Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, August 21, 2019

Alqawarin da ciwo complete (Duniyar hausa novel)

adsense here
Alqawarin da ciwo complete (Duniyar hausa novel)

[03/11 1:51 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da ciwo 1•••
????????????????????????????????

Asalin iyaye na mutanen katagum ne ta jahar bauchi. Gidanmu babban gidane a garin katagum,kuma ALLAH ya albarkaci daukakain zuri'armu da arziki dai dai misali,sakamakon muhimmaci da iyayenmu suka dora akan harkan noma. idan ka shiga gidanmu, zaka iske sassa guda ukku, na farko na wan mahaifina ne baba sada da matansa biyu da 'ya'yansa,sai mahaifiyarsu babanmu itama anan sassan take. Kana matsawa sassan kanin malam sada ne wanda maihaifina ke bi masa . Sai namu sasssan shine na karshe a gidan da mahaifinmu malam habibu da mahaifitarmu inna amina, ita kadaice gun mahaifinmu da 'ya'yansu biyar duk hudun maza ne sai ni kadaice tilon mace a tsakiyarsu. Ni sunana RAHMA amma yawancin "yan gidanmu sukan kirani da Ramatu amma sam babban yayanmu ya hana a kirani da sunana sai dai RAHMA don kuwa yace shine asalin sunana ko a cikin ALKUR'ani. Ranar da aka haifeni mahaifina ya shigo gidan ckn murna don kuwa lkncn da aka haihu yana gona sai wani daga ckn yayyena ya hau keke ya garzaya ya shaida masa. Bakin mahaifina bai iya rufuwa ba sai da yazo ya ganni. Ya dauke ni ya kura min ido tare da tofa min addu'o'i yana mai gdy ga ALLAh DA YA AZUrta shi da samuna sannan gashi na dauko kamannun mahaifiyata, ita asalinta bafaulatanar Ningi ce. Ana cikin murna ne sai ga babban yayanmu mai suna Aliyu ya shigo dakin cikin hanzarinsa bakinsa washe sbd murna,kasancewar duk gayyar 'ya'yan gidanmu babu diya mace sai yau akaina aka fara haifo mace. Mahaifina ya mikowa yaya Aliyu ni ina nade cikin zani , ya amshe ni ckn murna da bata misaltuwa, ya kura min ido na tsawan lokaci yana jinijina irin baiwar kyau da Allah ya bani. Har kusan awa guda ina rike hannun yaya ALIYU(Babansa shine babban wansu mahaifinmu baba sada kenan)
[03/11 1:51 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da ciwo 2•••
????????????????????????????????

Irin dumbin addu'oin da yaya aliyu ya tofa min a wannna lkn basu misaltuwa, mahaifina ya sake shigowa ya iskeni rungume bisa ikin yaya aliyu, ya dube shi yana murmushi yace'A'A alyu har yanzu kana nan gurun jinjira ne? lallai wannna diya ta iri tuta ta ko dai itace matar?" yayi dryr jin dadi ckn jin kunya aliyu yace "ni wlh baba kyan yrnyr nan har tsoro yake bani, da ace idan ta girma zata yadda da hadin aurenmu ai da sai ince utace natar kawai, don wlh ina sonta babal baba na yayi murmushin gamsuwa da maganar yaya aliyuya dube shi yace" ai shike nan aliyu in dai har kana son diyar nan wlh na dau alkawarin baka aurenta sai dai in kaine da kankakace ka fasa auren amma babu fashi in sha ALLLAHU" Aliyu yayi murmushi ya sake duba na yace'haba baba duk fa ckn zuri'armu ba a taba haifan wanda ya kama kafarta a kyau ba'baba yayi dry yace ' haka dai kake ganmi amma ai kuma kunyo gadon kyau kuna maza n shiyasa kake ganin haka to wanna shine asalin alkawarina ure na da yaya aliyu tun ranar da aka haifeniina ckn tsumma kenan. gsk na tashi cikin kulawa da shagwaba ta ko wane fanni gun uwa da uba kai da dukkan illahirin zuri'ar gidanmu babu ma kamar gun yaya Aliyu. Wai shi dole tattali na yake a matsayin matar da zai aura idan mun girma. Shi yaya Aliyu duk cikin dangin mu shine ya sami isashen ilimin zamani mai zurfi shima a dalilin wani makwabcinmu da ALLAHJ ya hada jinin dansa da yaya aliyu har zumunci mai karfi ya kullu tsakanin iyayenmu. Makwabcin namu Alhaji yakubu mutum ne mai arziki sai ya zama ya koma da shi garin bauchi sbd a lokacin sun kammala karatunsu na sakandire. Duk gidanmu dama su kanyi karatun firamare da na sakandire daga nan sai su kama kasuwanci. Nima ba a bar ni a baya ba na sami yin karatun firamare tare da kulawar Aliyu nake samun daukakar karatuna, don kuwa ya dauki son duniya ya dora a kaina duk zuwan da zaiyi daga bauchi in da yake karatu sai ya siyo min abin da yasan inaso ko kuma wanda zai sani farin ciki. haka kuma baya komawa sai ya tabbatar ya koya min wani abuna daga karatun islamiyyah da boko.
[03/11 1:51 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da ciwo 4••• ????????????????????????????????

Dakin mahifiyarsa muka wuce kuma har a wannan lokacin aliyu rike yake da hannuna muna shiga ta kalle mu tayi murmushi,tace " har kun gama gaisawa da gwaggo" yace" eh, mun gaisa kin san nace maki yanzu bauchi zanje ina son gobe in dawo nan jibi sai in koma lagos" nayi karaf nace" wlh yaya nima zan bika bauchin" ya dubeni yace " kinga yamma tayi bari idan zan sake zuwa sai inje da ke" na make kafada nace " wlh yau na ke so" ganin na bata fuska na soma masa kuka sai yace" come on, meye abin kuka? shikenan je ki shirya kizo mu tafi" innarsu tace " ai dama kai ke bata rahaama gidan nan dole in tace sai tayi abu babu yadda za'ayi ta hanu, yanzu in aka yi auren haka zaka ci gaba da sangartata sai abinda take so za'ayi?yayi murmushi yace, " to ya zanyi inna? kin dai san rahama yarinyace dole in dinga bin lamuranta a hankali kinga yanzu idan ina matsa mata sai ta tsane ni ko an tashi yin auren tace bata so na kinga anyi ba ayi ba kenan" inna ta tabe baki tace " yayi maku dai dai sai kuje kuyi ta kwamacalarku mudai muna nan yan kallone da bada shawara" yayi dariya yana kallona nima shi nake kallo yace "kije ki shirya mana ko ince na fasa zuwa dake" nayi tsalle cikin murna na fice da gudu zuwa dakin gwaggo don kuwaa nan komai nawa yake ku san ma itace ke rike da ni. ina cikin shiryawa ne ya biyo ni dakin gwaggo a lokacin na saka riga ina kokarin zage zip din" ya jawo ni gabansa inda yake zaune a gafen gado har yafara zagemin zip din sai ya fasa yace" gsky ki canza wasu kayan wadannan basu da guga, ina riga da wandon da na siyo maki a lagos"nace " suna nan ban ma taba sawa ba kunya nake ji a ganni da wando kamar namiji" yayi dariya yace "lallai rahama da sauranki to ki shirya idan muka yi aure riga da wando sune kayan sawanki ko anguwa zamu kuwa" na fiddo ido nace" haba yaya aliyu ai sai ayi min dariya duk in da muka shiga" yayi murmushin sa da ke birgeni yace"ai mu a lagos ba ruwan kowa da kowa, kowa harkar gabansa yake yi kinga sai muci karenmu ba babbaka ko? na rike baki abinka ga yarinta sai nace " yaya kare ake ci a lagos din? ya tintsire da dariya har hular kansa na faduwa ya dube ni yace " kai rahama ba dai yarinta da shirme ba. tunda baki gane nufi na ba shike nan a bar maganar maza jeki chanza kayan mu tafi yamma tana yi" da yake dakin gwoggo ciki daya ne kuma kaya na a dakin suke shi yasa dana dauki wanda zansa sai nayi hanyar fita zuwa wani dakin don in canza , sai aliyu ya rikoni ya na dariya yace " lallai rahama wato yanzu an soma girma ba za'a iya tubewa a gaba na ba ko?  yayi kyau da kika fahimci haka" cikin dariya nace" malamin islamiyyan mune fa yayi mana wa'azi yace babu kyau mu nuna tsiraicin mu ga kowa" yace " sai ga wa akace ku nuna? na sha mur nace " ni ban sani ba' yayi murmushi yace " to ai ya kamata ki tambayi malam din don kar insha wuyar fahimtar dake nan gaba" ya sake ni na fice ni ba komai yasa a lokacin na tsane tubewa a gaban mutane ba illa yan nonuwan da suka soma fitomin. amma shekara daya da ta wuce sam bana jin kunyagaban kowa tubewa nake hatta wanka a tsakar gida na kan yi abina tun innata na min fada har ta gaji, yaya aliyu ko da bulala yake ritsani har ya samu na daina.
????????????????

 Zaune nake gaban motar yaya aliyu akan hanyar mu ta zuwa garin bauchi sai shara gudu yake yi ni kuma sai zuba masa surutu nake yi yana kwasar dariya, ana sallar magariba muka iso gidan Alhaji yakubu inda suka rike yaya aliyu har sai da yasami aiki a lagos snnan ya bar gidan . Duk da yake ina karama suka bar garinmu katagum amma basu manta ni ba haka nima ban manta wasu daga ckn yaran gidan ba. haka suka shiga dawainiya da mu har sai da suka ga mun yi salla mun ci abincin dare sannan hankalinsu ya kwanta. ina zaune cikin yaran gidan a babban falonsu ne yaya alyu ya shigo shi da babban amininsa dan alhj yakubu kuma shine babban da a gidan. kabir ya dube ni yace"sannu rahama bakin bauchi" nayi dry ta na risina na gaida kabir yaya aliyu yace " gata nan yau ta makale mini dole sai ta biyo ni bauchi" suka yi dariya kabir yace "ah! to ai gara ta zama cingam din aliyu tun da ta san kaine mijin" aliyu ya dube shi yace " ki taso muje can gidan kabir sai ki kwana gurin madam din sa" ba'a son ranta ba na mike suma yaran gidan suka rikeni wai su sam kar in tafi sbd sabon da muka farayi da su dama gani bani da bakunta. yaya aliyu ya shiga lallashinsu da cewa " kuyi hakuri gobe da sassafe zan kawo maku ita sai ky yini tare kafin mu koma katagum da yamma " haka suka hakura suka kyale ni muka nufi gidan kabir, duk zaman da suke yi na hira a babban falon gidan kabir da matarsa sakina da yaya aliyu uffan ban iya cewa sbd hirar tasu ta manyace ni nama fi maida hankali na ga kallon da aka saka a falon. kabir da sakina watan su biyu kenan da aure shi yasa sam basu iya boye sirrin soyayyarsu gaban kowa duk yawancin hirar da suke yi na lura sakina sai wani mannewa take a jikin mijinta shi kuma yana yi yana shafar sumar kanta. tsananin haushinsu ya kama ni a raina nace " yau ga yan iska dama abinda suke yi kenan? kai ALLAH ya dai kyauta musu daga sun zama miji da mata kuma sai su kama halin yan iska ni kam ko anyi auren mu da yaya aliyu ba ruwa na da wannan iskanci". na cigaba da sake saken abinyi kawai sai na tsinci kaina da yingyan gyadin karya don dai in bar falon karin cigaba da kallon abin haushi. kabir ne ya fara lura da gyangyadin da nake yi gashi duk na wani takure cikin kujera tamkar mai jin sanyi. kasancewar kujerar 1 seater ce. ya ce "subhanallahi, aliyu mun bar diyar mutane na gyangyadi" ya dubi matarsa yace "sakina a ba karamar amaryanmu gurin kwana" ta mike cikin hanzari tace " duk na san gajiyar hanya ce ta so muje rahama" ni kam duk na kosa in bar falon don tsoro da haushi. cikin tsakar dare na tashi na nemi sakina a gadon na rasa kuma na san tare muk shiga bargo muka yi bacci to ko ina taje oho? sai da safe bayan nayi wanka ina shafa mai sannan ta shigo dakin sanye cikin rigar bacci ta dube ni tace"A'a rahama har kinyi wanka? na ce 'eh yanzu nayi tun cikin dare nake nemanki, ina kike ja? tayi murmushi tare da gyara maballin gaban rigarta ta ce"wlh daga zuwa kaiwa kabir kayan shayi shine bacci ya kwashe ni a dakin sai yanzu natashi" na yi shiru a raina ina cewa, " kya ji da shi kuna can kuna iskancin banzanku, ni na tsane ku yanzu zan bar maku gidanku" ta dube ni tace " bari inje inyi wanka nima' nace" to sai kin dawo" ba tare da na kalle ta ba. mun kasance a babban falon su. bisa dinning table muna yin kalaci cima iri-iri sakina ta shirya mana. muna kammalawa na mike na dubi aliyu nace " yaya aliyu ni dai mu tafi can gidansu ummasalma" (ummasalma kanwar kabir ce kusan sa'annin muke da ita) ya dubeni yace" amma kya bari nima in yi wanka ko? wai meke faruwa ne duk kin wani canza ko shagwabarce zata taso? na sha kunu abina yayi dry tare da mikewa ya nufi kewaye. hakika jama'ar bauchi sun karramamu,musamman iyalan alhj yakubu don kuwa da zamu tafi abin arziki iri iri suka bamu. sbd kaunar da suka nuna min sai naji kamar kar in tafi har kuka sai da mukayi ni da kannin kabir. jininmu ne kawai ya hadu da yaran gidan cikin kwana daya da yini daya da nayi tare da su. bamu isa katagum ba sai bayan sallar magriba kasancewar sai yamma mu ka barbauchi. washegari shikuma yaya aliyu ya koma gun aikinsa a lagos **** ***** ***** *****
[03/11 1:51 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da ciwo 3•••
????????????????????????????????
Tun ina yar shekara goma na iya karatu da rubutun hausa haka nan na turanci na kan iya karantwa ko in rubuta. Ina dada girma kyauna yana kara fitowa sutura sai wadda na zaba nake sanyawa kuma iri iri masu tsada shiyasa na fita daban da sauran kawayena,ko kudin scholarship yaya aliyu ya samu duk a kan hidima ta suke karewa. Ina yar shekara goma sha daya yaya aliyu ya kammala karatunsa na jami'a digiri guda biyu ya samu. Ba tare da wani bata lkc ba ya sami aiki a lagos kuma mukami mai girma ya samu. nan da nan ALLAH ya daukaki yaya aliyu ga mota sabuwar yayi ya saya sannan ya gyarawa iyayenmu gidan da muke zaune komai dai yaji a gidanmu. a wannan lokacin da daukakar yaya aliyu tayi kamari shekaru na sha biyu amma zaka dauka na kai sha biyar sbd girman jiki. shi kam maihaifina har ya fara shakku akan al'amarin aurenmu da aliyu sbd yadda yaga yanayin da aliyun ya shga na azurcewani kuma gani ba wani girma nayi ba duk da yake a cewar baba ba zan wuce shekaru sha biyar ba za'ayi aurenmu da yaya aliyu, akwai wani zuwa da aliyu yayi daga lagos lokacin ina zaune a sassan mahaifan aliyu a dakin kakarmu ina ninke mata kayan sawanta kawai sai ganin mu2um nayi yayi sallama ya shigo ckn dakn. sanye yake cikin lallausan bakin boyel sai kyalli yake yi, habawa ban san lkcn da nayi wurgi da kayan dake hannuna ba nayi tsalle na rungume shi tare da fadin "lah! yaya aliyu oyoyo". shima cak ya daga ni sama ya rungume sannan ya sauke ni kasa muna kyalkyala dry ya dubeni fuskarsa cike da fara'a yace,"rahama naji kin kara nauyi ne me su inna suke baki ne idan bana nan?" nayi dry nace,"Allah yaya aliyu duk kayan dadin da kake kawo min ne daga lagos suke sani yin kiba", yayi murmushi yace,"zo mu zauna ki gani ga wasu na siyo miki" muka zauna bisa gadon gwaggo(kakarmu kenan), ya dubeni yace"ina gwaggo ne? nace, "tana bayi yanzu ta shiga" yace" ok, ai na aza ta tafi anguwa ne' ya fiddo min da kwalayen biskit zuwa su chakulet da wasu irin gwangwanaye na biskit wasu na sansu ya saba siyomin irinsu wasu kuwa ma ban taba ganinsu ba, ya bude biskit din kwali yace," bude bakinki kiji irin wannan akwai dadi", ba bude bakin ya bani na gutsura ina ci tare da gyada kai alamun yana da dadi ko?" na gyada kai nace, "wlh very sweet". yayi dry tare da ja mini labba yace,"uhm rahaman kwadayi", muka saka dry. nima na dauko biskit guda daya nace," nima yaya aliyu bude bakin ka in baka",ya kuwa bude bakin na bashi muka yi ta dry. ya sauko cakulet yana saka min a baki kenan gwaggo tayi slm ta shigo. hannunsa na bisa baki na muka tsayamuna kallon gwaggo, ta duni aliyu tace," yauwa ka dawo har ka fara sangarta ta ko? sai ka tafi ka barmu da jijalin shagwaba, ka riga ka shagwaba ta da bata abinci a baki shi yasa idan ka tafi take zama da yunwa" ya fiddo ido cikn mamaki yace "ashe zama da yunwa kike yi rahama? to daga yau na daina baki abinci a baki" gwaggo tace"ah! to ku dai kuka sani yrnya 2un tana karama ka koya mata dabi'un turawa ai in agama an kusa ayi aurenku mu huta ku tafi can ku karata". ya ware ido cike da mamaki yace " wana irin aure gwaggo? shekarun rahama fa sha biyu ko kin manta ne? haba ai ko za'ayi aurenmu sai ta kai shekaru sha bakwai zuwa sha takwas". gwaggo tace" ba dai a gidan nan bane za mu bar rahama ta kai shekaru sha akwai tsanani sha biyar, to ba ga sa'anninta ba nan duk an yi musu baiko wasu ma har an sa musu rana" yayi ajiyar zcy a ransa yana tunanin ALLah dai ya taimake shi su bar rahama ta dad girma kafin ayi auren su. tabbasa yasan rahama yake so har kn ransa to amma aurensu ba yanzu ba duk da yake ko sun yi aure ba zama zata yi ba cogaban karatunta na sakandire zata yi har zuwa jami'a maganar haihuwa ma in sunyi aure in sha ALLAHu BABU ITA SAI AN KAMMALA KARATU. GWAGGO TA KATSE MASA TUNANI da cewa, "ali ko dai ka canza ra'ayin aurenka akan rahama ne? naga daga yin maganar auren ka canza fuska kwata kwata" yayi ajiyar zuciya yace " wlh ban canza ra'ayina game da aurenta ba, ai ko don in faranta maku rai zan yarda in auri rahama balle ma har ckn raina ita nake so" gwaggo ta saki wani murmushin jin dadi dangane da maganar yaya aliyu tace, " to Allah ya nufe mu da ganin lokacin auren" yace "amin ba wai na dauke shi da muhimmanci bane, illa dai kawai na kanji dangi nace min matar aliyu nima haka na dauka wani lokacin har baba aliyu na kance masa amma sai inji yace kar in kara kiransa baba sai dai yaya.bayan sun gaisa da gwaggo suka dan taba hira ya kawo irin turarrurrukan da ya kan siyo mata a lagos masu kamshi da tsada ya bata sannan ya riko hannuna muka baro dakinta tana ta shi masa albarka.
[03/11 1:51 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da Ciwo 5••• Aliyu ke zaune a babban falon gidansa dake birnin lagos, wanka yafito a wannan lokacin da agogo ya nuna karfe biyar na yamma. sanye cikin jallabiya farasal sai dan karamin stool da ke gabansa wanda ke dauke da tiren kayan marmari, ya dauki wani koren apple ya gutsura tare da cigaba da kallon tauraron dan adam din da ya kunna, kararrawar falonsa da yaji ana dannawa shi yasa ya rage sautin talabijn din ya mike yaje ya bude kofar. babban aminisa ya iske a kofar wato sagir gurin aikinsu daya a nan hannu suka tafa tare da dry, suka karaso cikin falon, sagir na cewa " ban yi expecting zan same ka ba na dauka yauma tafiyar dare zaka yo" ya ce " kai last two weeks da nayi tafiyar dare ban ji dadi ba shi yasa nayo asubanci ko 20 mins ban yi da isowa ba" sagir yace" you are welcum" ya ce" 10q" suka zauna aliyu ya turawa sagir tiren kayan marmarin nan gabansa sannan ya nufi firij ya kawo masa maltina da ruwan sanyi. sagir "ai tun kafin in fara da komai bari in isar maka da sakon mutuniyar taka tun da ka tafi ta hana ni sukuni" ya ce" hala taiba don na san ba mai nemana garin nan sai ita" yace " kai ma aikasani cewa tayi mun inzo inyi checking ko ka dawo in yi mata waya yanzu zata zo sannu da zuwa" aliyu ya kurbi ruwa ya aje tambulan din yace" don ALLAH sagir share ta kawai gobe ma hadu ofis don wlh yanzu a gajiye nake ban son tazo tadame ni da surutu" sagir yace" ni kuma gashi zuwa nayi ka rakani gurin mutuniyar kasan har mutanen zariya sun zo ran friday bayan tafiyarka sun kawo sadaki da komai da komai har sun tsaida ranar biki 1 mnth aka sa shine nake so muje da kai ayi arrangin abubuwan" aliyu yace "ashe kayi (serious) akan auren nan? to Allah ya sanya alheri" ya ce"amin" ba su bata lkc ba suka nufi gidansu safiya. asalinta haifaffiyar kano ce aiki ya kawo iyayenta lagos yawancin rayuwarta duk a nan lagos din ta yi ta. washe gari a ofis duk wata hanya da aliyu zai bi ya kaucewa gainin taiba yayi hatta ofis din da ya gargadi masinjansa kada ya bar kowa ya shiga. ba komai yasa aliyu ya tsani haduwarsu da taiba ba illa azalzala masa da take yi da maganar ya aureta shi kuma ya san abu ne mara yiwuwa na farko alkawarin aurensu da rahama abu na biyu kuma sam iyayensa ba zasu amince masa ya auri bayarabiya ba dk da yake itama musulmace to amma da kamar wuya wai gurguwa da auren nesa. yana dawowa gida wanka da sallar la"asar kawai yayi sai ga taiba a gidansa. ya bude mata kofar falonsa tana shigowa ta rungume shi tace ' haba (darling u came back since yesterday) amma sai zilliya kake min a ofis yau, to gani ba biyo ka ko sannu da zuwan nawa ne baka so? ya dan yi gajeren murmushi da bai kai zuci ba sannnan yasa hannu ya banbare taiba daga jikinsa yace" no! ba haka nake nufi ba kinsan yau monday akwai ayyuka masu yawa a ofis dina dole in ga sun kammalu shi yasa tunda kinzo shikenan ko?" ta isa kan kujera 2 seater ta zauna a maimakon ya zauna a kusa da ita kamar yadda ya saba zama a'a sai ya nemi kujerar gefenta ya zauna sannan suka gaisa. Ta tashi da kanta ta nufi firij dinsa dake falo ta bude ta zabo mango juice ta dawo ta zauna tana shan juice tana masa hira amma shi sam hankalin shi baya tare da ita illa ma wasu takardu da yafi maida hankalinsa a kansu yana sa hannu.Ta dube shi tace,"Aliyu yaya su inna a bauchi duk suna lfy? ya amsa mata,suna nan kalau suna gaisheki shi kanshi sai da ya dan murmushi saboda karyar daya shirgawa Taiba yanzu na cewa su inna na gaisheta. Shi koda wasa bai taba furta musu yana neman wata Taiba ba balle susan da zamanta. Murna ce ta bayyana a fuskar Taiba saboda taji surikanta suna gaisheta. Tace, ina amsawa,wai darlin yaushe zaka kaini in gaidasu ne? Gaskiya ya kamata in sansu suma su sanni. Yayi ajiyar zuciya yace, zuwan ki ba zai yiwu ba yanzu ba tunda ba wata kwakkwarar maganar aure tsakaninmu, amma ki bari nan gaba zasu sanki idan kin zama surikar su. Dadi ya lullube ta saboda jin maganar aure yau a bakin Aliyu. Haka dai ta cigaba da damunsa da surutai akan maganar aurensu sai da aka kira sallar magriba sannan tayi niyyar tafiya saboda ganin yayi wo alwala zai fita salla masallaci sannan suka fita tare.

????????????????

 Duk bayan sati biyu Aliyu ya kan ziyarci mahaifarsa katagum ko yayi kamar ba zai je ba idan ya tuna Rahamarsa da irin shirmenta na yarinta sai kawai yaji ita yakeson gani. Ko yabi jirgi in yamma tayi in kuma ba yamma sai ya tafi a motarsa. Yauma kaman kullum ranar jumaa da hantsi yayi sallama da ofis ya nufi katagum. Karfe takwas na dare ya iso gida dakin Gwoggo ya fara isa saboda duk ya leka dakunan su innarsa bai gansu ba ya iske gwoggo tana jan casbaha ta idar da sallar isha kenan. Yayi sallama ta juyo ta dubeshi tare da amsa sallamar tana cewa, "Ah,ah mutanen ikko barka da sauka. Yace yauwa Gwoggo kuna lfy? Tace Lafiya kalau, zauna mana yace, Ba zama zanyi ba inason in shiga masallaci inyi salla ne, na leka dakinsu inna duk ba sunan lafiya ko? Gwoggo ta sauke mayafin dake kanta zuwa kafada tace, Wlh Ali gidan ba lafiya ina jin duk suna sasan Habibu, kasan Amina ba lfy to wlh jikin yaki dadi. Ya fiddo ido yace,"subhanallah, meke damunta? Anje asibiti kuwa? Duk haka ya jerowa gwoggo wadannan tanbayoyin guda biyu tace, To gashinan dai ciki ne gareta tana shan wahalarsa shine jiya jini kuma ya tsinke yana ta zuba muna kyautata zaton bari ne to rashin ganin gudan cikin ya fito shi yake samu kokwanto dama gobe ake shirin zuwa asibitin idan jinin bai tsaya ba, Duk Aliyu yabi ya firgice ya dubi gwoggo yace, bari inyo sallah sai mu tafi asibiti yanzu, yaushe ne zaa zauna da mutum a gida yana zubda jini, ya fice cikin sauri ya nufi masallaci. Kafin ya dawo gwoggo ta shiga sasanmu take sanar da mu zuwan Aliyu. Jin haka yasa naji dadi a raina nasan mai lallashi na yazo don kuwa tunda inna ta fara ciwo na sukurkuce sai aikin kuka saboda nayi mugun shakuwa da inna ta.Yana shigowa dakin innata na isa jikinsa da sauri na kwakume shi ina kuka ya rungume ni yana lallashi, shima yaya Aliyu idonsa ya kada yayi ja saboda irin yanayin ciwon da ya gani na innata. ko zama bai yiba yace su fito da ita a tafi asibiti a lokacin duk iyayan mu maza suna nan sukace ya bari sai gobe tunda dare yayi sannan shi kuma gashi tattare da gajiyar tafiya yace shi sam bai amince ba dole suka hakura da tashi shawarar aka nufi babban asibitin Bauchi da ita a wannan daren. Naso in bisu don har Yaya Aliyu ya saka ni a motar amma babana yace sam bai dace aje dani ba, haka na hakura na shige gida da gudu ina aikin kuka ganin haka yasa Aliyu ya biyo ni ya lallasheni sannan yaja motar suka tafi, washe gari ranar asabar itace ranar da bazan taba mantawa da ita ba a tarihin rayuwata. Ranar bakin ciki, ranar kuka, ita ce ranar da na gwammace in koma ga mahaliccina. Ina zaune a dakin innarmu bayan na gama share dakin na goge leda ko ina na tsaftace shi sai na yi wanka na shirya tsaf abina ina jiran dawowar su yaya aliyu daga bauchi don in sake binsu zuwa ganin innata a asibiti domin tun da suka tafi jiya basu dawo ba illa baba sada ne kawai ya dawo da safe ya shaida mana an kwantar da ita. Ashe bayan tahowarsa bai fi da awa daya ba ALLAh ya amshi ran mahaifiyata. Ni dai ina zaune a dakin sai naji hayaniya a tsakar gidan mu ina shirin fita inga ko menene sai na ci karo da yaya aliyu ya kutso kai ckn dakin idonsa yayi jawur tabbas kuka yayi inna ta lullube cikin zani aka shige da ita uwar daki. duk da yake bani da wasu shekaru masu yawa amma hakan bai hana ni fuskantar inda aka sa gaba ba. Tabbas inna rasuwa ta yi haka naji zcyta tana gaya min. na dubi aliyu a firgice na ce "ya aliyu mene ne sam yaki yarda mu hada ido illa kawai ce min yayi" sun sallameta ne? nace " ta mutu ko? tambaya ta ta tsorata yaya aliyu sai yace ' waya gaya miki? karya ne' mahaifi na najiyo daga ckn daki suna maganar likkafani habawa sai na kankame aliyu ina gunjin kuka nace ' haba yaya aliyu gashi nan ance ta mutu kana cewa karya ne, wayyo ALLah na yau na shiga uku! ban kuma sanin in da kaina yake ba sai da yamma lis bayan an kai inna kushewar ta. ganin nayi kwance bisa cinyar yaya aliyu yana tofa min addu"o"i yana ganin na bude ido yayi ajiyar zcy yace,"sannu ko rahama,yanzu me ke damunki? na bude baki na da kyar nace " yaya aliyu ina inna ta ke? ya dan yi jim tamkar ba zai yi mgn ba har sai da na sake maimaita tambayata sannan yace " tana daki" to kai ni in ganta, taji sauki? abin da nace kenan ido na kyar kansa yayi saurin cewa " an maida ta asibiti' na tashi daga jikinsa na zauna nace " gashi na hango m2ne cike da gida sannan zakace inna bata mutu ba? ni wlh na san ta mutu boye min kake" sai hawaye ke zuba min shar shar ya kwantar dani a kirjinsa yana share min hawaye tare da aikin lallashi na. tabbas sai anan ne na dada sakankancewa inna ta rasu ina tausayin kai na sai dai nafi tausayawa " yan kanni na guda biyu. mutuwa kenan mai raba da da mahaifi ta raba masoyi da masoyi 'kwana biyu da rasuwr inna duk na fita hayyaci na snd mugun sabo da shakuwar da muka yi da inna shiyasa ake cewa ba mutuwa akewa kuka ba sai sabo shi dama turken wawa ne. na kode na jeme sbd rashin cin abinci ina zaune a takure can sakon gadon gwaggo sai ga yaya aliyu ya leko dakin daga ni sai gwoggo ne a dakin ya isa inda nake a takure ya gurfana gabana yana duba na yace" rahama kin ci abinci? na gyada kai alamar eh ya dubi gwaggo yace wai taci abnci gwaggo? ta girgiza kai tana duba na tace ' sam bata ci komai ba ina ga tun kokon safe shima kadan ta sha gashi yanzu ana neman karfe ukun rana' ya kada kai ckn damuwa yace ' in akwai abinci bani yanzu zata ci shi' gwaggo ta miko masa shnkafa da miya ckn langa tace " kila da yake kai ne ta ci amma ni nayi lallashin duniya taki ci har fushi nayi don taci abinci amma a banza" ya amshi abnci tare da ckli ya zauna gaba na ya soma bani abincin da kyar nake ci sai ina jin abincin har wani daci yake min a baki, sai da yaga na koshi sannan ya kyale ni. ya je dakin sa ya kawo min katuwar gora ta (five alive) da babban gwangwani na biskit yace idan na kasa cin abinci sai in dinga ci. yadda kasan ban rasa mahaifiya ba haka na koma a gidanmu, kowa ka gani lele na yake babu ma kamar gwaggo da ta shiga sangarta ni tamkar ni kadaice jikarta. sai abn da naga dama nake yi a gidan nan sam bata son taga an takura ni yanzu ta hau fadan ni marainiyace, shi yasa ma riko na kacokan ya koma hannunta. kakanni na na gurun uwa sun so kwarai su tafi dani can gurinsu a ningi in zauna amma fafur gwaggo ta kiya, hakama kanwar mahaifiya ta da take aure a garin bauchi ta so a bata ni kasancewar itama 'ya'yanta duk maza ne amma sai bata sami nasarar dauka ta ba gwaggo ta hana kowa. A wannan lkcn shekaruna sha uku daidai yadda na taso da kiba yanzu duk sai na rairaiye na zama yar siyat sai kyau da na kara wai nice har samari ke kawo min daukin neman aure gun babana amma ya kan basu hakuri yace ya riga yayi min miji yaya aliyu. Duk wanda yaji ance zan auri yaya aliyu mamaki yake yi sbd haduwa irinta yaya aliyu ga ilimi ga tsafta ga kyau ga kwarjini wasu har abin dry abin yake basu wai babban ma'aikaci kamar aliyu ne zai auri yar ficikar yarinya kamata kai lallai yaudarar iyayen mu kawai yake yi in ma auren alkawari ne to sun cuceni don kuwa nan gaba kara aure zai yi ni ko in wulakanta basu san shine alin bane da kansa ya furta yana sona tun cikin tsumma kuma har yanzu wannan kalmar ta so tsakanina da aliyu bata gushe ba a zuciyarsa nima kuma raina ya na son dan yayan nawa ko don sbd yadda yake tattali da riritani ako da yaushe.
[03/11 1:51 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da Ciwo 6•••
????????????????????????????????

 Yau juma'a na yo kwalliya ckn leshi da yaya aliyu yayi min da salla, bkn wata kawata hanne ake yi har an kai ta gidan miji yau ne ake mata jere nima sauri nake in tafi duk da na san yaya aliyu na bisa hanya. ina fitowa soron gidanmu muka yi aringizo da shi zai shigo hannun sa rik da yar jakarsa yayyane ke biye da shi da kaya niki niki bauhunna abin masarufi ne rinsu suga,. omo , shinkafa, katan katan na taliya kai tarkace dai irin wadda ya saba kawowa iya yenmu daag lagos, ya dubeni ckn shai'awa yace " a 'a yar matasa ina zuwa? ko kwalliyar juma'an tar abn mai gida ne? to ga ni na iso" muka tintsire da dry ban sami gaya masa inda zani ba sai na amshi yar jakarsa muka dawo ckn gida yana rike da hannuna. ya isa dakin gwaggonmu ya wuce aka shiga jero masa kayan abinci fankasau kawai naga ya cini ka mina zaune a gefa ina kallonsa har ya kare sannan ya dubeni yace " wai ina zaki na naga har da yafa mayafi? na gaya masa inda zani ya rike baki ckn al"ajabi yana duban gwaggo yace " yanzu gwaggo da gske an yiwa hanne kawarta aure? tace " kwarai kuwa shine abin mamaki? yace" haba gwaggo wai me yasa har yanzu kun kasa gane illar da auren wuri ke jawowa, ki duba kiga fa kawarsu jummai da akai mata auren wuri inace gunrin haihuwa ta zama yar yoyon fitsari sbd bata isa haihuwa ba wannan ma kadai ai ya ishi iyaye ishara su dinga barin "ya" ya suna kaiwa shekaru sha takwas shine munzalin aure yanzu don Allah ina ranar jummai anan an cuceta an cuci rayuwarta gashi naji ance babu rai ya zo sbd wahala, haba don Allah"GWoggo ta numfasa ta ce " a gaisheka bature koko ince likita bokon turai.wannnan irin sharhi? to mu wannan shine gata ga ya'yanmu ba gara muyi masu aure ba da suje su dauko mana abin gori" ya ce " ni ina gani duk wannan ya danganta ga irin tarbiyya da iyaye suka ba yaro ne ko kuma sakaci daga garesu,amma babu wani maganar dauko abin gori, kuma yawanci iyayen mu mata ai su sukejanyowa kansu abin gori sbd dorwa 'ya'ya mata talla a madadin zuwa makaranta kinga kuwa dole yara su lalace can gurin yawon tallace-tallace. ni kam ina gdy ga Allah da yasa mu ana gidan baku da wannan dabi'ar ta dorawa yara talla abu daya ke damuna yanzu game da karatun rahama ina son ku kyale ni in nema mata makarantar gaba da firamare ta kwana a garin bauchi tunda ta kammala firamare" gwaggo ta kwabe baki taba jinjina kai tace" sam ban amince ba tun lokacin mahaifiyarta na da rai bamu amince ba balle yanzu da bata da rai, ai sai ka jawo mana abin surutu da zagi a garin nan yaushe ne zamu yadda ka dauki rahama yar shekara sha uku ka kaita wani gari wai karatu shima ai zubda mtunci ne ina marabar dambe da fada, da talla da makarantar kwana? ya ce" wlh da akwai maraba sosai gwaggo kinga makarantar kwana idan kaje tamkar kana gaban iyayenka ne tunda baka ayi sakaci da yaro ba balle har ya fita ya dauko abin kunya  tsabar kara2 da koya tarbiyya shi ake koyawa sabanin 'yan talla da suke shiga tashar mota da kasuwa suna felle rashin kunya son ransu ba kwaba balle tsangawam haka zaki ga yarinya ta zage tana zagin kato sbd ya sayi abinta ya hana ta kudi ko kiga ta kama shi da kokowa duk muna kallonsu a tashoshin mota da kasuwanci to ina ranar wadannan muggan dabi'un? wlh garin kokawe-kokawenna ne zaki ga sha'awa ta ingiza wani katon dama ba mata gare shi ba yaja yar mutane sako ko wani shagon ya lalata ta kinga shi ai talla bai tsinanan komai ba daga karshe idan akayi rashin sa"a yarinya ta riga ta saba da cudanya da maza da kashe kudi shi kenan ta sami hanyar bin maza. Yayi tsaki ckn takaici yadda kasan ni ake dorawa tallar, gwaggo tace' mu dai babu dayan da zamuyi ba talla babu kuma wani zurfin karatu ga diya mace sai aure mu shi muka sani kuma shi muka gada kaka da kakanni muma ta hanyarsa aka same mu kaga ko ai ba maki aure ba" yadda ka san in saka hannu aka in yi ta zunduna ihu haka nakeji sbd jin gwaggo ta kafe ba zanyi karatun boko ba, ni kam buri na ke nan ba ni son aure tun daga kan abin da ya sami kawata jummai na yoyon fitsari duk kuma musabbabin auren wuri ne sai ina rayawa a raina tabbas kila nima haka ce zata same ni tunda gwaggo ta kafe ita ra'ayinta na aure kuma babana ba shi da zabi sai gwaggo.

????????????????

Abu daya ya kan sani jin dadi a raina idan na tina cewa yaya aliyu na za'a aura min kuma shi mai son ayi karatu ne to kaga kenan bani da matsalar karatu sai ta wajen haihuwa na runtse ido na ckn tafukan hannayena tamkar zanyi kuka, yaya aliyu ya fuskanci nufi na na son yin kuka sai yace " rahama taso muje ki wuce gidn bkn nima zani inyi sallar la'asar. shi a tunanin sa hanani tfy da yayi shine musabbabin bacin raina bai san hirar su da gwaggo ce ta tada man hankali ba. muka fito ya shiga ya gaida su innarsu sannnan muka nufo kafar gida anan ne muka hadu da babana aliyu ya risina har kasa ya gaida shi baba yace ' ikon Allah ashe ka iso grn" yaya mutan ikko da ikin naka yace lfy kalai baba" yace " madallah idan ka kintsa ina son ganin ka" yace " to baba bari in yo sallah" baba ya shige ckn gida ni kuma muka wuto jkn motar yaya aliyu ya fiddo kudi sabbi ' yan naira goma-goma na dubu daya ya mika min yace" gashi sai ayi haidmar biki ko? na sa hanni biyu na amsa nayi gdy, ya nufi masallaci ni kuma na koma gida na ba gwaggo kudin dannan na tafi. mahaifina sun kebe da yaya aliyu a dakin kofar gida bayan sallar isha'a baba ya dubi aliyu yace dama ba wani abu yasa nayi kiranka ba sai game da maganar rahama, shin har yanzu kana son ta? aliyu ya gyada kai yace ' kwarai ina sonta baba ni ban ma taba tunanin zan dai na son rahama ba "yace toh alhmdlh tunda kana son rahama,kuma wai sbd mu iyayenku kake sonta ko ra'ayine na kanaka, shin kayishririn auren rahaam? aliyu yace eh to gsky baba ni banyi shirin komai yanzu ba illa shirin karatu nke mata ina son in samo mata mkrntr yammata ta garin bauchi sai ta cigaab da karatunta tunda nasan ko za a yi mgnr aurenmu sai nan gaba kaga lkcn ko ai uku ta kammala ya isheta idan akayi auren sai ta cigaba da karatun" baba yayai ajiyar zucy uace " wannan shine ana dara ga dare yayi, ai yanzu ba maganar cigaban karatu ga rahama illa zamcen aure shiyasa nayi kiranka don inji naka ra'ayin idan ka amince za'a daura aure ka tafi da matarka in yaso tayi karatun can a dakinka tunda shine burinka" nana da nan zufa ta karyowa yaya aliyu sbd jin wannan kalamai na mahaifina ya share zufar data tsattsafo masa a goshi da hannunsa ya ja numfashi a lokaci guda yace " baba ko ka manta shekarun rahama sha uku ne yanzu yace kwarai ina sane ban manta ba cancantar hakan shi yasa na sanar da kai ban sani ba ko ka canza ra'ayinka kanata"ya ce ni sam ban canza ra"ayi na ba amma a tawa shawarar ina ga zaifi kyua a dan bar ta ta kara dan girma ko nan da shekara biyu ne kaga lokacin ta kai shekara sha biyar baba yace wlh aliyu da ra'ayi na kenan amma sai rasuwar uwar yarinyar nan ya ruguza komai kaga yanzu ikon rahama ya koma hannun gwaggo babu mai tsawatawa rahama a gidan nan yanzu gwaggo ta hau sababi tace za a takurawa marainiya, ba wai na raina rikon da gwaggo take mata bani illa yanzu sai abinda take so take yi a ckn gidan nan ko ni ka mina tsoro kar wata ran a wayi gari rahama ta dauko mana abin kunya sbd sakacin tarbiyya kaga gara in yi mata aure hankali na zaifi kwanciya shi yasa na shaida maka in kana yi ayi da kai don kuwa masoya sun fara sintiri har da mai gari na son ta mahaifinsa ya aiko kuma wlh kowa ya zo na kan shaida masa nayi mata miji kaga da muguwar rawa gwanda kin tashi, kar su ji haushin na hana su aurenta su yaudareta su lalata mana ita ko su hure mata kunne ta bijire mana shi yasa gara ayi auren mu huta"
[03/11 1:51 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da Ciwo 7•••
????????????????????????????????
Har yanzu Aliyu zufa yake yi shi sai yana jin mgnr tamkar a mafarki wai yau shine da auren rahama yar shekara sha uku abin da bai taba kawowa a ransa zai faru nan kusa ba.ya shiga jerowa baba illar auren wuri ke kwowa amma sam baba ya kiya sai ma ce masa yayi ' ai ni aliyu gara ko me zai faru da rahaam ya same ta a dkn mjnta sabanin ya sameta a gabanmu, in har son da kake wa rahama na tsakani da Allah ne to gra ka amince da aurenku in kuma ba haka ba to ni daman na san yaudararmu kke yi kamar yadda mutanen gari ke zunden hakan, kaga sai in nemi wanda zai rike min ita tsakani da Allah in bashi aurenta" kwakwalwar aliyu tayi caji tare da daukan zafi snnan zuiyarshi ta sosu don jin wai mutanen gari na zunde akan irin son da yake wa rahama nan take yba baba tabbacin zai aure ni amma sai yace " shi kenan na amince dari bisa dari da aurenmu da rahama amma ina neman alfarma ka a daura gobe kamar yadda nai kace ayi hkr har sai sati na sama idan na dawo sai a daura ranar asabar in yaso lahadi sai in tafi da ita. kuma kar kuyi wahalar yi mata wani abu komai da zata bukata zata same shi a can idan ma babu zan siya mata baba yace haab aliyu ai ko da muke iyayenka gaba daya ai ba a yi haka ba ydda akewa duk wata 'yar gata muma haka zamuyi wa rahama ko don kare mutuncin ta a can gaba" aliyu ya dago manufar baba da yace can gaab wato kar ya goranta min wata rana amma sai yace " haab haba baab yaushe ne gani a raye zan bari kuyi wahala akan auren rahama ai ko ba ni ta aura ba ni ya kamata in yi mata komai na kayan daki balle ta zama mallaki na. ina son ku kwantar da hankalinku da zarar an daura aurenmu rahama kadia zan tafi da ita ba tare da komai na dawainiya ba ina son ma tun yanzu ka sanar da yan uwa" baba dai murnace ta coko masa ciki sbd jin kalaman aliyu sannan babban abin farin ciki yadda ya nuna halacci akan maganar iyaye bai biire masu ba duk da yake shima yana so auren washegari maganar aurenmu da yaya aliyu duk ta watsu ckn danginmu kowa sai yake da wannnan aure babu kamar gwaggo wadda sbd murna guda ta dinga rangwadawa ni ko muna zaune gefenta kawai sai na saka mata kuka ni a dole ba na son aure. don gsky ko da can da ake cewa aliyu zan aura ni a wasa nake daukan abin sai yau ne na tabbatar gsky ne da naga ana ta rabon goro da alawa, sannan naji ana cewa wai da an daura zai tafi dani lagos. wlh ba komai yake sani kuka ba sai idan na tuno da jummai kawata wadda a sanadin aure gashi ta nakasa gurin haihuwa, shikenan nima yanzu da anyi auren idan nazo haihuwa zan sami matsala duk da yake ma ni a lkcn ban san komai game da aure ba. na cigaba da aikn kukana gwaggo ta matso daf da ni tadafa kafadata tana lallashina tace " haba yar lelen gwaggo meye kuma abin kuka daga zancen aure? ko ba kya son yaya aliyun nake ne? na dago ido na yayai jawur nace " ni gwaggo ya zaku ce wai zai tafi dani lagos ni kadai ni wlh ba zan bi shi ba" gwaggo tace " toh shikenan ni zan shirya idan aka daura auren mu tafi tare sai ya hada mu mu biyu kin yarda ko? na yi saurin gyada kai nace " na yarsa kema acan zaki zauna ko? ta ce kwarai kuwa" sai da ta gama lallashi na da dadadan kalamai sannan ta dauki buta ta fita.

????????????????

 a bakin kofa suka hadu da yaya aliyu zai shigo dakin. Tace " yauwa Ali sai ka shiga kayi lallashi mutuniyar ka kukan aure take? yayi murmushi yace " yanzu gwaggo dan Allah waye ya tabo min amarya kin san fa yarinyace? tace wlh babu wnd ya tabo ta ganin ana raba goro da alawa shine ta saka kuka" ya shigo dkn ya zauna daf dani ya riko hannuwa na ckn nasa yace " haba rahamata ko ba kya so na ne? na dago ido na da suka jajir na kalle shi ga wasu sabbin hawaye na zuba amma bance uffan ba ya sake cewa" kina so na rahama na gyada kai na tabba cin eh yace ok to kiyi hkr ki daina kuka babu abun da zai same ki idan akai maki aure ko wani yace maki wani abu zai samekine? na girgiza kai yace to gaya min abinda ke saki yin kuka ko kina tsoron wani abun ne? nayi saurin cewa eh" ya dan fiddo ido yace " me kike tsoro? nace "ni haihuwa nake tsoro" kawai sai naga ya tintsire da dry yace " wa ya ce maki zaki haihu? nace" ba ina gani kowa aka yi mashi aure haihuwa yake ka duba fa yadda jummai ta zama yanzu tana can abitin kano za a yi mata aikin ni wlh tsoro nakeji" na sake rushewa da kuka ya kwantar da kaina bisa kirjinsa yana share min hawaye yace " come on, ki kwantar da hankalinki, in dai haihuwa kike tsro(i promise yhu ) nayi maki alkwari ba zaki haihu da wuri ba in Allah ya yarda sai a lokacin da kika kai munzalin haihuwa (do u agree)? kin amince? na gyada kai ya ce to yi min yar dryr nantaki mai ban sha a wa" bansan lokcn da na kyalkayle da dry ba d dai dai lkcn gwaggo ta shigo tana kallonmu ta ce " iko sai lillahi rahama yo ina kukan?anya wannan ba zaki kwacen dan saurayin mijin ba?? mu ka sa dry gaba dayanmu. A gaskiya aliyu ya shiga halin rudani da ya koma lagos, don kuwa ckn sati gudan da baba ya diba masa don har " yar rama sai da yay. ba wai baya son aure na bane illa kankanta da yake ganin nayi, daga gida har ofis baya samun walwala ya rasa yadda za'ayi ya sanarwa da abokansa na lagos yadda yake daukan kansa mai bala in aji a birnin lagos yaushe ne zai iya furta musu zai auri yar shekara sha uku. tabbas yawancin frnds dry zasuyi masa sbd yadda matsayinsa yake. ya so ma ace ya gayawa aminisa sagir to yana shakkar kar ya gaya masa shi kuma ya gayawa amaryarsa safiyya kaga daga nan tonon silili yazo kenan. shi kam dole aurenmu ya zam na sirri har sai yaso don kansa sannan zai bayyana ni ga abokansa a lokacin da ya tabbata idan suka ganni sai sun san ya iya zaben mace aliyu ya shirya kansa ckn kaftani a shadda ya isa gidan sagir da misalin karfe takwas na dare. Bisa teburun cin abinci ya iske su suna cin sbinci, safiyya ta sha ubansun kwalliya na wani(lace) tayi kyan amarci har ta gaji sai yaji innama ace yadda rahamansa ke da bala in kyua gaka take babba ga waye wa,gsky da sai tafi safiyya hadewa tunda zai dinga sai mata kaya masu tsadar gske, sai dai kash kafin yaga rahama cikakkiya haka za a kwashi shekaru biyar koma fiya da haka. sagir ya mike ya tarbo shi ckn fara'a suka zauna dinin table din ya dubi safiyya yace " amarya kin sha kamshi yaya amarci? ckm mirmushi tace " amarci gamu nan a cikinsa tsundun" suka yi dry ta mike ta shirya masa abinci a gabansa ya dube ta yace " kayya safiyya gsky da kyar zan iya cin abinci nan bana jin dadin jikina" sagir yace " wai meke damunka ne ckn satin nan duk wani (so weak) nake ganinka? yayi dan gajern murmushi yace " kai dai barni kawai sagir probs na iske barkatai a katagum abn ba dama" ganin bai fito fili ya sanar da sagir matsalar dake katagum ba sai shima ya bar zancen illa kawai yace " to Allah ya kyauta kuma ya jisshe mu alheri amma don Allah kayi kokari ka ci abinci ko yaya yake ni kaina bana jin dadin ganin ka haka duk da ban san problems din ba ( but yhu must try to eat)" ganin sun takura shi sai ya soma cin abincin amma sam baya jin dadin abincin ko rabi bai ci ba yaji bai iya ci gaba da ci dole ya hakura ya dinga kwararawa cknsa tacaccen ya yan itatuwa. hirar ma sama sama suke yi, safiyya ta dubi aliyu tace " shin aliyu ko ka sami min wata yar kawa ne? ni naga tunanin naka(so deep) ne yayi dan yake yana dubanta yace ' ta iya yiwuwa haka ta iya yiwuwa kuma ba haka ba abin ne wani iri( i don't knw hw to explain but tym will tell) tace " au haka ne abin yar boyo? yace kingane ko safiyya wata yarinyace nake nema ckn wasa ashe iyayenta sun yi (serious) da batun shine suka ce in fito ayi mana aure to ni kuma a shekaru na sai ina ganin ban isa aure ba ko safiyya ta tintsire da dariy har da kyakyatawa ta dubi sagir tace " dear kaji wani shirme gun wannan tsohon tuzurun in yarinyar bata ce kayi mata tsufa ba ai ka auna arziki ko ni yanzu ai tsoho na aura don dai ina son abi na haka ne amma yaushe? suka yi dariya sagir yace ' yanzu nan safiyya nine tsoho? to ki sha kuruminki kwanan nan zan karo maki kanwa wadda tafiki yarinta under 16 zan auro sai ki tabbatar cewa yanzu irinmu 'yan mata ke nema ido rufe" ta shagwabe fuska tace " don ALLAH na tuba dear kar muyi haka da kai daga wasa sai tsole ido" sukayi dry duk wata damuwa da aliyu ke tattare da ita ta kau sai jefi-jefi da yakan tuno nan da sati war haka ya zama ango.
[03/11 7:17 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da Ciwo 8•••
????????????????????????????????

 Yana zaune a ofis din sa ranar alhamis ana gobe zai tafi katagum ke nan yayi bala in zurfi ckn tunani gashi dai gobe zai tafi amma har yau ckn abokansa babu wnd ya san cewa zai yi aure shi bawai auren ne bai so ba ila kankantar rahaman  da yake gani. Nan take sai ya tuno da babban amininsa a bauchi wato kabir yayi hanzarin janyo wayrsa ta (landline ya latsa ko minti guda ba'ayiba ya samo layin kabir suka fara da gaisuwa sannan aliyu yace "KB yaya madam? kai ma ya kake da bauchi?" yace " everything is fyn ai nayo zaton ba zaka neme ni ba in yaso ranar daurina auren sai mu hadu a katagum sai in ga abokin da ya finin" aliyu yace " oh kb am sori wlh ayyuka ne sun yi min yawa a ofis ashe ka sami labarin daurin auren? ya ce nima jiya alhajinmu yake sanar mani su baba na katagum sun aiko masa da gron daura aure shine nima na sani, aliyu (what is happening) ne akan auran nan? ya ja dogon numfashi yace, "kai dai bari kawai kabir wlh kai kanka shaida ne ina son rahama (too much but) ni ban shirya mana aure yanzu ba (last week) na zo ma su baab da maganar zan sama mata (boarding scul) ana bauchi to anan ne nana ya ke sanar da ni shirinsa na aurenmu gsky kuma na amince da hujjar da ya kafa min na dalilin auren amma don Allah kabir ina son kar ka sanar da kowa maganar auren na don kuwa zai zamo (in secret) ckn sirri ka gane ai?" yace gsky(i don't understand wat u mean) shin ko kacanza ra'ayin aurenka da rahamar ne? gsky yarinyar is very nice ga tsabar kyau ni ina ganin nan da 2 yrs idan kayi kiwonta sosai zata yimaiko har ka gaji moriyar ta" suka sheke da dariya abin ka ga shakiyyan abokai aliyu yace" wlh (i never change my mind but the prob is) ka san ni da nuna matsayi akan komai nawa (could u imagine frnds) anan lagos dariya zasu min idan suka san zan auri yar shekara sha uku? (dat is y) na ke son kayi (taking care ) daga kai sai sakina ne ckn frnds dina suka san auren nan. kabr ya sauke wani gwauron munfashi yace" kana ganin haka zai yiwu? shin ina ka taba ganin aure ya boyu ko ayi zaman aure ckin sirri? ina ce lagos zaka kai rahama? kana ganin zai kyautu ka boye ta gidanka ba tare da kowa ya sani ba? ya ce " kwarai zai yiwu kai dai ka taimaka min da abinda nak so daga baya zan sanar da kai (plans) dina" yace" shi kenan sai mun hadu a katagun" aliyu yace "yaushe zaka zo? Ina ganin nima gobe da yamma zamu isa can sbd daura auren na safe ne" yace " amma gida zaka bar sakina ko? yace " kai zai wuya in bar ta a gida ita kanta tana son zuwa katagum din kaga daganan sai su raka amarya lagos ko? aliyu yace"what! dn Allah ka rufa min asiri akan zancen kai amaryan nan kai ana abu cikin sirri zaka janyo tonon silili. gsky ko su baba na shaida masu bana bukatar 'yan rakiya wa rahama daga ni sai ita zamu tafi duk mai son zuwa gidanmu ya iya zuwa daga baya" kabir yace '" gsky ni aliyu na rasa inda kasa gaba, anya kuwa kana son yarinyar nan ko dai auren dole su baab zasu hada ba su sani ba? ni kam ina tausayawa rahama irin zaman da zatayi a gidanka muddin baka son ta illa biyayyar iyaye yasa ka aureta. don ALLAH aliyu in baka son yarinyar nan ka gaya min wlh na san yadda zanyi in fahimtar da su baba su hakura da auren yanzu" yayai murnushi har sautin ya isa kunnen kabir yace "wlh, wlh kaji rantsuwa kanen? ina son rahama tsananin so kuwa ta yadda bana jin zan iya rayuwar aure ba tare da ita ba kuma ina tsammanin ko ckn tsumman goyo aka ban auren rahama zan iya amsa inyi rainonta har ta girma a hannuna bale yanzu na tabbata rainon da zanyi mata bai wuce(2 to 3 yrs) ba kafin mu soma zaman aure na sossai sbd haka kr kayi kokwanto akan auren muko na dole ne don biyayyar iyaye ina son ka saka shi a cikin ire iren auren soyayyar daka sani kamar irin naka da sakina kil ma ya zarta naku" suka yi dry, kabir yace shin wani abu da bangane ba shine maganar rainon da naji kana cewa zakayi wa rahamar(i don't understand)?" ya murmusa yace " kar kayi kokwanton abinda nace . Zanyi rainon raaham har sai naga ta zama mace sosai sannan zan fara dora mata lalurar aure kaga tayi girma ta sami ishasshen ililmi akan abin ka gane yanzu? ya numfasa yace " kwarai na gane manufarka, amma abin da kamar wuya yadda kake gwauro a bakaa auren wadda kake so sannan kace zaka zura mata ido kai ban yarda ba kunma ba zan taba yarda ba" aliyu ya keec da dariya yace " ni kam zan iya kuma wlh wannan alkawaru ne nayi in sha Allahu sai na cika shi(5 yrs) zan diba ma rahamar kaga lokacin zan nemi hakkina (she is 18) ai yayi ko? anan kama kabir yayi dry iya son ransa yace" kwarai yayi daidai amma wlh wannan alkawarun da ka dauka wa kanka nasa masa suna ALKAWARIN DA CIWO! kuma sai ka fadi haka da bakinka. to wai tsyaa idan ita rahama ta nemi hakkinta fa ya zaka yi?" yace " nasan zai yi wuya ta nema sbd na lura bata san komai ba game da sha'anin aure kuma tun yanzu tana min kuka wai ita tsoron haihuwa take yi tunda kawarta ta zo hihuwa ta zama yar yoyon fitsari kaga ke nan na sami madogarar da zan dinga kafa mata hujja ina tsorata ta da abun in kuma har ta matsa shi kenn" yace " wlh aliyu wannan alkawarin da ka dauka zai yi wuya kuma n tabbata kafin rahama ta bata kai ne na farko na san kuma kai ne zaka sha wuyar alkawarin" suka yi dry gaba daya sun kusan fin awa guda suna hira a waya daga karshe sukayi sallama.

????????????????

Haka aliyu yaci gaba da shirye shiryen zuwa katagum daura auren sa ba tare da ya sanar wa da kowa ckn abokansa ba balle gurin aikinsu. shi ko dan irin hutun nan da angwaye suke dauka na cin amarci bai nema ba sabod yasan shi ba wani amarcin da zaici tunda kwna biyu kacal zai yi a katagum sai ya dauko amaryarsa zuwa gidnasa lagos.sagir ya kusa ya dago abin da ke faruwa da yage setin akwatuna a dakin baccin aliyu amma da yake wayom aliyu ya zarta misali sai ya juye shi bai bai ya shirya masa karyae na wani cousin dinsa ne y siyo masa zai yi aure. taiba kuwa har kuka tayi sbd ganin aliyu ya rame a ckn satin nen. Ana sauran kwana daya daurin aure na da yaya Aliyu ya iso garin katagum,ranar jumaa kenan da misalin karfe bakwai na marece lkcn sallar magrib,ko cikin gida bai shiga ba ya nufi masallaci don yin salla.Tare suka jero da babana daga masallaci zuwa gida suna tafe suma tattaunawa gane da daurin aurenmu gobe.Dakin da yaya Aliyu kan sauka na soro nan suka shiga shi da baba,ya nuna masa akwatunan da ya yomin na aure guda hudu shakare da kaya masu tsadar gaske yawanci duk dinkakkune tun a lagos ya bada aka dinka sannan ya fiddo rafar kudi yan dari bibbiyu na dubu ashirin ya mikawa baba yace,gashi baba wannan sadakin rahama ne,baba yana rike da kudi a hannunsa yace,"haba Aliyu yaushe ne kana dan mu har sai ka bada sadakin rahama.To ka bar abinka kayi wata hidimar ni ba zan amsa ba",Aliyu yace,"Aa baba baayi haka ba sadaki ai shine aure kuma ya zama dole a ba rahama sadakinta muddin ina son aurenta tunda ba sadaka kuka ban aurentaba ba kuma ko sadaka ne dole diya take ba baiwaba ta cancanci sadaki''.Baba yayi ajiyar zuciya yace, kwarai na san da haka ko auren sadaka da ake bayar wa ai dole a biya sadaki balle ma ku kuna son junanku. A matsayi na na kanin mahaifinka ni zan biya sadakin.Yayi saurin cewa aa baba wlh na yafe maka tunda ina da hali na ni dai fatana ku dinga mana addua kuna sa mana albarka tare da fatan ayi a saa.Yace shikenan Allah yayi maka albarka ya albarkaci auren ya ce amin baba. Aliyu ya nemo yan matasan gidanmu suka jida Akwatunan suka shige dasu cikin gida dakin goggo shi kuma na biye da su da dan kit a hannunsa.A lkcn ina takure bisa gadon goggo ina rusa kuka sbd yan uwa da suka tasani gaba wai sai sun samin lalle.Aliyu yana shigowa suka tasa shi gaba da tsiya wata abokiyar wasanmu tace,lah!lah!me zan gani?yanzu nan angonne da kanka dauke da akwatin kayan lefen?lallai zamani ya canza maimakon kayi kiranmu mu zo mu kawo shine ka kawo da kanka?ina ganin ma amaryar bari mu kai makaba kai ne zaka kai abarka chan legos din,Yayi murmushi duk da yake Aliyu sam ba mai son surutu bane valle irin wadannan wasannin abokan wasa inkaga yawan maganar aliyu to a gaba na yake ko kuma ana magana akan abinda yashafeni.Ya dubi msi maganar yace,Au baba bai gaya muku babu yan kai amarya ba?Daga ni sai ita zamu tafi in yaso daga baya zanzo da kaina in kaiku kuga wuri sukace gsky mu wannan tsarin bai mana ba,ya zaka maishe mana ya tamkar ba yar dangi ba gashi ita kenan mace a gidan kamar rai daga rahma fa an gama auren ya mace a gidan nan don Allah yaya aliyu kayi hkr ka barmu mu raka ta muna son ganin birnin ikko,Yayi dan murmushi cikin ire iren murmushinsa masu burgeni in dai bai amince da maganarkaba haka yake irin wannan murmushin yace shikenan zamu tattauna dasu baba za'a san abinyi. Ni kam ina leken sa ta cikin mayafi na ashe ya hankaltu da ni sai naga yayi saurin aje akewatin hannunsa ya nufo inda nake ya zauna a gefen gadon yasa hannunsa yana kokarin yaye rufar da nayiwa fuska ta yace"Amarya ba dai har an fara kukan amarcin ba ne tun yanzu?Yana cire mayafin yaga fuskata sharkaf da hawaye nan da nan sai naga ya hade rai ya juya ya kalli wadanda ke shirin sa mani kalle yace"Yanzu don Allah har kun farasa yarinyarnan kuka tun yanzu?gsky zamu bata da wanda yasata kuka shin me kukayi mata hafsa?Tace wlh babu illa dai sa mata lalle da muka zo yi shine abin kuka mu kuma wlh sai mun sa mata tunda muma haka aka yi mana"Yace a kan al'ada kawai sai ku sa min ita kuka? Ina dai sa lallen nan bawai ya zama dole bane to yau akan rahams an dai na,suka sheke da daria shi kuma ya juya ya ci gaba da lallashina na da cewa yi shiru kinji baby na babu mai bata miki jiki da lallen aure in dai ina gidannan sai dai in sun yarda in sa maki da kaina.
[03/11 7:17 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da Ciwo 9••• ????????????????????????????????

Suka yi dariya tare da cewa,ai zaka iya tunda ma lefen da kanka ka kawo.Ke kam rahama kinyi sa'ar miji mai tattali da lallashinki Allah yasa ya dore haka"suka fice suna dariya shi kuma ya cigaba da lallashi har da hirarraki har sai da yaga dariyata sannan ya nufi sassan mahaifinsa.Yana fita danginmu tare da su gwoggo suka antayo cikin dakin don ganin kayan lefe na. Kaya kam sun amsa sunansu kowa sai tofa albrkacin bakinsa yake tareda sam barka masu mamaki nayi sbd irin yawan kayan tare da haduwarsu. ni kaina duk da a lillibe nake sai da na dinga liken kayan ta ksan mayafina. lallai yaya aliyu ya jibgo mini kaya na gani na fada. Ina jin masu kirgwa suka ce zannuwa kala talatinne cif. duk sakankance gurin ganin kaya ashe masu niyyar sa mana lalle basu fasa ba sai ji nayi sun yaye lullubi na sun goga min lalle tare da fesa min nono daga bisani suka feshe ni da turare. In banda aikin kuka babu abin da nake yi. Karfe takwas na dare su kabir da sakina suka iso kasancewar suna da dangi da kuma gida a katagum shi yasa suka sauka a gidnsu. washegari da misalin karfe tara na safe aka daura aure na da yaya aliyu. wlh ni tamkar a mafarki nake ganin abin ban tantance da gaskiyar haka ba sai da naji abokan wasa na rangadamin guda suna cewa yau na tabbata matar aliu gobe sai lagos sannan ne na saka kuka sbd jin zan tafi wata uwa duniya lagos in bar iyayena . ni kam dari bisa dari ina son yaya aliyu illa lagos din ne bana son inji ana cewa zan tafi. ni a son samu nama a ce bayan auren a nan gidanmu zan zauna shi kuma ya dinga zuwa kamar da amma ina babu yadda za'ayi haka ya faru. ban sami ganin yaya aliyu ba sai bayan sallah isha'i aka sani nayi wanka aka bani wata tsaleliyar atamfa ckn kayan aure na na saka sai sheki da kyalli na keyi ni kaina na san na kara kyau a ranar fiye da nawa na baya. aliyu ma da ya shigo dkn gwaggo ya ganni rudewa naga yayi har yana rayawa a ransa anya zai iya cika alkawarin daya kudirta a ransa na kyale ni?

????????????????
Gsky da yana ganin nayi kankantar aure amma yau sai ya ga na kara yi masa girma tamkar yar shekara sha biyar ko sha shida da ma ganu da manyan gabobin girma irin na mahaifiyata. ya tsaya kusan minti biyu yana kare min kallo sama da kasa ni kam kaina a sadde yake a kasa gaba daya yau kunyarsa na ke ji. daga ni har shi kamshin turare muke mai dadin gske. haka nan ya daure yace " rahama' na amsa ckn sanyin murya " na'am" gabansa sai da ya ba da ras! da yaji murya ta domin yau itace rana ta farko da murya ta ta sa shi jin sanyin jiki ya sake cewa " raahama yau kuma baki iya kallo na sai dukar da kai ko nayi laifi ne baki ganni ba tun bayan daura aurenmu? na yi saurin dago kai nace masa" ni wlh ba haka bane" yace " to menene? nace " ba komai" yace " ko kunya ce " na gyada kai nace "uhm" yayi dariyarsa ta kasaita yace" yanzu nan kunya ta kuma kike ji rahama? ashe abn da sake wai an baiwa mai kaza kai. to bari kiji yanzu ni aliyu na zama mijinki tsakanin mu babu zancen jin kunya duk wata damuwarki ni zaki gayawa tunda yanzu dani zaki zauna. kinga gobe idan na tafi dake gida na can lagos to komai ya kare najin kunya daga ni sai ke zamu zauna babu su gwaggo ko su baba a kusa kila ma sai kin haihu zaki zo gida su ganki, haba wa kaman jiransa nake sai kawai na saka masa kuka shi kansa da ya san maganar da yayi zata sani yin kuka na tabbata da bai fade ta ba. kuka na shiga yi ba kadan ba duk ya bi ya birkice ya shiga ckn rudani ya ce " subhanallahi! meye abin kuka don nace ba zaki ga su gwaggo ba ko don nace zaki haihu? to yi hkr ni sam na manta kina tsoron haihuwa ba zan yarda ki haihu ba kinji? bil hakki da gskiya ni fa tsoron haihuwa nake har bana kaunar in ji ance wani ya haihu. da yaga na dan tsagaita da kukan sai yace" ba kya son ki bini lagos ki ci gaba da karatun ki? nace " ina son karatun amma ni bana son tafiya lagos dinne idan munje wanene zai taya ni zama? yace " ni zan taya ki ko ba kya so? nace " ina so to idan ka tafi gurin aiki fa ya zanyi? ya ce " ai inajin a lokacin ke kuma kin fara zuwa makaranta, kinga lokacin da zaki dawo nima na taso aiki ba shike nan ba idan na dauko ki a makaranta sai mu wuce gida abin mu" nace " dawa zan dinga kwana?" yayi murmushi yace " dani mana ko ba kya so?" na dan yi murmushi nace " ina so" washegari lahadi da aka wayi gari na ga ana ta min shirye-shiryen tafiya ga dangin mahaifiyata sun ce aladole ko mtum biyu ne sai sun raka ni gidan miji na, shi kuma yaya aliyu ya tubure sam baya son ' yan rakiya. dole haka kowa ya hakura ni dai bani da wani aiki ranar sai kuka sbd jin wai ni kadai zan tafi sai aliyu wanda ko duk kawaye na da ake masu aure dangi da kawaye ke raka su gidan mazajensu har ma a kwana amma ni yaya aiyu ya hana. su gwaggo da iyayenmu maza sune suka tasa mu gaba ni da yaya aliyu suna man nasiha" baban aliyu shi aliyun yafi tsananta fada da nasihar akansa yace"don Allah abba (sunan da su kan kira aliyu da shi kenan sbd sunan kakanmu ke gare shi) ya ci gaab " ka kula da amanar yarinyar nan kar ka kuskura ka ci amanarta ko musguna mata don Allah ka kula da addininta duk da yake na san rahama akwai son addini to amma kayi kokari ka kula sosai. mu dai nauyinta ya tashi a kanmu ya koma gare ka to kar kayi sakaci ka bi ta sannu a hankli sbd ka san yarinyace akwai tsabar kuruciya a tare da ita, Allah ya taya ka riko ya baka zama lfy kuma ya albakarkci auren" gaab daya dakin aka ce amin. baba na shima yayi mana nasiha shima kaninsu yayi mana sannan suka fice daga dkn sai mu sai gwaggo. itama ta dora da tata nasihar daga karshe tace ' to mai gida na ga dau yar kanwarka nan ka bi ta sannu kan hankali na tabbata zaku yi zama lfy tunda ku na son juna. amma don ALlah ka rage irin sangarta rahama da kake yi sbd yanzu zaman aure zaku yi ya ban banta da irin zaman da kukeyi da. ke kuma ban hana ki shagwaba ba amma ban da rainu da rashin kunya, kar ini kar in gani in ba haka ba ni in zo in amshe mijin inyi zama na a lagos ke kuma ki dawo nan dakin" muka yi dan murmushi sai a nan ne na san nayi murmsuhi amma da kuka kawai nake yi. haka aka sako ni gaban motar yaya aliyu ina ta aikin kuka yan uwa suka zagaye motar suna mana Allah kiyaye hanya. kabir ma yace suna na zuwa shida sakina. muka yi sallama da yan uwa motar mu ta daga ni daya tilo kamar yar mayy sai aliyu. motar jeep yar karama mai(tint glass) wato irin mai duhun nan haka ya dinga sharara gudu yana yi yana lallashi na sbd kukan da nakeyi.
[03/11 7:17 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da Ciwo 10•••
????????????????????????????????

Mun bar garin bauchi sosai sannan na saurara da kuka sbd na fara jin bacci, ido na a lumshe yaya aliyu ya dubeni yace" rahama ya akayi ne" na dago dara daran idanuna da suka zama tamkar an gulof sbd kuka na kalle shi nace " na am" yace kina jin baccine ? nace ' eh' ya ce "ok bari inyi parking sai kikoma baya ki kwanta ko? yayi parking a gafen hanya ya riko min hannu na fito na koma gidan baya na kwanta ya cire malim malim din da ke jikinsa ta lallausan shadda ya lilliba mini sannan ya koma mazauninsa ya ce gaba da tuku. ya zuge dukkan gilashan motar ya kunna mana A.C sannan ya saka mana kaset na turanci wakar celen dion ta (A NEW DAY HAS COME) tun ina jin wakar har sarkin barayi ya sace ni kwance ckn babbar rigar yaya aliyu ina shaker kamshin ni'imtaccen turarensa (HEAVEN).resemble amma gsky she is beautiful ko zaka ban aurenta idan tayi girma don na san yanzu karatu take ko?Yace ja bari sai ta girma in tana sonka sai in baka ita(second wife)suka yi dariya na kalli Aliyu alamar tambaya a ido na ya kashemin ido daya tare da roko hannuna yace to ismail sai gani na biyu,Yace yanzu kiri-kiri kunki tsayawa kuci abinci ko?Ko dan asmau bata nan 'matarsace asmau'Aliu yace wlh bahaka bane akwai abinci da muka taho dashi kasan kuma we are on our way kar muyi dare bisa hanya ga yarinyan mutane.Mukayi sallama dashi muka nufi mota sai da muka ci sinasir da miya wanda aka ciko mana kula dashi sannan muka kama hanya muna tafe muna hira abinmu.

????????????????

Na shirya tsaf sannan na tsaya ina kollon yanayin dakin,gsky ya hadu kafet ya mamaye dakin ja sai labule a zagaye suma jajaye sai gado makeke da dressing mirro dinsa ga wardrob a manne a bango kai duk dai wani abu da zai kayata dakin an saka shi.Na fiti fslo na iske yana salla ganin haka sai na nemi kujera na nitse ins kallon tsarin falon shims ya hadu iya haduwa,babu abinda babu har wani guri naga an kebe a falon sbd yin karatu cike yar kantan take da littafan addini dana boko dirowar katakon dake falon kuwa shake take da electronics kayan wuta na zamani. Yana idar da sallah ya nufo guri na yace harkin kammala?Nima ina shigowa naga kina sallah shine na shiga wanka gashi har nayi sallah.Na gyada masa kai, bari in sa kayan bacci in zo muci abinci sai ki kwanta ko?" na gyada masa kai, kafin ya wuce dakinsa sai da ya kunna min tauraron dan adam sannan na ga ya haye benen da ka gidan ina tsammanin nan ne dakinsa. ya fito sanye ckn riga da wando ba bacci muka isa gun cin abinci, kula biyu ce daya sakwarace da miyar agushi wai shine nawa abincin dayan kuma salad ne shine nasa a yadda yace min shi baya cin abinci mai nauyi da dare. ya kawo mana juice da swan water muka ci muka sha. muna kammalawa ya riko hannuna muka shiga dakin da nayi sallah ya dubeni yace " kina jin bacci ko? na ce "' eh" ya ce , " to ga gado nan sai ki hau ki kwanta ni a dakin sama na ke kwana zaki iya kwana anan ko? ckn tsoro nace " ni ba zan iya ba ka san a gida ba na kwana ni kadai. gsky a gurinka zan kwana" yayi shiru yana tunani wai ashe shi yana son ya din ga nisanta ni da shine sbd kar ya kasance muna yawan cudanya da juna ya zamto ya karya alkawarin da ya daukar wa kansa. ya dubeni yace " kiyi hakuri ki kwanta a nan kinga can saman akwai sanyi da yawa" na make kafadata nace" ni dai na ki sai dai kazo nan mu kwana" yayi dan shiru sannan yace " shikenan zo muje dakin nawa" muna fitowa falo waya ta dinga ringing ya dauka suka gaisa da wanda ya bugo masa ina jin yana ce masa " eh wlh ban dade da dawowa ba, eh don Allah kar ka zo da safen ma hadu a ofis amma na san zan zo very late sbd wasu yan matsaloli. ok good nyt a gaida amaryar da ba ta tsufa" suka yi dariya tare da ajiye wayar. ya kalle ni tare da yin murmushi na lumshe ido na ya sake yin murmushi yace " duk baccin ne" come on let's go" gsky da muka shiga dakin baccin yaya aliyu rudewa nayi sai warware idanu nake ina kallo yadda ya kayata dakin(ALJANNAR DUNIYA) haka na fada a zuciya ta. wlh ni ban ma san yadda zan fadi irin shiryuwar dakin ba, yadda kasan a kasar waje haka yake. da yake gadon yaya aliyu makeke ne ko da muka kwanta akwai tazara tsakanin inda ya kwantar da ni da inda ya kwanta. domin kuwa mutum biyar zasu iya kwanciya a tsakiyarmu ba yare da wani ya matsi wani ba. in banda snyin kamshi babu abin da ke tashi a dakin, hatta bargin da ya lillibeni shima na sa kamshin daban, balle kuma shimfidar gadon yadda ka san anyi barin turare haka kamshi ke tashi. na saba a gida in zanyi bacci in rabu da jikin mutum amma yau sai ga aliyun da nake mannewa in yi bacci lokacin muna gida ya juyan baya. ban san lokacin da na mirgino na kankame shi ta baya ba. ina yan munfarfashi yace" menene kuma? na dauka kinyi bacci? nace " ni tsoro nake ji? yace " tsoron me?" nace " tsoron dodo" ya kyakyale da dariya yace" har yanzu rahama kina nan da wannan tsoron?to ki kwantar da hankalinki kiyi bcci ni daki na ba dodo" na dan fara masa yar shagwaba ta yace " ok don't cry bari in kunna fitila ki nuna min dodon"
[03/11 7:17 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da Ciwo 11•••
????????????????????????????????

Yana daga kwance ya latsa fitila haske ya gauraye dakin ya juyo ya kalle ni yace " nuna min dodon" nayi yan waige waige na nace" ni ban ganshi ba kila ya gudu ne" yayi murmsuhi ya ce " ke kin cika tsoro kiyi baccinki ni babu dodo a daki na" haka na kankame shi sannan muka yi bacci. wahsgari tun da asuba aliyu ya tadani muka yi sallah.tun da muka idas bamu koma bacci ba. karatun alkur'ani ma ya koya min wasu littattafan na addini. sai wajen shida na safe sannan muka kammala karatu. banda kur'ani ma ya koya mun wasu littattatafan na addini. sai wajen shida na safe sannan muka kammala karatu ya dubeni lokacin ina zaune dirshen a gabansa bisa kafet yace " yaya har yanzu kinajin baccin ne? na gyada kai nace " wallahi baccin bai isheni ba" yace " ba kya jin yunwa kenan?" nace " ni ba yanzu zan ci abin ci ba sai rana ta fito" yace "a she halayyarmu daya ta zo muje mu kwanta zuwa 8:00am sai mu tashi sbd zanje ofis" na dube shi nace" yaya aliyu idan mutum yayi aure ba ana bashi hutu a gurin aiki ba" gsky tambayar da nayi masa ta jefa shi ckn mamaki da al'ajabi ya dubeni fuskarsa cike da tsoron halayyata na wayau yace" waya gaya maki ana ba mutum hutu idan yayi aure?" nace " lokacin da abokinka kabir yayi aure ba hutu naji kace ya dauka ba har suka yi tafiya da sakina ya sauke numfashi yace " anyi haka, to ni ban dauki hutu ba sai nan gaba kila ma nan da shekaru biyar" nace shekaru biyar? lokacin ai aurenmu ya tsufa" ya kyakyale da dariya yace " ashe kin tsufa lokacin?" nace "ai ni yarinyace ina jin kai ne dai zaka soma furfura lokacin" yayi dan murmushi yace " to shekara biyar din nan da kika ji nace a lokacin ne zamu fara cin amarci" nace " ni ban gane ba" yace "zaki gane (but not now) zo muje mu kwanta" sai takwas da minti biyar muka tashi bacci. aliyu da kansa ya shirya min ruwan wanka a bayi ya raka ni har sai da yaji na fara wanka sannan ya nufi kicin kafin in fito in shirya har ya kammala mana abin yin break fast. lokacin daya fito wanka ni kuma na saka wata super holland koriya ina zaune gaban madubi.

????????????????

Aliyu ne ya shirya min fuskata da hoda da jambaki hatta daurin kallabin shi yayi mani na zamani na fito tsaf da ni. ya leko ta madubi yana kallona muka yiwa juna murmushi yace"gsky kinyi kyau haka zaki dinga yi min kwalliya ko da yaushe kin gane' bana son in ga kin zauna ba wanka ko ba kwalliya" nace" sau nawa zan dinga wanka a rana?" yace"sau uku, kin ga da safe daya sai na rana da na dare kin gane?" nace" na gane" karfe tara da kwata aliyu ya nufi ofis dinsa. da zai tafi kulle ni yayi a ckn gidan bayan ya nuna min yadda zanyi amfani da wasu abubuwa na gidan.amma yace maganar dafa abinci sai ya dawi daga ofis zamu dafa tare. Na kasance a gidan miji na aliyu ckn jin dadi da kwanciyar hankali. komai nake bukata da rawar jiki yaya aliu ke mani shi. haka ya kasance kullum cikin koya min girke girken zamani da duk wasu abubuwan da kaina bai waye da su ba. nan da nan sai na canza nayi kiba fatar jiki na ta rika sheki sbd canzawar yanayin da na smu. duk fa wannan zaman da muke har yanzu a matsayin wa da kanwa muka don kuwa aliyu ko da was bai taba tunanin neman hakkinsa na aure ba. kuma tun zuwan mu aliyu ke nema min makarnta amma ta kwana yace zanyi don ba zan manta ba ranar wata monday da ya dawo gun aiki yazo min da albishir dun samun makarantar, mun danyi rigima, ina zaune a falon kasa bisa kafet ina buga TV game yaya aliyu ya bude kofar falon ya shigo tare da yin sallama. ya kalle ni muka yi wa juna murmushi na taso da dan gudu na cikin sassarfa na tare shi ya rungume ni da hannu daya daya hannun kuma ya murza key ya kulle kofan. haka ne ka'idar gidanmu kullum a rufe da key tamkar(prison) gidan yari. idan aliyu zai fita ofis yake kulle ni da key har sai ya dawo in kuma yana gida har yayi baki to zaice in tashi in shige dakin sama wai a cewarsa baya son su ganni. tunda na zo gidan nan ban tba hulda da kowa ba, ko gaisuwa kai hasali ma bana zama in yayi aurei baki balle su san matar tana ckn gidansa(AURAN SIRRI) haka na lakaba wa aurenmu suna, ko anguwa bama zuwa tunda ban son kowa ba a garin lagos,sau daya ne muka fita zuwa saloon aka yi min retouching da gyaran kumba, da zamu dawo ya biya da ni wani katon (SUPER MARKET) mukayi (shopping) itama wannan fitar da daddare mukyi ta. kai ko mai gadu da yaron gidan yaya aliyu wanda ke masa wanki ba su sanni ba balle su san da zama na a matsayin matar uban gidansu. bayan yaya aliyu ya rufe gidan muka karaso ckn falon yana tallabe da ni a gafe guda ni kuma ina rike da jakarsa, ko zama baiyi ba ya shiga wanka. yana fitowa gurin cin abinci ya wuce yana cewa yau fa yunwa nake ji seriously me kika tanadar min ne?"
[03/11 11:01 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da Ciwo 12•••
????????????????????????????????

Na soma bude kulolin da ke kan teburin nace" kaga ni yau burabiskon shinkafa nayi maka hade da stew, in kuma baka son stew akwai miyar agushi, sai kuma juice ga kuma gasasshiyar kaza wadda nayi mata hadi sosai sun yi maka?" yayi murmushi ya dube ni yace, "anya ke kika yi girkin nan rahama?nace waye ka aje a gidannan da zai taya ni?l" ya ce " ban aje kowa ba amma abin da mamaki" nayi dan murmushi" naja masa kujera ya zauna nima na zauna muka shiga ckn cin abinci. yana ci yana yaba girki nawa shi wai yayi bala'in mamakin yadda akayi farat daya na loyi girki lokaci da muka kammala da cin abinci babban falon muka dawo ya kwanta rigingine a 3 seater yace in dinga matsa masa kafadunsa. nan fa na shiga matsar kafa da luguiguita ta tamkar yadda ya koyar dani. ban gushe ina masa ba sai komai ya birkice masa ya fara sauke numfashi da saurida sauri. can kuam sai naga yayi saurin janye kafafunsa ya mike ya zauna muna kallon juna. a yadda naga idonsa tamkar na mai jin bacci yace min" na gode rahama bari sai zuwa anjima sai kici gaba" ya dafe kansa da hannu bibbiyu yayi shiru na kusan minti biyu sannan ya dago fuskarsa ya dubeni yace "albishirinki" nace " goro" yace "yau dai makarantarki ta samu" na ware ido ina murna na bi na kwakume shi ina tsalle shi kam sai dariya ya kemin. sai da ma gama turmurmusanshi sannan yacr" amma gsky yaya aliu na gode Allah ya saka maka da alheri" kai na langabe a kafadarsa ya shafo sumar kaina yace " ban sani ba ko zaki yi murna don kuwa boarding na sama maki" na gintse fuskata ina kallonsa nce" boarding fa kace yaya aliyu! gsky ban san ka gaji da zama da ni ba sai yau. shin laifin me nayi maka da kake son rabuwa da ni? in har na takura maka a gidanka ne to ka mayar dani can gida katagum" da manne nake jikin aliyu amma maganar da yayi ta tfy makarantar kwana sai ta sa na koma karshen kujera ina mtsar kwalla. ya matso kusa da ni don lallashi amma sai na mike ckn kuka zan gudu daki yayi hanzari ya riko ni na fado jikinsa y matsa ni gam ya shiga aikin lallashi na tare da share min hawaye yace" haab rahaman aliyu meya abin kuka don nace zaki tafi makarantar kwana? wlh ba wai na gaji da zama da ke bane. ina jin dadin zama na da ke, abin da yasa kika ga nayi haka ba don ki sami isasshen lokacin yin karatu a can shi yasa, amma kinga in kina nan ko ni bazan barki kiyi karatu ba sbd idan ina ganinki a kusa dani ko mai ke zance kiyi mani daga ince rahama hada min juice sa raahma yi min tausa in yi bacci kin gani amma in kina can sai aikin karatu kawai ba dawainiyar yaya aliyu" na danyi murmushi ckn kuka nace" ni dai bana son(boarding) na fi son day" to wai ina ka taba ganin matar aure tayi makarantar kwana?" yace wlh suna yi in baki yarda idan kikaje zaki gani akwai su da yawa wadanda mazajensu suke so suyi karatu irinki. Don Allah ki kwantar da hankalinki bana son in ga kina damuwa akan abinda bai taka kara ya karyaba.In kuma sbd gani na ne to zan dinga zuws gunki a kai a kai kin amince?Nayi shiru ina dan alamun shagwabs a fuska ta ya sake mannoni jikinsa yace come on rahamar aliyu don't worry ki ban karfin gwiwa mans kinsan education is better than any thing. Nace har aure?Yace wannan daban ne amma ai akwai difference tsakaninsu kinga for you nw you are married ilimi kadai ya saura maki idan kika sameshi dole ke banbanta da rayuwarki ta da can sannan ko ya'ya muka haifa tarbiyar da zaki koya musu zata zamo cikin wayewa da ilimi.Ko ba kya son yayan mu so zo su iske mamansu mai ilimi ce?Na boye fuskata a kirjinshi ina cewa ka manta ni fa bana sin haihuwa?Yace kya so?to ashe nima baki sona?Nace ina sonka mana ina tsoran haihuwar ne yanzu.Yayi murmushi yace ki kwantar da hankalinki inshaAllah ba zaki haihuba sai kin gama karatunki nan da shekara biyar masu zuwa,a lokacin shekaranki 18. Murna ta kama ni don jin aliyu na ya goya min baya akan kin son haihuwa.Na sake narkewa a jikinsa shi kuma ya shiga shafata tamkar ya sami mage gar wani bacci bacci na dinga jin yana kwasats mi zanji?hannuwan yaya aliyu cikin rigata har ya fara shafar kirjina wai!

????????????????

Ai sai na kwala ihu a firgice shima a firgice ya dawo daga duniyar daya lula.Yayi sauri ya sake ni ya dafe kanshi yana sauke numfashi ni kuma ina makure a gefe guda tamkar wanda taga abin tsoro.Sai da ya gama jinyar kansa sannan naga ya suri mukullin motarsa ya mike yace min Rahama bari inje anguwa yanzu zan dawo,Nace nima zan bika yace No,kiyi hakuri ba zan dade ba ina kallon sa ya fice daga gidan bayan ya kulle ni kamar yanda ya saba.

????????????????

  Ranar juma' a bayan saukowa masallaci muna zaune da aliyu a babban falonmu na ksa, lokacin kusan watannina biyu a gidansa, wallahi idan wanda ya sanni a katagum ya ganni lokacin zai yi bala'in mamaki wani ma ba zai gane ni ba sbd girma da kyau d ana kara cikin 'yan watannin nan. jiki na kuwa yayi jajir gashi lugui-lugui yadda kadan idan ka latsa jikina jini zai zubo haka na koma sbd jin dadin da nake gidan aliyu, ga uwa uba kwanciyar hankali, ni kam a wannan lokacin babu abin da ke damuna saboda yadda aliyu ke tarairaya ta tamkar kwai. shagwaba ta kuwa har ta zarta wadda nake masa a katagun don kuwa yanzu idan na tubure har goyi yake min ya dinga zagaye falonmu dani. aliyu baya taba yin bacci sai yaga nayi tukuna hankalinsa zai kwanta. abu daya ke takura ni a gidan aliyu shine rashin fita ko da kofar falonmu ne ya hanani sam. idan na tambayeshi dalilin yi min haka sai yace wai auren kulle yake min in kuma sai inyi dariya ince ko dai auren sirri? gsky idan nace masa haka ya kan yi mamaki har tsoro abin yake bashi saboda ganin na fara dago manufarsa da inda auren mu ya sa gaba. nice ke zaune kan doguwar kujera 3 seater shi kuma aliyu yayi kwance dai dai bisa kujerar amma kansa yana bisa cinyata ina masa susa a kansa wani lokacin kuma sai inyi masa kitos idan ya shafa yaji sai yayi dariya yace" sa comb ki taje min kar in yi baki su gabbi da kitsi ni ba mace ba" nace " ba sai kace masu amarya ce tayi maka ba" yayi murmsuhi yace" ai lokacin da zasu sanki a matsayin amarya bai yi ba da na gaya masu" nace" wai ni yaya aliyu wannan wane irin aure ne za a dinga boye abu tankar zaman haramci? yace " auren sirri kenan ko ba haka kika sa masa suna ba" nayi dan murmsuhi da ke birge yaya alliyu nace ' haka na sa ma aurenmu suna amma ka san wani abu da zanyi maka in toni asirin auren? yayi saurin girgiza kai yace" ban sani ba sai kin fada nace"abinci zan taci mai yawa kullum har sai naga ciki na yayi kato kaga sai in haihu kawai yaron yayi ta tsala kuka kullum neighbours da masu gadinka idan suka ji kukan baby dole ka gaya masu gsky kayi aure matar ta haihu" aliyu yayi dariya a ranar tamkar cikinsa zai fashe har sai da ya barar da tiren apple din da yake ci ya fadi kasa. ni kuw aina kallonsa ya dube ni yace" yanzu ke don ALLAH WA YA GAYA MAKI ABINCI Kawai ake ci a haihu? nace ni babu wanda ya gaya min nwa tunanin ne kawai t me ake ci don Allah ga ya min? ya sake yin dariya yace " ki bari zan gaya maki amma ba yanzu ba, na san ko na gaya maki ba zaki yarda ba shi yasa nake son ki tafi makaranta zaki fahimci wasu abubuwan da suka shige maki duhu but i was surprise ace baki san komai akan aure ba gashi duk anyiwa kawayenki aure ko da yajke ke yarinya ce amma da a babban birni kike gsky zai yi wuya ayi wa kamar ki aure bata fahimci yadda zaman aure ya ke ba. well ni naji dadi ma da baki yi understanding wani abu ba sai dai ina doubting akan makaranatar nan da zaki kar kije kikoya shedanci ki rusa min plan dina" nace kananufin in zama shedaniya kenan yace no ba haka bake nufi ba" kafin inyi magana mukaji ana knocking tare da bugawar kararrawar kofa. aliyu ya kalle ni nima na kalle shi ya dan bata rai tare da yin tsaki yace, mutum ya baro ofis ya dawo gida ma ba za a barshi ya huta da iyalinsa ba. haka kurum ina ckn hira da amarya ta na jin dadi za a takurani Allah ya kyauta" ya tashi zaune ni kama dariyar mugunta nake masa sbd na son kitsone a kansa kuma na san bashi da masaniayra abin da nayi masa. ya dube ni yace"rahama nayi baki kije dakinmu na sama idan ma kammalar da su zanzo" na bata rai nace" ni da na gaji da wannan zaman boyon da kake mini ka maidani tamkar wata mijiya ko dodo" yace kiyi hakuri idan kika tafi makaranta nextweek zaki ga nmutane sosai" ya mike ya riko hannina sai da ya kai ni bakin matakalar bene ya ga na fara taka steps sannan ya nufi kofa ckn hanzari domin kuwa ana ta buga kofar. sai da yaga bacewa ta sannan ya bude.
[03/11 11:02 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da Ciwo 13•••
????????????????????????????????

Mi zai gani? kabir din bauchi ne tare da sakina, ckn murna ya tarbe su yace" kb mutan bauchi kai ne da sakina?' suka yi dariya kabir yace""ah, to gamu unexpected ba sanarwa" suka karaso cikin falon aliyu ya shiga kwala min kira nayo zarya ckn sauri na leko naga su sakina na washe baki ckn murmsuhi lah! sannunku da zuwa mutan bauchi" ckn gudu na sauko na isa gun sakina na rungume ta muka wuce ckn kujera. ni kam murna ce ta cika min ciki sbd yau naga idon sani. aliyu ya riko hannuna ya mikar dani yana cewa"wannan wace irin murna ce ba kya ganin abin da ke gaban sakina ne? sai a lokacin na lura ashe sakina ciki gare ta ya fito sosai. nayi sauri na nufi kicin na shiga shiryo masu abinci"kabir yace" ai sallah zamu yi tukuna kafin muci abinci" aliyu suka fita da kabir nu kuma nayi wa sakina jagora muka nufi daki na na kasa. tana idar da sallah muka dan soma hira ina tambayarta labarin mutan bauchi da na katagum ta dube ni tace" wai me aliyun naki ke baki kika yi bul bul da ke tamkar zaki fashe? nayi dariya nace ba komai sakina nima ina mamakin yanayin jikin nawa" tace" ko dai zamu sami baby ne? na sinne fuskata ina dariya nace " don Allah sakina ki bar fadan maganar bebin nan tsoron haihuwa nake yi" aliyu ya leko yace" sakina ki fito kuci abinci' suna kammala cin abinci muka koma babban falo muka zauna muka shiga hira. kabir ya dubi aliyu yace "wai mutumi na me kake ba yar amaryan nan taka ne tayi saurin girma haka dubi fa har ta kusan cimma sakina" yayi murmushi yace "wlh nima abin mamaki yake bani yadda kasan ana hura mata iska ko in akaita asibiti ne su duba min ita? gaba daya muka kwashe da dariya kabir yace' ina ganin mun kusa zuwa lagos shan suna ne kaga idan aka yi na sakina ba dadewa sai ayi nata" aliyu yace " wai! wai! kana son yanzu ta sakawa mutane kuka kenan wai ita tsoron haihuwa take alhalin har yanzu bata fuskanci inda auren yasa gaba ba" anan ne naga alamun mamaki karara a fuskar su kabir, aliyu ya dube su yace' kuna mamaki ne? kar ku manta fa har yanzu rahama karamar yarinya ce, komai sai a hankali zata fahimce shi. yanzu haka ma na kammala mata shirya shiryen tafiya makaranta kun ga a can kanta zai waye sosai" kabir yace "zaman ta ma anan lagos zai iya sa kanta ya waye in har zaka hada ta cikin matan abokanka. Yace abu mai wuyar kenan,don gsky har yau babu wanda yasan na aje macen aure a gidannan balle har a kaini ga hada rahama da matan abokaina,in banda kai da ya zama dole ka sani babu wanda ya san nayi aure,gsky ina kishin rahama sosai"kabir yace,Don kana kishin ta sai ka aje ta gida a takure?shin waye baya kishin matarsa?koko ku kunfi kowane?Aliyu ya kalleshi tare da kashe mishi ido daya nufinshi abar maganan.Kabir kam ya dau haske sai yace eh to kanada gsky da kake boye ta kar wani ya gani ya kyasa mukayi dariya dukanmu. Muna kichin nida sakina muna shirya abincin dare a nan na har take koyamin wasu girke girken da ban saniba,sai dai tayi mamakin yadda akayi na koyi girkin zamani tunda ban taba fita unguwaba.Ta waigo ta dubeni tace wai rahama ina Aliyu ya kaiki kika koyi girki ne?Ni naga har kin kusa ki fini kwarewa?nayi yar dariya nace,wai!sakina rufamin asiri yaushe zan fiki kwarewa a fannin girki ku fa tsohon hannune kums ko a shekaru ai kin darani.Wlh wani littafin girke girke yayana ya siyo min a ciki na koya amma wasu da kanshi ya koyamin"Tayi dariya tace lallai yar gatan yayan ta,wlh kuna burge ni".Ita ta shirya mana lafiyeyyen abinci ni kuma hadadden juice na mana.Da sakina ta sha sai da tayi santi. muna kammalawa da kcin muka yo wanka muka gabatar da sallar magriba na bar sakin a dakina na nufi dakin yaya na don in shirya jikina. har a wannan lokacin basu dawo daga masallaci ba, wasu ubansu riga da siket na saka yan kanti ne da aliyu sukaje meeting portharcourt ya siyo min su tsaraba. har da wani flat shoe kalan kayan ban ma taba sa su ba sai a ranar. na taje gashin kaina na daure shi da ribbon na sake shi a baya na, ina shirin yafa gyale a kaina ne yaya aliyu ya murdo kofar dakin ya shigo tare da sallama. ya bini da kallon sha'awa, ya iso daf da ni ya ziro hannuwa ta bayana ya makalini a jaikinsa yana rada a kunne yace, " rahama wanna irin kwalliya duk kin rudani na kidime gaba daya anya zan barki ki fito falo da wannan kayan? na dan juyo muna fuskantar juna nace"me kayaan suka yi, ba kai ka siyo min su ba? yace " kwarai nine amma dubi fa yadda sukai fitting dinki yadda na rude ai kowa ma in ya ganki zai rude, kin san muna da baki a gidan ki bari idan suka tafi sai ki sa min su in yi ta ganin abina amma yanzu ki canza wasu" da yake wasu akwatunan kaya na suna nan dakinsa sai muka isa gun akwatin ya fiddo min wata atamfa na cire kayan jikina na saka ta nan ma yace in cire ta wai dinkin tunda stela ne hips dina ya fito. na saka wani lace wai shima ya matse min kirji na da kyar dai ya amince na saka wata babbar riga ta shadda hadi da zaninta.. ya taya ni daurin kallabi na shima gashina da ya malalo a gadon baya tattare shi yayi ya tura cikin dan kwalin ko sili daya babu a waje. na dube shi ta cikin dan mirror nayi murmushi nace" duk kishin kar a ga gashin rahamar ne? amma ai za a ganni ko? yace " don dai kabir ne amma da ban da shi ai ba mai gane min sweet baby na, na haramta" muka yi dariya, ya riko hannuna har zamu fita sai ya tsaya yace" kin san abin kunyar da kika yi min dazun" na girgiza kai na nace" a a ba dai laifi nayi ba? yace " ashe kinyi min kitso a kaina muna fita da kabir yin salla ya sa hannu yana warware min kunya duk ta kamani haka ya tasani gaba da shakiyanci wai ashe har sakina ma ta gani" nayi wata ajiyar zuciya nace" wai! Allah na nima har naji kunyar ba zamma iya fita falo ba" yace" yaushe kuma nima kunyar ai bata yi min illa ba balle ke muje kawai.

????????????????

Muna fitowa muka iske su zaune bisa doguwar kujera, sakina cikin shiga ta alfarma tayi kwance jikin mijinta yana mata tausa suna ganin mu sakina ta dan mike cikin jin kunya tace"a'a amare sannun ku da fitowa" muka yi murmushi nace"yauwa sakina ya gajiyar kicin?" tace"babu gajiya" bayan mun kammala da cin abinci ne aliyu yace ya kamata mu fita yawon shakatawa ckn garin lagos, amma ganin yadda sakina ta nuna tsabar gajiya a jikinta yasa kabir yace mu bari sai gobe da safe sai mu fita tunda week end ne. wajen kwanciya saboda kowa yasan halin shagwaba ta shi yasa kabir baiyi tunanin cewa mu kwana da sakina ba sai yace, shi da ita zasu kwana dakin bakin falon mu washe gari asabar misalin karfe goma muka gama shirin mu tsaf, yawo muka yi niyyar zuwa sai inda mai ya kare, ni kam har Allah Allah nayi gari ya waye don in fita yawo tunda na sami yancin zuwa ganin gari albarkacin zuwan su sakina. mun fito gaba dayanmu kofar falon mu aliyu na kokarin rufe falon kenan muka ga motar kirar starlet ta shigo harabar gidan, duk muka maida hankalinmu gun motar har ta iso daf da mu tayi fakin. aliyu da ke kokarin rufe kofa sai ya fasa shima motar yake kallo ga dukkan alamu ma cikin zullumi da mamaki yake, wata kyakkyawar yarinya wadda kallo daya zaka mata kasan bayerabiya ce itace ta fito daga cikin motar ta bangaren mazaunin direba. ta iso gurinmu cikin fara'arta tare da sallama ta cigaba da cewa.a'a aliyu gaskiya kayi wuyar gani ashe baki gare ka a gidan" ta juyo gurin mu tana" ina kwananku baki daya muka amsa mata shi kam aliyu kallon ta kawai yake ya daure yace mata" taiba daga ina haka da safen nan?" cikin rashin jin shakku tace " wallahi daga gida nake gurin ka nazo kasan mun kwana biyu bamu hadu ba, tunda na tafi ibadan jiya na dawo shi yasa na kasa daurewa sai na zo na gan ka" ya dan gintse fuska cikin rashin walwala yace " to gani kin ganni ko? ina sauri ne zamu fita anguwa da baki na sai mun hadu a ofis ranar Monday?" ya juya ya kalle mu yace" wannan itace sakatariya ta taibat abdullatif" ya dubeta yace" taiba meet my frnd kabir and his lovely wife sakina sannan ga lovely sister dina rahama daga bauchi suka zo" ta sake kallonmu cikin fara a tare da yi mana barka da zuwa. banyi mamaki ba da naji aliyu yace ni sister dinsa ce saboda babu wanda ya san yayi aure balle su san ni a matsayin matar sa, ta sake duban shi  yana dan kallona ta wutsiyar idonsa sannan ya ce mata, ok mu shiga ciki amma fa sauri muke yi ina fatan maganar ki ba mai daukan lokaci bace? tace ban yi tsammani ba" ya dubi kabir yace" kabir ku dan jirani a mota ina zuwa two minutes pls" ya bude gidan suka shige mu kuma muka nufi cikin mota muka zauna aliyu yana ganin ni yarinya ce amma bai san kishi na nan dankare a zuciya ta ba. ganin sun kebe da wata mace su biyu kacal yasa haushi da kishi ya cika min ciki. da kam ban nuna a fuskata ba amma ganin sun fiye da mintuna goma banga sun fito ba ya sa na bude motar zan bisu in ga uwar da suke yi. kabir ya dubeni ya ce "ina zaki rahama?" nace nayi mantuwa a daki ne na rufe motar na dumfari falon gabanasai dukan uku uku yake yi, ina yane labulen falon tare da sallama anan naga abin da ya firgitani. taiba ce rungume da mijina suna tsaye tana masa magiya har da kuka a idonta.[04/11 11:25 am] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da Ciwo 14•••
????????????????????????????????

Tsoro ya kamani kamar in juya sai na daure na wuce cikin gudu na shige daki na dake kasa, na hada kai da bangi ina sharar kwalla. cikin rawar jiki aliyu ya hankade taiba gefe guda tare da yi mata kashedin kar ta kara zuwa gidansa. a hanzarce  ya nufo dakina yana ganin halin da nake ciki duk ya rude ya matso ya rungume ni a jikinsa yane cewa" rahama menene?" nayi shiru ya sake cewa" kukan me kike yi" nan ma shiru nayi illa aikin sharan kwalla da nake yi. ya riko hannuna muka koma bakin gado ya zauna sannan ya dorani bisan cinyarsa yace" to gaya min me ya saki kuka?" na dube shi nace" yaya aliyu ashe kaima dan iska ne?" cikin mamaki yace subhanallah! rahama me nayi haka da zagi?" nace" au baka ma sani ba?" to wanna wacece naga ta rungume ka?" cikin rudani yace" ba nace maki sakatariya ta bace, to shine wai take so na ni kuma na gaya mata bana sonta, kina gani dai ita ta rungume ni kuma ni har ga Allah ba dan iska bane kamar yadda kika dauka cikin kuka nace me yasa baka hanata ba ko ka ture ta" kasan haka zata faru shi yasa kace ku shigo daga ciki da ban shigo ba wa yasan abin da zaku yi" aliyu ya dafe goshinsa yace innalillahi to na dau laifina ba zan kara ba, kiyi hkr tashi mu tafi kinga har sha daya ta wuce ga shi mun bar su sakina a mota kar suji shiru na make kafadata nace na fasa zuwa ku tafi kawai yace " no kar muyi haka da ke dan Allah my rahma, kinga munyi baki kar ki fara bullo da wannan hanya, haba sweet baby ta kin san bamu taba samun misunderstanding ba sai yau kiyi hkr this is d first and d last ki yafe min" ya mikar da ni yana share min hawaye da handkerchief da kyar da jubin goshi ya shawo kaina muka je toilet ya wanke min fuskata da kanshi yayi mun make up har sai da ya sani dariya sannan hankalinsa ya kwanta. shi mamaki abin yake bashi, wai ni rahama yar 13 and half yrs har na san zafin kishi ashe idan na kai 18 yrs ya shiga uku kenan muna fitowa falo muka yi kicibis da su kabir ne ya fara magana" wai me ke faruwa ne ko amarcin ne ya motsa zaku shanyamu a mota" muka dan yi murmushi ni kam nawa bai kai ciki ba aliyu yace"ah! to ka san halin amare shagwaba ce ta tashi yanzun nan" duk da wannan karyar da yayi musu na lura sun dau hasken abin da ya faru a fuskokinsu naga alamun tambaya. ikon Allah abinka ga yarinta kafin awa guda da faruwar haka har aliyu yasa na mantA mun sami matsala, don tun muna cikin mota ya maidani garau sai hira muke tare da kwasar dariya. gaskiya ranar mun yawatu a garin lagos daga wannan super market sai mu fada wannan har gurin hoto muka je daga karshe ya kaimu gidan wani abokin aikinsa alhaji sharif bayarabe ne. kamar kullum a matsayin kanwarsa ya nuna ni. hakika mutumin nan akwai kirki don kuwa ya karramamu a matsayin mu na yan uwan aliyu, ya shaida mana shi masoyin aliyu ne hakika kuma mun shaida duk da yake matarsa yace tayi tafiya amma ya sa yaron gidansu ya shirya mana abincin alfarma don kuwa anan mukayi lunch. da zamu tafi ya bamu dubu ashirin ni da sakina. ranar lahadi washe gari kenan su sakina suka koma bauchi. ranar kam nayi kuka har suka yi kamar kar su tafi sabisa zuwansu yasa na sami sakewa ina fita kuma naji dadin zamansu a gidanmu. aliyu yayi lallashina har ya gaji haka muka kwana ina masa kuka waini ala dole sai ya kaini gida katagun, yayi min wayau wai in bari sai week end sai mu tafi.

????????????????

Bayan tafiyar su sakina da sati daya aliyu ya fara min shirye shiryen tafiya makaranta, duk wani gata da ake yiwa mai shirin tafiya makarantar kwana nima mijina yayi mini. daga JS3 zan fara karatun sbd hazakata, ana gobe zan tafi muna kwance da aliyu cikin bargo munyi shrin bacci kenan, kai na bisa hannunsa nayi matashi ya kira sunana na amsa yace gobe fa kamar wnn lokacin kina can kwance cikin daji yanzu ya zaki yi gurin kwanciya gaki mage wajen son jiki" nayi tamzar zanyi kuka" nace nima abin da nake tunani kenan shiyasa nace maka bana son boarding ni dai nafasa zuwa" ya makaleni a jikinsa yace" ashe ba kya son karatun kenan" kiyi hakurizan dinga zuwa ina ganinki every week sannan kinga zaki samu kawaye su dinga debe miki kewata" nace" to kai kuma ya zaka yi idan bana nan?" yace " ya kuwa zanyi rahama? ai dole inyi hakuri da rashinki tunda ina son kiyi karatu ko in kara aure ne kafin ki dawo? na zabura daga kwance na tashi zaune hannuna na rawa na kunna fitila mai haske na dube shi fuskata a daure nace " aure? dama shi yasa zaka turani makaranta don kayi aure? dama samarin katagum sunce ba sona kake ba biyayyar iyaye ce gashi yau na gani. wallahi tashi yanzu ka maida ni gida ba zan kara kwana a gidanka ba tunda aure zaka yi" shima ya tashi ya zauna muna fuskantar juna yace" yi hakuri my sweet baby wasa nake maki ba zan sake yin aure ba insha Allah daga kanki na gama come on karki tada min hankai in kasa bacci mana"ya rungumo ni jikinsa yana lallashi kuka kawai na saka masa dama can kiris nake jira saboda bana son tafiya makarantar sai kuma gashi ya tsokano jangwam. yace " don Allah ki bar kukan nan nace maki wasa nake yi" cikin kuka nace" ga yammata nan suna zuwa har gida wurin ka ai rannan naga abin da kuke yi" ya dafe kansa yace" ya salam! shin rahama sau nawa zan gaya maki gaskiya ta ki yarda ne? wallahi ke kadai nake so a raina, kuma na fadi maganar aurennan ne don in gani kina sona sai gashi na gani tabbas kina sona har da kishi na ma tun da ba kya son inyi aure. yanzu dai mu bar wannan maganar mu kwanta kinga dare yayi sosai"nace fa yanzu na daina sonka ka maidani gida kawai! hankalinsa ya kara tashi ganin na kiyin bacci wai dole gida zai kaini gashi tsakiyar dare gari kuwa ba nan kusa ba. yace" shikenan gobe zan maida je kiyi hakuri kiyi bacci' haka muka kwana ina ta masa kuka ni fa a nawa tunanin na dauka da gske auren zai yi shi yasa zai kaini makaranta. Da gari ya waye ma ban hakura da duk da lallashi da magiyar da aliyu ya kwana yana min, don kuwa har na kammala shirin kayana a akwati shi kawai nake jita. hankalin aliyu in yayi dubu ya tashi idonsa yayi ja har wata yar rama naga yayi ta zullumin irin kukan da nake. ya dibe ni ina zaune a gefen gadon dakina na tasa akwati gaba yace" kin gama shirin kenan?" na gyada masa kai ya sake cewa" ke yanzu nan da gaske tafiyar kike so? nan ma kai na gyada masa ya dan yarfar da hannunsa tare da kada kansa gefe guda yace" ok, tunda haka kike so bari in nemo wanda zan hadaki da shi ya kaiki gida" nace" ni bana son kowa kai nake so ka kaini tunda kai ka kawo ni garin nan sai kayi masu bayanin zakayi aure" yace" wai ke baki san wasa bane? ni kam ba zanje katagum yau ba tunda ni kike son na kaiki sai ki bari sai na shirya sai mu tafi" nace" ni dai ba zan jira ka ba yau na ke so jeka ni koma waye yazo ya kaini ina so in ma mai saida kawuna ne kaga shike nan sai ya saida kaina ka huta sai kayi aurenka" ko uffan bai ce min ba sai ya girgiza kai ya fice abinsa. ina jinsa ya rufe gidan da makulli alamun ya fice kenan. ba shi ya dawo ba sai bayan azahar yana shigowa dakin na mike tsaye nace" ya zo ne?" ya dubeni yace " wa kenan" nace" wanda zai kaini katagum" ya zauna bakin gado ya riko hannuna yace " zo nan ki zauna kiji" ban yi mas musu ba na zauna kusa da shi ya fuskance ni sosai sannan yace" wanda zaku tafi tare na fasa hada ku shi ne na aike shi can katagum din yaje ya kira min baba sule(mahaifina kenan) kinga idan yazo sai inyi masa bayanin yadda kika tada min hankali daga maganar wasa kinga in ya amince maki sai ki bishi ku tafi" nayi tsam da raina ina kallon sa tsoro ya baibaye ni don kuwa tabbas ina tsoron babana idan nayi laifi sam shi baya daukan wargi balle idan yazo yaji abinda ya hadamu da aliyu tabbas kilama bugu na zaiyi.
[04/11 11:25 am] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da ciwo 15•••
????????????????????????????????
Na sauke numfashi nace" yanzu yaya aliyu meye na aikawa a dauki baba?dama so kake ya zo ya buge ni tunda yanzu baka sona na saka kaina a tsakanin cinyoyina na fara kuka ya matso ya dafa ni yace"meye kuma abin kuka?tunda kin matsa min zaki tafi gida kinga ai gara in kira baba kila shi kya ji maganarsa tun da nayi lallashin kinki hakura" nace, shi ke nan na hakura da tafiyar amma makarantar na fasa zuwa" yayi dan murmshi yace" bari dai baban idan yazo sai kiyi masa bayani, nikam makaranta nayi niyyar zuwan ki kuma ba zanyi asarar kudina da lokaci a banza ba. shin kinsan irin dimbin kudin da na kashe wajen nema maki makarantar nan? haba rahama ki tausaya min mana amfanin kanki na fa" nayi shiru ina tunani tabbas naga irin zirga zirgan da aliyu ya dinga min akan karatun nan kuma hakika amfanin kaina ne to ina laifin sa da wani ne ma yaushe zai yi min wannan gatan. cikin hanzari na mike na soma harhado kayan da na san ya siya min na tafiya makaranta har na gama kallo na kawai yake yi na dube shi na risina a gabansa nace" yaya aliyu don Allah kayi hakuri abin da nayi maka daga yau na daina, tashi ka kaini makarantar" kwalla na tsiyayo wa kunci na saboda nadama shima tausayi na ya kamashi ya janyoni na kwanta bisa cinyoyinsa ya shiga shafar gashin kaina yana kara lallashi na. yace" na yafe maki rahama ta amma ba zamu tafi ba sai naga kin saki jikinki kina walwala da dariya sannan zamu tafi bana son mu rabu yadda kike din nan hankalina ba zai kwanta ba" na dago idona muka kalli juna muka yi murmushi yace, naga daya saura na biyu, nace" to goya ni kaga daga yau zan dade baka goya ni ba" yayi murmsuhi yace" rahama shagwaba ho" nace"mhm ni dai goyani" ya juya min bayansa na haye har da kwantar da kaina nayi lamo tamkar wata baby. haka ya dinga zagaye babban falon gidan mu da ni har wani bacci naji yana kwasata. ya dubi agogo yace" kinga yanzu uku har ta kusa kinyi sallar azahar kuwa? nace " nayi tun karfe daya" yace" abinci fa kinci" nace, ban ci ba" yace" subhanallahi me ya hanaki cin abinci? fushi ko? ashe har yanzu baki daina fushi da abinci ba idan anyi miki laifi come on sakko muje kici abinci" na sauko muka nufi kicin ina kallon sa cikin sauri ya dafa min taliya da yake muna da stew ko minti ashirin ba'ayi ba ya kammla, muka dawi falo ya zaunar dani yana bani har na saba in ba shi ya zauna ya bani abincin ba ban cika ci ba, karfe hudu dai muka kammala shirinmu ya fidda kayan tafiya ta ya zuba a booth din motar sa jeep mai tint glass don yawanci in zamu fita ni da shi a wannan motar muke fita don kar a ganni makarantar da aliyu ya kaini ta masu kudice ta "ya"yan wane. bayan ya kammala min registration ne muka fito muna sallama ya dube ni 'karfa ki manta duk a takardunki na sa miki ke(single) ce baki da aure kin ji ko" nace" wai duk meye hujjar yin hakan" yace, babu wata hujja illa dai bana son a dinga baki wani matsayi wanda kuma shekarunki ba su kai ba kin gane?" nace " eh" . ya ci gaba da yi min nasiha kan yadda zan kula da kaina da yadda zanyi hulda da mutane kuma ya gargadeni da cewa kar inyi kawaye barkatai in rike sirrin dake tsakanin mu ni da shi. ido na ya ciko da kwalla na matso zan rungume shi ya rike hannuna yace" no, kinga kiyi hakuri next week zanzo in sake ganin ki" a haka muka rabu da ina zubda hawaye shi kan shi aliyu cikin tsananin damuwar rabuwa dani yake don dai gwarzon namji ne shi yasa bai taya ni zubda hawaye ba amma idon shi yayi ja alamin ya shiga damuwa. A wannan rana sam ban iya bacci ba saboda tunanin rabuwa ta da mijina sai kuma uwa uba gurin kwanan yau babu aliyuna a kusa balle in makale shi gurin kwanciya. gani da tsoron tsiya sannan gadon da nake a sama yake. na dai samu na rungume fill na dinga tsiyayar hawaye. Sati na dayaa makaranta aliyu ya ziyarci katagum wanda tunda muka yi aure yau kusan watannin mu uku amma zuwansa na biyu kenan da kuwa duk bayan sati bibbiyu yake zuwa. mutan gida aka tare shi da murna kowa sai ware ido yake ya ganshi da ni amma sai suka gan shi kwal. sai bayan sallar magriba sannan ya samu sararin kebewa da gwaggonmu ta dubeshi tace" aliyu wai yaya kanwar taka ne lafiya take ko? yayi murmsuhi yace" lafiya lau gwaggo duk tace in gaisheku" tace " bata yi maka rigimar sai ta biyo ka ba? a'a bata yi rigima ba ai yanzu ta fara yin hankali shagwaba ta soma raguwa" gwaggo tayi murmsuhi tace" yar nema wato ita dadi gidan miji har ta soma manta gida ko? to ba zan yarda takwace min kai ba tunda gashi kaima kafi wata guda rabon ka da garin nan, ina zan yarda" cikin wasa irin na kaka da jika gwaggo ke wannan maganar Aliyu shima yayi dariya yace" wallahi gwaggo yanzu ne na sami saukin rahama akan rigimar zuwa gida saboda yanzu ta soma zuwa makaranta, amma ko ranar da zata soma zuwa kwana mukayi tasa min kuka wai ita in kaita katagum, da kyar ta lallasu.

????????????????

Gwaggo tace" rahama kenan har yanzu har kasa ta makaranta?" yace" yanzu satinta guda da soma zuwa zaman gidanne ba dadi ita kadai gata da tsoron tsiya" tace" ai da ka samo mai tayata zama ne ko anan babu masu aiki ne? yace"uhm,uhm gwaggo gara dae ita kadai din masu aikin ne basu da kirki. kinga yanzu ba abinda rahama baya iya ba na aikin gida ta iya girkin zamani ba abinda bata iyaba"tace" iye kace shi yasa ta boye mana kai. gaka nan fa ka kara kiba abinka da zama kamar bature hala itama tana nan ta bindige? yayi dariya yace, "ai gwaggo idan rahama tazo sai an sare wannan yar kofar taki don kuwa fadin yayi mata kadan ta zama giwa abinta" tace masha Allah kaci gaba da kula da yar uwarka ka kula da maraicinta kaga dai yarinyace komai sai a hankali zata sani musamman zanatakewar auren abu ne mai sauki mai wuya sai ka kula haka aliyu yayi kwana kinsa biyu a katagum duk rabin hankalinsa yana guna duk da yake ina makaranta amma sai yana ganin tamkar wani abu ya same ni bayan nan. a daddafe aliyu ya iya hakurin wata guda bai ganni ba kasancewar principal din makarantar mu abokin sa ne shi yasa yazo ganina na ga ya tsuke fuska yana kallo na tabbas na san baya rasa nasaba da irin ramar da nayi. principal ya fita ya barmu a ofis din yana fita na nufo aliyu idona cike yake da hawaye ya ware min hannuwansa na fada jikinsa ina kuka ya tallabo fuskata yana duba na shima fuskarsa kumshe da tausayina"rahama me zan gani haka?" ya sa hannu yana taba kashin wuyana wanda kuwa da bani da shi ya sake cewa" meye wannan rahama? ba kya cin abinci ne?" na girgiza kai nace" wallahi yaya aliyu karatu da wuya gashi ni kadai babu kai kullum tunaninka nake yi ni dai mu tafi gida ba zan iya ba"hawaye ya zubo a kunci na ya fiddo handkerchief yana goge min hawayena yace" come on, kiyi hakuri dole ne za ki sha wuyar karatu tunda ba daga farko kikafara ba,amma na san insha ALLAH kafin karshe na term dinnan zaki gane wasu abubuwan idan kuma kika dawo gida zan dinga miki lesson kinji? sai maganar tunani ki daina yi zai iya jefaki cikin matsala ki tsaida hankalinki gurin karatu kawai ko ba kya son ki zama doctor rahaama ne? nayi murmushi nace " ina so mana amma ni......sai na kwantar da kaina bisa kafadarsa yace"amma ne?nace" amma ni ka dinga zuwa ina ganinka every week" yace" ok,i will try and do my best in ga nazo every week yanzu me kike so?" nace" babu komai duk provision dina suna nan ko kwata banyi amfani da shiba" yace" ashe ba kya cin abinci kenan shiyasa kika yi dan wuya" nace"ina ci tunani ne kawai" yace" to in na dawo naga wannan kashin wuyan zamu yi fada da ke ina san inga kamar da". Ranar da aka yi mana hutun zangon karatun mu duk na bi na kosa aliyu ya zo dauka ta. muna zaune ni da kawata maryam sulaiman kowa yana jira azo daukansa, kasancewar sunan babanmu daya shi yasa muka yi abota kuma na lura halayyarmu zata zo daya. dakinmu daya da ita asalinta haifaffiyar zariya ce, amma aiki ya kawo mahaifinta lagos. maryan ta girime ni da shekaru kusan biyu. na dubi maryam nace" ni wallahi maryan na gaji da zaman makarantar nan duk na kosa yaya aliyu ya zo ya dauke ni mu tafi gida gara ku kun saba da makarantar" tace" wane sabo ai komai dadin makaranta gida ya fishi. wai shin rahama wannan aliyun da kike damu na da zancensa shi menene naki" naga kullum zancenki baya wuce na yaya aliyu" nayi murmushi nace"yaya nane kawai"ya"ya maza muke ni da shi shakuwa ce kawai kika ga yasa ina yawan ambatonsa, muna cikin hira ne na hango motar yaya aliyu tayi fakin a bakin get din makarantarmu tun kafin ya fito na mike cikin hanzari na isa gurinsa yana hangoni ya bude motar ya fito cikin fara'a muke duban juna yace" iye yan makarantar ba. kinga yadda kika yi kyua kuwa kinyi " yar kiba abinki ko kefa da duk kin damu kanki kin rame nima kin sani cikin zullumi.[04/11 11:25 am] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da Ciwo 14•••
????????????????????????????????

Tsoro ya kamani kamar in juya sai na daure na wuce cikin gudu na shige daki na dake kasa, na hada kai da bangi ina sharar kwalla. cikin rawar jiki aliyu ya hankade taiba gefe guda tare da yi mata kashedin kar ta kara zuwa gidansa. a hanzarce  ya nufo dakina yana ganin halin da nake ciki duk ya rude ya matso ya rungume ni a jikinsa yane cewa" rahama menene?" nayi shiru ya sake cewa" kukan me kike yi" nan ma shiru nayi illa aikin sharan kwalla da nake yi. ya riko hannuna muka koma bakin gado ya zauna sannan ya dorani bisan cinyarsa yace" to gaya min me ya saki kuka?" na dube shi nace" yaya aliyu ashe kaima dan iska ne?" cikin mamaki yace subhanallah! rahama me nayi haka da zagi?" nace" au baka ma sani ba?" to wanna wacece naga ta rungume ka?" cikin rudani yace" ba nace maki sakatariya ta bace, to shine wai take so na ni kuma na gaya mata bana sonta, kina gani dai ita ta rungume ni kuma ni har ga Allah ba dan iska bane kamar yadda kika dauka cikin kuka nace me yasa baka hanata ba ko ka ture ta" kasan haka zata faru shi yasa kace ku shigo daga ciki da ban shigo ba wa yasan abin da zaku yi" aliyu ya dafe goshinsa yace innalillahi to na dau laifina ba zan kara ba, kiyi hkr tashi mu tafi kinga har sha daya ta wuce ga shi mun bar su sakina a mota kar suji shiru na make kafadata nace na fasa zuwa ku tafi kawai yace " no kar muyi haka da ke dan Allah my rahma, kinga munyi baki kar ki fara bullo da wannan hanya, haba sweet baby ta kin san bamu taba samun misunderstanding ba sai yau kiyi hkr this is d first and d last ki yafe min" ya mikar da ni yana share min hawaye da handkerchief da kyar da jubin goshi ya shawo kaina muka je toilet ya wanke min fuskata da kanshi yayi mun make up har sai da ya sani dariya sannan hankalinsa ya kwanta. shi mamaki abin yake bashi, wai ni rahama yar 13 and half yrs har na san zafin kishi ashe idan na kai 18 yrs ya shiga uku kenan muna fitowa falo muka yi kicibis da su kabir ne ya fara magana" wai me ke faruwa ne ko amarcin ne ya motsa zaku shanyamu a mota" muka dan yi murmushi ni kam nawa bai kai ciki ba aliyu yace"ah! to ka san halin amare shagwaba ce ta tashi yanzun nan" duk da wannan karyar da yayi musu na lura sun dau hasken abin da ya faru a fuskokinsu naga alamun tambaya. ikon Allah abinka ga yarinta kafin awa guda da faruwar haka har aliyu yasa na mantA mun sami matsala, don tun muna cikin mota ya maidani garau sai hira muke tare da kwasar dariya. gaskiya ranar mun yawatu a garin lagos daga wannan super market sai mu fada wannan har gurin hoto muka je daga karshe ya kaimu gidan wani abokin aikinsa alhaji sharif bayarabe ne. kamar kullum a matsayin kanwarsa ya nuna ni. hakika mutumin nan akwai kirki don kuwa ya karramamu a matsayin mu na yan uwan aliyu, ya shaida mana shi masoyin aliyu ne hakika kuma mun shaida duk da yake matarsa yace tayi tafiya amma ya sa yaron gidansu ya shirya mana abincin alfarma don kuwa anan mukayi lunch. da zamu tafi ya bamu dubu ashirin ni da sakina. ranar lahadi washe gari kenan su sakina suka koma bauchi. ranar kam nayi kuka har suka yi kamar kar su tafi sabisa zuwansu yasa na sami sakewa ina fita kuma naji dadin zamansu a gidanmu. aliyu yayi lallashina har ya gaji haka muka kwana ina masa kuka waini ala dole sai ya kaini gida katagun, yayi min wayau wai in bari sai week end sai mu tafi.

????????????????

Bayan tafiyar su sakina da sati daya aliyu ya fara min shirye shiryen tafiya makaranta, duk wani gata da ake yiwa mai shirin tafiya makarantar kwana nima mijina yayi mini. daga JS3 zan fara karatun sbd hazakata, ana gobe zan tafi muna kwance da aliyu cikin bargo munyi shrin bacci kenan, kai na bisa hannunsa nayi matashi ya kira sunana na amsa yace gobe fa kamar wnn lokacin kina can kwance cikin daji yanzu ya zaki yi gurin kwanciya gaki mage wajen son jiki" nayi tamzar zanyi kuka" nace nima abin da nake tunani kenan shiyasa nace maka bana son boarding ni dai nafasa zuwa" ya makaleni a jikinsa yace" ashe ba kya son karatun kenan" kiyi hakurizan dinga zuwa ina ganinki every week sannan kinga zaki samu kawaye su dinga debe miki kewata" nace" to kai kuma ya zaka yi idan bana nan?" yace " ya kuwa zanyi rahama? ai dole inyi hakuri da rashinki tunda ina son kiyi karatu ko in kara aure ne kafin ki dawo? na zabura daga kwance na tashi zaune hannuna na rawa na kunna fitila mai haske na dube shi fuskata a daure nace " aure? dama shi yasa zaka turani makaranta don kayi aure? dama samarin katagum sunce ba sona kake ba biyayyar iyaye ce gashi yau na gani. wallahi tashi yanzu ka maida ni gida ba zan kara kwana a gidanka ba tunda aure zaka yi" shima ya tashi ya zauna muna fuskantar juna yace" yi hakuri my sweet baby wasa nake maki ba zan sake yin aure ba insha Allah daga kanki na gama come on karki tada min hankai in kasa bacci mana"ya rungumo ni jikinsa yana lallashi kuka kawai na saka masa dama can kiris nake jira saboda bana son tafiya makarantar sai kuma gashi ya tsokano jangwam. yace " don Allah ki bar kukan nan nace maki wasa nake yi" cikin kuka nace" ga yammata nan suna zuwa har gida wurin ka ai rannan naga abin da kuke yi" ya dafe kansa yace" ya salam! shin rahama sau nawa zan gaya maki gaskiya ta ki yarda ne? wallahi ke kadai nake so a raina, kuma na fadi maganar aurennan ne don in gani kina sona sai gashi na gani tabbas kina sona har da kishi na ma tun da ba kya son inyi aure. yanzu dai mu bar wannan maganar mu kwanta kinga dare yayi sosai"nace fa yanzu na daina sonka ka maidani gida kawai! hankalinsa ya kara tashi ganin na kiyin bacci wai dole gida zai kaini gashi tsakiyar dare gari kuwa ba nan kusa ba. yace" shikenan gobe zan maida je kiyi hakuri kiyi bacci' haka muka kwana ina ta masa kuka ni fa a nawa tunanin na dauka da gske auren zai yi shi yasa zai kaini makaranta. Da gari ya waye ma ban hakura da duk da lallashi da magiyar da aliyu ya kwana yana min, don kuwa har na kammala shirin kayana a akwati shi kawai nake jita. hankalin aliyu in yayi dubu ya tashi idonsa yayi ja har wata yar rama naga yayi ta zullumin irin kukan da nake. ya dibe ni ina zaune a gefen gadon dakina na tasa akwati gaba yace" kin gama shirin kenan?" na gyada masa kai ya sake cewa" ke yanzu nan da gaske tafiyar kike so? nan ma kai na gyada masa ya dan yarfar da hannunsa tare da kada kansa gefe guda yace" ok, tunda haka kike so bari in nemo wanda zan hadaki da shi ya kaiki gida" nace" ni bana son kowa kai nake so ka kaini tunda kai ka kawo ni garin nan sai kayi masu bayanin zakayi aure" yace" wai ke baki san wasa bane? ni kam ba zanje katagum yau ba tunda ni kike son na kaiki sai ki bari sai na shirya sai mu tafi" nace" ni dai ba zan jira ka ba yau na ke so jeka ni koma waye yazo ya kaini ina so in ma mai saida kawuna ne kaga shike nan sai ya saida kaina ka huta sai kayi aurenka" ko uffan bai ce min ba sai ya girgiza kai ya fice abinsa. ina jinsa ya rufe gidan da makulli alamun ya fice kenan. ba shi ya dawo ba sai bayan azahar yana shigowa dakin na mike tsaye nace" ya zo ne?" ya dubeni yace " wa kenan" nace" wanda zai kaini katagum" ya zauna bakin gado ya riko hannuna yace " zo nan ki zauna kiji" ban yi mas musu ba na zauna kusa da shi ya fuskance ni sosai sannan yace" wanda zaku tafi tare na fasa hada ku shi ne na aike shi can katagum din yaje ya kira min baba sule(mahaifina kenan) kinga idan yazo sai inyi masa bayanin yadda kika tada min hankali daga maganar wasa kinga in ya amince maki sai ki bishi ku tafi" nayi tsam da raina ina kallon sa tsoro ya baibaye ni don kuwa tabbas ina tsoron babana idan nayi laifi sam shi baya daukan wargi balle idan yazo yaji abinda ya hadamu da aliyu tabbas kilama bugu na zaiyi.
[04/11 11:25 am] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da ciwo 15•••
????????????????????????????????
Na sauke numfashi nace" yanzu yaya aliyu meye na aikawa a dauki baba?dama so kake ya zo ya buge ni tunda yanzu baka sona na saka kaina a tsakanin cinyoyina na fara kuka ya matso ya dafa ni yace"meye kuma abin kuka?tunda kin matsa min zaki tafi gida kinga ai gara in kira baba kila shi kya ji maganarsa tun da nayi lallashin kinki hakura" nace, shi ke nan na hakura da tafiyar amma makarantar na fasa zuwa" yayi dan murmshi yace" bari dai baban idan yazo sai kiyi masa bayani, nikam makaranta nayi niyyar zuwan ki kuma ba zanyi asarar kudina da lokaci a banza ba. shin kinsan irin dimbin kudin da na kashe wajen nema maki makarantar nan? haba rahama ki tausaya min mana amfanin kanki na fa" nayi shiru ina tunani tabbas naga irin zirga zirgan da aliyu ya dinga min akan karatun nan kuma hakika amfanin kaina ne to ina laifin sa da wani ne ma yaushe zai yi min wannan gatan. cikin hanzari na mike na soma harhado kayan da na san ya siya min na tafiya makaranta har na gama kallo na kawai yake yi na dube shi na risina a gabansa nace" yaya aliyu don Allah kayi hakuri abin da nayi maka daga yau na daina, tashi ka kaini makarantar" kwalla na tsiyayo wa kunci na saboda nadama shima tausayi na ya kamashi ya janyoni na kwanta bisa cinyoyinsa ya shiga shafar gashin kaina yana kara lallashi na. yace" na yafe maki rahama ta amma ba zamu tafi ba sai naga kin saki jikinki kina walwala da dariya sannan zamu tafi bana son mu rabu yadda kike din nan hankalina ba zai kwanta ba" na dago idona muka kalli juna muka yi murmushi yace, naga daya saura na biyu, nace" to goya ni kaga daga yau zan dade baka goya ni ba" yayi murmsuhi yace" rahama shagwaba ho" nace"mhm ni dai goyani" ya juya min bayansa na haye har da kwantar da kaina nayi lamo tamkar wata baby. haka ya dinga zagaye babban falon gidan mu da ni har wani bacci naji yana kwasata. ya dubi agogo yace" kinga yanzu uku har ta kusa kinyi sallar azahar kuwa? nace " nayi tun karfe daya" yace" abinci fa kinci" nace, ban ci ba" yace" subhanallahi me ya hanaki cin abinci? fushi ko? ashe har yanzu baki daina fushi da abinci ba idan anyi miki laifi come on sakko muje kici abinci" na sauko muka nufi kicin ina kallon sa cikin sauri ya dafa min taliya da yake muna da stew ko minti ashirin ba'ayi ba ya kammla, muka dawi falo ya zaunar dani yana bani har na saba in ba shi ya zauna ya bani abincin ba ban cika ci ba, karfe hudu dai muka kammala shirinmu ya fidda kayan tafiya ta ya zuba a booth din motar sa jeep mai tint glass don yawanci in zamu fita ni da shi a wannan motar muke fita don kar a ganni makarantar da aliyu ya kaini ta masu kudice ta "ya"yan wane. bayan ya kammala min registration ne muka fito muna sallama ya dube ni 'karfa ki manta duk a takardunki na sa miki ke(single) ce baki da aure kin ji ko" nace" wai duk meye hujjar yin hakan" yace, babu wata hujja illa dai bana son a dinga baki wani matsayi wanda kuma shekarunki ba su kai ba kin gane?" nace " eh" . ya ci gaba da yi min nasiha kan yadda zan kula da kaina da yadda zanyi hulda da mutane kuma ya gargadeni da cewa kar inyi kawaye barkatai in rike sirrin dake tsakanin mu ni da shi. ido na ya ciko da kwalla na matso zan rungume shi ya rike hannuna yace" no, kinga kiyi hakuri next week zanzo in sake ganin ki" a haka muka rabu da ina zubda hawaye shi kan shi aliyu cikin tsananin damuwar rabuwa dani yake don dai gwarzon namji ne shi yasa bai taya ni zubda hawaye ba amma idon shi yayi ja alamin ya shiga damuwa. A wannan rana sam ban iya bacci ba saboda tunanin rabuwa ta da mijina sai kuma uwa uba gurin kwanan yau babu aliyuna a kusa balle in makale shi gurin kwanciya. gani da tsoron tsiya sannan gadon da nake a sama yake. na dai samu na rungume fill na dinga tsiyayar hawaye. Sati na dayaa makaranta aliyu ya ziyarci katagum wanda tunda muka yi aure yau kusan watannin mu uku amma zuwansa na biyu kenan da kuwa duk bayan sati bibbiyu yake zuwa. mutan gida aka tare shi da murna kowa sai ware ido yake ya ganshi da ni amma sai suka gan shi kwal. sai bayan sallar magriba sannan ya samu sararin kebewa da gwaggonmu ta dubeshi tace" aliyu wai yaya kanwar taka ne lafiya take ko? yayi murmsuhi yace" lafiya lau gwaggo duk tace in gaisheku" tace " bata yi maka rigimar sai ta biyo ka ba? a'a bata yi rigima ba ai yanzu ta fara yin hankali shagwaba ta soma raguwa" gwaggo tayi murmsuhi tace" yar nema wato ita dadi gidan miji har ta soma manta gida ko? to ba zan yarda takwace min kai ba tunda gashi kaima kafi wata guda rabon ka da garin nan, ina zan yarda" cikin wasa irin na kaka da jika gwaggo ke wannan maganar Aliyu shima yayi dariya yace" wallahi gwaggo yanzu ne na sami saukin rahama akan rigimar zuwa gida saboda yanzu ta soma zuwa makaranta, amma ko ranar da zata soma zuwa kwana mukayi tasa min kuka wai ita in kaita katagum, da kyar ta lallasu.

????????????????

Gwaggo tace" rahama kenan har yanzu har kasa ta makaranta?" yace" yanzu satinta guda da soma zuwa zaman gidanne ba dadi ita kadai gata da tsoron tsiya" tace" ai da ka samo mai tayata zama ne ko anan babu masu aiki ne? yace"uhm,uhm gwaggo gara dae ita kadai din masu aikin ne basu da kirki. kinga yanzu ba abinda rahama baya iya ba na aikin gida ta iya girkin zamani ba abinda bata iyaba"tace" iye kace shi yasa ta boye mana kai. gaka nan fa ka kara kiba abinka da zama kamar bature hala itama tana nan ta bindige? yayi dariya yace, "ai gwaggo idan rahama tazo sai an sare wannan yar kofar taki don kuwa fadin yayi mata kadan ta zama giwa abinta" tace masha Allah kaci gaba da kula da yar uwarka ka kula da maraicinta kaga dai yarinyace komai sai a hankali zata sani musamman zanatakewar auren abu ne mai sauki mai wuya sai ka kula haka aliyu yayi kwana kinsa biyu a katagum duk rabin hankalinsa yana guna duk da yake ina makaranta amma sai yana ganin tamkar wani abu ya same ni bayan nan. a daddafe aliyu ya iya hakurin wata guda bai ganni ba kasancewar principal din makarantar mu abokin sa ne shi yasa yazo ganina na ga ya tsuke fuska yana kallo na tabbas na san baya rasa nasaba da irin ramar da nayi. principal ya fita ya barmu a ofis din yana fita na nufo aliyu idona cike yake da hawaye ya ware min hannuwansa na fada jikinsa ina kuka ya tallabo fuskata yana duba na shima fuskarsa kumshe da tausayina"rahama me zan gani haka?" ya sa hannu yana taba kashin wuyana wanda kuwa da bani da shi ya sake cewa" meye wannan rahama? ba kya cin abinci ne?" na girgiza kai nace" wallahi yaya aliyu karatu da wuya gashi ni kadai babu kai kullum tunaninka nake yi ni dai mu tafi gida ba zan iya ba"hawaye ya zubo a kunci na ya fiddo handkerchief yana goge min hawayena yace" come on, kiyi hakuri dole ne za ki sha wuyar karatu tunda ba daga farko kikafara ba,amma na san insha ALLAH kafin karshe na term dinnan zaki gane wasu abubuwan idan kuma kika dawo gida zan dinga miki lesson kinji? sai maganar tunani ki daina yi zai iya jefaki cikin matsala ki tsaida hankalinki gurin karatu kawai ko ba kya son ki zama doctor rahaama ne? nayi murmushi nace " ina so mana amma ni......sai na kwantar da kaina bisa kafadarsa yace"amma ne?nace" amma ni ka dinga zuwa ina ganinka every week" yace" ok,i will try and do my best in ga nazo every week yanzu me kike so?" nace" babu komai duk provision dina suna nan ko kwata banyi amfani da shiba" yace" ashe ba kya cin abinci kenan shiyasa kika yi dan wuya" nace"ina ci tunani ne kawai" yace" to in na dawo naga wannan kashin wuyan zamu yi fada da ke ina san inga kamar da". Ranar da aka yi mana hutun zangon karatun mu duk na bi na kosa aliyu ya zo dauka ta. muna zaune ni da kawata maryam sulaiman kowa yana jira azo daukansa, kasancewar sunan babanmu daya shi yasa muka yi abota kuma na lura halayyarmu zata zo daya. dakinmu daya da ita asalinta haifaffiyar zariya ce, amma aiki ya kawo mahaifinta lagos. maryan ta girime ni da shekaru kusan biyu. na dubi maryam nace" ni wallahi maryan na gaji da zaman makarantar nan duk na kosa yaya aliyu ya zo ya dauke ni mu tafi gida gara ku kun saba da makarantar" tace" wane sabo ai komai dadin makaranta gida ya fishi. wai shin rahama wannan aliyun da kike damu na da zancensa shi menene naki" naga kullum zancenki baya wuce na yaya aliyu" nayi murmushi nace"yaya nane kawai"ya"ya maza muke ni da shi shakuwa ce kawai kika ga yasa ina yawan ambatonsa, muna cikin hira ne na hango motar yaya aliyu tayi fakin a bakin get din makarantarmu tun kafin ya fito na mike cikin hanzari na isa gurinsa yana hangoni ya bude motar ya fito cikin fara'a muke duban juna yace" iye yan makarantar ba. kinga yadda kika yi kyua kuwa kinyi " yar kiba abinki ko kefa da duk kin damu kanki kin rame nima kin sani cikin zullumi.[04/11 8:38 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da ciwo 16•••
????????????????????????????????

Nayi murmushi nace"ai naji shawararka na daina tunani sai karatu kawai" yace "yauwa kin kyauta. ina kayanki suke mu tafi?" na koma gurin maryam na sanar mata da zuwan aliyu ta tayani kwasar kayana muka zuba a mota sannan ta matsa suka gaisa da aliyu na dube shi nace ya aliyu wannan itace kawata da nayi sunan ta maryam sulaiman" ya dan dubi maryam yace" sannunki maryam ya kika ji da kawar ki mai shagwaba ko bata maki? tayi murmushi tace" tana yin shagwaba sosai komai kuka tace gurin yaya aliyu zata tafi hala ita ce autar gidanku? yace" ai rahama ta wuce auta duk gidan mu ita kenan mace kwaya daya shi yasa muke ji da ita tamkar rai dole ku ganta shagwabbabbiya don Allah ku dinga hakuri kunji" mun danyi hira sannan na shiga mota muka yi sallama da Maryam har ta juya zata tafi sai ta dawo tace' au rahama na manta baki bani address din gidan naku ba' na dan yi jim alamun tunani yau dai karya ta kare aliyu ya ari baki na ya riga ni cewa"ai karma tayi wahalar baki address don gobe garin mu zan kaita acan zata yi hutu kinga kar kizo baki same ta ba" tace " ai ko ban same ta ba sai mu gaisa da matarka tun da tace min gidan ka take zaune kaga nan gaba na huta da neman gidan' yace" ina jin duk gaba daya da matar tawa zamu tafi ki bari idan muka dawo sai in zo in dauko ki a gidanku in kawoki namu gidan kinga kin huta da bin address" tace" to shike nan sai na ganku" muka ja motar mu ina daga mata hannu. ya dubeni yace" amma rahama me yasa daga yin kawa zaki yi gangancin bata address din gidanmu? kin san fa gidan mu ba gidan zuwan mutane bane. sai dai naji dadi da kika shaida mata a gun matata kike zaune ashe kina da wayau"nayi murmushi nace" wallahi yaya aliyu maryam tana da kirki ne shi yasa kaga haka, amma ni kaina sam ba zan iya bata address din mu ba tunda gidanmu sirri ne" yayi dariya yace" ko?" nace" shakka babu" tun a cikin garejin mota da yyi prking muka fito ya soma hadani da jikin sa na dubi kwayar idonsa ina murmushi yace wallahi rahama nayi missing dinki sosai a gidan nan har bana jin dadin zaman gidan, balle ma idan dare yayi na kwanta ni kadai babu ke babu yar shagwabarki yana lakuce man hanci  nace" yau gani na dawo ai sai mu bude sabon babi  yayi murmushi yace inyeh! yana makale dani a gefensa kamar wani zai kwace masa ni. tunda muka dawo aliyu bai je ko ina ba yana manne dani ina zuba masa shagwaba tare da bashi labarin yanayin makarantarmu. sai da akayi kiran sallar magriba sannan ne ya nufi masallaci ni kuma nayi hanzari na nufi bayi nayo wanka tare da dauro alwala. ina idar da sallah na caba kwalliya da wata atamfa dinkinta ya fiddo min da kyan fasalina. ina zaune a tsakiyar gadon baccin dakin yaya aliyu na baje littattafan da na zo da su daga makaranta duk gurin Maryam na samo su da yake ita ma"abociyar karatun littattafan hausa ce da novel anan ne fa kaina ya dada wayewa na san ko ni wacece da matsayina a gidan miji na. akwai wasu abubuwan dana karanto amma ni har yau basu taba faruwa tsakanina da miji na ba. yanzu kam babu abin da ban sni ba na harkar auratayya, oh! ashe shi yasa yaya aliyu kwanaki can yayi ta min dariya da nace zan ci abinci ciki na yayi girma na haihu ashe abin ba haka ba ne da sauran aiki a gabana. to shin wai me yasa shi yaya aliyu bai nema hakkinsa a guri na ba wanda ko duk cikin littattafan da na karanta angwayen littattafan irinsa basa saurarawa amarensu balle ni gani yanzu wata na bakwai gidan aliyu ko zancen bai taba min ba. to ko baya so na ne? ko kuma yana tausayi na ne tunda ni yarinya ce? amsar da ban gani ba kenan har yaya aliyu ya dawo sallar isha ya iske ni na tasa littattafai gaba ina aikin tunani shima gadon ya hawo ya zauna kusa dani ya shiga duba littattafan ina lura da fuskarsa da ta cika da mamaki ya dubeni yace" rahama ina kika samo wadannan litattafan?" nae"gurin maryam na samo su na kusan gama karanta su ma" yace" wato ba kwa karatu sai na soyayya ko" nace,"wallahi muna karatu sosai don kada inyi tunani ne kawai yasa na koyi wannan karatun kaima kasan nayi kokari tunda ta biyar nazo cikin mu hamsin da biyu nan gaba ma ta daya zan zo" yayi murmushi yace" amma sai kin daina karanta wadannan littattafan" na miko masa wasu guda uku nace"duba fa wasu duk na addinine ko baka son in dada sannin yadda zan zauna da kai da yadda zan kula da hakkinka?" maganata ta dan jefa shi cikin tunani yau kam ya san dole ya fayyace mun irin zaman da yake son muyi don kar in shiga damuwa. dama yasan dole in koyo wasu abubuwa da nake da duhu a kansu a makaranta. ya duba su kusan minti uku suna hannunsa sannan ya numfasa ya dube ni yace" zo muje ga abinci can muci dama yau nake so idan kindawo muyi wata magana dake" nace" to" na tattara littattafan ya mikar da ni tsaye na tashi muka sauko falo muka ci abinci.

????????????????

Sai da muka yi shirin kwanciya har ya ja bargo ya lillube mu sai naga ya tashi yace, nima in tashi na zauna muna fuskantar juna ya dubeni sosai yayi dan tunani sannan yace" rahama nasan komai daren dadewa dole akwai ranar da zaki fahimci cewar ban baki wani hakkinki na aure ba, to yanzu na san ko ban fada ba kin fahimci haka kuma tabbas na san akwai zargi a zuciyar ki na dalilin da yasa ban baki wannan hakkin ba, to yau na kudirta zan fayyace maki dalili na sannan kema naji naki ra"ayin in kin amince min shikenan in baki amince ba to yau zan baki hakkinki na aure" kunya da mamaki suka cika min ciki na dukar da kaina ina wasa da yan yatsuna ya cigaba da cewa "a rayuwa ta babu macen da nake so har cikin raina irinki shi yasa ba zan so inyi wani abu na danne miki hakki ba,sannan ba zan so inyi wani abu da zan zamo nan gaba ya cutar da rayuwarki ba ko in ga kin shiga cikin wahala ba shi yasa nake tausaya miki na kasa kusantar ki at ur age gsky ba zan so ace kin haihu nan da shekara daya ba duk da yake nasan har yanzu baki fara jinin al'adarki ba ko kin fara?" kaina a sunkuye na gyada masa kai alamar na fara. gabansa ya buga ras!ras! ya dubeni yace' kin fara yaushe? nace, lokacin ina makaranta wannan ciwon da nayi har aka aiko maka kazo dinnan shine ya wahalar dani" ya numfasa yace, sau nawa kika yi? nace" sau daya ina jin ma yanzu na kusan yin wani amma wata likitar makarantar mu tace tunda yanzu na soma kila sai bayan wata daya ko wata uku ko shekara zan kara ya danganta da yanayin jiki na" jikin aliyu yayi sanyi ya ja dogon ajiyar zuciya yace kinga wannan shi ne nake tsoro to ashe ma kin fara. yanzu idan Allah ya kaddara a yau idan na sadu dake zaki iya daukan ciki tunda yanzu mahaifarki a shirye take ta dauki ciki kinga nan da wata tara haihuwa a wannan lokacin shekarun ki ba zasu kai sha biyar ba. gaskiya ina tsoron karki sami matsala wajen haihuwar saboda karancin shekarun ki dhi yasa na dau alkawarin a zuciya ta zan kyale ki har sai kin cika mace sannan zan dora maki lalurar aure ko kina son ki sami matsala irin na kawarki jummai? kinga itama gurin haihuwa ne ta sami matsalar yoyon fitsari saboda karancin shekaru in kuma kinga babu damuwa shikenan yau sai in baki hakkinki" tsoro ya mamaye min zuciya dama ni a duniya babu abinda nake tsoro irin haihuwa saboda yadda naji ana cewa mata na shan wahala. Sannan uwa uba abin da ya sami jummai ashe karancin shekaru ke kawo haka, to ashe nima hakan na iya faruwa a kaina, tunda ta girme ni, da kusan shekara ido na yayi zuru zuru don tsoro da zullumi na dubi aliyu nace" ni dama bance maka ina so ba wallahi na amince ko nan da shekara goma ne" yayi murmushi yace"a'a ba shekara goma bane shekaru biyar na yi alkawari lokacin auren mu kin san shekarunki sha uku yanzu gashi watan mu bakwai da aure kinga kin kusa shekara sha hudu to ni aliyu na dau alkwarin ba zan nemi hakki na na aure ba sai kin cika shekara sha takwas kinga lokacin kin kammala karatunki kina shirin shiga jami'a kuma ina ganin a lokacin ne zaki zama cikakkiyar mace yar shekara sha takwas kin isa haihuwa kin isa komai kin amince ko" nace" na amince 100% amma ina ganin anya zaka iya cika wannan alkawarin?kasan alkawari yana da saukin dauka amma cika shi shine wuyar" yace" haba yaushe zan kasa cikawa ni fa nayi alkawarin sai dai in kece zaki sa in karya" nace" miye nawa a ciki ai ni nawa mai sauki ne kasan mu mata akwai mu da kunya da kawaici balle akan wannan abin balle naji ana cewa da farko da wuya ni kam na san kila ma mutuwa zanyi" aliyu ya tintsire da dariya har da kwalla yace" amma rahama kin cika matsoraciya ashe ranar sai munyi dan karamin yaki a gidan na?" ina dariya nace "kasan yakin badar to shi za ayi kai dai Allah ya kaimu shekaru biyar din Ya ce Amin.Nan fa na shiga kogin tunani shin Anya taya aliyu zai iya cika alkawarin mai wuya kuwa?kai da kamar wuya don a irin littafan da nake karantawa na fahimci duk maza basu da hakuri da juriya akan wannan naga akan sha takun saka tsakanin su da matayensu idan suka ki basu hakkinsu naga kuma irin damuwar da mazan ke shiga idan matayensu suka haihu kwana 40 ayi ta rigima da su balle ni nawa mijin ba daya kanwar biyu ya daukarwa kansa alkawarin shekara biyar to ko neman mata zai dinga yi? ko kuma bashi da lfy ne?Don naji wasu mazan sai ace basu da lfy,to ko aliyu yana da matsalane ya boye min?
[04/11 8:57 pm] ?+234 802 874 8204?: ????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da ciwo 17•••
????????????????????????????????

Zumbur na tashi zaune tare da yaye bargon da aliyu ya rufa min na laluba gadon mu banji shi ba ban san sanda ya fita ba ashe ina aikin tunani ya shiga bayi. Ya fito yana daura belt din rigarsa yana ganina a zaune naga ya dan ware ido yayi min murmushi yace,kina nema na ne? nace eh yazo ya zauna kusa dani ya ce gani menene?Nace shin aliyu ko baka da lfy ne kake boye min?yace lafiya ta kalau me kika gani? nace gani nayi duk namiji mai cikakkiyar lfy ba zai daukan ma kansa wannan alkawarin ga matar sa ta sunna ba. Ya dubeni cikin mamaki yace haka kike gani? Lfy ta lau tausayinki ne kawai zai sani in tursasa zuciya ta hakura da ke,nace to yaya zaka yi da sha'awata idan ta bijiro maka?ko kana menan mata ne? A firigice ya dubeni baki bude yana mamakin irin zantukan da ke fitowa baki na yace yanzu rahama harkin fara zargi a ranki wlh koda wasa ban taba rayawa a raina inyi masha'a da diyar wani ba aiko bana tsoron Allah dole inji tsorin cutar da ke yawo cikin alu'mma (HIV) Balle tsoron Allah na nan lullube a zuciya ta sannan ina tsoron kar abinda nayiwa yar wani ayima tawa dan fadan Allah ne duk wanda yayi zina da yar wani to hakika za'ayi da yarsa ko kanwarsa ko mamansa tunda suma uwayen wasu ne, gara mutun ya tsaya inda Allah ya aje shi. Ke na gaya miki tausayin ki yasa na kyale ki sannan akwai wasu kwayoyi da likita ya bani nake sha duk lokacin da sha'awar jima'i ya taso min kuma kin san ina yin azumin litinin da alhamis duk don ya karemin sha'awata ina fatan kin gamsu? Na gyada kai nace na gamsu amma ina tsoron kar ka kasa cika alkawarin nan bayan na sakankance kazo ka tubure min. Yace to yanzu me kike son ayi?nace muyi alkawari a rubuce babu mai karya shi sai wa'adin shi ya cika,Ya ce wannan mai sauki ne kawo biro da takarda guda biyu.Na tashi na kawo masa ya amsa yayi rubutu kamar haka"Ni aliyu nayi alkawarin bazan nemi hakkin aure na a gurin matata rahama ba har sai nan da 5yrs sbd wasu dalilai masu amfani a gare mu ni da ita. Itama ta amince da wannan alkawarin Allah bamu ikon cika shi amin.Da ya gama rubutawa ya bani na karanta yace yayi haka nace yayi sannan yasa hannu nima nasa ya sake rubutawa a wata takardar ya saka a ambulan biyu muka sake sa hannuwanmu kamar yadda yara ke kulla alkawari. Haka mukai bacci zuciyoyinmu cike da tunanin wannan alkawari babu ma kamar ni da nake ganin abin kamar a mafarki.Tunda na dawo yau sati daya nake wa aliyu naci da magiyar ya kaini katagun inga iyaye da yan uwa, amma fafur ya kiya sai wani hutun tun ina masa kuka har na hakura. Ranar wata juma'a lokacin sati na biyu da dawowa hutu aliyu ya tafi gun aiki ya kulle gidan kamar yadda ya saba ina cikin baccin rana wani azababben ciwon mara ya tashe ni daga bacci.A firgice na tashi ina nishi na rike marata gam gam ina kiran sunan yaya aliyu kan kace kwabo duk na fita hayyacina. Aliyu bai dawo ba sai bayan sallar juma'a tun daga falo ya shiga kwala min kira yasan duk lokacin dawowarsa a falon kasa nake zaune don in tarbe shi amma sai yaga falon wayam yana isowa dakin baccin mu ya ganni a makure cikin bargo ina makyarkyata nima abinka ga yar shagwaba ina ganin sa na saka kuka ya saki jakar dake hannunsa ta ofis yayo kaina da gudu ya dauko ni cak ya dora bisa jikinsa nan fa yaji jikina zafi rau ya sake rudewa yace Rahama menene?Me ke damunki yau na shiga uku nabar yar mutane zata mutu.Ina lafe a jikinsa hawaye na zirara a ido na yi magana a hankali nace wayyo yaya aliyu zan mutu marata ciwo da kaina don Allah ka kaini asibiti kar in mutu".Hankalinsa ya tashi nan da nan naga idonsa yayi ja yace zaki iya tashi in kaiki asibiti?Nace bazan iya tafiya ba marar ta rike sosai kaini bayi inyi fitsari.Ya daukeni cak zai kai bayi anan ne yaga jini ya bata gadonmu face face sai ya fahimci jinin hailatane yazo min shine dalilin ciwo na.Ya kaini bayi ya sani a baf nayi fitsari ya debo ruwan hita ya ciremin kaya na yai min wanka nima tunda jinin ya zubo sai na dan sami relief na ciwon.Muka fito ya canza min kaya ya zaunar dani bisa kujera ya kwashe zanin gadon da blanket ya kai toilet ya dawo ya canza sabon zanin gado ya rufeni ya rankwafo da fuskarshi zuwa kunnena yace"bari inje in samo maki magani a asibiti ciwon ya lafa ko?Nace eh ya lafa ba kamar dazu ba yace to sannu Allah ya sawake ya sumbaci kumatuna ya fice. Haka na kasance ina shan magungunan da Aliyu ya amso min gurin doctor tare da kulawa ta musamman daga gareshi har na kare kwanakina biyar na al'ada. Yanzu shekarata guda cif gidan aliyu, harkar karatuna tana ta bunkusa tare da taimakon Allah da na mijina, har wannan lokacin ban samu aliyu ya kaini katagum ba sai a wannan hutun da na zana jarabawata ta JSCE shine yace zamu tafi. yadda kasan anyi min bushara da gidan aljanna haka naji duk na kosa washegari tayi na tafi a wannan daren aliyu ya dauke ni a mota muka tafi yin shopping har saloon ya kaini suka yi min gyaran gashi. bamu muka dawo gida ba sai kusan sha daya na dare. washegari tun da na idar da sallah asubahi muka kammala shirinmu muka kama hanyar bauchi . a cikin mota aliyu sai dada jaddada min yake akan in rike sirrin alkwarinmu kar in bari kowa yaji ko da gwaggo ce.

????????????????

Mun iso katagum bayan sallar la'asar gidanmu ya kaure da murnar gani na kowa ya dinga fadin albarkacin bakinsa kan irin kyan dana kara ga girma da nayi na ban mamaki.ina kishingide a dakin gwaggo bayan na idar da sallah isha muna hira tace" wai rahama wannan saurin girma iina zaki kaishi ne, me maigidan namu yake baki ne duk kin canza kinyi jajir abinki? nayi dariya nace" gwaggo wani irin abinci mai dadi tsofaffi basa cin irin sa sai mu yara dana sani na taho maki da shi" tace uhm,uhm , rike abinki wane ni tsohuwa da cin wannan abinci, wannan sai irinku Allah dai ya budi ido lafiya" wato su a tunanin su gwaggo ciki gare ni basu san ni ko hanyar garin da cikin yake ban sani ba' nayi murmushi nace" ji gwoggo ido na ni ai a bude yake kamar wata makauniya" au baki ma san budewar idon ba" to ciki gare ki in ma noyewa kike yi dubi jikin ki duk yayi danye danye ga nonuwanki duk sun ciko ai alamu ne na bayyanar cikin fari. Na dan lumshe idona ina dariya, gwaggo tace au dariya ma kike min ko? yar nema sai ranar fitar abin tazo ido ya raina fata ina ganin ma anan zance ya bar min ke sai kin gama wanka kya koma ko kuma ni ku tafi dani don gaskiya ba zan yarda ya tafi da ke da cikin nan ba gara da babba a kusa da ku" na dan tashi zaune nace' wai gwaggo kina ta hakilon zance an gaya maki ciki gare ni? wallahi bani da kmai" tace" ke ban son sakarci har mu iyayenki ma boye mana cikin zaki yi? in shi mijin naki bai sani ba to bari ya shigo in tambayeshi" na kwanta kan gadon gwaggon na ja lallausan bargo na dukunkune amma fuskata na waje a haka mukaci gaba da hirar domin ciki na naji yana murdawa zuwa marata a raina nace" toh abin yazo kenan na wata wata? muna hira ina dan cije lebe ashe gwaggo ta lura tace" ke lafiya" nace mata"wallahi cikina ke ciwo ta mike zumbur tayi waje ta sa aka kira aliyu cikin hanzari ya shigo ya zauna a gefen gadon da nake yana tattabani yace" menene rahama" ko lokacin period dinki yayi ne? na gyada masa kai alamun eh yace" ina magungunanki suke ina ganin in kika shah zaki samu relief" nace" duba cikin jakata ko cikin dan kit din can suna a leda" ya tashi da hanzarinsa ya dubo magungunan ya tadani zaune ya debo ruwa ya shiga fiddo magungunan zai banu gwaggo tana gefe tana kallonmu ta dube shi tace" wadannan magungunan da zaka dirka mata na menene? ba naji likitoci suna hana masu juna biyu shan magunguna barkatai ba" ya juyo yana duban gwoggo cikin mamaki yace"gwoggo wa ya gaya maki ciki ke ga rahama? kai gwggo kin cika abun dariya" tace " au kaima zaka maishe ni sabo tumakin ce irin yadda matarka tayi min? in ku duk kun taru kun zama sakarkaru baku san ajiyar da Allah ya baku ba to yau ku sani rahama dai ciki gareta kuma ina tsammanin cikin nan yayi wata biyar zuwa shida dubi jikinta duk ya canza, Aliyu yayi murmushi yace" wallahi gwoggo bata da ciki jin dadine kawai yayi wa rahama yawa shi yasa kika ga tayi haka" tace" eh lallai naga jin dadi gashi nan ma ina gani" muka yi dariya aliyu ya fiddo magunguna ya bani na sha sannan ya kwantar dani ya dan rankwafa yana min rada a kunne yace" ko zaki bini can daki na mu kwana? ko kuma ni in zo nan mu kwana" na dan harare shi nace" naki kana son ace bani da kunya ne" yace" zaki iya kwana ke kadai a gadon nan gashi baki da lafiya?" nace" zan iya mana in ma ciwon ya tashi baga gwggo ba" yace" amma kinsan zaki fi jin dadi idan nine a kusa dake ba gwoggo ba" nace" to ya zanyi yaya aliyu tunda ba a gidanmu muke ba" gwaggo tace" kai don ALLAH ka zo ka wuce ka kyale yarinyar nan ta samu bacci da wanne zata ji, da ciwon da ke damunta ko da fitinarka, shi yasa nace ai nan zata zauna ta haihu ina dalilin wannan binbini.????????????????????????????????????????????????
•••Alqawarin da ciwo 19•••
????????????????????????????????

Idona ya dan kawo kwalla nace ni har ga Allah bana bukatar wannan abin a raina kuma ni ban ce ka danne min hakki ba ni don in rabu da ciwon nan shi yasa nace haka, amma tunda haka kake gani to kayi hakuri insha Allah ba zan sake furta wannan maganan ba zanci gaba da dauriya da wannan ciwon har Allah ya kawo min iyakar sa sai naji kuka ya kufce min na tura kaina jikin cinyoyina naci gaba da zubda kwalla hankaln aliyu ya tashi yayi fakin motarsa a gefen hanya yasa hannu ya dago fuskata tare da kiran sunana nan fa ya sake dimaucewa ganin ina kuka kasarika ya Shiva lallashina har dai na hakura ya bude jaka ya dauko hoda ta ya shafa min a fuska wai don kar muje gidan su kabir suga fuskata a kode. Na dube shi nace don Allah ka kaini gidan mama bintu in gaisheta tun lkcn bikinmu rabo na da ganin ta "kanwar inna ta ce" Yace to. Na ga tsalle da murna gun sakina data gan mu ni kam Allah Allah nake in dauki dan bebin data haifa lkcn ina makaranta aliyu ke gaya min haihuwarta gashi har yayi wayau yana zama.Na sure shi daga kan dan keken zaman shi na rungume shi muka zauna a falo muka fara gaisuwa. Aliyu ya dubi sakina yace Madam wai ina oga ne ko kin boye shi ne? tayi daria tace wace ni sakina wannan sai amare su rahama sune masu boye ango daga shekara sai shekara ake ganin sa a bauchi. Yar wayar ma ya daina yi mana. Muka tintsire da daria nace wato sakina laifi na kike gani kenan ko? Bai shaida muku ina makaranta bane. Ni ma kaina yayi min wuyar gani tunda boarding nake. Sakina tace iye kice ke yar gatace in banda dan gata wake boarding ni da nawa ogan zai yarda ai da ABU zaria ya barni na tafi amma sam yaki. Aliyu yace ai gara da yaki ina amfanin zama ba mata ni kaina na dawo ina dana sani karfin hali kawai nake. Kabir ya budo kofar dakin baccin du ya fito sanye da rigar wanka(bathrob)yana rike da dan karamin tawul yana goge sumar kansa,yana yin arba damu ya saki wani murmushin dadi yace,iye mutanan ikko ne?kuma kun rama ne zuwan unexpected ba sanarwa. Suka dan rungume juna sannan suka zauna, sakina ta shiga jero mana kayan lashe lashe muna ci muna hirar yaushe gamo. Kabir ya dube ni ya dubi aliyu sannan yace Aliyu meke faruwa da rahama ne?naga tayi fari tas kamar mara jini ko ka harbeta ne? suka tintsire da dariya ni kam kunya ce ta kamani,aliyu yace wlh tun jiya da muka zo take ciwo haka muka kwana babu bacci shine fa muka zo ganin likita yanzu ma daga asibiti muke. Suka ce subhanallah me ke damunta? Yace gata nan dai ciwon ciki da mara shine matsalarta every month ni har tausayi take bani idan lkc yayi. Da yake su kabir wayayyune nan take suka gane matsalata, Kabir yace Allah ya sawake ai ni nayi zaton ciki ne ashe har yanzu kuna nan kuna yanga. Wannan matsalar irinta sakina ta dinga samu tun kafin in aure ta da mukayi aure kuwa two months yayi yawa sai kaji shiru babu ciwo ashe mahaifar da abinda take so ya kalle ta yana kashe ido. Duk mukayi murmushi ita ko ta dan kauda kai. Aliyu cikin damuwa yace kunga kuda yake kun san kan abin gashi ina fadar matsalar kuka gane amma su gwoggo suna can sun sakani a kwana su ala tilas wai ciki rahama ke gareta da na bata yan magungunan da take sha na saukin ciwon sai sukace na zubda cikin na bata magunguna ba tsari tun da suka gata fara bleeding kuma ita dama rushing yake mata yanzu suna can cike da ni na zubar musu da cikin jika. In banda abin su ni da nayi abin ai zan fi su son shi da tattalinshi. Kabir yace, Halin tsofaffin mu kenan basu san gaskiyar abuba su hau kai su zauna yanzu wannan ai Allah kadai zai fissheka. Sakina tace to ke rahama baki gaya musu gaskiya ba? Nace, wlh tun a daren jiya na ke gayawa gwoggo gsky amma sai tace karya muke yi nida mijina wai sakarcin kuriciya ne har Allah ya bamu kyauta bamu sani ba. Suka yi murmushi kabir yace gwoggo ho ba dai rigima ba yanzu duk haushin ku xasu dinga ji.sai karfe uku muka nufi gidan mama bintu tayi murna kwarai da ganinmu har itama tadan tambye ni cikin hikima ko ciki gare ni na gaya mata gsky ta muka rabu muna kewar juna. Koda muka dawo daga asibitin bauchi hnkl su gwoggo bai gama gaskanta zancen mu ba suna ganin dai kawai nayi bari ne kila cikin rashin sani muka yi sakaci cikin ya zube, kwanan mu biyar muka koma legos. lkcn dana shiga ajin karshe na secondary a wannan lkcn shekaruna 17 duk inda hadaddiyar mace ta kai na wuce nan. Na cika nayi dam komai na jikina ya amsa sunansa. A wannan lkcn kam aliyu ya shiga ukubar rayuwa tun kafun wannan lkcn yake dandanan azabar alkawarin daya daukarwa kansa. Tun yana min magiya akan mu karya alkawarin nan har ya hakura, wani lokacin cikin dare zan farka in iske shi yayi tagumi ya kasa bacci ni kam na san dalili gani da son jikin tsiya bana kwanciya sai a jikin aliyu ko abinci zanci sai a cinyarsa zan zauna in kuwa zaune muke sai na rabu da jikinsa sannan nake jin dadi.Tunda na fara rikita masa jiki ya nemi ya dinga nisanta ta amma ina na riga na saba dole ya dinga hakuri da halina. Yau ma na gama aiki ke nan a kicin na shigo daki don in watsa ruwa na cire kaya na na Fada toilet ban ko dauko towel ba saboda nasan ni kadai ce dan lokacin dawowar ya Aliyu bai ma yi ba na shiga na maido kofa na rufe na taka wurin kwqmin wanka kawai naji an riko ni ta baya an matse ni tsam tsam na kwalla kara wayyoh innalillahi wainna ilaihi rajiun way...naji an rufe man baki ke rshma nine fa ya aliyunki ne ya juyo da ni sannan na dan nutsu nace yaushe ka dawo ban sani ba zan Fara zuba. Shagwaba ta na tuna ba kaya jiki na shima kuma naji haka ai nan na rude ina ture shi da son raba jiki na da nashi shi kuma yana kara ruko ni ya Aliyu dan Allah ka kyale ni in fita an ki a kyale ki wa yace ki shigo nace wlh ban San kana ciki ba ai ka sani dai sai ma kara matse ni yake yana sansana tada shasshafa man jiki ni kuwa duk na rude ba kaman ma da nake jin jikin mu na haduwa kowa zindir haihuwar sa tsoro kunya duk ya dabaibaye ni shi kau bai ma San inayi ba sai na Fara masa kuka ganin bai jin magiya kuka na gaske kaman yana zaran raina da kyar ya sake ni yaja ni wai muyi wanka tare tunda wanda yayi ya baci nan ma na tubure saboda na gama tsorata na jawo towel na daura na baro shi ya gama. Sannan nayi nawa bayan faruwar hakan sai da yayi aikin lallashi sannan na koma normal dan ina tsoron yace zai kusance ni.

????????????????

Ranar wata juma'a a lokacin mun sami hutun skul bayan saukowa sallar jumaa aliyu ke zaune a falonmu na kasa ni kuma ina can bayi ina wanka dana fito na caba kwalliya cikin riga da wando jeans ne wandon rigar kuma t shirt ce har belt na nema na tsuke. Ni kaina nasan nayi kyau, kuma nayi shigar tsokanan fada, shigar dake tada ma aliyu hnkl, duk ya kidime. Ban daura dankwali ba illa na zubo gashi na ya sauko a kafaduna na feshe jikina da turare kusan kala biyar sannan na sako flat shoe na nufo falo gurin aliyu ina tafe ina rangwada tare da rausaya jikina ga cingum mai dadin kamshi ina taunawa a baki na.Na fara tako steps din bene ina saukowa,Kamshin turare na shiya fara sanar masa nice a tafe sbd bugar hancinsa da yayi. Ya tsaida karatun jaridar da yakeyi ya tada kai ya dubo sashin da nake tahowa ya dan lumshe idon sa yana kallo na ni kuma na sakar masa mayaudarin murmushi har na karaso wurinsa. Ya sake duba na sama da kasa, sannan yayi ajiyar zuciya yace"my sweet baby kinyi bala'in kyau sai dai ina neman alfarma don Allah,Na rausayar da kwayar idona cikin sigar jan hnkl sannan na zauna bisa cinyoyinsa na sargaho hannuna a kafadarsa nace alfarmar me kake nema yaya na? Ya danyi shiru sannan yayi magana cikin damuwa yace Don Allah rahama don son annabi ki tausaya min ki mallaka min gangar jikinki a daren yau na miki alkawari ko mai kikeso a duniyan nan zan mallaka miki in dai baifi karfi na ba, Na dan bata fuska kadan ina dubansa nace" haba yaya aliyu sau nawa kake son muyi ta tada zancen nan? ina ce yau shekarunmu kusan hudu da aure? duk iya hakurin da kayi na shekarun nan baka gaza ba sai na shekara daya? ni na fa yadda na hakura da ciwon mara ta na tsawon shekarun nan dole kaima ka jure ina ce kai da kankaka dauki wannan alkawarin? ko ko so kake mu zama munafukai saboda rashin cika alkawari?" idon aliyu ya kadu yayi ja ya dubeni cikin tausayin kansa yace" na san ni na tsiro da wannan alkawarin amma yau dole ki hakura mu karya shi ki tausaya min wallahi na shiga tsananin ukuba saboda rashin samun hadin kanki, wannan ALKAWARIN DA CIWO!

Ranar nan haka na masa zama office na dawo gida na sakar ma kaina ruwan sanyi ko naji sauki ke kuma kika kara jangwalo man kuma kika hana ni samun sukuni da ke kina gani dai lokuta da dama da kyar nake samun bacci gaskiya ban iyawa dole mu aje wannan ALKAWARIN DAn yana da matukar CIWO!!!
adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *