma cikin gida"

Inna cikeda tausayin  Jidda tace tou kita Addu' a"


 Jidda tanashiga  ta iske momy falo samun wuri tayi tazauna

Momy tace "harkin dawo  ne??"
Tace "
"Eh Momy "
 

Kamanshi wani turare taji saurin waigawa  tayi taga Khalil maido idanuwanta tayi ta cigaba da Kallonta samun wuri yayi yazauna yayi

Momy kuwa mikewa tayi tabar falon

Jiddq!! Khalil yakirata  juyowa tayi tace "yaya Khalil"

Yace "Jidda  meyasa tun lokacin da akayi maganar  dake maimakon kibani   kulawa  wadda  masoya keyi Amma daga  yaya Khalil baki furta komai"

Jidda sadda Kai tayi tace "yaya Khalil zandinga Baka"

Yace "yauwa
Yanzu tashi zakiyi  kirakani
Super market kayan Amfani sunkare"

Jidda jitayi batason gardama dashi Tace "OK"

D'aki kawai tashiga tazuro hijab suka fito mota suka shiga
Sai  sahad store


Hajiya zainab zaune tayi tagumi dady yafita yadawo
Hameed cikin wata murya  yace "Jidda!! Dasauri momy tataso
Hameed!! Sannu 
Hameed yace " momy kice Jidda tazo gareni Karna mutu"

Wani numfashi yaja sai gundarin jini

Hajiya zainab dagudu tafita

Khalil sungama sayayar sunfito wayarshi yaji  tayi Kara dagawa jinayi yace ganinan
Juyowa yace ma "Jidda zamuwace Asibiti jikin patient daakwoman yatashi"

Asibiti  suka nufa.

           Hospital

Dasauri yayi parking din motarshi
Yafito yanufi  D'akin da kwantar da Hameed yayi

Jidda jitayi kawai  tanason ganin  wannan patient din
 Bin bayanshi tayi
Khalil yanashiga yaga halin da Hameed yake ciki momy sai kuka  take

Gadon daake tura marar lafeeya Akasa  Hameed

Sai Emergency room.

Daidai isowar Jidda

 Kallon wadda ke kwance bisa
Gadon tayi  wata Kara  tasaki

Yaya Hameed!!!!
Tasulale sumamiya



Luv you my fans💚💙💜
[3/3, 11:14 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝


💝💝💝💝
            💝💝
               MUNA TARE
 

               Na
Hapsat Musa




®
Perfect writes forum

P.W.F.




91_95





Jidda kallon wadda ke kan gadon tayi ido hudu tayi da Hameed wadda baisan inda kanshi yake ba

Wata kara tasaki Yaya Hameed!!!

Tafadi sumama Khalil rikecewa Ganin Jidda tazube kasa gakuma Hameed cikin wani matsanacin Hali.

Waya yadauko cikin rudewa yakira Sameer
Dasauri Sameer ya iso yana office dama

Dora Jidda itama Akayi  wani D'aki ne Wadda Ake bada taimakon gagawa wato Emergency room

Sameer tsaye kanta shikuma Khalil yanufi  wajen Hameed zuciyar sa cikeda wasi wasi meyaha Jidda da wannan inata sanshi dahar ganinshi yarazanata.


_After_one _hour_

Jidda tafara buda idunawanta Ahankali dishi  dishi tafara gani  can kawai ta wani zabura tamike.
Daidai shigowar Khalil
D'akin

Dasauri yanufi wajen Gadon yace "Jidda menene haka"

Cikin kuka tace "yayaKhalil   Ina fatan yaya Hameed yana da rai bai mutu ba don Allah ka kaini naganshi"
Mikewa tayi Almar sutafi

Khalil cikeda mamaki yake binta.

Ganin bashi da Almar tafiya
Jidda takara fashewa dawani
Cikin sheshekar kuka tace "yaya Khalil don Allah ka kaini naga yaya Hameed"

Khalil yace ",Jidda kwantar da hankalin  Zan kaiki kiga ganshi Amma waye wajenki"

Jidda Tace "zanfadamaka nidai burina yanzu na
Ganshi"

Khalil juya baya yace "zo muje"

Bayanshi tabi har D'akin da aka kwantar da Hameed suna shiga. Kota kan su momy da dady ketsaye

Dagudu ta nufi gadon da Hameed ke kwance
"Yaya Hameed katashi don Allah gani gareka kar ka mutu kabarni inhar kamutu bani da  kingi moruwa tare dani wallahi yaya Hameed kaine  jinin jikina kace MUNA TARE abadan Da'iman

Jitayi Andafata  momy ce Hajiya zainab tadafata tace "kiyi shiru kinji ya'ta zai tashi"


 Jidda dago fuskar tayi cikin saurin domin kwata kwata bata ga Akwai mutum ba
(So kenan😂)

Sunkuyar dakanta kasa kawai tayi.
Alhaji hamza naira banza kuwa cikin murna cikin Ranshi yana Hamdallah ga Allah yau ciwon  Hameed yakare.

Juyowa yayi wajen Khalil wadda yayi mutuwar tsaye yace "Doctor kaga damuwar Hameed nan shine ciwon shi nataikai tamaka shine silar CIWON shi"

Khalil dama tuni zuciyarshi dama tafara wani dam cikin ranshi kuwa  cewa yake
 Dama silar damuwa   Jidda kodayaushe zaka Ganta cikin wani yanayi har sanadiyyar shigar ta damuwa  Hameed ne

Alhaji hamza naira banza yakatsemashi tunanin dayake yace "Doctor yanzu yajikin Hameed din"

Khalil yace nayimashi wata Allura sainan da kwana ukku sai farka insha Allah "

Alhaji hamza naira banza yajuyo wajen Jidda yace  "yarinya inaso ki hadani da iyeyenki yanzu basai Anjima ba"


Jidda dago fuskar tayi takasa magana  

Khalil yace "babu damuwa zamu iya  tafiya"

Nan sukafito suka shiga motar Khalil sai gidan Alhaji Ibrahim
Parking yayi duk suka fito runguda sukayi sai cikin falon cikin Sa'a Aka iske momy wato hajiya maryam sai Alhaji Ibrahim zaune
Cikin falon.

Jidda da  Khalil sukafara shiga sannan Alhaji Hamza shida matarshi Hajiya zainab

Tareda sallama suka shiga momy Hajiya maryam mikewa tace "Khalil tare kuke da baki ne"
Khalil yace "Eh"

Samun guri sukayi sukayi suka zauna  dasauri momy tadauko musu ruwa sukasha hade da juice mai sanyi.
Bayan sunsha ne

Khalil yace yace "dama maihaifan wannan patient din ne wadda nake fadamiki momy"
.

Cikin fara'a momy tace "sannuku yajikin nashi"

Hajiya zainab tace "Alhamdullah"

Alhaji hamza naira banza gyara murya yayi yace "wato  Ina tafe da wata magana"
Inason ganin  iyayen wanna yarinyar yanuna jidda"

Alhaji Ibrahim yace "inafatan  lafeeya"

Alhaji hamza naira banza yace "babu komai sai Alkairi "

Alhaji Ibrahim yace "to Alhmdlh"

Juyowa yayi wajen Khalil yace "kiran malam Abdullahi kacemasa yatafo damai Da'kinsa"

Khalil mikewa yayi domin cika umurni  mahaifinsa
Zuwa yayi yafadamusu yadawo

Baayi minti biyar saigasu sunshigo 

Samun wurin sukayi suka zauna

Alhaji Ibrahim yace "tom ga iyeyenta sai kafadi Abinda ke tafe dakai"

Alhaji hamza naira banza  gyaran murya yayi yace to Alhamdullah godiya ta tabbata ga ubangiji

Dafari zanfara Neman Afuwar malam Abdullahi wato mahaifin Jidda.

Malam Abdullahi yadago fuskarshi.

Alhaji hamza naira banza yace " zakayi mamakin haka daga gareni

Nine dai sunana Alhaji hamza naira banza mahaifin Hameed.
Nakasance natsani talaka bana son tarayya dashi ko kadan Anahaka sai Hameed yakawo maganar yana son
Yar wajenka natambeyeshi
Meye sa'anarka yafadama faci kake na hurgaleshi da wannan maganar
Nadauka yabar maganar

Rannan nazo shiga D'akinshi sai naji yana waya har yana cewa zai budemaka shago kadai na faci sai Azo Ayi maganar bikinsu naji taikacin haka nan zuciyata tabani shawarar natura Hameed  kasar England Akan wani company na nanumashi na Aminche daya dawo zaayi maganar shi da Jidda

Hameed yana tafiya nahau bincike domin yafadaman unguwar nan naji gidan dasuke haya suke nan Aka bincika mai gidan wadda yabasu Haya naba direba na
Makudan kudi Akan Asayi gidan nan da malam Abdullahi yake ciki

Insukatashi  nasan Hameed inyadawo yaga basunan sai manta Ashe  bahakabane
Tun lokacin da yadawo yaga basunanyashiga halin ciwon zuciya.
Yau gani inarokonku kuyafeman  nayi nadama nagane kudin  basu sayen komai    A rayuwa iyakarka dasu nan duniya"


Malam Abdullahi yace "nayafemaka"

Alhaji hamza naira banza yace "Nagode kema Jidda kiyafeman"
Sunkuyar dakai Tayi tace "nayafemaka"

Alhaji hamza naira banza yace "Alhmdlh sai magana tagaba inason kuba Hameed Auren Jidda gobe Adauramusu domin sonake Abinda kunneshi zaifara ji kenan"

Malam Abdullahi yace "saidai kayi Hakuri Jidda tanada miji yanzu kingin wata2 bikin"

Khalil yadago fuskar shi yace Baba nahakura nabarma Hameed ita Domin da Hameed tafi dacewa  da rayuwarshi take Neman salwata kuma duk wadda yafaranta ran mumuni dan uwashi tamkar yafaranta ran musulamai duniya  ne"

Alhaji Ibrahim yace "ka kyauta Khalil Allah yayi maka Albarka "

Juyowa yayi wajen Malam Abdullahi yace "Ka  Aminche  Jidda tazamo matar Hameed?"

Malam Abdullahi yace "Wallahi Alhaji nabaka komai komai kayi lafeeya Lau.

Alhaji Ibrahim yacema Alhaji hamza naira banza " gobe kakawo goro da sadaki A daura  Auren Hameed da Jidda"

Dagudu Jidda tabar falon

Shima Khalil cikin karfin haliyamike yanufi D'akinshi
 Fadawa yayi bisa gado domim kanshi yaji yana juyamasa
Allah sarki Khalil.




BATTERY LOW☹☹
[3/4, 3:54 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝.  
            💝💝
             MUNA TARE
                    Na
                Hapsat Musa


®
Perfect writes forum

P.W.F.


GODIYA GAREKU MASOYANA ADUK INDA KUKE NAGODE DA KAUNARKU.
SAKON GAISUWATA GAREKU

Mrs Asheer🎓
Hasweet
Sakeena kabeer
   Nana A Usman             
Salma Lagos
Mumcy husna
MissAysheer (Zarah)
Eashar💞
Aysha(rufaidah)

NAGODE ILUV YOU ALL MASOYANA💛💚





96_100





Jidda tanashiga D'aki fadawa tayi bisa Gado Murna yau Allah yahada da muradin ranta wadda kodayaushe badai sonshi yaragu Cikin zuciyarta saidai
Akullum  ya karu.

Momy  ta turo kyauren D'akin tashigo kusada  da Jidda tazauna.
Tace " Y'ata  dama Akwai wani cikin ranki Amma baki taba fadaman ba Harki kika Aminche da Khalil yazamo miji Agareki"
Jidda dai saddar da Kai kawai tayi    batace komai ba

Momy tace "nasan dalilinhaka Jidda nagode da karamchi dakikabamu  kin nunaman zaki iya sadaukar da farin cikinki Akan  namu
Har yanzu kina matsayin ya'ta saima Abinda yakaru cikin Allah yayimaki Albarka
Yabaki zaman lafeeya da mijinki"

Nayi saurin cewa Ameen
Domin Jidda kunya kawai takeji tasaddar dakanta kasa.


Bayan su Alhaji hamza naira banza sungama magana suntafi

Alhaji Ibrahim yajuyo wajen
Baba yace ",inafatan malam Abdullahi banyi shishigiba ko?"
Baba yace  "wallahi Alhaji bakayi shishigiba kodan zaka iya komai kayiman Abinda bazan mantaba"
Dady yace "nagode"
Nan dady. Yafara kiran Abokanshi da yan Uwa da  Abokan Arziki Akan Akwai daurin Aure gobe.

                _Hospital_

Momy ce hajiya zainab tare da Alhaji hamza naira banza suka shiga D'akin da Hameed yake kamar yadda suka barshi yana kwance
Dady cikin murna yace My son Zan cika burinka zaka Auri wadda kakeso"

Itama momy cikin murna takirasu hanan da Hannefa tafamusu cikin murna sukace zasuzo jibi domin sunada  test gobe.
 Shima nan Dady yakira yan Uwanshi yafamusu Domin iyeyenshi duk sun mutu kuma shikadai suka Haifa
Shiyasa yamallaki dukiya  mai tarin yawa.


Sameer yashigo D'aki cikin sanyi jiki domin daowarshi kenan  Dady yafamashi komai 
Kusada da Khalil yazauna yace "Brother!!!" Khalil yadago fuskar shi ya kalleshi saurin   kaudar da damuwar Fuskarshi yayi   yace "Brother yaushe kashigo banji shigowar kaba  ne??"

Sameer yace "tayayazakaji shigowata kashiga tunani 
Nidai Abinda zance maka brother don Allah karkasa komai cikin ranka har kaje  kahadu dawata lalura"
Khalil yace "karkadamu Brother insha Allah daga yau nadaina tunanin Jidda"
Sameer yace yauwa ussaini na"
Khalil yace "ninema ussaininka nariga fa zuwa duniya"
Nan suka cigabada firar su ta  yan uwa


               Burin masoya



Yau burin  Hameed yacika Jidda tazama Mata Agareshi wadda dady Alhaji Ibrahim ya Amshi  sadakin Jidda yazama uban  Amarya
 
Akan sadaki 50k
Ancika sai kace ba gayayar gagawa ba
Andaura Aure Ango nabisa Gadon Asibiti Anyi taro Antashi lafeeya


Jidda kuwa tana D'akin inna wani farin ciki taji yana shigarta kaji su  jidda😂😂
  Domin yau burinsu yacika sunzama Mata da miji
Wannan kenan

Baba da inna ne D'aki daJidda
Baba yace "to Jidda yau dai kinzamo matar Hameed dama can Allah yace shine mijinki babu Abinda zamuce sai godiya ga Allah maihafim Hameed yanemi kije kicigaba da jinyar mijinki har ya warke zuwa Anjima insha Allah zaki tafi Asibiti har yawwrke"

Jidda sunkuyar da kanta kawai tayi tatashi tabar D"akin

Baba yajuyo wajen inna yace "kinga takadariya KO"
Inna murmushin tayi kawai

Jidda nafitowa kuwa. Zashige part din su momy
Cikin karo tayi da Khalil  dasauri takoma baya tace "yaya Khalil ya Hakuri bangankaba"
Yace dama tayaya zaki ganni kina cikin farin ciki yau kinzama matar Hameed

Dariya kawai tayi taruga cikin gida.



Direba  ne yazo daukar Jidda domim tafiya Asibiti sukayi bankwana da momy  tashiga bangaren inna sukayi bankwana sai Asibiti.

                 _Hospital_


Suna is a Asibiti direba yaajeta tashiga bangaren D'akin Hameed cikin kunya ta tura kyauren tashiga Hajiya zainab cikin murna ta tatashi tataro Jidda  Jidda kuwa sai sunkuyar dakai take.
Hajiya zainab tace "kidaina jin kunyata kiji ko"
Gaidasu tayi cikin Fara"a
Alhaji hamza  ya Amsa   domin yanzu Alhaji hamza naira banza  yasaki da tsanar talaka dayayi

After 10 minutes
Su dady sukayi ma  Jidda bankwana tunda ga matarshi kusadashi.
Suna bankwana.
Jidda nurse suka Kara shigowa suka duba jikin Hameed suka fita.

Jidda dawowa tayi ta tsaya kusada Hameed kuramashi idanuwatayi tana Hamdala
Cikin ranta
Gadon da  Hameed yakesama Jidda tahau jikinshi tashige ta runkumemeshi kamar wani zai kwaceshimatashi
Daganan barci yadauketa cikeda farinyaugata  Gado Daya da Hameed dinta

              Washe gari

Doctor Khalil yaturo kyauren D'akin da Aka kwantar da Hameed yayi yashigo Domin Kara duba jikin Hameed
Abinda yagani yasa shi juyawa Domin Jidda ce ta runkumemeshi dasauri yafita.

Bayan kamar minti 10 dafitarshi Jidda zumbur tamike ta kalli Agogo  karfe 8:45am dasauri tadiro daga bisa  toilet tanufa tana fashin sallah wanka tayi kawai  tazura doguwar Riga
Dama tasako kayanta cikin dan Akwati

Turo kyauren D'akin Akayi  su momy ne suka shigo dasauri Jidda taje ta Amshi kayan  Hannuta
Har kasa ta durkusa ta gaidasu
Momy tace "Jidda hada breakfast kici kinjiko
Jidda sunkuyar dakai tayi momy tace Bari nahadamiki kaina nan momy tahadamata  tea mai kauri hade da soyayan dankali.

Hameed ne yafara motsa Hannushi momy talura dasauri  tajoyo wajen dady tace "kaga yanan juya Hannushi"

Dasauri dady suka taso shida Jidda suka  nufo gadon Anhankali Hameed yafara buda  idanuwanshi sukafara dishi dishi
Arba yayi da Jidda Kara buda idanuwanshi yayi yace
"Momy nahaukace  idanuwana  sunfara gizo Jidda nake gani gabana"

Momy tace "Hameed ba gizo bane  Jidda ce gabanka kuma matsayin matar ka"

"Momy na dagaske kikeaman KO kikayi man da hankalina ya kwanta
Juyiwayayi wajen dady yace dady dagaske"
Dady yace dagaske ne Hameed "

Khalil ne  yashigo   D'akin  dasauri yanufo wajen Gadon  ganin  Hameed kwance kuma yana magana  Kara dubashi yayi yace "Juliet ciwo yakare ko"

Hameed murmushi karfin hali yayi  kawai.

Nan Khalil yakara dubashi yaga babu wata matsala yanzu.

Yacema su momy yanason ganin su office
Akabar Jidda da Hameed sai Aikama juna sako suke na Kallo
Sundauki minti goma suna Kallon juna.

Hameed cikin murya shi ta marar lafedayi  yace "my Jidda matso kusada Dani pls dasauri Jidda tafada  bisa  Hameed  rungume tayayi tsam tsam jikinshi
Kawai sainaga  Hameed da Jidda suna kuka
Kiss din Jidda  ya cigaba dayi nan naga Hameed sai rude  dasauri nafita  daga D'akin

   

Luv you my fans💚💛
[3/5, 8:07 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
            💝💝
             MUNA TARE
               Na
           Hapsat Musa



®
Perfect writes forum

P.W.F.





101_105







Ganin Hameed yana nema fita hayyacisa yasa Jidda tashi jikinshi
Hameed yace "meyafaru my Jidda zaki tashi?"


Cikin shagwaba tace "yaya Hameed Baka lafeeya fa kuma gadon Asibiti kake"
Hameed murmushi yayi yace "ganinki yadaukeman kowane ciwo taredani  My Jidda kisani kece rayuwata inasonki my honey"
Jidda tace "yaya Hameed nima kasan inasonka fa"

Turo kyauren D'akin Akayi kyakyawan yan Mata ne guda biyu cikin shigar Arabian gownt.
Da sallama suka shigo
Gurin da Hameed yake suka nufa.

Sukace  "yaya Hameed cikeda da murna da farin ciki suka furta haka"

Hameed yace "sisters kune tafe yanzu"
Cikin murmushi sukace "yaya mungagara munzo muganka ne"

Waiwayo yayi wajen Jidda wadda tunshigowarsu babu Abinda tace sai kallon su datake.
Yace "my Jidda kinga kanena nan Hanan da haneefa"

Jidda cikin murmushi tace "sannuku"
Cikin fa'ara suka nufo wajen Jidda sukace "my Aunty ciwon yaya yawarke tunda gashi gaki KO"

Sunkuyar dakai kawai Jidda tayi.Su haneefa sunyi murna dazabin yayan nasu
 Domim tun lokacin ciwon ya'yanasu suka san kudi Ba Abakin komai suke ba  mutum yafi komai daraja Arayuwa ko yayake.

Turo kyauren D'akin daakayi Akashigo momy ne tare dady suka dawo daga office din Khalil yabasu wasu shawarari game da ciwon Hameed.

Dagudu su haneefa suka rugo suka rungume momy.
Itama momy cikin farin ciki ta rungume su.
Jidda duk kunya ta isheta ga kuma wani mayatatacen kallo da Hameed ke aikatamata.
 Saikace ba wadda yasha jinyaba .
 Sunan har lokacin tafiyar su yayi Akabar Jidda itada Hameed dinta.
Har waje Jidda tarakosu takoma ciki
Tanashiga  D'aki Hameed yakara binta da wannan Kallon nashi
Cikin shawgaba Jidda tace "wai yaya Hameed tundazu sai kallo na kake"
Hameed yace my Jidda bazan gaji da kallon ki ba kodayaushe wallahi"
Jidda murmushi kawai tayi
Tace "yaya Hameed bacci nakeji"
Hameed yabuda fadada kirjinsa yace zoki kwanta nan my Jidda naji dumin ki domin yanzu kinzama mallakina halak malak"
Jidda shigewatayi kirjin Hameed
Hameed Kara runkumeme Jidda yayi jikinsa. Kamar wani zai kwacemashi ita har bacci yadaukesu cike da farin ciki da Annushuwa.


              Bayan sati  daya


Hameed yawarware sai kace babu wani ciwo da yakwanta  inka ganshi yakara wani fari da haske kyau nashi yakara fitowa
Yau kwana daya da bashi sallama.
Yau kuma zasu koma katsina.

Hammed ne zaune  sai Jidda sai Baba, inna,  Alhaji hamza naira banza, momy hajiya zainab
Momy hajiya maryam sannan Khalil da sameer
Sai Haneefa da hanan

Alhaji Ibrahim ya gyara murya yace "godiya ta  tabbata ga Allah dayabamu ikon haduwa nan
Muyima Annabi Muhammad (SWA) salati goma goma
Nan falon yayi tsit Anayi shuganbamu Annabi salati.
Bayan kowa yagama sukayi Addu'a Aka shafa.

Alhaji hamza naira banza yace "Babu Abinda zance face namika godiya ta ga Allah daya hadani da mutanan masu karamchi  Nagode sosai da Abinda kukayiman Nagode 
Yajuyo wajen  Khalil yace
Doctor banida bakin godemaka nagode inhar banmaka shishigiba domin har ga Allah inason hada zuri'a daku.
Nabaka Auren   Haneefa inhar Baka Aminche ba kafadaman tunda wuri domin ita Hanan sundaidaita da wani dan Abokina inka Aminche kafadaman"

Khalil sunkayar dakanshi yayi yaji baza iya ba dady kunya ba yayimashi kyauta kuma yace bayaso
 Yace "na Aminche  dady kuma Nagode da kyautar dakayiman.

Alhaji hamza naira banza yace "Nagode sosai  Khalil"

Yajuyo wajen Baba yace malam Abdullahi Abisa  Abinda na Aikata gareka  Gidan danasaya don na cusguna maka  nasa Anyimishi gyare gyare  na makallah mashi yazama naka har Abada don Allah kar kace komai   Malam Abdullahi"

Baba saboda murna kasa cewa yayi komai sai hawaye yau Allah ya mallakamashi gidanshi nakanshi
Juyowa. Yayi wajen Dady yace "babu Abinda zance face nace  Allah yasakamaka da gidan Aljanna"

Yajuyo wajen dady Alhaji Ibrahim yace "Alhaji  Katayani godiya wajen shi"

Alhaji hamza naira banza yace ma dady "don Allah karakace komai nayi wannan Abu saboda Allah"

 Alhaji Ibrahim yace "Allah yashigemana gaba to" suka Amsa da Ameen

Alhaji Ibrahim yace" nima Malam Abdullahi inada wata karamar super market Akatsina na mallakama maka ita nima naga harkar business Dina yayi yawa katsina  kuma nagama gini na Zan koma can dazama"

Inna da Jidda da baba kuwa fashewa sukayi da kuka jin kyautar da Allah yayi musu lokaci daya Allah kenan
Nan

Ba kunya Hameed yaja Jidda sukabar falon.

Sun shirya tafiya Akan Gobe zasu tafi katsina

Hameed D'aki yashiga yarungume Jidda jikinsh yace Haba "my Jidda meye nakuka" Jidda kara shigewa jikinsh tayi tace " Heart beat bakaji kyautar dakayiman ma baba ne"

Hameed yace "naji Jidda  Allah kenan mai Azurta bawanshi Akan  duk wadda yaso kidaina kuka kinji my secret"
Nan yarrrasheta tadaina kuka
Sumbatar yafara ta ko ina lebenta wadda suke matukar burgeshi  yajawo yafara kiss dinshi kokarin zage ma zip din Riga yake kawai har yazuge zip din  zai tura Hannushi cikin rigar
Jidda takadarshi cikin wata murya "yaya Hameed kayi Hakuri wani nafa iya shigowa.

Kallonta Jidda ta tsorata ganin yadda idanuwan Hameed suka koma ja kamar mai ciwon ido

Dawata kasalaliyar muryashi yace "Jidda inabukatar naji duminki" wallahi Kara matsowa yayi Jidda mikewa tayi dagudu tafice domim ta tsorata ganin  yadda Hameed yakoma lokaci daya.

Hameed gyara jikinshi yayi shima yafito falon
Yanafito ya iske Jidda cikimsu Haneefa sai fira suke Kamar sundade tare.dinan
Shima samun kujera yayi sukacigaba da fira shidasu sameer
Khalil da Haneefa suke.
Hameed shima Abu kadan ya kalli Jidda.su dady dama sun shiga ciki.

                _Washe gari_

Su dady duk sun shirya sunhada kayansu su Khalil kawai Akabari Akan suma zasu tafo inda inda sunduba cikin doctors dinsu  Akan wadda zasubar Amanar Hospital dinsu.


        Har Airport suka rakosu harsuga tashin jirginsu sannan sukayi bankwana.

              Katsina


Jirginsu ya iso katsina A filin jirgin Umar Musa yar Aduwa(Allah yajikan Umar Musa)

Dady Alhaji hamza naira banza yakira direbanshi yazo yadaukesu Gidan Alhaji hamza naira banza suka zarce dama momy tayima  ma'akatan gidan suna tafe Anshirya girki kayatatace
Kan dinning suka cika cika cikinsu
Sannan sukayi bankwana  direba dady Alhaji hamza naira banza yakaisu Alhaji Ibrahim gidanshi wadda Ankamallah komai har saukar Alqurani Anyi ba saudauya baso biyu ba
Wadda yake Aikoda kudi Akemashi.

Bayan direva yakai su dady yadawo zaikai su inna nanfa Jidda tafashe da kuka zasu tafi subarta  domin bata taba rabuwa dasu ba sai yau
Suma su baba dauriya kawai sukayi dama inna tun katsina tayi Mata nasiha.
Momy hajiya zainab taja suka shiga ciki tanagamusu hannu.

Dady yace "to Hameed buri ya cika Jidda tazama matarka KO"
Hameed sunkuyar dakai yayi cikeda farinciki
Dady wasu takaddu yamikomashi yace "Amshi nan takadar gida nane dake  nan gaba damu nabaka shi har Abada yazama mallakinka Akwai komai na bukata ciki hatta Kayan sawa naka da Jidda Akwati Ashirin da hudu kowa shabiyu shabibiyu
Yanzu kadauki matarka kutafi  Momynka dama tunkafin mu I so tasa kande da larai sungyara Allah yabaku zaman lafeeya"

Hameed cikin murna yace "nagode dady Allah yakara Nisan kwana"
Nan momy itama takara yi musu nasiha ga zaman Aure.
Har waje su haneefa suka rako su Akan gobe zasu shigo in sun dawo school.

Hameed mota suka shiga bakin hanya yafita yasayi kaza sai sai cartoon din juices Kala Kala
Gidan yanufa
Masha Allah gidan yayi kyau ba karya 
Wurin parking yanufa yayi  sungumar Jidda yayi kamar jaririya suka shiga ciki

Bai zarce da ita KO Ina sai bisa gado  ya ajeta.
Jidda runtse idanuwanta tayi kawai  Hameed kusada ita yazauna yace "my Jidda tashi muyi wanka sai muyi sallah"
Cikin shagwaba tace "yaya nagaji kumafa nayi sallah ni"

Yace "my life  tashi kiyo wanka nima zanshiga bangaren nayi wanka"
Fita yayi Jidda mikewa tayi tadinga kallon bedroom dinta yayi kyau komai milk And morron ne
Wanka tashiga sabulu masu kamshi taradda dasu cikin nishadi tayi wanka ta tafito
Gindin mirror taje ta taradda Anjera mai mai Kala
Shafawa tayi
Wurin Akwatin kayan ta tanufa wadda tatafo dashi daga kano wata yar kwalba ta jawo wadda  momy taba  hajiya Maryam wadda   tace sai zatayi bacci zata fesa
Nan ta shafa jikinta  KO Ina
Nan jikin Jidda yadau kamshi  kamar tayi wanka turare

Rigar bacci tajawo wadda bata sawaba  tasa duba jikinta tayi taga yadda tayimata kyau 
Hameed yaturo kyauren D'akin yashigo rarumar hijabi tayi cikin kayanta tayi tasa   Hameed murmushi yayi Yace "zomuje D'akina  sungumar tayayi sai part din shi yace " oya shiga  kiyo Alwalla
Cikin direrren kafafuwa tace "yaya Hameed nayifa"
Yace "Wannnan dabam Ai
Take"

Shiga tayi tayo Alwalla suka tada sallah ra',aka biyu sukayi
Suka sallame nan Hameed yashiga kwararo Add'ua suka shafa

Jawo bakar ledar daya shigo da ita yayi yafiddo ya aje bisa plastic yafara ba Jidda  Abaki harta cemasa takoshi  kwanciya  zatayi saida safe
Hameed yace "ok"

Tayi hanyar zuwa  D'akin ta takashe fitilar gefen Gado 
Tareda jero Addu'a ta  shafa,
Sama sama  takejin  mutum Abayanta  zatayi ihu  ya. Toshemata baki da Hannusa
Yace "my Jidda  nine" shiru tayi  shikuma  rungume ta yayi yana shakar kamshi  turerenta wadda ya gigitashi  ga tausasar fatar jikinta  mai kamada Audiga
Samvatu yafara yima Jidda
Gabadaya jikin Jidda yasaki
Hameed yasamu  damar  sarrafa Jidda  yadda yaso
Jidda kuka tafashe dashi
Jidda Tasha Albarka wajen Hameed kuka kawai take
Hameed  kam yatafi wata duniya
Wadda baitaba shigartaba.
Nidai daganan basan Abinda  yafaruba naga Hameed yatashi razane
Naso daukomuku rahoto
Amma  waya tanunaman battery low
Kubiyoni


Luv my fans💛💚💙
[3/7, 9:02 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

           
         💝💝💝💝
                     💝💝
                      MUNA TARE
                          Na
    Hapsat Musa


®
Perfect writes forum

P.W.  F.




106_110






Hameed dasauri yatashi yashiga girgiza  Jidda  ganinta ta suma dasauri yabude firji yadauko ruwa yashiga yayafamata wani dogon numfashi taja dasauri Hameed ya rungume Jidda jikinshi tsam tsam yace "my Jidda sannu kiyi Hakuri bazan karaba"

Kwantar da ita yayi yashiga toilet  yahada ruwan Dumi yasa dettol yadawo yasungumi Jidda  harta cikin toilet yashiga da ita cikin bahon wanka.
Cikin shagwaba tace "nidai  kabarni nayi pls"
Yace "A,a my Jidda kibarni nayi miki kinji"
Nan Hameed yayimata wanka yabarta ta tsarkake jikinta.
Cikin towel yadota kamar baby yakowata bisa gado shima shiga yayi yayi wanka yatsarkake jinkinshi
Yadawo bisa rungume Jidda yayi jikinsa cike da farin ciki da walwala sukayi bacci.



Basu farkaba sai karfe  7:00am
Cikin sauri suka tashi domin sallar Asuba ta wucesu.
Alwalla sukayi sallah
Suka koma wani baccin rungume da juna tamkar wani zai gudu yabar daya.

Cikin bacci Hameed  yaji Ana kwankwansa gida A hankali yatashi domin  bayasan yatadda Jidda dake bacci.
Kofa yanufa yabude yaga larai da kwando.
Cikin girmamawata
Tace ",yallabai inakwana dama Hajiya tace ga Karin kumallo akawomuku"
Hameed Amsa yayi  yamaida kofa yarufe
Bisa Dinning table ya Ajeshi
Bisa Gado yakoma shafar fuskar  Jidda yafara yi Ahankali  yaga bata motsa. Kiss dinta yafara
Cikin Alamun bacci tabuda idanuwanta   Hameed yace "my secret tashi  ga momy can ta Aikomana da Breakfast"
Jidda sauka tayi tashiga toilet tayo wanka tafitowa
Tanufi D'akin ta  shiraywa tayi cikin wata super. Red And yellow ga Dinkin yayimata cif cif dakagani  gaka sabuwar Amarya😛😛

Hameed yashigo ya isketa tana daurin kallabi bayanta yazo rungumeta yayi yana shakar dadan turerenta.
Rikota yayi suka hau bisa dining
Bisa cinyarshi yadora yashiga  zubamusu Abinchi  Abaki yadinga ba Jidda. Itakam salon shagwaba tabude sai wani narke mashi take kamar jaririya shikam sai rarrashi yake.
Bayan sunguma Breakfast ne Falo suka dawo suka zauna Jidda matashi tayi da cinyar Hameed sukacigaba da Kallo.
Duk yinin Ranar babu inda yafita yana cikin  gida suna soyewa da my jiddarshi.


            After one month


Hmm masu karatu basai nafadamuku irin shakuwar da soyayya Jidda hameed ba  wannan lokacin soyayya suke kamar me.

Kwance take  bisa   jikin Hameed   Jidda cikin shagwaba tace   "My hubby yaushe zaka kaini gida daganan muje gidan Aminai kasan mundade bamu haduba suna cikin kewata"

Hameed shafa fuskar Jidda yayi yace "my Jidda gobe  yayimiki?"

Cikin murna tace "yayimani yayana mijina farin cikina abin Alfahrina"
Yace  "iluv my Jidda"

Kwankwsa kyaure Akafara yi Hameed yatashi yabude  Hanan ne da Haneefa suka shigo
Cikin fara'a Jidda ta tarbesu nan Hameed yashiga ciki yabarmusu dama yanason duba wasu files na company rigimar Jidda ce tahanashi tundazu sai shagwaba takemashi shikam inahar yana tare da Jidda baya iya komai

Nan tadauko musu girki hade da juice Nan Haneefa tace "Aunty na kar bikina da my Khalil gaskiya zaki koyaman girki nan naki hade da juice naki mai dandano"
Domin yanzu Haneefa zuba soyayya suke itada Khalil kamar me  sundawo katsina har Angina musu wata hospital din kaji Aikin manya

Jidda murmushi tayi tace "shikenan sai kinzo."

Hanan tace "hardani my Aunty"
Jidda tace  "shikenan duk zankoyamaku"
Nan sukacigaba fira kamar me domin Jidda wani lokaci gidansu Hameed take yini sai yadawo yabiyo yadauketa.
Har lokacin tafiyarsu yayi sukayimata bankwana sukatafi.

Jidda D'akin Hameed tazarce ta iskeshi yanaduba wasu files jikinshi kawai tayi masauki
Cikin shagwaba tace "love Aiki kakene"
Yace "Wallahi kuwa my Jidda zamuyi meeting nan da one week shine nake ta shirye shirye"
Jikinshi takomata takwanta nan Hameed yakarice Aje laptop din yayi da files yashiga shakar jikin Jidda
Kiss yacigaba da sakarmta ta ko Ina jikinta daganan suka duda duniyar masoya


Kuyi Hakuri nayi kadan bamu da nepa Amma gobe zanyi da yawa Insha Allah

Luv my fans💙💚💛
[3/8, 7:25 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
             💝💝
               MUNA TARE
                     Na
                  Hapsat Musa
                     
®
Perfect writes forum

P.W.F.



 111_115






Jidda ke ta shiri yau zataje taga Baba da inna sai kuma Aminanta na rai da rai
Wato beelatu Lawal da Rukkayya Hamisu.
Cikin wani material maroon tashirya yanada kwalliyar Golden tadoramasa Hijab Golden Masha Allah karkuso kuga kyau da Jidda tayi
Falo tafito wajen Hameed tanufa Cikin muryar shawgba tace "yayana  nashirya muje"
Hameed ya waiwayo wajen Jidda yaga kyau datayi
Sakin baki yayi yace "Anya my Jidda zamu fitahaka kinga yadda kikayi kyau kuwa"

Jidda didire kafafuwata tashiga yi tace "don Allah my Blood muje zakabarni nakwana Gidan inna ko"
Hararar wasa yasakarmata yace "kinaga zanyi jure rashin ganinki har nayini daya  ko kinaga Zan iya jure rashin. Tautasar fatarki ne"
Jidda tace"Allah ko love"
Yace "muje  inbahaka kuma nace nafasa zuwa muzauna cikin Gida"
Dasauri Jidda tace "sorry sir"
Rungume da juna suka fito
Suka shiga mota Gidan su rukky yafara kaita
Shiga tayi tareda sallama
Rukky tana bakin rijiya tana Jan ruwa Amsa sallamar tayi juyowa tayi wazatagani Aminiyarta  dagudu ta jefar gugan tarugu ta rungume ta
Mama dake Da'ki dasauri tafito "lafeeya rukkayya kika kwatsa wannnan Kara"
Ganin wadda ta rungume ne yasata Saki baki jidda!!
Har kasa Jidda ta durkusa ta gayarda mama
 rukky Jan Hannuta tayi suka shiga ciki D'akin ta
Cikin mamaki rukky tace "Aminiya inakikashige munje gidanku yafi sau nawa Amma bamu taradda dake"
Jidda murmushi tayi tagayamata komai.
Rukky tace "yanzu kinzama matar Hameed kenan"
Jidda tace "kwaraiko"
Rukky tace "gaskiya Aure yayi  kinga yadda kika canza kikara wani haske da kyau"

Jidda  bugu takaimata tace "banaso iskaci fa"
Rukky tace "wallahi Aminiya bakiga yadda kika canza ba  dama Muhammad yace "man zai turo naketa noke noke  Bari na Aminche kawai  nima naji dadin Auren na Da'kina nacigabada karatuna kinsan ko belly Sadeeq shima   ya Aiko Ansarana Kingi One month"
Jidda tace "yan  rainin wayo dakunce bazakuyiba"
Rukky tace daina wannan maganar Aminiya muncanza"

Wayar Jidda tayi Kara dasauri ta mike cikin  sauri tace "wayyoni Aminiya namanta da  my Hameed" waje surar jikka   tayi  tafito D'akin mama tashiga tayi bankwana suka fito tare  har wajen dasauri Jidda ta isa  gareshi Cikin tausarsar murya tace "sorry my sugar natuba"
Kamo kunne natayi yace "Ashe kinsa  kiyi laifi"
Cikin kukan shagwaba tace "zafi fa my Hameed"sannan yasaki rukky tana tsaye tana kallon  love.
Jidda wajen rukky yajuyo " my Hameed ga rukky fa"
Nan suka gaisa  Jidda sukayi musayar number tabata Address din gidan ta
Sukayi bankwana sanna suka tafi

Gidan su belly suka nufa itama tayi murna dazuwan Aminiyart daya tamkar da dubu itama  sukayi musayar number tareda bata Address.
Gidan Inna daganan suka nufa
Hameed yana parking
Jidda tafito dagudu  inna ta iske zaune dagudu tafada  jikinta  inna tace "lafeeya ki jidda" Jidda tace "inna murna Ganin ki ne fa "
Hameed dake shigowa yaduka har kasa yagayar da inna  cikin wani Kallo yace "kekuma daga buda mota sai ki wani shigo da  gudu"
Inna tace  Ai kamar yarinya goye take"
Zumboro baki ta kalli hameed wadda sukadai suka San ma'anarshi.
Jidda tace Inna "Baba bayanan ne?"
Inna tace "yaleka shago Amma yanzu kingansh"
Tashi tayi tazubomusu tuwon hade miyar kubewa sai tashin Kamshi yake takawomusu ruwa masu sanyi nacikin firji. 
Shiga tayi ciki tabarsu nan suka ciyar da junan su suka gama

Basu jimaba saiga Baba yadawo  Jidda tayi murna ganin Baba yadda yacanza inna ma ta canza
Jidda tagodema Allah.

Har lokacin tafiyar su yayi sukayimasu bankwana sukatafi
Inna ceke da murna da farin ciki ganin  yadda Jidda yadda ta canza.tayi kyau.

Daganan gidan su Hameed suka nufa sundade sannan suka tafi gidan cikeda farin ciki  da Annushuwa.

        BAYAN WATA HUDU.


JIDDA tafara rashin lafeeya  zazzabi Asibiti suka nufa nan Dr kesanardasu tanada ciki dan wata ukku sai fatan Allah yaraba lafeeya
Domin bamai laulayi bane shiyasa har yayi wata ukku basu Sani ba
Hameed sungumar Jidda yayi yagewaye office din da ita cikeda murna
Nan fa wani salon shagwaba yabude wajen Jidda
 Ba Kullum Hameed ke zuwa office ba.

Yanazaune yana rarrarrashinta
Yauma zaune yake  Jidda tana jikin shi tana  taunar Apple Abakinta   shikuma yana shafa kanta kamar jaririya.

Aka kwankwasa kyauren Hameed yatashi yabude su Haneefa ne tareda Hannah sai sameer Khalil sai wata budurwa  Hameed washe baki yayi yace "yau muna tareda manya baki Ashe
 Jidda jin yace sunada Baki Da'ki tashige tazuro Hijab  tafito cikin murna
Natarbesu nan taja Hannun Haneefa suka kawo musu juice. Tareda Abinchi
 Domin yanzu kingi 2 week bikin Khalil da Haneefa sun fahimci juna kamar me suna zuba soyayya
Sai sameer da  sadiya   patient dinshi ce daganan soyayya ta kullu sai Hanan da Angonta Ahmed
Sunyi nishadi Anyi fira domin yanzu da Hameed dasu Khalil sunzama yan Uwa .



Jidda ce tsaye kitchen itada  Haneefa da Hannan
Suna girki

Jidda tace yau "dai zanyi MACARONI SALAD Domin my hameed nasanshi"
Haneefa da hanan sukace  "mudai kallon ki My Aunty"
Jidda murmushi tayi tace  "Anatsu  Agani sosai"
Jidda tatanadi

_macaroni_
_kabeji_
_Gurji_
_karas_
_Albasa_
_tumatir_
_kwai_
_Man salak_
_Bakar hoda_
_peas_

Yadda tahadashi shine :_

_ta_ _dafa_ _kwai_ _ta_Aje _gefe__guda_
_sai_ ta  _zuba_ _macaroni_
A _tunkuya_ ta _yanka_ _kabeji_ da _Karas_ da _tumatir_ da _Albasa_ ta _zuba_  da _bakar__hoda_
Ta _barsu_ _sukayi_laushi, sanna ta sauke.
Sai tajuye A coller  takawo  da dafafen kwai ta yanyanka Akai tadawo  man salak  tahada ta cakuda.

Tace "wannan Angama"
Haneefa tace "Aunty   kibani nadadanana"
Jidda tace "Bari A idar
Yanzu zamu hada   FRUIT DRINK Abubuwan dazamu hada

_Abarba_
_Gwanda_
_Ayaba_
_Kankana_
_lemon_tsami_
Lemon zaki
_kwa_ _kwa_
_sukari_

Duk bayan ta feraye  su tasa A blender ta markada su tatace da rariya  mai laushi, tadankara sugar   da madarar ruwa,
Tasaka  A firji  tabarshi yakara sanyi sosai

Tajuyo wajen su  Haneefa tace  "nakamallah Yanzu zanje nayi wanka"
Haneefa tace "Aunty ibarmu mutafi dashi Gida kawai
Wannnan soyayyar taku Aimantawa kukeda mutum"
Murmushi kawai tace "Haneefa keama dai kin Kusa Auren "
Nan tadauko coller da jug ta ibarmusu suka yi bankwana sukatafi.
Jidda  wanka  kawai tashiga  kan  Hameed yadawo. Dirzar  jikin ta tashigayi kamar me hade da sabulu mai Kamshi
Tana fitowa tanufi Gindin mirror tahau shafa mai  simple make  up tayi tajawo wata doguwar Riga Atamfa tasa tafeshe jikinta da turare
Karar mota Hameed taji  dagudu tafito   shima buda Hannuwanshi yayi tafada cikin kirjinshi  yace "my Jidda nace kidaina  Gudu fa"
Tace nadaina My Happiness"
Rungumatar yayi suka shiga ciki
[3/9, 5:21 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝💝
💝💝💝💝
            💝💝💝💝
                        💝💝
                      MUNA TARE
                           Na
                        Hapsat Musa


Perfect writes forum
P.W.F




116_120







Rungume da juna suka shiga ciki suna shiga Jidda tafara ta Amshi jikkar takaita ma'ajinta  tadawo. Hameed yashiga wanka kan yafito harta fiddomashi kayan dasai sa  shirt ce mai gajeran hannu sai wando There quarter.
Harda turaren dasai fesa duk tafiddo taaje.
Fita tayi takara jera Abinchin bisa dining table tashirya komai
Takoma D'aki  iske. Hameed  tayi zaisa Riga dasauri ta isa gareshi Cikin muryar shagwaba tace "yahaka my Hameed kamanta Aikina banason kanashiga Aikina fa zamuyi fada fa"

Hameed yace "sorry  My only one baza karaba" tareda kaimata sumba Abaki
Jidda tagama shirya Hameed tafesa mashi turare  kamo Hannushi tayi suka nufi dinning  table
Bisa kujera daya suka zauna suna ciyar da junansu A baki
Hameed sai gyada Kai yake saboda santin girkin jidda dayakesa kunnen mutum yakusa tsinkewa
 Sunagamawa suka fito waje
Wajen swimming pool suka nufa suka zauna suna firar masoya har magariba ta gabato suka shiga ciki Hameed yayi Alwalla yanufi masallachi. Jidda kuma tada sallah D'akinta  dama tasan sai Anyi isha'i zai dawo .

Anatada isha'i tayi toilet tashiga takara wani wanka  tanafitowa tasa wata rigar pink  ta bacci  takara feshe jikinta da turere ta ko Ina jikinta tafito. Falo tana kallon wani film din Hausa   Ansayoshi  A Arewa 24 jinin jikina.
Bada jimawa ba sai ga Hameed yadawo shima samun wuri yayi yazauna Jidda tashi tayi tadauko mashi fruit drink tahada tadawo jikinshi ta kwanta
Har time din kwanciya yayi suka kwanta rungume da juna cike farin ciki da Annushuwa.Asuba tagari.

           Washe gari



Sunyi sallar Asuba sunkoma sun kwanta kafin gari yakara haske Jidda farkawa tayi takalli Agogo taga 7 saura kuma 8 am Hameed ke fita  Ahankali ta zame jikinta daga wurin Hammed ta nufi toilet tayi wanka tana fitowa tazura wata ready made din doguwar Riga tashafa ma jikinta mai simple make up tayi tadauko. Turare tashafa jikinta

Wurin gadon da Hameed yake tanufa sungunawa tayi    tafara huramasa kunne tare da shafar fuskar shi Ahankali  komawa tayi tafara sakarmishi Kiss Ahankali  Hameed yafara buda idanuwanshi yaga Jidda gabanshi cikin  tsari jikinta sai tashin kamshi yake  jawota yayi jikinshi cikin shagwaba tace "my Hameed time yayi fa na tafiya office"

Yace "Jidda  kece Kullum inmunatare mantawa nake da komai"
Dakyar Jidda ta lallabashi yashiga toilet  yayi wanka kanya yafito harta fiddo mashi  kayan dazai sa shadda ce tafiddomashi Dark blue hade da hularta sai takalma sannan  tureren .

Kitchen jidda tanufa Domin hada breakfast kan time din my hameed yayi ICCE TEA
Abubuwan da  Jidda tanada kuwa

Ganyen shayi
_sukari_
_lemon_tsami
Na'a_na'a
Kanumfari
Citta.

_yadda_ta hadashi shine:_
Tadora ruwa a tunkunya  tasa ganyen shayi da na'a_na'a da kanumfari da citta sai tadafa sukari da ruwa ta matse   lemon tsami  A Kofi ta  ajiye a gefe daya
Tatace ganye shayin da rariya  tazuba sukari da lemon tsami tasaka A firji don yayi sanyi kafin lokacin.

FRIED PLANTAIN
tashiga hadawa Abubuwan data hada sune.

Agada
Fulawa
Madara
Ruwa
Bakar hoda
Mai

Yadda tahada sune
Ta kwaba fulawar ne da gishiri Maggi da bakar hoda  ruwa_ruwa sai ta yanyanka Agadar yanka rawul tana tsomawa Acikin fulawar gefe guda  tazuba mai A kasko yayi zafi sai ta dinga sa wa tana soyawa.

Hameed ne yanufo kitchen "my Jidda mekeke girkawa haka gidan duk yadau kamsh"

Jidda tace  Kai "my Hameed banda zugani fa"
Yace "Allah kuwa"
 Tasanya A warmers duk Hameed yana binta da kallo hartagama  jerawa Dinning table
D'aki suka nufa tashiga shiryawa Hameed
Cikin Jidda yataba wadda yafara fitowa yace "Kwana biyu mundaina gaisawa da baby na sakar ma cikin yayi kiss yace my baby zanfita kayima Abbanka Add'ua"

Jidda dariya tayi tace "Kai my hameed yazaayi yajika"
Hameed yace yajinimana"
Nan suka fito sukayi breakfast tayimishi rakiya har bakin mota tare da Addu'a Allah yakikaye yabada sa'a




Bikin Khalil tareda Haneefa sai sameer da sadiya sai Hanan da Ahmed gidan su Hameed da gidansu Khalil yacika da mutane su Jidda sunzama manya sai hidima suke   Ana Aurar da kanne😛😛
Yau Ake party kuma duk wuri daya zaayishi suduka Angonan sunhada Kansu
D'aki suke zaune Anata shirye shirye tafiya duk Amare Haneefa da hanan duk sun sha make up A fuska  sunfito Amare  ga kunshi sunsha Jidda ba a barta Abayaba tayi shiri Cikin wani swiss lace pink Kai Jidda tayi kyau ga dan ciki yafitomata
Wayarta tayi Kara tanadubawa taga  Hameed ne fita tayi waje domin Cikin D'akin hayaniya tayi  kawayen su hanan

"Hello my dear"
"Kizo ganinan bangaren momy"
"Ok"
Bangaren momy tanufa shiru taji ta tsaya ta waiwaye jitayi kawai Anjawota
Sunfada D'aki
Hameed yace "my Jidda wannan shirinfa sai Ina ??"
Tace "Kai my hameed kamanta da partyn Din  su hanan ne"

Yace "zuwa zakiyi ne ?"
Tace "Eh"
Yace "Babu inda zaki"
Tace "haba  my hameed wasa kake KO?"
Yace "A,a dagske  nake "
Matsar hawaye tadinga yi tare da direren kafafuwa  jawaota yayi jikinshi "oya zokoyiman tausa ma"
Babu yadda ta iya zuwa party yafasu
Wayarta tayi Kara tana dubawa taga Haneefa ce daga tayi "hello Haneefa".
Haneefa tace "Aunty bazaki tafi ba"
Jidda tace "ganinan tame nida Hameed"

Haneefa murmushi kawai tayi tadatse  wayar tasan bazasuba

Hameed yace my " Jidda pls kije kitchen kihadaman coffee"
Tashi tayi tanufi kitchen
Tana fitowa  tayi cinkaro da momy
"Ahhh Jidda baki tafiba ne"
"Momy Hameed zahadama  coffee ne Amma yace bazanjeba"    Momy  tace Ai shikenan"

Jidda tanufi kitchen tahadomashi takawomashi  yanagama sha yajawo Jidda jikinshi sunata firar masoya .
Har Aka dawo daga party

             Washe gari

Karfe 11 Aka daura Auren Khalil da Haneefa sai hanan da Ahmed
Sai karfe 2 Aka daura na sameer da sadiya
Sai fatan Allah yabasu zaman lafeeya.

Marece nayi Aka Kai kowace gidanta tare da nasiha subi mazajensu
Hanan Akafara kaiwa sannan Haneefa
Ga gidan su Khalil ga gidajensu

Hajiya maryam tayi murna ganin Jidda sosai domin Allah yasamata kaunar Jidda

Daganan Hameed yawuto yadauki Jidda Khalil  yanayimashi tsiya Hameed saidai yayi dariya  kawai

Suna isa wanka kawai sukayi suka kwanta  tare da gajiyar Biki

Sai fatan Allah yaba Amare zaman lafeeya.

Ameen
[3/9, 7:27 PM] Hapsat musa 💝: 💝💝💝
💝💝💝

💝💝💝💝
           💝💝
           MUNA TARE
                Na
    Hapsat Musa

®
Perfect writes forum
P.W.F

121_125

```LAST``````PAGE```



          After 6 months



Yau tunsafe  Jidda ke nakuda, kasancewar Akwai ta da raki, barama  idan ta kusada Hameed shikam rudewa yayi  kiran momy yayi  awaya yafadamata  ga Jidda nan bata lafeeya.
Momy da tuni ta Dade  da jiran wannan ranar  tace  to wuce. Asibiti da ita, gatanan tafe.

Jidda kuwa cewa take "yaya Hameed kakiramani inna mutuwa zanyi kayafeman don Allah duk Abinda nayimaka"
Hameed yace "Jidda kidaina fadin haka bazaki mutuba  MUNA TARE tare zamu mutu"
Sungumar tayi sai mota    Allah yakaisu Asibiti lafeeya
Labour room kawai Aka nufa da ita Hameed sai shiga Aka dakatar dashi
Wayarshi yadauko yakira Baba yace mashi gasunan Asibiti Baba yace gasunan tafe
Kusan tare suka iso sudasu dady.
Nan sukayi cirko cirko
Baajimaba sai ga wata nurse tafito tace "cograt!

Hameed Yace " tsaya tukum yaya lafeeyar matata yake"
Nurse tace tana "cikin  kwanciyar Ahankali tasamu barci ne yanzu"
 Hameed Ajiyar zuciya yayi cikeda farin ciki  Yace "Masha Allah me Aka samu?"
 Tayimasa nuni da  baby dake rungume Hannu momy dasauri yakarasa  yana murmushi sai dai  yakasa cewa tabashi yagani.

Momy tace "tom inna baby girl ce sai dai muyi Hakuri domim yanzu  tasaye zuciyar mazajenmu"

Inna Amsartayi cikeda murna Ganin diyar Jidda da Hannuta Tamika baba shima yayi Mata Addu'a
Dady ma yakarbeta
Yayimata Addu'a
Dady yace "my son tundazu na Lura dakai fa kamar ka kwace baby nan daga Hannun mu"
 Hameed dariya kawai
Dady yace karbeta   Hameed yakarbeta yayimata Hudduba Akunnuwanta.

D'aki da akwantar da Jidda suka shiga Domin nurse tace musu tafarfado

Dasauri Hameed ya isa wajen Jidda sannu my Jidda
Itakam kunyarsu momy take
Nan Akabasu sallama duka suka wuce gidan Jidda harda inna
Akadorama Jidda ruwan zafi na wanka
Itama baby. Girl Akayi Mata
Inna tadorama Jidda tuwo miyar taji daddawa sannan takara sai dare sannan suka tafi Akabar Momy wajen ta domin tace zata kulata.

Haka momy tacigabda kula da Jidda kamar yarta domin Jidda Akwai shigar rai


              *RANAR* *SUNA*




Anyi suna na kece raini sosai domin hameed YaceYace baayi komai  a bikinsu dole Ayi buduri
Andafa Abinchi Kala Kala
Yan perfect writes sun hadu suduka rumfar su dabam

Can nahangi jannart tana  Asuwaki da naman kaza sai tura noma take.tana zare idanuwa

Big sister nayima maka magana
Don Allah big sister kijawota hakanan karta bamu kunya
Big sister jawota tayi
Amma duk dahaka sai datayi guzirin wani Cikin jikka
Waiwaye idanake tayi  ta watsamata harara kamar na duketa nakeji

Aminai Jidda sunzo rukky da beely kowace da goyen babyn ta Abaya
Su Haneefa kuwa sai laulayi Ake

Anyi taron suna Antashi lafeeya
Sunan diyar  zainab Amma zasudinga kiranta
          (Fannah)


         After 3 years


Hameed ne kwance dagudu  baby fannah tahayeshi Abba kataci kaikaini nasha Ice cream daganan ka kaini gidan wajen Aunty haneefa da Aunty hannan naga Amnah da Fadila

Hameed Yace to "yi sauri kije kiroka mana ummy inta Aminche sai muje"
Noke kafada tayi   tace " A'a  Abba  Kaine babba tunda kafi Momy karfi bazata iya dukan kaba ,
Zo kawai muje  Ainaga lokacin dazata  Gidan inna sai da ta rikoke"

Hameed dariya Yace "Fannah"
Jidda ce tashigo  tace  "me Ake tautaunawa ne"

Hameed Yace "babu ruwanki
Baby taso muje inkaiki wajen Aunty ki"
Jidda wani Kallo ta wurgamashi
Tace "wacece kuma haka Yace "Amaryaki mana"
Muntafi sai mundawo ja hannu fannah yayi suka fita
Sun sha yawo sannan suka dawo Har gidan inna sukaje sannan Gidan momy.


Jidda tana falo dagudu baby fannah tace ",momy kinga ice cream Dina  zaki sha"
Jidda tace A'a sha kayanki"

Hameed yashigo yazauna kusada Jidda
",my Jidda tace tana gaidaki"

Jidda tace "wa"
Yace "Amaryaki"
Dasauri tabar falon
Tashiga ciki
Hameed binta yayi Akabar  fanah tana shan ice cream tana kallon tom And Jerry


Kwance ya isketa zama yayi kusada ita tare da rungumota

"Haba my Jidda meyafaru"

Cikim kukan shagwna tace
"Bakaine kake cewa zakaya yoman Amarya ba"
Kara rungume yayi tare da dariya yace "wasa nake
Miki my Jidda
Ke kadai kin isheni
Har mutuwa
Jidda Inasonki
MUNA TARE Abadan Da'iman
Ruwa ko iska bazasu rabamuba"

Jidda tace "nima inasonka mijina uban yayana mijina Aduniya mijina Aljanna
MUNA TARE  har Abada habibibina
Nan sukafara sakarma junansu Sumba cikeda da so da kauna.

ALHMADULLAH


Nan nakawo karshen muna tare dafatan ya fadakar kuma nishardar daku

Godiya gareku masoyana
Nagode da kaunar Ku babu Abinda zance sai dai Allah yabarmu tare MUNA TARE  har Abada luv you All❤❤


Jinjina gareku
PERFECT WRITES FORUM
Kungiya mai Albarka mai
Hadin Kai inasonku sosai yadda Baku zato
Allah yakara hada kanmu


Hmm
Babu Abinda zanfada
Bakina bazai furta komai
Kinuna kauna gareni
Kinjawo ni jikinki
Big sister Mrs Lameedo
My Aunty
Rokona A kodayaushe Allah hada fuskokinmu
Nagode nagode na kaunar ki
Mrs Lameedo
Luv so much




Luv masoyana sai kunjini
Cikin wani sabon novel
❤❤❤❤❤❤❤
adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *