Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, June 17, 2019

Zahra yar'amana complete hausa novels wattpad

adsense here

Zahra yar'amana  complete hausa novels wattpad


Zahra yar'amana.
1-95
Written by
F.A.Ya'u


I am forever grateful to Allah(S.W.A)

 In Dedication to my Parents.

My appreciation goes to
Salma Ali Wada
Zakiyya Aminu Ibrahim
Hawwa Usman Ya'u
Rasheeda Isah (Mrs Idris)
For their helpful support.

One love to Readers no word to express by thanks.





Banhakuri
 Ina mai kara bawa makaranta hakuri kan sauyin suna na wannan littafi daga yar'amana xuwa Zahra yar'amana hakan yasanya nayi kokarin hade muku shi a page daya nagode.




     Bismillahirrahmanirrahim


Kuka kawai take kai kace an aiko mata da sakom mutuwa wai badake nakeba wallahi kika sake na dauko hijabina baki shigoba saina kure miki gudu na kamaki nakuma dakekin mara mutunci kawai ahankula take bin bangon kai kace wata wahainiya ce saida taxo daf da ita ta xuro hannu xata cafketa tai wani tsalle ta koma baya lallai ma yarinyar nan nikikai ma haka ko jibi yadda kika sanya na kurje hannu na tai ciki a fusace.

   

Dasauri ta bi bayanta tana kuka dan Allah umma kiyi hakuri baxan kuma ba xan wanke karma ki wanke sai afkin ki cuci mutum kixo kina bashi hakuri shegiyar yarinya mara tarbiya tako hauta da duka kai kace tasamu jaka saida tai mata lilis sannan ta saketa dauran inkin gama kukan ki fice inkin dawo na dada miki munafika ta shige daki.

   

    Au baxaki tashi kimin abunda nasakiba ko dukanne be ishekiba yar marasa mutunci to inma malan kike jira ya dawo ki hadani dashi ba yanxu xai dawoba sauran ya dawo naji lbr gobe kici na jaki .
  Zara yau bazaki makarantar bane xani yaya so nake na gama wannan wanke wanken to kiyi sauri karki makara dakinshirya ai damun tafi tare lah yaya kai tafiyarka karka rasa exam din to sai kin tawo to yaya Allah ya bada sa'a amin ya leka daki umma na tafi to dan albarka sai ka dawo yana fita umma ta leko ke wai yaushe xance miki kidaina kula yaronnan umma dan Allah kiyi hakuri wallahi baxan kuma ba ta dungure mata kai kima kuma.

   Umma na tafi ke zonan ina xaki umma makaranta mn eyye wato makaranta mn ko kin gama aikin dana sanyaki eh umma to sai kindawo tamurmusa gami dayin zauro ke sunan datake kiranta kenan zonan tazo ta durkusa ba wata nakaranta da zaki kinma daina zuwa tasa kuka umma dan Allah kiyi hakuri nace kinmun lefine .

  Kuka kawai take tana rokon umma kan tabarta ta tafi makaranta itako tai mata banxa tuwonta ma take ci tana sautaron waka ta cillo mata kwanon data gama ci maxa jeki ki wanken daga nan ki wuce dakinki in inada bukatarki xan nemeki sun sun ta mike tai gun wanke wanken bayan takai kwanon madafa tai xaure dan nanne dakinta yake indai malan benan ko yai tafiya ke ta juyo kikace kin gama komai eh umma kya iya tafiya anman inna fito naga wani aikin wallahi kika dawo saina dakeki jitai kamar ta daka tsalle dan murna saidai ba dama aduniya tatsani abinda xaisa yau ace baxata makaranta ba dan bata da inda take jin sukuni kamar nan din duda goma saura haka ta daure tai makarantar dan ta fiye mata gidannasu sau dubin bubata.

   Tai sa'a ba'akoma break ba dan haka ta saje da sauran yara daketa wasa kamar ba'a lokacin taxo ba.
    
      *******************

Zarah!!! Na'am yaya ganinan ta fito rike da hijabinta kinshirya ne a'a yaya wai mai tasa kwanakinnan bakyasan mutafi tarene ko kekenne bakyasan hawa tai dariya lah wallahi yaya ba haka bane ban karya bane katafi karka makara to aishikenan kiyifa sauri karki makara kinji ko to yaya se kadawo.

 Muhammad kenan dan kimanin shekara goma sha shida xuwa sha bakwai sanye yake da uniform dinsa na Rumfa college inda yake ss3 yayin da zara ke primary 4 anan Kwalli special primary sch.

    Furai yarinyar nan kuwa ta dawo eh tana daki kasanta bata san zaman waje kodai kika hanataba kajika kaima dai malan inna hanata maye ribata kinga ba musu nace muyi ba maza kiramin ita mezata maka yau naji ikon Allah shikenan mutun da diyarsa baxai kirataba sai ace danmai yi hakuri mai ya maxa ni kiramin ita tamike tai ribabben dakin da shine na xaran tun rasuwar ummanta.

  Ke kixo inji ubanki kuma sauran inya tambayeki kinci abinci kice a'a saina karya miki kafa inya fita gobe ta juyo dan komawa inda malan din yake asanyaye ta mike sabida wata irin yunwa takeji ga wani irin ciwo da kanta yake har wani jiri ke dibarta rabonta da abinci tin jiya tunjiya da safe shima dan da sch ne tasamu kawarta taxo da abinci suka ci yau ba mkranta gashi yini tai tanai ma umma aiki ko kanxo ta hanata yaya muhd mai sai mata kosai shima tunjiya baya gida.

   A hankula ta xauna baba sannu da xuwa yawwa zara kinko ci abinci tai saurin kallon umman dake gefenta tako gallo mata harara eh baba naci anya kuwa kin koshi eh nakoshi anya kuwa ni banga alamar koshi atattare dakeba ya miko mata na gabansa da umma ta ijiye ungo ci wannan umma tai saurin mikewa wa wallahi baza ta ciba aiba ubanta ya sayoba ke Fure mene haka bansan wulakanci aikaji mainace wallahi baxata ciba tabari in ubanta ya sayo sai taci aike naki uban ya sayo ko kai malan karka xageni kan shegiyar yarnan taka yanzu diyar tawa ce shegiya to karya nai wallahi ki kiyayeni nine ubanta karki kara sheganta min diya hhhhh lallai eh kaine ubanta seka fadan sanda ka auri uwarta abincine dai ko ki cinye abinci yai tsaki yai waje.

    To mayya aisaiki koma dakinki ko kin wani xuban ido kamar xaki cinyeni ta mike tai dakinta ke xonan dan wallahi ban yarda dakeba sai kin fadan inda kike cin abinci sai kin fadan dan iskan dake baki abinci tsananin ciwon da kanta keyi da yadda cikinta ke murdawa yasanya maganar umman ma taji kamar tana kwara mt ruwan xabi aka kawai saita juya danyin dakinta aiko umma ta kufa ta fincikota lallai yarinyar nan wato ga yar iska na mgn shine xaki wuce dakinki ko tako jawota kofar sakin muhd ta ciro wayar cajar fitilarta ta hau duka ko ihu bata iyawa se hawaye kawai dake bin kunxinta kan umma ta ankara sai ganin yarinya tai asandare na shiga uku karfa yarinyar nan ta mutu ga dan rigimar nan na gari wato malan aiko sallamarsa dataji ta kara daga mata hankali.

     Salati ya saki furai karfa kiyi kisan kai kasantuwarta jaruma mai taurin rai in nakasheta ma ai na rage mata takaici ta murguda baki gami da yin dakinta ganin da ranta ya debo ruwa ya shafa mata a fuska sa'annan ta farfado shayin da yasayo mata ya bata kasantuwar cikinta ya nade tana gama sha tayo amansa subhanallahi ya fada gami da daukanta yasanyata bayan mashin dinsa sai asibinta Wata tazo dake nan bayansu saida suka saka mata ruwa koda ya kare suka rubuta mata dan mgni sai isha'i suka baro asibitin.

Wai yau malan baxaka fita ba dake kike sawa na fita a'a gani nai shuru har tara baka fita ba shine nace bari na leko ko lpy to banga dama ba ko xaki fito dani ne tai tsaki dan Allah ka shekara adakin ta kade labile gami dayin dakinta.

    Shima tsaki yai gami da mikewa yai madafa kofi ya dauko yai waje koko mai xafi ya sayona xara ya amso kosan da tun daxu yabada kudin saida ya biya kanti ya sayo madara yar ashirin da biyar ya dawo gida.

   Tana kwance adaki ya shiga dakin yai kaca kaca duk tarkacen umma ne yace zara ya jikin ina kwana baba lpy kalau yar albarka taso ki karya saida ya tabbatar ta koshi sa'annan ya bata magani ta sha yadan gyara mata dakin kafin ya fito.

      Saida yai wanka ya shirya tsaf da niyar fita sannan ya leka dakin Furai Furai ni xan fita sauran indawo intarar kin bugarmin diya ko kin hanata abinci kibari randa kika fara ciyar damu saiki fara hanata tai dariya to inna hanata mai xaka mun sakinki xanyi wallahi akan yata tas xamu rabu ta rike hanci tana buda sai mai to akaina aka fara rabuwar aure balle irin auranka auran kaddara auran jidali eh duk naji anman wallahi kitsaya kiji rufe ido xanyi na manta da yayan dake tsakaninmu in hadaki da police kinsan inada shaidu duk unguwar nan duk wanda na kira sheda ne abinka da mutumin kauye da tsoron yan sanda banda abinka malan mai kuma yakawo maganar wadannan masu bakar xuciyar nidai na fada miki wallahi ko yau na dawo na taras kin mata abinda bai gamshenma kisan makomarki.
        *****************

Tun daga wannan lokacin xara ta samu saukin duka da horon yunwa saidai faduk wani aikin wahala ya koma kanta bata da takaimai mai lokacin kanta kafin ta tafi sch aikine inta dawo ma aikine ta rage hanata abinci duda bawani isarta yake ba yafidai babu.

   Yar albarka kina inane ta fito da sauri gani baba kinje makarantar kuwa eh naje daxunma na dawo to yayi kyai xoki gwada kayannan muga koxasu miki ta karba tana dariya jeki ki gwado muga kai anman sun miki kyau kamar mai saidawar yasanki saida nace baxasu mikiba yacw mai xai hana tai dariya nagode baba Allah yasa da alkairi amin zara'una.

   Nifa malan ban gane mai kake nufiba dan maine xaka dinga sayawa wannan yarinyar kaya alhalin ni ba isata yai ba to banda abinki har yaushe na siyo miki ina dawo wata wancan watan kena siyowa to naji anman ai wannan nuna banbanci ne in gaskiyane ai muhd ma na bugata eh nayi rashin adalcin komai xaki ce sai dai kice ba xan siya masa ba to karka siya dadinta bani Allah xai kona ba sau ki godema Allah tunda ba kabarinmu daya ba yai tsaki gami da shigewa dakinsa.

Kasan tuwar bata san take makara a makaranta yasanya duda karancin shekarunta ta sabarma kanta tashi tun asuva ta kammala komai yau ma haka ta kasance kiran sallar fari ta farka kafin biyar ta gama komai tai sallah ta dauko kayanta xuwa dakinta dan kar baba ta ganta a dakin zaure dan haryau baisan tana kwana adakin xaureba sai ya duba yaganta adakin ummanta sannan ya kwanta ko tai bacci sai umman muhd taxo ta maidata dakin xaire bakwai dai dai ta gama shiryawa umma na tafi ina makaranta ubanki ne xaimin wanke wanke wanken umma ai nayi eyye kin isa wato ina mgn kina mgn ko watakan ga sa'arki yi hakuri umma anman nayi wanke wanke tau ta bata mari nafiskanci yarinyar dan na dena dukanki kin rainani to banyi sanyi ba maxa ni jeki kimin abinda nasaki ga mamakinta kwanikan data wanke an kada kuka da manja an sheka musu haka ta gama umma ta kara debo mata tabarmi wai ta wanke ta shiga daki dan cire uniform koma maxa dasu nake san wanke.

  Sai tara ta gama a haka ta tafi ajike zara yarinya ce nai kwaxo duda kasantuwar bata xuwa kullun kusan kullun a makare take anman hakan baisa take iya daukan ta biyar ta shidaba bata taba wuce ta gomaba a makaranta sun dena sukanta dan muhd da kansa yaje ya musu bayani sun kuma fuskance shi.
        

             *****************

           Yanayin garin yasanya yau malan musa tashin su zara da wuri hadarine ya hado bakikkirin ga iska dake kadawa mai karfi tunanin xara daya wanda bai wuce dakinta data ke kwanaba wato dakin xaure ga muhd benan dama yananan ne tasan iyaji ruwa xaixo ya maidata dakin ummanta to ya tafi sakkoto yin jamb ga dakin wata irin mahaukaciyar xuba yake ga kanta na wani irin ciwo sauran yan makaranta ta gani suna gudu dan xuwa gida jitai inama itace ace take murnar komawa gida.

        Ruwan da ya sauko yasanyata rugawa da gudu xuwa gida ganin yadda ruwan ke xuba yasa ta shige dakin xaure kasantuwar da wuta yasa ta ganin yadda dakin daxu ta fita tabarshi fes anman ynx yai kaca kaca duda kanta na ciwo haka ta gyarashi kukan sauro ne kawai ke tashi adakin  takardunta da bataso ta kunna hayaki ya turnuke dakin ta daga labile tana korosu waje aiko dip aka dauke wuta umma dake sallah ta hango haske itako xara koda hayaki yadan kare taje tsinmokaranta ta rufa tuni bacci ya deveta da'alama  taji dadin baccin jitai an bugeta eyye sannu yar kanta watakan banma isa kixo kicemun kin dawoba ko wallahi umma naxo naga kika sallah ta daki bakin shegiya wadda ba'a fadi saita karyarta.

   Maxa ni kixo kimin wanke wanke umma daxufa na wanke eyye wato harkinkai nasanyaki aiki kice baxakiyiba ko to wallahi invaki wankeva baxakici abinda na girkaba wato ga baiwa ingirka inbaki onmiki wanke wanke to vaxai yiwuba yi hakuri umma xan wanke karma ki wanke kibarshi banso tasan halin umma dan haka ta fito ta fara wanke wanken .

  Kwanukan data wanke daxu duk Anbarbaxasu ruwa ya musu duka aiko tana farawa wani ruwan ya tsugewa ahaka tana wanke wanken ruwan na dukanta koda ta gama umma tace saita wanke gidan atakaice ruwannan akanta ya kare kije kidauki tuwonki yana nan a kwanonki tuwan ya sandare sanyi kalau miyarma ruwa duk ya shiga haka ta dauko tai daki.

    Dakyar take iya tura tuwon danma yinwar datakeji ne daba lallai ta iya ciba yadda yasandare yadda xaxxabi ya rufeta ko sai karkarwa take umma ta shigo to muna fuka kinxo kin lanjarw anan salon malan yaxo yaganki ta mike tai dakin ummanta.

   Da'alama tanajim dadin baccin dan kayan data kima ajikinta tadanji dumi umma tasa kafa ta doketa a firgice ta farka wato kekinji dadin harda bacci maxa ki koma dakinki ta mike batai ishaba  tai alwala dakyar tai sallah .

     A bude ta taras da dakin umma ta barbaxashi hawaye suka xubo mata ta goge abinta gami da dan marmatsar dasu taja gefe ta kudunduna dan umna ta kwace kayan rufar.

  Cikin dare ruwa ya tsuge kamar da bakin kwarya ga iska mai karfi data ke bugawa sanyi  da iska gamida ruwan dake digowa sun hanata bacci.

 Iskar data tasoce ta yaye rufin dakin yai gefe kasan tuwar da wuta wta yasata saurin mikewa danyin gefe aiko wani cikin rufin yai sa'ar yankarta a cinya tako kurma ihuuu tafadi nan sauran suka rufeta karfin ruwan yasanya sumalan rashin jiyo kararta.
                                                                   
      ******************

Koda malan ya fito bai kawo komai akan yayewar rufin dakinba dan saninda yai babu komai mai anfani adakin dan haka alwalarsa kawai yai ya wuce sallar asuba koda ya dawo baibi takan dakinba ya fadama umma abinda ya faru dan yataras da har lokacin baccinta take atsorace tace nashiga uku wane daki malan dakin xaure mn ta dafe kirgi gami da waro ido ya kalle ganin yadda ta tsorata ganin asirinta xai tonu ta mike bari naje na dora dumame ta fice kai tsaye dakin umman xara ta wuce tana addu'ar Allah yasa ta dawo nan duda wani barin na ranta na fadi mt Allah yasa ma xaran ta mace kowa ya huta. Dan hk kawai ta hadama malan kari ta kai masa fatanta yaxo ya fice tunda garin xai bari inyaso inya dawo yasamu lbarin rasuwar ta ta aminta da xuciyarta.

    Ya shirya tsaf har yakai xaure da mashin dinsa ya juyo kinga bari naduba dakinnan ah ah da saurinta kaga malan kayi wankanka tsaf karka bata jikinka kabari xan gyara yai dariya banda abin furai  nida xanyi aikin gini kan in wuce bata jiki na ina saidai kar'akuma ya xira kai dakin yadan farabmatsar da kwanukan gami da daga wasu ga mamakinsa yaga jini jikin wani kwanon da sauri ya daddaga sauran da dan birbishin bululluka sai ayanxu ya tuna yau ba xara ce tai dumameba bai kuma ganta tana wanke wankeba kamar kullun tabbas kuwa xara ce ba shassha yadda yaga furai ta tsorata zaran kuwa yagani kwance cikin jini baijinma tana da rai surarta yai yai waje.
   Muktar ya hango yana goge  dan sahunsa yai wajensa da sauri shima ganinsa dauke da xaran kamar gawa yasanyashi saurin kama mishi da ita suka shigar da ita dan sahun  yatada baiko tambayi  inda suka nufaba yai bammali dasu   koda sukaje babu likita ko nurses babu sai primary health officers sukuma sukace abin yafi karfinsu dan haka yai murtala dasu nan sukace sai sunxo da police domin yanayinta yanayin wanda akai hatsari gaba daya sun dururuce sai can muktar ya tuna da abokins hanxa police ne ya kirashi awaya ya masa bayani kaga wallahi mashin dina ba mai banda kuma kudin mashin wallahi kana inane ina gwale police station to gani nan.
    Koda sukaxo da Hamza ai sai sukace musu babu gado duk yadda sukaso karvarta nurse din taki shikam malan yama gama fidda rai da yarinyar muktar ke kara bashi karfin guwa kai tsaye nasarawa ya wuce dasu koda suka isa yai emergency dasu da gudu ya dauketa sukai ciki sukai kuwa kacibus da wata doctor ta tausaya  musu duda ta tashi anman hk ta tsaya ta basu tai makon gaggawa ta baima malan takarda gashinan ana bukatar wannan da gaggawa dan sai anmata yar karamar tiyata sai mun mata dinke dinke in kakawo kabaima nurse xata baima doctor mai duty kai tsaye ya wuce gurin rubuta kudi sai dai mai kudin sunfi karfin tunaninsa baidasu bai kuma bada ajiya ba ya dawo ya xauna ya rafka tagumi.
   Komai ya tuna oho yai dakin da xaran take Allah sarki muktar har ynx vai tafi ba ya bashi takardar ya duba dan rokon likitar ta tafi muktar yace wallahi baba banda ko dari jiya nakai balance dake mashin din bane ya tsurama yarinyar ido tausayinta yakamaahi yarinyar tun xuwanta duniya take wahala har yau furai ta hanta sukuni.
   Muryar nurse yaji na cewa malan kaifa muke jira kakawo abinda doctor ta rubuta in ba haka ba kadauki yarka ka kara gaba ya kalleta dudu du batafi sa'ar kharima yarsa ba anman tarike kugu tanai masa tsawa kabi kawani tsareni da ido ko so kake inxama maganinne yi hakuri yanxu xanhe ah karma ka kawo tai tsaki tai daya gadon.
   Muktar ya dafa baba gwanda akawo kudin kar yarinyar ta galabaita wallahi muktar bandashi to baba mai xai hana kasaida mashin dinka to banda abinka ina xan samu mai siya shi ba kamar goal bane eh to hakane anman da gwaji akan dace muje nasan wani mai siya  summa manta ita daya suka bari suka tafi.
       ******************

   Nurse ce taketa bala'i haba wannan ai rashin mutunci ne mutane sukawo yarinya su gudu subarta fada take ba kakkautawa.
  
   Kai wannan nurse din ta fiye fada bari na leka naga waya tabota doctor din yai dariya indai mairo ce sai ka gaji da jinta.
   
  Matashin saurayin dabaifi shekara sha takwas ba ya fito daga office din yadda yaga yarinyar ta bashi tausayi haba nurse ku dubata mn mudubata kamar yaya baka ganin halin datake ciki ne ko so kake ni inxama mganin da xamu mata mun basu wanda suka kawo sun gudu ya fiskanci nurse din yar xafi ce don haka yai tsaki ya koma office din doctor.
  
    Pls doctor kataimaka ka ceci rai yarinyar na cikin wani hali aikaji mai tace basu kawo alluran bane ni rubuta min sai in kawo yace muje naganta bayan yadan duddubata ya ya rubuta masa mgnin shi kuma yai wajen biya.
  
   Datai makon Allah dana yaron doctor yai mata komai shi kuma yaxauna dan kula da ita.
 
  Duk inda muktar yasan xaikai malan dan sayen mashin dinsa yaje anman ba labari dan saidai sice bayan sati yaxo ya amshi kudin sai asannan ya tuna ita daya ya bari  hankalinsa ya tashi watakilma ta mutu inyaje to maixaice da ma'aikata suna tafe muktar na kwantar masa da hankali har suka isa.
  
   Inda suka barta wayam hankalin malan inyai dubu ya tashi wata nurse ya gani xata wuce ya tambayeta ta nuno masa emergency room tana ciki da sauri ya shige gadonta ne na karshe tana kwance sai wani matashin saurayi dabaifi muhammadunsa ba axaune abkujera da'alama bacci yakeji muktar yace baba bara naje gida karsuga ban musu sallama na tafi toshikenan dan albarka nagode yaron da ke xaune ya dago kai yaga yana shafa mt kai kasanta ne baba eh yaro diya tace Allah sarki ya mike daga xaman da yake ga guri xauna yi xamanka.
  
   Anman baba mai yasa ka tafi ka barta wallahi ba tafiya naiba naje nemo kudine gashi duk yadda xanyi nayi bansamuba haka ne karka damu anbiya anman dan Allah baba kadena irin haka gangancine kaxo kabarta ba kowa gwandama ka tsaya inma mutuwa tai ku koma da ita eh hakane duk na gigice ne wallahi ai dakyar muka samu nurse tabar xancen da cewa tai baxata tafi ba sai ka dawo wallahi police xata hadaka yaxaro ido towa ai ansha kanta akiyaye gaba dai insha Allah.
  
   Ya mike baba ni bara naje kar anaiman agida to yaro baka fadan nawa aka kasheba yai murmushi baba kenan karka damu ni dan Allah nai wallahi nagode yaro Allah yasaka yanata saka albarka yaron na amsawa Allah ya kara sauki amin yaro sai dai baka fadan sunanka ba yashafa kai sunana *Zaem* kijerar da ya tashi malan yabi yaxauna tunanin yanayin rayuwar xaran duk sukabi suka cika masa rai yadda aka haifeta yadda take tayuwa duk suka dawo masa baisan sa'adda hawaye suka biyo kuncinsa ba.
     **********************
     ***********

 
*wace ce Zahara*

Dina haifaffiyar garin kano ce mahaifinta hamshakin dan kasuwane sananne afadin Nigeria su shida iyayansu suka haifa biyu sun rasu tun suna yara sai yayansu mai suna zaem mai bimasa zikir sai ita Dina dan autansu salman kasantuwarta mace daya da suka mallaka yasanya duk san duniya suka dora mata.
  

   Lokacin da dina ta kammala secondary ne yasamu damar tafiya sch of hygiene inda take environmental health.
   Ranar da baxata taba mantawa da ita ba itace ranar exam dinsu ta parasitology ta xauna gefen wani saurayi shi dan EVT ne yayin da ita take yar EHT kafin akawo papers har sun saba sunata hira akan nata course din yafi dole ya girmamata shi kuma yana ta zolayarta.
  
   Tundaga sannan suka xama frnds indai ba lecture ce dasuba xaka samu islam cikin mata duk inda kaga dina kaganshi kai ko agidansu dina ansan da xaman abokinta islam.
   
   Ada dina batasan hygiene anman yanxu koda dad yai mata batun yin jamb ai sai cewa tai tafisan kawai tai diploma a health inyaso daga baya tayi degree din aiko ya kyaleta.
   Dina batasan tasaba kuma tanasan islam ba sai da sukai hutun semester ending dake shi ba dan kano bane ya hostel ne .
  
   Dina na NDll dad yace aure xai mata da dan abokinsa aiko tahau ta dire ita basansa tana da wanda takeso yace waye ta fadi mai yace shikenan ya aminta anman xai bincike.
  
  Sati biyu da batun yakira kan yanasan ta rabu da yaronnan baida asali tace ina ita haka takesan abunta duk yadda yaso ta rabu dashi taki .
 
  So yagama rufe mt ido dad yace shikenan tayaji xai auranta dashi anman tasani bashi ba ita yayunta sukai sukai taki ita ta yadda haka aka daura auran.


Murna gurin sabbin ma'auratan ai ba mgn idanunsu ya rufe basa tunanin komai haka islam ya dauki matarsa sai bauci gaba daya suka watsar da karatun.

  Zuwansu bauci komai dai dai yake tafiya kafin rayuwa tai wuya su kwaso su dawo kaduna anan dimma ba dadi tsi tsi suke in anci na rana ba lallai asamu na dareba haka dai sike hakuri ana haka Dina ta samu ciki gata da dan banxan laulayi duk tabi ta rame komai yai musu xafi.
       ****************
  Cikin ta nada wata bakwai tace xata kano ganin gida yace ina ba inda xata bacin basanta sukeba tace itadai haka xata tafi.

  Agajiye ta sauka ga yunwa da takeji yadda mamanta ta ganta yasa dasauri da abinci ta fara taryarta aiko sai loma kamar ba dina mai kincin abincin data sani bace aiko sai hawaye dad yana dawowa yace vaisan xance ba taxo tabar masa gida tana kuka mama nayi yan uwanta na bashi hakuri yai kemai mai haka bata kwanaba ko abincin bata gama ciba ya korata.
  
   Haka ta dawo gida tana kuka  maiyasa dad baxai mata uxiriba ta gane kuranta .

   Duk yadda dina xatai islam yakaita danginsa yaki yanxima yashiryane dan xuwa xaitawo da kakarsa tai tai xata bishi yace tayi hakuri inta haihu inxasu maida kaka sai su tafi tare ahaka sukai sallama ya tafi.

Kwanansa hudu da tafiya ta haifi diyarta mace dayake yabar komai ranar suna aka yanka rago taci sunanta *zahara*.

  Tun abin bai damun dina har tafara damuwa dan yau watan islam uku bako labari bashi ba kakartasa har bauci taje sukace baixoba daman ai daga Niger yaxo canma vasu da tabbacin inda yake koma dan canne aiko tai kuka mai isarta ita bama kanta takemaba sai yarta itace abin tausayi.

  Watanta tara da haihuwa ta kuma gwada xuwa gida aka kuma kwatawa bama su tsaya suji bayanintaba ko ganin abinda ta haifa suka korota ta dawo kaduna.


Tun dawowarta daga kano jiki yaki dadi ciwuka kala kala ga ba dangi kusa sai wata makociya dake kula da ita.
Shekaran zara biyu tana gudunta ko ina harda dan gwarancinta yarinyace mai shiga rai tashaku da makociyarsu ita take mt komai wani sa'inma agunta take kwana itama ta yayeta.
       *****************
  
  Yaukam jikin dina yaki dadi hajiya barira keta bata baki kan ta rage damuwa sai tai murmushi umma kenan nidai ko bayan raina kitaimakeni ki riken xara koda babanta xai dawo kibashi diyarsa haba kekuwa cuta ba mutuwa bace sai kikaga kinga girmanta ni ban ganiba.

Zara xaune keta faman bugun uwar da gwarancinta ki tashi ta mike ta dauko takalmi yadda taga tanayi kamar xata daketa ganin bata kulata ba sai kuka umma barira ta shigo haba dina yaxaki bar yarinya na kuka aiko yadda ta ganta ya kidima ta subhanallahi ta dauki xara aiko babu uwar ta mace.

   Tun rasuwar xarah babu wanda yaxo gurinta dan naiman xara haka take ta kula da ita itama fa sai kansar mama dan haka kaninta sunaiman dake kano yaxo ya tafi da ita da yar amarta.
 

  Tun zuwansu gidan matar malan furai tabi ta tsani yarinyar dan kawayenta sunce watakil yar malan dince yayarsa ta rufa masa asiri ta rike yarinyar ko lekowa batai dan in ba haka ba kuwa taci na jaki.

       ********************

Yayan malan biyar hudu mata daya namiji duk sunyi aure muhd ne kawai agida Allah ya hada jininsa da xara duk yadda umma taso rabasu ta kasa hakan yasa take cewa xaran mayya ce.
  Muktasira itace babba zulfa mai bi mata sai bilkisu mansura itace karama

Muktasira da bilkisu kamar uwarsu sike sun tsani xara vabu irin hantarar da basa mata indai sunxo gidan.
  Mansurace dai ba sawa ba fitarwa bata shiga sabgarta yayinda zulfa ke tausayin yarinyar ko kwancen kayan yayanta ita take kawowa har saboma tana kawo mata halin malan gaba daya ta deve su.
  
   Ko bayan rasuwar umman xaran zulfa tace xata dauki xaran umma tace indai ta dauka sai ta tsine mata lokacin xara na primary 3 aiko axaba kala kala dan daman idan umma nasa wa arage mata.

  Makarantarma sai ta gadama take barinta duka ba kama hannun yaro abinci ba koyausheba duk wai tanasan ta mutu.

  Maganar xara da yaji ya katse ms tunanin da yake tace baba kuka kake yace a'a gumi ne ta yun kura xata mike bari naima fifita sai ta kasa wash kafata sannu xara kiyi hakuri asannu xaki warke to baba.
  
   Wajan hudu zaem da kakarsa suka xo dan tun da yakoma yabata lbri tace xata xo koda malan yagansu yaji dadi duda bai sansuba sai yaji ya yarda dasu ya barmusu xara yace xaije gida ya dawo .
 

Koda malan ya koma gida baibi takan furairaba wanka yashiga sannan yaxo dan yin sallah itako koda taga yadawo shidaya batare da gawa ba sai takaici duk ya rufeta dan taso ace ta mutu duda tana tsoron kar axargeta.
 Sai bayan yama idar da sallane ya tuna baiko ci abinci ba tun karin safe tana kallonsa ya gama komai xai fice bata tambaye shi mai jiki ba malan baxaka ci abin ci bane yako watsa mt wani kallo gami da tsaki ya fice.

   Saida ya tsaya ya sayi biredi duda bashi ya dauka sannan ya wuce asibiti sunanai sai dai xaran na bacci zaem ya fice inna nabgefe a xaune suka kara gaisawa da da malan sannan take kara tambayarsa mai yasamu xahran yake fadi mt ai gini ne ya fado mata ta nuna tausaya warta sosai kafin su tafi harda ajiye masa kudi gashi koxa'a naima yaiko ta godiya.
        *******************
   Satinsu biyu a asibiti aka sallamosu ta warke sosai saidai karayar dataine sai ahankali.
Duk xaman dasukai a asibiti umma furai bata taba koda dawasa tace ma malan yamai jiki ba balle tai gigin cewa xataxo dubata a asibiti balle kuma sauran yayanta inka dauke mansura da taxo sau daya sai xulfa da kullum sai taxo muhd kuwa shi yaxama mai jinya harsun saba da xaem kai kace sun shekara danshima kullum yana tafe shida kakarsa.
  Makotansu xaran kuwa kullun sai an samu mai xuwa.
 
  Koda suka koma gida ma kullun gidan akwai masu xuwa kaxalika da abinda xasu kawowa xaran ko an baima umma cewa take bataso duda kuwa ranta naso.

  Ko agidanma umma bata kalletaba balle tamata sannu kallon kirki bata isheta ba dan tafuskanci malan babu abinda xaiyi sai muxurai duda kuwa randa xasu dawo yaja mata kunne kan xaran takuwa ji dan saidai hararar ba damar duka.

  Yadda xulfa'u ke wani kula da xaran ke mata girki yasa take masifar jin haushinta harma fiye da muhd danshi tace xahra ta lashe ms kurwa kumadai tafi sansa dan tace da namiji jari.
Ba'abinda ke kaita dakin xahra sai abinci shim daga bakin kofa take tura mata tai gaba.
       ********************
Zahra ta warke sosai dan harta koma makaranta ayanxu komai yai mt sauki tun wani duka data mata malan bayanan makota suka kira mt hijba shikenan ta dena dukanta saidai uban aiki dan ita in akwai abinda ta tsana jami'ai masu saka uniform dan haka saidai xagin da masifa agidan in malan bainai xara da ita damai xaman kanta daya ne babu kwaba ina xaki ko ina kikaje babu ruwan umma dik dadewar daxarai aguri ita burin umman yau yarinyar ta lalace tunda dai taki mutukedai.

Tun kwanciyar xahra a asibiti xumunci ya kullu tsakanin gidansu xahra da gidansu xaem dan har hutu take xuwa yi musu sunyi harsun gaji kan malan din yabasu xahran yace ina shi xai rike diyarsa.

Awoyi na shudewa kwanaki na tafiya kaxalika shekaru yau take ranar farin ciki gurin xahra dan yauce final pape dinsu a waec wadda daga ita sunyi bai bai da secondry murna gurinta ba'a mgn tun jiya da dare in tafarka saitaga still dare ne gani take goben taki xuwa gashi kuwa taxo burinta ya kusa cika xata kammala makaranta ta auri isma'il dinta abinsanta  wanda tun tana karama batasan kantaba yake kula da ita ko lokacin daxata tafi garko malan baisan boarding shi ya sama mata day science lokacin yana teaching a science and technical lokacin da ya kammala masters dinsa yasamu lecturing a northwest university dan ashekarar aka bude ta duda kuwa da karancin shekarunsa.

Umma furaira bata taba daukan batun ismail da gaskeba sai da taga ankawo kudin aure har dubu hamsin kai hargidan daya gina saida munafukai suka kaita aiko hankalinta ya tashi dan ko rabin kudin auren ba'akawo ma yayanta ba acewarta babu ta yadda bare mara asali xatafi yangida kuma ba yanxu ta shiryama auran xarah koma xatai aure tai alkawarin ba inda xata hutaba.

  Aikuwa takanas ta aika muhd ya kira mt atine dillaliya ta saida mata kayanta kawarta xata rakata gurin malamanta tace indai tana raye saita hana aurannan ko xata tafi tsirara.

  Yayin da adaya hannun dangin zaem sunma malan kara dan kayan daki kam sun kammala mata malan sai xumudi yake burinsa sai cika xai aurar da xarah duk yayansa inkadauke xilfa da muhd shima da yake yana xariya babu mai farin ciki duda kuwa umma tacema xulfa inbata cite hannunta kan mgnar auranba sai ta tsinemata hakan yasa ta dena zuwa ta koma haduwa da xaran gidansu xakiyya xaton umma ta ji batunta.

Iya kololuwa hankalin umma yakai ga tashi ganin kullum batun auren kara karfi take kudinta nata tafiya abanxa dan xara duda ta taso cikin halin rashin kwaba mutunce mai ruko da addini bata sakaci da addu'a kaxalika shima angon.

Kinsan mai sai kin fada na gano mana mafita kinga inbatun yandanfarar malaman nanne kibarni dan Allah ke matsalata dake kin cika garaje tunda munbi tacan va'adace ba inkina dabkudi kawai gobe kishirya sai kura me kuma xamuyi acan acandinne uwar ismail ke aure muje mukitsa mata xata iya hana auran kema daba dankiba kike gyashin ya aureta inaga uwassa kinkawo shawara Allah yakaimu goben kedai.

        ******************
Da duku duku haka suka tafi kasan tuwar malan baya gari ai kuwa tara ma acan ta musu saka makon binta tasan gidan sun kuma saba da mahaifiyar ismail din lokacin tana aure anan unguwar gini sunko samu karbuwa  ai kuwa suka xugeta tas karya da gaskiya haka suka fada mata zaran mabai *shegiya ce* ai kuwa ta hau taxauna nasani dan bananan ne akeso a cuceni a batan xuria to wallahi baxai yiwuba bunkuma xanyi aurannan sai dai in bani na haifi ismail ba anman wallahi baxa'a yishiba binto ta xaro ido kibi suwa ai sai dai ki bari in mun koma kyaxo salon kijamana salalan tsiya sai yanma suka baro kurar umman ismail nata xuba musu godiya banda kayan kauye data jibgo musu suka tawo rai fes burinsu xai cika.

Aikuwa washe gari sai gata taxo tanata kumfar baki ba irin fada da rashin mutun cin dabatai ba wai tasan makircin marikiyar ismail dinne dan mai baxata yadda nata dan ya auri xaran ba ke banda abunki da nawane yace yanaso wlh ba abinda xance to muna fika wallahi bada dana ba baban ismail ya hau ya dire sai anyi.
   Takanas taje gidansu xaran ta wanketa tas umma na xugata itadai xara bata da ta cewa sai kuka
Ganin da gaske baban ismail yake baxai fasa auren ba yasa ta kira ismail kasani wallahi ko bayan taina inka auri yarinyar nan wallahi ban yafe maka ba yanxu kuma in ka aureta wallahi saina tsine maka wlh kagi na rantse yana kuka yana bata hakuri ina bama ta kwana a unguwar ba .
Ala dole ismail yasamu mahaifinsa kan ya fasa ya hakura juyin duniya ya fadi dalili yaki to wallahi baxaka maidani karamin mutun ba inba dalili wallahi sai anyi nan ya fada masa komai yanxu ita kubra abinda ta daukanma kanta kenan ai bakomai xan samu mahaifin yarinyar to baba na gode kayanma abar mata basai ankarbo ba to shikenan Allah yamaka albarka.
Koda ya samu malan ya fiskance shi karkaji komai ba abinda xai samu alakarmu kasan mata sai hakuri kaya kuma kuxo kukarba bakomai wlh ai yariga ya barmata to shikenan Allah yasaka da alkairi.
Nasiha sosai malan yama xahra kafin ya fadi mata abin da yafaru aikuwa bata gama sauraron abinda ya ke fadeba taji komai ya dauke mata sai ganinta yai ruf ta fadi subhanallahi yai kanta xara'u xara'u....

Dasauri ya debo ruwa ya shafa mata a fuska kamar sau uku sannan ta saki ajiyar xuciya idonta ta dora akan baban nata ta fada jikinsa tana kuka dan Allah baba karka fadan ba mafarki nake ba ya dagota haba xara'una karki bani kunya mana kefa mutunce da nasanki mai tawassali kiyi hakuri daman Allah yayi ismail ba mijin ki bane ki cireshi aranki Allah xai kawo miki wani wanda ya fishi ta share hawaye anya kuwa akwai wanda yafi ismail kul ki daina fadin haka kinji ko in akace Allah ba'a kawo komai kinji ko to baba yawwa xahran babanta.
Koda ismail yaxo gidansu xahra kin fitowa tai dakyar malan yasa ta fito yadda ismail yaganta ta kara bashi tausayi saiyaji kamar ya bijirema ummansa basuyi wata hira ba sai baki da hakuri dayai ta bata tana kuka yanayi duk dauriyarsa haka suka rabu tana ganinsa har yabar lokon nasu dan akafa yaxo yana barin lokon wani sabon kukan ya kwace mt da gudu ta shige gida.
Abinda ya faru yasanya xaran cire batun makaranta aranta dan tasan daman shine xai samo mata makaranta duk tabi ta rame ta kara baki takasa cire ismail aranta.
       ****************
   Wata uku da yin haka zaem yaxo hutu dan yn abuja can gidansu da yake acan yake karatu ya tausaya ma xaran nan yake tambayarta makaranta tace ai ta hakura da karatun haka yai tamata nasiha ya karbi takar dunta kan kace mai ne yasamo mata health technology.
   Fara xuwanta makaranta da yadda suke cudanya da jama'a yasa ta fara cire komai aranta dan daman harda kadai ci duda karatune bana wasaba anman xara tafi da kyan fani tayi kiba fiye da kwanaki sunyi nisa da yake ijmb take ana fara saida form din jamb muhd ya sai mata lokacin yi nayi ta je ta xana tai sa'a kuwa ta samu sosai tai murna sosai.
Kasan tuwar har yanxu muhd baya aiki yasa umma bata taba tunanin karatu wata hanyace ta cigaban mace ba dan danginsu duk suna kauye ita gurinta cigaban mace ta auri miji mai kudi hakan yasa bata taba yunkurin hana muhd yima xara hidimar karatu ba .
  Xahra tanasan makaranta burinta akullum ace taci exam dinsu dan taje ita bata burin xuwa university.
  Koda aka kafe exam din babu sunan xahra wato bata ciba aikuwa tai kuka kamar mai muhd yai tamata nasiha harta hakura.
Koda aka fara bada admission a buk tai sa'a sun bata abinda ta naima wato MBBS .
Karatu ya kankama tayi alkawarin baxata kuma barin damuwa tasanyata ta fadi a karatunta ba komai tare suke da xakiyya wadda take biochemistry tare sukai primary anan unguwarsu daya sai xafira wadda take lab science ko fa duk rintsi tare suke xuwa tare suke koma .
   Yau zafira bataxo dan daman ita take kawosu xakiyya ta tafi capteria dan cin abinci ita kuma axumi take tace baxata iya rakata ba zaune take tana bin daliban da ke shawagi da kallo iska mai dadi na kadata har bata sanin sa'ad datake sakin murmushi wanda ke kara ma fuskarta kyau.
Kamar ance daga idanki wani matashin saurayi ta hango ya nufo inda take tai kamar bata ganshi ba ta ci gana da kallon jama'a dan xatanta banan yayo ba kamshin turarensa mai ratsa xuciya ya daki hancinta tai saurin dago kai yaiko sa'a suka hada ido yako sakar mata murmushi tai saurin daike idanta sannu ko yace da ita ko xan iya xama mai xai hana mai xai hana da'alama kanwar tawa bata da rowa ta murmusa gefen kumatunta ya kara lutsawa ahankula ya fadi subhanallah shi bai taba ganin black beuty ba sai yau ita din xara ce cikin mt.
   Zahra ba fara bace xamu iya cewa ma baka ce mai matsakaicin tsayi dan baza'a kirata doguwaba ta kuma fi karfin a kirata gajeria mai yawataccen gashin kai dana ido gashin girar ta akwance kamar an xana mt idanunta dai dai wanda suk dace da fuskarta bata cika hanci ba saidai ya dace da siririyar fuskarta bakinta dan karami wanda bai cika san mgn ba gashinta baki ne sidik wanda yake har goshi in har bata dauro dan kwali har gaban gishinba sai ka ganshi .
  Shirun dasu danyi ne yace baki fadan sunanki ba tai dariya baka tambaya ba to ynx na tambayeki sunana zahra'u sulaiman jafar what ya fada tai saurin kallonsa ya daga mata gira ni sunana jafar sulaiman muhd tai dariya haba koda naji ashe kakale ne shiyasa ka isheni da mgn au isarki ma nai eh mn tun da kaxo nan kke xuba kamar radio kin mant tibi ne tai dariya naga alama anman dai ke sabuwar daliba ce eh wane faculty medcine wane course medcine and surgery masha Allah abinda kullum nake san naga mata na karanta tai dariya kai wane course ne biochemistry nai degree a unimed ynx ina masters dina anan kafin tai mgn xakiyya da ta karaso gurin tai mgn shine kina kallo xamu shiga lecture ko ki kirani ko dan wulakanci yi hakuri ban kulaba eh ai bakya kula ba tunda kinata soyewa kefa bakida m fa tai dariya har z ma banida ta juya ga jafar yi hakuri inata xuba bamu gaisa ba ai bakomai na xatama baki ganni ba tunda na tawo kai na hango dan badan kai ba nasan ba lallai in ganta ba ka haskata yai dariya kodai ta haskani ba sukai dariya baki daya kinga ni na wuce ya juya ga xarha kai wannan frnd din taki yar cafta ce ya sunanta zakiyya anman ba course dinku daya ba ko mai yas ka tambaya naga tace ta tafi lecture ke kina xaune tai dariya eh ita tana biokmiss3 ya kada kai bari na wuce to sai anjima.
  Zahra yar'amana

     50-100
   
   Na F.A.Ya'u

 Inda sabo ta saba in basu da lecture ko suna jiran daya anan suke xama tun insun xauna basa shiga sabgar kowa har yakai suna hira da duk wanda ya xo.
   Yanayin yadda jafar yake nuna kulawarsa akansu dik abinda ya shige musu duhu yana kokarin fitarsu haske yasa suke kiransa yaya baya nuna banbanci yadda yake wasa da dariya da zahra haka yake da zakiyya da zafira baxaka taba cewa ga wadda yake so cikin su zakiyya yake koyama karatu takai ta kawo invasu da lecture xama suke suji karatun da yake mt dan ba karya ya iya koyarwa.
   Duk irin gorin shegiya da umma ke mt bata taba yadda ita din shegiyar bace dan kullum baba cikin kareta yake shine babanta bata taba yadda ita din ba diyarsa bace ko fasa auranta da ismail ce mt yai mahaifiyarsa ce bataso dan taima danta mata abu daya tasani tai makanta alkawarin cire duk wani namiji aranta da rayuwarta ko waye kai dik yadda kuke kana kawo mta batun soyayya kun bata.
   Juyi kawai yake yakasa bacci in ya rufe idansama zahra yake gani tana sakar masa tassausan murmushinta akullun ya tunkareta da batun da ke ransa sai yaga tana ms wani kwarjini kullun ji yake santa na karuwa cikin ransa xumbur ya mike daga kwanciyar da yai dan tunawa da yai da hirarsu da mubarak watakilma kana nan kana haukanka ita tanacan tana da wanda takeso kananan tana faman kiranka yaya waikai awayo xakai winning din love dinta sai dai ka ganta da ibin aurenta ina baxai yuwuba ya dauko wayarsa cike da kwarin gwiwa yau xai fada mt ya wuta ma ransa sunanta ya danna kira yanaji ya fara shiga ya gyara xama gami da kara kankame wayarba kunnensa kai kace in bai haka ba baxai jiyo mai take cewa ba.
       ***************
Har kiran ya katse bata daga ba akaro na biyu ya kara gwadawa sai yaji akace tsaki yaga gami da fadawa gado ya shiga tunani karar wayarsa yaji kwanciyar da yai yaji dadinta dan hk baijin xai wani tashi dauka.
   Yah jafar jiya ka kirani bana kusa naxo da gudu daukan wayar dai ta fadi nakuma biyo kiran kaki dauka ayimun afuwa yai dariya daman ba'a rikeki ba suka sawo wata firar.
   Mutuncin su xara da jafar mutunci ne mai karfi wanda duk mai hira dasu yasan da wannan mutunci tuni mutuncin nasu ya shafi muhd da zaem dan sun xama abokai duda jafar da zaem basu taba ganin juna ba hakan bai sa sun kasa gaisawa a waya ba. Balle kuma shi mai uban gayyar babu wanda bai san da xaman yan matanba a gidansu musanman xaran.
     Yau basu da lecture dan haka ta roki malan tanasan xuwa gidansu xaem dan yi week end malan bai hn taba dan inda sabo tun tn karama take xuwa.
  Akofar gidan dan sahu ya sauketa malan wato kakan xaem yana kofar gidan kamar koyaushe indai yamma tayi anan xaka ganshi yn jan carbi ya ganinta ya washe baki ita m ta saki fuska ta durkusa ta gaidashi kafin tace dan tsoho ana nan ana kwashe ladan to ya ranki so kike in mace ko dan karki auri tsoho ai kai mutuwa ba ynx ba sai mun mace mun barka gadin duniya yai dariya wani rufan asiri da gadin duniya aikai dinne bakasan mutuwa in ba gadin duniya ba mai xakayi ko istiqfar din dakai m ya isa yai dari ai inxan shekara dubu bai isaba baba kenan waya ganka da shekara dubu tab yankwani tasa dariya bata jira amsarsa ba tai ciki bari naje gun daya tsohuwar karta ce in koma ya bita da kallo yana dariya yarasa mai yasa yakesan yarinyar sun saba sosai tun tana karama yake gojen babanta ya bashi ita yaki anman jinta yake kamar su zaem kodan baida jika mace ne oho.
Da sallama ta shiga da ladidi sikai ka cibis bayan sun gaisa take tambayarta ina hajiya tn sama ta kada kai tai xamanta anan dan film din mutamin ta ake wato SRK .
   Au zahra kece kika xo shine bazaki iya karasawa saman mu gaisa ba aikece mutun ya tsufa anman kullun yana sama gani nai ana wannan film din na xauna kalla ah koda naji aike duk inda indiyawa suke kinanan tai dariya Allah ba hk bane samanne baxan iya hawa ba yimun shiru mutum sai san jikin tsiya in baka motsa jikinka ai cutace xata kamaka hh wace cuta sai dai karame da'ace karame ai gwara ace kayi kiba eyye lallai ni da'ace ba karatun lpy kike ba zahra da anga shirme a hakanma mai makon kidinga abinda xai ciyar da lpyr ki gaba kinbar san jiki xai cuce ki kaga su kaka kenan kikga ni xoki hadan kayannan dasu gobe Alhaji xai tafi shago.
Duda Alhaji ya tsufa yayansa sun taso sunai ms komai hakan baisa yakashe xuciyarsa ba kullum yn xuwa shago in xaem nanan su tafi tare dan yace jira sai wani ya baka ko roko shike kawo raini .
  Tunda zaem yazo hutu kullum yn gidan su zahra suna shan fira duk irin abinda umma ke mai bai kulawa.
Yauma kan hanyarsu ne na xuwa makaranta dan yace yau xafira ta huta shi xai kaisimu xai kuma xo ya tafi dasu hirarsu suke gwanin sha'awa zahra ce agaba xafira da xakiyya abaya tun kunnowarsu area din akan idan jafar karaf ya dora idanunsa kan xarah dake dariya hankalinsa inyai dubu ya tashi wani kishi ya cika masa rai..
Saida suka dan jima a motar kamar bazasu fitoba sannan zafira da xakiyya suka fito suna dariya ita kuwa zara fafur taki fitowa wai ita ba'anan zafira ke sauketa ba shi kuma yace wlh ba inda xai kara jin ya rantse su xakiyya suka fito fitowa yai yaxago barin da take ya bude gami da dan durkusawa haba kanwis pls ki futo kinga na rantse ta juyar dakai gami da makeshi alamar a'a ya kaikaici idonta yai mt gwalo karaf a idanta aiko tace vaxata fitoba yai saurin durkushewa ya km kunnensa pls kinga na rantse tai dariya daga yau saika daina saurin rantsuwa jafar yana daga nesa vaijin avinda suke fade saidai idanunsa na hango ms drama dun da suke idanunsa suka kada sukai jajur lallai yarinyar nan ta rainashi wato bama ta taba xata santa yake ba kenan ita tanacan da wani yi hakuri yar kanwata ki sauko xan saya miki ice cream da chocolate promise yace promise ta fito tana dariya yai saurin rufe motarsa da karki fito mn can ta hango jafar xai juya da sauri tai gunsa yah jafar ta kwala ms kira kamar karya tsaya xuciyarsa tace xamto jarumi mn ta karaso dan Allah kaxo ku gaisa dawa inkaje ka gani to baxani ba wallahi sai kaje me duda sun saba wasa yau sai yaji yarinyar ta bashi haushi tama raina ms hankali wato hartana da kwarin guwar nuna ms masoyinta ni na jama kaina ya fada dakaimai bansan mgnr ta fitoba dan haka ya maxe ban saniba bata cika jan xance va ita sai ta basar nadai fuskanci yah jafar bakasan kugaisa da yah xaem sai yaji duk kunya ta rufeshi mai ys yacika garaje yai dariya haba ni ba isa suka yo gurin kafin su karaso zaem yaxo ya mika ms hannu jafar ko eh ai na ganeka yai dariya mai yasa kannen nw sunce kai farine yah mubarak baki kaga in akace xa'a hadamu xan gano tunda kune kawai frnd nasu na kusa yai dariya ina mubarak din shi ance bakine kamar yar dunarmu xahra tasan da ita yake tace dadinta mai fadinma dunanne oho dai nafi wasu ko ba hk ba jafar sukai dariya baki daya.
   Abu kamar wasa zahra tarasa mai yasa take jin zafin mata inta gansu da jafar koda kuwa ada tana ganinsu tare koya batasan ace baya kusa da ita suna hira to wai mai hakan ke nufi ta tambayi kanta sansa kike kishinsa kike xuciyarta ta bata amsa iba baxai yuwuba ta fada a fili.
      *********************
Haba malan karka bada maxa mn karasa waxakai shakko koma ince tsoro sai mace kasan Allah danine da tuni anrufe wannan babin dan wallahi da tuni na fada mt uhum mubarak kenan ai garani na na iya fada mk kaida ka kasa fadawa kowa kabarshi yn nukurkusarka kai kuma ka vada wa kenan kaga malan bansan sharrifa ai shiyasa naga san na ramar dakai hhhh to wace sharrin naka ya hango oho pls kafadan sai dai inka yadda na fadi ba dai dai ba xaka fadan ko wace eh naji wace inbanda zakiyya hhhh jafar yaushe ka fara duba yai dariya aiko karamin yaro xai fiskance ku gaba daya kunasan juna kun kasa showing kai kake ganin haka mata sunada wuyar fahinta kuna mutunci kana cewa kanasanta sai wulacin kaga ni shine banso hhhh to basan gaske kake ba aishi so bakaji ana cewa rigar wahala ba to dole kasata kafin ka warke.
Tun jafar da mubarak na boye boye harsuka hakura suka bayyana abinda ke ransu soyayya mai karfi ta shiga tsakaninsu yayin da zafira da zaem tuni sukai nisa asan junansu.
  Jafar ya takurawa zara kan yanasan aturo dan hk tasamu muhd ta fada ms dan bata da kamarsa shine yasamu malan y fada ms yaiko farin ciki sosai dan burinsa ya aurar da zara'unsa . manya sun shiga mgnar tun sa'adda umma taga irin kufin da ake kawowa na nagani inaso kawai hankalinta ya tashi sosai hankalinta bai kara tashiba saida taji sunan mahaifin jafar hankalinta ya tashi sosai dan haka ta tashi tsaye sosai.
   Abu kamar wasa asirin da umma take ya fara daukan jafar dan insuna tare da xara sai yadinga jin haushinta zahra ta kasa gane kansa dan kullum ynx sai sunyi fada yaita mt fada.
Takanas umma taje gidansu jafar ta fadawa umman jafar aikuwa tahau ta xauna fada kamar mai taima umma godiya.
   Abu kamar wasa sai gashi yaxama gaske dan mahaifiyar jafar tace ita bata yadda adaura auran ba ta inda tashiga batanan tashiga ba mahaifin jafar bai dauki abin da mahimmanci ba ganin ya dau abin dawasa dan hk taje tasanar da innarsa taxo tai ta bala'inta indai yasake aka daura bashi ba ita yai ta bata hakuri dakansa yaje ya samu yayanta yace ya vashi lokaci danyai buncike.
  Kawun nasa yakirashi kamar yadda nace mk xanyi bincike nayi abunda suka fada hakane yarinyar batada asali yayarsa taxo da ita daga kaduna kawu yafa tabvatar mana shine ya haifeta ehto koshi ya haifeta to bada aureba.
   Inko haka ne gaskiya malan sule bai kyautaba ta yaudaremu aida sai ya sanar damu komai inmumga xamu iya muyi gaskiya koda inada niyyar dana ya auri yarsa tunda ya rufeni baxan yardaba.
  Koda yakoma gida yakira jafar ya fada masa yadda suka yanke bai wani damuba dan daman kwanannan hanya kawai yake nema da xasu rabu  balle kuma ga wannan mgnr .
Tun abin vai damun zahra har yaxo yana daminta rabonta dashi yau sati biyu kenan takirashi yafi a kirga akashe wataran kuma ta kari ringing dinta yaki dauka tunaninta ko baida lpy dan haka yau tasa aranta after lecture xasu  je gidansu itada su xafira dan dubo ko lpy.
   Basuyi maganar ba jira take sai anfito ta musu mganar lecture dinma gaba daya batasan mai akeba duk bayan minti kadan sai ta duba wayarta ada indai xasu shiga ajaka take ajiye wayar anman yau tana hannunta ji take karta ajiye jafar ya kirata kamar ance duba ta duba alamar sako ta gani ya shigo tana ganin daga jafar ne ta saki wani murmushi da batasan ma ta sakiba bata wani jiraba ta bude shi.
   *Assalamu Alaik*
*Bana bukatar tambayar yaya kike ko lafiyarki dan banjin kin cancanci haka* 
   *Zahra ban tabajin ko ganin axxaluma munafuka macuciya kamarki bantava tsanmanin kedin haka kike ba zahra kin cuceni mai yasa tun farko kika kasa fadan ke wace ko da yake kinso munafinta ta keda macucin marikinki da kike fafa dashi inasan kisani ki kuma daka aranki babu ni babu ke ki mance dani pls kamar yadda na dade da cireki araina kitaima kawa kanki ko sunana kikaji karki tuna dani balle kiyi tunanin kin taba soyayya da me sunan*
                     *Jafar*
Hawaye ne kawai ke bun fuskarta da gudu ta mike tabar ajin tama mance a lecture room take gaba daya suka bita da kallo malamin ya tabe baki gami da watsa hannu alamar i don't care ya cigaba da abinda yake.
  Da'ace lokacin da zahra ta tari adai daita sahu tasan idan taxo gida abin da zata tadda kenan dana san wani gun xata ce ya kaita ba nanba.
      ****************
Malan mahaifinta ta gani tsaye yana hawaye wasu mt na xaxxaga bala'i sina ganinta suka hada da ita sukai mta tatas taja malan sukai ciki dan ita saima taji gaba daya kukan ya dauke.
Ada zahra vata taba yadda malan bashine mahaifinta ba bata taba yadda batada iyaye ba sai yau tabbas buri yayi kama da mutun dan ko bahaushe yn cewa ba rami mai yakawo rami.
Ganin malan baijin dadi tun bayan abunda ya faru yasa zahra takasa tunkararsa da batun da ke ranta duk tabi ta rame tai fiyat baka ganin komai sai dogon hancin nan idanunta sun fada alamar cuta.
  Tun bayan cin kashin da'aka ma malan jiki yaki dadi kullun cikin cuta da wannan an samu ya lafa sai wancan tun yn iya fita har abu yaki dadi makarantarma xahra ba koyaushe take xuwaba tana kula da malan koda muhd yaxo hutu dakyar ya roki malan suje asibiti ai kuwa suna xuwa aka basu gado jininsa ya hau sosai ga xuciyarsa data kamu .
 Hankalinsu ya tashi sosai abu kamar wasa ciwo yaki dadi daga karshema nasarawan suka maidasu Aminu kano.
   Yau kam jikin dadan sauki zahra na xaune akan kujerar da ke gefen gado malan na bacci muhd kan tabarma yana bacci duda itama din ba cikakken bacci take ba tana dan gyangyadawa sama sama kamar daga sama taji muryar malan zahra bakiyi bacci ba tai saurin bude ido eh baba ya miko mata hannu tai saurin kamo hannayen gani baba kece zahra eh nice baba sai gani tai yana hawaye sannu baba ciwonne bari na kira doctor yi xamanki ba ciwo bane inaso muyi mgn kaf labarinta ya bata har yadda yaxo gurinsa kiyafemun xara'una naso kaina da tun farko ban bari kinsan iyayenki ba ban bari kin taso da sansu ba sai nasa miki sona da kaunar yan uwana na bari kullum addu'arki akaina take karewa bacin iyayanki suka fi bukatar addu'arki tasa hannu tana goge masa hawayen yayin da nata yaki tsayawa haba baba ka daina neman afuwata ko kadan ni baka mun komai ba nasan kamun haka ne dan kana sona duniya banda wani uba bayan kai umnata kuma Allah ya jikanta kije dakina xakiga wata akwatu to ciki akwai dan wasu abu buwan na ummanki to baba Allah yakara sauki jitake kamar tai tsuntsuwa taje gida dan yau xatace ta rike wani abu na ummanta .
  Washe gari sukai sallama da malan tai gida dan kawoma muhd abinci.
   Tana xuwa gida dakin malan ya shiga tahau dube dube taiko sa'ar ganin akwatun a kuryar daki jikinta na tawa ta bufe ba komai sai hotuna guda biyu sai yan takardu na makaranta ta bude hoton matasa ne guda biyu mace da namiji sanye da uniform din hygiene sai dayan macen ce kawai .
   Kallon hoton take cikin ranta tana jin dadi duk su biyun sun kwanta mt arai wani sansu ke shiga ranta ta rungume hoton a kirjinta sai takejin dama ummanta ce ta rungume da yau tafi kowa jin dadi bata wani dade ba tai asibiti dan tanasan xuwa ta tambayi malan ko dayanne mahaifinta duda kuwa taga kamarsu daya amman tafisan tabbatarwa.
  Su aunty xulfa tagani duk sunyi tsaye a bakin dakin muhd nakai kawo tai saurin xuwa gun anty xulfa aunty lpy ya jikin baban yana ciki tun daxu likitoci ke kansa ana hira kawai sai haki kinga har yanxu basu fitoba sai hawaye wayyo babana Allah ya baka lpy kaine gatana kai kadai karagemin banida kamarka xulfa ta ruketa kiyi shuru zahra xai warke Doctor ya fito yana share gumi gaba daya sukai guns ya kallesu ya dubi muhd biyo ni office ku kuma ku jirashi sukai office din.
Naga kai kadaine na miji yan uwan naka duk mata ne nasan xaka fisu dauriya duniya ba matabbata vace komai yai farko xai karshe sai kunyi hakuri likita ban fuskance kaba ya jikin malan din jiki kam yayi sauki cuta ta tafi na har'abada malan yaje inda ba'a dawowa muhd yasa salati sai hawaye likita bai hanashi ba sai dayai mai isarsa sannan yace Allah yajikanka baba ynx likita xamu iya daukan gawar yana fita gabaki daya su shidan da yayansu da sukaxo sikayo gunsa yana ganin yan uwan nasu sai kuka tausayinsu ya kara kamashi musanman zahra suna ganin haka suma suka fara kuka aka rasa mai rarrashin wani muhd yai ta maxa ya je yasamo mota suka dauki gawar sai gida.
Zahra bata kara yadda ta rasa malan ba saida taganshi kwance cikin likkafani kan makara jitake kamar karya ne babanta xai tashi masu daukan gawa suka daukeshi sukai waje wani sabon kukan yaxo mata ta mike xata bisu juwa ta debeta ta xube yub jama'a suka kanta.
  A hankula take bude idanta da xatonta aranta tana fadin Allah yasa mafarki nake anman mai mai makon ta dora idanta kan malan kamar yadda in ta suma shi take gani kanta sai ta dora kan wasu kuka ya kwace mata shikenan na rasa babana mai sona tasani duniya bata da kamarsa wayyo ni na shiga uku shikenan babu wanda xata bugu kirji tace shidin mai santa ne tasani komai da yafaru akan ta ne wayyo kai cona .
  Bayan arba'in malan salihu abokin malan ne yaxo da wasiyar malan kan yace yanasan a hada auran zahra da muhd sannan ya bata dakin mamarta kyauta daman gadon yayar tasa ne ta kuma bata da sahannun doctor sai shaidu biyu umma ta hau ta dire ina wallahi bata yadda shiko muhd yace ina sai ya cikawa babansa burinsa.
Tun tasowar zahra muhd yake santa saidai sirrin da mahaifinsa ya boye yasa ya kasa bayyanawa dan gudun wani abu ya tabbatar dashi ya bayyana baban ya rasu baxai taba yafewa kansa va.
Aure kam ansa rana komai anma zahra muhd sai rawar kafa yake waishi ango abunda umma bata saniba yadda batasan auran xahrama haka bata so tanai ma muhd din karane kawai dan wani sa'inma intaga ya xage yana mata kalaman soyayya ko yana kokarin faranta mata har mamaki take wato shi namiji baida kunya ko kadan yama manta ita kanwarsa ce ita inyana wani abun kunyama yake ba.
      Yau sauran sati guda auransu da muhd har mamaki take wai ita xata auri yayanta koya xasu xauna da umma ko xataso xurriyarta aikema kinsan baxata taba soba muhd ya tafi xariya dan karbo wasu takardunsa zahra na kwance umma ta shigo da sauri ta tashi xaune adan tsorace dan ita bata taba ganin xuwan umman ya xame mt alkairiba..
So nake in rokeki alfarma ki taimake ni ki bar gidannan dan Allah ki daure ki bar mn gidanmu ki tai mk ki bar mn xurriyarmu ta huta dan Allah kibarni ha karasa rayuwata cikin jin dadi ina tabbatar miki inkika ci gaba da xama damu tabbas nima ciwon xuciya xai kasheni kamar yadda ya kashen miji ta durkusa tana gawaye wallahi zahra na tsaneki ki daure kisa aranki kin taba rayuwa damu zahra ta mike basai kin rokeni ba xan tafi insha Allah xanyi abinda kika ce harta kai waje ta dawo au dankinga ina rokonki shine xaki dawo takarduna xan dauka ta diba dana ummanta tabar gidan gaba daya kwakwalwarta ta tushe ta manta da kowa da komai kidaure ki mance kin taba rayuwa damu abinda take tunawa kenan to yaxatai ta manta dasu kibar kanon kawai tabi shawarar xuciyarta sai tasha tana sauka a adai dai ta samu taji mai lodi na fadi kanya babura magarya batun yauba taji ana cewa magarya nijar ce xuciyarta ta ce to mai xai hana kibar Nigeria dinm tinda kowa yaki acikinta ta aminta da xuciyarya dan haka kawai ta shiga.
Hatsarin ya farune dai dao lokacin da suka wuce kanya wata mota ta tunkaro su mai motarsu yai kokarin kauce mata saidai mai ya kasa yai dadi inda ya daki wata bishiya baiko shura  ba yayin da da dama suka suma wandama basu sumanba basusan inda kansu yake ba inkadaike wani yaro dake kuka kan ummansa yana ta tashi rayika kam anrasa.......

 


  
 
*Zahra Yar'amana*
*95-100*
*Na F.A.Ya'u*

*wannan paging naki ne zulaihat Abdullahi isa (my zuly)*

Cikin wadanda basu san inda kansu yake ba harda zahra dan tayi mummunar buguwa ga karaya kafa da hannu banda daddaujewa.
   Kai tsaye asibitin garin aka kaisu abin yafi karfinsu taimakon gaggawa kawai suka iya basu aka wuce dasu asibitin koyar wa dake xariya har sukakai su asibitin zahra batasan inda kanta yake ba.
  Sai da zahra tai kwana bakwai da barin gida sannan muhd ya dawo dauke da tsaraba kala kala wadda inka dauke tsirari duk na zahra ne a kokarinsa na kyautata mata daya ke da yadawo masallaci ya wuce koda ya dawo daga masallacin yaga umma taxubo ms abinci iya saninsa dik runtsi zahra ke zuba wa kowa abinci bai ce komai ba zatonsa ko umma ta sauya tsarin ya cinye ya baima umma tsarabarta bega tsaraba nan xuciyatsa ta dan zargu duda yasan xahra ta sauya anman hakan baisa ta dena bashi girma ba ya mike gami da ture kwanon abincin yai dakinta wayam yaga dakin sai kura da tarkace da yada da haushi yakara kuleshi iyakar saninsa da zahra bata kaxanta tun tn yarinya to dan mene se ynx data girma adan fusace ya fito yana tambayar umma wai ina yarinyar nan ta shigene taji tambayar kamar daga sama gabanta ya yanke ya fadi ta hade rai wacce yarinya fa umma zahra fa nake nufi au kace karuwa haba umma inda kara kodanni aikya rangwantawa xahra yanxufa surukarki ce ta xaro ido rufan asiri dannan Allah ya kiyashe ni da surukuta da wannan tambadaddiyar maras asali naji umma ynx dai tana ina tatafi yawan ta zubar dinta kasan ta tsotsa a mama yadan kada kai umma mai kike nufi abinda nake nufi shi nake nufi yau rabonta da gidannan har na manta rabonda nasata a idona kwana bakwai mun kwanta da ita bamu tashi da itaba kasan tsintacciyar mage malan kesanta anman ita batasan malan da xurriyar malan tunda gashi dan kawai yace ka aureta ta gudu bai karasa jin batun ummanba yai waje idansa ya kada yai jawur iyakar kololuwar tashin hankali hankalinsa ya tashi fatansa Allah yasa tn gidan su zaem koda yaje suma hankalinsu yai mummunan tashi dan bataje ba tun rasuwar malan sukai sukai ta dawo tace tunda da ran malan bai bada itaba bayan ransa baxata vada kanta ba gidansu xafira yaje da xakiyya suma hankalinsu atashe yasa mesu dan sunxo nemanta fanin bata xuwa sch umma ta koresu.
    Duk inda muhd yake tunanin zara na xuwa yaje ba labarinta nan ya kom asibitocin dake garin kano da police stations babu koda mai kama da ita.
     Muhd ya kasa dangana akullum ranata fito akullum sai ya fita sati uku kacal da batan zahra yabi yai baki ya rame muhd da yake fari doga mai yar giba dedai shi shine yai baki ya rame kai kace yai jinya ne.
    Tun jafar naganin abun kamar wasa har'abu yaxama babba kullum baya iya bacci sai tunanin zahra tabbas koda jikinsa sun abince sun br xahra xuciyarsa baxata taba iyawaba sai ayanxu yakejin haushin kansa toma wai ada mai yasameshi bashi da buri ayanxu inbanda yaga zahra yasani da wahala ta iya yafe ms anman xaiso gwada sa'arsa koda sau dayane shi ya amince koda daga sama ta fado yanxu xai aureta.
    Yau yai niyar zuwa har hall dinsu dan bata hakuri ko mai xata mai yaji xai jure yau sati uku kenan yana jele tsakanin faculty dinsu danasu zafira baya ganinta inda suka fara haduwa kuwa kullun sai yaje babu kosu xakiyar yasani tanasan gurin tasha fada masa watakil yanxu ta tsani wajen duk lefinka ne inji xuciyarsa .
    Yau kam lecture dinsu gabaki daya ba wadda bai shiga ba saidai ba xahra dan haka yana fitowa yai faculty dinsu zafira koxaiga daya daga cikinsu zafira ya hango suna mgn da wani ta hangoshi ta hade rai baima kula da yanayin fuskarta ba dataga da gaske ita ya doso dasauri tace muklis mu hadu anjina ok yace tai saurin yin gaba ganin haka yasa yadan dada sauri pls zafira badanniba dan sanki da annabi dan girman Allah ki tsaya kariga ka cuce ni ka hadani da wanda ba'a hadani dashi nakiyi minti uku xan iya baka taja ta tsaya inajinka daman xahra nake san gani tadan xaro ido ne kace yasan taji bai kasa aguwwa ba ya mai maita wai wace xahran kake nufi xahra nawa kikasan inada ta tabe baki lallaima kai harkana da karfin guwar kiran sunan xahra ka kirata taka kai harka na da damar kiran zahra taka mai yasa ne wasu mutanen gabaki daya basa aiki da kwakwalwarsu to inasan fada maka burinka ya cika zahra ta bata inma neman ta kake ka karadata to sai kaje ka xuba ruwa a kasa kasha tai tsaki tabarshi nan tsaye kamar dutse.
   Tunda ya koma gida ba'abunda yake iya tunawa sai batun zafira burinka ya cika zahara ta bata gabaki daya haushin kansa yakeji yakasa ko sau daya yaji xafin xafira na maganganun datai masa da gaske xahransa ta bata kuma a dalina gaskiya baxan tava yafema kaina ba.
   A hankula take bude idanta dishi dishi take gani daga bisani ta dora idanunta kan fankar dake wulgawa a ta maida kallonta gefe inda tai arba da robar jinin dake shiga jikinta gefenta kuma wata ce kwance daure da robar ruwa hakan ya tabbatar mata tana asibiti ne ta yunkura xata mike da sauri doctor din dake rubutu kusa da ita ya komar da ita hihakuri kina da ciwo ne ta daga ido ta kalleshi sannu ko ya kike jin jikin bata ce komai ba kingaji da kwanciya ko tai shiru nurse da ke baima wata magani ya kira sister tagaji da kwanciy xaunar da ita to doctor ya wuce daya gadon sai da yagama round dinsa ya dawo gadonta badai abin dake damunki ko bata ce komai ba illah ta bishi da ido.......


     *Zahra yar'amna*
*100-105*
*Na F.A.Ya'u*
Baxan gaji da gode miki ba 
Zulaihat Abbdullahi Isa amaryar gobe.

Asannu ahankali jikin xara ya a kyau yau satinta  na biyar kenan a asibiti yanayin kulawar da likitan ke bata yasanya tadan bafara sakin ranta dashi yadamu sosai akan rashin lafiyarta duda ta kula halinsa ne haka bawai ita daya yake ma haka ba duk marasa lafiyar dakin na yabonsa.
   Sunyi sabo sosai da doctor nasir dan har mahaifiyarsa ya kawo ta dubata abincinta da magani duk shine.
   Yau bashi da aikin safe na dare gareshi dan haka yashigo asibitinne dan duba jikin xahran xaune yake kan kujerar dake gefenta suna fira kai kace sun shekara da juna can yace kinga yanxu kin warke sarai sai abinda ba'a rasaba ina xatonma jibi xamu baki sallameki tai dariya ai doctor da temakonka komai yai dedai intambeki mana inajinka wai ko ina xakuje kukai hatsarinnan taishiru can tace magarya yai dariya ashema yar kasarmu ce kinsanfa babana da dan niger ne a wane unguwa kuke a magarya nima bansani ba tace yakada kai badai kyasan fadamun to yanxu bananba ko number din wani naki ne kibani nakirasu dansuxo daukanki sai hawaye nan yahau rarrashinta saida tai mai isarta haba zahra kiyi hakuri mn innan miki wani abu kiyi hakuri ta share hawayenta doctor baka mun komai ba wallahi tunawa danai cewar banda kamar kaina bani da wani daxan bugu kirji inkira da masoyi na yasani kuka uwata ta rasu marikiyyata me sona yarasu babana yarasu banda sauran wani da xankira mesona haba zahra rashin iyaye bashi ke nufin baka da kowa ba sai kace mara dangi taisaurin cewar haka nake doctor banda dangi iyayena basu da dangi yakada kai kodai kin bar gidane bakisan komawa ta fuskanci me yake nufi wato zata yawon duniya nan ta baahi labarinta tun daga wayonta har yaxuwa inda sukai hatsari ya tausaya mata sosai .
   Koda ya koma gida yasanar da iyayansa komai na xara suka tausaya ya rokesu alfarmar zai kawo zahra gidan suka amince.
    Koda aka sallami zahra kai tsaye gidansu zahra aka wuce da ita dakyar nasir yasha kanta ta amince dan cewatai tafisan tai rayuwarta ita kadai bata son takara sabawa da wasu karshe su gujeta karba ta mutunci ta samu kannensa biyar Fadima ita ce kusan sa'ar zahran dan haka dakin fadimar ta sauka duda tadan girme mata .
     Yanayin yadda suke mata yasanya ta gamsuwa iyalan gidan sun san darajar mutum ko daki ta shige sai fadima ta kirata tun tana dari dari harta sake ana komai da ita duda har yanxu tana dingisawa haka ta daure komai na aikin gida take yi duda kuwa sunada masu aiki.
    Yau suna zaune a falo tadan kalli mumy mami pls ki rokar min dad atai maka a bincika mini kayana gurin police tai dariya yanajinki ai yace indai bata da bakin fadi mini ni baxan jeba tai dariya pls dad to shikenan xan dubatai godiya.
    Dady da mu'allim da ita sukaje suna gurin aka bugowa dad waya yanada baki a office anan ya barta ita da mu'allim ya wuce an futowa da zahra kayan tai sa'anata yananan da yake yan tarkace ne takarba sukai gida da mu'allim.
    Hoton ummanta kuwa kullum sai ta kalleshi na tsawon lokaci kafin tai bacci ji take kamar ummanta ce take kallo wani abu dake bata mamaki bai fice daya saurayin dake kusa da ummanta ba kamarsu da dadinsu Fadima take gani sai dai takasa yadda gani take kamar idanunta ke ganin haka dan haka tabar batun aranta.


*Zahra Yar'amana*
*105-110*
*Na F.A.Ya'u*
Yau zahra sun fita da fadima dan dady yaima abokinsa dake nan college of health zariya mgn kan yanasan form yai sa'a kuwa yace taxo ta karba dan ya gaji da xaman da take saidai tai girki ta kwanta yai takaicin katsewar karatunta dan cewarsa damar da tasamu bakowa kesamunta ba ta karatun likita.
  Gidan shiru nasir ya shigo yan aikin gidanma duk suna bangarensu mami ce kawai a xaune tana kallo ya xauna kujerar gefenta gami da cewa wash ta dan kalleshi yadan rissina mami sannu da gida ta amsa da yawwa yau ina yan matanki naji gidan shiru daxunnan suka fita nasan yanxu suna hanya nasan wannan uwar gantalin ce ta jasu ko tai dariya kaidai kanasan dorama fadima lefi to ba ita ce ta jasu ba aiken dady ne yasosa keya alamar jin kunya ya mike yunwa nakeji wallahi yau mai aka dafa mn mutuminka ne ya yamutsa fuska kai fadima bata kyautawa wallahi tai dariya nasiru kenan to dai yau ba fadima ce tai girkinba zahra ce mami sanin tane bakiyi ba tsaf xatasa zahra ta dafa dan tasan banso oho dai kaji dashi Allah dan inajin yunwa ne da baxanci ba kaga ni karka isheni inbaka ci xaka iya bar mana abunmu be kwantai ba yaxanyi haka xan tuttura.
   Duk runtsi nasir be cin abinci awaje danshi irin mutanan nan ne masu kyan kyami hakan yasanya dasunyi tsiyar da yan matan gidan sesu fara dafa abinda beso musanman fadima da basa rabo da hatsaniya seta jera sati tana girka abinda beso.
   Yana mita ya bude kular hadadden kule le ne a ciki wanda yaji hanta kwai da attaruhu kamshin ya bugi hancinsa baisan ya cinye duka biyar dinba sai da ya tsiyayi lemon dake gefensa lemon amarba hade da madara mai sanyi yaji wani sanyi ya xiyarci kirjinsa yakai hannu dan sake diban ala la yaji wayam mami ya fada ta kaga ni ka isheni inbaka ci kabar min abuba ba adole wai kuwa kinga abinda suka ragen a'a tace wai aras mai xa'a ragen sai alala guda biyu tai dariya ni nadauka ma daya ne kaida baka iya cinye biyu haba ashe daya ne nake xaton biyu ne shiyasa ban koshiba tai dariya gaskiya zahra ta ciri tuta ka cinye alala biyar kace biyu ne na sara mata ya suri jug din lemon mami se nadawo ina kuma xaka min da kofi mum kinsan aiki inyai yawa in ina korawa dashi na rage xafi tai dariya ashe iskanci ne da yake sawa kake cewa bakasan kule le yasosa keya mami duk cikin yunwa ne kaji dashi ta fada.
   Koda su zahra suka dawo sunci dariya ai kuwa da ya dawo fadima ta takura masa da tsokana yai dariya ai duk cikin yunwa ne kaidai kawai kace kaji dadin abinci eh naji kema kiyi xuciya ki iya adinga jin dadin naki ki dinga yima mutane abinci kamar magani aiko fade kake fadima badaga nan ba wajen girki yai dariya girkin turawa ba sukai dariya gabaki daya.
   Tunda jafar yasamu labarin batan xahra komai ya kwance masa damuwa tabi tai masa yau asannu ahankali yake ramewa iyayansa sun kasa gane masa tunsuna fada sun koma nasiha abu kamar wasa sai gashi shine harda kwanciya a asibiti ganin yadda ya tada hankalinsa kan batun zahran yasa kakarsa da babarsa sukace asirine duk inda sukaji me mgani sesunje karshe wani malami ya fada musu ba'asiri balle shafar aljanu tsabar damuwa ce ganin dagaske xasu iya rasashi yasa mahaifiyar tasa yadda kan cewar ya auri xahra mahaifinsa da kawunsa sukace ina su kunya sukebji baxasu iya roko malan ba tace ita xata ummansa ma tace xata kharima wadda lokacin karbo kaya harda ita agaba gaba wajen rashin mutunci tace xata haka suka shirya suka tafi.
    Umman muhd ta amshesu hannu bibiyu muhd dake gefe bai ganesu va ya gaidasu cikin mutunci daman mai gidan mukaxo nema muhd yadan gyara Allah sarki hala baku samu labarin rasuwarsa ba fatan lpy suka jajanta gami da musu gaisuwa kafin su dora da batun da yakawosu gwaggwo harda karfin halin cewa ina sirikar tamu ne ko tana makaranta muhd bai bari umma tace wani abuba ya fara.
    Sai yau kukasan shegiya nada anfani kenan ai nadauka kudin masu tsarki kamata yayi kuje ku nemi mai tsarki irinku ku masu kudi kanku kawai kuka sani wato kunci kashinku akan baiwar Allah yanxu kun lallabo dan ku karasa ruguxama zahra farin cikinta wato kashe mn uba da kukai be isaba sai kun dawo to wallahi ku sani indai ina raye ni muhd to xahra ta fi karfin family dinku saidai ya mutu cikin fushi da daga murya yake mgn pls kunga ku tashi kubar mn gida tun kan inci mutuncinku cin mutunci na nawa kuma tunda bka duba firfira taba yai tsaki da Allah ku tashi dannasan baku da gado cikinsa haka suka bar gidan jiki ba kwari aikuwasuna fita umna tai kansa da fada sin sin ya fice yabar gidan dan dai uwa uwace da'ace umma ba ita ta haifeshi ba akan xara xai iya komai sedai uwa duk rashin halinta tafi karfin raini akan dan tudun kofar gidan ya xauna besan sadda kuka ya kwace masa ba.
     Mami wai ina yaran nan ne yansu sukai sama xasu shirya wai yau birthday din isma'il yayan salma nasan sarkin yawonnance ta shirya musu kamar kasani ana xaune daga daga waya ta azazzalesu su tashi su tafi ai dole xa'aje shan xaki dan Allah mum wai banyi kyauba mum takalleta inji ai ko gasar kyau kyaxo ta daya tasa dariya daman nasani ba wannan mu'allim din bane wai ban kyau ba kyaleshi bakin ciki yake danshi baki ne inji nasir yai dariya bayan da bleach aka wanke ki kina jari riya kinajinsa ko mum kyaleshi kai kinji ummi na zahra suka sauko sanye da irin kayan ummi sunyi kyau sosai ina iklimar inji mami tace wai zulaihat ce xata xo ta fasa binmu to shikenan fadima ta dau key din dake kan center table din dakin mami mun dau aran mototarki nasir da tunda suka fito hankalinsa gaba daya ya koma kan xahra tai masa kyau sosai mami se mun dawo harsun kai bakin kofa nasir yace kutsaya nakai ku kai yaya kai yaya kai kullum se kadinga takura mana inbaxan kaiku ba kwa iya koma wa ba dole suka yadda saida yagama wulakancinsa yai wanka sannan ya fito duk akan niyarsa nasu fasa dan wani kishin zahra yake ji.
    Gabaki daya suka hakince a baya yako hade rai mai kuke nufi ce muku akai ni direba ne fadima tace ummi tashi ki koma gaba ta turo baki tabdi Allah vaxan komaba pls aunty xahra koma wato ni kika raina kunga ku nake jira inna koma gida wallahi baxakuba xahra tace fadima ki shiga adawo wa na shiga promise tace promise ta koma gaba duda ba haka yasl ba haka yaja suka tafi cikin nishadj da farin ciki suke tafiyar kai kace basune daxi suke kunkuniba sai hira suke irin ta yan uwa masu san junansu.
    Har jikin motar ya rakota sunjima suna mgn wadda nasir baijin mai suke cewa ya sunyi kamar minti biyar su fadima suka fito ta bude ta shiga gaba isna'il yadan rankwafo sai naxo ko ka cika mai maita magana af kayi lefi baka gaida yayan muba babbama kuwa kinsan inkina kusa bana ganin komai ya xagayo babban yaya afuwan a cunkushe nasir yabashi hannu suka gaisa bai kawo komai ba xatonsa ko haka halin nasir din yake.
    Tunda suka fara tafiya ba wanda yace kala dan nasir ya kure radio koda sukaje gida bau jira sun fitaba ya bude ya wani buga mirfin kofar yai ciki fadima tace ram maxa ya baci muje mu bashi hakuri inji xahra tab wallahi baxaniba aikodai nima baxani ba mai mukai masa inji fadima ya huce nidai sai naje se kindawo kya dawo da sacacciyar gwiwa.
     Kai kawo kawai yake adaki zahra ta shiga afusace ya juyo nakiraki ne ta kada kai nadai xo baka hakuri ne nace kunmin lefi ne ta ce a'a nadai dauka kodan mun dade ne no ba haka bane pls xaki fita anman yaya anman what pls out sin sin ta fice jiki a salube....

*Zahra yar'amana*
*110-115*
*Na F.A.Ya'u*

Http:/fayau26wordpress.con

*Banhakuri*

_Ina mai baima masoya wannan Labarina hakuri sakamakon tsaiko da yasamu wajen rubutu hakan ya farune sakamakon Exam danake anma yanxu alhandulillah nagama insha'Allah nan bada jimawa ba xan kawo karshensa_


*Cigaban labari*

Jiki bakwari zahra ta fito daga dakin su Fadima ta gani bakin falon nasa suna ganinta sukasa dariya ansace mata gwiwa wooo wani k'ululun bakin ciki yaxo mata wuya kamar tai kuka tadai daure ta shanye to ya ranku fes inji ummi ai daman anfada miki kikaji anfada miki shi yaya anai masa gwaninta ne dallah ni matsa ta turesu ta shige tai bayan gida dan karsu hangota.
    Zaune suke suna karin safe yashigo sanye da suite ash yai kyau sosai sosai rike da rigarsa ta aiki ya'ajeta a kujerar dake falon yai dining area morning papa morning son anfuto kenan eh barka da safiya mami barka ka makarafa wallahi inakwana yaya yaran suka hada baki inakwananmu kannes ke xuban abinci ba ke anan gun inji Fadima fada masa dai inji dad haba papa kai kake sawa yarannan na raina ni wallahi saunawa xance kadena kiransu dake sorry papa Fati zuban abinci ta turo baki xatai magana kinga bansan raini maxa zuba masa inji mami afusace ta tura masa gabansa yafara ci yana dariya yadan saci kallon zahra, zahra'u ba gaisuwa bata kalleshi ba tace nagaishe jine bakaiba ok kinsan nazama kurma jiya bata ce komai ba ta mike tabar gun dan ta fuskanci magana yakeso.
    
    Da gudu ta biyo ta kinga Fadima banasan abinda kike mun kibani ita kuma tana dariya inkinga na baki saikin min alkawari abayan Nasir ta buya yaya boyeni tana ganinsa ta guya tana fadin ki cinye zahra zahra yake kwala mata kira tai kamar batajishiba tai ciki ya ture fadima dake bayansa ke barasa wace irin mutunce kin fiye tsokana sekije ki bata hakuru tunda kinsa tai fishi ta turo baki kai yaya kullun ni kake baima lefi ta shige ciki tana sambatu yasa dariya kowa datasa rigimar ya fuskanci zahra fishi take dashi yarasa me yasa takasa fuskantarsa yarasa meyasa takasa gane kishinta yasashi yin haka bawa yai dan bata mata rai vane.
    
    *Zahra Yar'amana*
    *115-120*
    *Na F.A.Ya'u*
    
    Http://fayau26wordpress.com
    
    
    Fadima ya gani kwance afalon ah yar hutu yau baxa'a sch din bane bata vashi amsaba sai daga kai datai bai damu darashin amsarba yace meyasa baxaki ba ko baku da lecture zahra dake saukowa tace bata da lpy ne ayya ya fadi gami da saurin taba jijinta subhanallahi tun yaushe tasha magani a'a ya mike bari na kawo miki tai saurin tashi nafa warke ai bance baki warkeba ungo sha ta yamutsa fuska ko kisha ko inmiki allura wallahi takarba tasha dakyar sai asannan zahra tace ina kwana yaya lpy kalau ya fice tashiga dakin mami, mami na tafi kisa fadima ta koma daki nasa taci dangakali dakyar to zahra saikin dawo Allah bada sa'a amin mami.
    
    Tsaye taganshi jikin motarsa tai kamar bata ganshi ba ganin sun gaisa ganin ta wuceshi yasa yakira sunanta zahra taja ta tsaya na'am yaya kefa nake jira zan saukeki lah yaya karka makara zan hau bus yadan kalli agogonsa yanxu bakwai tai haryanxu da time xatai magana yadora hannu kan bakinsa shiiii alamar tai shuru karkice komai muje ko tashiga sunyi tafiya me nisa yadan kalleta zahra tace na'am fushi ake dani ko haba yaya aika fice inyi fishi dakai ko eh mana inda tai dedai da shigarsu makarantar ta bude ta fito tadan rankwafa nagode yaya tai ciki.
    Tsaye suke daga gani gaba daya sunajin dadin hirar dasuke yadda take yawan murmusawa kallo daya zaka musu kayi zaton sunyi shekaru suna soyayya yadda saitin hancin motarsa ya kallosu haka idonsa akansu lokacin yai dedai da sakin dariyarsu gabaki daya wani kululun takaici ne ya zo masa wuya jiyai kamar yaje ya shake matashin dasuke tare yafi minti goma amotar kafin ya fito baiko kalli inda suke ba yai ciki wai meyasa zahra ta kasa fahintar abinda ke ransa meyasa takasa fahintar shi ba santa yakeba face kaunarta kaicona ya fada gami da dukan bangon.
    
    *Zahra Yar'amana*
    *120-125*
    *Na F.A.Ya'u*
    
    Http://fayau26wordpress.com
    
    
    Zaune suna kari ummi tace papa kaface in akai albashi xaka bamu kudi muje shopping to lashe money yaushe na fada kai papa kai papa sunan banza ne fa kuma kace no bad names in islam yai dariya ah lallai yarinyar angirma sai aure tai saurin cewa papa when are u giving the money waini yaishe nace zan bada tace Allah ka fada yadan daga kai alamar tunani anya kuwa Fadima tace lokacin da malan me karatun juma'a yace maka sun iya hadda ohhh na tuna yanxu dai ku bari ayi albashin muslim yai saurin cewa jiyafa naga kana lissafa kudi mami tace to kajifa baxaka musu wayo ba towo kace inada sa'idinawa suka sa dariya baki daya ya mike vara naje karna makara kibama yaran dubu bibiyu manyar shida shida suka saka ihoo that's our real papa zahra tace mungode papa gabaki daya suka hada baki thank you papa sauran akwaxo alawowi aikaima kasan su zasu kwaso inji mami.
    
    Ya jima yana kallonta daga gani tana cikin nishadi kallon ball din da muslim da mua'allim sike take ya fiskanci muslim take goyon baya dan tin tsayawarsa ya ga in muslim yaci saita saka ihuu goal yayin da in mu'allim ne sedai ta vata rai zuciyarsa ke azazzalarsa yaje kusa da ita ya zauna ahankula yake tafiya hakan besa taganshi ko jin takunsa ba sai kamshin turarensa daya doki hancinta tai saurin juyawa suka hada ido sannu yaya tace kafin ta mike da xummar barin gun muslim ya kamota yah zahra bafa mu gama kwallonba kije ki cigaba da kalla ya kamo hannunta zuwa inda ta bari Nasir ya kalleta dagaske dai fishi kike dani ko ta kada kai ba haka bane kawai dai kawaidai me zahra bakomai kinga wallahi sekin fada kawai bansan takura makane yaya dannaga kamar bakasan nake xuwa inda kake ohhh my goodness ya fada waya fada miki haka eyyi tai shuru atakaice dai alokacin suka shirya tana goyon bayan muslim shi kuma mu'allim.
    
    Yau yakuduri niyyar duk rintsi duk wuya saiya bayyanama zahra burin ransa zaune take dankoron nata na gefe muslim sunata hira yadan zauna suka taba hirar tare yadan kalli muslim jeka kace islam ya gyaran daki kai kuma kaje gidansu muhd kakarbon sakon da ya vaimaummansa to yaya.
    Zahra na'am yaya wata magana nakesan muyi tamaida hankalinta gunsa inajinka ada nadauka tausayinki nake shiyasa nake damuwa da lamarinki anman daga baya sena fuskanci ba tausayi bane so ne anman danai tunani nai kokarin barin araina sai na gano baso bane kauna ce zahra nadade inasan fada miki nadade insan ki fuskanci rayuwata baxatai dadi ba sedake nafuskanci ke kadai ce macen dazan iya rayuwa da ita nadade da fuskantar kaunarki nake nadade da fuskantar ......cikin kuka ta mike so fa kace yaya so so sai kuka da gudu tai ciki ya mike gami da bugun goshinsa da hannu ohh my God.......


*Zahra yar'amana*
*110-115*
*Na F.A.Ya'u*

Http:/fayau26wordpress.con

*Banhakuri*

_Ina mai baima masoya wannan Labarina hakuri sakamakon tsaiko da yasamu wajen rubutu hakan ya farune sakamakon Exam danake anma yanxu alhandulillah nagama insha'Allah nan bada jimawa ba xan kawo karshensa_


*Cigaban labari*

Jiki bakwari zahra ta fito daga dakin su Fadima ta gani bakin falon nasa suna ganinta sukasa dariya ansace mata gwiwa wooo wani k'ululun bakin ciki yaxo mata wuya kamar tai kuka tadai daure ta shanye to ya ranku fes inji ummi ai daman anfada miki kikaji anfada miki shi yaya anai masa gwaninta ne dallah ni matsa ta turesu ta shige tai bayan gida dan karsu hangota.
    Zaune suke suna karin safe yashigo sanye da suite ash yai kyau sosai sosai rike da rigarsa ta aiki ya'ajeta a kujerar dake falon yai dining area morning papa morning son anfuto kenan eh barka da safiya mami barka ka makarafa wallahi inakwana yaya yaran suka hada baki inakwananmu kannes ke xuban abinci ba ke anan gun inji Fadima fada masa dai inji dad haba papa kai kake sawa yarannan na raina ni wallahi saunawa xance kadena kiransu dake sorry papa Fati zuban abinci ta turo baki xatai magana kinga bansan raini maxa zuba masa inji mami afusace ta tura masa gabansa yafara ci yana dariya yadan saci kallon zahra, zahra'u ba gaisuwa bata kalleshi ba tace nagaishe jine bakaiba ok kinsan nazama kurma jiya bata ce komai ba ta mike tabar gun dan ta fuskanci magana yakeso.
    
    Da gudu ta biyo ta kinga Fadima banasan abinda kike mun kibani ita kuma tana dariya inkinga na baki saikin min alkawari abayan Nasir ta buya yaya boyeni tana ganinsa ta guya tana fadin ki cinye zahra zahra yake kwala mata kira tai kamar batajishiba tai ciki ya ture fadima dake bayansa ke barasa wace irin mutunce kin fiye tsokana sekije ki bata hakuru tunda kinsa tai fishi ta turo baki kai yaya kullun ni kake baima lefi ta shige ciki tana sambatu yasa dariya kowa datasa rigimar ya fuskanci zahra fishi take dashi yarasa me yasa takasa fuskantarsa yarasa meyasa takasa gane kishinta yasashi yin haka bawa yai dan bata mata rai vane.
    
    *Zahra Yar'amana*
    *115-120*
    *Na F.A.Ya'u*
    
    Http://fayau26wordpress.com
    
    
    Fadima ya gani kwance afalon ah yar hutu yau baxa'a sch din bane bata vashi amsaba sai daga kai datai bai damu darashin amsarba yace meyasa baxaki ba ko baku da lecture zahra dake saukowa tace bata da lpy ne ayya ya fadi gami da saurin taba jijinta subhanallahi tun yaushe tasha magani a'a ya mike bari na kawo miki tai saurin tashi nafa warke ai bance baki warkeba ungo sha ta yamutsa fuska ko kisha ko inmiki allura wallahi takarba tasha dakyar sai asannan zahra tace ina kwana yaya lpy kalau ya fice tashiga dakin mami, mami na tafi kisa fadima ta koma daki nasa taci dangakali dakyar to zahra saikin dawo Allah bada sa'a amin mami.
    
    Tsaye taganshi jikin motarsa tai kamar bata ganshi ba ganin sun gaisa ganin ta wuceshi yasa yakira sunanta zahra taja ta tsaya na'am yaya kefa nake jira zan saukeki lah yaya karka makara zan hau bus yadan kalli agogonsa yanxu bakwai tai haryanxu da time xatai magana yadora hannu kan bakinsa shiiii alamar tai shuru karkice komai muje ko tashiga sunyi tafiya me nisa yadan kalleta zahra tace na'am fushi ake dani ko haba yaya aika fice inyi fishi dakai ko eh mana inda tai dedai da shigarsu makarantar ta bude ta fito tadan rankwafa nagode yaya tai ciki.
    Tsaye suke daga gani gaba daya sunajin dadin hirar dasuke yadda take yawan murmusawa kallo daya zaka musu kayi zaton sunyi shekaru suna soyayya yadda saitin hancin motarsa ya kallosu haka idonsa akansu lokacin yai dedai da sakin dariyarsu gabaki daya wani kululun takaici ne ya zo masa wuya jiyai kamar yaje ya shake matashin dasuke tare yafi minti goma amotar kafin ya fito baiko kalli inda suke ba yai ciki wai meyasa zahra ta kasa fahintar abinda ke ransa meyasa takasa fahintar shi ba santa yakeba face kaunarta kaicona ya fada gami da dukan bangon.
    
    *Zahra Yar'amana*
    *120-125*
    *Na F.A.Ya'u*
    
    Http://fayau26wordpress.com
    
    
    Zaune suna kari ummi tace papa kaface in akai albashi xaka bamu kudi muje shopping to lashe money yaushe na fada kai papa kai papa sunan banza ne fa kuma kace no bad names in islam yai dariya ah lallai yarinyar angirma sai aure tai saurin cewa papa when are u giving the money waini yaishe nace zan bada tace Allah ka fada yadan daga kai alamar tunani anya kuwa Fadima tace lokacin da malan me karatun juma'a yace maka sun iya hadda ohhh na tuna yanxu dai ku bari ayi albashin muslim yai saurin cewa jiyafa naga kana lissafa kudi mami tace to kajifa baxaka musu wayo ba towo kace inada sa'idinawa suka sa dariya baki daya ya mike vara naje karna makara kibama yaran dubu bibiyu manyar shida shida suka saka ihoo that's our real papa zahra tace mungode papa gabaki daya suka hada baki thank you papa sauran akwaxo alawowi aikaima kasan su zasu kwaso inji mami.
    
    Ya jima yana kallonta daga gani tana cikin nishadi kallon ball din da muslim da mua'allim sike take ya fiskanci muslim take goyon baya dan tin tsayawarsa ya ga in muslim yaci saita saka ihuu goal yayin da in mu'allim ne sedai ta vata rai zuciyarsa ke azazzalarsa yaje kusa da ita ya zauna ahankula yake tafiya hakan besa taganshi ko jin takunsa ba sai kamshin turarensa daya doki hancinta tai saurin juyawa suka hada ido sannu yaya tace kafin ta mike da xummar barin gun muslim ya kamota yah zahra bafa mu gama kwallonba kije ki cigaba da kalla ya kamo hannunta zuwa inda ta bari Nasir ya kalleta dagaske dai fishi kike dani ko ta kada kai ba haka bane kawai dai kawaidai me zahra bakomai kinga wallahi sekin fada kawai bansan takura makane yaya dannaga kamar bakasan nake xuwa inda kake ohhh my goodness ya fada waya fada miki haka eyyi tai shuru atakaice dai alokacin suka shirya tana goyon bayan muslim shi kuma mu'allim.
    
    Yau yakuduri niyyar duk rintsi duk wuya saiya bayyanama zahra burin ransa zaune take dankoron nata na gefe muslim sunata hira yadan zauna suka taba hirar tare yadan kalli muslim jeka kace islam ya gyaran daki kai kuma kaje gidansu muhd kakarbon sakon da ya vaimaummansa to yaya.
    Zahra na'am yaya wata magana nakesan muyi tamaida hankalinta gunsa inajinka ada nadauka tausayinki nake shiyasa nake damuwa da lamarinki anman daga baya sena fuskanci ba tausayi bane so ne anman danai tunani nai kokarin barin araina sai na gano baso bane kauna ce zahra nadade inasan fada miki nadade insan ki fuskanci rayuwata baxatai dadi ba sedake nafuskanci ke kadai ce macen dazan iya rayuwa da ita nadade da fuskantar kaunarki nake nadade da fuskantar ......cikin kuka ta mike so fa kace yaya so so sai kuka da gudu tai ciki ya mike gami da bugun goshinsa da hannu ohh my God.......




*Zahra Yar'amana*
*125-130*
*Na F.A.Ya'u*


Http://fayau26wordpress.com


Dasauri ya bi bayanta anman saidai kan yaje ta shige daki dokar gidance maxa basa shiga dakin yan matan gidan kamar yadda suma inba kirawo waneba bame shiga dakin dole yakoma falo koxaiga fitowarta anman har'akai magariba bata ko leko ba ko agun cin abinci yaita xuba idon ganinta babu ita ga mamakinsa ba wanda yace tana ina abinda be saniba ta cema mami sinada aikin makarata.
    Duk wata hanya da zahra tasan zasu hadu da Nasir ta tosheta kullun da irin tsirfar datake fito da ita dankartazo cin abinci iya damuwa kam Nasir ya damu.
    Kai muktar wannan wane irin abune kaji kuwa yadda na tsorata yasa dariya irin wannan zurfi a tunani haka kaidai bari wallahi ina cikin matsala subhanallahi meyafaru haka nan ya fada masa komi da yadda sukai da zahra ni abihda ke damunana be wuce yadda yarinyar nan taki yadda mu hadu yai dariya yanxu yar wannance matsalar Nasir ya hade rai kaifa dan iskane mene kuma abin dariya yi hakuri kasan me zakai kaje sch ka sameta ya mike shiyasa nakesanka wallahi ni aibanyi tunanin haka ba katsaya mn kaji bari sena dawo be jirashiba se sch dinsu zahra yai sa'a malaminsu bexoba be wani shawuya ba aka nemo masa ita tana ganinsa ta hade rai ina kwana yaya lpy sarkin gava bata ce komaiba tace kafito muje can bai musaba sukai dan nesa kadan inda be cika hayaniya ba.
    Zahra rannan muna mgn kika tashi bakiji karshentaba tai saurin kallonsa wace mgn aukinma manta tace kasan dan adam ajixine ehto hakane barina tuna miki magana kan soyayya danai miki tayi tuni hawaye suka wanke mata fuska tadauko kasa yaya dan Allah kabar maganar so dinna dan Allah sabida me sabida banasan jinta karmar so ita ce ke rushen farin cikina kana sane da zaman karo nake agidanku kanasane da a inda na girma nai hankalima sun kasa yadda jininsu ya auro ni balle su danaxo indai baso kake su koreni ba dan guntun farin cikin dana damu ya tafiba zahra ki saurareni ni yaya ba abinda zan saura ka k'yalen rayuwata incigaba da yinta haka tafiyemun da 'di pls zahra ki tsaya kiji bata tsayaba balle taji abinda zaice tabar gun ba abinda tai masa ne ya bashi aushi ba bace kukan datake inda abinda ya tsana ve tsani yaga mace na kuka balle zahra da yakema son da bema kansa jin kukan yake har jikin ransa.
    *Zahra Yar'amana*
    *130-135*
    *Na F.A.Ya'u*
    
    
    
    Kasan Allah da matsala da'akai me yanxu daga gun mutuniyar nake anmanfa an kuma muktar yasa dariya danace ka tsaya me yasa kaki kaga ni inbaxakaban shawara ba to ka kyaleni kasan me xakai mami da abba zaka samu suyi mata magana inasu tace tana tsoro kaga kuma ka kawo shawara.
    
    Kamar kullum in angama cin abincin dare mami da abba sukan zauna sudan tattauna da sauran yaran gidan tara dedai yaran suka watse nasir yazauna yanata sosa geya yana satar kallon iyayen mami ce ta rafkoshi lpy kuwa naga kamar da mgn abakinka daman daman kaga inbaxa fadaba kabar gunnan yadan murmusa daman papa kan zahra ne me kuma tayi bakomi daman inasan auranta ne na mata mgn taki amincewa mami tai dariya aini nasan arina kinga maganarki ta xama gaskiya kaje xansa ummanku ta mata mgn ya sunkuyar da kai Allah ya kara girma suka ce amin.
    Mami da kanta ta samu zahra take mata maganar bata nuna taurin kaiba ta amince ko bakomi su mami sunfi karfin komi agunta balle auren dansu.
    Tun zahra na zuzzuk'ema Nasir harta saki jiki dashi suke kwasar soyayyarsu tun tanajin kunyar mami da papa harta sake dan su nunawa ma suke basusan tanaiba ba'awa i jada nisaba akasa ranar auransu wata uku sakamakon wata hudu masu zuwa Nasir zai tafi German dan karo karatu papa yace da matarsa zai tafi murna gunsa ba'a mgn.
    
    Yau sauran wata daya bikinsu zahra angama komi lokaci kawai ake jira kamar ko yaushe bata fasa zuwa makaranta ba tana bayi tana wanka mami ta shigo tana kiranta kixo hajiya falmata taxo zata miki kwatancen gidanta tunda akasa ranar aurennan mami bata gaji da kaita ko samo masu gyaraba kamar ance kalli gefe taga alamar takarda karkashin filo harta juya xata fita saitaji tanasan ganin ko mainene tana dagawa hotunane fuda biyu takalli budurwar jiki suna yanayi da zahra saidai ita Fara ce tas yayin da zahra baka ce ta duba dayan waxata gani matashiyarce da papa wato babansu Nasir dasauri tai waje sai dakin papa kira take kwala masa dasauri ya fito lpy kike kirana haka duba ka gani yakarba hannu na rawa nine ai Dina ce wannan ai matata danake fada miki ina kika samo wannan kaini gunta dan Allah agun zahra naganshi baijirata ba yai saman yaran tana shafa mai yasameta ya mika mata wace wannan takarva umma tace ummarki ni mama tace zahra ke yatace yatace zahara ya juya ga mami hadiza yau ga yata alhamdulillah yayin da tuni zahra ta sume tun lokacin da yace 'yata ce ke mami tai kaitanta shima ya.


  *Zahra Yar'amana*
*140-145*
*F.A.Ya'u*




Wai dagaske kike ko da wasa wallahi nanne gidansu yah zaem da nake fada maka bayan yah muhd banda kamarsa ya hade rai baya na daiko tai dariya nasan u can sacrifice for him ina yarinya i can sacrifice for many thing banda ke anman u are my life sai daishi ya hakura tasa dariya ahhh lallai kasan dai vaxa'amun auran dole ba shi zan zaba wallahi baki isa ba wallahi harnai yawa ta hade rai kamar gaske au haka kika ce eh din to wallahi zan baki mamaki sai gani tai yana kokarin juya mota ina kuma zaka zan koma kaduna in andaura mn aure ma dawo tasa dariya tana bashi hakuri haba kasan da wasa nake kayi hakuri da wasa nake sannan yajuya suka shiga gidan.

     Har suka fito daga mota suka shiga gidan zahra na cike da mamakin anya nanne gidansu ummana tasan kowa na gidan koda wasa bata tabajin sa'adda wani ya furta sunada diya dina ba akoda yaushe in inna na mgn sai dai tace yayanta shida duk maza kenan indai in gidan su ne har yanxu fishi suke da ita.inko haka ne kuwa zatai komi su yafe mata.

     Zahra bata kara tsinkewa da mamaki ba saida taga suna shiga inna ta gane papa cikin rawar murya take fadin islam kaine ko mafarki nake malan malan take kwala kira shima yana fitowa ya ganeshi dan bai mancewa da wannan fuskar fuskar data rabashi da diyarsa daya ke so dasauri ya rukushi ina Dina cikin hawaye papa yace malan mu zauna inyaso kaji komi.

     Tunda ya fara bada labarin inna ke kuka sai asannan ta kalli yan matan da suka shigo tare ina jikan tawa sai asannan taga zahra ta mike daniyar zuwa gun zahran itama ta taso suka rungume juna suna kuka ashe jinin muce shiyasa muke santa ashe jinin diyarmu ce tilo da muke so sauran yan uwa duk duk sun iso suna masu farin cikin ganin jinin dina saidai suna masu alhinin rashin yar uwarsu.
     Cikin kuka zahra ke nemawa ummanta gafara sukace ai tuni suka yafe mata rashin ganin hotunanta hakan ya farune sakamakon in malan ya gani saidai yaita kuka yana damuwa ganin haka yasa aka boye su dan rage masa damuwa.

     Nasir na zaune yana jiran fitowar zahra ta fito sanye da doguwar riga Golding ta nada mayafin rigar duda ba wata kwalliya tai va tai kyau sosai inbanda baka ce da sai ace bala rabiyya ce musanman a idanun masoyinta sallama yakeson suyi da yake kakanninta sunce su anan zata zauba bikinma anan za'ayi tunda ta fito yake kallonta sai taji duk kunya ta rufeta tunda ta gaisheshi ta kasa cewa komi jitake kamar ta koma ciki.
    Zahra yace yadda ya ambaci sunan yasata saurin dagowa sukai sa'ar hada ido yasakar mata murmushin dake narkar mata da zuciya murmushin dake kara mata sansa na fuskanci ni kadai nake budirina kan soyayyar mu kodai fasa auran xa'ai tai saurin dagowa me kace nasan kinji sabida me kace haka sabida na fuskanci da cutar wa kullum saina rokeki kice kina sona anman koda wasa kinkasa ko sau daya fadamin yai dariya ai kaidinne ba sanka nake ba kai kuma ka kasa fuskantar haka jira nake kace zahra kice kina kaunata sai ince Dr. Na ina sanka ina kaunarka zan kaunace har bayan rai Dr. Na kasa aranka zahra me kaunarka ce zahra taka ce tace baka jiba ya dago ina kaunarka tai ciki da gudu ya rungume hannunsa ak'irginsa dadi na ratsashi yai murmushi ahankula yace zahra nima ina kaunarki jiyake kamar ya jawo auransu adaura yanxu zahra kenan sarkin kunya zanso ganin ranar da zakice kina sona ba hanyar guduwa inga yaxakiyi da kunya.
    Yau su nasir sukaxo dan zuwa gidan baban zahra me rasuwa yau cikin farin ciki take dan tana dokin ganin su duda tana tunawa da maganganun umma zahra ki daure ki mance damu sai dai batajin zata iya mantawa da iyalin babanta wanda yasota alokacin da kowa ya kita taya zata mance da ahlinsa kosu sun k'ita sunyi sa'a duk suna gida dan ummance ba lpy duda halin datake ciki besa ta gane zahran ba zahra naganin halin datake ciki hankalinta ya tashi sai fada take me yasa vasu kaita asibiti nan ta kamata sai asibiti.....



*Zahra Yar'amana*
*145-150*
*Na F.A.Ya'u*

_Wannan paging nakine_ *Rasheedat Isa Mrs Idris* kinfi _kowa san Zahra yar'amana ina alfahari dake cikin Fans dina_




Koda umma ta warke kuka ta dinga yi kan tayi hakuri ta auri muhd kan zahra tace wani abu nasir ya rigata ai nine mijinta sati me kamawa za'a daura auranmu umma tasake fashewa da kuka ada ta hana zahra aure dan karta je inda zata huta sai gashi tasamu fiye da wadancan inkyaune akwaishi in kudine yanadashi in illimine yanadashi ahankula tace wannan izinace babu wanda ya isa ya hana abinda Allah ya baka.

     Tun zuwansu zahra gidansu muhd Fadima da muhd suka kulla soyayya tun tana zuzzukewa harta ware kankace me mgn taje gun manya.

   Zahra ta ziyarci kawayenta su zafira ansha hira kuwa sunyi murna sosai anan ta basu katin dan su gayyato former mate dinsu ba buk nan Zakiyya ke fada mt itamafa sauran wata daya bikinta ita da muktar zafira tai shiru eyye wato harmun fara surukutar haba yarinya kema kinsan inzanji kunyar kowa vanda taki suka sa dariya ai dannaga sai kifini sanin komi tai dariya zafiran uncle zaem kenan.
     Iya kyau kam amarya da ango sunyi kyau faden kyansu ma bata lokacine da yake andaura aure wanda dubban jama'a suka shaida hakan yavasu damar ruko hannun juna ranar families day sunyi kyau ba karya yan bikin kansu sunyi kyau.
   Saida aka kwana biyar ana shagali kafin akai amarya gidan ta na wucin gadi kafin su wuce german.
     Rayuwa me dadi suka tsarama kansu momi yadda sukeso yake tafiya akullum kara kaunar junansu suke basasan abinda zai raba su aikima adole nasir ke futa.
      Wata daya da bikinsu akaina zakiyya da muktar zafira da zaem muhd da fadma shima nasu bikin kam ya kayatar .
    Ana gama biki suka tafi german inda Nasir zai karo karatu acan zahra itama tai karatunta fanni noma wato agronomy shekararsu biyu acan ta haifi yayanta maza duk biyun sukaci sunan babanta me rasuwa wato baban muhd dayan kuma baban nasir alokacin data haihu take ganin kamar nasir zai sauya saitaga shi kamar ma alokacin aka bude masa babin kaunarta .
    Shekararsu hudu da aure yayan zahra biyar sun saba da uban dan ita kullun tana sch be kuma yadda da daukan nany ba dan tunda ya gama nasa yakoma dan raino ko makaranta baya bari ta tafi dasu suna gunsa .
    Zahra na gama karatunta suka dawo gida Nigeria sunyi kyau sosai da yaransu kaikace turawane inba mgn sukai ba dan sun dage yaran sun iya hausa dan basa son yaran su taso bada yarensu ba koda suka dawo nasir be shawara da itaba ba ya sayi fili ya gina mata tamfatsetsen kanfani na sarrafa kayan noma sai budewa akaje yi da ita tai murna sosai ta gode masa kan kace me kanfanin ya shahara ba iya Nigeria ba harda sauran kasashe makofta.
    Yadda taga umma hankalinta ya tashi bata da lpy sosai muhd baya gari tunda yasamu lecturing a ABU yakoma kaduna sai lokaci lokaci yakanxo matan duk suna gidajensu  basu san jikin yai tsanani haka ba hankalinta atashe takaita Aminu kano nan sukace saidai india zahra tai komi kan futar umma waje .
    Zahra har niger naje ta dauko kakarta kawun babanta ya lalace ya zama abun tausayi shima ta tawo dashi dakyar tasamu ta shiryasu da babanta ta bashi jari.
    Har gida taje ta duba jafar suka yafi juna anan suka kulla xumunci har bikinsa taje ummansa tai ta neman gafararta tace ai vakomi.
    Koda umma ta dawo ta warke simul tai takuka tana kara neman afuwa ayau ta kuma yadda da karin maganar bahaushe dana kowane kahaifa bakasan me moraba gashi ita anhar mata zahra uwatta tarasu ita tana mora.
    Zahra zaune tana bin yaranta da kallo yan biyu na game mansur na rubutun haddarsa smally ta fado kanta tana dariya yayin da hafix ya biyo ta mamanmu kinganshi ko ta tareshi haba yarona nasanka da hakuri kaifa babbane mai tamaka itace ina wasa da tsuntsuna ta sakeshi ya gudu wallahi mamarmu bansaniba ya gudu to kaji bata sani ba ayi hakuri zan siyo ma wani yasa ihuuu yawwa mamana shiyasa nake sanki waima mamanka mamanmu dai ke kuma wayasa dake mamanmu kinga yanaimun rashin kunya ko kul yayarka ce vata hakuri sorry sis ya wuce tace mamanmu bakice sagira ta ban hakuri ba bashi hakuri ta turo baki sorry bro yai dariya its a bygone issue ya wuce Nasir ya shigo rige da jaka ta mike ta katbo jakar ta cire ms takalmi da rigar sama tai ciki da lemo ta fto yakarba yana kara wash tace ansha aiki kedai vari wanka ko ci duk wanda kika ce girmanki ne ai to shikenan wankan ai saimuje ko ta dangabe kai baka ganin da yara ya kwaikwayi maganarta to ainima yaron ne kayi hakuri kaje pls kiyi hakuri mu tafi tare pls tasan halinsa dan haka ta dago shi muje ko sukai dakinsa tana shiga ta fito da gudu tana dariya ya kada kai shima yana dariyar yai bayi.
    
    Wai in tambayeki yn cin abincin yn mgn mai kika zubama abincinnan naji yana zaki zaki aff mantawa kai daci daci yake ohh haka nefa me kika xuba masa maganin mallaka inaso kaxama mijin tace yai dariya yarinya kin makaro aini kan tace ne Allah ko kina mamaki ne ya kurbi lemon lalala yanaji zafi kamanta tafasa yake suka saka dariya baki daya.
    Yana zaune yana kallonta tana shafa mai ya mike yana tayata shafawa sukajiyo kukan sagira ya lakace mata man a hanci ya fice yana fita ta fada jikinsa tana kuka dakyar yasamu tai shiru mene ba yaya ce ta dokeni ba to muje haba yaya me ya hadaku ba itace na aiketa taki xuwaba haba sagira kidena kiwa ke kuma banda duka ya kwantar da ita kan gadonta yaja musu vargo ya musu addu'a yawwa yan yarana sai da safe zahra ta turo eyye yaranka ma ko to sarkin kishi yaranmu.
    
    Dakin yan mazan suka wuce sagir na game sulaiman yai bacci hafix rubutu nasir ya kwace rumote din game din zahra ta rufe littafin naxa akwanta dare yayi suka lullubesu suka rufo musu kofa sikai waje.
    
    Rayuwa kenan wataran tasaka dariya wataran tasaka kuka wai yauni zahra nake dariya nakejin dadi nakeda miji da yarana masu sona masu burin faranta mun Allah kabarni da iyalina ta vaya taji ya rungumota Amin maman sagir tana dariya ta daga kai ta kalleshi yadaga mata gira batasan afili take mgn ba ahankula ta kuma cewa Alhamdulillah.
    Nima anan nake cewa Tammat billah daya bani ikon kammala wannan labari lpy.
    *Godiya*
    Gaduk wani ko wata da yabada time dinsa ya karanta wannan labari fatan duk kuskuren dake ciki za'amin afuwa dan adan ajixine nayi labarinne dan ilmantarwa nishadan tarwa bawai dan cin zarafin kowa ba wanda yaga wani abu da yashafeshi akasine bawai danshi naima kirkirarrene ba labarin wata ko wani bane.
    *Abin lura*
    
    _Komi na duniya dan hakuri ne ba'a taba dawwama cikin yanayi daya_
    _Dana kowane kishi kan yaya ba namu bane mata dan bake kika haifa ba bai kamata ki dinga azabtarwa ba bakisan wane anfani zai miki agaba_
    _Abin da Allah ya baka ba wanda ya isa ya kwace koda zai hado duk duniya_
    
    *Taki Dabance*
    *Salma Ali Wada*
    _Loves u fans badan kuba da tuni nadena rubutu karfamin guwa dakuke kullum yasa nake kara dagewa dan kara saku cikin farin ciki_
adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *