Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, August 26, 2019

BAQIN CIKI COMPLETE (list of hausa novels)

adsense here
BAQIN CIKI COMPLETE (list of hausa novels)


HADA DOCUMNTS BY
ESHAAT SMILER HOM OF HAUSA AND


BAKIN CIKI 1***1 Sarautar Uban dawaki babbar
sarauta ce a garin fandagori can cikin jihar naija.
Babban gari ne wanda al'ummar cikinsa suka
bunkasa wajen noma da kiwo. Gidan uban dwk
Alh Awaisu Malami katafaren gida ne cike da
zuri'a masu yawa na kannensa guda 2 kuma
shine babbansu kat! Sassan sa yafi na kowa
girma da tsari ginin zamani. Matarsa daya Haj
Halima da yaya maza uku a jere. Abdulkadeer,
Abdulkareem da Abdulrahman sai kandensu "ya
mace tilo a cikinsu Sakina, sunan mahaifiyar
uban dwk gareta shiyasa suke kiranta "Mama".




Santaleliyar yarinya wacce Allah yayiwa sura
tamkar ita tayi kanta kusan zuri'ar gidan haka
suke da kyau na fulani. Amma ita mama ta fita
daban wajen cikar sura daka gganta dole
gabanka ya fadi sbd tsabar kyau. Shiyasa tun
shekarunta basu kai ko'ina ba samari suka
yanyameta kowa na so, musamman cikin
gidansu watau yan'uwanta abin har yana so ya
zama rigima a tsakaninsu. Saida Uban dwk da
kansa ya tara su ya soke maganr soyayya da
Mama ya kuma kar wanda ya kara kiranta da
sunan tadi. Yayi haka ne don a sami masalaha
da zaman lfy. Allah kuwa ya taimaka kowa ya
gama bacin ransa ya hakura. Baya ga haka yana
ganin Sakeena bata kai shekarun da zata tsoma
kanta kogin soyayya ba alhali tana tsaka da
karatunta mafarin kenan da zata tafi babbar
sakandire yayi kokari ya samar mata makarantar
kwana ta yanmata dake bakori (FGGC Bakori)
Sannan hankalinsa ya kwanta amma wann
hukunci nasa yayiwa wasu daga cikin iyaye mata
ciwo har suna ganin sbd kyaun da Mama take
dashi ne yasa ake wulakanta yayansu suka rinka
ganin kamar suna sn su dauki dogon buri ne su
dora mata. Tabbas uban dwk nada buri akan
yarsa tilo mace saidai yasha bamban da irin
burin da matan gidan ke nufin ciki zukatansu
wanda bazai wuce ya aurar da ita ga hamshakin
me kudi ba ko basarake. Shi burinsa yarsa tayi
zurfin karatu kamar sauran yayyinta maza
wadanda a halin yanzu Abdulkadeer major nr na
soja, Abdulkareem accountant ne a CBN, sai
Abdulrahman dake NYSC a Jalingo. Ya kuwa
lashi takobin ko bashi da rai yan'uwanta su cika
masa wann buri nasa. Kwanci tashi Mama ta
shiga SS2 kuma yau sukayi hutun 2nd term tun
safe Uban dwk ya tura drivernsa ya daukota,
basu iso fandagori ba sai bayan la'sar kowa na
ta murna musamman yara da suka yanyameta
suka kwashe mata kaya zuwa sassansu. Ta shigo
da sallama Ummanta ta tarbeta ta rungumeta, ta
shiga sauran sassan ta gaishesu, Salisu da
Danlami kadai ta samu acikin samarin sassan.
Ta zauna suka taba yar hirar skul sannn ta tashi
koma sassansu tana shiga ummanta tace
Abbanki na nan ya dawo ta wuce da sauri ta
sameshi a falonsa, bakinta har kunne ta dan
rankwafa tace Allah ya taimaki mai martaba!
Fara'arsa ta karu: Allah yabar min Mamana na
shigo akace kin shiga sassa. Ta zube gabansa
tace eh naje gaishesu ne, ina yini Abba? Lfy lau
ya karatu? To mungode Allah, yace ina report
sheet a kawo na gani. Ta mike taje ta kwaso duk
takardun yayi ta dubawa yana fadin da kyau!
Bayan ta kammala ya dubeta kinyi kokari sosai
Mamana na baya miki amma har yanzu kina da
yar matsala a biology sai kin kara bada himma
kinsan dalili? Ta kada kai yace kara matsowa
kiji ta matso kusa dashi sosai kafin yace: buri na
ki zama likita Mamana, sbd a rayuwa ta ina
sha'awar in ga ya mace likita, abin yana burgeni
kwarai, shiyasa tun ranar da Allah ya bani ke
nake ta addu'ar Allah ya raya minke in samu in
cika burina, ko kuwa ke bakya sha'awa? Tace
sosai ma nakeson zama likita Abbana. Kuma
I.S.A zan kara himma don ganin na gama da
biology. Ya dafa kanta cike da farin ciki yace
yauwa Mamana, Allah yai miki albarka tace
ameen Abbana. Daga nan suka ci gaba da hirarsu
saida akayi sallama dashi ya tashi ya shiga
babban zaure inda Majalisarsa ke taruwa.
Mamana ta koma gurin Ummanta a kicin suna
aikin abinci tana bata labarin abnd Abbanta
yace, Umma tace yallabai kenan Allah dai ya
cika masa wann buri nasa tace I.S.A Umma
saina zama likita. Tace Allah ya yarda wai waya
gane min Mama da farafen kayan nan? Mama
tana dariya tace na dan ratayo wann abun da
suke sawa a kunne ina takawa ana ga Dr
Sakeena nan zuwa. Suka fashe da dariya.
Washegari misalin 10:am Mama ta fesa ado da
koriyar atamfa sannn ta dora after dress ta yafa
mayafinta ta sami Umma a daki, sai ina? Zani
gaida Inna saude ne. A'a kice dai zaki gun
Baraka. Tayi dan murmushi Umma ai duk dayane
Idan na gaida Inna ta sai muyi hira da Baraka
kawata... Uhummmn... To kodai lauya zaki zama
a fasa likitan nan? Tayi dariya wai kinaso ki
hada ni da Abba kenan.. Lallai kam to kice ina
gaida Sauden idan ta gama dinkunan ta baki
kizo min dasu, shikenan amma ina fata akwai
nawa aciki. Umma tace babu naki aciki duk
nawa ne, Mama ta dan kirne fuska kai umma ai
kuwa zan zabi daya aciki, tace duk zannuwa ne
ciki da alakum rigunan kuma masu hannu ne,
zan canja style ni inaso a haka, to ban yarda ba
ki anso min kayana kawai idan ta gama. Ta
jinjina kai shikenan umma nina tafi, adawo lfy
karki dade... Ta saba jakarta tana fadin to
Umma.. Salis ne zaune a kofar gida tana fitowa
ya kare mata kallo sama da kasa kafin yace sai
ina kuma? "Gidan Inna Saude zanje" 'Okay na
kuwa ga Baraka jiya itama ta dawo". Ya mike
muje in rakaki ko bakiso? "Muje mana ta wuce
ya biyota suka jera. Wai Mama meyasa Abba
yake takuraki dayawa? "Kamar yaya?" Baya son
kina kula samari kin kuwa san har yanzu yaya
Ali yana sonki? Ta dube shi farin sani kuwa
tunda yana gaya min a sace amma fitinar duk
waya fara daukota? Yace a'a ba don muna uwa
daya uba daya dashi ba, abnd yaya Sa'ed yayi
bai kyauta ba, tunda yasan shi yana sonki
menene na shi na shigo nemanki? Ya fa san
halin Yaya Ali ba hakuri ne dashi ba yanzun nan
sai ya nuna maka hauka. Ta dan tabe baki tace
hmmmnn... Kai nifa karatu ma zanyi dama sun
sa ransu a inuwa, babu wanda zan aura acikinsu
koda Abba bai dakatar dasu ba.. Ya zura mata
ido kina wulakanci Mama kice dama kema ba
sonsu kike ba? Baka gane ba.. Me kikeso ki
fada? Karatu zai hanaki aure ne? Ta kada kai
nutsuwa nafi bukata sbd karatuna mai son
nutsuwa ne.. Me zaki karanta? "Akikin likita" ya
ware ido Uhmmnn.. Dokta Sakeena kenan! Tayi
murmushi har kasa naji gingiringin! Yayi dariya
daidai lokacin da suke tsayawa gefen babban
titi.. To Dr Sakeena ni anan zan juya.. "Ngd ai
kaga har nayi sauri da yake ana hira" yace dadin
abokin rayuwa kenan, don ma ba Ya Ali bane
tayi dan tsaki get lost donAllah ka rabani da
wann zancen, yana dariya ta tsallaka titi ta
barshi hanya shi kuma ya juya ya koma gida.
Mota yake kakkabewa ya cire shimfidar foot mat
lokacin da Mama tazo wucewa, yayi tsaye yana
kallon wata surar da bai taba gamo da irin ta
ba.. Kai ya kasa daurewa saida yayi mata
sallama.. Ta dago ido ta dube shi tare da
amsawa, sautin muryarta ya kara rikita shi ya
bita da sauri donAllah ko zaki 5mins kadai in
tambayeki? Ta tsaya caka tana dubansa, dogo ne
sosai "Allah yasa na sani" yace donAllah anan
garin kike? Tambayar tasata a mamaki tace eh
mana, amma ban taba ganinki ba sai yau. Tace
kasan daurowa take , gsky ne, ah suna nan Al-
Ameen ina minna amma nan gidan kaka ta ne,
na kawo Mamana ne ma yanzu sau dayawa ina
zuwa nan shiyasa kikaji na tambayeki. Haka ne
yau ne Allah ya nufa zamu hadu. Ya sauke
numfashi gsky ne, allah ya hadamu kuma take
nan kin kwanta min a rai ko zan san sunanki? Ta
dan kauda kai yanayin mata saida gabansa ya
fadi tsoro ya kamashi kada ya sha kayi. Ya
marairaice dan daure ki gaya min ba don hali na
ba, hali? Nasan halinka ne? Yace na mita da
bakin naci! Tayi dan murmushi Sunana Sakeena'
kai! Sunan nan ya dace da kykkyawar fuskar
nan! Anan unguwar kike? Ta dan kada kai can
gidan zani wajen kanwar Ummana, ok to gidanku
fa? Ta yatsuna fuska alamun ta kosa ta wuce,
harta fara takawa ya biyota na dameki ko? Yi
hakuri so ne ya kamani ki taimake ni, ta tsaya
ta dube shi da idanuwanta farare kal dasu tace
kasan Uban dawaki? Can tsallaken titi kenan? Ni
yarsa ce idan kasan gidan, nan ne gidan mu
saidai akwai matsala. Ya hadiye murmushin sa
Matsala? Na shiga uku a ina matsalar take?
Tace Abbana baya bari azo zance wajena yace
sai na gama karatu hasali ma bording skul
nakeyi daga hutu sai hutu ake ganina, ya danyi
shiru jim kafin yace to ya za'ayi yanzu Sakeena?
Gsky ba da wasa nakeyi ba ya kike ganin za'ayi?
Tace ban sani ba amma ina ganin hakuri zai fi
kyau, mu saurari lokacin kammala karatun, ba
kai kadai bane akwai wasu wadanda suka rigaka
magana kuma sun hakura. Yace su zasu iya ne
nikam bazan iya ba Sakeena! Ina sonki sosai
babu abnd nake rayawa a cikin rain aface na
aureki. Ta dan kara dubansa sai taji ya fara
zama cikin ranta. Matsalar kawai batasan yanda
zatayi dashi ba har tace yaje gidansu. Don haka
tace kayi hakuri Al-Ameen.. Ta wuce da sauri ta
barshi yana kira Sakeena! DonAllah tsaya mana
kiji.. Gidaje biyu ta wuce na ukun shien nasu
Inna Saude. Ta sa kai ciki tare da sallama
baraka dake tsaye tsakar gida tana gyara zaman
mayafinta ta juya da sauri baki sake suka
rungume juna.. Gidanku zan tafi yanzu a haba?
Wllh yanzun nan kewa Inna sallama har ta bani
dinkunan Umma tace dama nima ta aikoni
akansu, ina Innar? Tana ciki suka shige tare Inna
tace au Mama ce? Har kin rigata kenan tana
dariya ta zauna sannu Inna ina kwana? Ta amsa
lfy lau an dawo lfy? Tace wllh lfy lau inna, kinga
dinkinta dama za'aje kai mata Mama ta fiddo su
a leda ta daddaga kai amma atamfofin masu
kyau. Suka dan taba hira suka wuce dakin
Baraka kowacce ta cire after dress. Mama ta
fada katifa tace tun dazu ya kamata in shigo
gidan nan bakon unguwarku ya tare ni. Bako? A
ina?tace oho! Wai nan gidan Alh lado suke cewa
ko? Eh nan ne gidan kakarsa Al- Ameen yace
min sunansa, bakinta har kunne ta jawo
hannunta suka tafa ban mu kashe yar'uwa bakar
fata kice kinyi gamao da katar. Likita bokan
turai yau shiya kawo Maman tasa kenan. Ta ware
ido kina nufin Dr ne? Kwarai kuwa ko bai
kammala ba kiris ya rage, don tuntuni naji ana
fadin sabis yake, ta kama baki har kin kara min
son shi ina ma ace wann abu ya tabbata kusa
bikin likitoci, au kema likitance? Tace zauna nan
in gaya miki jiy-jiya Abba ya gaya mina bnd zan
karanta kenan, kuma gsky Al- ameen yayi min
matsalar kawai Abba. A'a ina cewa ya soke
maganar su Ya Ali? Eh mana to ai baki sani ba
soke maganar ita ta janyo min tsiyar. Kina zaton
su kawu baza suji haushi ba? Ance karatu zanyi
kuma wani yazo an bashi? Ai sai Umma tayi
bakin jini acikin gidan. Bansan yanda zanyi ba
shi kanshi yaban tausayi tahowata kawai nayi na
barshi kinsanni da karfin hali Baraka ta bata rai
kai yakamata a nemi mafita Al-Ameen yayi
kawata zan soki dashi don na hango kun dace
kwarai. Ta sata ta zabga tagumi ta zuba mata
ido, ina tsoron Abba Baraka bazan iya
dumfararsa da wann maganr ba bayan jiyan nan
yaja min kunne ya gaya min burinsa akaina ina
zansa raina nima inason Al-Ameen! Ta dafe
goshi ga koshi ga kwanan yunwa, Baraka tayi iya
tunaninta ta rasa mafita, sbd tsoron hanyar da
za'abi a dumfari Uban dwk don haka ta numfasa
tace to ai shikenan sai ku dauki hakuri idan
kuma yana iya dakatawa ya jiraki ko kuwa? Tace
kyaleni haushi ya isheni dauko wani topic din
kona manta da wann. Tayi yar dariya to ya skul?
Mu koma wancan fannin dame-dame suka faru?
Ta gyara zama suka tsinke da hirar makaranta
daga abinci sai sallah har zuwa bayan la'asar
lokacin da Mama ke niyyar tafiya da zarar ta
idar da sallah.Tana sallamewa yaro ya shigo wai
ana kiran Mama ta leko tace jeka kace ta tafi
Inna ta leko tace uwaki baki zuwa ko wanene?
Kai kace gata nan zuwa. Yaro ya fice inna taci
gaba da fada ba kyau wulakanci ko baki son sa
ki saurare shi ki bashi hakuri a zauan lfy, ta
shige daki Inna kenan bazaki gane ba. Ta maida
after dress dinta tasa mayafi tace Baraka zoki
rakani, donAllah ki tafi ke kadai kinsan sirrin da
zakuyi? Ta ja tsaki ta fito yana tsaye a kofar
gidan haba gimbiya, kuma saiki tafi kibarni da
tension? Ina kikeso nasa raina yau wllh ko abinci
na kasa ci sbd tunanin matsalar da kika ambato.
Tayi masa zuru tausayinsa ne zalla ke bin jinin
jinkinta tace kasan Allah nima tunani na ya kara
na rasa me zancewa Abba ganin yan'uwana ma
na jini ya dakatar dasu balle wani kuma
watakila kana bukatar auren ne da wuri kaga
Abba bazai amince ba. Ya goge zufar goshinsa
da hankici, don dai in jure ki karee sakandire zan
iya jira mana. Idan ma kinaso cigaba ne bayan
munyi aure ni zan dauki nauyin ki karanta duk
fannin da kikeso donAllah ki taimakeni kiyiwa
Abba wann bayanin. Ta dafe goshi! Wane zan
masa ya gane? Ya fada a ransa yace na dameki
ko? Yes nima nasan na fiye naci ga duk abnd
nake so. Yace mata tunda baki da abinyi ni ina
dashi abnd nake bukata daga gareki kawai ki
tabbatar min tsakaninki da Allah har cikin mind
dinki kina sona? Ki fada kanki tsaya kawai!
Mamana tana gab da fitowa zamu tafi.Tace Al-
Ameen na amince kar kaji wani shakku a ranka
amma...... Ya dan daga mata hannu don't sai it
pls! Kin faranta min rai Sakeena na tabbata zan
samu inci abinci ya wuce min. Sauran magana ki
kyale min, nace yanzu me zaki bani na rike na
alkawari? Al-Ameen fa na bata mmk na yadda
gaba daya ya sallama kansa gareta ko shiyasa
itama ya mamaye mata ko ina? Tayi dan
murmushi me zan baka kuwa? Ya nuna yatsanta
wann ring din yayi min kyau shi zaki bani, ai
bazai yi maka ba, inji wa? Miko shinan ki gani.
Ba musu ta zaro ta mika masa ya turawa
karamin yatsarsa zobe yayi zamansa daram
kamar daman can na sane.
BAKIN CIKI 1***2 Ya dubeta yana murmushi U
see? Mu biyu akayiwa zoben nan kika kama ke
kadai kika rike, tayi yar dariya "haka naji" "nima
kuwa hakan naji" amma matsalar ni bani da jar
azurfa dana baki wann kuma saidai kiyi warwaro
dashi ba dai zobe ba. Ta zubawa zoben ido yana
ta daukar ido ko in baki zoben haka? "Kawo" ai
yayi miki yawa gimbiya ayi min hakuri a biyoni
bashi in Shaa Allahu zan biya. To Allah ya baka
iko, ya kara zubo mata ido yace to ameen
gimbiyata. Ya cigaba da kallonta sannan ya
sauke numfashi wai yanzu zamu tafi gashi ban
gaji da ganinki ba. Yadda kikasan in saki a
aljihu in tafi dake. Tace ka saceni kenan? Yayi
yar dariya me karawa fuskarsa kyau da kwarjini
kamar yanda kika sace ni ba. Ji sukayi ana
tambaya ina Al-Ameen din ya nufa ne? Yace
gani Mama anan. Ta fada zaure da saurinta ta
fara dariya zoki ganta Mama donAlla! Ta kama
baki Oh ni Hafsatu Goggo fito kiga ikon Allah!
Itama yar tsohuwa ta fito ina kishiyar tawa duk
ta susuta min miji! Mama ta manne da bango ta
rufe fuska ruf da mayafi. Ta sulale kasa tun
kafin su karaso, Goggo zoki sha kallon yar bebi
ba irinki ba bude fuskar su ganki. Maman da
kanta ta bude fuskar yayin da take gaishesu. Ta
amsa cike da fara'a ah! Mashaa Allahu Al-
Ameen ka iya zabe, Allah yasa albarka Goggo
tace ameen dai. Ai ka kwantar da hankalinka nan
gida ne babu abnd zai gagara In Shaa Allahu!
Yace Allah yasa Goggo suka baro zauren Hajiar
na fadin kai fa nake jira karka shanya ni.. Gani
nan Mama, Mama tace Allah ya kiyaye ta amsa
da ameen. Ya gyara tsayuwa yace kingani? Bani
kadai nake sonki ba Sakeena sbd haka ki saurare
ni, tace ina nan ina sararonka Allah ya tabbatar
mana da alahiri, ameen gimbiyata to bari mu
lallaba tace Allah ya tsare amma zaka yi min
alkawari? Me zai hana? Fade shi indai ba zakice
in daina zuwa gunki bane , tayi yar dariya bashi
bane kayi min alkawarin zaka ci abinci idan son
samu nema mama ta dan jiraka kaci ko yaya ne,
kai Dr ne kasan matsalar rashin cin abinci ya
ware sosai yace waya gaya miki ni Dr ne? Tayi
nuni cikin gida yar'uwata dake nan gidan. Yayi
jim! Murmushi kawai yake fiddawa kafin yace its
true 4mnths back aka damka min letter of
appointment a ABUTH Zaria hope kinason Dr? ta
dube shi da gefen ido sai ya tsira mata ido
domin kallon yayi masa sosai ko shi kadai ya isa
amsar tambayarsa, in ba don son jin baki ba
bata ga ma dalilin wann tambayar ba don haka
ta juya zata shiga gida. Sakeena! Ya kirata a
sanyaye ta juyo dauke da murmushi tace a sauka
lfy Allah ya tsare ta karasa cikin gida don ta
lura idan ba hakan tayi ba bazai tafi ba kuma
ana jirransa. Gaba daya kasala ta sauko masa
ya sauke numfashi ya jima tsaye bakin zauren
sannan ya fito wajen mota inda Mamansa ke
jiransa. A hakikanin gaskiya Al-ameen ya kamu
da wata sabuwar cuta wacce shi kansa a
matsaynsa na likita bai taba cin karo da
maganinta ba. Duk iya karatnsa da yayi kuwa.
Sosai yake ji a ckn ransa idan bai auri mama ba
babu makawa zai fusknci matsala. Shi yasa
tunda ya damki hnya baya iya magana da kowa
illa addu'ar Allah yasa sakeena matarsa ce!
Hakazalika al'amarn yake wajn mama, tas!
Al'ameen ke neman rusa shirinta na son zurfn
karatu, kamar ynda tayi wa Abbanta alkawari. A
halin ynzu kam shirun da tayi bisa shimfida tun
shigowarta gidan, tunanin auren al'ameen take
yi, kuma da son samu ne kar aja lokaci mai
tsawo. Anya abbanta zai yarda kuwa? Baraka ma
taso ta kauda mata wannan tunanin, amma ta
kasa. Ta yunkura ta tashi zaune tace, "bari in
wuce baraka". Kallnta kawai take yi, ta mika
hannu ta jawo jakarta ta rataya, tayi waje.
Yaynda baraka ta dauko mayafi ta biyo ta. A
dakin inna ta sameta suna sallama, hannunta
daya rike da ledar kayan dinkin umman ta, "ki
gaida min ita da kyau, sai na zo" tace, "to zata
ji insha Allahu". Ta juya suka fito tare da baraka.
Sawun tayoyn motarsa ta tsaya tana kallo tsawn
lokaci, kafn ta dubi baraka, "al'ameen ya wuce,
ban jin zan sake ganinsa......." "wannan mugun
zato ne, me yasa kike wa kanki mugun fata?" ta
kada kai, "ba mugun fata bane, sauya ra'ayin
abba shine fargaba na, tabbas babu abnda zai
hana shi dakatar da al'ameen, tunda ya iya
dakatar da 'ya'yan 'yan uwansa na jini daya".
Tace, "ni kuwa a tawa wautar gani nake
al'ameen zai iya jiranki, tnda yana sonki". "lallai
kam wauta, baki ganin al'ameen ya girma sosai,
na tabbata a halin yanzu iyaynsa basu da wani
buri da ya wuce su ga yayi aure. Yaushe zasu
lamunci jirana shekaru barkatai masu zuwa?
Banzan tunani kike yi baraka, kawai ki yarda zan
iya rasa al'amee".! Ta fizgo hannunta suka wuce
tana fadin, "ni banji a jikina ba, kuma ai Allah
na nan, ba sai mu kai kukanmu gunsa ba" "haka
ne, dole in gayawa Allah, don gaskiya ban taba
jin wani sauyi a zuciyata ba, sai a kansa. Zaki
tayani kawata?" tayi dan murmushi tare da kamo
habar ta, "mama kenan, sai ma kin tambaya?
Matsalarki ai tawa ce. Ki sha kuruminki, insha
Allahu by nxt year zamu sha bikin likitoci, ranar
duk wani mai ciwo a fandagori zai warke" Ta
fara dariya, "au dariya na baki ko? Kinag dai
PANADOL shine tekaway dinmu, ANTI BIOTIC
kuwa su kowa zai sha a wajen dinner, to ina cuta
zata zauna?" Ta buge kafadarta tana kara
darawa, "surutunki yayi yawa baraka, ubangiji ya
cika mana burnmu" ta amsa da amin. A bakin
titi suka yi sallama akan zata ji duk yadda
al'amarin ya kaya nan gaba. Ta tsallako hanya
tana tafe zuciyarta kunshe da sake-sake kala-
kala. Wani lokacin ta kanji kamar kwalla zasu
zubo mata sbd tsabar damuwa. Ta shigo gida
yaran gidan sunyi nisa da karatun allo, kamar
kullum. Malamin su ke zuwa ya basu darasi.
Taja birki ta gaishe shi, ta wuce da sauri ta
shige gida, ta mika wa ummanta dinkunan ta.
Bata tsaya bata lokaci ba ta sungumo Kur'aninta
da sauran littattafai ta koma wajen malam ta
kwashi karatu. Sai da ta tabbatar karatun ya
kama bakinta, sannan ta koma dakinta ta ci
gaba da nazari. Hakan ya dan kauda mata
damuwar da ta tsinci kanta ciki yau. Shi yas ma
taki sassauta wa karatun, don bata son ummanta
ta fahmci wani sauyi a game da ita. Sun Sallaci
Isha'I sun ci abinci tana like gefen Abbanta
Umma ke fadin wann karon kuma ina zaki hutu?
Kanta tasye ta bata amsa wajen Ya abdulkareem
zani. Baki sake take kallonta wai! Wai! Yau
kuma aljanun can suka buga? Tayi yar dariya
umma kenan ai dama ba wai bana son zuwa
minna bane kawai Anti rabi ce matsalata kayita
aiki kamar boyinta. Ta dan harareta uhumn ke
kuma malalaciya uwar son jiki ba a haka ake
koyo ba? Ta kada kai a'a wllh naje hutu kuma
inyi ta aiki ina amfanin hutun ko Abba? Yace
kyalle Umman nan kema kike zuwa gunsu kiyi
zamanki wajen Abbanki inga me samin ke aiki.
Umma tace oho! Shi zaki goya miki baya? Ta ai
gidan wani zata aiki kam dole tayi shi ko anan
dinma. Yace ok hakane? Kinga kiyi tafiyarki Abj
wajen soja. Ta kada kai bari dai in tafi minnar
Abba, kasan shima yaya yana ta korafi wai ban
zuwa gun sa. Yace amma nasha mamaki.....
Name Abba? Son zuwa minar nan koda yake duk
yarinta ce take saki zuwa hutun nan da zarar kin
fara jami'a ajewa zakiyi, Umma tace likita ba!
Dokta Sakeena! Ta langwabe jikin Abbanta tana
dariyar dole amma cikin ranta tausayawa junan
su takeyi musamman Al-Ameen da kansa yake
rawa yana ganin matsalar me sauki ce abin ya
kara kashe mata jiki data dubi Abbanta taga
yadda muraran fuskarsa ta nuna alfahari da
kalaman Umma. Kwance bisa gadonta amma
barci yaki yuwuwa dabarar ta taje hutu minna ko
Allah yasa su kara ganawa da Al-Ameen koda
Uban Dwk ya soke bukatarsa. Shin yaya zatayi
ne? Mafita kam babu sai abnd Allah yayi. Ta
kuwa kwana gayawa Allah don ya zaba mata
abnd yafi alhairi. Ko karatu ko auren Al-Ameen
wanda zamu iya kiransa mai sa'a gwarzon da
yayi nasarar ciwo zuciyar Mama da yaki har take
tunanin dama ace burin Abban ta aure ne bason
zama likita ba. Shawara ta zauna kan jibi da
yardar Allah zata wuce minna. Sha biyun rana
daidai tana shimfide bisa gadonta tare da
muguwar kasala, shigowar Uban Dwk gida
dawowarsa kenan daga kewayen gonakinsa. Ya
daga labulen dakinta tare da fadin yaya dai yar
gidan Abba? Ta tashi zaune tana murmushi,
babu komai Abbana har ka dawo? Yace na dawo
Mamana lfy dai? Naga kamar jikinki a mace
yake. Ta amsa Allah ya taimaki mai martaba lfy
kalau Mamanka take bacci ne bai isheni ba. Ya
karasa shigowa dakin ya tsaya akanta yace ni
kuwa banason ki saba da yawan bacci Mamana
kin fa san karatun da zakiyi mai wahala ne
bayason lalaci ko kin manta ne? Ta dan rausaya
kai tana murmushi ban manta ba Abba ko
yanzun ma rashin abin yine yasa. Rashin abin
yi? To taso muje in dai abin yine ni zan baki shi
yanzun nan. Ta fara dariya meye shi Abbana?
Yace ki zagaye tsakar gidan nan sau 12, ta kame
baki wuuu! Abbba a tsakar ranar nan? Ai sai in
zube sumammiya, duk suka dauki dariya yayin
da wani matashin yaro yayi sallama sassan yace
ana sallama da Alhaji. Umma dake waje ta
karaso da sakon. Shi mutum ne me girmama
bakinsa don haka bai bata lokaci ba ya fice don
ansa sallama, wata zungureriyar marsandi ya
fara cin karo da ita a kofar gidan sannan
idanuwansa suka kai ga bakinsa maza su 2 a
tsaye wanda kallo daya zakai musu ka tabbatar
manyan mutane ne. Kai! Guda a cikinsu ma Uban
Dwk ya sanshi farin sani kuwa domin fitaccen
mutum ne a gwamnatin data shude ambassador
ne 10yrs back, watau Alh Saifullahi Sodangi
Lafai kuma marafan lafai. Take nan mamaki ya
saukarwa Uban Dwk ganin cewa babu abnd ya
taba hadasu na mu'amala. Cike da mamaki ya
bisu da sallama cikn fara'a suka yi musabaha,
sannan ya kira yaronsa Kalla yace maza ya bude
masa falon baki. Can suka rankaya da bakin
nasa, ya nuna masu kujeru yana fadin "bismilla!
Kai sannunku da zuwa!" Sun fara gaisawa kenan
kalla yayi sallama ya shigo da gorunan ruwan
(Swan) bisa tire da kofuna, ya aje gabansu. Ya
sake dibar gaisuwa ya fice ya bar falon. Uban
dawaki ya shayar da bakinsa suwan sanyi. Bayan
sun natsa Ambasada ya soma da cewa,
"watakila ka shaida ni, watakila kuma baka taba
sanina ba". Uban dawaki ya cafe, "farin sani
kuwa, mai girma marafan lafai". Suka yi 'yar
dariya, "babu shakka, to wannan kuma kanina
ne uwa daya uba daya, alh. Nuhu lafai". Uban
dawaki ya jinjina kai, "tabbas kuwa, ga kama
nan, sannunku da zuwa" Suka kara amsawa,
sannan alh. Nuhu ya zarce da bayani, "Allah mai
yadda yaso, kuma shi yake shirya al'amuransa
yadda yaga dama. Watau jiya yaron wajenmu
yazo garin nan, domin mahaifiyarsa, ya kuma ga
'yar wajenka wacce ta tabbatar masa cewa ita
'yarka ce. A hakikanin gaskiya dai yaro ya gani
yana kuma so da aure, shi yasa yana zuwa ya
sanar mana, mu kuma muka ce ai babu bata
lokaci dole mu kawo gaisuwa, tare da neman
izini. Domin a haln ynzu bamu da wani buri da
ya wuce Allah ya nuna mana aurensa, tnda ya
kammala karatu har aiki ya samu. Don a gaskiya
mun yaba da bayanin da yayi mana, yarinyar ta
fito daga babban gida. Ina fatan za'a karbi
kokon barar mu?
Go to Home
BAKIN CIKI 1***3 Uban dawaki yayi jim, shiru
yana tunanin me zaice da manyan bakinsa da
suka wanko kafa takanas takano suka zo da
babban alkhairi gidansa? Girma da kwarjinin
Marafa sun cika masu ido, har ya rika ji ckn
zuciyarsa bazai iya kabar da kokon bararsu ba.
Amma abin tambayar shine, ina burinsa na
tuntuni da ya kwallafa akan mama? Tun tana ckn
zanin goynta? Muryar ambasada yaji yana fadin,
"nasa daliln shirunka alh., Al'ameen yayi min
bayanin komai game da burinka na sakeena tayi
zurfin karatu. Wannan kuduri ne mai kyau, kuma
ni kaina ina sha'awar hakan. To amma ina son in
tunasar da kai cewar aure baya hana ilimi. Ina
roknka da ka tausayawa halin da al'ameen ya
shiga na fadawa tarkon son sakeena. Shi kadai
gareni alh, kuma daidai gwargwado soyayyar da
na nuna masa bata gurbata tarbiyyarsa ba. Yaro
ne mai ladabi da biyayya ga kowa, tare da
tsananin bin dukkan abnda muka umarce shi.
Dalilin da yasa kenan nima nake tsananin son
abnda yake so. Bana sanya wajen taimaka masa
da addu'a, a duk lokacn da ya tsinci kansa cikn
wata matsala kamar ynda na lura ya shiga wani
hali daga jiya zuwa yau da muka baro shi. Babu
sukuni a zuciyarsa, alh. Ka taimaka ka amince
wa al'ameen auren sakeena da zarar ta kammala
sakandare, karatu kuwa ko wane iri ne, ko a ina
ne sakeena zata yi shi da yardar Allah" Wannan
dogon bayani na marafa ya kwabe wa uban
dawaki guiwa, zcyrsa tayi rauni, ba zai iya ja da
nufin Allah ba. Ya gyara zama sosai yace, "ba
shakka naji duk abnda kuka fadi, kuma nayi
farin ciki kwarai da gaske, sbd haka na amsa
kiranku, duk da cewar ya kamata in shawarci
sauran 'yan uwana, amma babu komai zan yi
musu bayana idan muka zauna. Al'ameen ya ci
gaba da neman sakeena, Allah ya tabbatar mana
da alkhairi" Kawai gani yayi marafa ya daga
hannu sama yana fadin, "Alhamdu lillah!" ya
maimaita har sau uku, sannan ya dubi uban
dawaki, "bansan kalmar da zan fada ba alh......."
yayi murmushi, "ai ka fadi alh., tnda kayi godiya
ga Allah". Ya jinjina kai, "haka ne, to mun kara
godiya gareka Allah, ka nuna mana lokacin" duk
suka amsa da amin. Alh. Nuhu ya zarce da fadin,
"yanzu dame-dame ake bukata na gaisuwa da
baiko?" yace, "kar ku damu da wannan, da zarar
mun zauna da 'yan uwana zaku ji bayani insha
Allahu". "to babu laifi, muna saurare. Ina
sakeenar take? A kira min ita mu gaisa, don in
cika alkawarin da na dauko......" "alkawari?"
"kwarai kuwa, har mota ya biyoni yana fadin,
don Allah daddy in kunje ku isar da gaisuwata ga
sakeena, koda mahaifnta bai amince min
auranta ba. To kaji, dole in cika wannan
alkawari. A kira min ita inga farin cikn
al'ameen" Farin ciki ya lullube uban dawaki,
bakinsa har kunne ya mike, "Allah sarki, to tana
zuwa". Yayi ckn gida da hanzari ya sami Hajiya
Halima, "ina mama? Ashe bakin nata ne" tare da
mamaki ta tambaya, "bakinta? Kamar yaya?"
"zan miki bayani, je kice ta shiryo tsaf ta sameni
falon baki". Ya juya ya koma. Ita kuma dakin
mama ta wuce, gaban madubi ta sameta zaune
tana shafe-shafe, fitowarta kenan daga wanka.
Ta matsa gareta tace, "dama kinsan da zuwan
wasu baki gunki?" "baki?" ta kada kai, "daga ina
umma?" "ni zaki tambaya? To kiyi maza suna
falon baki inji abbanki". Ta juya ckn juyayi ta
fice. Mama kuwa kasake tayi tana tunani,
"baki?" Al'ameen ya fado mata a rai, nan da nan
farin ciki ya rufeta, ta mike da gudu ta nufi
dirowar kaynta, ta zuba ado ta rufa mayafi, ta
fito ta doshi falon baki gabanta na harbawa,
amma zuciyarta fara sol! Duk da cewar bata
tabbatar da hukuncin da abbanta ya yanke ba.
Sai dai tana da yakinin akwai alamun nasara,
tnda aka ce taje da gaishe su . Tayi sallama ckn
kunya ta shiga, ta sami wuri gefe ta tankwashe
kafa, "sannunku da zuwa". Kai bakin marafa da
kaninsa kamar gonar auduga, su kansu mama ta
girgiza su, sun tabbatar da al'ameen ya darzo,
fatan da suke yi Ubangiji yasa kyanta har ckn
zuciyarta yake. Cikin ladabi da tsananin kunya ta
gaishesu, su kuma suka amsa ckn farin ciki da
nuna kauna a zahiri. Marafa ya taso yazo
gabanta, ya tsuguna yace, "al'ameen ya zabe ki,
nima haka. Sbd haka sai ku rike juna amana.
Har Allah ya nuna mana lokacin da muke dakon
zuwansa, kin ji?". Ta kara yin kasa da kai,
sannan ta amsa da kai. Yace, "madalla, to mun
gode". Yasa hannu a aljihu ya zaro sababbin
bandir 'yan wazobia ya aje a gabnta, "wannan
kyauta ce don nuna farin cikina gare ki, sbd
zabar dana ya zama mijinki". Kunya kamar ta
nutse, da kyar ta iya fadin, "na gode. Allah ya
saka da alkhairi". Yace, "to me zan ce wa
al'ameen idan mun koma?". Ta yunkura a guje ta
bar falon, suna mata dariya. Shi kansa Uban
dawaki yana mamakin kansa, irin farn ckn da ya
tsinci kansa. Alh. Saifullahi ya mike, "to bari
muyi harama, mun gode kwarai, Allah ya
tabbatar mana da alkhairi". Suka yi musabaha,
uban dawaki na fadin, "amin". Yayi musu rakiya,
sai da yaga tashnsu sannan ya shigo gida.
"Saboda Allah mama haka kuka yi da abbanki?"
ummanta ke tambaya, ta kada kai, "wlh umma
ba laifina bane. Babu abnda ban gaya masa ba,
yaki yarda. Kinga wannan turowar ma ni bansan
da ita ba, kawai ce min yayi shi yasan ynda zai
bullowa al'amarin, don haka in sa masa ido".
Tace, "ke din ma kina sonsa ne, ai nasan halinki
sarai mama, ba don haka ba ko kallo bai isheki
ba. Kin bani mamaki wlh, watau shi yasa jiya
kika ce minna zaki hutu, ashe da manufarki....."
Abbanta ya cafe, "tabbas haka ne....." ya karaso
ciki ya zauna, yana dubanta yaynda gabanta ke
ci gaba da harbawa da sauri. "ya aka yi haka
mama na? Ki turo min babban mutum irin
marafa, bayan kisan zai yi wuya ince a'a ko?".
Hankalnta ya kara tashi, ido tam da hawaye
tace, "wlh abba ba haka bane, hasali ma ni
bansan shine mahaifnsa ba, domin ni bai gaya
min ba, ka yarda dani abba, don bani da nufin
saba maka. Duk hukuncn da ka yanke akan
wannan al'amarin bazan bijire ba". Tasa hannu
ta goge kwallan da suka zubo bisa kuncnta.
Yace, "matso nan mamana". Da rarrafe ta isa
gunsa, ya kamo kafadarta yace, "dubeni nan". Ta
dago manyan idanuwnta da suka fara jirkita ta
kalle shi, "na yarda da ke dari-bisa-dari
mamana, sai dai abnda nake hangowa watakila
ke ba zaki hango shi ba. Bayn aure mata sukan
fuskanci 'yan matsaloli musamman idan Allah
ya kawo rabo ckn gaggawa, wanda idan ba ayi
sa'a ba sai ya jawo koma baya ga komai nata,
ba ma karatu ba kadai. Amma bazan matsa ba
mamana, ya kasance nayi jayayya da shirn
Allah, don haka ina muku fatan alkhairi". Ta rufe
fuska da tafin hannunta, fuskarta na bayyanar da
murmushi. Jiknsa ta langwabe, dadi kamar ya
kasheta. Yace, "ho 'yar nema! Watau kice kina
son al'ameen ko?". Ta tashi a guje ta bar musu
dakin. Uban Dwk ya numfasa sannan ya dubi
Umma to ya kika ce? Kinga dai yanda al'amarin
ya kasance. Fuska sake tace yaya kuwa za'ayi
Alh? Tunda ka amince ai shikenan Allah yasa
hakan shine mafi alkhairi, yace Ameen. Baki ma
sani ba wai shima likita ne mun fito ina musu
rakiya shi baban nasa ke gaya min. Nace itama
abnd take son ta karanta din kenan. A hakikanin
gsky ya tabbatar min babu damuwa I.S.A zataci
gaba da karatunta, kinji inda muka tsaya dasu.
Sauran maganar gaisuwa da baiko nace su bari
mu zauna da yan'uwana. Ta numfasa gsky ne
hakan kuma yayi kyau saidai kana ganin bazasy
dora wani abu a zukatansu ba? Kasan fa su Ali
sun so ta ka hana kace karatu zatayi. Yayi dan
shiru jim, kafin yace kinyi magana amma ba
komai nina san bayanin da zanyi musu. Tace
shikenan sun dan jima suna maida zancen.
Mama kuwa tana dakinta rayuwa ta zame mata
sabuwa. Duk. Inda tajefa ido Al-Ameen din take
gani kwarjininsa murmushinsa salon maganarsa
da taushin murya mai dadi. Bayan sallar la'asar
lokaci ne da kannen Uban dwk ke dawowa daga
gonakinsu. Yaran nata daukar darasin
Muhammadiyya kamar kullum. Uban Dwk ya tara
kannensa a falonsa ya zayyane musu komai
game da abnd ya faru, nan taje ransu ya sosu ba
kadan ba kallon juna suke cikin al'ajabi suna
tambayar zukatansu. Ina karatun da akace
Mama zatayi? Ya kara gyara zama yace nasan
zakuyi wa zukatanku wann tambayoyu a game da
magana ta, sbd Aliyu da Sa'aeed dama sauran
samarin da suka yo caa akan Mama, suna neman
aurenta amma na hana, sbd dalilin zurfin
karatunta. Wannan magana wllh haka take cikin
zuciyata kuma shine buri na saidai marafan lafai
ya cika min ido kwarai da gaske, banjin kuma
zaku goyi bayan na bada masa kasa a ido ba,
alhalin da kansa yayi tattaki neman alfarmar da
bata fi karfina ba. Abnd nakeso in rokeku shine
donAllah don son Manzon Allah SAW kuyi min
uziri akan wann hukunci dana yanke karku zargi
komai sai alkhairi, ina fatan zaku bani hadin kai
dari bisa dari. Alh Basiru mahaifin su Aliyu kuma
yafi kowa yaya a gidan ya gyara zama yace Alh
ai wann al'amari na Allah ne kuma abin
alfaharinmu ne ace Mama ta sami cigaba domin
cigaba ne samun irin wann hamshakin zuriya ta
marafan lafai. Mama yar mu ce kuma muna farin
ciki tare da fatan Allah ya tabbatar da wann abu
kome kace Adamu? Alh Adamu karamin cikinsu
ubansu Sa'eed yace wann magana haka take Alh
mu munsan cewa Mama bazata auri kowa ba sai
wanda Allah yace shine mijinta sbd haka muna
murnar samun wann babban rabo daga Allah.
Cikin jin dadi Uban Dwk ke magana "godiya ta
tabbata ga Allah da yasa na sami hadin kanku
cikin sauki nayi godiya sosai, abu na gaba shine
sunyi maganar gaisuwa da baiko nace su dan
saurara min muyi shawara da yan'uwana. Me
zaku ce akai? Alh Basiru yace hakan shi ma yayi
kyau sai ta gama sakandiran ne ko kuwa yanzu
suke so? Yace a'a sai ta gama tukunna. Idan
haka ne zaifi kyau a bari ta gama din sai ayi
baiko a sa rana ko kuwa? Alh Adamu yace haka
yayi daidai. Allah ya nuna mana lokacin lfy.
Kowa ya amsa da ameen. Uban dwk ya shaida
musu kyautar kudin da Marafan yayiwa Mama na
tsabar kudi naira dubu hamsin. Aha! Gsky ta
bayyana abnd Uban Dwk yake so kenan ruwan
kudi. Haka zuciyoyinsu suka saka musu, ya
fiddo kudi ya nuna musu kafin yace saidai
maganata gsky wann kudi ko sisi bazan taba a
cikinsu ba zanci gaba da ajiyarsu cikin banki da
dukkan wata kyauta dazata zo daga baya har sai
wann abu ya tabbara iidan kuma an sami akasi
ba fata muke ba sai a mayar musu kayansu. Ko
yaya kuka gani? Sasan alh. Basiru suka tasu da
matansu suka kwnce musu abnda ya wakana a
falon uban dawaki. H. Hajo matar alh. Basiru ita
ta fara tsoma baki, "amma kuwa idan baka mutu
ba zaka ga abin mamaki kala-kala. Ynzu da
gske alh. Babba ne ya iya tararku da wannan
maganar? Ko ya mance abnda yayi a kan su ali
ne?" Alh. Adamu yace, "ya manta? Babu abnda
ya manta. Hasali ma sai da ya kara maimaita
zancn su". "tafdi!" inji h. Gaje, matar alh.
Adamu. "kai dai kaga dan-uwa kawai, ai dama
tun farko na fada, ba wani karatn da ake so tayi,
burnsu mai kudi ko basarake, sbd su ganin
mama tafi kowa kyau a duniya. Shi yasa suka
dauketa a matsayn wani jari gare su. Ai
shikenan, Allah ya bamu lfya. Muma namu
'ya'yan bamu fidda ran Allah zai azurta su ba.
Ba Dai kowannensu ya kama aiki ba? To muje
zuwa wai mahaukaci ya hau kura. Harda wani
za'a tara kudi a banki, don kawai kar ya baku
wani abu ne a ciki, shine yake muku 'yan
dabaru" "ni dama bance a bani ba, me zanci da
su?" inji alh. Basiru. Alh. Adamu yace, "balle
kuma ni, ai tuni na haramtawa kaina komai na
alh, tnda ya nuna mana kiyayya a fili". Ya tashi
yayi waje, alh. Basiru yabi baynsa. Yaynda h.
Gaje ke fadin, "sai musa ido mu gani, da wane
bakin h. Halima zata gaya mana zancan". H.
Hajo tace, "kema dai da son jin baki kike. Tnda
mijnta ya furta, ai ba sai ta maimaita ba, tana
nan tasa ido muje mata murna 'yarta tayi farin
jin". Tayi 'yar shewa, "Allah mai iko, kiri-kiri an
raina mana wayau?". H. Hajo ta ja tsaki,
"mtsww! Kina mamaki kenan, dama kin daina
wlh, domin an jima ana ruwa kasa na shnyewa.
Ba girin-girin ba dai, tayi mai. Ba auran gidan
kudin ba, kwancyar hnkali!" Tana rufe baki tare
da sallamar umma, suka amsa suna wani yatsina
suna yarfarwa. Ta zauna tana fadin, "na shiga
sasanki yara suka ce kina nan" "uhm! Ina nan"
"dama maganar 'yarku ce, ban sani ba ko su alh.
Sun gaya muku halin da ake ciki?". H. Hajo tace,
"sun gaya mana, yanzu haka ma shirn zuwa
sasan naki muke, sai kuma gaki. Ashe kuma
mama an fasa karatu aure za'ayi?" Tace, "to
yaya zamu yi, mutane sun cikawa alh. ido,
sannan da alama ita ma maman tana son yaron.
'ya mace kuwa idan ta nuna tana son aure, to yi
mata auran shine mafi alkhairi ga iyaynta". H.
Gaje tace, "gaskya kuwa, gidan hutu ai dole a so
shi. Ai kinga wadancan da yake ya ku bayi ne
bata ce tana so ba". Umma ta dube ta sosai, "me
kike nufi gaje?" tace, "me kuwa? Ita gaskya ai
daya ce, sannan arziki na Allah ne. Daga ali har
sa'eed bamu fidda masu rai ba". Ta tsura mata
ido cike da mamaki, kfn tace, "na wuce kiyi min
habaici gaje, domin ni ba sa'arki bace.
Kasancewar ali da sa'eed 'yan uwa ga mama bai
zama dole wani a cknsu ya aureta ba, domin shi
aure nufi ne na Allah. Shi ke kullashi, kuma duk
fassarar da zaku yi man kun dade ba kuyi ba.
Allah yasan zcyrmu akan komai". Ta tashi ta bar
sasan. Wata uwar shewa suka kwasa hannu
bibiyu suka tafa, "tabarmar kunya....," inji h.
Gaje, "da hauka ake nade ta!" h. Hajo ta bata
amsa.!
AKIN CIKI 1***4 Sasan alh. Basiru suka tasu da
matansu suka kwnce musu abnda ya wakana a
falon uban dawaki. H. Hajo matar alh. Basiru ita
ta fara tsoma baki, "amma kuwa idan baka mutu
ba zaka ga abin mamaki kala-kala. Ynzu da
gske alh. Babba ne ya iya tararku da wannan
maganar? Ko ya mance abnda yayi a kan su ali
ne?" Alh. Adamu yace, "ya manta? Babu abnda
ya manta. Hasali ma sai da ya kara maimaita
zancn su". "tafdi!" inji h. Gaje, matar alh.
Adamu. "kai dai kaga dan-uwa kawai, ai dama
tun farko na fada, ba wani karatn da ake so tayi,
burnsu mai kudi ko basarake, sbd su ganin
mama tafi kowa kyau a duniya. Shi yasa suka
dauketa a matsayn wani jari gare su. Ai
shikenan, Allah ya bamu lfya. Muma namu
'ya'yan bamu fidda ran Allah zai azurta su ba.
Ba Dai kowannensu ya kama aiki ba? To muje
zuwa wai mahaukaci ya hau kura. Harda wani
za'a tara kudi a banki, don kawai kar ya baku
wani abu ne a ciki, shine yake muku 'yan
dabaru" "ni dama bance a bani ba, me zanci da
su?" inji alh. Basiru. Alh. Adamu yace, "balle
kuma ni, ai tuni na haramtawa kaina komai na
alh, tnda ya nuna mana kiyayya a fili". Ya tashi
yayi waje, alh. Basiru yabi baynsa. Yaynda h.
Gaje ke fadin, "sai musa ido mu gani, da wane
bakin h. Halima zata gaya mana zancan". H.
Hajo tace, "kema dai da son jin baki kike. Tnda
mijnta ya furta, ai ba sai ta maimaita ba, tana
nan tasa ido muje mata murna 'yarta tayi farin
jin". Tayi 'yar shewa, "Allah mai iko, kiri-kiri an
raina mana wayau?". H. Hajo ta ja tsaki,
"mtsww! Kina mamaki kenan, dama kin daina
wlh, domin an jima ana ruwa kasa na shnyewa.
Ba girin-girin ba dai, tayi mai. Ba auran gidan
kudin ba, kwancyar hnkali!" Tana rufe baki tare
da sallamar umma, suka amsa suna wani yatsina
suna yarfarwa. Ta zauna tana fadin, "na shiga
sasanki yara suka ce kina nan" "uhm! Ina nan"
"dama maganar 'yarku ce, ban sani ba ko su alh.
Sun gaya muku halin da ake ciki?". H. Hajo tace,
"sun gaya mana, yanzu haka ma shirn zuwa
sasan naki muke, sai kuma gaki. Ashe kuma
mama an fasa karatu aure za'ayi?" Tace, "to
yaya zamu yi, mutane sun cikawa alh. ido,
sannan da alama ita ma maman tana son yaron.
'ya mace kuwa idan ta nuna tana son aure, to yi
mata auran shine mafi alkhairi ga iyaynta". H.
Gaje tace, "gaskya kuwa, gidan hutu ai dole a so
shi. Ai kinga wadancan da yake ya ku bayi ne
bata ce tana so ba". Umma ta dube ta sosai, "me
kike nufi gaje?" tace, "me kuwa? Ita gaskya ai
daya ce, sannan arziki na Allah ne. Daga ali har
sa'eed bamu fidda masu rai ba". Ta tsura mata
ido cike da mamaki, kfn tace, "na wuce kiyi min
habaici gaje, domin ni ba sa'arki bace.
Kasancewar ali da sa'eed 'yan uwa ga mama bai
zama dole wani a cknsu ya aureta ba, domin shi
aure nufi ne na Allah. Shi ke kullashi, kuma duk
fassarar da zaku yi man kun dade ba kuyi ba.
Allah yasan zcyrmu akan komai". Ta tashi ta bar
sasan. Wata uwar shewa suka kwasa hannu
bibiyu suka tafa, "tabarmar kunya....," inji h.
Gaje, "da hauka ake nade ta!" h. Hajo ta bata
amsa.! Umma na shiga sasanta ta iske baraka,
shigowarta kenan suna murnar ganin juna ita da
mama. "a'a baraka ce?" "nice umma, ina yini?"
"lfya kalau. Ya babanki da innar taki?" "duk suna
lfy. Tace a gaisheki. Wai dinkunan sunyi miki
kuwa?" "wle sunyi kyau" Mama ta cafe, "baki ga
ta cabawa abba ado ba yau tun safe?". Ta yo
mata dakuwa, "gidanku!". Ta wuce suna mata
dariya har da tafawa. Janye ta mama tayi ckn
daknta, "kamar kinsan ina nemanki kawata"
tace, "nima haka kawai naji ina son ganinki,
nacewa inna zanzo nan. Har tana min tsiya, wai
anyi hutun kenan, bama gajiya da bin hanya".
Suka yi 'yar drya, kafn mama tace, "kinsan wani
abu?" ta kada kai. "kawai dazu da rana sai ga
mahaifn al'ameen........" ta katseta ido waje,
"don Allah? Sai aka yi yaya?" tace, "uhm! In
gaya miki Abba ya amince! Kimji ynda nake ji
yau a duniya?". Ta cika da mamaki, "tafdi! Allah
ya saka masa da alkhairi" "ameen ke dai. Ni
ynzu al'ameen din nake son gani, idan yaji
wannan albishir din. Kinsan Allah, da ni duk na
hakura ina 'yar dabara inje hutu minna, idan
Abba ya hana ma rika gaisawa a can" Tace,
"amma idonki ya rufe, wa ya gaya miki a minna
yake da zama?" "nasan a zariya yake, amma
dole yaje minna, musamman idan yasan zai
ganni a can". "ke mama......" "meye?" "meye
kuwa? Allah dai ya nuna mana lokacn lfya". "to
ynzu zaki je hutun ko kin fasa?" "Gobe insha
Allahu zan tafi, amma dole in dan saurara in ga
ko zaizo goben" Tace, "kema kinsan dole gobe ya
dauko hanya, wannan babban albishir ina zai
tsoma ransa, idan bai zo ya ganki ba?". Suka
tafa suna 'yar driya. Har gab da magariba suna
tare, sannan mama tayi mata rakiya ta koma
gida. Inna saude kanta tayi farin cikin jin
wannan labari.! Duk da cewar maganganun su
Haj Gaji sun bala'in batawa Umma rai sam bata
gayawa Uban dwk ba gudun tashin hsnkali da
sabani, hakan yasa bata kwana da zancen cikin
ranta ba taci gaba da sabgoginta kamar ba abnd
ya farau. Mama kuwa ta kintsa kayanta a jaka
tare da sakonnin Umma wanda zata tafi dasu
don yin tsaraba, Abba da kansa yake gaya mata
kar tayi gaggawar tafiya watakila Al-Ameen
yazo kada suyi sabani, ya wuce gona da kazzin
idan har ya dawo daga goba bai zo ba shi zai
kaita, ba karamin dadi Mama taji ba sbd a zahiri
Abbanta yana nuna jin dadinsa da sauyin da
Allah ya kawo musu a lokaci guda. Mama ta
caba kwalliyar mamaki irin wacce take gigita
samarin gidansu duk sanda sukai tozali da ita
duk da cewar basanan Ali yana aiki da karamar
hukumar birnin gwari shi kuwa Sa'eed dan-
sandan-bada-hannu ne a Kd. Shi Sa'eed
Mamansa ce ta dauki abin da zafi tuni ya gane
ta wuce ajinsa ya fara neman wata anan Kd. Can
sassan ta shiga don gaishesu tare da shaida
musu zata tafi hutu kamar yanda ta saba idan
zata tafin. Tana shiga danlami ta samu yana
wankin kayansa ya zura mata ido harta iso
gunsa tana murmushi duk da cewar shi tasa
fuskar a daure take "wanki kakeyi?" "Uhmmn.....
Kuma a zaune don lalaci yaushe zai fita.. Yace
ni banson iyayinki.. Tace iyayi?? Wai naga sai
wani cin magani kakeyi baka koshi bane halan?
Ya dubeta sosai Yace Eh yunwa nakeji.. Saiki
kawo min abinci matar masu kudi! Baki sake
take kallonsa "matar masu kudi? Ban gane
nuffinka ba? Yace jeki abnd ya kawoki karki
hanani aiki na.. Ta gyara tsayuwa tace
maganarka tana da manufa danlami me kake
nufi da matar masu kudi? Sai taji magana daga
bakin Haj Gaje ai ba karya bane yaga kinyi kalar
matar masu kudi ne shiyasa ya fadi haka ai
kinga masu kudin suna zuwa aure ya tabbata!
Gaba daya ta daburce ta rasa ina wann magana
ta dosa ba shiyasa tayi tsaye tana kallon Haj
Gaje. Tace ki daina kallona idan baki gane ba ki
tambayi mai hankali yayi miki bayani. Ta wuce
abin ta cikin daki. Take nan ran Mama ya baci.
Ta juya cikin sauri ta bar sassan, kicibis sukayi
da Salisu ya dubeta da kyau yace ashe dama duk
abun yaudara ce koda yake dama kin gaya min
su Ya Ali basa gabanki, ta kalleshi tace kwarai
haka ne ko akwa me yi min dole? Sannan yin
kwadayi ma ai dace ne wani idan zai like yayi
kwadayin ma bai samu mtsewww... Taja dogon
tsaki tabar gurin yayin da Haj Hajjo ta tsaya
gabansa amma kai sakarai ne tsayawa kayi tana
gaya maka magana son ranta? Kai tsaranta ne?
Sakarai kawai. Itama taja tsakin ta wuce shi.
Haushi kamar ya hadiyi zuciya cikin sauri ya
fice kofar gida. Gaban Ummanta ta zube idanuwa
cike da kwalla tace Umma meke faruwa ne cikin
gidan nan ake yada habaici? Tace shine zakiwa
kuka? To ina ruwanki da abnd ke faruwa? Tunda
ba matsalar mu bace. Umma kinsan ban son
abin haushi idan su salisu sukaci gaba da yi min
habaici wllh zan basu mmk gara ki gayawa Abba
yayiwa tufkar hanci tun kafin gidan nan ya
yamutse. Ta zura mata ido kinga babu abnd ya
shafeki da surutunsu domin ba shi zai hana abnd
Allah ya shirya ba, biye masu zakiyi duk ku
haukace gaba daya? Ina so ki dauke kanki daga
gare su tamkar yadda nayi. Ta goge kwalla tace
kema sunyi miki ne? Tace tun jiya iyayensu suka
fara amma bai dameni ba don nasan wann abu
bani na shkirya shi ba ba kuma Abban ki bane
balle ke. Shiyasa ko shi Alhajin ban gayawa ba
sbd bana son hayaniya kin gane? Ta dan yi jim
sannan ta amsa da ka tana goge kwalla. Tashi ki
je ki wanke fuskarki. Ta mike zata wuce yaro
yayi sallama yace wai ance Sakeena tazo Al-
Ameen yazo. Gabanta ya yanke ya fadi ta zurawa
yaron ido ta rasa me zatace? Umman ce ta bashi
amsa to kace tana zuwa. Ya juya ya fita, kin
tsaya ki kam kije ki shiryo mana. Ta shige
dakinta sanyi na kwarar zuciyarta. Ta tsaya
gaban mudubi ta gyara fuskarta ta suro gyalenta
ta yafa tayo waje. Umma na tsakar gida ta mika
mata makulli tace ki kaishi falo karku tsaya a
waje. Fuska sake ta amsa ranta ya kara sol. Tayi
kofar gida cikin sauri amma cikin sanda ta leko
yana tsaye jingine da motarsa ya zurawa zauren
ido shiyasa tayi arba da idanuwansa masu haske
da girma. Sbd haka kunya ta lullubeta ta koma
zauren ta lafe tana maida numfashi kawai
muryarsa taji bisa kanta yana fadin sallama
gareki ma'abociyar kyau! Jim tayi shiru kamar
ruwa ya cita hannunta daya rufe da fuskarta
haka shima ya tsaya ya zura mata ido dauke da
murmushi mai isar da sako barkatai. A nutse ta
bude fuskarta ta dubeshi "sannu da zuwa"
taushin muryarta yasa jinin jikinsa ya tsinke yaji
son Mama ya kara malale kowane lungu cikin
zuciyarsa tamkar ya hadiyeta yakeji kai bai
tabajin azababben so irin wanda ya kama hsi ba,
ya numfasa yace gimbiya ta kenan. An fito lfy?
Tace kalau ya hanya? Yasu Baba sukaje gida?
Ya amsa duka lfy lau, tace mungide Allah. Yanzu
ka ban minti daya zan bude maka inda zaka
zauna, yace ni kadai? Gsky ban yarda ba! Tayi
dan murmushi to inda zamu zauna. Yauwa yanzu
naji batu gara da kika gyara. Ta wuce tana 'yar
drya. Shi kuma yayi wawan ajiyar zcya, ya dawo
jkn motrsa ya harde. Jimawa kadan ta budo
babban kofar get da ke can wani bangare na
katangar gidan, ta fito tace dashi, "bismillah!".
Bai yarda ta tsere masa ba, jerawa suka yi suna
tafe yana fadin, "ga Amarya ga Ango!". Ta ballo
masa harara, fuskarta kunshe da kyakkawan
murmushi, har suka shige falon. Ta nuna masa
kujera ya zauna, ita ma ta koma gefen damarsa
ta zauna, suka sake gaisawa. Yace, "to Alhamdu
lillah, godiya ta tabbata ga Allah wnda ya nufi
al'ameen ya zama angon sakeena. Ko kinsan
cewa jiya banyi barcin kirki ba?". Ta kada kai,
"me yasa?" "ban taba zaton abba zai saurari
kukana ba, shi yasa na kasance tamkar maraya,
ni kadai cikn daki, bana aikn komai sai na
addu'a, idanuwan nan sun fidda hawaye gaban
Ubangiji don neman biyan bukata. Beliete me ma
jinina ya hau kfn dady ya dawo......." ta katse
shi, "amma da ya dawo fa?" yace, "albishir din
da ya dawo min dashi ya hana min barci sbd
tsabar murna da farin ciki, cnt explain sakeena"
tace, "ka mamayi abba, kuma ni kaina nayi
mamakin amincewarsa, koda yake abba mai
saukn kai ne, kuma bai cika jayayya ckn
al'amarn rayuwa ba" "na yarda da ke. allah ya
sakawa abba da alkhairi, domin ya ceci
rayuwata. Ko har da taki?" Ta dube shi suka
hada ido, ta dan kauda kai. Tayi 'yar drya. Yace,
"ban damu ba, tnda ni nayi nasara". Tace, "ni
kuma bazan yarda da kai ba, sai naga alkawari
na". Ya zuro mata ido, "a tunaninki zan manta
ne? No sakeena, kece komai nawa, bazan taba
mantawa da wani abu wnda ke alaka da ke ba,
balle kuma ace alkawari ne......," Ya tura hannu
aljihu ya dauko wani dan karamin mazubi ya
bude, ya nuno mata wani gangariyan zoben
zinari yace, "ina jin wannan shine alkawarin ko?"
Baknta yaki rufuwa, ya matso gabnta ya
tsugunna ya miko mata, tasa hannu ta dauka ta
zurawa yatsanta. Wayyo! Al'ameen zuru kawai
yayi yana kalln zara-zaran yatsnta, zoben nan
ya zauna kamar da shi aka halicce ta. "tsarki ya
tabbata ga Ubangijn da ya halicce ki sakeena".
Ya dago ido ya dubeta, "kiyi min alkawari har
abada ba zaki daina sona ba". Tace, "insha
Allahu zaka sameni mai cika alkawari komai
wuya, komai tsanani zan jure akan alkawarinka.
Har abada kai kadai ne, ba wani sai kai"
Idanuwnsa suka kawo kwalla, murya sanyaye
yace, "na gode sakeena" tace, "kar ka damu". Ya
mika mata gidan zoben ta karba. Ya koma
mazauninsa ya zauna, abba ya gaya wa dadyna
kema irin karatu zaki yi, kinga ta kwana gidan
sauki, wai matar likita ta haifi panadol" Ta fara
drya, "oh, drya na baki ko? To shikenan, ai ba ke
matar likitan zaki haifi panadol din ba........"
tace, "au son kai ne abin?" "eh mana. Nawa
bouncing baby ne, baby boy ko girl? Zabar min".
Ta mako masa harara, ya hau drya. "well, daga
nan idan na tashi zariya zan wuce, sai kuma nxt
week zan dawo in sake ganin gimbiyata" tace,
"Allah ya kaimu lfya, nima anjiman zan wuce
minna wajn yayana zanyi hutu" Ya bude ido,
"owk, kuma shine tnda nazo baki gaya min ba, ai
sai in juya in kaiki, daga can in wuce". Ta kada
kai, "bana son ka wahala, ka wuce wurin aiki
abinka. Babu komai". Yace, "uhm...... To na
gode, amma ina fatan akwai phon number a can,
kin ga sai mu rika gaisawa ko?" tace, "eh akwai
land-line zan baka" Yayi ajiyar zuciya, sannan
yace, "yanzu ki bani labari, ku nawa ne a
daknku?" tace, "mu hudu, yaya abdul-kadeer
soja, shine babba, sai yaya abdul-kareem yana
CBN Minna, shine zani hutu gunsa, then yaya
Abdul-rahman yana kadna, lst year ya fara aiki
da ma'aikatar kimiyya da fasaha ta jiha, shi
kadai ne bai yi aure ba......" "sai kuma ke ko?".
Tayi 'yar dryar nan da yake so. Yace, "kun
burgeni, Abdul 3, ni kuwa tilo ne ckn gdnmu,
bani da yaya balle kani. Kadaicn yayi min yawa
sakeena". Tace, "kamar ynda gata yayi maka
yawa ba" "haka kike gani? No ba zaki gane ba,
naso ace akwai wasu, musamman kanne, na rika
yi musu 'yan mazurai ina cewa, kai ku bari
mana! You knw, smthn like that dai. Amma ka
zauna shiru babu mai maka fada, babu wnda
zaka yi wa? Babu dadi abin". Ckn tausayi tace,
"ai shirin na Allah ne" yace, "yes haka ne, na
yarda. Amma very soon zan samu many babies,
su zagayeni, dady kalla! Dady bani wannan!
Dady sa min riga! Kin gane? Ina son hayaniyar
yara sosai" Tana drya tace, "kana da aiki" "come
on, muna da aiki dai. Ai mu biyu ne muna
tsakhya, sun zagaye mu, na 6 can 6. Wuu!
Confusion! Wa zai gane min ke?" Hannunta
tallafe da kunci, ta zuba masa ido tana kallnsa
yana ta zuba bayani, idanuwanta suna nuna mata
yaran zagaye da shi. Shi yasa yana sa aya ta
fashe da drya. Yace, "drya ma na baki ko?
Yarnya gudu zanyi in kyaleki dasu" Ta dan tabe
baki, ta tashi tsam! Zata bar falon, yace "ina za
ki? Har kinji tsoro ne?" tace, "tsorn me? Ruwa
zan kawo maka, kaji dadin santin". Sosai yayi
drya, har ta bar falon. Ya koma a hnkali ya
jingina bayansa da kujera, ya rufe ido tamkar
mai barci. Wani kasaitaccen taro yake hangowa,
wnda cikarsa baya misaltuwa. Jimawa kadan ya
keto taron rike da hannun sakeenarsa, da ka
dube su kaga amarya da ango. Jama'a na musu
tafi, su kuwa baki yaki rufuwa. Bisa wasu
kasaitattun kujeru suka zauna, ta tsiyaya lemu a
kofi ta mika masa a baki, ya dauka zai fara
sha...... "Assalamu alaikum!". Ya bude ido a
hnkali, tana tsugunne gabansa rike da kofin
ruwa. "barci kayi? Lallai na dade da yawa, ayi
min afuwa". Ya saki wani wawan numfashi, ya
girgiza kai, "dogon tunani ne ya dauke ni. A
duniya bani da wani burin da ya wuce aurenki
sakeena.....". Yayi dan shiru jim! Yana kallnta,
ya kada kai, sannan ya karbi kofin hannunta, "na
gode". Ya shanye ruwan, ta zuba masa lemu, ta
koma ta zauna, ilahirin jiknta ya mutu. Wane irn
so al'ameen ke mata? Ta tambayi kanta. Tana
ganin ita ma irnsa take yi masa, domin itama
burinta ta zama mata a gareshi. Ko don ita
kunya na maida ita kurma, shi yasa yake ganin
shi kadai ke da buri a kanta? Zurun da tayi masa
a rashn sani, shi ya jawo hnkalnsa ya daina
kurbar lemun. Ya matso gabnta yasa mata kofn a
baknta, ta sha kadan ta dube shi, "ba kai kadai
ke da buri ba Dr., sanin kanka ne mu duka muna
da bukatar kasncewa tare. Idan baka sani, ynzu
na gaya maka ka sani, don ka daina damuwa".
Ya numfasa yace, "Allah ya tabbatar mana da
wannan buri" tace, "amin". A natse suka zauna
suka ci gaba da faranta wa junansu rai da
dad'ad'an kalamai. A nan yayi sallar azahar, ya
ci abnci, sannan yayi shirn wucewa zrya. Ita ta
jagorance shi ya shiga ya gaida umma, don ya
matsa kwarai yana son kai mata gaisuwa. Ta
kuwa ji dadi, ta kuma yaba da tarbiyyar sa,
yanaynsa da alkunyar sa.! Suna tsaye jikin
motarsa sallama taki karewa Ya Ali ya danno
kofar gidan da jakarsa akafada, bakinta har
kunne ta tarbeshi Ya Ali! Sannu da zuwa, ya
kalleta ya kalli wanda take tsaye dashi kafin ya
amsa. Ya mikawa bako hannu tare da sallama
(Allah Sarki ubana akwai jarumta!). Ita kuma
tana fadin Ya Aliyu kenan cosin dina ne, Allah
sarki inji Al-Ameen an dawo lfy? Yace lfy lau!
To madalla. Aliyu yace dauke da matsanancin
kishi da mamaki a ransa. Al-Ameen kuwa fadi
yake kuna satar kama da juna da an ganshi an
ga dan'uwanki, tace ko? To ai da Baban shi da
Abba duk dakinsu daya. A Birnin gwari yake aiki.
That's gud' ina ganin ya kamata in lallaba in
barki ku wuce ko? Kar dare yayi. Tace hakane,
kai din ma bana son dare yayi maka. To
shikenan karfe tara ISA zakiji wayata. Allah ya
yarda a sauka lfy. Ameen. Ya shiga mota ta rufe
masa tana kara fadin kayi tuki a hankali, yace
thank U. Ta juya zata wuce yayai kiranta
Skaeena! Ta juyo tare da murmushi yace "I love
you!" Ta kara fadada murmushinta ta rausaya kai
ta juya zata wuce Sakeena! Ta sake juyowa. I
love u! Tayi jim kafin tace I love U too! Ta ruga
cikin gida ya rakata da kallo bakinsa kamar
gonar auduga kasala ta rufe ya kasa tada motar.
Ta sake lekowa tayi masa bye-bye shima ya
daga mata hannu sannan ya sami karfin tada
motar yayi ribas yai kwana ya fada hanya ya
kara dago mata hannu ya wuce cike da begenta
tamkar yadda takeji a ranta. Tana shiga cikin
gida muryar Ya Ali kawai ke tashi yana
bambamin fada "ai dama haka rayuwa take
kiri'kiri jininka saiya wulakantaka don baka da
kudi! Muma muna kan hanya indai arzikine
abuna Allah! (Kana da gsky Baffaba!) Mama tayi
tsaye jikin kofar sassansu tana saurare haj Hajjo
tace nace dai kayi shiru haka ko? To kaci gaba
idan hakan shi zai sa a baka ita. Mama dai ba
saurana mata tafi ba ga yanmata nan bila adadin
duk wacce ka zaba sonka zatayi idan ita ma ba
kwadayi tasa wa ranta ba. Sbd haka kar in sake
jin wata magana ta fito daga bakinka akan wata
Mama! BARKA DA SALLAH
HAUSA Novels BOOK
BAKIN CIKI 1****5 H. Gaje ta cafe, "ki kyale shi
ya amayar da bacin ransa, kar ya zame masa
ciwo! Da wanne zai ji?" yace, "ai inna ba zata
gane ba mama gaje, wannan rainin arziki ne a
ckn gida. Uwa daya uba daya? Haba! Ya kamata
a duba!". H. Hajo tace, "wa zai duba? Lallai
ranka zai fita idan har zaka kwallafa wa kanka
wannan maganar!" Tana sa aya daidai da
sallamar uban dawaki, yayi tsaye yana kalln
mama na zubda kwalla, yaynda yaji muryar h.
Gaje na fadin, "babu wnda zai duba wannan
al'amari, tnda dai shi da kansa alh. Babban ya
ya yamutsa al'amarin!". Kalaman da suka fada
kunnuwan uban dawaki tare da bugun zcy, ya
zurawa mama ido tamkar ynda take kallnsa, "me
ke faruwa?". Bai gama rufe baki ba yaga Ali ya
fito a fusace, idanuwnsa na tsatso kwalla. Shi
kansa gabnsa yayi mugun faduwa, kasala ta
kama shi, ya rage sauri, "kai ali lfy?". Ya gnge
fuska, ya dan rankwafa yace, "sannu abba!"
"nace me ya faru?" "babu komai" "ina wasa da
kai ne? Kake gaya min babu komai!". Mama
tace, "abba tun jiya gidan nan a yamutse yake,
ana ta habaici tare da yada magana akan zancen
al'ameen. Umma taki gaya maka ne sbd gudun
fitina. Amma kowa gani yake yi sbd kudi ne yasa
ka amince inyi aure, bayn ka hana kowa kace
karatu zanyi. Me yasa za'ayi mana mugun
zato?" Nan da nan ransa ya baci, yayi fushi
sosai, ya kwalawa umma kira. Ta fito ta samesu
ransa bace. Ckn fushi yace, "kira min matan
gidan nan!" "lfya alh?" yace, "ban son jin wata
magana". Tace, "alh ka kwntar da hnkalnka kayi
hakuri har zuwa lokcn da mazajnsu zasu dawo.
Zai fi kyau duk abnda zaka fadi ka fada a
gabnsu. Ina rokn wannan alfarmar don girmn
Allah!". Alh. yayi jim! Shiru yana kalln umma,
kafn ya dubi mama yace, "kin shirya kayanki?"
tace, "eh" "to kwaso ki zuba a mota maza mu
tafi". Ya wuce da sauri daknsa, kowa ya kama
gabnsa, har da ali ba tare da wani ya kara cewa
komai ba. Kayn jiknsa kawai uban dawaki ya
canza, yayi rawani kamar ynda ya saba, ya fito
lokacn mama na tsakar gida da jakar kaynta tare
da tsarabar da umma ta bayar a kaiwa yara.
"Baki kai kayan motar ba?" inji abba. Tace, "ai
basu da yawa, su kenan" "wuce muje". Umma
tace, "Allah ya tsare, a sauka lfya". Ya amsa da
amin, yayi waje. Mama ta biyo baynsa. Ali na
zaune bisa dakali tmkar yayi bindiga sbd tsabar
fushi da kishi, domin sosai yake son mama.
Kuma yayi wa ransa alkawari zai ci gaba da
farautarta, sai yaga abnda ya turewa buzu nad'i.
Shi yasa ya aje wa ransa zai iya jiran ta gama
karatnta. Shi kuma zai ci gaba da gina kansa da
duk wani tanadi wnda zaizo daidai da jin dadin
rayuwr aurnsu. Ina zai sa ransa yau yaji dadi?
Yana ganin mama ta shige mota idanuwnsa suka
yo tam! da hawaye. Musamman wannan zuwan
ita yazo gani, sanin cewa sunyi hutu. Kamar ya
kwarma ihu. Ya mike ya sake fadawa ckn gida.
Alh. Ya bude mota, kalla ya matso, "ranka ya
dade tfya za kuyi?" yace, "ai tare zamu tafi da
kai, taso ka shiga mota. Minna zan kai mama
na" yace, "to shi kenan". Ya mika masa makulli,
"ka tuka motar kalla, bana jin dadin jiki na". Ya
amsa yana fadin, "assha! Allah ya sauwake"
"amin". Ya bude gidan baya inda mama take,
shima ya shiga. Jikn mama ya kara sanyi, tasan
abbanta ya kanso suyi tfya su 2 kacal! Suna tafe
yana bata labarin duniya. Ta tabbata bacin rai ne
yasa ya gayyato kalla ya tuka su, gudun afkuwar
wani abu. Sun mika tfya shi babu mai magana,
shirun sam baya mata dadi, sbd haka tace,
"Abbana kayi hakuri don girman Allah, kar
hnkalnka ya tashi akan wannan maganar". Ya
dubeta sosai yace, "dole raina ya baci, sbd an
zarge ni akan abnda ba shine a ckn zcyata ba.
'Yan uwana basu yi min adalci ba, na tabbatar
da saninsu mataynsu ke yada habaici da
kananan maganganu. Amma zanyi wa tufkar
hanci. Tnda babu wnda ya haifa min ke". "kara
kayi fada dasu abba....." yace, "ya za'ayi in
tsaya ina fada da kannina? Umarni kawai zan
bayar, kuma dole kowa yabi idan ana son zaman
lfya. A iya sanina na basu hakknsu, na zauna da
su na gaya musu uzuri na. Amma duk da haka
basu gane cewar komai na Allah bane. Ke dai
abnda nake soki dashi, ki rike yarn nan amana,
sannan ki kara kula da kanki, don tsare
martabar gidan nan" tace, "Allah ya taimaki mai
martaba. Mamanka na tare da albarkar umma da
abbanta, da yardar Allah ba zata basu kunya ba".
Yayi dan murmushi yace, "Allah ya kara yi miki
albarka". Tare da kalla suka amsa, "Amin abba
Sun iso minna la'asar sakaliya, shi yasa ruwan
alwala kawai alh. Ya fara tambaya. Yayi sallah a
babban falon gidan, yaynda jerin kayan abincnsa
ke jiransa. 'yan jikoknsa kuwa sai safa da
marwa suke yi. Ya idar da sallar, suna jiran su
tumurmushe shi. Ilai kuwa yana idarwa suka
zube a jiknsa, yana drya ya soma tsokanarsu"
"ameera tsohuwa mai majina" tace, "Allah ameer
ne mai majina" ameer yace, "karya ne abba,
kullum wa ake ba tishu in zamu skul?". Abba
yace, "kyaleta Uwair, waye bai san halima
tsohuwa bace? Mai majina kawai". Ai nan da nan
tayi fushi ta tashi fuu.... Zata fice,suna mata
drya. Sai ga sallamar anti Rabi. "momy kin
gansu ko? Wai nice mai majina". Ita ma dryar
tayi ta wuce ta zube gabn abba ta kwashi
gaisuwa, sannan ta tambayi mutan gida. Yace,
"duk lfyrsu kalau" Kuka ameera ke yi, yaynda
mama ta shigo da ita falon, "ynzu don Allah wa
ya taba min umma na?" yace, "kyale ta mai
majina ce, ni bana auranta!". Ta kara kware
baki, mama ta rungume ta, "kiyi shiru ki kyale
shi, ke ma baki auran. Me zaki yi da shi tsoho?"
ameer sai drya yake mata. Da yaga kukan da
gaske take ynsa sai ya jawota jiknsa, "wanene
ya taba min madam dita? Manta da ameer, tsoho
ne shima. Ina dady bai dawo bane?" ta amsa da
kai tana murzar ido. Anti rabi tace, "bai shigo
gida ba tukuna, amma yana bisa hnya". Yace,
"To Allah ya dawo dashi lfya" suka ce amin..anti
rabi da mama suka bashi wuri yaci abinci tare da
jikoknsa. Yan minticoci bayan kammalawarsa
motar Ya Abdulkareem tayi fakin a harabar
gidan, ganin motar Abbansu yasa ya fito da
sauri kalla ya tarbe shi ya karbi jakarsa yayi
masa sannu da zuwa suka gaisa, tare suka shigo
falon ya zube gaban Alh yana fadin oyoyo
abbanmu! Yace Abdulkareem dan Abba sadauki!
Ya kara fadada dariyarsa domin yana jin dadin
kirarin da Abba yake masa tun yana yaro sbd
tsananin kokarinsa wajen neman duk abnd yake
so musamman ilimi. A yaran gidan kaf! Babu
wanda ya fara sauke Qur'ani da karancin
shekaru sai shi, yana 14yrs yayi sauka kuma
yasan littattafai dayawa. Daka dubeshi kaga
Mama illa dara daran idanuwanta ne kadai suka
banbantasu. Kazo lfy Abba? Yasu Umma? Yace
lfy lau Mamana na kawo maka hutu.....Mama?
Yanzu haka tana ciki? Sai gata ta shigo falon ta
karaso gunsa da gudu ta zube jikinsa Yayana!.
Ya kamo kunnenta ba wani yayankitashi zakiyi ki
koma inda kika fito! Tace Allah sarki yayana dan
Abba sadauki! Ya dada mata duka suna ta dariya
"maras kunya ba Abj kika fiso ba? Ai dama nace
duk randa kikazo yan kafafuwan zan karya..
Tace, "tuba nake yayana, daga yau duk hutu
anan zan yi shi" yace, "naji amma ban yarda ba,
ke da soja ai sai Allah, watakila kema sojan zaki
aura". Ta kada kai ckn shagwaba, "a'a!" Abba
yace, "ai baka ma sani ba? To karkade kunnenka
kasha labari". "ko abba? To bani insha". Abba na
bashi labari, ita kuma mama na boye a bayn
yayn nata. Tas! Ya zayyane masa abnda ke
faruwa. Abdul-kareem ya cika da mamaki, "to
menene abn tashn hnkali a nan?" yace, "nima shi
na gani, har ga Allah zcya ta bata da wani nufi
akan wannan al'amari, amma tnda haka suka
dauko zamu tafi a hakan, kuma mama zata auri
wnda take so". Ya dan kada kai yace, "kayi
hakuri abba, kasan shi mutm a kullm yakan fi
son kansa maimakn neman zabn Allah. Abu
kankani sai a ruruta shi yayi girman da zai
rarraba kan zumunci. Abba ka dauki girma
kamar ynda ka saba, ka dauke kai ga
tsegunguman mata". Ya zura masa ido yana
murmushi, "dan abba sadauki! Duk abnda ka fadi
gskiya ne, shi yasa ma bazan gaya wa yaynku
ba, don nasan halnsa, daga ali har mutn gidan
babu wnda zai kyale idan hauknsa ta tashi".
Yace, "haka ne, kuma nasan ali yana son mama,
dole yaji zafi a rnsa, amma su a matsaynsu na
manya ai bai kamata su rika tnzira shi ba.
Abnda ya dace shine su nuna masa komai na
Allah ne. Amma muna musu fatan Allah ya
ganas da su. Ke kuma mama ki rike amana,
domin duk garin nan babu wnda bai san familn
marafan lafai ba. Babban gida ne masu mutnci.
So u hv 2 b very carefl, ke ma ki nuna wa duniya
kin fito daga babban gida mai cike da tarbiyya,
OK?" Tace, "insha Allahu yaya zanyi iya kokari
na". Yace, "to da kyau likita matar likita. Abba
kasan wani abu? Ai mu juma munyi bye-bye da
rashn lfya". Suna ta drya, anti rabi ta shigo
itama. Sun jima suna hira, sannan uban dawaki
ya bar garin minna tare da yarnsa kalla.! Anyi
sallar magriba lokacn da suka shigo Fandogari,
don haka a guje uban dawaki ya nemi bada
farali. Bai wani ci abnci sosai ba, sbd abncn da
ya ci da yammacin dazu a minna. Umma ya aika
ta tattaro masa kaf kannensa da 'ya'yan gidan
tare da ali. Duk suka hallara a falnsa, ya dubesu
ya fara magana ckn rashn jin dadi, "abnda yasa
nace a kira min ku, a gskya abnda ya biyo baya
sakamakn maganar da muka yi da ku jiya, sam
banji dadnsa ba. Basiru da amamu kar ku manta
gaba daynmu ciki daya muka fito, babu bare.
Kar ku bari tsegunguman mata su raba kawunan
mu, domin da halima da hajo da gaje tare suka
same mu. Bai kamata in gaya muku uzuri na ba,
ku kuma ku koma kuna min yankn baya wajn
mataynku, har su sami damar yada maganganu
marasa dadi akai ba. Ko ban haifi daya daga
cknku ba, ina zatn ni uba ne a gareku, kuma
daidai gwargwado ban shiga hakkn kowa ba. Ali
da sa'eed a wancn lokaci sun yunkuro,
kowannensu yana son auren mama, a gabnku
yaran nan suka rika rigima a junansu, gaba ta
kullu, babu mai kalln dan uwnsa. Sbd Allah idan
ban ynke wancan hukunci ba me ya kamata inyi?
Shi za'a tsaga mama gida 2 ne, ali ya auri rabi
sa'eed ya auri rabi? A gani na idn aka hana
kowa zai fi mana alkhairi. Ko da bani da ra'ayn
mama tayi zurfn karatu, ballantana ina da shi.
Wlh bani da wani buri akan mama da ya wuce
tayi zurfn karatu ta zama likita gabana. Amma
da Allah ya sauya al'amarinsa, ba zan iya
jayayya ba. Sai dai a cknku laf din nan na bar
muku zabi, idn akwai mai iya yin wani abu bayn
wnda Allah ya zartar bismilla, ina saurarnsa. Ni
kam na yarda nayi gmanin al'ameen Allah ne ya
turo shi, ban isa in koreshi ba. Kuna iya kirana
kuda sbd kwadayi, ba zai sauya komai a jikina
ba, don nasan har ga Allah bana bukatar sisin
kwabo daga al'ameen ko mahaifnsa. Na kare
maganata, idan akwai mai abin cewa yana da
damar fadi". Gaba daya ka rasa mai yin koda
motsi, sbd dogn jawabn uban dawaki ya tattaro
musu kunya ckn idanuwnsu, musamman matan.
Jin sunyi shiru, uban dawaki ya kara da cewa,
"idan babu mai magana kuna iya tfya, shikenan
magana ta kare" Har matan sun mike, alh.
Basiru yace, "ku zauna. A gskya munyi kuskure,
amma ynzu mun gane bamu kyauta ba ko kadan.
Kayi hakuri alh. Da yardar Allah wata magana ba
zata sake bullowa akan mama ba. Ku kuma hajo
da gaje ku ba alh. hakuri, har ma da h. Halima"
Da ganin fuskoknsu kowacce ba akan son ranta
take magana ba. Sun dai bada hakurin, kuma
abba da umma sun yafe, sun maida komai ba
komai ba, a matsaynsu na manyan gida, sun
nada gammo sun dauki girman kamar ynda
hausawa ke fadin Babba juji ne. Aik. Adamu ma
yayi nasa dan guntun jawabin na neman afuwa.
Kowa ya tashi aka bar Ali a zaune, ba tare da
yace wani abu ba. Abba ya dube shi yace, "akwai
magana ne ali?" ya karkada kansa da ke
sunkuye, sai hawaye shar-shar! Suka hau zuba.
Uban dawaki ya sauke numfashi, gaba daya
jiknsa ya mutu. Harga Allah bai taba tunanin
soyayyar mama tayi zurfi ckn zcyar ali haka ba,
wa ke ganin hawayn ali? Da yarntarsa ma ba
karamar azaba ke sanyashi kuka ba, shi yasa
yaci sunansa Gadanga! Domin kaf tsaransa babu
mai nuna masa yatsa. "zo nan ali!" yayi kirnsa
yana nuna masa waje bisa kujera kusa da shi,
"zauna kaji". Ya zauna yana goge kwalla. "abnda
nake sonka dashi ali kayi wa girman Allah ka
dauki imani ckn ranka. Wlh a zatona tuni kun
share maganar mama a zuktnku, ganin na jima
da soke maganar. Amma kayi hakuri, ka dauki
dangana kasa wa ranka, duk abnda Allah ya
hukunta daidai ne" Ya dan gnge kwalla ya dube
shi, "abba sa'eed ne ya hakura, amma ni burina
inyi ta jiran mama har zuwa lokacn da zata
gama karatnta. Kullum addu'a nake yi Allah yasa
a tsayn shekarun nan zcyr mama ta aminta da
ni". Ya numfasa ya kada kai, sannan ya ci gaba,
"bansan yanda zanyi ba abba". Abba ya rungumo
kafadarsa, "hakuri magani ne ali, ban son ka
tashi hnkalnka. Mama 'yar uwarka ce, ka
taimaka ka bata goyn baya tare da addu'ar fatan
alkhairi, kaji? Ka kwntar da hnkalnka, nayi
rantsuwa da mama tana da kanwa da na baka
ita. Amma tnda babu, ina son kasa natsuwa ckn
ranka, ka ji ni?" Yace, "naji abba, kuma na
gode". Umma tace, "nima dai hakurn nan shi zan
baka ali, gaba daya hawaynka sun kashe min
jiki. Amma babu abnda zamu iya yi, sai dai ince
Allah ya musnya maka da alkhairi" yace, "amin
umma". Abba yace, "to tashi kaje ka kwnta, ka ci
gaba da addu'a, komai zai wuce". Ya mike babu
kuzari ya bar falon. Shiru su umma suka yi
tsawn lokaci, kafn abba yace, "Allah ya kyauta!".
Ta cire tagumi tace, "amin. Da gaske ali yake yi"
"mtsw!" yayi dan tsaki ya tashi ya shige daknsa
dauke da tausayn ali, ya bar umma zugum! Tana
tunanin iska. Gidan yayi tsit! Ko da tasa
damuwar. Washe gari da wuri ali ya koma birnin
gwari don kara samun natsuwa. Idan bakwa
comments sai inga kamar littafin ne baiyi muku
dadi ba, na kuma sai inji bana son turowa din.

BAKIN CIKI 1***6 Karfe bakwai da rabi na safiya
wayar tebur ke ta bugawa a babban faln.
Dawowar anti rabi kenan daga rakiyar mai gidan
da yara da zai aje makrnta, kfn ya wuce wajn
aiki. Can gefn wayar ta nufa ta dauka tare da
sallama. Bai mance muryar da ya fara ji jiya
tawaya ba, don haka ya zarce da fadn, "ina
kwana anti?" tace, "lfya kalau, wa ke magana?"
"al'ameen ne'. Take ta fara fara'a, "au Allah
sarki, ya aiki?" "Alhamdu lillahi" "madalla, bari
in kira ta" "to na gode". Ta aje kan wayar gefe ta
wuce da sauri tana kira, "mama! Mama ki aje
girkn nan kizo, mutumin naki ya bugo!". Ta fito
daga kicn da sauri, suka hade a kofa. "wannan
likita naki da naci yake" "kai anti!" ta fadi cike
da fara'a. "ke dai jeki da sauri". Ta wuce tana
drya, ta dauki wayar, daddadar muryarta a
sanyaye tace, "hello!". Ya runtse ido yace, "hello
'yan mata ya aka yi?" tace, "kalau, an kwana
lfya?" "sosai ma, har da miyan barci". Tayi 'yar
drya, "kaji dadnka" yace, "har na kai ki? Nasan
barci kike yi aka taso ki". "haba, kamar wata
raguwa?" "ita ce mana. Kowa ya ganki ai yaga
kalalatu" "kai kuma kalala ba" Yayi drya yace,
"tun asuba nake tsaye ina shirn ofis. Na rataya
neck tie, shine nace bari in kira madam ta daura
min" Ta dan rufe fuska da hannu daya tana
murmushi. Yace, "baki ce komai ba" tace, "to me
zance?" "au ba zaki daura min ba?" tace, "na
daura!" yace, "ga abu a wuyana yana lilo kice kin
daura, don Allah ki daura min" Ya fada a
shagwabe. Tace, "yau na bani! To rufe idnka". Ya
kuwa runtse yace "na rufe" "me ka gani?". Ya
danne kan wayar a gefn wuynsa ckn tunaninsa
yake magana ido ruee, hannaynsa na aikin daura
neck tie din. Yace, "ga ki nan kin fito daga dakn
barci, kin zuba kwalliya da wani farin less, kin yi
kyau bebyna. Sai murmushi kike min, kin kama
neck tie din kina daura min........ "Wash!" ya
bude ido firgigi, jin ya shake wuyansa.
"menene?" Ta tambaya ido waje, ji tayi ya
shagwabe, "Gaskiya ba haka ake yi ba, ba haka
ake yi ba sakeena. Ai dai ba'a shake wuya". Drya
sosai ta kubce mata, "ni na shake ka?". Yana
sassauta daurn wuyn yana fadin, "da kyar fa
nake numfashi, so kike in suma?" tace, "kaga
zaka makara wlh, idan suka ma bulala babu
ruwana". Yace, "ya zaki ce in tafi? Kin bani
brkfst ne? Ga kofn tea nan a gabana, yi sauri ki
ban insha in wuce". Tace, "oya, dauki kofi kayi
bismilla". Ya dauka ya rufe ido yana kurba, yana
ganinta ckn idanuwnsa, itace ke bashi. "ka
shnye?" "minti daya, na kusa saura kadan". Ya
kwalkwale ya aje kofn, "yauwa, na koshi". Tace,
"good boy. To sai ka dawo ko?" "to me zan cewa
zobenki?" "ina gaishe shi". Ya zura wa zoben
ido, sannan ya sumbace shi yace, "wai yana
amsawa". Tayi murmushi, "shikenan, tek care,
ok?". Murya sanyaye ya amsa, "i will......." yayi
dan jim, tace, "ina jinka!" ya rada mata, "I love
u!". Ta dan numfasa tace, "me too!". Tayi saurn
kife kan wayar. Da baya da baya ta tafi har ta
jingina da kujera, ta wuce a natse ta zauna
shiru, hannunta na gugar zoben yatsnta. A lokaci
guda shi kuma al'ameen ya rataye kot dinsa, ya
suri makullai da jaka ckn kuzari ya fito ya kulle
gida, ya fada motarsa. Mai gadin rukunin
gidajen ya bude masa get. Bayn sun gaisa ya
mika masa dubu daya ya wuce. Mai gadi na ta
murna tare da sa albarka. Shi kam kullm ckn
sawa Dr. Al'ameen albarka yake, domin shi kadai
yake masa alkhairi duk safiya, yace yaci abnci.
Da ka dubi fuskar al'ameen zaka tabbatar yana
tattare da farn ciki ba karami ba. Tamkar ynda
mama ta kasnce babu sukuni sbd tsabar kewar
al'ameen dnta. Bayn ta gama ayyuknta tayi
wnka ta kimtsa, sai ta kwnta bisa gado ita
kadai, bata aikn komai sai tunaninsa. Al'amarn
kamar zai zautar da ita, domin da zarar ta tuna
shagwabar sa, "GASKIYA BA HAKA AKE YI BA!
Ba haka ake yi ba SAKEENA!! AI DAI BA'A
SHAKE WUYA!". Ta kan yi kamar zata mutu da
drya. Idan ta rufe ido shi take gani yana mata
yawo tare da yin abnda yake fadi a aikace. Kai a
hakikanin gaskiya al'ameen ya gigita zcyr
mama, ita kanta ba zata iya fayyace ynda take ji
ba game da so da kaunarsa. Duk ta kosa ya
dawo ofis, don tabbatar zai sake bugowa taji
muryar sa. Ilai kuwa yana shigowa gida biyar da
rabi na yamma a gajiye, kai tsaye wayar ya dosa
ya kira. Sai da yaji muryarta tsawn minti talatin,
sannan ya daina jin kasala. Har ya sami
natsuwar yin wnka, ya dan kwanta ya huta
kamar ynda ita gimbiyar ta umurce shi. Haka
suka kasnce suna renon jaririyar soyayyar su
gwanin ban sha'awa. Ita knta anti rabi abin na
birgeta har ta kan yiwa mama addu'ar Allah
yasa ynda al'ameen ke ji da ita abin ya dore har
ckn rayuwar aurnsu. Sun saba sosa, ba da mama
kadai ba, da kowa na ckn gidan babba da yaro
yasan al'ameen ta waya, kuma gaba daynsu
babu wnda bai kosa sati ya kare ba, don
al'ameen yazo su ganshi. Sai dai kash! Yanayn
aiki bai shigo minna ba sai karfe takwas da rabi
na safiyar asabar. Lallai ba karamin asubnci yayi
ba, sbd tsabar kosawa kai tsaye gidnsu ya wuce.
Kamar koda yaushe haka aka shrya masa tarba,
amma sammaknsa yai matukar ba maminra
mamaki, bata dai tmbaya bane don tasan daliln
ba zai wuce na sakeena ba, sbd gaba daya
wannan satin ita knta ta tabbata danta ya kusan
zautuwa, duk wayar da zai bugo labarin sakeena
yake bata. Suna gama gaisawa ya nufi kan
waya, tayi zuru tana kallnsa tare da saurarn da
wa zaiyi waya daga isowrsa? Tsammaninta ya
zama gaskiya, iabin ran nasa ya kira ya shaida
mata ya iso, kuma karfe goma insha Allahu yana
nan karasowa. Dadi kasheta mana! Ta kamo su
ameera abokn hirarta ta zayyane musu yaya zai
iso anjima kadan, duk suka dauki murna da
tsalle. Gagarumin shiri ya kankama, ta tsala ado
na fita tsara. Kai mama akwai kyau, yarnya
kamar aljana. Yaynta da anti rabi kansu kallnta
suke yi, duk da cewar sun saba ganin ta, kuma
sunsan mai kyau ce. Motsi kadan ta duba agogo,
karfe goma taki yi mata sauri.!! Dan alkawarn
kuwa goma daidai yana fakin a harabar gidan,
abnka da dan gari adireshn da ta gaya masa
tiryn-tiryn ya kawoshi gidn ba wata matsala. Ya
fito yayi tsaye jikn motrsa,ba tare da yasan
gimbiyr tasa na kallnsa ta tagar daknsu ba. Da
alama bai san ynda zaiyi bane asan ya iso.
Murya kawai taji a baynta ana fadin, "au leknsa
ma kike yi?". Ta juyo a firgice, duk kunya ta
rufeta, domin dai yaynta ne mai maganar. Tana
murmushi tare da boye fuska a jikn labule tace,
"a'a yaya". Yace, "zai fi kyau kije ki shigo dashi,
ba leknsa ta taga ba". Tace, to, ta wuce simi-
simi, yabi baynta da kallo yan 'yar drya. Ta
kama hannayn yaran suka fito tare. Kiris ya rage
al'ameen ya zube kasa, amma ilahirn jiknsa
babu inda baya rawa. Da sauri ya tokare jiknsa
damota ya zubo mata ido. Ita kuma sanyn gurin
ne ya bugeta, ya ratsha ckn fatarta har ya
tilasta wa tsigar jiknta tashi, sannan ta gane
ashe bata dauko mayafi ba sbd daburcewar da
tayi lokacn da yaynta ya kamata tana leke. Sbd
haka ta duka ta dauki ameera, suka karasa
gunsa. Fara'ar dole take yi a zahiri, amma gaba
daya ta tsargu, sam bata ji dadn fitowrta haka
ba. "oyoyo!" tace dashi. Ya sauke wawan
numfashi, murxa a dishe ya amsa, "kema
oyoyo!". Ya maida kallnsa kan yaran. Ya ci gaba,
"ga abokina ameer, ga kawata ameera. Zo
mana". Ya mika mata hannu. Da sauri taje gunsa
tana drya. Ya mama ta iya? Haka nan ta dake
tana jinsa da yaran, "wu! Kawata kina da nauyi
sosai. Shekarnki nawa?" tace, "4" tana nunawa
da yatnta. Yace, "kai kai kai! Gskya kin girme ni,
amma don gata har daukarki ake yi. Antnki na
sonki ko?". Mama ta watso masa harara, nufnsa
ya ganota ne? Ko kuwa duk tsabar tsarguwar ce?
Ita kuwa ameera drya kawai take yi. Ameer ya
tmbaya, "dama kai ne yaya al'ameen din?" yace,
"ni ne. Kana sona kaima?" ya makale a jiknsa
yace, "ina sonka". Ya rungumo kafadarsa, "to
Allah ya barmu tare". Yaynda ameera ita ma take
faman fadin, "nima ina sonka yaya". Ya zura
mata ido, yanaynta kamar sakeenarsa, nan da
nan ya sumbaceta yace, "nima haka ameera ta!"
Mama tace, "ya kamata mushiga daga ciki,
surutn yarn nan ba zai kare ba". Ya zura mata
ido baice komai ba. Tace, "muje mana" yace, "ai
ke muke jira". Bata so ta wuce gaba, shi yasa
tace, "Bismilla muje". Ya sauke ameera yana
fadin, "bari in dauko muku tsarabarku ko?". Ya
bude gidan baya ya kwaso ledoji 2 manya, ya
mika wa ameera 1 yace, "to muje ckn gida".
Yara suka yi gaba suka bar mama na ta nuku-
nuknta.! Suna shiga falon kafin ya gama
sallamar yaran ta sukake tabar falon, shi dai ya
dagi kai ne bai ganta ba yaran suka wuce da
ledar tsarabarsu. Ya aje ta hannunsa gefe ya
nemi waje ya zauna yana maida numfashi domin
har yanzu kirjinsa bugawa yakeyi shiyasa yana
zama kasala ta rufeshi. Jim kadan Ya
AbdulKadeer ya shigo tare da sallama Al-Ameen
yayi wuf ya mike dauke da fara'a ya mika masa
hannu suka gaisa suka tambayi juna aiki. Ya AK
yace kuma harda dawainiya? Yace ahaba ba
wani abu. Madalla an gode, zauna mana nizan
dan fita ne saina dawo yace to a dawo lfy. Baiyi
sakwan uku da zama ba Sakeena ta shigo jikinta
rufe da mayafi hannunta dauke da tire cike da
abubuwan sha gabansa ta aje, shi kuwa bai
daina kallonta ba ta dago ta dubeshi suka hada
ido tayi dan murmushi ta kauda kai, jikinsa ya
kara mutuwa, Sakeena! Ya kirata a sanyaye. Ta
kalleshi a nutse ido cikin ido suke kallon juna
wucewar some seconds kafin yace "nayi rantsuwa
zan iya rasa raina duk ranar da kikace ba kya
sona" ta sunkuyar da kai shiru batace komai ba.
Rayuwa zata yi min wuya muddin ban tare dake.
Don naga misali within these 7days. Ba don
inajin muyraki ba da bansan yanda zan kasance
ba. Idanuwanta suka ciki taf da kwalla ta zura
masa su tace sai ina gani kamar baka yarda
dani ba dokta, meyasa? Kwallarta dake neman
zubowa su yake kallo hankalinsa yayi tashin
gwauron zabi ya kada kai. Yace ba haka nake
nufi ba don girman Allah kar kiji min ciwo a
zucia hawayenki daya na digowa zai zama
tamkar tafasasshiyar dalma cikin raina. Nayi
rantsuwa Sakeena tsananin sonki ke zautar dani
yana sanyani sambatu ba tare dana sani ba. Kiyi
min uzuri bayin kaina bane kuma bazan iya
jurewa ba kin yarda dani? Take ta hadiye
hawayen tace na yarda da kai da duk abnd kakeji
nima ina jinsa. Kaga kuwa abnd yace doma ba
zai bar awai ba. Ya danyi lum da ido ya bude
tace rufe idonki. Ta danyi jim tana kallonsa kafin
ta rufe idon. Gashin girarta baki wulik!
Hakazalika na idanuwanta. Tasbihi Al- Ameen
kewa Allah mafificin halitta wanda ya zana surar
Sakeenar sa kafin yace bani labarin abnd kika
gani. Tayi wug ta bude idon tace ni ban iya wann
imagination din na ka ba. Nan da nan ya
shagwabe fuska gsky ba haka akeyi ba! Ba haka
akeyi ba sakeenan! Dariya sosai ta kubuce mata
ya bita da kallo komai kara mata kyau yake yace
gsky sai kin bani lbr kawai. Ta gyara zama tace
to shikenan, ta rufe ido ya zura mata nasa
idanun menene labarin? Tace wani busasshen
likita zaune bisa kujera kaga gemunsa.......?
Yayi saurin katseta bani bane sake wani! Ta bude
ido tana yar dariya. Pls kabar maganar lbrn nan,
kinsan Allah saikin bani lbr come on close Ur
eyes! Ta dan numfasa ta dafe kirji, Oh ni ya su!
Ta sake rufe ido tayi dan shiru yana kallonta
meye lbrn? Tace duk inda ka duba tsaf yake
cikin gidan haka dakin amaryar yake. Bansan
yanda zan bayyana kyaun ta ba, daga nin wanda
ya shigo ango ne adonsa ya bayyanar da kyaun
surarsa. Gefenta ya zauna ya dauke mayafin
kanta sannan yayi kiran sunan Sakeena! firgigi
ta bude ido kamar an kira sunana? Ya kada kai a
hnkli cigaba da lbrnki ba wanda ya kira ki. Tace
ai nagama. Ya rumtse ido ya dafe goshi Ya
Salam! Kin katsewa angon nan jin dadi gsky ba
haka akeyi ba. Tayi murmushi ta matso gaban
tire ta tsiyaya masa juice din ta bashi Ungo ka
sha zahiri. Ya dan ware ido kina nufin nine
angon? Sosai ma" yasa hannu ya karba yana
fadin amazing watau nine angon? Ya kurbi juice
yaci gaba "Hakika ban taba jin lbr mai dadin na
yau ba" ko? Gsky ina ganin ma shiyasa Mami
tace in kawo miki wadannan kayayyakin. Ya turo
mata jakar ledar katuwar gaske tabita da kallo
tace kai Mami harda dawainiya haka? Yace dan
Mami ya zama ango kinga dole ta kawo kayan
siyen baki koba haka ba? Ta dan rufe fuska ta
bude tace hakane to nagode Allah ya saka da
alhairi. Ya amsa da amin. "Amma kinsan wani
abu? Nifa ban yarda labarnki ya kare ba, sbd
haka ina binki bashi, duk ranar da na nema dole
ki biyani". Tace, "Allah ko?" "ba sai na rantse
ba, wannan dole ne". Ckn zolaya tace, "na'am?".
Yayi 'yar drya yana kallnta. Shi yasa tana dago
ido suka hada, tace, "ka ga yayana?" "naga
yaya, har mun gaisa. Kunyi kama sosai, haka
ma saurn suke?" tace, "haka suke". Yace,
"bambancnku ido, naki kamar na agolan
nufawa!" Fuska kumbure take harararsa. Ya
kylkayle da drya, haushi ya isheta, bata san
lokacn da ta figi filon kujera ta jefa masa ba. Ya
ko cafe filon ya rungume a kirjnsa yace, "ni kika
jefa?". Ta juya idanuwatana ci gaba da
harararsa. Kai! Kamar ya zare yake ji. "ba komai,
nima zan rama" ya fadi yana mata duban kauna.
Sun kwarari hira kamar ba gobe, kawai basu
ankara ba suka ji azahar tayi. Ko wannensu yayi
sallah, ta kawo masa abnci da saurn kayan
tande tande. Shi yasa ta kira masa su ameera
suka ci abncn tare suna ba juna labari. Tabbas
mama ta yarda al'ameen na son yara. Nama har
na hannun ameera ci yake wnda ta tattauna ta
gutsira ta sanya masa a baki, yaran na tare dasu
har karfe 3. Anti rabi tayi sallama falon suka
gaisa da al'ameen, sannan ta kada yaran don
shirin islamiyya. Jimawa kadan suka fito,
ameera sanye da hijabi. Tace, "yaya sai mun
dawo!" yace, "daga ina? Come on kuzo nan".
Suka ruga gunsa. Ya mika musu kunci, "oya kiss
me". Kowannensu ya sumbace shi, shima ya
sumbace su yace, "to a dawo lfy" suka ce, "nty
bye-bye. Tana murmurhi ta daga musu hannu,
ita ma tace, "sai kun dawo". Suka ruga suka bar
falon. A lokaci guda mama da al'ameen suka
kalli juna, suka yi murmushi mai isar da sako
iri-iri. Mama tayi zugum! Tunaninta lallai idan
al'ameen ya zama uban 'ya'ynta, tabbas za su
sami kulawa. Saukar filo taji gum! A jiknta, kai
ba karamin firgitata yayi ba. Ta dubeshi yana
mata drya, "ai na gaya miki zan rama, me kike
tunani?". Ta kara sakan masa harara, sannan ta
dauke kai. Yace, "nasan tunani iri daya muke yi,
ko ba tunanin 'ya'yanmu kike yi ba?". Ta sha
mamaki, ta ynda take kallnsa kawai ya gane ya
canki abnda take tunani.! Ya amsa da amin.
"Amma kinsan wani abu? Nifa ban yarda
labarnki ya kare ba, sbd haka ina binki bashi,
duk ranar da na nema dole ki biyani". Tace,
"Allah ko?" "ba sai na rantse ba, wannan dole
ne". Ckn zolaya tace, "na'am?". Yayi 'yar drya
yana kallnta. Shi yasa tana dago ido suka hada,
tace, "ka ga yayana?" "naga yaya, har mun
gaisa. Kunyi kama sosai, haka ma saurn suke?"
tace, "haka suke". Yace, "bambancnku ido, naki
kamar na agolan nufawa!" Fuska kumbure take
harararsa. Ya kylkayle da drya, haushi ya isheta,
bata san lokacn da ta figi filon kujera ta jefa
masa ba. Ya ko cafe filon ya rungume a kirjnsa
yace, "ni kika jefa?". Ta juya idanuwatana ci
gaba da harararsa. Kai! Kamar ya zare yake ji.
"ba komai, nima zan rama" ya fadi yana mata
duban kauna. Sun kwarari hira kamar ba gobe,
kawai basu ankara ba suka ji azahar tayi. Ko
wannensu yayi sallah, ta kawo masa abnci da
saurn kayan tande tande. Shi yasa ta kira masa
su ameera suka ci abncn tare suna ba juna
labari. Tabbas mama ta yarda al'ameen na son
yara. Nama har na hannun ameera ci yake wnda
ta tattauna ta gutsira ta sanya masa a baki,
yaran na tare dasu har karfe 3. Anti rabi tayi
sallama falon suka gaisa da al'ameen, sannan ta
kada yaran don shirin islamiyya. Jimawa kadan
suka fito, ameera sanye da hijabi. Tace, "yaya
sai mun dawo!" yace, "daga ina? Come on kuzo
nan". Suka ruga gunsa. Ya mika musu kunci,
"oya kiss me". Kowannensu ya sumbace shi,
shima ya sumbace su yace, "to a dawo lfy" suka
ce, "nty bye-bye. Tana murmurhi ta daga musu
hannu, ita ma tace, "sai kun dawo". Suka ruga
suka bar falon. A lokaci guda mama da al'ameen
suka kalli juna, suka yi murmushi mai isar da
sako iri-iri. Mama tayi zugum! Tunaninta lallai
idan al'ameen ya zama uban 'ya'ynta, tabbas za
su sami kulawa. Saukar filo taji gum! A jiknta,
kai ba karamin firgitata yayi ba. Ta dubeshi yana
mata drya, "ai na gaya miki zan rama, me kike
tunani?". Ta kara sakan masa harara, sannan ta
dauke kai. Yace, "nasan tunani iri daya muke yi,
ko ba tunanin 'ya'yanmu kike yi ba?". Ta sha
mamaki, ta ynda take kallnsa kawai ya gane ya
canki abnda take tunani.! Ya kada kai yana dan
murmushi, "haka zaki haifa min su, nima in
sanya sunan dady da mamyna ko?". Ta dauke
kai don ya bata kunya. Yace, "no ba maganar
kunya bace, ai daga ni sai ke ne anan, Allah
shine shaida, shine kuma zai bamu muna zaune,
tnda yasan muna so, muna kuma bukata.
Ubangiji kasa hakan ya tabbata, kice min
amin!". Ta kara kasa da kai, amma ckn randa da
manyan baki tace AMIN.! Yace, "shikenan, ai
nasan kin amsa, mata da irin nasu salon? Wanne
ne al'ameen bai sani ba? Kice in rufe ido in baki
labari". Tace, "bana son ji". "yarnya da kinsha
labari, don sunaynsu kaf! Sai na gaya miki". A
karkace ta kalle shi, bata dai ce komai ba. Zai
kara magana tasa yatsnta 2 ta toshe kunnuwnta.
Ya kece da drya, "baki son ji ko? Ai nima na
fasa fadi, sai ranar tazo, da kaina zan yiwa
idanuwan nan tiyata in cire kunyar". Ta mike
tana 'yar drya, tace, "kaje kayi sallah, lokaci
yayi". Yace, "yes madam!". Al'ameen kenan, tare
da gimbiyarsa ya wuni zungur! Amma ganinta
bai ginshe shi ba. Har abuja yasa ta kira waya
suka gaisa da ya A-kadir da matarsa amina.
Yarnsu daya mai sunan kakansu Isma'il, shi
yasa ma suke kiransa Malami. Hnkaln al'ameen
bai kwnta ba sai da ya amsa gaisuwar karamin
yaya, watau A-rahman, ya gabatar da kansa, ya
tabbatar da kowa na maraba da shi. Sannan ya
kara samun natsuwa. Gab da kiran magriba da
kyar da jibin goshi yayi ta maza, yayi sallama da
kowa ya koma gida. Duk da haka sai da ya sake
kirnta a waya da daddare. Tsoro mama ta rika ji,
irn wannan sabo da al'ameen yayi da ita! Tabbas
zai sha wuya idan ta koma makrnta. Tausaynsa
ya zauna a ranta, don ba shi kadai ba har ita
kanta zata ji jiki, domin kuwa dai al'ameen ya
riga ya zama bargo da jini, kashi da tsoka, jijiya
da fatar da suka hade suka zama SAKEENAH!
BAKIN CIKI 1***7 Washegari ma kamar jiya karfe
goma zuwa bayan sallar azahar. Tayo masa raki
tare da su ameera, haka ya zura mata ido ya
rasa inda zai tsoma tsumman ransa. Gajiya tayi
da tsayuwar ta kada yaran tace, "ku wuce muje".
"sakeena!" ya kirata, ta tsaya cak! Sannan ta
dawo baya ta tsaya saitinsa. Bata kalle shi ba
sai da yace, "pls ki dubeni sakeena" Ta dago su
raurau da kwalla ta kalle shi. Yace, "ki
taimakeni ko fasfot ne na hotnki ki bani na wuce
dashi". Tace, "sai dai in duba maka wajn anti".
"hnzarta don Allah ko na iya tfya". Da sauri ta
wuce ta barshi da yaran. A daki ta sami anti rabi
tace, "ki taimakeni anti, Dr. yaki tfya wai sai na
kawo masa hotona". Tayi dan murmushi, "ai
wannan likita naki sai a hnkali, je ki dauko
album ki duba masa". Ta kwaso manyan album
guda 4 ta darzar masa guda 2, daya nata, daya
suna tare da su ameera. Ta nemo ambulan ckn
takardn yayanta ta saka su ciki, tayi waje. Tana
mika masa ya bude ya zaro su ya duba, yayi
jim! Kafn ya sumbaci hoton, 'yar kunya ta
kamata, ta kauda kai. "Sakeena!". Ta dube shi,
yace, "na gode, kinga na sami abokiyar hira ko?
Ga kuma abokina da babbar kawata". Tayi shiru,
ya sake cewa, "kinyi shiru, are u jelous?" Da
mamaknta tace, "na me?" "zan wuce da madam
dina, kuma a gabnki na fara nuna mata love".
Tayi dan murmushi, "lokaci na wucewa Dr. ban
son dare yayi maka" Ya lumshe ido, ya bude
yace, "zan tafi sakeena, sai munyi waya ko?" ta
amsa da kai. Ya juya kan yaran, "to ameera, sai
wani satin ko?" tace, "zaka kira waya?" "sosai
ma. Ameer sai na kira ko?" suka yi musabaha ya
tafi yana fadin, "to yaya?". Ya shige mota suka
rufe masa, "Safe journey! Allah ya tsaye". Ya
amsa, "amin SAKEENA TA! I love u". Tace, "me
too". Ya yiwa mota key, ta janye yaran gida.
Yayi kwana ya bar harabar gidan, suna yi wa
juna bye-bye! Al'amura sunci gaba irn haka,
kullm son sakeena kara zama yake wani wuri na
musamman ckn zcyar al'ameen, tamkar ynda
mama ke jin rayuwarta ba zata taba tfya daidai
ba, ian bata jin ko da muryar Dr. nata ba. A haka
ta kammala hutnta na sati 3, duk sati yake zuwa
suga juna. Yau shine satin karshe da mama zata
koma gida, daga can sai makrnta. Akwai
alkawarn zata je gaida maminsa kfn ta koma,
sbd haka tana zaune ckn shiri tare da 'ya'ynta
'yan rakiya. Karfe goma na safiya yana kofar
gidan. Babu bata lokaci ya kwashesu ya aje
katafaran gidan mahaifnsa. Suna ckn mota basu
fito ba yake fadin, "saura ki shiga kina min
kauyanci, sai nai miki allura a gaban mamin,
inga tsiya" . Ta watso masa harara, kunyar me
zanji? Muje ckn ka gani". Yace, "kamar da
gaske" "uhm.... Bari ka gani". Ta bude murfn
mota ta fito tana fadin, "ameer ku fito mu je". Ya
fito yana drya, ya budewa su ameera kofa suka
fito, ya kamo hannaynsu ya dubeta, "to muje
ko?". Tace, "muje mana". Yana murmushi yana
fadin, "ha! Ha!! Yarnya yau zanga ynda zaki yi a
gaban surika". Ta yamutsa fuska tace, "kasan
Allah zan koma". "to shikenan!" "wlh baki isa ba,
idan na rika kururuwa ina ihu, duk sai na tara
miki jama'ar unguwar nan". Ta bishi da kallo
yana mata drya, ita kuma tana wani irin
murmushi mai sace zcya. A zahiri ya ganota
kunya take ji, shi yasa take 'yan kame- kame.
Kawai fitowar mami suka gani, "oyoyo sakeenar
mu!". Nan da nan ta daburce, kasa zata shige ko
sama? Da sauri ta durkusa, "sannu mami!" ta
mika hannaynta ta dago ta, "taso, taso muje".
Ta rungumeta jiknta, "yan yarori sannunku da
zuwa". Ta fadi tana kallnsu ameer. "shigo dasu
mana". Ta wuce rike da mama, ya bisu da kallo
kamar ya zubda kwalla sbd murna da farin cikn
da ya lullube shi. Ya sauke numfashi, ya ja
hannunsu ameera ya bi bayansu mami. Har dakn
barci ta shige da mama, ta nuna mata kujera,
"zauna nan!". Ta zauna kai a sunkuye, ya shigo
da yaran, yaynda mami ke fadin, "ki saki jiknki
sakeena, nan gdnku ne, kuma ni bana surukar,
'yata ce ke. Kinji?". Ta kara rufe fuska da mayafi
tana dan murmushi, ta silalo ta kwashi gaisuwa,
mami na amsawa baknta kamar gonar auduga.
Yaran ma suka gaisheta, ta tambayi sunaynsu,
kowannensu ya gaya mata. Kusa da mama
al'ameen ya zauna baknsa har kunne, "mami ya
kika ganmu? Munyi matchn ko?" tace, "ai kana
zama kawai naji na kosa ta shigo gidan nan,
yanda kasan in boyeta". Yace, "kinsan ynda za'a
yi? Mu kulleta a wani daki, muce bamu ganta
ba". Dariyar mama ta karu, ta kara sunke kai
tana jan mayafi. Mami tace, "idan ma muka yi
hakuri dan lokaci kankani ne, Ubangiji dai ya
bamu aron rai da lfya. Kuma Allah yayi muku
albarka, na gode kwarai da gaske sakeena. Duk
mai son tilon dana gaskiya nima bani da kamar
sa. Sbd haka ku rike amanar junanku, kinji
sakeena?". Ta amsa da kai. Yace, "ina su Iya?
Basu san amaryata ta iso bane?" tace, "suna
kicin tun safe suke shirya mata abncin tarba".
Ya mike, "bari in kirasu, ai ko ladi bata zo ba ya
kamata Iya tazo taga amaryar dan Iya.!" tace,
"maza jeka". Ya fice. Mami na masa drya,
wannan amarya ana ji da ita. 'Yar dattijuwar na
zaune tana yankar ganyen latas, ya fado yana
kira, "ina Iya ta ne?" tace, "gani nan dan Iya". Ya
tsugunna baynta ya yada kansa a kafadar ta, a
shagwabe yake magana, "baki san amaryar dan
Iya ta iso bane?". Ta kara fadada fara'arta, ta
aje wuka, "ina na sani? Ynzu tana nan ciki?"
"tana dakin mami, taso muje. Iya yau mu 2 zaki
goya". Tace, "ya zama dole". Ta yunkura ta tashi
tana kiran Ladi, "maza kizo amarya ta iso!". Tayi
gaba ya biyota suka shigo dakin, yayi azama ya
koma kusa da mama. "ya kika ganmu?". Ta
rangada guda, daidai ladi na kawo kai, "lallai iya
harda guda?". Tace, "abnda yafi guda ma zanyi
ladi, wannan amarya zubin larabawa? Gskya dan
iya kayi sabe, Allah ya tabbatar da alkhairi".
Gaba daya suka amsa, amin. Shi kuwa ji yake
tamkar yau yake angwanci, bai san lokacin da ya
kai hannu ya rungumo kafadarta ba yace, "Iya
kenan, mai raino na". Da sauri ta zame ta sulale
kasa ta makure. Mami tace, "hayaniyar ta isa
haka, aje a kawo musu abin sha" Kafn kace
kwabo tsakar dakin mami ya cika da kayn lashe-
lashe da jus kala-kala. Al'ameen ya zuzzuba
musu, ya mikawa yaran. Sannan ya juya kan
gimbiyar ya miko mata, taki karba. "nifa ban son
kauynci, kinsan Allah zan miki dure!". Mami
tace, "wai tsaya, bakuwarka ce ko tawa?" yace,
"taki ce maminmu". Tace, "to tashi ka bamu
wuri. Don me zaka dameta? Duk ka kanainaye
min ita, maza tashi ka tafi harkoknka". Ya
marairaice, "baki tausayina mami? Daga yau fa
bazan sake ganinta ba sai karshn watan da zamu
shiga, sannan ba waya ba komai? Pls mami ki
barni in zauna". Ta tafa hannu, "ya Rasulu, ni
indo! To bari in tashi, watakila ni take jin
kunya". Ta yunkura zata tashi, "don Allah kar ki
daka ta tashi, ki dauki komai ki ci, ki sha lemu
kinji? Sai kinci kin koshi a gidan nan zan
tabbatar kina son dan Aminu na". Ta fice,
al'ameen din yana drya. Ya kara matsowa, "kinji
abnda tace ko? Nima yau zan gani, kina sona ko
a'a". Ya jawo tiran soyayyen naman kaji, meat
pie, donat, lafiyayyen cincin da samosa, yace,
"to Bismillah, iya cinki iya son da kike min". Ta
dubeshi tace, "wannan wayau ne, a wane ckn zan
zura tulin kayan nan?" yace, "oho! Ni dai na kare
magana, kuma kina jin abnda mami tace". Tayi
shiru tana kalln tire, kafn ta dubeshi, "don Allah
ka tayani ci". Yayi 'yar drya, ya dauki samosa ya
kakkara wa yaran. Ya sake daukar daya ya kai
baknsa, "mu tayaki, kema fara ci". Duk kunya ta
isheta, da kyar tasa hannu ta dauki meat pie, ta
juya gefe ta gutsira. Ya zura mata ido jim!
Sannan ya dauki kofin lemun ya miko mata, "sha
in kara ganin ynda kike so na". Ta karba ta dan
kurba. Ya jawo ameera jiknsa ya rungume,
"kinga ynda antinki ke so na?". Oho! Ina ruwan
ameera, me ma ta sani banda drya, tana amsawa
da kai. Sai ga ladi dauke da wani tiren ta aje
wani dan matsaikaicn kek da duminsa. Yace, "a
gaida ladi". Tace, "likita irin wannan zaman da
kake yi kyanshi a buga muku hoto". Yace, "ko
ladi?" "gaskiya". Ya fice suna masa drya, jimawa
kadan ya dawo da 'yar karamar kyamara a
hannunsa. "ai kema zaki iya daukar mu ladi, ba
wuya. Duba nan ki gani, saman nan kawai zaki
latsa". Yana saitawa ya fara bada misali, sai dai
kawai mama taji wal! Haske ya wuce. "ai kin
gane ko ladi?" "na gane likita". Ya mika mata.
Mama kuwa sai kalln ikn Allah take yi, ya dawo
gefnta ya zauna, ya taro su ameera, ladi tayi ta
yi musu hotuna. Wasu tare da yaran, wasu su
kadai. Ladin ya tura ta kira mami, itama ta
zauna suka yi hotunan tare, fadi take, "wannan
shagali yayi kyau". Mama kuma bata sake ba sai
da al'ameen ya tafi sallah. Sunci sun sha, sun
bar gara birjik! Kamar ma basu taba ba. Kafn ya
dawo ta gama shirin tafya. Ga ledoji tuli,
kayayyakin da mami ta bata. "ban gane ba?" Ya
tambaya, har da kama kugu hannu 2. Tace, "gida
mana". Ya langabe kai, "gaskya ba haka ake yi
ba, ba haka ake yi ba sakeena. Ai dai sai la'asar
ya kamata ko?'. Tuni take ta drya zancnsa, kafn
tace, 'ka manta yaya na jirana ne?'. Ya runtse
ido tamau! "oh my God!". Ya bude ya kara
matsota, ya zura mata ido, "kamar ki ta zama a
gidn nan sakeena, bana so ki tafi". Ta sauke
numfashi, "kayi hakuri". Yace, "yaya zanyi
sakeena? Ya zama dole, amma ki bari zuwa
karfe 3 sai mu tafi" "Allah yaya zai yi fada, kana
so ya bata min rai ne?" ya kada kai, "bana son
kowa ya bata miki rai sakeena, kin gama
shiryawa?". Ta amsa, "na gama. Ka ga kayan da
mami ta ba ni? Sunyi yawa Dr, kace ta rage".
Yace, "me yasa ke baki ce ta rage ba?" "kunya
nake ji" "oh, nine mara kunya kenan?". Tayi dan
murmushi, "ba haka nake nufi ba yallabai". "to ai
mami tasan kinfi karfn wadannan tarkacen ne,
shi yasa ta baki su. Gaba daya shopping din
makarnta ne. Bari in zuba miki a mota ko?".
Tace, "na gode!". Sai ga mami ta shigo. "mami
barin in maidata gida, yaynta na jiranta zasu
wuce". Tace, "yana da kyau! Sakeena na gode, a
gaida min mutan gidan. Insha Allahu duk ranar
da na shigo fandagorin zanje mu gaisa da
umman taki". Tace to. Ya kwashe kaya ledoji
hudu, mami ta riko hannayen yaran suka fito,
tayi sallama da su iya. Har mota mami ta raka
su, tana tsaye suka fice. Suna tafe a mota suna
hirar Mami, zcyar mama gwanin dadi, surikarta
na sonta, kuma ta nuna mata kauna. Yayanta na
waje yana ta faman duban agogo. Al'ameen yayi
fakin suka fito. Yaran suka ruga gunsa, take nan
suka fara bashi labarin ina da ina suka je, kamar
shi ma bai sani ba. Bayan sun gaisa. Yace mama
tayi sauri ta fito da kaynta, don shi a shirye
yake, ita kadai yake jira. Ta shiga ciki da sauri
dauke da kayan da ta samo, sbd tana so ta nuna
wa anti Rabi, kuma ta dibarwa su ameer wani
abu. Haka kuwa aka yi, anti rabi na ta sa
albarka, ita kanta ta samu mayuka masu tsadar
gaske, da turare guda 2. Mama da yara suka fhto
da kaya suka zuba. Hankalnsa a tashe yake.
Ganin suna satar kalln juna, shi yasa yaya yace,
"ina zuwa". Ya shiga daga ciki don ya basu guri
suyi sallama. Ya zura mata ido yace, "sai nazo
visting, Ok?"tace, "shikenan, ina saurarnka".
"zanzo miki da pictures din da muka dauka ki
gani". "to". Suka yi shiru sai kalln-kalln suke yi.
Idanuwnsa tam da kwalla yace, "gskiya gobe ba
don da wuri zaku wuce ba, zuwa zanyi. Ban
ganki ba, banji muryarki ba. Anya kuwa zan
jure?". Haka nan nata idanuwn suka yi ja, ta
bishi da kallo, amma ta kasa cewa wani abu.
Motsin fitowar yayanta yasa tayi firgigi, ta wuce
da sauri ta bude mota ta fada. Muryar anti rabi
taji bisa kanta tana fadin, "to matar likita a
sauka lfya, ace ina gaida umma da kyau da
kyau". Tace, "zata ji". Ameera kuwa kuka take yi
zata bi ta. Hnkaln mama ya kara tashi, tace,
"yaya mu tafi dasu mana" yace, "islamiyya ce
bana son suyi missing, kyale su kawai sai wani
lokaci". Ya ja murfin mota ya rufe, yayi mata
key. Al'ameen ne ya dauke ta, "yi hakuri kawata,
anjima kadan muma zamu bi su". Bata yi shiru
ba, amma ta rage sautin kukan. Suna kalln
motar ta bar harabar gidan, ameera kuwa ta
kara wage baki. Al'ameen ya jefata a kafadarsa
ya rungune, kirjnsa shima sai bugawa yake. Shi
kansa yana bukatar rarrashin, shi yasa yayi
tsaye jiki ba kwari. Tsawn lokaci sannan ya
dagota ya share mata hawaye. "Manta da anti,
ba ma yi da ita, tnda ta tafi ta barmu. Yi shiru,
yi shiru. To jeki wajen momi, sai na dawo ko?".
Tace, "yaushe zaka dawo?" "duk lokacn da nazo
garin nan zanzo insha Allahu". Ya ajeta gaban
mominsu, yace, "anti zan wuce, sai wani lokaci".
Tace, "to mun gode kwarai da gaske. A gaida
mutan gidan". "zasu ji". Ya wuce yana dagawa
yaran hannu. har suka iso fandogari mama bata
cikin sukuni ranta bace yake kwarai. Ganin
Ummanta yasa ta saki jikinta. Kowane sassa
umma ta turata, tace taje ta gaishesu kuma ta
gaya mata an sulhunta. Gab da sallar magrib
uban dwk ya dawo daga Kd gaba 1 siyayyar skul
yai mata bayan isha' suka taru a falo suna cin
abnc. Umma ta baje masa kayan data sami a
gidansu al-ameen yasa abarka,sann yace ta aje
su tukunna. Umma tace a'a Alh naga akwai
abubuwan ci wadanda zasu iya lalacewa, yace
banason amsar kayayyakin nan amma bakomai
ki bata wadanda kike ganin zasu iya lalacewa
kibar sauran. Tayi murmushi Alh ho!
Abdulkareem yace danAllah kubar mata kayanta
tayi amfani dasu. Menene? Aiba fata akeyi ba
kuma sani kanka ne Abba babu abnd zai gagara
koda an sami akasi karka da mu Abba. Nasan
surutai sunyi yawa akan mama cikin gidannan
haka bazai hana ta amsar kyauta daga
masoyinta ba. Yace Allah ya shige mana gaba
suka amsa da amin. Yayan yaci gaba da fadin
gsky yaron nan yana son mama kullum waya sau
2 sau 3 wkend kuwa idan yazo tun safe sai
yamma. Umma tace ai ta kare kuma tunda ba a
waya a makaranta Abba yace baki tausayinsu
kenan? Tace ina ruwana? Suka fara dariya mama
ta hada rai. Abba yace ni inaji kyaleta kinji yar
Abba? Ta kara matsawa gunsa ta lafe. Yaya yai
yar dariya yace abin harda shagwaba? Ido kamar
an matse kwado ba inji Umma. Duk suka fashe
da dariya ita kuwa kukan shagwaba takeyi.
Washe gari da sassafe karfe 8am tare da yayanta
suka iso gidansu baraka sbd shima yanason ya
gaida innarsu. Ta kuwa ji dadin zuwansa ita da
megidanta su kuwa kawayen suna can kebe lbr
ya tsunke kamar kurna na zuba. Ita dai baraka
wangame baki kawai tayi tana mamakin wann
kasaitacciyar soyayya data kullu cikin kankanin
lokaci. Tabbas ta shaida domin itama na tattalin
kayan skul da mama ta kawo mata sun ishe ta
tafiya skul. Jaka inna tasa albarka banda
alhairin da AK yai mata da megidan. Kafin ya
gama sallama dasu inna mama da baraka sun
sulale sun tafi gidan goggo wato kakar alameen.
Harda manya goro guda 10 suka satowa inna
cikin wanda take siyarwa Goggo ta nuna nata
murnar taga kishiya suka bata goro ta amsa ta
jujjuyashi tace na toshiyar bakine wann? Lallai
kinsa in bar miki mijin. To naki wayon kenan?
Suna ta dariya suka fito ta rakosu har zaure tana
sa musu albarka. Suna fitowa suka hangi yaya
tsaye yana jira suka karasa da sauri, yi hakuri
yaya. Ina kukaje masu yawon tsiya? Baraka tace
mun danje wajen wata kawarmu ce. Yace I see..
Daga zaure inna ke fadin kaji karya ko? Ni
nasan gidan goggo Hausi sukaje kakar alameen.
Ya kama baki yace Allah ya shiryeku. Inna sai
wani lokaci. Ya bude mota ya shiga inna na
fadin Allah ya tsare agaida Rabi da yara. Mama
da baraka suka rungume juna sannan ta shiga
mota tana yiwa inna sallama yaja suka wuce.
BAKIN CIKI 1***8 Suna isowa gida, me mama
zata gani? Motar al'ameen aje gefe guda. Gabnta
ya yanke ya fadi, haka ma yayanta ke mamaki,
"wannan ba motar al'ameen bace?" "ita ce yaya".
"mama biyoki yayi?". Tayi shiru tana 'yar drya.
Yana fakin yabe fadin, "kai wannan mutum yana
damun kansa da yawa. Pls ki gaya masa ya rage
sonkh, kaq ya zame masa illa". Ta sauke ido
kasa tana murmushi, tana kuma murzar zobensa
da ke yatsanta". Yace, "je ki mana, tnda ba zaki
iya gaya masa ba". Tace, "yaya kenan". Ta fito
yaynda yayan ke fadin, "nayi laifi ko?". Ta kada
kai, "a'a wlh". Ba shi ckn motar, sbd haka ta
tabbatar yana falo. Don haka ta wuce ckn gida.
Ido waje tana magana, "umma sai naga motar
al'ameen a waje?" tace, "nima haka abbankuya
gaya min. Yana can falo tare da alhajin"". Ta
nemi waje ta zauna har da tagumi. "au zama
kuma zaki yi?" "ummi kince suna tare da abba,
sai kuma imje?" tace, "to zauna. Amma kinsan
dama ku yake jira ku dawo ya maida ki makrnta
ko?". Tayi shiru. "saura kije ki shantake da
surutu. Sannan ki gaya masa don Allah ya rage
sonki, zai iya zame masa damuwa". Tuni take
kallon umma ido waje, har ta wuce ta bata wuri.
Ta zabga tagumi hannu biyu zugum! Tunaninta
yaya zata yi ta dumfari al'ameen da wannan
maganar? Tabbas ita kanta tasan al'ameen ya
makance a sonta, da zai rage din da zata so
hakan, don bata son duk wani abnda zai raunana
mata shi. "Mama!" taji an kwala mata kira, ta
dawo daga duniyar tunani firgigi, ta dubesu tsaye
bisa kanta. Abba yace, "tunanin me kike yi?"
tace, "ba komai abba". "to yana falo, kiyi sauri
ki ganshi muce. Wai rokona yake in barshi ya
kaiki, tnda duk hanyar daya ce. Nace masa a'a,
ya barshi yaje gun aiknsa". Jiknta ya kara
mutuwa, ta juya salalau-salalau. Yayanta na
fadin, "ni dai nace ta gaya masa ya rage sonta.
Dis is 2 much!". Abba yace, "duk wannan ma bai
taso ba, amma a ganshi tare da ita a mota, ai
zan shiga bakin duniya, kuma daga ckn gdn nan
maganar zata fara. Ba ni a ckn wannan tsarin,
ba wai kuma don ban yarda dashi bane. Je kayi
wanka kayi shirn komawa". Ya wuce, shi kuma
ya wuce sashn da ya kwana don yin wanka.
Kwalla ta tsaya take sharewa a kofar falon,
zallar tausayn al'ameen ne ya tilasta mata zubar
su. So ba zai taba zama laifi ba, amma ya
kamata al'ameen ya rika bi a hnkali, kar son da
yake nuna mata ya zama laifi a wajn iyaynta.
Sai da ta natsu sosai ckn ranta, sannan ta tura
kofar ta shi shiga tare da sallama. Ya amsa yana
kallnta, ta wuce ta zauna rai bace. Da sauri ya
matso gunta ya tsuguna, "da inga irhn wannan
fuskar taki gara na kwanta gadn asibiti sakeena.
Gaya min waye ya taba min rayuwa ta?". Gaba
daya tsigar jiknta sun tashi, ta dan numfasa
tace, "kai da kanka ka tabani Dr." "ni? Me nayi?"
"nasan kana sona Dr, ni kaina zan iya dafa
Kur'ani in rantse. Wlh yadda kake ji haka nima
nake ji. Bana son kana tsananta damuwa ckn son
da kake min, domin ina jin tsorn kar wani abu ya
illata min kai. Ganinka da nayi yau ya fadar min
da gaba ba kadan ba. Wnda ya tabbatar min
cewa zaiyi wuya jiya in kayi barcin kirki, sbd ba
muyi waya ba. Me yasa? Kar ka mance makrnta
zan koma, inda ba waya, sai fa in kazo visiting.
Kana nufin ba zaka yi sukuni ba tsawn wannan
lokacin? Rashn sukuni ba shi zai tara maka
damuwa ba? Kai fa likita ne. Ka gaya min me
yawan sa damuwa a rai yake haifarwa?" Yayi
zuru yana kalln ynda idanuwnta suka kawo
kwalla. Ta kara fadin, "tmbayarka nake, ka gaya
min?". Ckn sanyin murya yace, "abubuwa masu
dama da kan iya nakasa lafyar mutum. Amma
kar kiga laifina sakeena, sonki nake yi". Kwalla
suka malalo bisa kuncnta, lebe na rawa tace,
"yayi yawa Dr.! Ka rage don Allah, bana son na
rasa lfyrka". Tasa hannaynta da sauri ta rufe
fuska, ta ja numfashi mai sarke da kuka mai
tsuma rai. Wani kululu ya tokare masa wuya,
kansa ya dau zafi, zcyrsa na zugi tare da tashn
hnkali. Da kyar ya kalato miya a baknsa, ya iya
fadin, "SA... SAKEENA!". Ta dago ido jajur! ta
dubeshi. Ya mika mata hankicif, "don girman
Allah ki gnge hawayn nan Sakeena. Kin kuwa san
ciwon da kika dasa min yazu? Komai zai iya
faruwa dani, muddin hawaynki ya ci gaba da
zuba". Tasa hannu ta karba ta goge kwallan ta
numfasa ta dubeshi a hnkl alkawarin da mukayi
wa juna Allah zai tabbtr mana dashi nima ina
sonka Dr. Ya koma dirshan ya zauna farin ciki
ya mamaye zuciyarsa yace duk jawabin ki na
yarda dasu sakeena. Kuma zan kiyaye
shawarwarin da kika bani, tare da yin adduar
Allah ya sanyaya min zuciyata duk lokacin da
ciwon son ganinki ya kamani, rokona gareki
shine ki taimakeni ki daina zubda hawayen ki ko
alama banason ganinsu. Tace daga yau bazan
sake ba, muddin ina ganin ka cikin nutsuwa.
Yayi dan murmushi an gama my princess. Tace
to yanzu ka tashi in rakaka ka kama hanya ka
isa wajen aiki da wuri. Yace a'a kar muyi haka
dake kije ki shirya ku fito kina gaba a motar
Abba ni kuma ina take miki baya. Kash! Saidai
babu jiniya dana makala kowa yaji ya kauce
hanya gimbiyata zata koma skul. Ko ba haka
ba? Ta dan shagwabe gsky ba haka akeyi ba, ba
haka akeyi ba Dr! Aidai zaka sa Abba yayi min
fada. Ya zura mata idanu yana dariya to
shikenan bari inyi gaba tunda kin amince min.....
Ka zama prince ba ta tari numfashinsa. Ya kara
rausaya kai ah! Lallai ngd. Ya mike to muje ki
rakani. Ta tashi suka jero na shiga na gaida
goggo. Ah haba yaushe? Dazu da mukaje gidan
Inna ta da yaya. Amma kin kyauta naji dadi
nima idan nabar nan zan shiga in kai mata cfane
karfa kiyi kishi. Tayi yar dariya aini bana kishi
da goggo, sbd me? Ya tambayeta yana kallonta
ido cikin ido ta bashi amsa sbd aronka na bata!
Ya fashe da dariya zan kuwa gaya mata idan ta
zauneki ba ruwana. Sukaci gaba da dariya har
gaban mota ya bude ya shiga ta rufe nasa "take
care" Allah ya tsare. Ameen kikace arona kika ba
goggo ko? Ta tura masa hula gaban goshi ta
ruga cikin gida yabita da kallo duk kasala ta
rufeshi. Ya sauke wawan numfashi ya gyara
zaman hular yana kada kai fuskarsa dauke da
murmushin kauna. Yayiwa motar key yayi ribas
zai wuce kamar walkiya ta bullo ta daga masa
hannu da sauri ya dago nasa fara'arsa ta karu.
Hanklinsa ya kwanta yaga abar sonsa. Bayan ya
gama da goggo da kanta ta kaishi ya gaida inna
daga nan ya tambayi baraka don ya sha jin
lbrnta a bakin mama. Ta fito suka gaisa babu
wanda baiyiwa hasafi ba musamman baraka da
yake ganin zuwa wajenta shine silar haduwarsa
da mama yarinyar da yakeji tamkar itace ransa.
yana fitowa ya shige mota ya doshi babban titi
yana kawo kai motar Uban dwk na hayewa
kwalta. Abba bai sahida shi ba Amma ita mama
tuni suka hada ido sukaiwa juna murmushin
mmki nan da nan ya takewa motarsu baya wann
sa'a da yawa take (dan anace saida ya bitan
kuwa). Cikin kuzari yake tukinsa suna tafe yana
biye dasu a hnkl har zariya daidai shataletalen
kofar doka take cewa Abba ko kasan Al-ameen
na binmu a baya? Ya dan dubeta kadan ya juya
bansani ba ina yake? Tace gashi can bayanmu ai
tun daga fandogari tare muke. Yace oho! Nidai
ina ganin mota tana bina a baya- baya ban
ganeshi ba. Kofar get din asibitin (A.B.U.T.H
ZARIA) daura da kamfanin maizar nan sukayi
fakin kowa ya fito. Ashe kai ke bina a baya? Ya
dan sunkuyar da kai yace ai ina fitowa gidan
kakata na ganku. Yace yayi kyau to bari mu
wuce aikai ka iso gida ya amsa eh yana satar
kalllon mama. To shikenan mama mu wuce . Ya
koma cikin mota itama ta shige yayi azama ya
rufe yana fadin a sauka lfy Abba. Ya amsa amin.
Idanusa na kan mama sukaja suka tafi. Alameen
ya kama aiki kamr yanda mma ta maida kai ga
karatunta amma zukatan suna cike da tunanin
junansu. 43 days cif da komawarsu kasancewar
sun koma a tsakiyar mnth shiyasa ba ai musu
visiting ba sai nxt mnth ending. Kai sun sha
wuya musamman dr da yake ganin kamr 43yrs
sukayi ya kosa sosai yazo domin lahadin ce yake
rawar jikin zuwa yaganta. Isowarsa kenan da safe
ogansu na sashin Doctors ya kirashi ya mika
masa takarda tare da cewa zai representing
dinsa a taron fida na arewa wanda za*ayi a
bauchi. Nan take hnklinsa ya fita daga jikinsa a
kasalance ya dawo office dinsa ya cilla paper din
on table ya dora hannu aka kamar ya kurma ihu
sai innalillahi kawai yake furtawa! Wayyo Allah
na shiga 3! Tamkar ya mutu. Jiyayi anyi
knocking table dinsa ya dago ido jajur! Ya dubi
mutumin dake tsaye yaya dai? Yayi guntun tsaki
yace dr lawan yaushe ka shigo? Yace jst nw
menene? Yace noting kawai banson zuwa
bauchin nan ne gsky ina da abinyi wkend dinnan
kuma idan ta raya min zanki zuwa saidai mu
kwashi yan kallo da prof! Tofah. Ya ware ido
sosai yace kai lallai kana neman barin kujerarka!
To don me? Yace ba damuwata bace..... Ya
katseshi look Alameen ban taba jin haka a
bakinka bana tabbata uzurinka me karfine amma
karka bata 10 1 bata gyaru ba. Kayi hakuri
kawai! Kai tsaye yace bazan iya ba! I want to see
her! Raina namin ciwo sosai konaje seminar nan
oga bazai sami bayanin da yake bukata ba. Ya
bude baki yace mutumina kace U re in luff
kawai! To menene prob din? Nxt wk basai kaje
ba. Yace bazai yiwu ba boarding skul take
sunday za'ai musu visiting day idan ya wuce sai
nxt mnth, mundade bamuga juna ba. Cool dwn dr
naga ka harzuko dayawa amma shawarata kawai
kayi hakuri. Itama bazata so taji ka sami prob
da aikinka sbd ita ba, I believe she wl understand
ur excuse duk ranar daka gaya mata.n Yaysi
shiru yana nazarinmaganganun hakika yace wani
abu daya tuna irin nasihar da sakeena take masa
akan ya daina matsantawa akansa akan
soyayyarsu somin sun amince da juna. Ya
numfasa yace na hakura dr lawal, sky da hnklina
yayi mugun tashi ina bukatar ganita dr. Aikai
kana da mata kasan sirrin abun. Yayi yar dariya
ya buga kafadarsa mutumina ka tashi daga dr ka
koma mr lover-lover tunda dai ka amince bari na
koma office. Yaushe zaka tafi? Idan mun tashi
I.S.A. To a dawo lfy ya amsa ameen. Ya wuce
yana me lover-lover! Yayi dan tsaki yace kp
quite my frnd! Yayi dariya ya fice. Ranar lahadi
cikin skul kowacce kagani tana cike da farin ciki
sbd yau zasu ga mutanen gida wuri ya rincabe da
baki kala kala sun zauna ana hira da ciye ciye
kusan mama ce kadai ke kaiwa da komowa tana
bilayin neman ta inda dr zai bullo. Wanda dalilin
zuwansa ne yasa ba wanda yazo mata daga
gida. Amma har la'asar ta bada baya ba lbrnsa.
Tun tana fitowa har tay zamanta cikin hostel.
Tunaninta meya hana shi zuwa? Babu amsar data
fara zuwa ma ranta sai wata gagarumar matsala
ce ta rashin lfy. Anya kuwa rashin lfy zata iya
hanashi zuwa yau? Kai babu makawa yana
kwance ranga ranga baisan hakin da yake ciki ba
nan take hawaye suka tsnike mata harda na zuci
kanta yayi dum! Har cikin idonta takejin ciwon
har dare tana kudundune a gado duk iya
rarrashin da frnds dinta sukayi a banza. Bata iya
cin komi ba sai jiri ke dibarta idan ta tashi
sallah ba bacci jikin yaci gaba da dumamewa
kafin safiya ta kwana a skul clinic. Wasa wasa
fa mama jiki yaki dadi. Kwananta 2 a asibitn
makarnta, amma abu kullm kara gaba yake.
Zazzabi, ga rashn cin abnci. Ko an matsa mata
amayar dashi take yi, duk ta galabaita ta fita
hayyacnta. Ganin haka yasa shugabar makrnta ta
tura babban asibtin koyarwa dake zariya don ta
sami kulawa sosai. Nan take aka bata gado,
metiro din hostel ke jinyarta. A wannan ranar
biyar na yamma Dr. Al'ameen da Dr. Lawal suka
hadu a ma'ajiyar motoci, kowanne yayi fakin ya
fito, "Ah! Mr. Lover!". Fuska ba walwala yace,
"Don Allah ka daina, kar ka ynka min sabn
suna". Ya matso yana masa drya. Suka tafa, "to
ya aka yi? U look very weak, me ke faruwa ne?"
"menene ma bai faru ba? In gaya maka tnda na
dawo Bauci bani da lfya, kawai bankadar
magunguna nake yi kar in kwnta warwas!". Ya
nuna shi yana masa drya, "bebinka ko? Come on
kar ka damu, zaka ganta da zarar wata ya kare.
Zaka rnd ne?" "no, kawai na fito ne sbd bana
son kwnciya a gida, tunani ke damuna" "ok, to
zo ka raki ni female ward in duba wata yarnya da
na kwntar dazu da safe. Na barta uncncios, ban
sani ba ko ynzu ta fara gane mutane". Yace, "ba
matsala, muje". Suka wuce yana fadin, "ai naji
oga yana ta fada, wai report din nan kamar ba
kai ka rubuta shi ba". Yace, "kyale dan rainin
wayau, nima ina jinsa tn jiya ya fara conplain.
"Dr. Lafai ka kuwa zauna wajn seminar nan? Naji
kana kame-kame ne?". A raina nace, "ai sai
kayi, wa yace kaki zuwa da kanka? Ai kadan ma
ka gani ckn aikn magudi". Dr. Lawal ya kama
drya, "bansn ka da haka ba mutumina, gskya
wannan baby ana ji da ita" "sosai ma". Suka
fada dakin ckn natsuwa. Kai tsaye wajn gadn
sabuwai mai jinyarsa ya dosa, al'ameen na biye
dashi. Tana kwnce rabin jiknta na rufe, gaba
daya ta rame, fuskarta ta tsuke kwarai. Alameen
bai gasgata idonsa ba shiyasa ya runtse ya sake
budewa yayin da dr lawal ke tambayar mai
jinyarta yaya dai mama? Ta kuwa tashi? Tace
har yanzu dr amma da aka yi mata allurar dazu
ta motsa. Dokta lawal bai kara fadin komi ba
sbd mamakin yadda Alameen ke zare ido yana
takawa a hnkl bakinsa na ambatar Sakeena! Jnkl
tashe ya kalli dr lawal yaushe aka kawota? Yace
dazu da safe kasanta ne? Sakeena ce. Yace yes
sunanta kenan. To ai itace nake baka lbr. Baki
sake yace kai danAllah? Ya dubi mama kamar
yayi kuka meya faru da ita mama? Tace
kawayenta dai sunce tun ranar lahadi wai ko
babu wanda yazo wajenta visiting shine take ta
kuka taki cin abnci har abin ya zame mata ciwo.
Ina ganin ma principal ta aika aka gayawa
iyayenta don suzo suga halin da take ciki. Tuni
ya nemi kujera ya zauna yana fadin
Innalillahi......! Kaga irnta ko dr lawal? Yace be a
man karka manta acikin ward muke ido jajur
yake dubansa dame-dame ka shirya mata? Yace
karka damu duk abnd ya dace na riga na bata
duba folder din kagani. Ya karba hannunsa na
rawa ya karanta abnd ke rubuce dole tasa ya
gamsu da abubuwan da dr lawal ya shirya mata
don yasan abnd yake. Amma da son samu ne a
bata maganin da zata warke yanzu yanzun nan
shi yake so. Ya mika masa folder yace is this ur
only plan? Yace zomuje daga waje... Hodijan! To
nima zanyi daga wajen office sai kuma naje gida
In Shaa Allah! Al'ameen yace, "no! I cnt go any
where. Dr. Lawal je ka gama aiknka ka koma
gida". Maman mkrnta bata gane ba, don haka ta
tambaya, "haka dai kasn sakeena ne?" Dr. Lawal
ya bata amsa, "shine wnda zata aura, kuma
likitnmu ne a nan asibitn". Da mamaknta tace,
"ba shakka! Lallai baiga ta tfya ba, sai yaga
mata ta mike. To Allah ya taimake mu, ya kawo
sauki da gaggawa". Suka amsa da amin. Ya kai
hannunsa ya dafa saman goshnta, ya zuqa mata
ido, ckn zcyrsa kuwa tambaya yake, "why? Why
Sakeena?". Ya kada kai yayi dan tsaki ya sauke
numfashi mai dauke da hucin zafi. Anan Dr.
Lawal ya bar shi, haka maman makrnta ta bashi
wuri, ta fito ta baza tabarma tayi kwnciyarta
tana hutawa. Ya maida kallnsa bisa ledar ruwan
da ake kara mata, kamar yasa hannu ya kara
gudnsa ko zaisa sakeenarsa ta mike. Ya rike kai
hannu 2-2, zufa yaci gaba da kwarara ckn
jiknsa. Ya dago kai a hnkali ya ci gaba da
kallnta, yana hadiye hawayn idanuwnsa. Ji yayi
an dafa shi, muryar Dr. Lawal ke magana, "an
kira sallah Dr." ya dube shi gwanin tausayi yace,
"har ynzu fa bata farfado ba". Dr. Lawal yace,
"come on al'ameen, ka barwa Allah komai mana.
Taso muje muyi sallah mu dawo" ya mike yana
ajiyar zcya, suka fice yana waignta. Cikn sujada
ya dade yana addu'ar neman agaji wajn Allah.
Tare da Dr. Lwl suka sake dawowa. Tun daga
shigowarsu suka hngo maman mkrnta dafe da
hannun da ake kara mata ruwa, kamar baknta
motsi yake? Al'ameen ya kwaso sauri iya dire
gabnta. Dr. Lwl na biye da shi, fadi yake,
"matsa! Matsa mama." maman makrnta ta kauce
da sauri. Ya zauna ya kamo hannun sakeena,
yana kira. Ita kuwa sai zare ido take tana dube-
dube. Bata gane inda take ba. "yaya dai?" Dr.
Lwl ya tambaya. "she is back!" ya bashi amsa,
jiknsa na rawa. Gaba daya suka dauke hnkaln
masu jinyar dakin zuwa gare su. Kowa sai kallo
yake yana Wa kansa tambayoyi. Alameen kuwa
kira yake sakeena! Sakeena! Ta zura masa ido
sannu a hnkli brain dinta ta ta dawo aiki
idanuwanta suka fara washewa face din da
takeson gani ta bayyana a idonta shiyasa ta rage
kallon da take masa yace nine sakena! Kiyi
magana naji hawaye suka tsinke mata shar!
Shar! Ya zaro hankici ya shige share mata. No
pls karkiyi kuka my Queen! Dr lawal ya yafito
maman skul da hannu ya juya suka fice ita kuwa
sakena kallonsa takeyi har yanzu bata gasganta
abnd take gani ba. Nace ki daina kuka nine
Alameen dinki. Kwallar basu daina sauka ba tace
a ina nake? Ya hadiye hawayen da suka cika
masa ido yace asibiti ne sakena me yasa zaki
kwanta ciwo? Tace dama lfyrka kalau ka kasa
cika min alkawari? Ba haka bane sakena ogana
ne ya turani seminar bauchi ba yadda zanyi ne
kinsan yanayin aikin kuma dole nayiwa
shugabana biyayya. Ta runtse ido ta matse
hawaye sannan ta bude tana kalllon sama tace
Allah nagode maka daka sa tunani na ba gsky
bane. Ta maido kallonta gareshi taci gaba, gaba
1 tunanina ya tsayane ga rashin lfy ce kadai zata
iya hanaka zuwa guna na yarda na amince da
hakan kuma zuciata tana kara tabbatr min
kwance kake magashiyan. Bansan ciwon nan ya
kamani ba dr amma nasan yawan tunanina da
tsananin da zuciata ta shiga.jikinsa ya kara
mutuwa tausayinta ya kara lullubeshi ki yafe min
sakena ISA bazan sake ba ni kaina naji ajikina
na tsananin rashinki, tace ba laifinka bane Allah
na yarda daka kai farin ciki nakeyi da Allah ya
nuna min kai cikin koshin lfy. Yadan numfasa
yace ngd sakenata zaki sami sauki a hnkl dr
lawal ya shirya miki magaunguna masu kyau da
zasu taimaka ki samu sauki kuma ga Alameen
dinki a kusa dake.
Go to Home
BAKIN CIKI 1***9 Ta dauke kai tana murmushi.
Ya bita da kallo yana jin kamar ya tsaga zcyrsa
ya saka ta. "sakeena!" yayi kirnta, ta juyo ta
dube shi, "ya zaki juya baki ce min komai ba?"
ta lumshe ido. "ko ganina ba zaisa ki warke
ba?". Bata bude idon ba ta amsa, "sai dai in
jikaka likita in sha". Yayi 'yar drya, "ko? To in
shiga bokitin can kenan?" "Um" "zan shiga fa!
Da gske nake yi. Kin wani rufe ido, ko labari zaki
bani" "uhm...." ta sake fadi. Ya gyara zama
yace, "to ina jinki, bani in sha". Tayi shiru, "ko
barci kike ji?" ta bude ido ta kalleshi, idanuwn
ta sun dan kada. Ya kura mata ido, "yaya dai?"
ba komai" "a'a sakeena. Me ke miki ciwo?" "kar
ka damu" Ya kara matsowa, "ba zaki gaya min
ba? To wa kike so ki gaya wa wnda ya fi ni? Ki
gaya min shi in kira miki shi" tace, "cikina ne
kawai ba wani sosai bane. Dr. Nasan zai daina".
Rai bace yace, "ya aka yi kika sani?" tace, "sbd
ina ganinka Dr. Allah kar ka damu, ba sosai
bane". Ya dafe goshi tare da sauke numfashi, "da
akwai maganin da yafi wannan da na baki
sakeena!". Ta yunkura tana kokarn tashi, "ina
zaki?" "zan tashi zaune ne, don in nuna maka na
ma warke" "no, ki kwnta na yarda kin warke". Ya
sa hannu ya maida ta, ya kara ja mata mayafi,
"kinsan abnda nake so da ke?" ta kada kai. "duk
snda aka sami mishkila baki ganni ba, don Allah
ki daina mummunan tunani a kaina. Kin ji?".
Tace, "insha Allahu bazan sake ba". "kinga haka
ake yi, idan ban ganki ba inyi hakuri, haka kema
in baki ganni ba kiyi hakuri. Shikenan baza muyi
ciwo ba ko?" "gskya ne. To bani labarin Bauchi.
Ya garin yake?" "bansan komai ba game da
garin, domin nima a yamutse na shige shi.
Bansan ko'ina ba, daga dakin taso sai dakin
barci na......." "gaskya ba haka ake yi ba, ba
haka ake yi ba Dr.". Ya dan murmusa, "ya ake yi
sakeena?" "ni dai ka bani labari" "ok labari? To
saurara kiji". Ya lumshe eyes ya zazzage mata
halin da ya shiga, kaf a bauchi. Ya bude idon a
hnkali, suka kura wa juna eyes, "kinji labarin?"
"naji, amma wane bayani ka rubuta a wannan
shiriritar?" "me kuwa banda shiriritar. Kinga shi
bai sami abnda yake so ba, nima ban samu ba"
"magudi ko?" "ba shi bane. Allah haushi ya bani"
"nima haka" "Allah ko?" "ah! To bambance min
zukatan" yayi drya ya lakuce mata hanci, "kin
kureni". Ta kauda kai tana murmushi. Hira fa ta
tsinke, sun ma mance inda suke. Dr. Lwl ne ke
tsaye hannaye ckn aljihu, sannan al'ameen ya
dago ya dube shi. Yayi murmushi, "mr. Lover
lover, kace ba haka ba, ynzu sbd Allah bayn
likita, kai wanene?" yace, "al'ameen ofcourse! Ko
my princess?" "ahaf! Ita tana ma da bakn
magana ne? Ta dare min gadn patient, ashe duk
karya ne lfyrta lau". Suna drya yace, "banda
sharri" "tsakani da Allah haka mai ciwo yake?
Well ku dai kuka sani. Ni zan wuce gida" "da
wuri haka?" "da wuri? Lallai ne. To duba
agognka ka gani". Ya dubi agogo cike da
mamaki, "12 saura kwata?" "kana tmbaya ne?
Baka yarda ba kenan". Yayi shiru yana kalln
mama. Dr. Lwl ya kara matsawa yana duba ta
yana fadin, "ina fatan dai kayi issha'i?" "ina fa!
Shi yasa nake mamakn gudun lokacin". Yayi
rubuce2 ckn file din, ya rufe "ina zaka san lokaci
na gudu, kana kalln mai kyau. Nan zaka
kwana?" "yes, amma bari muje nayi sallah.
Sakeena inje inyi sallah ko?" tace, "maza
hnzrta". Suka yi sallama da Dr. Lwl yana ta yi
mata tsiya, sai da taja mayafi ta rufe fuska sbd
kunyar maganganunsa. Sun fito dr lawal ke
tambyrsa donAllah ina ka samo wann sarauniyar
kyau haka? Yana murmushi yace itama yar niger
state ce iyayenta yan fandogari, yace gsky
yarinyar tayi ko kasan na kusayin barmbabama?
Kamr yaya? Yace aini nan na dage ne iya karfina
in samu ta warke saina gabatr da kaima. Yaja ya
tsaya ya watso masa harara me kake nufi? Ya
kamoshi yana dariya a'a dr maida wukar pls!
Aini an wuce nan wajen tunda dara taci gida.
Trust me wllh tuni na janye kudurina kasan ni
banda rufi ya fizgoshi come on mu tafi mana ai
ya wuce. Yace bakikkirin nake ganinka bazan iya
jerawa dakai ba in banda iskanci ma last year
kayi aure hange-hangen me kakeyi? Ya kyalkyale
da dariya karkayi zato ba daina son matata nayi
ba nikaina bansan abnd ya rikitani ba amma ina
baka shawara ka gayawa sakena ta rika sa nikab
kyaunta is too mcuh gsky! Ya murtuke duk kishi
ya cikashi ya dunkule hannu ya nunashi "kayi
sa'a kaine wllh dana farfasa maka baki!" Yace
fasa mana nima nasan I deserve it but is nt my
fault. Alameen yace u noe wat? Ka kyalemin ita
ni zan dinga duba kayata. Kaga kuma inda baka
isa ba kenan, ya zura masa ido yace I noe wat to
do! Ya wuceshi da sauri yana kwafa. Dr lawal ya
bishi da gudu yana fadin do ur best my frnd ina
maka fatar Allah yasa sakeena matarka ce. Suka
jeru suna kaoon juna ya amsa ameen ameen
kuma ya isheka haka! Ya fashe da dariya suka
tafa mr lover lover! Suna tafe yana tsokanarsa. A
taikace Alameen nan ya kwana duk da mama ta
roke shi akan ya koma gida abinsa amma ya
kafe don yasan ko ya koma gidan hankalinsa
bazai taba kwanciya ba balle ya samu yin bacci.
Kafin a sallameta sai da iyaynta suka samu
labari, suka isa asibitin. Bayan taji garas aka
sallameta, principal da kanta tazo da mota aka
wuce da ita makrnta, suna ta kewar juna da Dr.
****** Karshn wannan watan Allah ya yarda ya
sami zuwa mkrnta ganin sakeenarsa. Wuri na
musamman ta tanadar musu, shoppn kuwa har
maman da tayi jiyyarta sai da ta samu. Sun
tsunduma ckn hirar dnya ckn jin dadi da
farntawa juna rai. Har gaba da azahar yaya
Abdl-kareem da yarnsa suka iso. Kawai ji tayi
nana kirnta wai tayi baki. Tana isowa ta hngo su
ameer, ta kwaso gudu ta rungume su, suna ta
murna. Ta koma gun yaynta tayi masa sannu da
zuwa tare da tmbayar anti Rabi. Yace, ita ma
taso zuwa, amma bata jin dadi ne, tana kwnce.
Tana drya tace, "Uhmmm.... Nasan maganar"
"ban gane kin san maganar ba?""ai da kaji anti
na ciwo to ta kamu ne". Yayi murmushi,
"gidanku! Ashe baki da kunya?" "wayyo yayana,
ba haka bane. Allah ya bata lfya". Du koma gun
su ameer, "kuzo muje, yaya al'ameen na nan
yazo". Suka rankaya gaba daya wajnsa. Yaran na
hango al'ameen, ameera ta kwala masa kira,
"yaya!" ya juyo cike da mamak ya tarbe su.
Sama yayi da ameera, bakinsu yaxi rufuwa. Bayn
sun natsa, al'ameen ya gaida yayan, sannan ya
koma kan yarn yana ta biyewa shirmensu. Mama
ta fiddo kayayyakn da suka kawo mata, harda
lafiyayyn abinci da soyayyar miyar kaji, ga drnks
masu sanyi. Ta zuba wa kowa suka ci, ga ice
cream din da al'ameen ya kawo manyn robobi,
su kai ta sha. Suna yn azahar suka juya, yarn
basu so hakn ba, dadynsu ne ya takura musu,
domin suna son hira da yaya al'ameen. Shi kuwa
dan gogan bai baro bakori ba sai shida na
yamma ckn kewa da tunanin juna mai yawa.
Haka al'amura suka kasnce, duk kashn wata ya
samun kai mata ziyar. Idan suka samu hutu bata
zama a fandogari, tana minni ko abj sbd
al'ameen yafi samun saukn zuwa ganinta duk
sati. Rantsatssiyar soyayyarsu mai ban
sha'awace, domin tana da tsafta, basu da burin
da ya wuce na aurn juna. Sannu a hnkali mama
ta fada zangn karatu na karshe, jarabawa kawai
suka fusknta. Kowa ya zage damtse yana neman
ya tsallake kalubalen da ke gabnsa, ranar kawai
suke jira. Yaynda iyaye da 'yan uwa da abokn
arziki suka dukufa taya su addu'a, Al'ameen na
gaba-gaba. Kwatsam! Sakamakn takardn da
suka tuwa wata jami'ar binciken cututtukan
kwakwalwa da ke Rasha ya fito, bayan shekara 1
wa wata 2 da aika takardun. Su 3 ne suka yi
nasara, 1 daga ibadan, 1 daga Legas sai
al'ameen daga nan arewa. Wayyo Allah! Wannan
tfya tayi masa bazata, ynda ya kosa mama ta
gama makrnta a sa musu rana! Ga kuma tfya ta
fado masa na watanni har 9. Yaya kenan?
Hakika al'ameen na farn cikn wannan nasara,
tare da godewa Allah. Amma wani bangare na
zcyarsa cike yake da damuwar nisan da zai yi,
wnda zai kara tsawn lokacn aurnsu. A tunaninsa
da zarar ta gama mkrnta za'a saka ranar aurnsu,
wnda ba zai wuce wata 2 ba don kammala
shirye2. Ynzu mecece mafita? Sati 3 cur! Yana
kai kawo don kammala takardun da suka kamata
tun daga 9ja har Rashan. Duk da haka damuwr
da yake kaynta na ckn zcyrsa tana wahalar dashi
kwarai da gaske. Yau komai ya kammalu a
hannunsa, kuma ana sa ran saura kwana 8
jirgnsu ya daga zuwa kasar Rasha. Yau din ne ya
iso gida, amma don ya kawo kuknsa wajn
mahaifnsa tare da neman mafita. Yana zaune
cknsu, da ka dubi ynda yake maida jawabn zaka
gane yana ckn damuwa. "ba wai bana farn ckn
wannan ci gabn bane, matsalata sakeena. Dole
za'a ce sai ta dawo za'a sa biknmu". Mami ta
fara magana, "wannan wajibi ne, kaima ka
sani......" "bana son haka mami, ya kamata kuyi
wani abu. Ko da ranar a sanya kafn in bar kasar
nan". Dady yace, "saurn me kake yi na neman
asa ranar kafn ka tafi? Yarnyar nan bakina da na
babnta yace min an baka ita, bana jin akwai
wani abnda zaisa ya sauya baki. Uban dawaki
dattijo ne na kwarai, kuma sakeena na sonka,
tamkar ynda kake son ta. Insha Allahu zaka
dawo ka sameta a matsaynda ka barta, watau
matar da zaka aura". Kwalla suka cika masa
idanu,yace, "na fahmci duk abnda kuke nufi
dady, sai dai zanfi samun natsuwa idan da zaka
taimaka min ka koma wajn abba ka kai masa
kuka na. Pls dady ka taimaka min". Gaba daya
jiknsu yayi sanyi, barin mami. Ta dubi marafa
ckn taushn murya, "ka taimaka masa alh. Ko ya
sami natsuwar karatun. Allah ne ya jarabe shi da
tsananin son yarnyar nan. Babu ynda muka iya
da al'amarn Ubangiji, illa taya shi da addu'ar
fatan alkhairi". Ya sauke numfashi, "kema knsan
dole in je, don bani da wani farin ckn da ya wuce
na al'ameen. Kawai nauyn uban dawaki nake ji,
sbd tun farko ba haka muka yi dashi ba". Taceh
"ai muna da kwakkwaran dalili, nasan shima zai
fahimci uzurnmu"."haka ne, karka damu
Al'ameen, ina tashi daga nan Fandogarn zan
wuce. Allah ya shige mana gaba". Sai a lokacn
ya saki fuska, murmushnsa ya bayyana sirrin
zcyrsa. Ya rarrafo ya aje kansa jikn marafa, "na
godo sosai Abbana". Ya dafa kansa yana sa
masa albarka. Kamar yanda marafa yayi
alkawari bai bata tym ba fandogari ya nufa shi
kadai yayi sa'ar samun uban dwk a gida. Bayn
sun nutsa ya kwashe abnd ke tafe dashi kaf ya
gaya masa nan take Abba yace ni kaina nayi
wann tunanin tun randa na sami lbrn taiyarsa.
Amma ban furta ba tunda baku bukata ba sbd
haka Alamen yayi tunani, yaushe ne zai tafin?
Cikin fara'a ya amsa saura kwana 8, yace to
kuna iya kawo komai konan da jibine sai asa
ranar. Bakinsa har kunne yace mashaa Allah kai
mungode Alh Allah yasaka da alhairi. Yace kai
haba ai duk meson naka ya gama maka komi.
Ya kara godiya sukai sallama cikin nishadi. Ba
karamin farin ciki Alameen yayi ba kowa nata
murna. Ranar litinin tawagar mata da manyan
maza 2 daga lafai dauke da kayan sa rana suka
sauka gidan goggo hausi tasawa kaya albrk sann
suka wuce gidan uban dwk harda innar baraka,
sbd kara sassan Alh Basiru aka saukesu bayan
an gaisa matan suka gabatar da kayayyaki komi
12, sann ga wani akwatin kaya suttura zalla da
takalma kamar wani lefe. Mazan kuwa suna tare
da iyaye maza a falo ba bata tym suka yanke
10mnths, bayan sun dan taba kayan abincin da
aka kawo musu suka tafi suna godia suma
sunayi. Alameen na kwance yaji shigowarsu ya
makale a falo yana jin yadda suke yabon yan
gidansu mama da sauri ya shige dakin iya yace.
Ki goyani ansa min rana tace har sun dawo ne?
Sun dawo iya wata 10 aka sa, ta rangada guda
tace Allah ya nuna mana lfy yace zaki goyani a
ranar ko iya? Dadi ya lullubeshi ya kankame iya
yana murna. Can ma sun tarar da mata'yan tarba
cikin su harda Innasaude watau Innar Baraka.
Sabodakara, asasan Alh. Basiru aka sauke
su,bayan an gaisa,matan suka gabatae da
kayayyakikomai doxin.Sannan ga wani akwatin
kayasutturu ne zallah datakalma kai kace kafe
aka hado.Yayin da mata da kesa albarka, su
kuma maza sun tareda 'yan uwansu maza a falo.
Babubata lokaci su yanke watanni gomamasu
xuwa, in Allah ya kaimu.Daga nan aka
wadatabaki da abinci kala-kala da ababensha.
Kai! Kowannebangare sun ga karamci, don
hakabaki sun wucesuna xuba godiya suma 'yan
gidansuna yi. Al-ameenna kwance a gida yana
jirandawowar 'yan kai kaya, yanamakale gefe
cikin falon, yana jiyadda sukemaida bayani, har
da kyakkyawartarbar da akayimusu. Da sauri ya
tashi ya sulaleya fada dakun Iyabakinsa kamar
gonar aduga, yatsugunna a bayanta,ya kwantar
da kansa, Iya ki goyani, an samin rana.Tace, har
sun dawo ne? Sun dawoiya, wata god,a aka sa,
ina dawowaxaku sha biki. Ta ramgada gudakafin
tace, Allah ya nuna manalokacun lfya.
Yaceameen, amma dai zaki goyaniranar ko iya!
Dadinxancenta yasa ya kara kankame tayace,
haka nanne iya, yanxu me ya rage? Tacebabu,
sai fatan Allahya tabbatr da alkhairi. Yace
AminIya ta. Yace laluba aljihunsa ya ciro
goronfari kalda shi ya mika mata, tasa hannu
taansa, ta bishi dakallo yace, xan xo ki gutsiri
goronnan, ki taunasaboda mahimmancinsa. Kai
tsayeta ba shi amsagaskiyya baxan gutsira ba,
ka fadilabarinka kawaiinaji, ya wuce shikenan.
Yayi kyarda ido yana kallonta sannan yace,jiya
iyaye na sun kia wasuabba kaya an sa mana
rana. Kaibata yarda da abindataji ba, shi ya sa
ta xura masa ido,ba ake yi ba Dr. Aidai be
kamata ka xolayeni ba.Alhalin kasan halin
danake ciki. Yayi mumrmushin jindadi yace, ba
xolayabane my Princess. Magana hakatake kuma
ni na nace sai aka sakamana ranar, dan in samu
sukuninda nutsuwa idan na tafi. Ta
saukegwauron numfashiyana kallo ta gutsiri
goron, shiyasa tana dagowasuka hada ido.
Dariya ya kubcemata, ta rufe fuskatanayi. Sanyi
ya kwarara cikinransa, ya dafe kirji yasauke
numfsahi alhmdlh! Nagodema Allah daka nufi
xan yi tafiyarnan cikin farinciki. Bakin
Mamayakirufuwa, duk iya yinta, don ta katseshi,
abin yagagara, hakan ya hana wata kalmafitowa
dagabakinta, shi kuwa so yake yajitabakinta,
bazaki cedani komai bane? Tace me xan ce?Ya
kamata kitayani murna. Tace, to ina
tayakamurna. Allah ya nuna mana lokacinlfya.
Yace ameen my Princess.Toki kwantar da
hankalini, sabodaxams dinki kinsabamu da wani
buri a halain yanxunda ya wuceabubuwa guda
biyu, kicijarabawarki, sannan Allah yanuna mana
ranar auranmu. Kingawadannan abubuwaguda
biyu, su nake so ki aje acikin ranki a waje na
musamman.Bayan haka ki sance mai
yawanaddu'atare da neman biyan bukatunkiwajen
Allah. Kifahimce ni? Tace, sosai na fahimceka
dr. Kuma ISAxan nutsu, bisa hanyar dakadorani,
ina fatan baza'ayo min kishiya a Rasha ba.Kyar
yake kallontayace, me ake nufi da kishiya?
Tana'yar dariya tace, baka ma santa ba?Yace
gaskiya ban taba jin wannankalmar ba, ko za
kimin bayani? Kinga sai in karu.Tace abar
maganar tunda baka saniba, ni kuma induk
jikina hankaline , baxan tabayarda ba. Ya
maidahularsa kansa, dariya sosai yakeyi,ni kinga
nayi kalarmatan turawa? Ni wlh mace ta cikafari
ma bata birgeni. Amma kigakalar ki? Ke ba fara
ke ba wankantarwada ba, kina gigita ni ba
kadanba. Gabadaya kinhada abubuwan da
nakeso, banjinakwai 'ya macen daxata tsokane
min ido, ballewadannan kaxaman masuwarin
najasa...... Ta katse shi, yaisa haka
dadinbakin.... Baki yarda ba kenan?Tace, ai ba
anan take ba, mkrntarba ko ina daga kasashen
duniyaakexuwa ba? kasani ko wata mai iriinkalar
da kake sozata bayyana? Loacin da xakagigice.
Sakeena na Yayi xugum! Yana kallon ta takare,
ya dankada kai yace, Ina fatan dukkalamn nan
wasa nekike min, idan kuwa da gaske nasai ince
kaico na niAl'ameen da xan iya cin
amanarsakeena. Xanso kifayyace min gaskiyar
dakexuciyarki, don ki fiddanidaga kokwanto.
Jikinta yayi sanyi,ganin tsabar gaskiyya cikin
kwayaridonsa. Murya sanyaye tace,Allah wasa
nake yi dr. Har cikinraina, na hakikanceka amsa
sunan ka. Ya xura mataido, haka itamatake
kallonsa. Kamar bai gamsu dabayaninta ba.Tayi
dan murmushi da sake fadin,wlh, kaji
rantsuwarmusulmi? Dari bisa dari na yardadakai,
na amince cewar babuabinda xai faru da xoben
alkwarina. Yamaida kallonsa bisa xoben, yayidan
murmushi yace,sai na mutu xa'a raba ni dashi.
Yadubeta, kinsanwani abu! Ban taba yi wata
fargabaa game dake ba,me yasa ke kika samu
shakkuakaina? Tacetambayar ka na ta nuna min
bakauarda wasa nakeyi ba, yacenayarda, amma
ina mamaki ne,baka yardanbakenan, to kar ka
ga laifina kishine, yayi 'ya dariya,naga alama,
sai dai naji dadi,domin sai ana sonmutum ake
kishinsa ko? Ka ganekenan. Yace, Iya!To ni ya
aka yi na boye nawakishin? Tace oho.Watakila
kuma naka sikelin yayikasa nan, me kike nufi?
Tayi shirubata son ta bayyana. Yace kinsnAllah
karya kikeyi. Ta dubeshi,tana dariya tacekarya?
To fiddo xuciyarka a gwada.Yace. Na yarda,kema
fiddo taki. Tun yaushe ni nafiddo? Kaine
kamakara, shi yasa nace sikelin ya yikasa. Dole
kayarda. Ban yarda ba! Dole kayarda, ban yarda
ba! Dole kayarda! Ta Marairaice, gaskiyya
bahaka akeyi ba! Ba haka ake yi ba sakeena,zaki
yi min wayau?Tuni take masa dariya, ganin
yaddayayi turus! Doleya sha kaye, kallonta kawai
yakeyi,dadi ya karakamshi. Sun nannagihira har
xuwagabatowar la'asar.Dole yayi harama, a
zahiri ma harya makara, yaushe ya kai minna,ya
gama shrinsa, ya wuce abuja? Koaahalin yanxun
din ma xaune yakeshiru, gabadayansu ido ya
raina fata. Shirunyayi yawa. Mamace tayi ta
maza ta mike tace, mujena rakaka. Yakunkuwa
ya tashi da kuar, ya wuceya bi bayanta,babu mai
magana har jikinmotarsa. Ya jingina rungume
dahannayen sa ya xubi mata ido, dongirman
Allah kuna bari mkrntar,karki bata lokaci
afandogori ki koma Minna ko abuja.Zan cigaba
da kirahar xuwa ranar da zanyi dacensamunku.
Idanuwan tasuka fara tara kwalla tace, kar
kadamu, ko kwanabaxanyi ba, xan wuce,
ISA.Shikenan, in tafi? Tace, xansohakan, don kar
kai dare. Ya budemota yashiga ta rufe masa. A
sauka lfya,ina gaida Mami daIya. Yace zasu ji,
don Allah ki kulamin da kanki,kinji? Tace ISA
zaka sameni yaddaka barni.Promise? Promise
Dr. Yayi danmurmushin damuwayace, I love u!
Tace me too! Yakara fadin so much? Ta juya
dagudu tayi cikin makaranta..... bita da kallon
kirjin sa na bugawa,ji yake kamar ganin karshe
yayimata a duniya. Nan taje idanuwasasuka
kawo kwalla, cikin tashinhakalin yayiwa mota
key, ya maida hular sakeya, sannan yaja mota.
Can tamadubi yahango ta tsaye rungume
dahannayenta, babu alamun laka ajikinta.
Tausayintaya kama shi, nan da na hawayen
samasu dumi suka soma kwarara.Yayi sauriya
jawo hankacif, yana sharewa harya fice daga
gate din sch din. Hakamama ta ke ta xubda
hawaye,daren nan bata iya cin abincin kirkiba. A
gurguje, ya tsayazariya yayi sallama da
jama'arsa,musamman mutuminsa Dr. Lwal.Daga
nanyayi wa minna tsinke, kai tsayeyana shiga
Minna gidan Yaabdulkareem ya nufayayi musu
sallama. Sai alokacin yalura aunty Rabi na
kayan tsohonciki. Yashare minti goma tare da
suAmeera, sannan ya rarrashe shu yatafi. Yaya
natayimasa fatan alkhairi. Ya karaso gidayayi
sallolin dake kansa, ya dawofalo inda su dady ke
jiransa. Ladita baibaaye shi da abinshi
daabubuwan sha, amma baicina kirki ba, wai don
ma Mami tasabaki ne, shi yasa yayyafita.
Sunraba dare daiyayen sa suna ta hira, kafin
kowaya fada makwancinsa. Al-ameen
baisamibarcin ba domin da xarar ya runtsaido.
Mama yake hangiwa tsaye tamadubinmotarsa
kamar marainiya. Bayason ganinta a wannan
yanayinkuma ya kasasauya wani tunanin. Tabbas
yasan,tana cikin damuwa, ya kan jikwallah sun
kawo masa dauki cikinidanuwansa. Washegari
tare daDadynsa suka wuce.Abuja inda suka hadu
da sauranlikitocin guda biyu abokan tafiyasa,a
harabarwani hotel inda su sauran likitocinsuka
kwana. Daga can sukadunguma filinjirgin inda
aka gama tantance su.Karfe sha biyu daidai
jirginsu, yatashi ya nausaRasha. A wannan rana
mama tawuni add'ar Allah ya saukar matada su
al-ameenlfya. Sannu a hankali kuazarin ta
yadawo jikinta, ta maida hankalintaakan karatun
jarabwa kamar yaddaya umarceta. Satin da ya
zagayosuka fara cinkwakwa, jarabawa a aikace,
watau(pratical). Wasa-wasa sun
kwashekwanakiashirin da bakwai suna
jarabawa,daga nan suka shiga shirye-shiryeyaye
su tareda abada kyaututtuka. A wannanrana
makarantar. Babu masakatsinke dajama'a. Mama
ta sha mamaki data ga Mami a cikin
tawagarbakinta. Ta kwasoda gudu ta xube ta
gaishe ta. Ta sahannu ta dago ta, ta
rungume,Allah sarki sakeena. Al-ameen yacein
gaisheki da kyau, kuma in gayamiki
Congratulation!Ta sadda kai tana murmushi,
Abbaya ce baki amsawa? Taruga BayanUmma
taboye, kowa na mata dariya. Tajatawagar ta
xuwa babban dakintaron, ta nemamasu kujerun
xama, wuri daya,mai daukar bidiyon da suka zo
shiyana ta daukarkai da kawowarsu da na
sauranjama'a. Ba'a jima ba, shirye-shiryesu
kakankama. Dalibai sahu-sahu,yarurruka kasar
nan nata fitowasuna nuna al- adunsu. Bayan
angama shkawata aka fara gabatar dajawabai. A
ciki har da na tshuwar (Headgirl). Mama ta
turance baki dakalamaimasu dadi da ma'ana.
Daga bisanita mika dan kwalin ta ga
sabuwarshugabar'yan mata wacce ta gaje ta.
Badakyaututtuka suka biyo baya.Sakeena
UwaisMalami tasha kira, don karbarkyauttuttuka
inda tayi nsa dagafannoni daban-daban na
darussan aji da gasa kalauku da ta shiga,
musammandebate a sci.Bayan an kammala,
shugabarmkrnta ta sallami baki, sai
daukarhotuna ya balle. Kowa ya mikakyautarsa,
sai dauke su hoto. Abbada Umma suka bata,
mami tata dauko nata xungureriyar tace
amadadin Al-ameen ne, ta batakyautar, dominshi
ya umarce ta da ta kawo. Anyimusu hoto, mai
bidiyo na dauka.Duk yayyintasun sami halarta,
banda soja, yanabakin aiki, amma matarsa tazo,
dadansumalami. Ali da sa'aeed duk sunsami
halarta kuma kowa yaxo daabin mikawa.Daga
nan suka baje wa ni fili, sukaci abinci yayin da
sauran 'yanmakaranta basu bar mama sukuniba,
kowa yana xuwa suyi hotuna daita har da wasu
bakin dabata taba gani ba, kawai ta burgesu ne
suka kirata yin hoto. Basubar makrntaba, sai
bayan la'asar, kayan mamatuli a bayan motaci.
Tana farinciki,sai daitana jinsa kalilan ne idan ta
hangataron nan babu liktanta. Ammaalhmdlh!
Dagayau maraici ya kare, xa su ke jinjuna a
waya. Abinda ke kara matakuzari kenantare da
kosawa su isa gida. Kaitsaye direban Mami
wucewa yayimdon yamma tayi sosai. Gida fah
yacika makil! Ana sha'ani, wannantaro bai tashi
ba, sai daabdul- rahman ya gabatr da
xancenauransa da yarinyar da yake nemaa
cankaduna. Kuma iyayenta sun bukacidaya turo
magabatan sa. Farin cikiya karalullube kowa,
saboda haka washegari, bayan kowa ya kama
hanyargida. Ubandawki da 'yan uwansa suka
shiryaranar da za suje kai gaisuwa. Ba abar
Mama afandagori ba, kamar yadda tayi waAl-
ameen alkawari. Kwanan ma yazama dole ne,
saboda dare yayi,amma ko baraka bata tsaya jira
ba,tabi yayanta minna,duk da cewar Anty Amina
ta sotfya da ita abuja, sai dai sabodatshon
cikinAunty Rabi, kowa yafi bada karfinda ta fi
minna kawai. Sun iso lfya,ita kantaAunty Rabi
tana ta murnar xuwanMama. A wannan ranar
bayansallah isha'i sunabaje a falo, suna kallon
kaset dinbidiyo da aka yi bikin makrnta.Aunty
Rabi na tasanti tana fadin, gaskiyya kallo
yawuce ni. Suna tayi mata dariya,lokci guda
waya ta dauki ruri.Falon yayi tsit! Gaba daya
hankulansu suka koma wayar.Kafin kowa ya
motsa, ameera taruga wajen ta dauka Hello! Ta
fadada karfi,yayin da ddynta ke kokarin
tashi.Daga bangaren aka amsa, hello myfriend!
Ameera,Ya Al-ameen ne, Kawai tasai ta saki kan
wayar tana fadin,Hah! AuntyYayane; walhi yaya
ne!

BAKIN CIKI 1***10 Wannan soyayya ta su Al-
ameen dasakeenar sa ko a film ba'a taba nuna
irinta ba. Sannua hankali bikin abdulrahman
yana ta kara matsowa, a'yan tsakanin ne
jarabwar su Mama ta fito. Allah daikon sa
sakamakon ta yayi kyau matuka, domin
tanadaya daga cikin ajin farko. Tsalle da murna
wajen Mama abin ba'a cewa komai, ba ita kadai
ba, kowa yataya ta murna musamman dan gaban
goshin nata,daga can yake gaya mata a halin
yanxun yana tare daabokan karatunsa, suna
liyafar taya ta murna. Donhaka kowannen su dai
tayi magana da shi, tayi masagodiya. Babu bata
lokacu Abba ya fara bincikar mata makaranta a
zariya, amma aka ce ba'a fara siyar daform ba
tukunna, jin haka yasa hankalin Al-ameen
yatashi, sam baya so Abba yayi wahalar karatun
mamakuma, ai cewa akayi a gidan sa xatayi
karatunta. Nantake ya kira wayar gidansu, ya
kuma yi sa'a dadinsana gida, saboda haka ya
marairaice ya bayyana masalarsa, Dady yace,
wai me ke damun ka neAminu? Haba Aminullah!
Menene a ciki, idan ta farakaratun? Yace, ni dai
Dady nafi so ta fara bayan aure,kamar yadda
aka shirya tun farko. Yace, wanan yarorigimarka
tayi yawa, saboda Allah ya kake so inyi?Kaje
wajen Abban, kui magana. Kai tsaye ya bashi
amsa, ba xan iya ba, gaskiyya sai dai ka hk,
bakasan nauyin da nake ji na uban dawaki ba.
Sabodahaka ba inda xani, wannan karon dole ka
hkr. Kuma niban ga wani abin xafi ba, idan
sakeena ta fara karatuyanxi. Cewa xatayi ta fasa
auranka? Kamar zaiyikuka yake fadin, ba haka
bane, Dadyi amma ina tsoron mata a jami'a,
yace, ban son shirmen ka, kayarda Da Allah shi
daya ne mai xartar da komai,sannan ka rike
sakeena da xuciya daya, na tabbataba xa ta ci
amanar ka ba. Ya numfasa yace, shikenanDady,
na gode. Sukayi sallama ya aje waya.
Dukjawabin da dady yayi masa, hanlainsa bai
kwanta ba, don haka yake sake kiran waya gidan
Yaya Abdul.Mama ce kuma ta dauka. Bayan sun
gaisa, ya faratambayarta, yaya maganar
makaranta? Tace, tananan, form din ne har
yanxun ba su saki ba, yace,saboda Allah menene
na wahalar da Abba, yanayawon neman makai
makaranta? Hakki na ne sakeena, don Allah ki
taimake ni, ki gaya wa Abba yabari in dawo,
bayan auranmu, sai ki tsundumamakaranta. Tayi
'yar dariya tace na tsunduma kamarwani kogi?
To menene idan na fara yanxu? Gaskiyyaban so
my princess, pls ki rushe maganar nan sai
nadawo. Ta yaya? Ki na cewa sai na dawo. Babu
mai tilasta miki, tace wa xan gayawa? To sai dai
in gaywaAunty Rabi, tunda ka nace da alama
kana da watamanufa. Yayi murmushi yace,
manufar kenan gudadaya, xallar kishinki, bana
so wani ya san cewa bakida aure, ya lallabo
yace xai miki magana. Aikomuryarki yaji, wlh ya
cuce ni. Ta kama baki tanamasa dariya, a
gaisheka. Dariya kike yi? Dagaskenakeyi, kina da
kyau sakeena, ba karamin jarumi bane xai kalle
ki ya dauke kai. So pls kic gaba daxama gida
har na dawo, in maida ki tawa, ni kadai, aikin
gane? Tace, ba dole ba, ya na iya da Maigida?
Yafara dariya yana fadin iye! Dan sake fadi inko?
Tace,Maigida takobi. Kaina xai fashe uwargida,
in dainafadi? Yace, a'a ci gaba madam. Idan kan
nawa ya fashe, kin san yadda xakiyi. Tace ya
xan yi? Hakanan xa'a sha bikin. Kina fa dada
tunxura ni. Ji nakenakfi kowa awajen nan. Tace,
sa ranka a inuwaAmeer da Ameera suna tafe....
Me kikace? Me nacekuwa? Don Allah ki
maimiata. Allah na manta. Yamarairaice,
gaskiyya ba haka akeyi ba, ba haka akeyi ba
sakeena. Ai dai banji ba sai ki maimaita ko?
Tanata masa dariya tace, sai da safe. Yace, a'a
rufeidonki. Kin rufe? Ta rufe tana fadin, uhm.
Yace, kingansu? Su wa? Ameer da ameera. Suna
tsakiyar mu.Ameer ya cire min hula ya sanya a
kansa. KingaAmeera? Wayyo, kamar ku daya my
princess, shagwaban ta kawai takeyi a ajiki na.
Oh ma Godmwhat a lovely family. I lobe U
sakeena, I really meantit. Murya sanyaye ta
amsa, me too dokta. Tayi saurita kife wayar ta
ruga dakin ta, tayi sufa bisa shimfida,ta datse
ciki ta rasa duniyar da xa ta sa ranta tajisanyi.
Haka ta raba dare tana juyi, bata san lokacin da
barawon ya sace ta ba. Kamar yadda ya
tsaramata haka ta aikta, domin bata bata lokci
ba, ta samiAunty Rabi ta gaya mata, abinda
dokta ke bukta. Taxura mata ido jim, kafin tace,
wannan dan nawa yafiye rikici wlh, menene
banbancin fara karatunkiyanxun da kuma lokacin
da ya bukta? Kar fa yayi miki sakiyar da ba
ruwa, ki shiga gidan yayi mirsisi!Da saurinta
tambaya, kamar yaya aunty? Tace, ayiauran ya
ce bai san maganar karatu ba. Tayimumushi da
bai kai ciki ba tace, Haba anti kamarwani jahili,
ai dokta baiyi xubin irin wadannan mutanenba.
Tace, oh haka ne? Idonki ya rufe kina son sa ko?
Ai shikenan, ni 'yar sako ce kuma ko an tambaye
nishawara ba xance a'a ba. Tace, kinyi daidai
antina,kin kuma san Yaya na ji dake, idan kika
ce eh dinnan, babu sauyi. Tace, banson zakin
baki, inda yakexuwa neman 'yan matansa sani
zakiyi? Ya ya mutsfuska tace, wannan kuma
sharrin kine. Ta dada mata duka. Ai gaskiyya ne
anti, dan Abba sadauki ne,bawan Allah bai yi
xubin shaidanu ba. Ke da kanki, kikace idab
bashi ba, sai rijiya. Tace, a'a sai masai barijiya
ba, meye ajikin Yayan naki da za'a fada rijiya?
Ta gwalalo mata idanuwa tace, ayi kurumaunty,
kar ayi 'yan tone-tone, don ni har na hango ki
agidan Zoo! Tace, kan biki! Lallai yarinyar na ki
gagadon barcina, to ko ke din suke kwakwaxo a
kanki,ma zaki gwada min? Ta kece da daroya
tana fadin, aidama ni ban fadi ba. Aunty ke ce
xaki raina min yaya, alhalin koda mai kwado, ya
dara gaya. Tace, naji saikije wajen kwadon ki
gaya masa da kan ki, a kyalegaya agefe. Ta
rungumo ta, ayya my Aunty ba ma'yar haka dake
surukuta ta kaina! My lovely wife! Tatabe baki
tace, haka naji masu kyau ke da Al-ameendin
naki hakane? Tace ban so surutu, sai in fasa ta
kara kankakme ta, yauwa my swthrt, ke kadai ce
harabada. Tace, ko baki fadi ba. Haka ta lallaba
ta sukasasanta, don ta san halin Aunty Rabo, da
wasa xatace ba xatayi abu ba, amma sai sai ki
sha mamaki,taki ai watarwar da gaske. Ba yaya
Abdulkareemakadai, su Abba kan su sun sha
mamaki da wannan sako da yazo kunnuwansu,
sai dai Abba baiyi jayayyaba, du da yana shakku
cikin ransa, yana jin kamar Al-ameen ba zai bar
ta yin karatun bane. To amma idanya dubi
iyayensa, sai yayi saurin kauda wannantunanin.
Yanxun bikin abdulrahman shi suka gaba,sun
kyale fafutukar makarantar mama. Shi dai dadi
bai san yadda akayi ba kawai an masa ne
makarantarce bata samu ba, sai wata shekara.
Tun sati biyun sasuka wuce aka fara gabatar da
shirye-shiryen biki tahanyar kai kayan lefe
kaduna. Tun daga lokacin sumama babu xama,
kusan kullum fita sukeyi xuwakasuwa, domin
yawancin abubuwan bukata, daga nan minnar xa
su taho da su. Satin daya shigo shine yakama
kwana shida biki, don haka a gobe su mama
damutan gidan za su wuce Fandagori. A daran
ranarraba dare sukayi suna hira da Al-ameen,
saboda xasukwana biyu basu motsin juna ba.
Washegari dasassafe yaske bugowa. Sai da
kalamansa suka sa Mama kuka, don kalamai ne
masu ratsa xuciya, suhana ta sukuni, shi ya sa
bakinta gum! Tana tunanitare da kewar Doktan
ta, ji take kmar tace su sauketa koma gida. Ta
dai ya daurewa sannu a hankali tatattaro
nutsuwarta wuri daya, ta dauki dangana. Sunisa
kuma, ganin Ummanta ya debe mata kewar
masoyinta. Bayan sun ci abinci, sunyi sallolin
su,sannan suka ci gaba da tattaunawa akan
shirye-shiryen biki. Karfe biyar dai-dai lokacin
ne rana tayisanyi. Mama ta sheko wanka tayi
shafe- shafe, bayaga hoda bata karawa fuskar ta
komai ba, ta daukowata atamafa 'yar ingila
ruwan bula ta sanya, ta daura dan kwalin ta, ta
ziro bakaken takalma, ta yafo bakingale ta
rataya jaka. Duk wannan shirin na tafiya
wajenBaraka ne, wai nan ma ba kwalliyya tayi
ba, kawaiyanayin jikinta ne baya boye kyan da
kaya ke mata.Ta sallami Umma ta kama hannun
Ameera suka fitotare A kofar gida suka ci karo
da Ameer, yanaganin gari shi ma yace zaije.
Tace yaje ya fadi a gida,don kar a neme shi.
Daga nan ya kwaso takalman sa.Ya sheka a guje
cikin 'yan dakikai ya fito suka wuce.Suna gaba
tana biye da su, suna xuba mata labari,iya ko
jinsu bata yi, don tayi nisa a tunanin Doktan ta,
kalamansa ke shiga suna fita a kunnuwanta,
"kwanakigoma banji muryarki ba sakeena? Ai
yayi yawa, kitaimake ni kar ki sa asiri na ya
tonu a makarantarnan. Xauntuwa xanyi cikin aji
in kasa gane komai".Idanuwan ta suka tara
kwalla, tayi sauri ta shanye su,tana fada aranta,
ba xan xauna ba, ana gama biki xan koma......
Sannu 'yam mata! Muryar ta fito. Samaribiyu ke
xaune bisa benci a kaofar wani katon shagodaf
da bakin titi. Daya fai sol! Ga dogon hanci
damatsakaitan idanuwa, duk da cewa a xaune
yake, kana kallon sa zaka gane dogon gaske ne.
Gashinkansa kuwa mai santsin gaske ne, har
yana nannadewa duk da cewa bai da yawa
akansa, watauyayi aski. Kwalli ram! Ya xauna a
idanuwan kamarmace. Ga kuma alamar gashin
baki baki wulik! Akwance, guda kuwa wankan
tarwada ne kuma zamansa kusa da na farkon, ya
dushe gaba daya kyan sa.Gaba dayansu, ta san
su, amma tuni suka bace a kwakwalwarta, domin
shekaru masu yawa rabon ta dasu. Sannan ko a
wancan lokacin babu wata alakantsakanin su.
Shi yasa a yanxu take masu kallonmamaki,
yayin da farin yake kara fadada murmushinsa,
sannu ko? Ya sake fadi. Wani guntun tsaki
tayi,ta wuce abinta, sukayi sa'a babu wata mota
mai xuwa, don haka ta rike hannun yaran suka
tsallakatitin. Ka gani ko? Na gaya maka karka yi
matamagana, ba zata saurare ka ba. Yayi
murmushi yace,ko bata suarare ni ba, dole ne ma
ta so ni, domin irinwadannan su ne ke nema
kuma ban taba daga ido nadubi yarinya nace ina
son ta ba, tayi min kallon banza ta xubar ba.
Yace yau ka samu, saboda haka dukabinda kake
takamar ka na dashi, yau ka hangowacce ta fi
ka, kar ka kuma ka mance, bikinta sauran'yan
watanni suka rage, mijin da xa ta auran ma
bashianan kasar, kaga kuwa yafi ka komai. Ya
ja dogontsaki, aikin banxa, to meye ruwa na
dashi? Kasan Allah yarinyar nan sai dai in ban
so ta bi ra'ayi na ba,cikin dan kankanin lokaci
zan birkita ta, ko? Wlh, kajina ranste, yace
hakan dai babu kyau, tunda na gayamaka bikinta
ya kusa, sai ka hkr. Yace, kai ba xanhkr ba,
yanxu ma na fara sonta. Yana dariya yace,sai ka
shirya yaki da manyan kasa, na lura har yanxu
ba ka hankaltu ba. Yace, bar maganar nan tun
kafinran ka ya baci, don Uban ka! Yace, nayi
shiru. Zai fimaka kyau. Ya tashi daga kantar
shagon sa ya komaciki ya xauna a kujera. Bai
kara tankawa na wajen ba,haka shi ma bai sake
cewa da shi komai ba. Yayin daita ma mama ke
tafe tana sakin tsaki kamar tsaka. Ranta bace
tayi sallama gidan su baraka. Barakar ketsakar
gida tana wanke- wanken yamma. Tayi
tsallesama ta runtuma a guje suka runguma
juna. Inna taleko daga daki da sauri tana
tambaya lfya? Sai tagansu rungume da juna, tayi
dan tsaki tace, Ammadai Allah ya shirya ku,
kunji yadda gabana ya fadi? Suka nufo gunta
suna dariya, wayyo Inna, kinsankwana biyu ba'a
hudu ba. Tace, ku rika nutsuwa,girma kuke
karawa. Mama tace, to Inna. Suka shigedaki,
suka gaisa da Inna, sannan suka dawo
indaBaraka ke wanke wanke ta baro su Ameera
wajenInna. Ta kawo wa Mama kujera ta xauna
tana wankewa. Mama na mata dauraya. Ina
mutuminki?Tayi dan murmushi tace, karki sani
kuka don Allah,yau da kyar zan iya barci baraka.
Ko? Kuna da abindariya ke da likitanki nan, tace,
baiki tausayinmukenan? Tace shagwabar kawai
ke damunku, shi yamarairaice, ke kin
marairaice,, to wa zai rarrashi wani? Da kan mu
muke rarrashin junanmu. To yaza'ayi, ke kuwa
soyayya. Tace, baku da laifi, in gayamiki nima
na kamu. Ta mika mata hannu, ban mukashe,
don Allah, a ina yake? Suka tafa suna dariya
kafin tace, danKagara, wani dan aiki ya kawo shi
na garin, na yiniguda, in gaya miki ashe rabo na
ne. Muhammadsunan sa, yana aiki a sakateriyar
nan ta kagara. Tajuya idanuwa tace, ba shakka
ta muhammad. Allah yatabbatar da lkhairi. Tace,
amin. Suka kara tafawa, ai zaki ganshi, dan
kyakkyawa shi ga addini. Tace, baikai Aminu na
ba dai. Ta tabe baki tace, naki kikasani, ni kuma
nawa na sani. Kowa da gwaninsa.Tace,
gaskiyarki, kuturu ma sarki ne a gidan sa.
Shikika raina ma wayau? Tace, ba haka bane
wlh, aimisali ne kawai. Tace, na gane kowa jin
kamsa yakeyi a inda yake takama? Mama ta
gyara zamatace, har kin tuna min, wai yahse
wannan me masunansa? Wannan da aka jefe
babansa wajenkwartanci? Tace oh! Kina nufin
Dan liti? Yauwa shimyaushe ya dawo gain? Tace,
ai ya jima zai kai satibiyu. Ta tabe baki, na gaua
bude wani shago ne? Kai mutane ba su da
tunani, menen na barin Dan liti yaxauna garin
nan har da ba shi hayar katon shago?Tace,
manyan gari ma basu kore shi, wai zai koreshi?
Wai kin san ma wani abu? Yanxun nana xan
wuce,wai sannu 'yan mata yace dani. Tace, haka
yake,anyi gadon banza ido a mata. Shi jinsa
yake mai kyau, marasa tunani na binsa yana
lalata su. Kingashekarunsa shida rabonsa da
garin nan, amma yanadawowa 'yan mata na
masa layi, yana tijara su. Takaici ya ishi mama
tace, kwadayi, ba an ga ya dawo daabin duniya
ba? Ai mata mun shiga ciki, kwadayi kekai mu
ya baro mu. Allah ya shiryemu, tace ameen dai.
To wai shi da yayi miki magana menene nufinsa?
Ido waje tace oho! Shi ya sani, ke da baki wajen,
idankin tanka, nima na tanka masa. Allah ya isa
ma nayimasa, daya katse min tunanin dokta na.
Suka tafa,Baraka ta mike ta dauki kwandon
kayan ta shige dashi kicin. Mama ta dauki
tsintsiya ta sa ruwa ta kora wurin, ta share tas!
Suka koma dakin Baraka. Hirar takoma can tare
da tsara shagalin biki. Gab da akekiran magriba.
Mama ta baro gidan Baraka tayo matarakiya,
suna rike da hannauen yaran har bakin titi.Anan
Baraka ta tsaya tace, to sai na zo goben ko?
Tace, ina jira, don Allah ki zo da wuri. ISA, lah!
Kinga mutumin naki da zai rufe shago, ya hango
ki ya fasa.Kar ki bi ta wajen sake hanya. Kinsan
Allah bai isaba, bazan dauki nisa saboda shi ba,
idan ya matsamin sai ya sha mamaki, don xan yi
masa wnkinbabban bargo, kafin nan bar garin
nan. Ina son kimatar likita, amma ki tsaya bata
lokacinki wajen danliti asara ce, ki wuce kawai,
shi ya fi. Allah kokawata? Don dai ba ke yake
wa magana ba, shi yasahaushin bai damunki.
Tayi 'yar dariya, haka ne, ammaina rokon ki,
karki kula shi, ba don ni ba sabodaDokta. An
gama, kinsan wani abu? Cewa yayi idanwani yaji
murya ta kawai, ya cuce shi, abinda na tuna
kenan. Saboda haka kwalelensa, ba zaiji ba. Suyi
'yardariya. Kuje, yanxun xa'a kira sallah, sai
goben. Allahya kaimu. Ta sallamu su ameer, ta
tsaya sukatsallaha, sannan ta juya ta koma. Kai
tsaye mama tazao zata wuce. Dan liti bai
daddara ba, ya sake yimata magana, 'yan mata
an dawo? Ko kallo bai isheta ba, wannan karon,
ya daga murya ya sake fadin,Haba 'yammata ai
rika sauraran masoyi mana, don ba'a san inda
rana zata fadi ba! Kai, Dan liti yayi sa'atayi
alkwarin ba zai ji muryarta ba, amma da
yajiamsar da ba zai sake marmamrin kula ta ba.
Dawannan haushin ta iso gida. Suka yi alwala da
yaran sukayi sallah. Dare ya raba barci, yaki
zama cikinidanuwan ta saboda zafi biyu suka
hade mata, gakewar muryar sanyin ranta, ga
kuma takaicin rashinba Danliti amsa, har yanxun
yana mata kaikayi axuciya. Idan ta tuna kalaman
sa na karshe, ta kanjikamar zata mutu. Wai ba
'a son inda rana zata fadi ba? Ta kan kuta, ta
shanye hwayen idanuwanta. Hakata wayi gari da
ramar rashin barci, shi ya sa take jinkasala.
Xuwan Baraka ya sa ta gyagije ta mike
sosai,suna ta aiki. Ba'a jima ba, ango ya iso.
Gida ya karagauraye wa da shewa da guda.
Bayan sallar la'asarmutanen Abuja suka iso.
Sannu a hankali gida ya cika da 'yan biki na
nesa da kusa. Tundaga lokacinake ta dora
tukunya ana saukewa.... Ranar juma'a akwai
dinner a kd. Don hakaango ya kwashi su mama
da baraka tare da su danDanlami ya wuce da su.
Mama kam sai da mucetsarki ta tabbata ga
Allah gwanin halitta, ka ranste daAllah itace
amaryar. Tana gefen Yayanta, ya na ji daita.
Samari kowa idonsa na kanta. Cikin abokansa
kuwa babu wanda bai taya ba, amma ya ce mus
ansanya mata ranar 'yar watanni suka rage
bikinta.Kash! Duk wanda yaji sai ya numfasa.
Lallai Al-ameen gaskiyya, sai ma yanxu take
kara jinjinwatunanisa. Bata gama shan mamaki
ba, bayansundawo daga diner, misalin goma na
dare, suna sashin baki a gidan ango, inda aka
xubawa amarya kayandakinta. Suna tare da
Baraka hirar dinner kawai sukeyi. Dan lami ya yi
sallam ya shigo yace wa mamayaya Ali na
kiranta. Tace lfya? Yace kalau, yana canbaya. Ya
fice abinsa. Ta dubi Baraka tace, kinji
watasabuwa kuma. Tace, wata tsohuwa dai, ai
kun jima da Yaya Ali. Abin ne ta motsa, kin san
gyambo ne, tace,Allah ya ba shi sauki. Ameen
dai. Ta figi gyale ta yafata same shi a bayan
gida yana xaune bisa dakalinsokawe da fara'arta
ta tayi sallama, ya amsa. Ganinfusakar ta sake
ya sa shi ma jin sanyi cikin ransa,tace wai kana
kirana? Yace eh ina kuma fatan xaki saurare ni,
ta kara matsowa tana fadin me hana yaAli? Meya
faru? Ya mike daga inda yake yace ga gurixauna,
tace a'a yay Ali kayi xamanka kawai, no kixauna
ai ni nace ko? Ta xauna tana murmushi sannanta
dube shi suka hada ido, ya akayi? Yace
babukomai Mama, kawai so nake muyi hira. Ta
sunkuyar da kai tare da numfasawa. Yace nasan
tuni kin mantada ni cikin ranki, amma ni na kasa
mama, waccesahwara xaki bani? Ta dago kai ta
sake dubansa,tace me xaisa na manta da kai Ya
Ali? Karfa kamanta jininmu daya, dubi
fuskokinmu kamar mu daya,don me xan manta
da mutum kamar ka? Ashe lallai xan iya
mantawa da su Ya abdulkadeer. Ya
saukenumafshi yace, haka ne, amma kin san ina
miki waniso na daban ko? Sao dai ke kinyi nisa
da soyayyarwani, har kun kusa aure. Ba wai ina
masa ynaka bayabane, so nake ki gane har
abada ni mai sonki ne, bakuma xan taba fidda
rai da ke ba, sai ranar da na ga an shafa fatihar
auranki. Xanyi farinciki, idan har zakiyarda mu yi
hira koda labarin Al-ameen zaki rika bani,wlh
xan saurareki. Ta runtse ido, tausayin Ya Ali
yaryfeta, sai dai runtse idanuwan da tayi bata
ganinhotunan kowa face na Al- ameen dinta. Tayi
sauri tabude, idanuwanta suka kada, a sanyaye
take cewa, kayi hkr Ya Alli, komai mukaddari ne
daga Allah. Kayiaddu'ar Ubangiji yayi maka
sauyi na alkhairi. Sannankuma ina so ka sani,
ban taba kin ka cikin raina ba,kuma ba xan taba
kinka ba, shi aure nufi ne na Allah.Shi ne yake
shirya abinsa yadda yaso. Ina fatan kafahimce
ni? Ya gyara tasyauwa yana kallonta, yace, na
fahimce ki mama, na gode da gudunmawarki.
Toamma bana so kana damuwa. Yayi dan
murmushi, nadaina kanwata. To kai sai yaushe
zaka yi auran? Sairanar da na daina ganin Mama
a matsayin budurwa.Ta kalle shi tana 'yar dariya,
ka tsufa Ya Ali, ka fagirmi ya Abdulrahma. Kana
so a fara maka kiran gwauro ko? Hakan bai
dameni ba. Ni ya dameni, aceyayana gwauro.
Yayi dariya, nace ki bari na tabbatarna rasa
wacce nake so, sai in rufe ido in kwaso kowace
ce inyi maneji. A'a yayana, tsakani da Allahzaka
aureta, ai sunnan ba'ayin ta da maneji. Iba
dace,ibada kuwa akwai hakkoki cikinta.
Gaskiyane, amma kin san shan kojo kwanciyar
rai. Kuma kowane soyana da mizaninsa a xuciya,
ni na san babu macenda xan so tamkar yadda na
ke sonki. Ya Ali kenan,ka bar maganr nan don
Allah, na yi karya ne? Banfada ba. Bari na shiga
ciki, kin gaji da surutu na ko?Ta kada kai, a'a
wlh kawai barci na ji ya soma kama ni. Kindai
gajin kena. Eh, toh da xak duba agogonkakila ka
ganr dare yayo. Ya duba agogon ya dubeta,sha
daya da rabi ne kawai. Tayi sauri ta mike, wuu!
Aikuwa na kawai bane, dare yayi yaya. Kai
kankaidanka ganni da wni a wannan lokacin,
dole ka koranigida. Uhm hakane, amma banda
Al-ameen, don ban isa na rabaki da shi ba, do
ne? A matsayinka nayayana, idan bayi dai-dai
ba, dole ka hukunta ni kotare da wa nake. Yayi
dan murmushi, to na gode. Saiwani lokacin
kenan? Uhm..... Sai da safe. Allah yakamu lfya,
Ameen. Ya wuce ba tare da sake waigowaba. Shi
kuwa kallonta yake tayi har kule ya sauke
numfashi, ya koma inda ta tashi ya xauna, shiru
jimsannan ya kada kai cike da damuwa.
Damuwar mamaba a kan tausayin Ya Ali kawai
ta tsaya ba. Ji takekamar tayi abinda ba dai-dai
ba ga Al-ameen. Shi yasa xuciyarta ta rasa
sukuni ta rika korafo wajenBaraka. Allah ya sani
ba tadi tayi da Ya Ali ba, illa ta saurare shi ne
kawai don ta kwantar masa da hankali.Yaushe
rabon da yayi mata magana irin wannan?Tabbas
ta gane yana cikin matsala, dalilinsa da ya
sakenan ta tsaya ta saurari kalaman bakinsa,
wadandatake ganin amayo su xasusa ya sami
sukuni aransa.To ita gashi ta shiga matsalar,
gani take tamkar taci amanar doktanta. Ta
runtse ido hotunan sa sukabayyana gareta, yana
ta cuba murmushi muryarsa nafadin.. Shema
Alqali "Manufar kenan guda daya, zallar
kishinki.Bana so wani ya san cewa baki da aure,
ya lallaboyace xai miki magana, ai ko muryarki
yaji, ya cucuniwlh." A bayyane take magana
batare da sani ba, kayihkr dokta, Allah bada
wata manufa nayi ba. Barakadake kallonta, ta sa
hannu ta bubbuga ta. Ta mike firgigi dafe da
kirji, Innalillahi wa inna ilahir raji'un!Baraka
tace, wlh xaki xautu! Sambatu kikeyi, idanbaki
sani ba, ki sani yanxu. Ta numfasa tace,
barakaDokta na baya so kowa ya ji muryata. Har
'ya uwanki?To kunyi karya, dole aji muryarki,
musammamn su YaAli, domin dan uwanki ne,
kuma tare ya ganku. Shima ba irinsu yake nufi
ba, karki maida kankimahaukaciya mana. Ta
koma ta kwanta shiru,idanuwanta suka kawo
kwalla. Kada ki shiga rudun daxai dagula
lissafinki, a aikin baxa har karshenrayuwarki, ba
xaki daina magana da Yaya Ali ba, Al-ameen ba
zai hana ba, don ya san dolenkine. Dama kin
kwanta kinyi barci da ya fiye miki alkhairi. Ta
maida kai bisa filo taja mayafi abinta. Mama ta
saukenumafshi, ta gyara kwanciya bata san
lokacin dabarci ya sace ta ba. Tun safe suke
shirin tarbar 'yandaurin aure, karfe daya dai-dai
kafar gidan ango babumasaka tsinke da motoci,
bayan anyi sallah. Abokan ango tare da angon
kansa suka jagoranci tawagarxuwa gidan iyayen
amarya inda aka daura auranFadila ta ma
mallakar Abdulrahman halas malak!Daga cam
liyafar cin abincin rana akayi ta maza
zalla.Komai ya ji. Masha Allah! Babu bata lokaci
motocindaukar amarya suka koma, yayinn da
Mama da Baraka suka koma motar Abba. Anata
kirana sallarmagriba, amare suka suka
Fandagori, kebabban wurida aka gyara musu
cana aka sauke baki. Washe garisuka sha
gagarumar walimar da aka jima ba 'yikamarta ba
a Fandagori. Xuwa la'asar baki suka komakd,
aka bar amarya da lainta. Mama da baraka ke
tare da ita, suna ta tslkanarta, karfe biyar da
rabi ango yashigo, saboda haka suka fito suka
basu wuri. Daganan Baraka tayi sallama da
kowa, ta kwasokayayyakinta. Mama ta daukar
mata wasu suka kamohanya, tana yi mata rakiya
sun atafe suna hirar susuka doso shagon Danliti.
Da saurinsa ya fito ya xauna, yana jiran
karasowar su, suna xuwa kuwa yatanka, 'ya
mata ran gari! Ko kuna jin gaisuwa? Su kaba
banxa ajiyarsa, suka wuce. Sun dan jima bakin
titi,suna sallama kafin Baraka ta tsallaka, ta
kamahanyar gida. Mama ta juyo ta dawo, 'yan
mata ji manadon Allah! Dan liti baiyi xuciya ba,
ta kyale shi, ta wuce. Kawai ganinsa tayi ya sha
gabanta, haba 'yanmata, tunshekanjiya na ke
gaishe ki, me yasa bazakiamsa min ba? Bakin
ciki ya turniketa, kamar ta kurmaihu bata san
lokacin da ta amsa masa ba cikinxafinta. Tace,
wai dole ne? Ko ka ganayi kama dashirginka?
Yace Ya salam! Maida wukar 'yan mata, ba fada
bane, A zato na so bai taba zama laifi ba.Taja
dogon tsaki ta wuce shi. Ya daga murya ya
sakefadin, a daina fada da masoyi, don ba 'a san
inda ranaxata fadi ba! Taf! Yayi biyu kenan.
Kamar xata daure,amma ta kasa, cak!!!! Ta ja ta
tsaya, ta juyo ta dubeshi har ya koma maxaunin
sa, kusa da bokinsa, na rannan. Ta tako a nutse
taxo gefensa, ta tsaya sukakarewa juna kallo.
Yayi dan murmushi yace, ko ke fa?Ai idan kace
so an gama magana 'yan mata. Ta gyaratsayuea
fuska daure, " wai ba kai bane danliti? Ni ne.Dan
wajen buzu mai shayi ko? Ya
hadiyemurmushinsa, kwarai nine. Ta kara
kankance idanuwa, ta cigaba, wanda yaje
kwartanci din nan akakama shi, ya ci dan banxan
duka, wuya ta kashe shi,ko bashi bane? Wani
irin kallo yake mata, bai iyacewa komai ba, ta
kara karkacewa tace, ai kodamuke yara ba mu
da wayau sosai, tarihin bai bacemana ba na
munana ayyukansa, muna ganinsu cikin
idanuwan mu. Hijira a gudu bayan 'yan shekrau
adawo, ba shi xai goge rubutun ba. In bnda
abinDanlita, ai bindin rakumi yayi nesa da kasa,
kumagaskiyar hausawa da suke cwa kwarya bai
kwarya.Dube ni da kyau, kai kanka ka sanni ba
abokiyarhadin ka bace. Don Allah a rika nutsuwa,
ana tunanin abinda ya dace. Taja tsaki ta wuce
su, suna kallonta.Baby wanda ya motsa. Sun fi
sakwan uku bayantafiyarta. Babu wanda ya
tanka baokin yace, kaga irintako? Sai da nagaya
maka wannan yarinyar ba xatasaurare ka ba,
gashi ka jawo ta zagi baba.Idanuwansa sukayi
ja! Yace, ta kuma debo ruwan dafa kanta ba. Xan
nuna mata tabbas ni dan gidanbuxu mai shayi
ne. Ai ni dama irin wadannan 'yan jinkan nake
nema, inyi maganinsu. A'a dan liti baka
dagaskiyya. Tun farko na gaya maka yarinyar
nan an samata rana, bikin ta ma ya matso. In
banda iskanci irinnaka, menen na yi mata
magana? Mu da muke gari ma, bamu ce xamu
neme ta ba sai kai da ka dawokwanan nan? Mu
ma ai mun sa cewa tana da kyau,amma mu ka
basar. Dahskiyara da tace kwarya tabikwarya. To
wannan karon xa ta hau akushi, kuma taxauna
daram dam!!! Yace, wlh kayi karya.
Billahillazi,yarinyar na sai ta dauki cikina
kuma.... Ya tsohe masa baki. Babu ruwana
danliti, idan ka jawo bala'inda yafi karfinka. Ka
ga muna xaman lfya, ba uwa bauba a garin nan,
gara ni bani da tabo... Amma kai kana ganin
abnda ya faru zamangarin nan ya ggareka ,
yanxu ka samu ka dawo harankarbe ka , don
Allah kayi kokari ka zauna damutane lfy. "Ai ba
saboda Allah bane da shiri na,nadawo, shi yasa
kaji bakin kowa gum! Sai itace maibakin rashin
kunya. To zanyi maganinta , wadanda ma suka
fita taurin kai, na gama da su balle ita.Kasan
Allah yarinyar nan sai ta raina kanta ..." Danliti!
Karka fara wannan danyen aikin , ina ba
kashawa. Kasan tana da yaya babban soja ko?
Wlh yakwashe ka ya kai bariki, kai kanka idan
aka aje kagaban mirrow baza ka shaida kanka
ba".. Ya ja dogon tsaki, "Aikin banza, kai ka ke
tunanin soja, sojanbanza. Sojan wofi" da kwalli
kake takama Dan liti,gashi nan kuma a idon ka
ban ga yayi tasiri ba, bansoka matsa da yawa
Dan Liti, watakil rabon whla kejanka" Ayuba na
ce ba ruwan ka, nkna sha alwashinzanyi maganin
yarinyar nan. Kasa ido za ka ga abinda zai
faru"... Ya zura masa eyes yana mmakin sa,
dazaiji shawarar sa daya kyale yarinyar nan
tunda Harda Allah ba ajin sa bace, idan aka bi
salsala. Ammashi Dan Liti ko ajikin sa, watakil
ajali ke kiransa,kamar yadda ya faru da
tsohonsa...
BAKIN CIKI 1***11 Washegari anti amina da anti
rabi suka shiryatafiya. Tun dare mama ta hada
kayanta tace ita mazata bi su,fasa karin
kwanakin da tace zata yi.Gabadaya suka rufe ta
da tsokana wai sbda alamin zatakoma.Tace eh
sbda shi din ne haramun ne? Ita kadaita san
abinda ke damunta. Duk da ta ba danliti amsa,ji
take kamar amsar tayi kadan ko alama batason
ganinsa balle tahi munanan kalaman
bakinsa,shiyasa ta zabi data koma minna tayi
zamanta canhar lokacin da alamin zai dawo.
Allah da ikonsakuma,anti amina ta kafe tare
zasu tafi wannan karon.Gaskia hankalin ta zai fi
nutsuwa a minna sbda tana gani bebi alamin
tana renon sa yana mata dariya idanta kira shi
dokta.Ita kanta anti rabi bata so hakanba,sai dai
ba yadda ta iya dole mama ta bi anti aminata
nace.Suna ta zuba kayan su a mota.Yara
damanya na taya su,bayan sun kare suka kara
sallamada kowa duka suka yo musu rakiya har
da marya da ango.Mama ta shiga bayan mota ita
da malami.Yayaali ya tsaya jikin tagar ya zuro
mata ido "wai damadake za'a wuce? Tace eh
mana."Na zaci zaki yiwaumma kwana biyu".Tayi
murmushi,naso hakan ammaai zan dawo,yaushe
kenan? Ni ma sai inzo mugaisa.Tayi er
dariya,gaskiya ba zance ga lokacin ba,watakila
ma sai alamin ya dawo,"Ke don Allah,kusan
wata uku kenan ashe zaki iya tafiya ki barumma
tsawon wannan lokacin? Tace ba haka bane Sai
ga yaya soja ya fito tare daabba,shi yakatse
musu zancen.Abba ya leko,toauta na a kula
dakai kin ji? Tace to abba",yayanyace "abba har
wanirarrashinta kake yi,jaririya ce? Yaceitace
mana,damaina son gaya maka ka
dainarankwasar min ita'.Yawaigo gidan bayan
yanafadin,rankw ashi abba?Irin wannan?Abba ya
bude murfin motaryace,"auta nafito! Fito ki bi
abdulkareem. Tafito dage da kai har dakukan
shagwaba,masu dariyanayi.Shi ma ya fito
dasauri,sorry abba,sorry! Ya kamakunnuwansa
yarike,"na rantse ba zan sake ba" tacuno baki
tamakale kafada,ni ba zan bi suba.Yaya yace,"za
ki tsallen kwado awajen nan,I'm telln you,ki
shigamotamu tafi!Ta kara turo bakin,abbayace
'yi hakuri komaki kyale shi".Har ta tura kai
zatashige ta sakedagowa ta dubi umman ta
tsayekofar gida tanadariya,ta ruga wajenta ta
rungumeta,umma zan dawonan ba da dadewa
ba.tace wuce kutafi". To Allah ya tsare. Ta
saketa,ta kwaso sauri bata san yaddaakeyi ta
dawo ta bangaran inda yayaali yake
tsayeba,kawai ganinsu tayi daf dajuna,ta bi shi
da kallokafin tace,ba zan dade ba,zandawo."
Jikinsa yayi mugun mutuwa yace,adawo
lafiya"'amin".Ta bude mota ta shiga yataimaka
ya rufe kofaridanuwansa na kallonta,Ta
sunkuyarda kai,ita kantabata san abinda ya
kashe mata jikiba,sannan batasan me take
tunani ba,Ji tayi motana tafiya ta dagoda sauri
tana daga wa kowa hannuhar suka bace.Ta
maida kanta jikinmota ta jawo malami
tarungume.suna isowa daidai shagondanliti,daga
muryayayi yace "Allah ya kiyaye hanya!Ta ballo
masaharara,yaya nta na
fadin,"amin""amin".Tana harararsayana mata
murmushi har da dagamata gira,ta sakidogon
tsaki,"ke da wa? Anti aminata tambaya,tace
mantuwanayi.Yayanta yace 'ba zan koma ba!
tacenima bance ba yaya ai ba waniabun damuwa
bane namanta". Suka fada titi,komadamuwar ne
ba zankoma ba lazy girl"tace "lazy soja"ya
kyalkyale dadariya yana kallon
motarabdulkareem tana bin su abaya yace,ni ko?
Za ki shiga guardroom yarinya,jikin ki zai
gayamiki".Suka kalli juna ita da
malamisukatintsire da dariya haka suka
cigabada tafiya. Har suka iso minna anan suka
tsyasuka karayiwa juna sallama
sannanabdulkareem ya daukihanyar unguwar
su,su kuma sukacigaba da tafiya.Sun isa abj
lafia,sojoji biyu kegadin gidan suka budemusu
get. Bayan sun yi sallolinsukowa yaci abindayake
sha'awar ci daga nan mamada anti amina suka
shiga gyaregyaren wuri.Karfe tara na darelokacin
neda mama ta gama shirin barcibayan wankan
datayi.Suna kwance da malami wanilittafin
labarin yaratake karanta masa,anti amina
tashiga dakin tace,gadoktan ki can akan layi
dama yasan yau zaki dawo?Ido waje ta kada kai
tace a'a kilasun yi waya da anti rabi ne ta
gayamasa,ba mamaki je ki dauka.Tasauko kayan
barci ne jikin ta rigada wando ta rugafalon kasa
ta dauki kan wayar dakeaje gefe,tayimasa
sallama,ya amsa muryarsa nabayyanar dafarin
cikin zuciyarsa.Watau abj kikagudo ko?me
kikenufi da kika baro dokta acan?'Yardariya tayi
tace,shi ma yaji yaddanake ji.Baki da hujja
yarinya kikomagun sa kafin mami taci ki
tara.Zankoma yallabai,toya karatu,ya rasha?To
ba laofoamma rasha kin sansai maneji da nake
yi,zuciyata nagun ki myprincess.Tana murmushi
nima inatuhumar kadokta,waya gaya maka ina
nan?Yace kawai na kira ne inji ko suanti sun
dawo,inyi musu barka dadawowa.Sai take gaya
min kemakina abj,ta dannumfasa tace ta
kyauta.Ko?Allah,dama ina tatunanin ina zan ji
ka?Allah sarkisakeenta,to ya biki? Tace anyi an
gama lafiya amarya na can tare daangonta.da
kyau,saura namu ko? Tayi murmushi batace
komai ba,ba zaki amsa min ba? Me zan ce?
Bayankasan hakan?yace to Allah ya nuna
mana,ki karahakuri na kusan dawowa kin ji?
Idanuwanta suka kawokwalla.Na kosa dokta,baki
kai ni ba sakeena,ni kadai na san yadda nake
ji,kin san irin son da nake miki kekanki kin san
ina wahala anan tsawon watannin danayi ban
ganki ba sakeena yasa idanuwa na sunmakance
alhali lafiyar su lau,dul abinda na kalla
bayagamsar dani my princess hakuri kawai nake
yi. Tagoge kwallan bisa kuncinta,ta numfasa,no
sakeena,pls kar ki gigita ni,stop crying,please!M
uryana rawa tace dole in yi hawaye dokta,domin
na fi kafuskantar kalubale shiyasa na kosa ka
dawo ayi takare,Yace kalubale? Wane iri sakeena
ta?kowa zuwayake nema na,kare da doki
ma,shiyasa na gudo abjdon inyi musu nisa.Yayi
hucin zafi,ya fahimci ta shiga damuwa,kar ki
saurare su sakeena kullum ki rikakallon zoben
alkawarin mu sannan kar ki manta akwairanar
auran mu a kanki. Nauyi ne babba a kan ki
myprincess pls,kar wani kalubale yasa ki qi
saukewa,kitaimake ni dom girman Allah". Ta
kara goge hawaye,ka daina roko na doktadomin
kai ma kasan cewa ban iya rayuwa da kowaface
kai,idan kana roko na sai in ga kamar baka
yardadani bane.Da sauri ya amsa na yarda dake
sakeenakema in har kin amince da magana ta to
ki sharehawayenki ki daina kuka zuciyata ta
daina konewa. Ta share fuska tare da kokarin
tsaida hawayenta,nadaina dokta,yace good girl!
To bani labari me kikashirya a bikin mu? Tace
me zan shirya baka nan? Nikuwa kinga list din
nan anan rubuce,karanto min inji?Da farko
akwai immunization day,wasu manyamanyan
allurai ne na tanadar don amarya.....Dariyarta ta
katse shi shima ya fara dariyar,ki tsaya kiji
mana!me zan ji?Wannan shirin naka almara ce
kamasake.Na riga na gama shiri na ba zan sake
ba,yarinyaallura biyu da safe,biyu da rana,biyu
da daddare,shidakenan.Sosai ma,duk a jiki na,ah
to,sa wasa kiga aiki.Ta cigaba da dariya
hankalinsa na kara kwanciya,kokari nsa ta
manta da waccan maganarshiyasa ya dage da
bata dariya har dare ya fara nisabasu sani ba,ai
kuwa yayi nasara don ko data je takwanta bata
yi tunanin komai ba,tace labarin dayarika bata
har tayi barci mai rai da koshi ne. Kwanabiyu
cif!yau zuwanta abj kuma ko a daren yau
alameen ya kira sun sha hira tana ta kewar
bebialameen ta kwanta barci,sosai take son
ganinsashiyasa ta kwaso hotunansu ta tsibe tana
kallo hakata bata lokaci tana kallon doktan ta
sannan tasumbace shi,ta tattara hotuna ta maida
cikinjakarta,ta dawo ta kwanta ta zurawa
malami ido amma a zahiri ba shi take kallo
ba,wani tunanin candaban take yi,bata san
lokacin da barci ya sace ta ba Tsintar kanta tayi
tare da danliti bisa benci akofar shagonsa cikin
wani irin nishadi na banmamaki.Wani abu suke
ci wanda bata tantance komenen ba.Ta sanya
masa a baki ya cinye,shi ma yadauko yasa
mata?Ta sake daukowa ta kai masa bakishi ma
ya kara mika mata sai ta hade da yatsun sa ta
cije,ya rika yarfawa yana fadin,"wash! Sakeena!
Wlhda zafi! Ita kuwa dariya take yi har da kama
ciki,yakawo mata duka ta tashi da gudu ta mika
hanyargida,tana gudu tana waigensa tare dayi
masadariya.shi kuwa kwala mata kira yake mai
karfi yanaamsa kuwwa "sakeena! sakeena!!
sakeena!!! Ta yunkura ta tashi zaune dafe da
kirji tana fadin,innalillahi wa inna ilaihir rajiun!
sharkaf tayi da zufa kumatana ta numfarfashi
tamkar wacce ta sha gudunfamfalaki. Ta lalubi
fitilar tebur ta kunna ta cigaba dazare ido tana
dube dube,mamaki ya isheta tanatambayar kanta
'me ya hada ta da danliti? Barcin da bata sake
komawa ba kenan har gab da asuba alokacin ne
wani sabon barci ya dauketa,ji tayi ana
tabubbuga ta,ta bude ido a natse ta dubi mai
tashi Malami ne a tsaye yana mata dariya,gari
yawaye anti ki tashi mu yi sallah.Ta tashi da
sauri tadubi agogo karfe shida daidai,ta duro ta
fada bayi tayoalwala tayi sallah,wani abinda ke
daure mata kai shafta mance da mafarkinta,a
zahiri ta san tayi mafarkiamma ta kasa tuna
irinsa. Haka ta wuni tunani babu kuzari a jikinta
kuma ta kasa gayawa kowa. Hattaalamin da bata
iya boye masa duk wata damuwartayau ta kasa
gaya masa mafarkinta mai ban mamakiballe ya
taya ta addua.Dare yayi sosai lokacin dabarci ya
sake dauketa kamar jiya haka ta sakeganinta da
danliti. Babu bambanci da mafarkin jiya,ta farka
a firgice hankalinta ya tashi,gaba daya kanta
yayamutse tana jin muryarsa yana kiran sunanta
cikinkunnuwanta,shiya ta zuwa yatsunta,ta tashi
ta runtseido tamau!Tana fadin inna lillahi wa
inna ilaihir rajiun!Sannu a hankali ta daina jin
kiran. Ta makure a gadota rasa abinda ke mata
dadi a duniya,gab da asuba wani barcin ya sake
sace ta,yadda take zaune amakure gefen
gado.Malami ke tashinta ta bude ido tadube
shi,yace a zaune kika kwana anti? Da kyar
tatashi sosai ta zauna,wuyanta yayi mugun
rikewa,yakage,ta kasa motsa shi,tace ya aka yi
na tashizaune?Yace oho nima ynzu na tashi na
ganki a zaune. Ta jujjuya wuyanta tace,wash!
wuya na ya rikemalami ban iya motsa shi.yace in
kira momi? Tace aa kyaleta, yanxu zai warware
in na tashi,yana tsaye yana kallonta tana ta juya
wuyan har tasamu ya saki, ka yi alwala ne? Ya
ce aa . To jekayimana ka fito, ya wuce ya yayo,
ya dawo itama dashiga toilet, ta kama ruwa
tafara alwala, Sakeena! Tajian kira ta. Ta waigo
da sauri, bata ga kowa b, tayi jim, a tsaye
sannan ta ci gaba da alwala ta kare ta fito
taysallah. Wannan yinin tayi tunanin Dan Liti,
gaba 1mind dinta, ta koma fandogari. Har Anti
Amina ta lurabatab cikin sukuni. Yau da wuri Al-
Ameen ya kirawaya 8:30 ma bata gama yi b,
tana daki ta idar dasallar isha. Malami ya shigo
ya gaya mata yaya Al Ameen ya kira, takalleshi
up n down tace kace masaina zuwa.. Ya juya ya
fice, shi kansa da yake yaro,yaji mamaki , don
bai saba gani b, Da taji waya harrige rige sukeyi
wajen rcvng. Tay guntun tsaki ta tasorai bace ta
sauko falon suna ta hira da malami yanabashi
daria. Tayi tsaye, tana kallon sa, kafin yace gata.
Ya miqa mata , ta amsa ba fara'a, tace
hello.Yace Amincin Allah ya tabbata gare ki my
princess...Kai ma hak. Yau kuma yanga kike ji,
kika barni damamaki? Ko amarci ne ya fara tun
yanxu? Tayatsuna face tace " sallah na ke," Oho
yau na bugoda wuri ko? Na kosa inji ki ne my
wife.. Tayi far da eyez tace ka kyautah wa
kanka...... Banda ke? Watakila, banson gulma.
To yakike? Kalau, aa ba kalau b, kamar
sakeenata batacikin walwala, waya taba min ke?
Wa zaitabani kuwa? To ai ban saba jin ki haka b
my princess ko bakida lfyne? Lfy lau nake. Ina
shakku gaskia, karki boye minsakeena, gaya mi
meke damunki? Ta danyi shiru, hawaye suka cika
eyez dinta,murya na rawa Lnibansani ba Dr.
Kayimin pryr raina yana baci nekawai"jikinsa yay
sanyi karki damu mama in shaAllah zan miki,
kinsan Dan Adam ajjizi ne, 9 yake baicika 10 b,
dole wata rana kaji ba daidai b. Haka lyftake,so
karki damu, ok? Nagode, ki manta kawai. Kinsa
wani abu? Kishin kishin naji wai skul dinnansuna
son rike ni, kamar yaya? Wai in zauna anan
inyimasu aiki.... Banjin zan iya ko da sunyi man
tayin.Don me? Ke kingoyi baya ke nan. Baci
gaba bane? Niban ga wani abu a cikin sa b.... Ni
nagani, wayau nekawai suke mana , a haifi
mutum a kasar sa, yayi girma ya gama whlar
studyng a kasarsa, tashi 1 watakasar ta gwada
masa money ya bar kasar sa. Alhalinal umar sa
na matukar buqatar gudunmuwarsa. Ni banda
sha'awar wannan, na fi so inyiwa kasa ta bauta,
badon kudi b sakeena , sai don tai mako ga
masubukata kin gane????? Uhm.... Uhm?? Haba
sakina ta, na ce ki sakiranki, ko naji dadi, kina
so in shiga damuwa ne? Tayihamma,gaba 1 taji
slp ya rufe mata eyez, yayi yardariya ya ce,
wannan uwar hamma, ai sai ki cinye ni,barci
kike ji? Wlh kuwa gaba 1 eyez dina sun rufe,.
Aikuwa ya kamata ki kwanta kiyi slp, in kyale ki
ko? Tadan nunfasa, kuma bana son kwanciyar.
No pls kijeki kwanta, Allah na yafe, ok? Sai
2mrw zankira inAllah ya yarda, sai da 2mrw ko?
Shi ke nan. Ki fa yibarcin, kar ki tsaya tinkng
komai. Ta amsa,to. Gudgirl I lov U my prncess. A
hnkli ta ce Me too... YaceSo much? Tace So
much! Murmushin sa ya kari yace to ayi slp lfy.
To. Ta fadi tare da aje kan wayar ta jimatsaye
tana tunanin iska, ta tako ta dawo daki
9pmdaidai. Malami har yayi slp. Bata sauya
komai jikin taba ta kwnta,shirun da tayi, bawai
Al amin take tnkba , fandagori kawai take
tink,can mind dinta ta koma,tana matukar son
ganin Dan liti. Yayin da shima al amin yake
zaune bisa bed yana tinkn yanayn sakinarsa take
ayau,don hka ya roki Allah daya yaye
mataabinda ke bata mata rai. Dukkansu sun raba
darebasuyi slp b... Yau mafarkin mama ya sauya
salo,domin a yau kiran da ya kwala mata yasa ta
tsayacak,! Tana kallon sa, tafiya zakiyi ki
barni??? Ta kada Kai.. Ya ware hnds dinsa yace,
Kizo nan don Allah. 2acigaba da kallonsa bata
motsa b, kizo mana nace,! Taruntumo da gudu ta
rungume sa, ta fasa kuka, ya riqeta tamau! Yna
fadin, ko ke fa? To kidaina cryng, donbanga
dalilin yin sa ba... Ya dago fuskarta yana
sharemata hawayen, ya isa haka, ki daina bata
hawayen ki? Kuka take yi sosai, tana kwance
rashe rashe bisagadon, ta jima tana kuka kafin
ta yunkura ta tashizaune,taja jikinta,ta jingina
da akanta kan gado tacigaba da tsiyayar hawaye
ana sharewa. Bata sakekomawa barci ba har aka
kira asalatu. Ta sauka tafada bayi tayo alwala ta
bada faralo,ta zauna shiru bisa sallaya.
Zuciyarta tana azalzala mata son ganinDan
liti...... Muryar malami taji yana fadin, har
kinkinyi sallah ne anti? Shine baki tashe ni ba?
Tadanruntse ido, ta bude,yi hkri malami,na
manta ne. Je kayo alwala,. Ya wuce bayi yayi
alwala ya fito yayisallah. Yana idarwa, wanka
yaje yayo yayi shirin skul. Bisa gadonsa ya
koma ya kwnat.jim yayi shiru cankuma ya dago
kai yace anti kifa tashe ni karki manta.Tace
bazan manta ba,ya koma ya kwanta.ya
bartazaune bisa sallaya. Anti Amina ce ta
shigo,karfebakwai da rabi wai barci ne ya dauke
ku? KaiMalami!... Ta bubbuga shi,yayin da
mama tay firgigi ta bude ido, skul din fa? Ka
kwanta kana ta slp?? Yasauko a firgice yace ,
nace anti ta tashe ni fa! NAGA ALAMA BAZAKU
IYA KARANTA WANNAN BAKIN CIKIN BA, gara
kawai a samu wani book, INA jiran ra'ayin ku,
masu so a cigaba suyi COMMENTS masu son
sabon littafi suyi LIKE.

BAKIN CIKI 1***12 Tace, Ita ma aunty ai ta
bingire, dube ta aza zaune take yinsa. Ta so kayi
breakfast dadin kana jiranka. Ta juya inda Mama
ke xaune tana famanxuba mika, Yayan ki zai fita
ne, ki fito ku gaisa. Tace,Gani nan. Suka fice da
Malami, ita kuwa mama bayita shiga ta wanko
Fuska ta fito. Suna bisa tebur ta same su fuska
ba walwala, ta ja kujera ta xauna, inakwana
yaya? Yace kalau, ya lazu Doktan ki?Murmushin
bai kai ciki ba tace, ai ni ban shi ba Yaya.Yace a
Yau kuma? Zamuyi waya ai, zan gaya
masaabinda kikace. Tayi shiru Aunty amina tace,
me yasami idanuwanki? Kamar sun kumbura? Ai
ba sa min ciwo, tace, to meyasa? Da alama dai
sun kumbura.Ta murje idon. Yayanta na cewa, ke
me zai dameki?Ita da take tare da lazy Dr. Suka
fara dariya, ita kuwayake takeyi. Ta sa abincin,
sai juya masa cokalitakeyi, ta kasa ci, da alama
tana son tayi matamagana ne. Amma ta kasa,
aunty amina ta kare mata kallo, tace wai
menene? Ta dago ido ta dubeta, tadubi yayanta,
jim kafin tace, Fandagori nake sonxuwa.
Fandagori? Me zakayi? Yayan ta ya
tambaya.Idanuwan ta suka yi rau- rau! Da kwalla
tace, ina sonxuwa ne kawai. Ya xura mata ido
yace, xo nan bebi.Ta taso a hankali ta zo gaban
sa ta tsaya. Ya kamo hannnayenta biyu yace, me
zaki yi a can? Bayan yaukwanan mu bakwai da
dawowa? Tace Umma na keson gani. Ya dubi
Aunty amina, yace kinji shagwabarbanza! Ke
kadai ke da Umman nan ne wai? To ba zaiki ba
ki ba, nan zaki zauna sai karshen wata. Ta
karamurtuke fuska. Don Allah yaya kayi hkr ka
bari in tafi. Ni wlh ko a motar haya xan iya
tafiya, ba sai direbaya kaini ba. Yace, motar
haya? Baki a tunaninki bebi,banso in sake jin
wannan maganar, karshen wata inada hutu zamu
tafi tare. Is dat clear? Ya fadi tare damatse
yatsunta da karfi. Tayi tayi ta kwace amma
takasa. Ya kara girgiza ya, ya kara fadin Is dat
clear? Ta kara cunno baki ta kauda kai. Ya saki
hannun yace je ki ci abinci, ta juya da gudu ta
haye sama.Aunty amina ta kwala mata kira,
Mama! Ya dagamata hannu, a kyaleta! Iya shege
takeji kwana biyu,ko baki lura ba? Tace haka ne
fa, ni ma ban ganemata ba kwana biyu. Ya dubi
malami yace, lazy man ayi sauri mana. Yace na
gama Dadi. Mu tafi kenan?Ya ce eh. Suka bar
tebur. Madam ta kwaso masajakar sa da hularsa.
Malami ya goya, ta sa jakar suka fito tayi musu
rakiya xuwa mota. Sai da suka fita,ta dawo cikin
gida. Kai tsaye wajen mama ta nufa,tana xaune
bakin gado ta kumbura suntum! Idanuwan ta sun
kada jajur! Ta kare mata kallo, sannan taxauna
gefenta, wai Mama me yake damunki ne?
Komunyi miki laifi ne? Ta kada kai. To me zai sa
ki tashihankalinki haka? Wajen Umma nake son
inje. Ai bahana ki akayi ba, tunda yace ki bari
karshen wata kutafi, sai kiyi hakr xuwa tym din.
Tayi shiru ba tace komi ba. Ta rungumo
kafadarta, wannan abu na banimamaki, kamar
yau kika fara xuwa garin nan? Dabakinki fa kika
ce kin fasa kara kwanankin da kikacexakiki,
balle ace matsa miki akayi. Tace sai da na
zokuma naji bana son zaman. To kiyi hkr,
tundaYayanki yace ba xaki motar haya ba.
Shikenan, yauwa autan Umma. Ni bari in je inyi
wanka, in dankwanta kafin rana tayi. Tace to,
auntyn ta bar dakin takoma nata. Ta aiwatar da
duk abinda take son yidaganan tabi lfyr hafo.
Bata jima ba, ta sunkuci jakarhannu ta rataya ta
yafa mayafi ta debo takalman tarike a hannu ta
sadado ta sauko kasa. Shigar ta falon ke da
wuya, wayar Al-amen ta shigo falon, gabanta
yayanke ya fadi, ta tsaya cak! Tana zare
idanuwan.Tsoron ta Allah, tsoronta kar karar
wayar ta tashi antyamina. Saboda haka tayi
azama ta nufi wajen wayar,ta daga kan taaje
gefe, ba tare da tayi magana ba,balle ta san
waye akan layi. Ta dan kara tsayawa, jim shiru
bata jin wani motsi ba, tayi hamdala ga Allah.
Taaje takalmanta ta xura tayi waje abinta.
Babufargaban komai ta doshi gate har tana
gaida masugadi. Suka amsa tare da fadin a dawo
lfya. Taceameen. Tayi waje cikin sauri ta bar
sashin unguwar tafito a sarari a inda ta samu
shatan tashi ta kai ta tasha. Tayi muguwar sa'a
fasinja daya akejira motarta tashi xuwa Minna.
Inda daga can zata sami MotarFandagori. Sha
biyun Rana Aunty amina ta farkabarcinta, ta
sauko falon kasa, tin daga nan ta faraganin
abinda bata sa ba ba, kayan abinci na aje
bisatebur yadda ta barsu. Mama ta bata kwashe
ta gyara wurin ba. Cikin ranta take fadin, lallai
yau Mama tsiyatakeji. Haushi ya isheta ta nemi
kujera tsakar falo taxauna ta shiga kwala mata
kira. Shiru bata amsa ba.Mamaki ya isheta, t
yunkura zata tashi idanunwantasuka kai bisa
waya, Ah ji wani sabon iya shege. Sumama! Ta
nufi kan wayar ta dauka ta mayar yadda take.
Tana jan tsaki. Ta hawo saman ta fada
dakinmama cikin zafinta. Ganin babu kowa a
dakin yasatayi turus! Cikin sanyin murya take
kiranta, mama! Kokina toilet ne? Shiru? Wai
malam yaci shirwa. Tabude bayin vata ciki.
Hankalinta ya tashi ta sauko dasauri tana kiran
Mama! Har waje. Daya daga cikin masu gadin
yake gaya mata ai ta jima ta da fita.Al'amarin
ya daure mata kai. Ta dawo falo..... Tana
mamakin mama. Karar waya yadawomata da
hankalinta, ta tashi taje ta dauka, hello! Muryar
aunty Rabi taji ta amsa. Hello aunty amina,Rabi
ce, tace nagane ai ya yara? Lfya lau wlh. Waime
ya smu wayar ku ne? Al- ameen ya kirani, wai
tunsafe yake neman layin, amma yana engage.
Tace, uhm.... Ke dai bari, ina nan ina ganin abin
mamaki.Kamar yaya? Tace, Mama ce daxun da
safen tacewaYayanta ita gida zata koma, yace ta
bari karshenwata ya kaita. Nima na rarrasheta,
har fa ta amince,wai kuma na tashi barci
yanzun, bata ba dalilinta cikingidan nan. Sannan
ina zaton ita ta cire mana kan waya ta aje gefe.
Cikin al-ajabi tace, to saboda me? Oho! Kuma
ba ayi mata komai ba? Wai zai yi mataRabi? Ko
da ma anyi matan ai be kamata tayi hakanba
ko? Tace gaskiya ne ka, ah to, ita da yayanta
ne.Ni ba babu ruwan. Tace, amma ai mama bata
dawannan halin, me yasa za tafar shi yanxun?
Wlh bakiji ba duk Al-ameen ya damu, nace masa
ya barizanyi tryn inji. Tace watakila don taga
kowa na rawarjiki ne da ita, shi yasa take son ta
lallace. Zata kuwayiwa kanta sakiyar da ba ruwa,
idan ta bari yaron nanya kubce mata. Aunty Rabi
ta numfasa tace, to yanxumenene abinyi? Tace,
yayan nata zan kira Yanxun in gaya masa ta
gudu, Allah ya sawwake. To ameen. Taaje waya,
sannan ta sake dauka ta lallatsa
lambobinmaigidan na Ofis, jimawa kadan ya
dauka, ta zayyanemasa kaf, abinda ke faruwa.
Nan take haushi ya rufeshi. Ya mike cikin fushi
ya fito daga Ofis, ya fadamota bai zame ko ina
ba sai tasha, jami'an union ya samu ya bayyana
masu kamaninnta, nan take sukabashi tabbacin
ta zo tashar ta shiga motar xuwaMinna tun safe.
Ran maza ya kara baci kwarai. Yafada motar sa
yana tambayar kansa, dama mama taiya irin
iskancin nan? Lallai zasu gauraya, zatayabawa
aya zakinta... Karfe uku da rabi mota ta aje
taabakin titi, ta fito ta gangagro saitin shagon
danliti, saidai shagon a rufe yake. Babu kowa
wajen. Ta tsayatana kallon kofar shagon kafin ta
wuce, tana tafe tanawaige ko zata ga Danliti ya
dawo, amma har ta dainahango shagon. Babu
alamun kowa. Taci gaba da tafiya ranta bace na
rashin ganin Danliti, xuciyartacike da tambayoyi,
tana hasashen menenemusababbin rashin xuwan
Dan liti shago? Tun dagakofar gida yara ke
kwala ihun mama oyoyo! Shi yasaUmma ta fito
har kofar sassan dauke da mamaki bisafuskar
ta. Suna hada ido tace ke kuma dga ina haka?
Ta kwaso da sauri ta rungume ta, Umma na!
Tayisauri ta dago ta, ta xura mata ido, meya faru
ne? Mekuwa Umma? Na dawo ne kawai. Ta wuce
uwar tabiyo bayanta, bata yarda da ita ba. Cikin
falo yara sunrufeta, tace, kuyi hkr ban siyo muku
komai ba, gakudin nan kuje ku siyo biskit. Ta
dauko Naira Hamsin ta basu., duk suka watse da
murna. Har yanxunUmma kallonta takeyi, tayi
dan murmushi tace, saikallona kike yi Umma?
Tace dole in kalle ki, kin shgokamar an koro ki.
Ni bawanda ya koroni, ke nake tamafarki Umma,
nace gaskiyya ni xan dawo. To inajakar kayanki?
Tana can, kamar yaya? Yaya ne yace baxan taho
ba, ni kuma na silalo na gudo. Ta daukisalati ta
sauke, kika yi me? Kanki na lfya kuwa?Mama ki
gaya min gaskiyya dawa kuka yi fada?
Taceumma ni ina fada ne? Da wan xanyi kuwa?
Umma kiyarda da ni, wurinki nazo. Ba zan taba
yarda dake baMama har sai Yayanki ya zo naji
ta bakinsa. Kuma wlh naji akasin abinda kika
fadam sai na bata miki raifiye da zatonki, kinji
nagaya miki. Na yarda, shikenan,Ina abbana? Ya
tafi kd, tayi 'yar dariya, Allah sarki inaango da
amarya? Yau kwanan su uku da komawa.Kije ki
zubo abinci ko sai kinyi sallah? Tace bari infara
cin abincin, yunwa nakeji. Ta tashi ta shiga ta
xubo abincin ta dauko ruwa ta dawo falon ta
xauna.Bata wani ci sosai ba, saboda cikinta ya
cushe dayunwa, don ko karin safe batayi ba,
bayan ta gamatayi sallolinta tayi wanka, cikin
kayayyakinta, dakegida ta dauko tasa. Ta fito
tace zata shiga sasa tagaishe su, daga nan zata
wajen Baraka. Umma tace daga xuwanki? Ba
inda zakije sai Yayanki ya zo najidalilin
dawowarki gida. Ta ya mutsa fuska, tace
kaiUmma! Barakara kamar wata bare, kuma wlh
damada xan tafi bamu sallama ba, na wuce, hkr
zanje nabata. Tace, tazo nemanki kinbi 'yan
abuja, amma bainda zaki, kinji na gaya miki. Ta
bata rai sosai. Ta jefar da gyele bisa kujera ta
koma dakinta. Ummatace, in kinso kiyi bindiga,
ba fushi ba. Ta shige natadakin. Jimawa kadan
mama ta fito cikin sanda ta lekafalon, daga nan
tana jiyi sautin Umma tana karatunQur'ani. Tayo
sanda takalmin ta a hannu, ta daukigyalan tayi
waje. Bata shiga sassan ba, kai tsaye waje tayi,
sauri take kar wani ya ganta. Yaran natakaratu
ta gaida Malam ta fice. Ga ta nan ga ta nan
harkofan shagon Dan-liti, farin ciki ya lullubeta
da tahango shi a bude. Sai dai kash! Tana isowa
ta iskeayuba ne a cki. Tayi masa sallama, cike
da mamakiyake kallonta har ya kasa amswa,
gaba daya tsigar jikinsa ta tashi. Ya xura mata
ido kafin yace, sannuko? Me za abaki? Tace ba
komai, don Allah ko danlitina nan? Ya kara
matsowa ido waje yace, a'a bayanan. Tayi dan
shiru jim, kafin tace yayi nisa ne, eh to,kano ya
tafi siyo kaya, amma watakila xuwa anjimako
gobe ya dawo. Ta numfasa cikin rashin jin dadi,
tace, shikenan nagode. Zan dawo xuwa goben. Ya
nadan murmushi yace Allah ya kaimu. Ta wuce
ta komagida. Ayuba bai gasgankanta idonsa ba,
sai da ya fitoya bi bayanta da kallo. Ya dora
hannu bisa kai yace,na shiga uku, amma Dan liti
anyi mugun dan iska! Baikoma cikin shagon bisa
benci ya xauna yana jimami! Mama kuwa tana
tafe har tuntube tayi saboda takaicinrashin ganin
Danliti. Ta shige gida can sassan sukawunanta.
Hajiya Gaje tace, a'a saukar yaushe? Tace daxun
nazo. Lfya dai ko? Tace kalau. To yamutan
Abuja? Suna lfya, ina su Dan lami? Ko sunsami
makarantar? Tace ai kuwa makrnta ta samu,
shekaran jiya ya tafi, ana can sakkwato. Allah
yataimaka. Amin. Umma tayi sallam sassan
suka amsata dubi Mama tace, Abbanki ya dawo
yana kira, tamike tana fadin to. Hajiya tace,
ashe autan Umma andawo? Tace eh wai hankalin
ta ne ya dawo gida.Sukayi 'yar dariya, Haj. Gaje
tace, ah shagwaba! Sai da auran yazo ake kwa
xucin gida? Kina wasa neyarinya. Suka fice suna
dariya. Abban yana falo azaune, ta shigo da
fara'arta, Allah ya taimaki maimartaba! Yace zo
nan. Ta matso jiki babu kwari tazauna akasa
gefensa. Mama me ya faru kika baroAbuja ko
jakar kayanki baki dauko ba? Tayi kasa da kai
tace, Allah abba babu abinda ya faru, cewa
nayizan dawo wajen Umma, shine yaya ya hana,
ni kumana gudo. Ya xura mata ido, yace, me ya
sameki? Kina ma gani kamar ba laifi kika aikata
ba? Haka kawaiki kamo hanya ki taho ke kadai,
ba tare da saninkowa ba, idan wani abu ya faru
dake, ya kike so mutane suyi? Wannan rashin
hankali ne, irin wandaban taba sanin ki da shi
ba. Ina fatan kuma daga shiba zaki sake ba? Ina
fatan kinji da kyau? Ta kara kasa daidon tace, yi
hkr Abba Insha Allah ba zan sake. Yanumfasa
yace yanxun saboda Allah kinsan awane
halisuke? Zaki gamu da Yayanki ai, kala bazan
ce masaba, yayi miki duk abinda yayi niyya.
Umma tace ni faabin daure min kai yakeyi. Wai
mama ta gudo? Ta kuta tana zuba mata harara.
Abba yace, tunda daiAllah yasa ta ido lfya,
mungode masa, sauran magankuma sai yayanki
yazo. Idanuwanta suka kwalla tana,duban abba
tace, Allah abba bada gangan nayi ba,kullum
mafarkin gida nakeyi, shine nace ni dai zandawo
in ganku. Yace, to kin ganmu ko shi kenan?
Tace ka gaya wa yaya idan yazo kar yace zai
bigeni.Umma ta karbe, ai ko shi bai ce ba, ni
zan sashi.Kuma tunda abin naki ya zama tsiya
anan din zaki tazama, na ga inda zaki samu ki
dauki wayar. Karyartsiya kikeyi! Ta turo baki tayi
shiru. Abba kuwa 'yardariya yayi yace, dama
kinyi shiru da bakini, da kanta zaki ji tana
neman hanyar komawa. Ba kuma zatanba,
yauwa! Ki ma sani. Ta shiga murza ido ko
alamarbacin rai bata ji ba, tayi shiru tana
sauraren suna tazazzaga mata tsiya. Ita bama
wannan ce matsalartaba, kusan ma da za'ace ba
zata koma din ba, ita adadinta. Damuwar ta
daya, tayi tozali da Danliti ko hankalinta ya
kwanta. Domin ko a daren yau ma takuma yin
mafarkinsa irin na jiya. Ya kira ta amsakiransa
har taje gunsa. Da wannan azalzalar songanin
Danlitin ta wayi gari. Allah-Allah takeyi, abba
yabar gidan, ta sulale taje ta duba ya dawo.
Kafin lokcinfitar sa tayi har tayo wanka ta chaba
ado. Yayan kuwa sammako ya bugo mata, karfe
tara dai-dai yanaparkin kafar gidan. Ya bude ya
but, ya kwasokayanta, da ganin yaddayake ya
wurgo jakar kasa zaitabbatar da afusace yake
kalla ya iso wajen dasurinsa yana masa sannu
da xuwa, ya amsa, kalla yakwashe kayan ya
shige da su cikin gida. Yaya abdulqadeer ya biyo
bayansa, sallamar sa hade takeda kwala wa
mama kira, Ina bebi? Abba da Ummasuka fito
falon. Yaya Babba sammako kayo haka?Abba ya
tambaya, yace ina fatan Bebi nan na. Yace ,ta
iso tun jiya, zauna mana! Yace ina take
tukunna?Umma tace tana dakinta tana jinka. Ya
wuce dakin abba ya bishi. Mama na makure
karshen gado, kaitsaye ita ya dosa, kafarsa daya
ya dora bisa gadonya mika hannu zai janyota.
Abba ya riko shi yanafadin, yi hkr Yaya babba ka
dubeni ka saurareni. Yadubi abba ransa bace
yace, abba yarinyar nan tana dahankali kuwa?
Ban iya barci ba fa saboda bacin ran abin da
tayi min jiya! Tana nufin tayi girman da ba zaa
gayamata taji ba? Saboda muna wasa da ita?
AbbayaCe, Allah ya huci zuciyar Soja. Zauna
kaji, zaunanace ko? Ya zauna yana kallonta
xuciyarsa natafasa. Umma tace, wlh da ka kyale
shi ya tattabajikinta ko hankalinta ya zl jikinta.
Abba yace ya dai karya ta kike so, kinsan irin
dukan da zai yi mata?Yadda ya hassalo din nan?
Ya juya kan Yaya yacigaba. Dubani nan Babban
Yaya, kayi hkr don girmanAllah, ni kaina na san
Mama bata kyauta ba, kumatun jiya na nuna
mata kuskuranta. Ni tunani na ma kowani abu ne
ya faru tsakaninta da maidakinka. Kayi hrk
babban Yaya da yardar Allah ba zata sake
ba.Idan kuwa har ta sake, duk hukuncin da ka
yankemata kayi daidai. Ke kuma bashi hkr,
maras kunyakawai. Tuni hwaye ke ta kwaranya
bisa kuncinta,murya na rawa tace kayi hkr yaya
don Allah. Ya ballomata harara yace, ga
komatsanki can na kwaso miki, idan na sake
ganin kafar ki cikin gida na, sai na karyaki.
Kuma daga yau mun bata, kar sake min magana!
Abba,Yace Allah ya huci xuciyar Soja, ai ba
zatasake ba. Ta ma sake! Ta rarrafo da sauri, ta
rungumebayansa, Allah yaya bazan sake ba kayi
hkr. Abbayace, Allah sarki tsaknin babban Yayya
da bebinsa, ai ba ajin kansu. Ko? Zuciyarsa ta
fara sauka, sannua hankali ya huce, ya jawo ta
gefensa ya zura mataido, ban sanki da rashin ji
haka ba Bebi na, sabodahaka kar ki kara idan ba
ki so mu bata. Ina fatan kinjini? Kwallan ta suka
wuce da gude, tace Allah ba zansake ba Yaya.
Ya share mata hwayen, ya wuce, shikenan, ki
zauna wajen Umma, shi kuma lazy Dr.Din me
zan gaya masa? Tun jiya yake damun mu.Tace ai
zan dawo. Haka xan gaya masa? Ta amsa daka,
yace an gama. Ya dubi Abba yacigaba,
munshirya abba, Umma ki yi hkr idan ta kara
guard roomxan sata. Tace yayi kyau. Abba yace,
Allah ya so ki 'yar nema, da kin jigata. Suka
fara dariya, yace dukda haka sai na dan tabata.
Ya duma mata dundutsakar baya, ta fasa kukan
shagwaba, tana susarbaya. Ya mike yana dariyan
mugunta, yayin da takefadin wayyo Allahna. Ka
dai jibgeta da wayau, injiAbba, yace ladan
sammakon da nayi, ta hana min xuwa ofis. Suka
koma falo suka gaisa. Karin safekawai yayi a
gurguje ya shiga sauran sassan ya
gaidakawunansa, ya fito ya sake dibar hanya.
Yau maAbba kd ya sake tafiya bin wata kwangila
da yakenema. Bayan sun gama ayyukan gidan.
Ummakwanciya tayi, ba dadewa barci ya
kwasheta. Nan da nan Mama ta kwashi takalma
da gyale tai waje ta nufishagon danliti, amma
kash! Ayuba ta sake samu.Dan liti bai dawo ba
kamar zatayi kuka, ta tsayadauke da tagumi.....
Ayuba yace, karki damu xuwaanjima, ninasan
bazai wuce yau ba. Tanumfasa muryasanyayetac
e, zanzo anjiman, Allah ya sayadawo
lokacin.Yace, amin ta juya ta fito ta danjima a
tsaye batasan abinda ke mata dadi ba.Salalau-
salalau ta komagida, ta fada dakinta, ta
kwantaranta na mata daci kamar tayitsuntsuwa
tabi shi kanon. Ta juyanan, tajuya can duk inda
ya jefa idonta,shi take gani yamiko hannayensa
yana murmushi.Yana fadin zomana! Jikin ta
gaba daya ya hauciwo, zazzabi naneman rufeta.
Har cikinkasusuwanta take jin ciwontamkar mai
sanyin kashi. Karfehudu bayan tayi sallar
la'arsar tasake sabon wanka ta sauya
kayatacewaUmma zata wajen Baraka.
Ummabatayi musu ba,saboda sun warware
matsalaryayanta. Cike da farinciki ta bar gidan
kuma xuciyarta najaddada matatabas taga
Danliti. Wayyo Allah! Ranta ne kawai kesaka
mata haka, saboda ta zaku tagashi, ayuba, ne
cikin shagon ahain yanxun kam ya rasa kalmar
dazai gaya mata. Ta zura masa ido,tace, kodai
guduyakeyi idan ya hango? Ya kada kaiyace, wlh
baidawo ba ne Mama. Ashe kasansuna na nan?
Yayidan murmushi yace, haba kamarwani bako a
garin?Asalin sunanki sakeena, ko banfada daidai
ba? Fuska sake taamsa, haka yake, amma
abokin kayacika yawo, dama haya yakedadewa.
Yace, kin sansha'anin kasuwa, watakila ma
bakano kadi ya tsayaba. A fada nan ne, a fada
can ananeman halali. Tacegaskiyya ne. Barin in
tsallakawajen kawata, may bekafin in fito. Allah
ya taimakeni yadawo. Yace, Allah yasa. Kin
damuda yawa, neman me kike masa ne?Ta gyara
tsayuwa tace, a'a tsakanida shi ne, so kake
kaji? Ya kada kai yana 'yardariya yace, wane
niinji sirrin ku? Sai dai in ce Allah yadawo miki
da shilfya. Tace amin, barin in je indawo. To
shikenan. Tabar wajen ta tsallaka titi.
Al'amrinkara daurewa Ayua kai yakeyi, yama
rasa yadda zai fassara shi.Kamardaga sama
wata mota (ToyotaCarina) tayi fakin akofar
shagon, me ayuba zai gani?Mutumin na sa nea
ckinta. Yayi azama ya fito dashgo, yayin da shi
maDan liti? Yace, siyo ta nayi. Motar?Ya
tambayadauke da mamaki. Yace, eh mana.Ya
bashi hannu suka tafa, ka tsulana tsiya mutumin
na a bayankasa, ya akayi? Yace yadda
akayikenan? Kasan itamota akwai kara aji, shi
yasa nashiyo, kada yarinyarnan ta dauke ni wani
gara. Yacekai! Don Ubanka dalabari, shigo dai
daga ciki! Yayi dangutun tsaki, tanata xuwa
nemana nakoa? Ya sakibaki ya na son kallonsa,
ka ma sanikenan? Ahaf! Kana wasa danine.... Ya
wuce ya bude but, yasake juyo wa ya kalleshi,
ka na nan tsaye? Ga kaya kazoka taya ni
cirewamana. Ya tako a hankali ya tsayagabansa,
kana bantsoro Danliti. Wlh kabi a hankaliMalam
mu kwashikaya in ka na kwasa! Mts.. Ya jatsaki
ya shigo fito da kaya yanashigewa da su shago.
Ayuba natayashi har suka kwashe. Tsakar
shagonya baza 'yartabarma ya zauna. Ayuba na
bisakujera, kofin ruwaguda ya shanye, ya aje
kofinsannan ya dubi Ayuba,duk kayi wani
la'asar, kai banza newlh, yace ai doleabin nake
da ban tsoro. Tsoro?Tsoron me xanji? In gaya
makayadda kasan Tv haka ake nuna
minitaakofar shagon nan. Sakeena a tafinhannu
na take,sai yadda naga dama da ita. Yacigaba
da kada kofardamarsa. Ayuba yace, xan
bakashawara mutumi na,tunda ka nace, ka
matsa sai da kabirkita hankalinyarinyar nan, kuyi
aure kawai kahuta da kwashe- kwashe.
Sakeenakarshe ce wajen kyau, ni ban mataba
sanin haka ta hadu ba, sai danatsu anan
tanamin magana. Kaga idanuwan takamar
madara!Mts.... Ya dan kada kai. Yaci
gaba,yarinyar nan inaiya ma cewa idan ka aure
ka hutamutumi nan. Adage yake kallon sa
tsawon lokacinkafin yace, aure? Wa zai aureta?
Kana hauka ne? Idan na aure ta,insiyo mata
kima? Yadda tageni,haka kowa sai yazage ta a
garin nan. A'a danliti! Karika sayan tsoronAllah
a ranka... Ya daga masahannu, ya isa
hakaAyuba! Naga alama kai ma sai nasaan
daure minbakinka, kar kaje kana min
shegensurutu a gari. Domin daddawa bazata
gayawa manda baki ba. Saidai ni bana zurfi
shige-shige irinnaka. Shi yasa nakeba ka
shawara ka aureta. Malamba ruwanka! Ni
banshakkar Uban kowa, irin ta irin tamasu taurin
kai biyuna baro da ciki a garinsu. Daya akano,
daya a zariya.Zaman da nayi a can kafin in
dawonan. Ido waje yace, iye! Kwarai!Me zai
danne ni? Kila ma yanxuduk sun haihu, wa ya
sani? Ayubaya kara la'asaryana kallon yadda
yake kadakafarsa, ko ajikinsa.Wata 'yar fulani ta
leko tana fadin,hannun ku dai! Adama fura? Dan
liti yace, dama tahamsin. Ta sauketa shiga
damun fura. Dan liti yafito ya zauna bisa benci
yana hirada 'yar fulani ya bar Ayuba.
AwadayaMama tayi a daddafe wajenBaraka, duk
hankalin tayana can tunanin ko Danliti ya iso?
Suka fito tare zasu wuce Baraka tace, Yau ba
zakishiga wajenkishiyar taki bane? Ta ya
mutsafuska, tace, kullumnazo sai na shiga
wajenta? TaceHala Dokta yayi laifi ne, ni nagako
maganarsa baki min ba. Tace ninadaina yayinsa.
Tayi 'yar dariya tacemama kenan.Ashe Dr, zaiyi
laifi har adainayayinsa? Dakata, kina nufin kin
warwareranar da akasanya miki? Tabbas haka
ne,domin hankali na ya fikwanciya da kai.Yayi
wani saurayinmurmushi cikinnishadi, nagode
sakeena, kin cetorayuwa ta, ban sanirin godiyar
da xan miki ba. Dadiya rufe ta, ta rausayakai,
nima na gode, kin gode? Menayi na godiya? Dole
ka godewa wame sonka. Ya kara jingina da
motayaxura mata ido, kamar na sace kisakeena,
kalaman kina gigitani, gashi banzo miki dakomai
ba, balle inbaki tukwici. Ta kada kai
tanamurmushi, ban sankomai naka. Ba kiso nake
na, al bahaka bane nufiba, so na gaskiyya baya
bukatarkudi. Allah ko? Eh mana. Kin
finigaskiyya. Amma duk da hakayakamata ace
na zo miki da waniabu, hausawasunce yaba
kyauta tukuici. Kar ki jikomai kyauta saikin ture
sakeena, tunda kika zabeni. Tace gaba
damurmushi tana fadin, to Allahyasa. Awa daya
da rabisuna tare, sannan sukayi sallama,ya
wuce, ta shigo cikin gidan.Umma na kwance bisa
doguwarkujera afalon, ta shigo simi-simi
zatawucem umma tace zonan Mama! Ta dawo
gunta zaunabisa kafet. Ummata tashi zaune ta
dube ta tsaff!Kafin tace, ke da akece kije ki gaya
masa an sanya mikirana, me ya kaikidadewa. Ta
sunkuyar da kai, batatanka ba, ban gane miki ba
Mama,kina so a zage mu a garin nan ne? Bikinki
fah saura wata uku ko kinmanta ne? To muba
kananan mutane bane, ko kingaya msa ko
bakigaya masa ba, ba zaki kara fita ba! Kinji na
gayamiki! Ba zaki kawo mana sakarciba, dan na
lura taketaken ki kenan. Idan kuma ba hakaba,
abbanki zai maida ki minna koabuja, tashi ki ban
wuri! Ta mikeda kyar fuska kumbure, ta
wucedaki. Umma ta bitada kallo ganin yanayim
fuskarta yasa ta kama bakicike da mamaki. Ta
jima zaunesannan ta tashi tarufe ko ina ta kashe
fitulu ta samiabba a daki. Waikasan yarinyar nan
sai yanxun tashigo? Ni fah ban gane
sauyinyanayin ta ba, ina mata fada tanabatarai,
yace ai na leka ta falon bakina hango su
sunawasu dararraku, ni ban ganewanene ba,
amma yayishigarsa tsaf harda motarsa. Kajiba?
Allah ya sagobe da kanka zaka fita ka
bashilabarinta. Ai kamarkin shiga raina,
kwanciyar nan danayi abinda nake ta tunani
kenan,karta hadu da romon baka, yajikirtatunani
nta. Ya kamata ka hanzartayin wani abu.
Yazama dole kar girma na ya fadi.Haka suka
kwan daabin cikin xukatansu. Ita kuwaMama ba
nantunaninta yake ba, hankalintakwance tayi
barci cikinshaukin son dan Liti. Da safe Abbaya
xaunar da ita yayi matanasihohi tare da jan
hankali, akankuskuranda take neman aikatawa.
Har yayi,ya gama batacekala ba. Abinda bai sani
ba, shinebabu kalma dayada ta shga kanta,
domin kuwa tananan akan bakanta,duk ta inda
za'a bullo mata. Danliti ne, ba sauyi.Bayan sun
gama ayyunkan su, tayiwanka Umma tayi barci
ta sadadata fice kamar jiya. A shago ta
samiDanliti, koda ganinta, sai yai tsayea kofa,
bakinsahar kunne ya mike, ah! Sanyinraina
kamar kinsantsundum nake cikin tunaninki.
Tatsaya rungume dahannaye ta zuba masa ido.
Tace,hum! Haka naji.Baki yarda ba kenan? Dubi
lissafinda nakeyi dole na aje shi don
banafahimta. Tayi dan murmushi, to yaka
kwana? Ya amsa barcin nan baiyidadi
basakeena, ko'ina najefa ido ke nakegani, kamar
zanzautu nake gaya miki. Tayi dariyafasa min
kai. Saiga Ayuba ya shigo, manya manyainji
kanana! Tadubi Danliti tace, ka yarda mugaisa?
Ku gaisa sanyin raina badamuwa. Ayuba ya saki
baki au saima kayarda zamu gaisa? To matar
kace?Ya kada kai,wane ni? Tafara dariya tana
fadinkadai ina kwana?Yace baxan amsa ba. Dan
liti yaceto idan bazakaamsa ba, ka fita ka bamu
guri,yace ai ko baka ce ba.Ya juya ya fice mama
na dariya,tace wlh baka da dama korarsa
makayi? Ah to yadawo ne? Ta kadakai a'a, yace
to shigo daga cikimana kya ta tsayuwaanan, tace
wlh karka damu datsayuwata. Yadan batarai me
yasa? Tace dan Allah karkabata ranka, yasaki
fuska nima na hkr banso natakura ki. Ammadole
kici wani cikin shagon nan,me xan miko miki?
Ta kada kaidon girman Allah ka barshi.
Yaceanan nezamuyi fada idan har baki sa
minalbarka ba. Me zanbaki? Ta sa hannu cikin
wani katontire ya dauki mintguda daya tace, na
dauka Allah yakawo kasuwa. Yazura mata ido
kawai, bai ce kalaba. Tayi murmushi tabare mint
din ta ajefa baki, kaganinama sha. Yace yanxun
duk girmanshagon nan ki rasa abinda zakidauka,
sai banzan sweet. Ta rufebaki tana dariyakafin
tace, baka gane manufa ta bakenan. Na
daukisweet ne saboda mahimmancinkalmar, kai
sweetheart dina ne, dole in sweet ashagonka.
Yayi 'yardariya yace, shagon mu zakice.
Toshagon mu. Yauwa yanxu najimagana. To ki
kara sweet dinmana, tunda ita kika fiso, zan
karabari sai zan tafi.Yace nabari sakeena ta. Sun
jimasuna hira, sai datakin taci tashin mama
daga barci,sannan tace masazata koma gida. Ya
dauki leda yacika mata da kayanzaki, ya bata.
Ta sa hannu ta amsatana ta xuba godiya. Ya
dago kantaya fito, barin in dan taka miki.Tace ka
barwa shagon wa? Bayanka kori Ayuba? Aiko
bakin kwata na rakaki ko? Ta fito waje tana
dariya, kawai saiga Barakata tsallako titi. Ido
sukayi da junabakinta har kunne,ta bar Dan liti
tsaye tayi gunta,kawata! Ta tsaya tanamata
duban da yafi gaban mamaki? Tace ban ganeba?
Kamar yaya? Daga shagonDanliti naga kin
fito,eh menene? A tunani na kodasiyayya ce,
ajinki ya wuce ki yi ta ashagon Danliti. Amma
sai nagakamarkun fito tare kina dariya. Ko
idonane? Tace kemuguwar 'yar sa ido ce wlh,
bamaganar sa ido bane,wai da gaske daga
shagon kika fito?Daga can nake.Amma dai
siyayya kikayi? Barakake kika haifeni ne?
Wannan irin tambayoyi, me yadame kine? Ta
fizge ledarhannunta, ta duba idan sweet kikeso
ai gara kitsallaka shagon Okundiri ki siya, yafiye
miki mutunci.Arnan? A waje na Okundiri ya
fiDanliti mutunci. Tagyara fuska tace, ni kuma
wajenabai fishi ba. Fadazamuyi Mama? Yaushe
kika faragood time daDanliti? Ban sani ba, ta
nuna tace,kina nufin yayi nasara kanki?
Baikamata ba, domin a iya sanina, bayaudara Dr.
Kike ba. Yaushe kikacanza? Ban sani baBaraka.
Haba mama, ai ko laifi Dr.Yayi miki bagirmanki
bane ki huce haushinkiwajen Danliti. Kigayawa
manya mana ayi masafada. To Ummamtsw.....
Ta fige ledar ta, ta dawotana kara zuba tsaki.
Baraka kuwatsaki tayi musamman da tagaMama
ta sake komawa wajen Danliti. Allah kadaiyasan
me sukace. Ta dai ga Mamata wuce, tanadariya.
Gabanta ya kara faduwa, tadafe kirji
tanaInnalillahi wa Inna ilaihi raju'un!Wlh sai
Umma tajimaganar nan...... KARSHE SAI MUN
HADU A NA BIYU
So Ko Kauna?
Go to Home
BAKIN CIKI (TRUE LIFE STORY) 2***1 Ta wuce
inda aka aiketa kamar zata tashi sama sbda
saurin ta dawo gida.Ta zube wa inna cefane,ko
zama bata yi ba ta fara fadin "inna mama na
cikin hankalinta kuwa? Tace,me tayi? "Kin san
danliti ya dawo....""Danliti?" Waye shi? Dan
gidan buzu mai shayi fa inna."Oho ,ina jin ki me
yayi? Lokacin da aka yi bikin yaya Abdulrahman
danliti yaga mama ya nuna yana son ta wlh a
lokacin ko kallonsa bata yi amma ban san yadda
aka yi ya shawo kanta ba,ynzun nan na gamu da
ita Ta fito shagonsa leda cike da kayan sweet."
Inna ta dafe kirji ido waje,mama fa kika ce? Wlh
inna ni kaina mamaki ya kusa kashe ni.Danliti
dan iska!"Inna tace,mun shiga uku ni saude wai!
Ban ga ta zama ba dole in bincika na tabbata
gidansu ba'a sa ni ba! Kai mama kamar mai
hankali,me zai tsone mata ido a wajen yaron
nan?Kai Allah ka shirya mana yara.Bari babanki
ya shigo Insha Allahu yau din nan za ni gidan
gara a yiwa tufkar hanci,kar ya kai mu ya baro!"
Ya kamata inna,ni ina ganin ma kamar fada
suka yi da Al-ameen don tun dawowar ta bata so
ayi maganar sa."To ba sai ta fadi ba,ko yayyinta
sun isa su kira shi su sasanta su balle ga
iyayensa a gari."Ni ma dai hakan na gaya mata.
Tace min babu ruwa na" "ita mama din ta fadi
hakan? "Ko yanzu ta maimaita min kiris ya rage
mu yi fada a titi,inna ta kuta,ta numfasa,kai
jama'a yara halin su sai su,Ita fa ta kawo shi ba
dole aka yi mata ba?Ta zabga tagumi bakin tana
maimaita salatin Manzo,Da azahar mahaifin
baraka ya shigo gida,inna saude ta maida masa
halin da ake ciki.Nan da nan ya bata umarnin
taje ta bincika,ai bata bata lokaci ba,cikin
tsakar ranar nan ta kama hanya ta nufi gidan
uban dawaki.Umma na daki tare da abban shi
ma shigowarsa kenan gidan aka gabatar masa
da abincin sa yana ci.-Inna ta shiga suka gaisa
sannan suka koma dakin umman.Bayan sun
gaisa da en hirarrakin zumunci kafin
tace.magana ce tafe dani yaya amma ki duba ko
alhaji ya gama cin abincinsa zan so in fade ta a
gabansa."Nan take jikinta ya mutu,tace me ya
faru saude?"To magana ce data shafi mama na
rashin jindadi shiayasa nace ba zan bari ta
kwana ba dole in zo in bincika,sai dai alhaji shi
yafi dacewa ya sani,tunda nayi sa'a yana
nan.Tayi dan tagumi......Subhanalillahi!Bari in yi
masa magana.Ta mike jiki a salube ta shiga
dakin abba ta iske ya kammala tace,wai magana
ce tafe da saude idan ka gama ka taso muje,To
muje gani nan".Ta gyara zama ta maida musu
abinda baraka ta gaya mata umma ta shiga tafa
hannu,abba kuwa sai daya mike."Kar dai ace shi
ne yazo jiya da daddare?Lallai biri yayi kama da
mutum,ina maman take? Umma ta dube shi ido
taf da kwalla,tana daki. Kira min ita!Ta mike ta
fita,har suka dawo tare babu wanda ya tanka
sbda tsabar mutuwar jinin jikinta,a darare ta
karaso dakin tana fadin,inna sannu da zuwa."Ta
zuba mata ido,ke ma sannu."Ta gaishe da abba
da umma na mata kallon mamaki,ta dube shi
suka hada ido,tace abba ga-ni" yace,wanene
yazo gun ki jiya?Ta sunkuyar da kai,tayi
shiru,ya daka mata tsawa,ko baki ji ne?Nace
waya zo gun ki jiya? Tana rawar lebe tace dan-
liti?"Kin kuwa san ko waye danliti a garin nan?
Tayi shiru,mama ni kike so ki mayar tsohon
bnza,ki tozarta?jiya me na gaya miki?To ni ba
hayaniya na kira ki mu yi ba domin a iya sani na
ke mai hankali ce,kin san abinda ya dace,kin fi
kowa sanin cewa saura 'yan watanni suka rage
bikin ki.Sannan idan kika nutsu kika yi tunani ba
mutuncin mu bane daga ke har mu ace an gan
ki,kina karakaina a shagon wani ma,balle danliti
sbda haka nake umurtar ki daga rana mai kamar
ta yau,bana son in sake jin wani labari
makamancin wannan!Ina fatan kin fahimce ni?Ta
kara sunkuyar da kai yayin da idanuwanta suka
fara tsiyayar ruwan hawaye,umma ta muskuta ta
karbe "kin bani mamaki ba kadan ba mama,wai
ma in tambaye ki,me kike nufi da bin sa har
shagonsa? Shiru babu amasa,umma ta
cigaba,wannan katon sakarci da me yayi kama?
A zaton ki abin birgewa ne yadda 'yan mata ke
tsayuwa kofar shagon samari suna amsar abin
hannun su?Ban taba zaton hakan zai fito daga
gareki ba mama kuma mun saurara miki ne
kawai sbda wannan shine karo na farko da irin
haka ta faru!" Inna tace,kin ga gidan nan da
dukkan jama'ar gidan dake cikin sa ana ganin
girma da mutuncin su musamman mahaifnki,don
girman Allah kar ki bari wani ya rusa wannan
ginin,ya hure miki kunne ya kai ki ya baro,kin ji
mam? Ta goge kwalla bata ce uffan ba,abba
yace,to mun ci mun rufe anan bana son ki sake
aikata wani abinda zai sa ayi miki zama irin
wannan,kin ji ni? Ta amsa da kai tana goge
kwalla.umma tace tashi maza muje ki dauko min
ledar kayan da aka ce ya baki,a iya sani na dai
baki da yunwar su,maza tashi muje!Ta mike da
kyar umma ta tasa ta suka je dakin ta dauko
ledar.Umma ta fizge cikin zafi tace,Allah yasa in
sake gani ko ji sai kin sha mamaki!" Ta fice ta
bar dakin,ta bar mama cikin tashin hankalin da
bata taba jin irinsa ba,har inna ta gama zamanta
ta bar gidan mama na aikin kuka a daki domin
dai tamkar sun kara debo soyayyar danliti ne sun
kara antayawa cikin zuciyarta.Ita wannan ranar
da suke kwakwazon an sanya mata ta jima da
manta saurayin ma balle ranar,ba shi a idon ta
ko birnin zuciyarta.Al'amarin ya daurewa
iyayenta kai,shin wai me mama take nufi da
kukan ta? Tambayar zukatan su kawai suke yi
amma basu da tabbacin amsa.Karfe takwas da
rabi cif! Lokaci ne da motar danliti ke fakin a
kofar gidan uban dawaki,kai tsaya ya aiko yaro
a kira masa mama,abba na nan a falo yana
gadin zuwansa don haka yace da yaron yaje yace
tana zuwa. Umma ta fito masa da kullin ledar
kayan kwalamar da ya ba mama Abba ya karba
ya bi bayan yaro kamar jiya,yau ma yana harde
jikin motarsa yana kada mukullai sai dai yau
kananan kaya ke jikinsa,gaba daya ya firgita
kofar gidan da kamshin turare.Yana hango uban
dawaki tilasa ya gyara tsayuwa yana 'yan kame
kamen gulma ko kafin ya karaso ya tsugunna
yana fadin,sannu alhaji,yace yauwa sannu,ya
sake fadin ina wuni? Lafiya kalau,mike abin
ka,magana zamu yi,ya mike a hankali yana
sunkuyar da kai kamar muminin gaske.Abba
yace magana guda daya ce nake so zan gaya
maka danliti,'ya ta sakeena na riga nayi mata
miji,tuni aka sa musu rana har ma lokacin ya
kusan zuwa da yardar Allah sbda haka ina rokon
ka da girman Allah kayi hakuri ka nemi
wata,daga yau kar ka sake zuwa gun mama don
tana da miji,ina fatan ka ji ni? Ya dan yi shiru
jim kafin yace naji alhaji amma nima ina roqon
arziki ka bar ni in rinka zuwa muna gaisawa,tnda
ba'a daura ba.Wlh..."Abba ya katse shi,ba zai
yiwu ba danliti domin koda babu alkawarin wani
akan mama kai kanka ka sani zai yi wuya ka
sami auranta,sanin kanka ne kaf garin nan babu
wanda ya san tushenka,kaje kayi tunani
mana.Ya saki baki yana kallon abba ran sa a
bace,abba ya mika masa keda yace ungo
nan,yasa hannu ya karba kafin ya cigaba da
fadin,abubuwan daka bata ne dazu tunda ba
auranka zata yi ba bai kamata ta amshi kayan
ka ba.Don Allah kayi hakuri ka nemi daidai
kai,sai da safe.Ya juya ya shige gida abinsa ya
bar danliti a tsaye. )Ya kara harde kafafuwansa
yana irin murmushin mugunta,sannan yace ko
banzo ba ita zata zo wajena,koda kuwa kasheta
zaku yi ta dawo.Dama ai zuwan nawa na hure
kunne ne ba wai neman nake da gaske ba."Yayi
er budurwar dariya ya bude motar sa ya shiga ya
sake fadin,sai ni dan gidan buzu mai shayi taba
ni kaga tsiya da bala'I!Ya ba mota wuta yaja ya
bar harabar gidan hankalinsa kwance.Sabanin
mama da take ji kamar ta saci jiki cikin daren
nan taje wajen danliti shiyasa tayi ta leken
falo,amma kash!Abba da umma sun ki tashi har
dare yayi sosai suna tattauna zancenta.Daren
nan bata yi barcin kirki ba sbda bakin cikin an
hana ta fita ganin danliti.Gari ya waye ko alama
umma ta ki sakar mata fuska,sam abin bai
dameta ba Allah- Allah take yi kowa ya kama
gabansa,itama ta samu ta sulale,ai kuwa abba
na fita karfe goma umma ta gama abnda take
yi,ta dare gado kamar yadda ta saba barcin
safe,mama ta gama caba kwalliyarta ta sadada
ta bar gidan.Ta kwarara sallama kofar shagon
danliti,ya taso cike da fara'a yana amsawa kafin
yace,a zatona ke ma zaki juya min baya ne,har
na fara shiga damuwa,jiya sam ban yi barci
ba.Ta dube shi cike da tausayi tace nima haka
danliti ko gyangyadi ban runtsa ba,me zai sa na
juya maka baya alhalin na san cewa nima zan
cutu? Ya zura mata ido a marairece yace,abbanki
ya nuna baya so na ban san yadda zanyi da
rayuwata ba sakeena,kar ki bari ciwon zuciya ya
kama ni.Kwalla suka taru cikin idanuwanta tace
ka daina fadar wannan maganar don Allah,in ka
ga na rabu da kai to sai dai su kashe ni in daina
numfashi,zuciya ta kai take so kuma bana
ra'ayin auran kowa face kai." Kwalla suka zubo
bisa kuncinta.Da sauri ya tauko sabuwar t鐭泂hu
kware ta ya yago ya miko mata,"share
hawayenki, ki daina kuka.Na yarda dake
sakeena,amma mece ce mafitar mu? Ta dan
kada kai tace, "zanyi tunani,ka ban dan lokaci
kadan,zan samo mana mafita.'ya daga kanta ya
fito ya gyara zaman benci.Yace zauna kiji Ta
zauna gefe shi ma ya zauna ya fuskanceta sosai
yace,me zai hana ba zaki gaya musu ni kike so
ynzu ba?Ta daga ido ta dube shi,jim,amma ba
tace komai ba,yace "kar kiji tsoron komai kai
tsaye ki gaya musu ke kin sauya ra'ayi ni kike
so,za'a yi miki tilas ne?Dole a baki wanda kike
so,don babu wanda zai zauna miki da shi,idan
kuma kina son in rasa raina ne shikke
nan........Ta kada kai tace,"nace ka daina fadar
rasa rai danliti idan ka mutu nima mutuwar zan
yi.Ka kwantar da hankalinka insha Allahu a yau
zan gaya musu na sami sauyi wanda hankalina
yafi kwanciya."Ya dafe kirji,ya lumshe ido
yace,kin sa naji sanyi cikin raina sakeena.Ya
bude ido ya bi ta da kallo ya cigaba,idan kika yi
min haka kin gama min komai sarauniya ta,ba
zan cika baki ba sai mun yi aure zaki ga tsantsar
son da nake miki,bana jin akwai wata 'ya mace a
fadin duniyar nana da zata sami irin gatan da
zan nuna miki." Tayi dan murmushi tace,Allah ya
nuna mana,yace amin.Ya dan gyara zama ya
sake gadin,"wai sakeena kin san cewa kin fi
kowa kyau a duniyar nan?Ta saki baki,ido waje
tace,duk duniya? Wlh duk duniya babu mace mai
kyau irin naki,ta kada kai tana murmushi
tace,"ka daina fasa min kai danliti,ni na san ban
kai ka ba,ya washe baki ya nuna kansa ya9e "ni
kuma? A'a ni dai kike son ki fasawa kan,ina ni
ina ke? kin gan ki kuwa?kin ga wannan dan
bakin naki dagwas ba karamin kashe min jiki
yake ba."Ta sunkuyar da kai tana 'yar dariya ya
bita da kallo yana shafo habarsa."Mama!"
Muryar kawai taji anyi mata wani gigitaccen
kira,gaba dayan su suka kalli mai magana,ta bi
shi da kallo babu tsoro ko wata fargaba tace,ah!
yaya ali! saukar yaushe?"Ya kara tsuke
fusk,yace me kike yi anan?"Tace me kuwa?Ba
komai,taso muje gida,kaje ina zuwa,"ina wasa
dake ne? nace ki taso mu wuce." "Ta dubi danliti
suka hada ido yace,tashi ku tafi sai wani lokaci
ko?Ta dan numfasa ta mike ta wuce,yaya alin
dake tsaye,ya bi ta da sauri ya
sameta,"mama,wai mafarki nake yi ko kuwa
gaske ne?Ta yamutsa fuska "da aka yi me?"
Zaune na gan ki kofar shago kina hira da
wani...." 'Wani? Ba ka ma san danliti ba?"Shut
up don Allah!waye danliti kike gaya min magana
ba dadin ji?Hauka kika yi?Ina mutunci ga'ya
mace tana hira da maza a kofar shago gaban
jama'a? Ban san ki da wannan ba,yaushe kika
canza mama? Ta ballo masa harara ta ja dogon
tsaki ta kwahsi sauri ta wuce shi,shi ma ya biyo
ta yana fadin,ban gane nufin ki ba?"Ta juyo ta
dube shi tace,wai menene yaya ali?"Shi kike
so?" 'Ai kaji,menene na sake tambaya? ya kara
cika da mamaki,'Ban fa gane shi ki ke so ba
mama.Ina Al-Ameen din?" Ido jajur! Ta dube
shi,"kai ka san wannan sunan,don girman Allah
ka kyale ni da tambayoyin nan." "Ba zan kyale ki
ba Mama,hasali ma sai na gaya wasu
Abba.Wannan ai zubar da mutunci ne da cin
amana!Me ya tsone miki ido a wajen Dan-Liti?Ke
ma kin shiga sahun 'yan matan da yake ruda da
kyan sa ne?Kai na ya daure Mama.Allah yasa
abinda na ke gani da ji ba gaskiya bane." Da
gaske ne yaya Ali! Kuma ko baka gayawa su
Abba ba,ni da kaina zan gaya musu."Ta zura da
gudu ta bar shi tsaye, shakare da
mamakinta.Kafin ya iso gida kansa,ya kusa
fashewa sbd tunani da al'ajabi.Rokon Allah
kawai yake yi Allah yasa mafarki yake yi. Kai
tsaye sasan su Mama ya zarce.Suna tsakar falo
umma ta tirke ta da tambaya,"Idan biki gaya min
inda kika je ba sai na sumar dake yau a gidan
nan!"Yayi sallama.Umma bata iya amsawa
ba,sbd bacin ran da take tare dashi.Ya-ce,'yanzu
na koro ta daga shagon Dan-Lati suna zaune
bisa benci suna hira Umma.Yaushe Mama ta
sauya haka? Tuni Umma ke sallallami,ta dafe
kirji ta-ce "shagon Dan-Lati ki ka koma Mama?
Mu kike so ki zubarwa mutunci a garin nan? Ai
kuwa baki isa ba,ba ki isa ba Mama!'Ji ka ke
tim! Ta rufe ta da duka ta ko'ina.kafin yaya Ali
ya kawo mata dauki,ta sha dan banzan
duka.Kukan ta ya watsu cikin sassa,matan gidan
da kananan yara suka sheko don ganin meke
faruwa?Al'amarin ya daure masu kai,ganin
Mama na birgima tsakar falo tana ture hannayen
Yaya Ali dake kokarin rarrashinta
BAKIN CIKI 2***2(TRUE LIFE STORY) Wa ya mutu
Ali? "suka tambaya,yayin da umma ta fito daga
daki dauke da wayar rediyo kafin su yi aune,ta
fara tsula mata.Haba gaba daya matan suka
cafke hannun Umma, 'Hajiya Halima! Lafiya
wannan abu haka?Me ta yi da zafi irin wannan
duka?" Umma na haki tace wai yarinyar nan ita
ce zata siyar mana da mutunci? Ta rasa wanda
zata tsaya da shi, sai Dan-Liti? "Dan-Liti? Waye
Dan- Liti?"Dan gidan Buzu mai shayi mana! Yau
kwana uku kenan muna fama da ita ta rabu da
yaron nan,ta ki! Jiya yazo kofar gidan nan.Alhaji
da kansa ya same shi ya gaya masa tana da rana
a kanta.shine don dibar albarka ta bi shi shagon
sa,yanzu Ali ya ganta ya koro ta! Wace irin tijara
ce wannan sbd Allah! Tuni suke kallon juna suna
tafa hannu,hajiya hajo tace "danliti kuma?Waye
bai san tarihin su ba a garin nan?Yaron da tun
tasowar sa garin nan basu da aiki sai bata
'ya'yan mutane koda baki da wayau sosai ai kin
yi dan hankalin da zaki gane buzu mai shayi
kasurgumin kwarto ne,shi kuwa danliti kananan
yara sau nawa ana kama shi dasu?Ko kin mance
ranar da dubu ta cika suka ci shegen
duka.Danliti ya sha da kyar shi kuwa buzu ya
shura barzahi?Me ya dawo da shi kike kwadayi
da har idon ki ya rufe kika kasa duban kazantar
dake tare dashi?Hajiya Gaje tace "duk ba ma
wannan ba kina nufin zaki fasa auran Al-ameen
ne?Umma tace,karya take yi sai dai bayan ran
mu,bari kuma alhajin ya dawo,yau din nan zai
maida ta minna tnda zaman naki anan abinda ya
haifar kenan!Ta tashi da gudu ta fada dakinta
har da danna sakata ta bar su nan suna maida
yadda aka yi. Shi dai yaya ali tunda ya sunkuci
jakar sa ya fada dakin mahaifiyarsa bai sake
kyakkyawan motsi ba sai tsabar tunani.Muryar
mahaifiyarsa yaji a kansa tana fadin,"kai kuma
yaushe ka shigo garin?"Firgigi ya dube ta
na'am!"Ta zura masa ido,nace yaushe kazo?Ya
sauke gwauron numfashi yace,"zuwa na kenan
inna".ciwon daya sami mama,ai ya same ni
domin jinin mu daya......"Gafara can sakarai kai
ka san wannan,da su ma sun san cewa jinin ku
daya ba'a hana ka auranta ba ai sbda haka ban
ga dalilin dogon tunanin da kake yi ba,don daga
ita har iyayenta basu san ka na yi ba!Gara tun
wuri ka halkantu ka gane cewar alhakinku ne ya
kamasu!Idan ba haka ba,ina mama,ina danliti?
Marasa asali da tushe ga tarin abin gori da na
kunya a jikin sa?"Ya dafe goshi idanuwansa suka
kara kadawa,yayi hucin zafi ya dubeta,"duk
wannan maganar bata taso ba inna abinda nake
so ki gane shine muddin mutuncin mama ya
zube,to martabar gidan nan gaba daya ta
fadi,ashe kuwa dole in damu tnda nima dan
gidan nan ne,ga shi kuma mama ta dauko
hanyar bada mana kasa a ido. Tace can dai zata
badawa iyayenta masu kwadayi,ban sa aka ba
balle ya dameni wahalar banza kake yi dama
ruwa da abinci ka samu ka ci,daya fiye maka
wannan sakarcin!Ya sake dafe goshi yana kada
kai,me yasa innar sa baza ta gane ba?Takaici ya
kara kama shi ya sunkuci jakarsa ya koma
dakinsu.Haj Gaje ta shigo saboda gulma ta
cigaba,sharri kala kala suka yi ta jifar uban
dawaki da su.La'asar sakaliya abba ya dawo
gida ya iske idanuwan umma sun jirkita jajur!Ga
kumburi sun yi,ko bai tambaya ba ya tabbatar
akwai abinda ke damun ta,don haka ya kasa cin
abincin data kawo masa,ya zura mata ido yace
kamar akwai abinda ke damunki sadiya? Tace
akwai matsala alhaji amma ka ci abincin sai mu
san abin yi."Fuska ki ta bayyana tashin hankali
dake tare da ke ban jin abincin nan zai iya wuce
min ba tare da naji damuwae ki ba.Gaya min
uwargida,ni kadai gareki wanda zai saurari
kukan ki."Ta dan yi murmushi karfin hali tace
mama zata siyar da mutuncin mu a garin nan
gara ka dauketa ka maida minna ko abj ta zauna
can har zuwa lokacin bikinta."Gaban sa ya fadi
yace,me tayi?Bata daina zuwa shagon yaron nan
ba,yau ali da kan sa ya koro ta tana zaune bisa
benci suna hira,benci fa a kofar shagon bakin
titi?Kamar mama yadda muke a garin nan take
zama tare da danliti?Ta goge kwalla,ina zan sa
BAKIN CIKI Alh,anya kuwa mama ce ke aikata
wannan abu?Hankalin alh yayi mummunan tashi
ya fuskanci umma da kyau ya sanyaya murya
yace,ki daina zubda mata hawaye halima ke
mahaifyarta ce,sai abin ya kara wargaje
mata......" "Ba yin kai na bane alhaji,hawayen ke
tilasta wa kansa zubowa."Yace duk da haka ki
rinka daurewa kina mata addu'a,insha Allahu
gobe zan maidata minna ko ta ki ko ta so dole
ta zauna.Ni abinda ban gane ba shine,tana nufin
ta fasa auran Al-ameen ne?Idan wani abu yayi
mata ai sai tayi bayani,ba wai ta nemi ta maida
mutane sakarkaru ba!Ina take ne?"Tace tana
daki a kulle tun safe daya koro ta,haushi yasa
nayi mata duka har ynzu bata fito ba."Ya mike
cikin fushi ya nufi dakin ya buga da karfi yana
fadin,"tashi ki bude kofar nan!"Tana budewa ya
cafko hannunta ya jawo ta zuwa falonsa,hakan
ya sanya mama cigaba da tsiyayar hawaye,ya
cillata tsakar dakin ta zube gefen ummanta.Ya
zura mata ido yace,"ashe wani lokaci zai zo da
zamu ce ki bar abu ki ki bari mama?Kin dai san
maganara auren ki da al-ameen ko?To ynzu nake
so ki gaya min manufarki ta bin danliti
shagonsa.Gaya min inji tun kafin mu tara 'yan
kallo!Tayi kasa da kai kukan ta ya karu.Abba ya
daka mata tsawa,"kuka na tambaye ki? Ki gaya
min dalilin bin sakaran yaron nan nace?Ta
cigaba da share kwalla tana mutsu mutsun rashin
gaskia,leben ta na makyarkyata tace,"shi....shi
na ke......na..na...ke so ab...."Umma ce ra doke
ta da bayan hannu tace rufe mana baki mara
kunya!"Ta dubi abba dake tsaye sake da baki
tace,"ka ji ko?Ni na san take-taken ta kenan!"Ya
matso ya cafki kunnenta cikin tsawa yake
magana."Idan barci kike yi to ki farka ki bude
kunnuwanki da kyau ki saurare ni! Ni ba tsohon
banza bane,in har kin ga ki auri yaron
nan,tabbaci hakika ni uwaisu na mutu an binne
ni cikin kabari na! Ya girgiza kunnen kamar zai
tuge shi,kin ji ni! Wannan itace magana ta
karshe da zanyi akan danliti kuma gobe ki shirya
kayanki zan maida ki minna!"Ya shirga mata
dundu tare da fadin,"tashi ki bani wuri!Ai bata
iya tashi ba nan ta baje ruf da ciki sbda tsananin
zafin dundun da yayi mata abnda bata saba
ba,sai ta ji shi har cikin kayan cikinta sun dau
zafi ba kadan ba,Ta fasa kara mai shiga zuciya
tace wayyo Allah na shiga uku! Na shiga uku!
Yaya ali ya mike a firgice,gabansa ya yanke ya
fadi ya fito da sauri yana tsinkayar kukan
mama,ya nufi sasa.Umman ke fadin,'ba ki shiga
uku ba mama sai nan gaba muddin baki dauki
nashihar da muke yi miki ba!"Hannu biyu yaya
ali yasa ya ciccibe ta ya mikar da ita,zafin duka
da tsananin BAKIN CIKI dake dankare cikin ran
ta yasa ta kwakume.Yaya ali bakin gado ya
zaunar da ita ya dago fuskar ta hannu biyu yake
share hawayenta,yayin da nasa kwallan ke
neman sauka,yace "haba mama ki yiwa kan ki
fada mana!"Murya na rawa tace,me nayi masu
yaya ali!Sbda Allah me nayi?"Me kika yi? ynzu a
wajen ki wannan ba laifi bane?Haba mama!Ba
haka kike ba,kin sauya da yawa kar dadin bakin
danliti yasa hankalin ki ya gushe,laifin me al-
ameen yayi miki kike so ki yi masa wannan
sakayyar?A zato na koda babu Al-ameen nine
mutum na farko daya kamata ki fara kawowa ran
ki don na dade ina yawo da ciwon son ki
mama.Ki tausaya mana me zai sa ki canza
kyawawan halayen ki? Ya Girgiza kunnen kamar
zai tuge shi. Kin ji ni! Wannan itace maagana ta
karshe da xanyi akan Dan-liti, kuma gobe ki
shirya kayan ki, zan maida ki bani wuri. Ai bata
iya tashi ba, nan ta baje ruf da ciki, saboda
tsanannin xafin dundun da yayi mata. Abinda
bata saba ba, sai taji shi cikin kayan cikinta sun
dau xafi ba kadan ba. Ta fasa kara mai shiga
xuciya. Tace wayyo Allah na shiga uku! Na shiga
Uku! Yaya Ali ya mike a afirgice, gabansa ya
yanke ya fadi, ya fito da sauri yana tsinkayar
kukan mama, ya nufi sasan. Umma ke fadin baki
shiga uku ba Mama, sai nan gaba muddin baki
dauki nasihar da mukeyi ba miki ba! Hannu biyu
Ya Ali ya sa ya ciccibeta ya mikar da ita, xafin
duka da tsananin BAKIN CIKI da ke dankare cikin
ranta ya sa ta kwakume Ya Ali. Bakin gado ya
xaunar da ita ya dago fuskar ta hannu biyu yake
share hawayen ta, yayin da nasa kwallan ke
neman sauka. Yace, haba mama kiyi wa kanki
fada mna! Murya na rawa tace, me nayi musu Ya
Ali? Saboda Allah me na yi? Me kikayi? Yanxu a
wajenki wannan ba laifi bane? Haba mama! Ba
haka kike ba, kin sauya da yawa kar dadin bakin
Danliti ysa hankalinki ya gushe. Laifin me Al-
ameen yayi miki, kike son ki masa wannan
sakayyar? A xato na koda babu a alameen, ni ne
mutum na farko daya kamata ki fara dawowa
ranki, don na dade ina yawo da ciwon sonki
Mama, ki tausaya mana, zai sa ki canja
halayenki? Ta xuba masa kwala- kwalan
idanuwanta da suka kara fitowa waje jajur! Tace,
Yaya Ali ina ganin girman ka, ka kyale ni da
wadannan surutan, don ba xa suyi tasiri ba. Ni
nace ina so Al-ameen, yanxun kuma bana son
shi Danlilti nake so. Ra'aryi nane, ba sai a kyale
ni ba, ko akwai wanda zai zauna min da shi? Ya
bita da kallo, ta sa aya kafin yace, ki daina
tunanin wannan ra'ayin na ki mai yuwuwa ne,
kin dauko katon aikin da xai rushe martabar
gidan nan a idon jama'a. Idan baki son Al-
ameen, ki musanya da ni Mama, zai fi miki kyau
a bisa shirmen da kie sonyi. Ta runtse ido tace,
yaya Ali je ka kawai! Ba ki son gaskiyya? Ta
kauda kai kwalla na tsiyaya. Ya sanya murya
yace, xan bar ki ki kwanta kiyi tunani sosai,
cikin kan ki. Ina rokon ki girma da Allah, ki
manta da kudirin da kika dauko. Bata tanka ba,
haka bata dube shi ba yace, A bakin tofa ya
tsaya ya kare mata kallo kafin ya sake fadin,
bana so ana taba jikin ki mama, tamkar ni ake
tabawa nakeji. Pls ki sauya tunaninki. Haushi ya
kara kuma ta, ta juya masa baya. Ya fice yana
kara waigen ta. A daren nan daga ita har Yaya
Ali babu wanda ya iya cin abincin balle barci.
Tunanin Mama shine xata ga yadda za'ayi a raba
ta da garin nan. Cikn xuciyar ta tasha alwashin
ko sun maida ta, zata dawo, dole su gaji su
kyale ta da wanda take so. Dalilin da yasa ke
nan, yau kwata-kwata taki bude kofar ta, kowa
yayi bugu, iyayinsa har kawunninta, sai dai
kalaman bakin su suka kare. Amma mama taki
bude kofarta. Duk wanda ka duba ransa bace
yake, musamman Abba, fuska kamar gobara ya
dubi Umma yace, dauko min tabarya! Ta mike a
salube ta shiga kicin ta dauko masa tabarya, ta
mika masa. Alh basiru yayi caraf! Ya karba.
Yace karka balle kofar nan yaya, asara biyu
xa'ayi..... Yace yarinyar nan dole ta bar garin
nan, ba xata xauna tana jawo min xagi ba, ana
kallo na tsahon banza, bansan abinda nake yi
ba! Buge min kofar nan, ko ka ba ni da kaina, in
sauketa! Kowa yayi cirko-cirko. Alh. Basiru ya
kai wa kofa duka da tabarya, sai ga sallamar
Yaya abdul- kareem. Basu gama amswa ba, yaci
gaba da tambaya, lfya? Me ya faru da kofar?
Abba yace, nayi farin cikin xuwanka, don ni ma a
yau nayi niyyar tafiya gunka. Me ya faru abba?
Umma ya naga kamar kina kuka? Yace, mama
ce.... Me ya sameta? Ya kwashe kaf halin da
suke ciki ya gaya masa. Kai! Bai gaskanta
kunnuwansa ba, shi yasa yace, abba ban yarda
da wannan maganar ba, ya kamata asake
bincikawa. Abba ya xuba masa ido jajur! Yace,
wannan maganar ni Uwaisu nake gaya maka ita.
Abdul kareem kasan kuwa ba za ayiwa mama
kage ba, domin ni na haifeta. Saboda haka gidan
ka xata xauna can har xuwa lokacin bikinta!
Yace, ya xama wajibi, don ganin nan da kuka yi
min xuwa nayi in tafi da ita dama. Al'ameen ya
damu kwarai har yana ganin kamar wani abu ne
ya faru da ita ake boye masa. Wlh jiya ya turo
mahaifiyarsa da yamma wai ta zo ta bincika
masa lfiyar mama, shine nace shi kwantar da
hankalinsu Insha Allah da kaina xanje in dawo
da ita. Wannan al'amari ya daure min kai.
Yaushe mama ta canza haka? Kawu Basiru yave
xancan banza takeyi, tunda ita ta kawo Al'ameen
har aka sanya musu rana, bata isa tace ta canza
shi ba! Wannan karya take yi. Haushi ya kara
kure yayanta, ya mike ya suer tabarya ya kaiwwa
kofar duka sau biyu kofar ta balle, bata a dakin.
Ya nufi kofar bayi ya murda can ma garkamen
yake, bai tsaya wata-wata ba, ya maka mata
tabarya. Bugu daya kofar ta wangem, sai ga
mama jikin bango ta fita hayyacinta saboda
tsabar kuka. Al'amarin tamakar mafarki yayana
yake gani. Ya xura mata ido, yace hauka kikayi
mama! Me Al-ameem yayi miki? Iye? Yayi miki
laifi ne da ba zaki fada ba! Sannan ki rasa
wanda zaki bi, sai dan liti! Kinji abinda nace?
Kin yi karya ki xuabar mana da mutunci a garin
nan! Zo mu wuce, ban son jin komai daga gareki!
Ta sulale kasa hannaye biyu bisa kanta, ta kara
fasa kuka mai tsananin gaske. Matan gidan suka
kutso kai cikin bayain suka tarairayo ta, suka
fito da ita dakin. Yaya yana fadin ko mutuwa
zakiyi yau, sai na tafi dake mu je can idan Al-
ameen ya kira waya, in tambayehsi a gabanki,
muji abinda ya hadaku! Amma yaro na sonki
yana tattalinki. Iyayeynsa na ririta ki, tashi guda
kice ba kiyi da shi, aikin san wannan karya
kikeyi. Ina kayan ta suke umma? Hada mata si
don baxan bata lokaci ba! Gaba daya suka
yanyame ta da fada kowa na fadin albarkacin
bakinsa, su Umma na hada mata kaya. Su
Hajiya Hajjo na rarrashi ta suna bata baki tare
da gyara mata jiki da fuska. Yaya Ali kuwa yana
xaune gefe rayuwa tayi masa bakikkirin! Ana
janta, tana togewa suka saka ta gabn motar
yayanta. Ya jefa jakar ta gidan baya, daga nan
yayi sallama ransa bace, ya ja motar yayi gaba
da mama. Dole ne ya saurar daidai shagon
Danliti, domin akan mahada shagon yake.
Tsayuwar su wajen, ya jawo hankalin Danliti
xuwa garesu. Ya xuba wa Mama idanuwan sa
suka sha kwalli rangadau! Haka ita take kallonsa
kwalla fal! Suna neman sauka. Ya daga kanka ta
fito kofar shagon, irin duban da yake mata ya
bayyanar da damuwarsa karara bisa fuskarsa.
Tausayinsa ya lullubeta, nan da nan hawayen
suka fara bulbula. Yayanta bai kula ba, kokarin
sa, duk motocin da suka kawo, suka wuce shima
ya samu ya haura. Yawanci duk manyan motoci
ne, kamar yadda akansan babban titi ne, wanda
ya mike ya tafi har lagos. Suna tsagaitawa ya
cilla tasa motar ba tare da ya fahimci Danliti da
mama sun ruga sun gama magana da
idanuwansu ba. Kawai ji yayi ta kara gocewa da
kuka mai karfi. Ya dan dubeta, ya kada kai.
Yace, Al'amarin ki na bani mamaki, look kina
jina? Saurare ni muyi magana ta fahimta. In
tambayeki xaki bani amsa? Hankalinta sam ba
awajen sa yake ba, balle ta saurare shi. Fuskar
Danliti take gani, irin yadda ya shifa damuwa
yana neman xubar da hawayensa, shi ya kara
dagula mata lissafinta. Yace, saboda Allah zaki
gaya min Al- ameen yayi miki da zaki juya masa
baya? Tayi shiru, danliti na cigaba da yawo a
idonta. Yace, kin kuwa san tun ranar da kika
dawo garin nan. Al-ameen ya rasa nutsuwarsa?
Ban iya kirga yawon wayoyinsa ba, tunaninsa
kina cikin wani matsanancin hali ne aka boye
masa. Kar ki saki reshe ki kama ganye Mama,
domin kowa yasan Danliti lalata rayuwar ki
kawai zai yi, ya kai ki ya baro ki tashar
danasani. Ki ga ya min idan Al- ameen yayi miki
laifi ne, ni da kaina xan masa magana in ja
masa kunne. Kinji? Bai yi aune ba yaga ta balle
murfin motar ta dire waje. Ta mulmula cikin
ciyayi. Cikn tashin hankali ya take birki.... Allah
yasa ba babu mota a bayansa, yayi fakin gefen
titi, ya fito. Can ya hange ta tana kokarin tashi,
amma ta kasa, kafin ya gangara wajen 'yan
tsirarrun jama'ar wajen sunyi caa! Kanta. Suka
ciccibota, suna sallalami tare da mamakin yadda
aka yi abin ya faru. Gaba daya gwiwowin ta
sunyi mugun kurjewa ta xura da gudu amma bata
je ko'ina ba mutane suka cafke masa ita. BAKIN
CIKI yasa ya dauke da wani mahaukacin mari
daya tilasta mata xubewa kasa. Wani dan dattijo
cikinsu ya kama shi. Yace, haba malam yaya
haka kuma? Baka ganin kaddarar da ta sameta?
Da ta mutu fa? Ku rinka kulawa da murafen mota
mana don gudun irin hakan! Idanuwan sa ajuye
yake magana, kyaleni da yarinyar nan baba! Da
kanta ta bude murfin ta fito! Iskanci ne kawai,
dama kin mutu, mu huta da wannan BAKIN
CIKIN da kike son jefa mu! Saboda haka xan
koma in gayawa abba kin bude mota ki diro, ni
kuma ba xan tafi dake ba, ki xauna kiyi duk
abinda kika ga dama agarin nan, tunda lalacewa
kika xaba. Allah ya shirye ki! Ya shura
takalmansa ya koma mota ya tayar yayi kwana
ya koma gida ya bar Mama anan tana faman
kuka, jama'ar dake wajen suna mamakin wannan
abu har sun kasa fassara shi. Dan dattijon nan
shi ya riko ta hankali suna tafe tana bashi
labarin wai auran dole ake son yi mata. Kwarai
kansa ya daure jin cewar ita 'yar gidan Uban
dawaki ce, don haka ya tasa ta har gidan. Amma
me? Suna xuwa kofar shagon Danliti ta xarce can
tayi xamanta bisa benci. Dan liti ya fito aguje da
ayuba, mamaki ya rufe ayuba, shi kuwa dan
gogan munafuncin ne yasa gaba, sai yazo ya
narke a gabanta. Yace, saboda me sakina,
kinaso ki rasa ranki ne? Tace gara in mutu da su
raba ni da kai, ya dubi Ayuba a gigice. Yace,
kawo min mukullin mota ayuba! Ya shige shagon
da surinsa, shi kuma ya juyo gunta ya marairaice
yake fadin, aure na Allah ne sakeena, ina so ki
yarda da wannan. Duk iya son da muke juna idan
Allah bai nufi auran mu ba, babu yadda xamuyi.
Don me xaki nemi halaka kanki? Bata bashi
amsa ba. Ayuba ya mika masa mukulan. Bai jira
tace wani abu ba, ya kamo hanninta taso muje
asibiti asa miki magani. Dattijon nan ya bisu da
kallo, duk tausayi ya rufeshi. Rashin sani kenan,
ya fi dare duhu, domin shi gani yake irin haka ke
jefa yara yawon banza..
BAKIN CIKI 2***3 (TRUE LIFE STORY) Wasu
iyayeyn na da ra'ayin rikau, idan kuma ka
bibibya kwadayi ne, wata kila wancan yafi
wannan kudi ne? Sai dai kuma ai uban dawaki
mutumin kwarai ne, me xai sa ya aikata haka
akan yarsa? Duk da cewar dan dattijon nan
talaka ne, ya doshi gidan uban dawaki, don ya
bashi shawara. Fuskar Umma a sharkaf da
hawaye take muryar ta har rawa takeyi, bai
kamata ka baro ta can ba abdul... Yaya xanyi
umma? Kona cusata cikin, sake fitowa xatayi.
Mama ba zata mutu a hannu na ba, umma ta tafi
inda take son xuwa, kanta tayi mawa. Fatana
kwai Allah ya yaye mata abinda ke damunta.
Kuyi hkr ku kyaleta anan domin ina mai tabbatar
muku xata xauna can ba dawowa xatayi ba.
BAKIN CIKI ya hana abba magana, sai A. Adamu
ya iya fadin, gaskiya, gara ta xauna a cigaba da
yi mata nasiha watakila a dace. Kuyi hkr Yaya
mu dauki wannan a matsayi kaddara. Kai abdul
idan ka koma Al-ameen ya kira ka kwantar masa
da hankali ka... In ce masa me kawu? Gaskiyya
xan gaya masa shi ma ya hkr da ita tunda ba ita
kadai bace 'ya mace. Allah xai bashi wata. Ko
kuwa? Abba ya dube shi, sai yanxun ya iya cewa,
karka gaya masa haka abdul, da yardar Allah sai
inda karfina ya kare akan mama. Indai ni na
haifeta kuma ni ne xan daura mata aure Insha
Allahu shine xai aureta. Kawai ka bashi hkr kayi
masa wannan bayanin da naga ya maka yanxun.
Ya dafe goshi yayi huci zafi kafin ya dubi
Umma. Yace ki share hawayenki, umma ki yi
mata addu'a Allah ya shiryata. Ni xan koma sai
yadda ta kama. Basu amsa ba, ya mike kawu
Basir da Adamu suka yo masa rakiya kuma suna
gaya masa kalaman da suka dace ya gayawa Al-
ameen. Da dan dattijon nan sukayi kicibis yana
sallam cikin xaure suka amsa nan take. Yace
baka shaida ni ba ko yaro? Nine wanda yaga
lokacin da yarinyar gidan nan ta bude murfin
mota ta fito, tayi min bayani ita 'yar mai girma
Uban dawaki ce, shine nace ai mai martaba yana
da saukin kai xan xo in bashi shawara game da
auran dole, yayan ya dube shi da kyau. Yace
hakan ta gaya maka? Yace, kwarai hakan ta
fada. Yace to tayi maka karya, kawu ka na iya yi
masa bayani, don na tabbata abba baxai iya
fitowa ba ahalin da yake ciki. Alh. Basiru yace
yanxun ina take? Yace tana can ta tsaya wani
shago har sun tafi, zai kaita asibiti. Suka dubi
juna, yaya yace, kunji ko? Mama ta tafi, bata jin
kira saidai addu'ar Allah ya shiryata. Ni na tafi.
Ya fice ya barsu nan tsaye. Alh. Basiru ya dubi
tsoho yace mun gode baba, amma kayi hkr,
bazaka ji komai daga gareni ba, saboda ban
sami izinin yin hakan ba. Maganata gaskiyya da
nake so ka gane shine karya yarinyar ke maka,
tare da shegantaka irin ta yaran yanxun. Mun
gode da kulawarka. Tsoho yace, shikenan nima
na gode, amma don girman Allah abi a hankali
asamu a sulhunta. A. Basiru yace ba komi baba
mun gode. Sukayi sallama ya shige gida. Tsho
ya kama gabansa cike da wasi-wasi cikin ransa.
Falon Uban dawaki A. Basiru ya koma ya
xayyane masa labarin da tsho yaxo da shi, da
kuma shawarwarin da ya bayar. Abba bai iya
cewa komai ba saboda tsabar bacin rai. Sun jima
suna tausar xuciyar Abba sannan suka koma
sasan su, inda matan suke xaune dirshan suna
xuba gulmace gulmace. Suna zagin mama da
iyayenta. Basu hanasu ba, hasalima zama sukayi
suka dora xancan babu dadin ji, ita kuwa baiwar
Allah mama, tana tare da Danliti cikin mota,
bayan fitowarsu asibiti, yana ta faman
rarrashinta, don ta daina kuka ta kwantar da
hankalinta, da kyar ya samu ta nutsu ta daina
xubda hawayen. Yayi fakin kofar shagon sa ya
juyo ya fuskance ta. Yanxun ya xamuyi mu
fuskanci juna abba ya gane cewar idan ba mu
auri juna ba, komai zai iya faruwa da mu? Tace,
ai ga misali nan na fara nuna masu kuma ba xan
fasa ba, ina nan akan baka na. Ya marairaice
yace wannan misalin bana son irinsa sakeena,
don bana son na rasaki. Gaba ki daya kin fita
kamanninki kin kuwa ci abinci yau? Ta kada kai,
abinci ba xai iya wuce min ba Dan liti ina cikin
wannan masifar meye illar ka? Da abba xai ce
samm baka dace dani ba? Ya lumshe ido, ya
bude kafin yace, saboda suna ganin ni bako ne,
bani da kowa agarin nan..... Ta katse shi, hakan
shine xai nuna daga sama ka fado? Wannan ba
hujja bace Danliti, son rai ne kawai irin na iyaye
ni kuwa ba xan yarda ba, sai dai muyi ta ba juna
wahala. Ya ja gwauron numfashi ya sauke, ya
lalubo yatsun ta ya runtse su cikin nasa, ya xuba
mata ido yace, nasan ki na sona sakeena, amma
ki daina damuwa ko sun hana ki xuwa wajena,
sannan ki daina wasa da rayuwarki, don tana da
muhimmanci aguna. Abu da gaba, ki daina zama
da yunwa, ita ma zata iya illata minke. Yaunxu
abinda nake so dake, ki zo muje shago in hada
miki tea ki sha, sannan kije gida ko sun zage ki,
kar ki ce dasu komai, don kar su sami damar
dukanki. Kinji bebi na? Ta amsa da ka. Tace,
yauwa mai kyau, to dan kalle ni mana, ta dube
shi suka yiwa juna xuru, jim kafin ta kauda kai,
tana dan murmushi, shima murmushin yayi yana
mata kllon kwadayi, ya ja yatsunta xuwa bakinsa
ya sumbata. (kuji dan iska). Ta kwace da sauri
ta kara sadda kai. Yace, bebi na kenan, sarkin
kunya. To muje ko? Zaki iya sauka ko in zo in
fito dake? Ta balle murfin batare da tace wani
abu ba ta fito, shima yayo waje yana kallon
yadda take dingisawa har cikon shagon sa. Ya
ba za mata tabarma ta zauna. Ayuba na mata
sannu. Akwai wani labule jikin wata kwana a
shagon, sai alokacin ta gane daki ne. Cikinsa
Dan liti ya shiga ya fito da filas da kofi da cokali
ya aje gabanta. Yace ga ruwan zafi, ki daga
idonki, ki duba duk irin madarar da kike so, ki
zaba na dauko miki. Tana murmushi tace, kai
wacce iri kake sha? Yace ai bana shan madara a
tea, ganye kawai nake sha. Kinsan buzaye ai?
Tayi dariya tace, ba'a raba su da jiko. Yace shayi
dai. Ta ciga da dariya tana fadin, to shayi, wai
menene sirrin shayin nan ne? Yace xan gaya miki
amma da farko wacce madara kika zaba, in
dauko miki? Na kowa ki sawa cikinki abinci.
Tace, bani peak ta ruwa. Ya mike ya dauko hade
da katon bread ya hada mata tea mai kauri,
domin duka ya juye peak din. Tana sha, suna
hira ya gaya mata ire-iren shayin su. Bayan ta
kammala, ya matsa gareta yace, yanxun ya
kamata ki koma gida kiyi barci, ki huta kinji?
Karki damu ko an hana ki xuwa nan, wane tym
zamu hadu. Ke dai kiyi addu'ar fatan samun
nasara. Tace, Insha Allahu zanyi. Yana
murmushi ya mika baki ya sumbaci kuncinta. Ta
sunkuyar da kai tana murza yatsunta. Ya zura
mata ido, gaba daya jikinsa yai la'asar, sannan
ya dago habarta, suka dubi juna, yace I love U!
Tace me too, yace, to ki tashi kije gidan, zaki
iya ko? Tace xan iya. Ta yunkura ya taimaka
mata mikewa suka fito tare ta sallami Ayuba, ya
dan taka mata kadan ya dawo, yana zuwa ya
kwashe da dariya, ya mikawa Ayuba hannu suka
tafa. Ayuba yace, baka da kyau dan iska. Yace
raina kama gayya! Gaskiyya ta gurzu, na
tausaya mata wlh. Shegiya akwai taushin fata,
baka ji ba kamar auduga, duk ta susuta ni. Ya
zura masa ido yace, tunda kuka shiga, na
karance ka, shi ya gaba na yayi ta faduwa, kar
ka sata labulan nan. Yace, ko na sata ba zata
hani ba, nake gaya maka kuma babu abinda zai
faru dani. Kawai dai ban yi niyya bane yanxu, ni
nasan abinda nake hari. Yace a dai rika tuna
Allah Danliti, shagalinka yayi yawa kuma ina ma
kwadayin cin ubanta nakeyi, ai har uanxun
duniya bata fara zaginta ba. Kaga da sauran
mutuncinta. Ya bishi da kallo, bai ce komai ba,
yayi tsaki ya tashi ya koma shago abinsa. Tana
tafe tana dingishi, ta iso gida, kanta tsaye bata
fargabar komai ta fada zaure, kicibus suka yi da
Ya Ali sabe da jakar sa zai bar garin. Ko kallon
sa batayi ba ta wuce, ya biyota yana kiranta bata
waigo ba, balle ta amsa, ta shiga sasan su har
falo yana binta. Su abba na kallon ikon Allah,
domin dai Mama bata saurara ba, cikin dakinta
ta shige. Ya Ali na shigowa ya gansu, ya ja birki
amma ransa na son ya shiga wajen mama, yayi
magana da ita, abba ya dube shi. Yace, Ali ka
daina wahalar da kanka abanza, mama bata
bukatar komai sai addu'a. Saboda haka ka kama
hanyarka ka koma bakin aikinka. To amma, kayi
hkr Abba, don girman Allah karku daketa, kamar
yadda kace nayi mata addu'a kuma kuyi mata
addu'ar. Yace, na yarda da kai Ali, amma ban
yarda auran kowa ba, sai wanda na aminta da
shi. Zan gani idan ita zata daura wa kanta aure
ko mune? Yace, haka ne Abba don Allah ina
rokon 2mins in ishiga in dayi mata nasiha, koda
bazata saurere ni. Ya suke numfashi yace, shiga
Ali, Allah ya sa taji abinda zaka gaya mata. Ya
aje jaka ya wuce cikin dakin. Tana kwance
niyyar barci ma takeyi, kamar yadda Danliti ya
umarceta. Yana shigowa ta runtse ido ta juya
baya, ya tsya kanta yace, komai zakiyi, dole in
gaya miki gaskiyya, tunda kunnuwanki naji.....
Fadan hakan yasa tai sauri ta toshe kunnuwan
nata da yatsunta. Yace aikin banza kike yi
Mama, kuma rayuwar ki na cikin hatsari, muddin
baki daina jefa su abba cikin BAKIN CIKI ba.
Menene anfani abinda kika aikata yanxu? Ki
kashe kanki a banza da wofi, ba asarar Danliti
bane, don na tabbata duk tsananin son da yake
mi, ba zai hallaka kansa ya biki ba. Ki nutsu kiyi
tunani. Akwai abinda magabatan mu ke hangowa
kan wannan ra'ayin naki. Ni zan koma kuma ina
fatan zanji canji daga gareki? Ya juya ya fice
bata re da ta daga kai ta dube shi ba. Wani
dogon tsaki ta raka shi da shi, wanda ya tilasta
masa juyowa ya dubeta ji, sannan ya karasa
ficewa. Ya dauki jakarsa ya kara yiwa su Abba
sallama, ya bar gidan ciki da Al'ajabin maras
misaltuwa a zuciyarsa. Bayan tafiyarsa, su
Umma suka shigo gunta ta tana kudundune ta
dunkule wuri daya, ko 'ina jikinta ciwo. Umma ta
zauna gefen gadon shi kuma Abba n atsaye
kanta, yace Mama barazanar kashe kanki ba zai
sauya abinda ke cikin raina ba, idan ma baki
sani ba, ki sani gara ki mutu da mutunci na ya
xube a idon duniya. Saboda haka fadowar ki a
mota bata girgiza ni ba balle ta cire daidai da
kwayar zarra na alkawarin da na daukarwa Al-
ameen da iyayensa. Mu zuba ni dake, duk wani
matakin rashin kunyar da kika hau, ni na fi ki
hawa matakin karshe! Ya juya ya bar dakin.
Umma ta kura mata ido, hawaye suka cika
idanuwanta, tace Mama zaki iya tashi ki saurare
ni? Ta shiru bata motsa ba, ta sake fadin, idan
har ni na haifeki kuma na isa dake, to ki tashi
zaune ki fuskance ni. Ta jima kafin ta yunkura ta
tashi fuskar ta sharkaf da hawaye, kamanninta
sun sauya, saboda fitinar da ta daukarwa kanta
a tunanin iyayenta. Umma ta zura mata ido,
kafin tace, nasiha xan miki, idan kiji ki dauka
wahala ta kare miki, idan kuma kince ba haka ba
to rayuwa zata cigaba da yi miki kunci, domin
Allah ne ya wajabta miki yi mana biyayya,
muddin ba mu sa ba masa. Ban jin akwai wani
dalili ko hujja da xaki gayawa ubangiji da ace
kin mutu sakamon bude murfin motar da kikayi,
ki fado lasa. Wannan ya nuna muraran kin kashe
kanki ne da gan-gan. Ma'ana kin mutu kafira.
Me zai jawo miki wannan masifar da hankalinki
da komai? Ko kuwa kina so ki nuna mana kin fi
karfin mu cikin dan kankanin lokcine ne? Kina
nufin mu sanya miki ido ki zubar da mutuncin ki
da mu a garin nan? Ban taba tunanin Mama, ke
din nan zaki zama kaza kici share baki a game
da irin so da Kaunar da Al-ameen da iyayensa
syka nuna miki. Haka kuma ban taba mafarkin
ke din nan zaki iya hango wani da namiji ya rufe
miki ido har kice kin fo sonsa akan Al-ameen.
Kina nufin daman can yaudara sa kike yi ba
tsakani da Allah kike sonsa ba? Har yanxun
mafarki nakeyi Mama, don ba gaskanya abinda
yake shirin fitowa daga gareki nake ba. Ki yiwa
girman Allah kir ki bari wannan magana ta zama
gaskiyya, ba ke kadai za'a zaga ba har damu
iyayenki. Na mu ma zai fi yawa saboda mune
muka isa dake. Yanxun abinda na rokonki shine,
ki share hawayen ki ki gaya min, laifin me Al-
ameen yayi miki kike son ki katse masa rayuwa?
Gaya min daga ni sai ke ce a dakin nan kuma
share hwayenki, muddin shi ne baida gaskiyya.
Ta shre hawayneta wasu suka xubo mata,
kalaman ummanta masu taushi ne dashiga
xuciya, amma kash Danliti ya riga ya gama da
ruhinta. Allah ya bashi sa'a ya kamata ahannu,
idanuwanta ba sa ganin kowa sai shi,
kunnuwanta ba sa sauraron kowa face kalaman
yaudarsa da izgilanci. Dalilin da yasa kenan
kalma daya bata tasiri a hrt dinta, a duk tsahon
jawabin da Umma tayi, da ka dubi fuskarta, zaka
gane bata yarda bane kawai. Murya cunkushe
tace, ni babu abinda Al'ameen yayi min Umma,
kawai raina yafi kwanciya da Danliti kuma shi
nake so na aura. Haushi kamar ya kashe Umma
ta mike tsaye. Tace, to baki isa ba! Mu dan Liti
baiyi mana ba, idan kina da wasu iyayen da za
su dauta miki auran to bismillah! Ya ci gaba da
fadin, ai kuwa bata isa ba, ni zanje in dauko ta
kuma dole ta auri wannan yaron tunda itace tace
tana so tun farko! Yace, Yaya duk yadda kake
tunanin al'amarin nan ya wuce nan, amma ka
gwada ka gani, kilan kai tafi jin tsoronka, sai
dai kafin nan xance Al-ameen din ya kira ka,
kuyi magana, don ni gaskiyya ban san me xance
masa ba. Yace ba wani abu xan rarrasheshi, ya
kwantar da hankalinsa, kaima yaunxun nan ka
kama hanya kaje ka yiwa Hajiyansa bayani, kace
kar su damu ba wata matsala bace babba. Ya
numfasa ya amsa da to kawai. Lallai babban
yaya yana dau kara abin wasa ne. Suna aje waya
Aunty amina ta nufo shi, me ya faru ne wai? Nan
take ya labarta mata abinda ke faruwa. Tun
kafin ya kare idanunwanta ke waje, wai kana
nufin Mama ta fasa auran Dr? Yace gara da
kikace wai, don bata ida ba. Ni xan je na dauko
ta, cikin gidan nan zata zauna sai ya dawo. Ta
kada kai cikin damuwa, tace amma mama ta ban
mamaki, me Dr? Yayi mata? Babu abinda yayi
mata, wani ta hango saboda rashin hankali irin
naku na mata da butulci! Tace wlh na yadda sai
dai matsalar banyi zaton haka ba daga wajen
Mama ba ganin yadda take nunwa Dr. So mai
tsanani, duk yaudara ce, kai gani kuma a zahiri
ai ta nuna. Amma ai tayi kuskure ni zan gyara
mata zama, don bata isa ta zubda mana mutunci
ba! Tace gaskiyya ne. Allah yasa ta gane. Ya
wuce tebur don cin abinci. Shi kuwa
abdulkareem, bai sami zaman cin abincin ba
gidansu Al-ameen ya nufa ba tare daya san wane
irin bayani xai iya yi masu ba, don hankalinsu ya
kwanta. A haka ya isa gidan. Nan da nan aka
tarbe shi da girmamawa da abubuwan kusa da
baka, marafa baya gari, saboda haka mami ce ke
tare da shi, ina fatan dai kaci abinci? Yayi dan
yake yace, Alhmdlh Hajiya, nagode. Tace amma
dai ko Juice kasha ko? Haba, kamar wani bako?
Yanata murmushin rashin nayi, yana kallo ta
xuba masa ta mika masa, Ungo sha don Allah.
Kuma maimakon kazo min da surukartwa, yau in
riketa cikin gidan nan sai tayi min sati. Ya aje
kofin lemo ya kara gyara zama, Yace Hajiya, hkr
na zo in baki, domin ban sami dawowa da Mama
ba,... Saboda me? Kodai maganar Al-ameen
gaskiyya ce, sakeena na cikin wani hali? Bata da
lfya ko? Ya karkada kai.... Tace karka bote min
komai Baban ameer, duk tsananin da sakeena ke
ciki, nasan yadda xan rarrashi Al-ameen don
hankalinsa ya kwanta. Gaya min me ya faru da
ita? Jikinsa ya kara sanyi, cikin taushin murya,
yace Matsala ce babba Hajiya, wacce ni kaina
ban da ita ba, sai da naje daxun. Ashe tun
komawar ta gida, wani yaro ya hure mata kunne,
shi ya hana ta dawowa. Su abba na ta fama da
ita kuma suna kan kokarin su don ganin raba ta
da shi. Na yi nayi ta biyo ni, taki hajiya, shine
Abba yace in zo in baku hkr kafin yazo. Insha
Allahu za'ayi maganin abin. Gaba daya hankulan
mu atashe suke, al'amarin yana daure mana kai.
Idanuwanta xuru akansa, hannunta bisa kunci.
Tace, wyyo Allah! Wayyo Allah! Me xanji yau mai
kama da almara? Ta goce da sallalami, yanxun
baban ameera kana nufin sakeena tace amanar
Al-ameen kenan? Idanuwanta suka cika da
kwalla, yayi da yaya Abdul ya kara kasa da
kansa. Yace, kiyi hkr Hajiya, a gaskiyya ban san
yadda xan fassara wannan al'amarin ba, amma
abinda nake so ki gane Abba ba xao rungume
hannayensa ya sanya mata ido ba. Haka muma
'yan uwanta. Muddin kuwa tana son albarka dole
tabi umarnin mahaifinta. Shi yasa ya fara turo ni
kafin ya zo da kansa ya ga alhaji. Haka kuma ku
rarrashi Al-ameen ya kwnatar da hankalinsa
komai zai daidaita cikin hukuncin Allah da
yardarsa. Ta cire tagumi. Tace, a gaskiyya ba
zan iya fuskantar Al-ameen da wannan maganar
ba, in katsa masa karatu. Na san ya damu
kwarai ya san halin da sakeena ke ciki, amma
ba xan iya gaya masa wannan mummunan
labarin ba, kuma na rokr ku don Allah ku
kyaleshi kawai. Gara abar shi cikin duhun da
agaya masa sakeena ta sauke alkawarin da ta
daukara masa. Na tabbata komai nasa zai tsaya
jarabawar su gab take da xuwa. Ni da kaina xan
iya xuwa na roketa, ta tausaya wa Al-ameen
karta kashe masa zuciya. Kwalla masu zafi suka
xubo bisa kuncinta bata re da saninta ba.
Hankalin Abdul ya kara tashi, BAKIN CIKI ya
dada lulluba shi. Don girman Allah Hajia karki
xubda hawayenki akan maganar nan. Da yardar
Allah komai zai gyaru. Kamar yadda kika ce kar
agaya masa ba, ba za'a gaya masa ba. Gara ace
masa bata da lfiya ne, xuwa lokacin da xa'a
shawo kanta. Ta goge kwallah, tace ina ganin
hakan zai fi sauki iyaka dai yayi tunanin jikinta,
mu kuma nan mu rinka gaya masa tana samun
sauki. Yace, to shkienan, Allah yasa mudace.
Don girman Allah hajiya kuyi hkr, sakarci ne
kawai irin na yara. Tace, ya za muyi baban
ameer? Dole mu rungumi kaddara. Ya mike babu
isasshen laka a jikinsa, yayi mata sallama ya
fice, batare da hajiyar ta kara ko motsi ba.
Wucewar awa daya da rabi tana zaune xuciyarta
cike da sake-sake iri-iri. Ji take kamar a
mafarki abdul yaxo mata da wannan mummunan
labari, wanda take ganin zai iya salwantar fa
rayuwar dant tilon danta da takeji da shi. Duk
fadin duniyar nan bata hada shi da kowa. Yaya
marafa zaiji, idan wannan labari yake kunnen
sa? Tabbas xai fita shga damuwa, domin yafi ta
sanya Al-ameen ransa, ko alama baya son yaga
ya nemi abu. Waya ta dau ruri a falon, ita ta
katse tunaninta tare da haddasa mata faduwar
gaba mai tsanani. Ta mika hannu ta dauka ba
tare da tayi hasashen mai kiran ba. Tayi sallama
cikin raunin murya. A raunane taji muryar Al-
ameen ya amsa mata kafin yaci gaba da cewa,
mami na, ashe sakeen ba ta da lfiya shine aka
boye min? Ni ban ma yarda bata da lfiya bane
Mami, kawai ku gaya min idan mutuwa tayi, xan
hana Allah ikonsa ne? Ai nasan yafi ni sonta,
kuma ta shi ce ban isa in hana shi amsat
kayansa ba.... Tace saurareni Al-ameen, kar
hankalinka ya gushe.idan baka yarda ba da
maganar yayun sakeena ba, ai ni mahaifiyar
kace, ba xan rufe maka komai ba, ka yarda ko
baka yarda ba? Murya na rawa ya amsa, Na
yarda mami, tace to sakeena bata mutu ba,
rashin lfya ce ta sameta aka maida ta gida.
Bana so ka damu da yawa, domin sosai take
samun sauki, gobe ma xan sake xuwa in dubo ta,
kaji? Ya numfasa yace, amma Mami me yasa
za'a ajiyeta gida? Akaita asibiti mana, ko can
xariya xanyi magana da abokina, na tabbata xai
kula da ita tamkar ni. Pls mamy ki basu shawara
idan kinje goben. Tace ba ciwon asibiti bane,
shedanu ne suka tabata, kuma su iyayen nata
suna tsye neman magani. Kai ma kasan xa su
xauna ba. Ni dai rokona gareka shine ka nutsu
ka kwantar da hankalinka, ka fuskanci jarabawar
ki mai xuwa. Ka zama mai imani da Allah, shi
xai sa ya karbi addu'ar ka idan kayi mata. Ka
jini? Ya goge kwalla, yace naji mami don Allah
idan kinje ki dafa kanta ki karanta mata ayatul
kursiyu, falaki da nasi. Idan har gane ki ko da
baxa ta iya miki magana ba, ki gaya mata Al-
ameen dinta na gasheta, kuma xan ciga ba da yi
mata addu'a har xuwa lokacin da xanji muryar ta
a waya. Idanunwanta suka tara kwalla. Tace,
Insha Allahu xan gaya mata, tare da dukkan
abinda kace, muddin kayi min alkawarin zaka
kwantar da hankalinka. Da sauri ya amsa, Allah
nai miki alkawari mami, kinsan bani da wani
buri daya wuce in faranta maku rai. Tace, Allah
yasa dalilin alkawarin da kayi min Ubangiji ya
yayewa sakeena abinda ya sameta! Yace, ameen
Mami na! Dadina bai dawo ba ko? Bai dawo ba
sai zuwa jibi. Yace Allah ya dawo da shi lfya. Ta
amsa da ameen. Yace ki gayawa su iya su taya
mu da addu'a, Allah ya taimake mu. Tace, xan
gaya musu. Al-ameen, karka damu kaji? Murya
raunane ya amsa, to mami sai kinsake jina. Bata
iya kara komai ba ta aje wayar, domin muryarsa
kawai ta isa jefa mutun cikin damuwa. Taci gaba
da xama dauke da tagumi tunani na cin xuciyarta
fiye da tunanin mai kallonta. Haka al-amarin
yake wajen Al-ameen, domin dai rayuwa tayi
masa tsauri kuma hasashen rashin lfiyar Mam
yafi koma zama cikin ransa. Ba don yayi wa
mamy alkawari ba, da babu makwa zai iya baro
abinda yakeyi ya dawo ya ganewa idon sa
Mama, tana cikin mummunan hali. Kafin kace
kwabo, kowa ya fahimci samun sauyin sa, domin
ya yamutse ya wayi garim duk kuzarin da
nutsuwar sa basu jikinsa. Yana zaune addu'a
yana tafe addu'a, haka acikin aji, hankalinsa
yafi rinjayea ga addu'o'in da yakewa mama cikin
ransa. 12pm washegari lokacin ne motar Mami
ke fakin kofar gidan Uban dawaki. Yayin da
mama ke kwance rankas ciwon jiki, sakamakon
fadowar da tayi daga mota. Can da nan bata iya
motsawa, Baraka ke tare da ita tana zazzaga
mata nasihohi, duk da ta san bata sauraron ta,
sai dai ya zama wajibi gareta, ta kara gaya mata
gaskiyya. Mami tayo sallama falon ta shigo,
gaban Umma ya yanke ya fadi. Ta amsa tana
fitowa daga dakinta. Yake baki kawai takeyi,
amma zuciyarta ta shake take da takaici tare da
BAKIN CIKI mai tarin yawa. Ga wata kunya da ta
yo wa idanuwanta dirar mikiya, mai alaka da
ciwon dundumi. Sannu da xuwa Hajiya! Ta amsa
mata da fara'ar karfin hali. Ta nuna mata kujera
ta xauna, tana kara yi mata sannu da xuwa.
Sannan ta debo mata abubuwan sanyi masu
ruwa. Ruwan ta fara xuba mata, ta mika mata ta
sha. Suka gaisa cikin girmama juna. Ta kara
gyara xama, tace, sai kika ganni da rana tsaka
ko? Fuska kunshe da tashin hankali. Tace ke dai
bari, nasan kin sami sako maras dadin ji. Ta
kada kai dauke da damuwa. Tace naji sakon da
ya hani barci jiya, wanda ya sanya ni rama kafin
safiya. Ina jajantawa shi kansa Al-ameen da ya
sallama rayuwarsa kaf kan sakeena. Nayi kuka
da wadannan idanuwan nawa, don na tabbatar da
amsata ba alkhairi bace a gareni, domin komai
zai iya faruwa ga tilon da na, farin ciki na kuma
sanyi idona. Shi ya sa nace xama bai ganni ba,
tilas inxo in rarrashi sakeena, ta tausaya min kar
in rasa Al-ameen. Wadannan kalami sosai suka
sanya hawayen Umma suka tsinke nan take, ta
rasa me zata ce wa Mami ta sanyaya mata rai?
Dole tayi kuma domin dai bata da kwakkwarar
mafada, mama na nan akan bakanta babu sauyi.
Da kunnunwata ta, taji lokacin da take gaywa
Baraka tabbas zata iya kashe kanta, saboda
Danliti. Mami ta cigaba da fadin ki daina kuka
Hajiya, Baban ameer ya gaya min tashin
hankalin da kuke ciki, kukan bashi da
alfanu.......
HAUSA
BAKIN CIKI 2***4(TRUE LIFE STORY) umma ta
hare kwalla ta katse ta Tabbas mama bata da
lafia ciwon daya kamata mai tsanani ne maganin
Allah, dole kuwa in yi kuka , don mama ta dasa
mana BAKIN CIKIN da ban taba tunani ko
mafarkin irinsa ba daga ni har Abban ta mu na
cikin rudu tare da mamakin yadda wannan
alamari ya kasanze haka, hakuri zakuyi hajia
sannan ku taya mu addua mama kam ko ta so
ko taki doke ta auri Alamin, tunda zabin ta ne na
farko bamu muka cusa mata shi ba. Hasali ma
bamu san lokacin da suka hadu ba. tsabat rashin
kunya ce irin t yayan zamani da rashin sanin
mutuncin mutane. saboda. haja hajia karki damu
kuma dabarar da kikayi wa alamin tayi daidai
sai dai akwai sauran rina akaba domin fadar
kalmar ciwon ma ba zai bar shi yayi sukuni ba.
Tace zaifi sauki akan a gaya masa gaskiar
magana ni na dauki dawainiyar kwantar masa da
hankali kullun ya kira waya. Tace to shikenan
Allah yasa mu dace ta ce ina sakinar take mu
gaisa Ta mike tana fadin Taso muje in kaiki
kwance ma take bata iya tashi. Ah me ya faru?
ina fatan ba dukanta kukayi ba, ta ce Baban
Amira bai gaya maki bude mota tayi ta diro kasa
ba? ido waje ta dafe kirji ta diro daga mota?
tace ya wuce wai! zo muje ki ganta ta tashi
dauke da mamakin tana fadin naga abinda ya
ishe ni ni yasu, sakina da gaske take bata son
Alamin. suka cusa kai dakin, baraka dake zaune
bakin gado ta mike tana gaishe su. umma ta
nuna wa mami wurin zama a bakin gadon tace
zauyna hajia kinga idanuwan maras kunya ta
juya kan mama taci gaba ga hajia nan tazo da
kanta inkinga dama ki bude ido ta kudundune
kai cikin pilli mami ta dube su tace ku bamu
wuri hajia ita baraka suka bar dakin mami ta
karasa matsowa tasa hannu ta birkito ta kuka
taga tanayi tasa hannu biyu ta tallafo kuncin ta
ta sanyaya murya tace sakina dan dubeni kinji?
ta dago idanuwa jajur ta dube ta hawaye suka
wuce bisa kuncinta. mami ta kara goge su . ta ce
na san ba'a siyan so mama da yau nayi cinikin
sa ko nawa ne na siya wa alamin, koda zai
kasance zani daya zai rage min a fadin duniya.
amma kash hakan ba zai taba yuwuwa ba, sai
nayi imanin ko dan yaya ne kin san mahimamcin
rike alqawari me yasa kika dauki alqawarin da
ba zaki iya cikawa ba? me yasa kika yaudari shi
kika bari tsananin son ki ya zauna a zuciyarsa?
kina so ki kashe shi ne sakina? ki tausaya min
ana gaya masa sakon nan zuciyar sa zata iya
bugawa ya mutu mama. shi kenan na rasa shi
kuma ban da wani alamin na sonki mama sai dai
ayi zancen dan adam ssaboda haka ki gaya mani
abubuwan da yake miki wadanda baki so har
suka sanya ki tunanin fasa aurensa. wallahi nayi
maki alqawarin zan masa fada tare da lallashi in
kuma. gargade shi kinji? gaya man matsalarki da
alamin. hawaye suka ci gaba da ambaliya bisa
fuskar mama domin ko sunan alamin bata son
ana ambatowa tsawon lokaci bata tanka ba sai
kwarara ruwan idonta kamar zai kare mami ta
sake fadin da alama alamin dai bai maki komai
ba sakina tsuntsun son sa ne kawai ya tashi
daga kansa ya koma wa wani ko? ta kara aje ido
kasa mami tai wawan ajiyar zuciya idanuwanta
suka kawo kwalla baki man halacci ba sakina a
iya tunani na mutuwa ce kawai zata raba ki da
alamin shi yasa gaba dayan mu muka dora burin
mu a kanki. bamu da wami buri face Allah ya
nuna mana ranar da zki zama mata danmu sai
gashi dare daya kin juya mana baya. A tunani ki
kinyi daidai? baki gudun kar amana ta ci ki
sakina? kiyi tinani cikin natsuwa duk wanda ya
ha'inci wani Allah ba zai kyale shi ba. zan barki
kiyi tunani kan magana ta. idan kin canza ra'ayi
ki koma minna zuwa gobe Alamin yaji ki
hankalinsa ya kwanta kinji? yace in gaishe ki
kuma yace inyi maki addu'a. Ta taimaka mata ta
kwanta a hankali idanuwanta rufe suke yayin da
mami ta dafa kanta tayi mata addu'oi da alamin
yace tayi sannan ta kirata ta bude ido. nizan
koma sai najiki a minna karki bari shaidan ya
rinjayeki ki bar mai tsananin sonki cikin kunan
zuciya nakasa zaiyi kinji? ta lumshe idon a natse
mami ta wuce ta bar dakin umma ta shiga tare
da sallama ta nemi wuri ta zauna yayin da
baraka ta fice. ta basu wuri ta saurareki? tace
to! bata dai tanka ba sai kuka da zan fito. ma
nayi mata addua' kallo na ta dinga yi. da alamun
za'a dace tace kwarai da gaske bari in lallaba
hajia zan shiga wajen gwaggo sannan mu wuce .
to a gaishe ta da kyau Allah ya kiyaye hanya
Suka wuce suna fadin"Amin"har kofar gida tayi
mata rakiya,motarsu ta daga ita kuma ta dawo
gida dakin mama a koma suka taru da baraka
suka ci gaba da yi mata nasihohi tana
kudundune bata tanka ba,balle su gane me take
nufi,Awa guda bayan tafiya mami yaya. Abdul-
kadeer ya iso gidan daidai lokacin kuwa Abba ya
dawo gidan,yayan tare yake da dakarun sojoji
guda uku,duk suka fito,suka toge suna sarawa
abba,sannan suka gaishe shi tare da yayan suka
rankayo yana ruwan masifa, maganar banza
yarinyar nan take yi,mu makace ta kawo shi ko
mu muka hadasu wannan ai iskanci ne yanzun
nan zan wuce da ita shiya na dauko kuratan nan
su yi min gadinta a mota na ga ta inda zata
fito,Nonsense kawai" Abba yace kayi daidai
domin ni mama ta ginsheni ko ganinta bana
sonyi cikin gidan nan,saboda "BAKIN CIKI",abu
kamar al'mara yana so ya zama gaske yarinya
ta bamu kunya ta zubar mana da mutunci basu
ma san sun shigo falon ba sai da umma tace
maraba da babban yaya yace sannu umma
bamuyi sallama ba ko?raina bace yake ina
mama?tana daki ina fatan tafiya kazo yi da ita
sosai kuwa umma akwai kurata uku nazo dasu
wadanda zasu gyara mata zama muddin tayi
yunkurin bata mana lokaci tace yayi kyau wallhi
yanzu ma hajiyar al-amin ta bar gidan nan
bakaga uwar kunyar da ta lullubeniba na rasa
inda zansa kaina Abba yace tazo kikace"tana ma
cikin garin nan bata wuce ba"Abba ya nemi waje
ya zauna ya kama kai,shi kuwa yaya babba
dakin ya nufa kina jina baza ki fito ba"umma
tace da wace kafar zata fito bayan ta kusan
kashe kanta,yace kadan ta gani amma yau sai
kin bar garin nan ko za ki mutu!Useless girl!kina
nufin ki zubar mana da mutunci ko,baki. Kai
wannan matsayinba,I swear,kin ji na rantse"yasa
hannu ya fisgo ta da karfin sa yana fadin"stand
up my friend"ta tsandara kara mai garfin gaske
saboda gaba gabobain ta suka amsa suka kaiwa
kwakwalwar ta zuwa falon dole gabobin suka
loma aiki ashe dama wuri suka samu. Ya
dankwafar da ita bisa kujera tace wayyo na shiga
uku yace"No lokacin bai zoba tukuna sai kin ci
gaba da bijire wasu umma I'am telling you! yau
abuja zamu wuce ki zauna can, sai lazy doktan
ki ya dawo ai ke ki ka zabe shi tun farko so now
you have no reason ki ce kin fasa bayan kun
kusa aure ya dubi umma yaci gaba karki ji
tausayinta ta umma ki fidda ta a ranki har sai
tayi biyayya a gareku, Ta kada kai tace tuni
mama ta fice min a rai balle tausayinta ko alama
babashi cikin raina ka tafi da ita duk abinda ya
dace kuyi mata don ta gane kuskuranta yace
wannan dole ne Abba bari mu wuce umma ta
fara magana bari in hado mata kaya yayin da
abba da babban yaya kamar zasu cinye mama a
falo kuka take tamkar za a zare mata rayuwa
umma ta fito da jakar kayan ta wurga mata gyale
bisa jiki,yaya soja ya mike tashi karki bata min
lokaci taki mikewa yasa hannu ya maketa
sannan ya cafko. ta yana fadin zan iya karya ki
u know dat! gara ki shiga hankalinki bai sake
taba har kofar gida ita kuwa umma cikin sasa ta
shiga ta gayo masu za a wuce da mama don
haka suka yo waje ganin yadda za a yi saboda
suji dadin karaars wa. A gaban su ya cilla wa
kuratan daya zo da su ya ce kusa min ita a
mota! kan kace kwabo mama na cikin mota,
suka sanya ta tsakiya yayanta na gaba sanda ya
jefa jakarta a but yaya ya juya da sauri ya zauna
matsayin driver babu bata lokaci ya murza
mukulli mota ta tashi ya bar wajen, idanuwan
baraka suka cika da kwalla nan da nan ta fasa
kuka ta koma cikin gida da gudu. sauran matan
na ta fadin Allah ya kiyaye hanya ubangiji yasa
a dace. umma ta juya ta shiga gida su suka biyo
bayanta . ganin hankalin umma yayi mummunan
tashi yasa hajia gaje ta janye hajia hajo cikin
gida ta mika hannu suka tafa sannan ta tallafe
haba ido waje tace Ashe abin har ya girman
haka? wanan sojoji kamar an zo kama
gagararren barawo? ta ce ai kamar hakan ne
tunda ta gagari iyayenta. zamuga ikon Allah
yarinya na neman tayi wa iyayenta bakin cikin
daula, sun ga samu zasu ga rashi ai kinga haj
halima kamar ranta zai fita sai kace dole suka
sake tafawa haj hajo tace Hakki ne nake gaya
miki kadan ma suka gani badai danliti ta jajibo
masu ba? Allah dai ya kiyaye lalacewa! ta tabe
baki Nayaushe kuma? wai ance wa kuturu Allah
ya laance ka! shagonsa fa take zuwa tsinancewa
ai ba sai an tambaya ba! hajia hajo tace Allah
shi kyauta haj gaje ta amsa na gaba domin dai
wannan ya riga ya faru anyi abin kunya maga
yadda za ayi! sun jima suna yada labaran banza
da karairayi kai duniya ina zaki da mu? rayuwa
kenan uban dawaki da umma suna kallon ikon
Allah suna fama da BAKIN CIKI sai fatan Allah
ya musanya masu alkhairi Mama kuwa tun
isowarsu Abuja take kudundune cikin daki duk
hargagin yaya soja baisa ta dauki lomar abinci
tasa wa bakinta ba,al'amari ya daure wa anti
amina kai ta zauna ta siga yayyafa mata
nasihohi da rarrashi ko Allah yasa ta gane amma
ina Alla bai nufa ba tukuna shi kuwa soja babu
abinda ya dame shi cewa yayi zai fi kyau da
zata bari yunwa ta kasheta a yau hakan kuma
shi zai tabbatar masa ta cika mai kunnen
kashi,yasa kai ya bar gidan amma kuratan
sojojinsa na nan tsare da gidan bayan masu gadi
mutun biyu ke nan yanzu sun zama su
biyar,kafin yamma mama taci kukan daya fidda
ta daga hayyacinta bama ta jin tarin yunwar da
ke cikin ta saboda tsananin tashin hankalin da
take ciki domin ita kanta ta san ta shigo kurkuku
zai yi wuya ta kara ganin dan liti sai dai tunanin
ta bai yanke ba duk tsananin da zata shiga baza
ta taba auren wani ba dan liti ba.
BAKIN CIKI 2***5(TRUE LIFE STORY) Saboda
haka taci gaba da zama cikin kunci da yunwa
har bayan sallar isha'I yayanta ya shigo gida
kamar shi alamin ke kira wayar sa ta hau
bugawa falon kai tsaye kan wayar ya nufa ya
dauka yayain da malami ya sheko da gudu don
yi masa oyoyo.anti Amina ta biyo bayansa daga
jin muryar al'ameen kasa yana cikin farin ciki da
doki cike da zuciyarsa ina yini yaya,yace lazy
dokta ya karatu?"Yana yar dariya ya amsa
Alhamdulillahi ai na kira can minna don in
tambayi jikin mutunniyar sai aka ce min ta sami
sauki harma ka taho da ita, yace haka ne amma
kasan yana yin rashin lafiyar sai a hankali cikin
dan kankanin lokaci sai ta birkice bari in turo
maka ita,koda kaji sauyi daga gare ta kar ka
damu haka yanayinta ya sauya,jikin sa yayi
mugun sanyi duk a lokaci guda gabansa ya ci
gaba da faduwa murya dishe yace to yaya Allah
dai ya bata lfy,ya amsa da amin ya aje kan
wayar gefe ya amsa gaisuwar iyalinsa sannan ya
haye sama ya fada dakin mama yana shiga ta
kara kudundinewa cikin bargo yasa hannu ya
kwashe bargon ya watsar gefr yace tashi zaune
sai ga antin ta shigo ta matsa bisa shimfidar ta
birkito ta tana fadin yi mata a hankali ke mama
tashi kinji! Ta ciccibo ta ta tashi zaune kamar
wacce ta shekara tana ciwo saboda tsabar fita
hayyacin da tayi Tausayi ya lullube antyn a
hankali tace kinaji na? Ga alamin cen ya kira
waya don Allah ki fidda mu kunya ki tashi ki je
ki saurare shi badon mu ba sai don girman
Alkawarin da kika daukar masa kafin ya tafi
tashi kije kudinsa na bin iska kinji? Tamkar
antyn na magana da dutse don ko motsi batayi
ba sai idanuwa ta ke ambaliyar ruwan hawaye .
Haushi da takaici suka rufe yayanta ya daka
mata tsawa mai tsanani sai ta zabura bazaki
tashi ba? Alamarin ya kara kure su cikin
mamaki sukaji wannan kalmar ta fito bakinta
Nifa yaya ba zanyi magana da kowa ba Gaba
daya suka ware ido baki sake sai dai shi soja
baya tsayawa yana kallon raini don haka ya cira
hannu ya tsnke ta da wawan marin da yayi
sanadiyyar daukewar numfashinta karkaf,ta zube
sumammiya ya nuna cikin zafi yace ni zakiyi wa
rashin kunya ba na wasa da ke ni zan iya karya
ki wallhy anti amina da tuni take kwasar salati
tace ai maganar karyawa ta kare tafa suma
yallabai yanzu me za a cewa Al'ameen din Yace
ta mutu ni tayiwa rashin kunya bata isa ba
wallahi!Mtsw"ya ja dogon tsaki ya bar dakin
falon ya sauka ya dauki kan wayar ya kanga wa
kunnensa hello al'ameen naji na ya amsa ina
kinka yaya yace kayi hakuri da mama al'ameen
ya katse shi me ya faru yaya ina take yace ta
suma al'ameen kayi hakuri da ita domin mama
ta riga ta sami matsala....". Ya sauke salati ya
katse shi yaya bazan iya hakura da sakeena ba
kowane irin hali ta shi ina son ta haka koda
kuwa ciwon hauka ne ya kamata,Roko na gare
ku shine ku taimake ni ku kai ta asibiti don
Allah ko nawane zan kashe yaya please ku
taimake ni ya goge hawayen dake zuba bisa
kuncinsa yayin da jikin yaya soja yayi mugun la
a sar cikin taushin murya yace kar ka damu
al'ameen zamu kaita kar ka damu kaji sai da
safe. Ko kamin ya gama amsawa ya kife kan
wayar al'ameen sai da ya lalubi wuri don baya
gani yadda ya kamata sauran abinda ke zuciyar
sa kuwa biro na ba zai iya rubuce shi ba domin
al'amarin gagarumi ne maras misaltuwa sai dai
muce Allah ka kiyashemu sharrin masu sharri
amin summa amin Anti amina keta faman
neman ran mama shi kuwa yayanta bai sake
komawa ta kanta ba dakin sa ya shige don yin
abubuwan da yake ganin suna da muhimmanci a
gare shi ita kuwa mama zafin. Mari da tsananin
yunwa tare da tarin damuwa su suka taru suka
jefa ta cikin doguwar suma awa daya da rabi ta
kwashe babu motsin rai sannan ta dawo
duniya,ta fasa kuka tana fadin wayyo Allah na
zan mutu wayyo Allah! wayyo!" Nan da nan
hawaye suka tsunkewa anti amina saboda
tausayin da ya kamata murya na rawa ta
tarairayo ta tana fadin mama ki tausaya wa
kanki wannan mugun halin da kika jefa kanki
kin kuwa ga yadda kamannin ki suka sauya wane
irin masifar so ne wannan na bala'I. Akan da
namiji kike wahalar da kanki a banza a wofi ki
mutu ya nemi wata ya aura,wannan sakarci ne
mama kiyi wa kanki fada tun dare bai miki ba
sannan ki sani idan kika ci amanar al'ameen
Allah ba zai kyale ki ba,ta fizge jikin ta ta sake
faduwa bisa shimfida ta kara fasa kuka, malami
ya budo kofa ya shigo cikin sanyin jiki ya karasa
gun su yace mami uncle al'ameen ya bugo waya,
kafin anti amina tace wani abu tuni mama tayi
wuf ta tashi zaune cikin sababi take fadin ba za
a zo ba kaje ka gaya masa bazan dauki wayar ba
dole ne sai na aure shi nace. Ba zan aure shi ba
duk ku taru ku kashe ni kowa ya huta ta sake
komawa ta dase ciki anti amina da malami suka
saki baki suna kallon ikon Allah. Jimawa kadan
ta dube shi tace,Mu je falon." suka fice jiki babu
kwari,musamman Malami da sababin ya bashi
tsoro ba kadan ba.Anti Amina ta dauki wayar
tayi sallama,suka gaisa kafin yace, Ya jikin
sakeenar? Ta farfado kuwa? 'Ta farfado Al-
Ameen, har ta samu barci. Ya sauke
numfashi,'Allah ya kara mata lfy. To amin.yace
Anti,don Allah ki taimaka ki tuna wa yaya tafiya
asibitin.Ni ina ganin babu abinda zai gagari
asibiti koda matsalar junnu din ne, akwai ta su
irin gudumawar da zasu iya badawa. Please Anti
a kai ta asibitin a gwada." Idanuwan ta suka
kara tara kwalla,jin yadda muryar sa ke rawa,ta
tabbata hawaye ne ke zuba bisa kuncin sa.Ta
numfasa tace "karka damu Al-Ameen,duk wani
iya kokari ana yinsa.inshaAllahu Allah zai dube
mu ya yaye mata wannan lalura.ka kwantar da
hankalinka kaji? Ya amsa,Hankalina ba zai
kwanta ba Anti,har sai naji muryar sakeena da
bakinta ta gaya min tabbacin samun saukin.Ban
san halin da sakeena ke ciki ba Anti,kowa cewa
yake tana samun sauki,amma ni ban ji alamun
ba a jiki na.zuciya ta tana min sake-sake iri-iri
akan sakeena kuma tana nuna min ita acikin
mummunan hali.jin muryar ta ne kadai zata
warware min rudun dana fada.....Anti Amina ta
amshe,komai yayi zafi mgnin sa Allah Dokta.ka
tsaya wa addu'a kawai ita ce kadai zata taimake
mu.shi kenan Anti,ngd.Idan Allah ya kaimu gobe
zan sake kira ko na dace jin muryar ta.Tace To
Allah ya yasa a dace.ameen Sukayi sallama ta
aje waya ta koma bisa kujera ta kama kai hannu
biyu ta matse kwallan ta tace wannan masifa
Allah ka yaye mana,muryar mai gidan taji yana
fadin kema zai zauna kina bata lokacinki yau mu
ma bazamu ci abinci ba ke nan Ta share fuska
ta dube shi yallabai ba ka ki kalaman dokta bane
su suka kara dafani wallahi ya ya zamuyi da
yarinyar nan ne yace oho!ni kizo ki ban abinci
ina jin yunwa ta mike ta nufi kicin shi kuma ya
wuce ebur yana kiran malami ya sauko da gudu
yana amsawa gani dadi kaima yau baza kaci
abinci. Bane yace ai na ci dadi to koma daki
kayi barci sai da safe,ya juya ya haye saman
yayin da anti amina ta fito da jerin kayan abinci
bisa tire ta jera bisa tebur sannan ta zuba masa
taja kujera ita ma ta zauna yana ci tana maida
masa kalaman al'ameen sai da ta kare ya kurbi
ruwa ya dube ta, Yace ni kinga duk wannan
shiriritar ina yi ne kawai saboda hajiyar sa ta
roki a rufe masa amma ni ban ga dalilin yawo da
hankali ba yanzu ina fa'idar yin shirun tunda
hankalin sa da ake so ya kwanta bai kwanta ba?
mama ko zata mutu shi zata aura to me ne ne
abin jin tsoron gaya masa matsalar da ake ciki
banda shiriritarku ta mata,ta ce ai ba haka bane
yallabai kaga kuma shi kansa marafa ya goyi
bayan hakan"shi ke nan sai ki yi ta rarrashinta
kafin gobe idan ta amince yin maga da shi shi ke
nan idan kuma taki kya nemi wata karyar ki
shirya masa kinga sharo karya ya same mu ke
nan sai abinda Allah yayi ina amfanin sa Ta
numfasa tace al'amarin hakuri zamuyi tayi
rokona gare ka don Allah ka daina dukanta
wallahi taurin kai zai kara mata ido waje yake
magana muddin tayi min rashin kunya zan
tabbatar da na hukunta ta yadda ya kamata don
ni ba sa'an ta bane,you know that so ba zan
dauki iskanci ba kina iya hawa sama idan kin
kare maganar,tace ran maza ya huce yallabai ba
ina nufin wani abu bane yaci gaba da cin
abincinsa bai tanka ba ta zura masa ido tana
dan murmushi ta san halin yan kayan ta idan
kayi magana kaji yayi shiru to kaima ka tsuke
dan bakin ka ka kama kanka shi zai fi zama
alkairi. Garin Allah ya waye,baya ga sallah babu
abinda Mama ta aikata,ta yada kai bisa kafet
tayi lamo kamar sumammiya.Gaba daya ta
rame,fuskar ta ta tsuke duk ta bushe idanuwanta
sun kode sun firfito waje, sbd tsabar
kuka.Malami ya fito wanka ya tsugunna gabanta
yace "鐭沶a kwana Anti?Tayi banza dashi,ya zura
mata ido,Baki da lafiya ne Anti? Tunda ku ka zo
da Daddy baki min mgna ba. Ta ballo masa
harara,sai na tsinka mka mari ka sake min
magana! Ta ja tsaki,ta juya kan ta wani
gefen.Haushi ya kama shi,ya tashi ya ci gaba da
shirin sa. Wannan karon kam bai gane kan gadon
Antinsa ba. Me ke faruwane? Karfe bakwai daidai
Anti Amina ta shigo,tana shigowa Mama ta
rintse ido. Anti Amina ta dauko bisa kanta,ta
dan dafa ta na san ba barci kike yi ba,ki tashi
don girman Allah ga Dokta can ya kira. Kamar
yadda na gaya miki jiya so yake yaji muryar
ki,hankalinsa ya kwanta ko da gaisuwar sa ki
amsa,zai ji dadi Mama.
BAKIN CIKI 2***6(TRUE LIFE STORY) Ku da baku
wurin in kun amsa.To Mama ta amsa. Haushi
kamar ya kashe anti Amina.ta mike tsaye tace,
kar ki tashi Mamaa,idan kin sake jin nayi mik閾�
mgn akan Al-Ameen,duk abinda kika so kiyi
min! Mts....... Ta ja tsaki ta wuce. Mama ta
rakata da nata dogon tsakin anti amina ta waigo
rike da kugu ta zubo mata ido,lallai mama,ni
kike yiwa tsaki? Yayi miki kyau! Taja kofa ta
fice.kan wayar ta duka rai bace. Tace, hello!
Yace hello anti,ta tashi? Bata tashi ba dokta.
(nace"dokto ka fiya nace dolene?) "ba matsala,ai
barcin ma yana da amfani a gareta.zan sake
kira,ngd ant閾�. Cike da tausayinsa ta amsa,kar ka
damu sai anjima. To suka aje waya. Ta haye
sama shake da haushi,amma bata nuna wa
yallabai ba,don ta san ita zai tsatstsage danya.
Iyaka tace da shi bata tashi barci ba Wasa wasa
mama fa har ta sake kai bayan la'asar batasa
kwayar abinci a bakinta ba hankalin anti amina
ya tashi kwarai da gaske mama kam bata cikin
hayyacinta gaba daya ta galabaita yunwa na
neman tayi mata illa koma in ce tayi
matan,shiyasa tana jin waya na ta bugawa taki
dagawa don tasab mai kiran kuma bata da
abinda zata gaya masa a hakikanin gaskiya ma
hankalinta yafi rinjaye akan mama dake ta zama
da yunwa tun safiyar jiya Tayi fada tayi rarrashi
duk a banza misalin karfe biyar ta hada tea ta
shigo da shi dakin wai ko Allah ya bata sa'a ta
dan kurba me zata gani mama ke ta madedewa
tsakar daki wata irin farar kuffa na hauhawa bisa
bakin ta,tasaki kofin tea ta tarairayo ta tana
sallalami kinga irinta ko mama nayi nayi dake
kice abinci kin ki kina so ki kashe kanki a banza
a rude ta sake bazamowa falo ta dauki waya ta
kira wayar ofishin yaya abdul kadeea ta shaida
masa halin da mama ta shiga Amma yanzu za a
fara wucewa da ita asibiti nan take ya bata izini
yace zai same ta asibitin babu baa lokaci soja
daya ya sakata mota anti amina na tare da ita a
gidan baya tana shafa mata ruwa a fuska sojan
na jan motar an bata gado ga ledar ruwa na aiki
a jikinta, wucewa minti talatin yayan ya iso ya
same su jugum jugum,suna kallon ta rai bace ya
watsa hannaye aljihu yace dama haka take so ba
kuma shi zai taimaketa ba muddin tana motsin
rai al'ameen ne mijinta so idan ta farfado ki fara
gaya mata kafin na dawo zan koma ofis muna da
mitin,tace to adawo lafiya ya wuce cikin
kuzarinsa kuratan sa na biye da shi har bakin
mota suka koma sannan guda ya bude masa ya
shiga direban yaja suka wuce,anti amina ta ci
gaba da zama dauke da tagumi zuciyar ta na
mata saka iri iri haka wayar al'ameen ke ci gaba
da bugawa cikin gidan ba a dauka ba malami ya
shigo gidan dawo war sa ke nan daga maka
ranta,kicin ya wuce kai tsaye saboda yunwa ce
ta koro shi ya debo abinci ya zauna ya fara ci
waya ta sake daukar ruri ya mike da filet din a
hannunsa yana kara lomar shinkafa da salad ya
dauki waya baki cike da abinci ya ce hello hello
malami al'ameen ne ba kowa ne a gidan yace eh
nima yanzu na dawo school mai gadi ya gaya
min sun tafi kai anti mama asibiti wai ta suma.
Jikin al ameen Ya kara mutuwa ya ce gaskiya
Uncle duk ta rame kamar ba ita ba bata magana
sai kuka Tunda suka dawo da dadi ba ta ci
komai ba ko ni bata. Yi min magana ba sai yau
ta ce za ta mare ni idan na sake gaishe ta wane
irin ciwo take yi uncle hawaye suka tsunke wa Al
Ameen. Bai san lokacin da ya kife kan wayar ba
malami yabi ta hannunsa da kallo. Bai gane
komai ba dan haka shima ya aje ya dauki
abincinsa ya cigaba da ci yayi sallar magariba
dadinsa ya shigo yayi masa sannu da zuwa ya
amsa ya haye sama ya cire kaki yasa kana nan
kaya jaket da wando ya sauko ya shiga kicin ya
hada kayan abinci cikin dan matsakaicin kwando
ya kira malami yace kai mota ya jirashi can su
tafi asibitin,yace dadi yauwa uncle al'ameen ya
kira waya dazun me kagaya masa na gaya masa
anti ta sume kunje kai ta asibit to ke ka kirani a
mota ya dauki kwando yayi waje jim kadan
dadinsa ya fito suka tafi har zuwa lokacin mama
bata gane kowa yayan ta ya zauna nan zuwa
goman dare sannan suka koma gida da malami
Anti amina ta kwana tare da ita kiran asubahin
farko ta dawo hayyacinta ido ta zurawa anti
amina kafin ta fasa kuka anti amina ta matsa
gare ta ta dafa ta saman goshinta tace me yasa
kike wahalar da kanki bayan ki na sane da cewa
aure tsakaninki da al'ameen babu fashi,ta goge
hawaye wallahi wallahi anti bazan. Taba cin
abinci ba har sai yaya ya maida ni inda ya
dauko ni kinji kuma na rantse bazan kaffara
ba,baki sake take kallonta tama rasa ta cewa
mama ke ci gaba da fadin na gwammace na
mutu da a raba ni da dan liti sabo da haka mu
zuba nida yaya idan jan idonsa zai sa in daina
son dan'liti anti amina tace gadkiya ne kuma
yanzu kika tabbatar min kinyi nisa ka kya jin
kira To abinda zan gaya miki shine ki guji bacin
ran iyaye rayuwa ki ba zatayi kyau ba muddin
kika bar mahaifanki da BAKIN CIKI sannan dole
ki fuskanci kalubale tunda kika ci amanar dokta
bazan rufe miki ba mama koda nan gaba in ta
Allah ta kasance zaki tuna dani kice na gaya
miki a asibitin nan wallahi yadda kika sanya
al'ameen kuka da radadin zuciya kema sai dan
liti ya dandana miki fiye da hakan Da namiji ne
fa ki bari ya gama shanye romon da yake hange
a jikin ki kisha mamaki daidaiku ke da rikon
amana su ajiye ki ke kadai suna girmamaki a
matsayin matar sunna mai tsananin kamanta
gaskiya shi ne zai ce kik zai kara aur amma
sauran shagalinsu suke sha a waje su barki hoto
a gida balle wannan Dan'liti daya sami shaidar
banza don haka kibi a hankali mama so ba
hauka bane tace na ji kin fada amman yarda ba
dole bane ko ashe kin gane domin ni duk abinda
mutun zai fadi akan Dan'liti ina daukar sa a
matsayin hassada ina abin hassadar ga Dan'liti
koda ban san shiba labarinsa ya gamsar dani
kuma na tsane shi idan kin tsane shi ki daina
maganar sa don zai sanima in tsane ki Ta ware
ido sosai tana kallon ta ban yi mamakin jin
kalamanki ba tunda kika iya shafawa idanuwanki
toka ba kya ganin mahaifanki ki balle ki saurari
nasihohinsu gareki kin ban kunya mama ban
taba zaton wata rana mai kamar wannan zata
zoba in sha Allahu zan rarrashin dadin malami
ya kyale ki duniya ta koya miki hankali,ido cikin
ido ta bata amsa zaifi kyau idan kika yimin
wannan kokarin haushi yasa anti amina ta mikie
ta fito babban falon asibitin tayi zaune har aka
kira asalatu tayi alwala tayi sallah ta je ro
addu'o'I tare da rokon Allah ya sanya wa
al'ameen dangana idan har ya rasa mama Cikin
shigar kakinsa tsaf ya shigo asibitin tare da
malami shi ma sanye da kayan makaranta
kuratan sojoji biyu na take masa baya dauke da
kwandon kayan karin kumallon safe a babban
falo ya same ta zaune bisa dardumar
sallah,malami ya fara isa gun ta ya gaisheta ta
amsa sojojin dake biye suka kwashi gaishuwa
yayin da ta miki ta tarbi yallabai amma fuskarta
babu walwala sannu da zuwa tace dashi ya amsa
yauwa ya dai jikin na ta, tana ciki shiga ka
ganta ai ta farfado tun asuba,ko?suka jera zuwa
dakin tana gaishe shi jin muryarsa yasa mama ta
runtse ido ya tsaya kanta yace ki daina matsr
ido nasan kina ji na ina fatan amina ta gaya
miki sako na saboda haka ina son ki gane
wannan sakarcin bazai firgitani ba abinda na
sani kawai al'ameen ya dawo a daura maku aure
middin kina numfashi sauran shawara ta rage
gare ki, Anti amina dake ta kallon ledar ruwa
tasa hannu ta dago igiyar tabbas abinda take
zato shine din. Ruwan ba a jikin mama yake ba
cirewa kikayi mama, ta juya kan yallabai tayi
masa kuri ka gani ko ta cire ruwan yaya ya kawo
iya wuya kamar ya nannausheta yake. Ji cikin
fushi ya juya ya fita anti amina tace da kanki ki
ka kama drip din ki ka tuge,sau dubu aka samin
sau dubu zan cire me ruwanku dani tunda baku
kauna ta tana rufe baki yayan na shigowa da
wasu nosis biyu amma abin karin haushin mama
taki yarda su mai da mata ledar ruwan nan basu
san lokacin da yayanta ya cire hannu ya tsinka
mata mari ba,sai da bakinta ya tsatso jini
saboda haushi da takaici kafin ayi haka ya bar
dakin anti amina ta biyo bayan sa ta bar nosis
na rarrashin mama yana shiga mota ita ma ta
fada ciki tace kayi wa girman Allah yallabai
karkayi fushi ka tsaya ka saurareni kar ki min
magana akan wannan wawayar yarinya," I have
finish with her, dama munyi waya da abdul-
kareem sun ce za su zo harda abdul-rahman so
suna zuwa zasu wuce da ita daga can su bata
kudin mota ta wuce fandogari zan iya kashe
yarinyar nan idan ina ganinta, tace wallahi ni ma
shawarar dana ke son in ba ka ke nan idan kaji
maganganun da mama ke fadi zaka tabbatar da
tayi nisa bata jin kira sai addu'a kawai zamu
zauna ne tana bamu wahala koda yaushe mu ma
asibiti a aikin banza?ba zai yuwu ba a irin take
taken ta tana gab da fara sufa mana zagi ku
kyale ta da dan-litin shi ne zai koya mata
hankali,yace ai an gama dokta zuwa kice ya
sallame ku kawai zan sake kiran abdul- kareem
din in ce su dame mi gida ta numfasa don murna
kafin tace,"!58,naji dadi yallabai Allah shi
taimake ka ita kuma ya shiryar da ita amin ga
break fast can kije kici ki kyale ta bari mu kai
malami school gada can zan shiga ofis to a
dawo lafiya amin,ta fito sannan sojojin suka
taso daga. Inda suke tsaye tare da malami suna
jiran su babu bata lokaci suka bar harabar
asibitin anti amina ta koma ciki tace wa nosis su
kyale ta su tafi abinsu guda tace oga zaiyi fada
madam idan ya shigo. ni nace ku tafi kawai abin
ku ba mu muka kawota ba,kuma mu zamu biya
bill ku wuce kwai ba wani abu"nosis suka wuce
da mamaki anti amina ta hada abin kari ta hau
ci bata sake komawa ta kan mama ba har likita
ya shigo misalin takwas da rabi na safiya anti
amina ta maida masa bayanini yallabai likita
yace a'a baza ayi haka ba nan ya ja kujera yayi
ta rarrashin mama,tayi shiru kamar da gaske
sauraronsa takeyi da kansa ya nemo jijiya ya
maida mata ruwan amman me yana gamawa bai
ko bar dakin ba ta sa hannu ta zare ta aje masa
robobin sa haushi ya shake likita ya jima yana
kallon ta sannan ya dauki (file)din ta yayi
rubutu,ya dubi anti amina yace kuna iya tafiya
gida madam da alama ba zamu shirya da
sakeena ba tace ai dama na gaya maka kayi
hakuri dokta kan ta tayi mawa tace ba wani abu
shawa ta kawai ia ce ku kyale ta ta auri wanda
ta zaba may be rabon wahala ke kiranta,tace
sosai kuwa dokta mun gode ji suka yi mama taja
wani shegen tsaki duk suka bita da kallo likita
yace I'am sorry for yau,a tunaninki kinyi abu Mai
kyau ke-nan? NO,ba hk rayuwa take ba. Ya
kamata ki rinka kulaw. Ya sa kai ya fice.Nosis
din sa suka take masa baya,kowanne su babu
wanda bai shak鐭� taikacin Mama ba. Tana hada
kaya direba na shigowa, yaya ya turo shi,idan
anyi sallamar ya kaisu gida. Shi ke nan kaya sun
tsunke karkashin kaba. Ya kwashe kaya,ta dubi
Mama tace, ki na iya tasowa muje gida,idan kin
so.Ta yunkura ta tashi,Anti Amina bata
saurareta ba ta wuce abin ta. Da kyar ta sauko
daga gadon,wani mugun jiri yayi tafiyar ruwa da
ita,ta koma dabas! Ta zauna.(maganin mara jin
magana,yarinyar nan tana ban haush鐭�! Mts!) Tafi
minti uku dafe da kai,sannan ta sake mikewa ta
daddafa bango ta fito tana layi. Kowa kallon ta
yakeyi,musamman Noisis din da komai ya faru a
gaban su,ai nan take aka shiga maida labari. A
mota ta same su. Anti Amina na gidan baya,duk
ta kulle sakatun kofofin biyu,saboda haka dole
Mama ta bude murfin gaba ta zauna tare da
direba. Ko a cikin gidan ma,babu mai kula
wani,hasalima Anti Amina kwanciyar ta tayi
tasha barci,bayan ta yi wanka ta sauya kaya.Ita
kuwa Mama taci gaba da sanya tsananin kunci
cikin ranta,ji take kamar ana hura wa zuciya ta
wuta.Tsananin son ganin Dan-Lati da kewarsa
suka hana ta sukuni. A yadda jiri ke dibar ta,sau
uku tana fitowa waje ta tsaya wai ko zata ga
lakwa-lakwa ta sulale ta gudu.Amma ina,ko
fuska babu a wajen kuratan nan,balle ta sami
hanyar fita.Don haka ta kifa ciki tsakar falo,tayi
ta sharara kuka har azahar,bata san lokacin da
barcin wuya ya sace ta ba. Anti Amina ta sauko
tayi girki ta gama bata farka ba.Dawowar
Malami ya kwarara sallama',shi ya tashe ta,tayi
doguwar mika tare da hamma mai kunshi da
yunwa da wahalar duniya. Ta tashi zaune taja
jikin ta,ta zauna ta jingina da kujera,wucewar
'yan mintoci.sannan idanuwan ta suka kwalli
agogo.karfe daya hard a rabi. Da kyar ta yunkura
ta tashi ta haye sama a wahale,tana shiga dakin
ta zube a kasa,sbd babu karfi a jikinta.Malami
da ke cire kayan makaranta,ya zubo mata
ido.yana so ya gaisheta yana jin tsoran mari. Ya
sauya kaya,ya fice daga dakin,wajen Momin sa
ya shiga idanuwan sa cike da damuwa. Ya zauna
kusa da ita,tana kallon yadda ran sa ke bace,don
hk ta rungumo kafadun sa tace, "Yaya dai,yunwa
akeji? Ya kada kai yace, Momi Anti fa zaa
mutu,ku maida ta asibiti.Allah bata warke ba. Ta
zura masa ido,tace,Ba laifin mu bane Malami,a
gaban ka ai kana kallo taki yarda asa mata Drip.
To ya take so muyi?" Yace, kawai ku kira mata
abba yayi mata fada. Wlh bana son Ant閾� ta mutu.
Ina son ta Mom鐭�,me yasa take ta wannan ciwon
ne? Ta kara rungume shi tace, kowa ma nason
Antin ka Malami,kuma babu mai son mutuwar
ta,Matsalar taki cin abinci ne,shi yasa ka ganta
haka. To sbd me? Tace kaga ka yi shiru da bakin
ka,kai yaro ne ba ruwanka da maganar
manya.kai da鐭� idan ka yi sallah ka roki Allah ya
bata lafiya. Yace, To Momi,tace. Maza kicin ka
zuba abincin ka.'ya fice tana kallon sa. Zuwa
karfe biyar Mama ta sake fadawa cikin
mummunan hali,bata gane kowa. Anti Amina ta
rasa inda zata sa ranta,domin ta rasa yadda
zata yi da Mama don ta ceto ran ta. Ta sauko
falo da nufin kiran wayar ofishin yallabai.
Shigowar mota harabar gidan,shi ya dauki
hnklnta ta zage labulan taga ta daga.Motar
Abdulkareem ke fakin a harabar aje motoci,ta
dawo da sauri ta nufi kofa cike da farin ciki da
baya misaltuwa. Ta bude kofar tayi waje,farin
cikin ta ya karu,ganin har da Abba acikin su.
Sannun ku da zuwa! Ta isa wajen tana fadi. Duk
suka amsa,sannan suka rankayo cikin gida.
Malami ya rugo ya rungume Abba. Bayan gaishe
gaishe suka tambayi Mama. Tace,tana daki babu
kyan gani,nama fito ne,in kira dadin Malami ko
za mu sake komawa asibitin ne,sai gaku. Wlhy
Abba taki cin komai tunda suka zo garin. Ban jin
tasa ruwa a bakinta,wannan masifa dame tayi
kama? Duk suka yi shiru sbd takaici,babu wanda
ya tanka har Anti Amina ta mike ta kawo musu
abincin da ababen sha. Ruwa kawai suka sha
Abba. Ya-ce, muje mu ganta. Duk suka rankaya
saman. Yanayin da suka riski Mama,ba karamin
daga hankulan su yayi ba. Abba ya zura mata
ido,idan da zai hadu da ita a hanya,ba zai shaida
ta ba,sbd sauya kamannin da tayi,sbd tsananin
son cikawa al-ameen alkawari ko alama bai bar鐭�
tausayinta ya rinjaye shi ba. Don hk ya dubi
sauran yace,wannan ba shi zaisa mutuncin mu
ya zube a idon duniya ba.sbd hk zamu koma da
ita asibiti,ta farfado.sannan mu wuce da ita
fandogari. Farin ciki na Mama ta mutu a dakin
nauran al-ameen wanan shne kwanciyar hnkli na.
Ku dauko ta mu tafi.
gaskiya ne abba shi kuwa yaya abdul-rahman
abin ne ya zame masa banbarakwai don bai taba
zaton labarin da yakeji abin ya kai haka ba duk
da yana jin zafin abinda mama tayi ,halin da
idanuwansa suka gane masa mama a halin yanzu
kwarai tausayinta ya kwanta a zuciyar sa shi ne
ya fara kai hannu ya ciccubo ta suka taimaka
suka sauko da ita kasa kamat matacciya,da kyar
likita ya karbe ta sai da yan uwanta suka yita
rarrshinsa sannan ya bata gado yayi mata duk
abinda ya dace. Acan yaya abdul- kadeer ya
same su bayan sallar magariba kafin ayi issha'I
suka rankaya gida akabar anti amina tare da
ita,kusan kwana sukayi shawarwari akan
al'amarin,kwana daya da wuni mama na kwance
magashiyan ledar ruwa goma sha tara ta
shanye,ana shirin daura mata na ashirin sannan
idanuwanta suka fara washewa ta gane inda take
hada ido da abba tare da karkaf yan'uwanta bai
haifar mata da wata nadama ba illa kuka da ta
fasa wai don su tausaya mata babu wanda ya
tanka mata wannan itace shawarar da suka
yanke babu wanda zai sake bata bakinsa don yi
mata fada amma zata sha mamaki ranar da
Allah ya yasa al'ameen ya dawo kasar nan,babu
wanda yace cikanki har ta gaji da shashekar
kukanta. A zaton ta shirun na su alamma ce ta
saduda ma'ana sun rasa yadda zasuyi da ita dole
suu sa mata ido anti amina ta fara bata ruwan
lipton tana kurba da kyar take iya hadiye shi
gaba daya Makogwaronta ya farfashe kafin gari
ya sake wayewa mama ta samo kanta misalin
goma da rabi kawai ganin su tayi sun shigo suna
gaya wa anti amina an sallame ta zasu wuce
yanzu bata yi mamakin jin haka ba don haka ta
amsa da to,Allah kara lafiya ita kuwa yar gigalar
murna ce fal cikin ta jin za a wuce da ita
fandogari nan da nan suka kwashe kaya,yaya
abdul-kadeer ya dauki matarsa,mama kuma tabi
ayarin komawa gida a minna suka yada zango
suka ci abinci tare da yin sallolin azahar da
la'asr in banda su ameera babu wanda mama
tayi magana dashi domin anti rabi ma ta sauya
fuska al'ameen dintama bai sami kulawa ba
suna idar da la'asar yaya abdul-rahman ya jawo
matarsa daga inda ya aje ta aka maida jakar
mama ciki ita ma ta fito ta shige gidan baya
abba na tare da karamin yaya a gaba Shi ya jasu
a hankali xuwa fandagori. tun daga kan kwana
hankalin mama ya soma kwantawa, domin dai
idanuwan ta sun hango wanda take son gani.
yana zaune bisa benci a kofar shagonsa, yayi
murmushi itama ta sakar masa nata. har motar
ta wuce, ba su daina leken juna ba. sai da ta
daina hangensa, sannan ta zauna sosai kirjibta
nata bugawa, ji take kamar ta balle murfin motar
ta fice taje gunsa. ya mikawa ayuba hannu suka
tafa. yace baka da kyau! Yace karya kak don
ubanka, kalle ni sama da kasa! ba kyawun sura
ba, ina nufin.... ya kai masa naushi a kafada, shi
ya katse shi. zan ci..... kai! ka kiyaye ni fa wlh!
me na gaya maka? yadda suka dauke ya ahaka
za su dawo min da ita. wahalar banza sukeyi
sakeena mallaka tace. yace ranar da Allah kuma
zai kama. ayuba baya wajen, duk ka gama
iskancin ka. ya ballo masa harara yace, to ko ka
na wajen me zakyi? kai ma ka ji da naka, don
ubanka. Menayi? ni nakai ka iskanci a garin
nan? dama wane kai, amma sannu a habkali
xzaka biyo ni mujera hanya watakila ma ka xarta
ni. ya tabe baki yace Allah ya sawwake, kai din
ma so nake na janyo ka baya. ka auri yarinyara
nan, ka manta da kudinrinka na wulakantata. ya
dafa shi yace ka dan kula da shagon, bari na je
nemo gasasshiyar kaza. kasan dole anjima ta zo
鎷� ya xuba masa ido kawai, bai ce masa komai
ba. yayi dan saurayin murmushin. ya mike ya
fada motar sa yayi birnin gwarin tsinke. kai
tsaye mama dakinta ta shige. umma bata
gasganta idonta ba, irin yanayin da taga mama
saboda haka tatashi tabi bayanta. Kallo daya
tayi mata taji kanta ya ci gaba da sarawa, wani
kululu ya daure xuciyarta, idanuwanta suka tara
kwalla, saboda tsabar BAKIN CIKI. Ta jima kafin
tace, Mama kina da hankali da tunani kuwa? Ji
tayi an dafata ta biyu, muryar Yaya abdul rahma
ke fadin, baki da lfya Umma, karki daga
hankalinki, abba yace ki fito ki kyale ta. Ya
kamo ta suka fito, jiri na dibarta, shi ya sa tace
yawuce da ita dakinta. Abba ya taso ya biyo su,
yayin da take kwanciya a gado. Gefen gadon ya
xauna yace, bai kamata ki bar ciwon ki ya tashi
ba halima, kin ji dai abinda Dr. Ya fada, jininki
ne ke hawa saboda damuwar da kika sanya a
ranki. Ki hrk kawai. Tace, ba alamun yin nadama
a wajen Mama, ni kaina, nasan haka,amma
shawarar da mu ka yanke da 'yan uwanta shine
mu sanya mata ido tayi shirmen ta, sai ranar da
Al-ameen ya dawo xata gane mu ma ba muyi
nadama ba. Abdul yace saboda haka ki kwantar
da hankalinki, ISA sai dai mama ta mutu a dakin
Al-ameen, ba zamu ji kunya ba. Su Yaya babba
da Iyalnsu duk sunce gaishe ki, sai sun xo. Tace
ina amsawa, Allah ya taimake mu, suka amsa
ameen. Abba ya dube shi ya cigaba, kai ma ya
kamata ka hanxarta wucewa yamma tayi sosai.
Umma ta amshe, ba xai bari xuwa gobe ba?
Yace, akwai aiki Umma, yanxun nake so na
lallaba. Ta dan kada kai. Tace, to Allah ya Tsare
agaida min safiyya da kyau. Zata ji, ki daina
damuwa Umma, komai xai wuce da yardar Allah.
Ta amsa da kai, tana fadin shikenan abdul, Allah
yayi maka albarka. Yace amin. Ya wuce cikin
hanzari. A tsakar gida ya hadu da su Haj.Hajjo.
Ashe da gaske ne kun dawo? Yara ke fada mana
yanxun. Yace eh, nima xan wuce kd kenan. Gaba
daya suke to Allah ya tsare! Ya amsa yayi gaba
abinda, su kuwa ciki suka kutsa kai dakin
mama. Kwakwazon surutun su ya sa Abba ya ta
so fito. Sannuku da dawowa Yaya. Yace yauwa,
ga haliman can a dakin ta. Haj. Hajjo tace, muna
nan mun ganin ikon Allah. Mama ta dawo kashi
ba rai? Yace haka take so, ai ku daina bata
bakinku, kowa ya sa mata ido. Haj. Gaje tace,
lallai kam wannan al'amarin sai ido. Allah ya
kyauta. Ameen. Suka fice tare suka koma dakin
Umma, suka isheta da surutu. Duk iya kokarin
mama na son fita a wannan daren abin ya
faskara, domin dai Abba ya kasa ya tsare a falo
har goman dare ya garkame kofar ya shige
dakinsa barcinsa. Allah da ikon sa, abba bai
xare mukulin ba, domin bai taba tunanin Mama
xata iya aikata wani abu a wannan tym din ba
lallai abba bai san Mama ta wuce tunaninsa ba.
Yana bada baya, taji motsin rufe kofarsa ta yi
wuf ta mike, takalmanta a hannu tare da
mayafinta. Tayo sanda ta fito jim, tsakar falon
bata ji mtsin kowa ba, sannan ta karasa kofar ta
bude ta cikin nutsuwa ta sulale ta fice. Can ma
kofar sassan hka ta bude ta, ta wuce zaurukan
gidan, ta zare sakatun ta bude ta fita ta maida
kofar ta sakaya. In bakayi bani wuri! Ta callah
da gudu bata ko jin rashin karfin jikinta, sai da
tayi rabin tafiya, sannan ta tsaya ta sa
takalmanta ta yafa gyalen tana ta xuba haki, ta
dau hanya babu jama'a sosai. Gata nan ga ta
nan har kofar shagon dan gogan. Ya tare da dije
a kofar shagon bisa banci, ta cukuikuye shi
kamar na goye fadi yake, wai dan Ubanki dole
ne? Kin fa matsa min da yawa, xan ci ubanki a
daren nan, in ga mai kwatar ki! Kawai ganin
mama yayi akan su. Ya banbare dije ya ture
gefe, bai bata lokacin ya daga kanta ya shige,
shagon yana jan tsaki. Mama ta daga itama ta
bishi. Dije kuwa mikewa tayi ta kakkabe jikinta
ta wuce tana kwafa. Ya hade rai a kujera, bai ko
kalle ta ba. Ta matsa gare shi murya sanyaye
tace, fushi kayi danliti? Ni ban yi fushi ba sai
kai? Ina can naki ci na ki sha saboda kai. Ashe
ka na nan ka tare da wata? Dubi yadda na rame
na sauya kamanni, saboda tunanin ka Danliti.
Bai kamata ka yi min haka ba. Ya dago
idanuwansa farare sol! Sunji kwalli ya dubeta, ko
mai nai miki ai kekika jawo, kinbi 'yan uwanki ki
manta da ni, ba dole in sami wata ba! Tun
yaushe kuka shigo garin nan? Nayi ta xuba ido,
amma ban ganki ba, me kike tunanin xan dauka?
Kafin tace wani abu ya fizgo hannunta xuwa
daki, yana kara fadin, idan karya nake yi, xo
muje ki gani! Ayuba dake kwance bisa katifa
yayi firgigi ya tashi yana kallon ikon Allah.
Ledar kaji ya janyo ya xaxxage su. Yace me kika
gani nan? Saboda ke na tafi har birnin gwari na
siyo miki gashin xamani kajin turawa. Dubi nan
juice ne kala-kala har sanyi su ya fita, baki xo
ba. Ba dole in yi fushi ba, in saurari mai so na!
Ta sauke numfashi, idanuwan ta taf! Da kwallah,
ba laifina bane Danliti, baka san irin bakar
wahalar da na sha ba, don kawai su dawo da ni.
Sau biyu ina kwanciya a ascibiti, dube ni da
kyau, kai kanka kasan ba haka nake ba. Amma
kayi hkr, tunda kana ganin kamar da gangan
nayi, ka hkr? Ya xura mata ido jim, sannan yayi
dan murmushi ya ware hannayensa yace, to
oyoyo! Ta sa hannaeyanta ta rufe fuska. Yace
kunya? Ashe baki so na, lallai na yarda ni kadai
nake haukan sonki. Yana rufe baki ta matso da
sauri ta rungunme shi. Ayuba, yayi gyaran
murya. Mama tayi wuf ta rabu da jikinsa. Ya
dubi Ayuba, yace malam ka fita ka bamu wuri!
Yace, ai ku ya kamata ku koma daga waje anan
nake so mu xauna, fita ka bamu wuri don Allah,
shago fah abude yake, ya yankura ya tashi yana
fadin, gaskiyya kuyi sauri ku gamacin kazaraku,
barci nakeji. Ba ruwanka wannan. Ya fice yana
waigen Danliti yana masa ishara da idanuwansa
dauke da gargadu, wanda shi kansa ya gane
nufinsa, shi yasa yake wani irin mur0ushin na
iya shege. Yana fita ya dubi Mama suka hada
ido dukkan su sukayi murmushi, sannan ya
kamo kafadunta yace, gashi dare yayi, amma
dole ki xauna ki cinye kajin nan, domin saboda
ke na siyo su. Ba tace komai bam ya xaunar da
ita gefen katifa, ya jawo kayan kwalama, ya baje
mata kajin, yana bata abaki, tun tana jin kunya
har ta saki jikinta, tana amssa sosai tana ci,
suka ci suka sha suna hirar bayan rabuwa. Bayan
sun kare. Danliti ya dubi agogonsa ya ce
shadaya da kwata yanxu, ya kamata kije gida
ko? Sai gobe, ina fatan xaki rika cin abinci don
ki gyagije kyanki ya dawo kamar da. Kinji ni?
Tace, naji kuma xan kiyaye, amma don Allah ka
daina bari 'yan mata na xuwa gunka, watarana
xamuyi dambe da su wlh, kaji na rantse. Ya
kyalkyale da dariya son ransa kafin yace, xaki
kuwa sha duka, don dai nasan sunfi karfinki.
Wannan jikin naki rugu-rugu babu kwari. Ya fadi
yana mammatsa hannayenta da kafafuwanta. Ta
yankura ta tashi tana cewa, haka kake gani, ka
maida abin wasa, zaka sha mamaki. Shima ya
mike ya kamo yatsunta, yace karki damu, ke
kadai nake so, ko da damben ya kama kuyi, xan
shigar miki balle ma banda lokacinsu. Ke me xai
dameki? Tayi murmushi, tace, to shikenan sai da
safe. Ya sumbaceta yace, muje na rakaki. Suka
fito yana rike da hannunta, tayi wa ayuba
sallama suka wuce. A kofar gida suka fuskanci
juna, tallafo kuncinta ya xura mata ido, yace
karfa ki damu da ganin Dije tare da ni, wlh ba
sonta nake ba, kawai ta matsa min ne dole muyi
soyayya, amma xan dauki mataki akanta, tinda
ta fara bata miki rai. Tayi murmushi, tace,
nayarda da kai, ina fatam Allah ya yarda mana,
ya bamu nasara abinda muka sa gaba. Da sauri
ya amsa amin sakeena. To sai da safe nagode,
wannan karon abin ya cigaba akan labbanta ya
sumbace ta. Ta juya da sauri, ta tura gida ta
shige ta maida sakatu. Danliti ya runtse ido ya
jinjina hannayensa, shege ni! Ya juya yana
takawa dda+dai kamar wani kasaitaccen
basarake. Mama kuwa sanda takeyi, kamar
barauniya ta turo kofar fa'aar dshigo ta mayar d
hankali ta kuleta, ta fada gado. Tana jan mayafi,
taji a; ttay bude kofa, tayi tsaye jim, sannan ya
mayar ya rufe. Muryar umma taji tana fadin,
menene alh.? Yace kamar motsin naji ana taba
mukulli.. Tace Innalillahi an shi ne? Yace amma
ban ga kowa ba. Ya dubi agogo, karfe sha biyu
saura kwata, dare ma bai yi ba sosai, to Allah
yai mana tsari da sharrin masu sharri. Yace
amin, je ki kwanta. Cikin fargaba suka bar falon.
Mama ta gyara kwanciya tana gyatsar naman
kaxa. Dan kanta tace kwanta naman kaza. Tayi
tunani Danliti har barci ya kwashe ta, shi take
marfi yana sa mata naman kaza abaki. Da safe
tayi wanka, duk 'yan ciwukan da suka rage ba su
warke ba, ta goga musu mai, ta shafa hoda ta
sa atamfah riga da xani, nan da nan ta dan yi
fasali, duk da cewa akwai rama sosai a jikinta.
Yau kam tayi dan kyan gani, ta fito falo wajen
Umma cikin kicin inda take aikace aikacenta,
tace sannu Umma ina kwna? Ta juyo da sauri ta
dubeta sama da kasa, tace kalau na kwana. Ta
kara matsowa tace, bari in gaida Abba, sai in xo
in tayaki aikin. Bata amsa ba ta fice, ta bita da
kallo sannan ta kada kai tace, Allah ya shirya.
Dakin Abban tayi sallama, ya amsa ya bita da
kallo, ta karaso gunsa ta tsugunna, ina kwana
Abba? Yace Kalau, ta dan dube shi, amma bata
kara komai ba, ta mike tayi waje ta koma kicin:
Umma me xan tayaki? Tace ban so, koma
dakinki kawai. Saboda me Umma? Ai ban isa na
fadi ko saboda mene ba, tunda kin xama
shafaffiya da mai. Je ki kawai ki sha xamanki.
Kai tsaye kuwa ta wuce daki abinta. Tana fadi
cikin ranta, kya gama girkawa, mu zo mu jajja
(hmmm mama tayi nisa walle). Kan Umma ya
sara ganin yadda mama ta wuce ko ajikinta,
bata damu ba. Mamaki bai gama kashe Umma
ba sai da ta hange ta kicin din tana diban abinda
take son ci. Tana kallo ta koma dakinta ta cinye,
ta maida kayan kitchen ta fito. Haushi ya kume
Umma bata san tym din da tace, Uban wa kika
ajewa kayan ya wanke miki? Tabbatacciya! Ta
dan bata rai ta juya ta kwaso kayna ta wanke.
Karfe 9 abba ya fita harkokinsa. 9:30 mama figi
gyale tayi waje, Umma nace na wanka. Ta sha
hirarta wajen Danliti har 12pm sannan ta
tsallaka ta gangara wajen Baraka. Sosai taga
sauyin fuska wajen Inna saude. Sam abin be
dame ta ba. Suna kebewa da Baraka tace.
Kawata ban gane ba, sai da nayi miki kallon
kurulla. Yanxun saboda Allah dawowa kikayi?
Tace ga ni kuma kina ganina. Matsala tace,
babu ruwan kowa. Mutane masharanta ne kawai,
saboda Allah yayi wa Danliti kyau da farin jini,
ga shi ya Rufa masa asiri, shi ya sa ake masa
hassada.... Ta katse ta, idan hassada ce, ai
kuwa kem kinyi masa da. Menen baki fada ba
akansa? Tace, Rashin sani ne, duk surutan da
akeyi wai dan Iska ne dan guguwa. Dan wata
tsiyace, ni har yanxun Danliti bai taba furta min
maganar banxa ba balle ya nemi aikata wani
shashanci. Rashin fahimta ne kawai yasa ake
masa zargi, kisan mutum mai farin jinin
'yammata (Kuji fa wai bai taba mata komai ba?)
baki ganin ko mace ce ta fiye samari sai arinka
mata wani irin kallo? Baraka ta sauke fuska,
tayi guntun tsaki, baki jin kira Mama. Allah ya
shirye ki. Ameen, ni bari in koma gida, dama
lekowa nayi mu gaisa kisan na dawo. Tabita da
kallo, ki na san kin dawo wajenki xano? Menene
anfani kawancen mu? Bayan ko na gaya miki
gaskiyya bakyaji. Allah ko? To Allah ya bamu
alkhairi ki gaida mohd dinki, in yazo. Yaushe
xasu kawo gaisuwane? Ko bai shirya aure bane?
Wlh ban masa zargin komai ba, amma sonsa bai
rufe min ido ba, ina bukatar in gama sanin ko
shi waye tunda ba gari daya muke ba. Ta tabe
baki, Baraka ke nan, Miss kakale! Ba kakale
bane, gaskiyya ce kawai, daga kinta sai bata.
Shi ya sa nake nuna mikita, don banson ki bata.
Ta mike hannu daya kame da kugu, tace,
nagode, ni nayi gida, kar Umma ta neme ni. Tasa
kai tafice. Baraka ta biyota, ta sallami Inna ta
rako ta iya zaure ta juya. Ta shige gida, tabar
mama dauke da mamaki. Tai kwafa tace, kiyi da
gwana yarinya. Ta kama hanya ta koma wajen
Danliti, wasa-wasa sai da ta bata mini talatin
anan, sannan ta karasa gida. Umma na zaune
tskar falo ta sha tagumi, ta gaji Mama ta shigo
babu ko tsoro ko fargaba tace, sannu da gida
Umma. Inna saude na gaisheki. Ta zura mata ido
ba tare da cire tagumin ba, jima kafin tace, da
izinin wa ki ka bar gidan nan Mama? Ta
mimmike kafa sosai akujera. Tace ai kinshifa
wanka ne Umma shi yasa banyi miki magana ba.
Umma ta numfasa, tayi hucin BAKIN CIKi tace,
lallai kin isa mama, duk son danliti ne yasa kika
zama maras kunya? To kibi a hankali, duniya
zata koya miki hankali, muddin kika dauke ta
kika goya. Ta figi gyalenta, ta mike cikin sauri
tana fadin, Uhm.....! Ta wuce ta fada dakinta,
tayi kwanciyarta. Umma ta kada kai, kwallah
suka xubo mata, ta share tace, Allah kana kallo,
munyi iya yinmu, amma shiriya na wajenka, kayi
mana gaji Ya Allah. Nan Umma taci gaba da
zama tana shan BAKIN CIKI tare da takaici mai
tarin yawa har aka kira azhar, ta tashi tayi
sallah. Abba ya dawo ta labarta masa, hannaye
biyi ya kama kai, takaici kamar ya kashe shi,
bai niyyara kara yiwa Mama wata magana ba
akan Danliti, amma dole tasa ya kira tazo
dakinsa ta xauna. Yayi mata kaca-kaca, sannan
ya sa mata dokar fita ko'ina, duk da yasan ba
dole bane tabi umarninsa. Tabbas hakan ne,
yadda Mama ta fito dakin bakin nan nata ya kai
wani gari wai shi ZUNTU. Shi kasna ya san
rashin kunyta Mama ta kai wani mataki na
kololuwa kwatance, ta xauna bakin gadon ta
tana fadin a fili, wannan shine bature ke kira
Impossible! Tunda kuka hana shi xuwa guna,
dole inje gunsa mu ga juna. Ta saki wani
lafiyayyen tsaki, ta yada kai bisa filo.........
Maganar mama dutse. 7days kenan babu abinda
ta fasa, muna iya cewa al'amarin kara haukata
yayi. Domin a halin yanxun Mama bata shayi,
agaban Umma zata dauki mayafinta, ta fice.
Umma na kira, tana fadin tana xuwa yanxu xata
dawo. Sau uku Umma na xuwa da kanta kofar
shagon Danlinti, tana taso keyarta. Jama'a na
kallon su, gwanin ban kunya. Sai da Abba ya
hanata xuwa. Yace tasa mata ido, tunda ta zama
gagararriya. Wannan abin kunya ya zama abin
yayatawa awajen su hajjo, duk inda suka xauna
xancan kenan. Babu abinda bai dawowa kunnen
Umma ba, sai dai tayi kuka ta share hawayenta
ta barwa Allah komai. Mama fa ta gagari kowa,
suna ji suna gani mummunan labari na ta
yaduwa har gidan Gwaggo Hausi. Daga can
labarin ya mika gidan Marafa. Nana take mami
ta tsani auran mama da Al-ameen. Shi kuwa
Marafa nuna mata yake su daina kama jita-jita.
Aure dai nufi ne na Allah, idan sakeena matar
Al- ameen ce, bbu makawa xai aureta, idan kuwa
ba matar sa bace si barwa Allah yayi masa zabin
alkhairi. Duk da haka al'amarin yana jefa Mamai
cikin tunani ba kadan ba, kuma da Al-ameen zai
ji shawarar ta, da ta umarace shi daya hakura da
sakeena, tunda shasahnci tasa gaba. Sallar
la'asar ta kammala, amma bata bar sallayar ba,
saboda gabatar da lazimi takeyi. Wata tasi tayi
fakin kofar gidan, direban ya fito ya bude but,
yana fido jakar kaya. Yana rufe but din, idanuwa
na suka nuna min Al-ameen a tsaye ya cusa
hannu gaban riga ya zaro kudi ya mikawa
direban, yace, ka rike chanji. Ya sunkuci jakarsa
ya wuce. Direba na xuba gdoiya. Ya tura karamin
gate ya shiga, bakin mai gida har kunne ya taso
da gudu ya amshi jakar yana fadin Maraba da
oga! Fuskarsa babu walwala sosai, yace ya
kuke? Lafiya lau oga. Ya shige masa da kaya
falo. Al-ameen yayi sallama, muryar sa ta dauki
hankalin duk wanda ke cikin gidan. Iya ta riga
kowa fitowa, wa nakehi kamar dan Iya? Ya nufo
ta fuska sake, ni ne iya, surprise ko? Ya dan
rungumo tana fadin, ai kaki koya min turancin
nan, da yanxun na gane nufinka. Yana murmushi
ya rabu da jikinta, ya dubi Ladi, Hajiya Ladi ina
fatan kunje kun duba min jikin sakeena ta? Tace
muna dai shirin tafiya da hada tsaraba. Ya ce,
baku da tsraaba? Gaskiyya kunyi min babban
laifi. Tace, mun san hakan amma tuba muke. Ta
ya kuke? Ta amsa lfya lau ya hanya? Yace,
Alhmdlh. Yana juyo wa sukayi ido hudu da mami
tana masa kallon mamaki. Ya nufe ta da sauri
ya rungumeta, Mami na! Idanuwanta suka tara
kwalla, ta kasa cewa komai har ya dago ya
dubeta, yayi dan murmushi. Yace, nayi muku
laifi Mami, kuyi min hkr na kasa daurewa ne.
Tace nagode Allah da ya kawo ka lfya. Amma
banji dadin xuwanka ba Al-ameen. Yace, na tuba
Mami, ki duba halin da nake ciki, kiyi min uzuri.
Ta dan kada kai. Tace, muje ciki ka sha ruwa ka
yi sallah. Suka wuce yana tambayar Dadinda.
Tace, xai dawo anjima daga kd. Yana xama Ladi
ta shigo masa da ababen sha masu sanyi. Bayan
ya jika makoshi, ya dubi Mami yace, ya jikin
sakeena? Na daina kiran waya, don kunnuwa na
ba za su jure jin mummunan labari ba, koda
yaushe. Dalilin da yasa kenan, nace ya xama
wajibi in xo inga halin da take ciki da idanuwa
na. Dan hutu muka samu na sati daya, shine na
yi anfani da wannan damar. Yaya yanayin jikin
nata yake? Ta numfasa sosai kafin tace, jikin ta
har yanxun a rikice yake, xan so ace Allah ya
saka maka hkr, da dangana akan sakeena,
domin kwakwalwarta ta jirkita Al-ameen.....
Hauka Mami? Kina nufin sakeena ta haukace?
Inna- lillahi wa Inna-illaihiri Raji-un!
Idanuwansa suka tara kwalla, ba xan iya hkr da
ita ba Mami, ko ba zata taba warkewa ba, sai na
aureya. Alkawari ne wannan Insha Allahu ba xan
karya wa sakeena ba. Tana ina ne yanxu? Ita ma
nata idanuwan suka kawo kwalla. Ta ce, tana
Fandagori, kuma ni ma xan so hakan Al-ameen,
domin duk abinda kake so, nima shi xuciyata
take matukat so da kauna. Amma al-amarin ya
sauya salo, ka dauki kaddara kayi hkr da ita,
hankalina zaifi kwanciya Al-ameen. Da gudu
hawayen sa suka wuce bisa kyakkyawar
fuskarsa, ya matso ta a hankali, ya dauko
hannayenta biyu ya matse, ya dubeta ido cikin
ido. Yace, har abada bana fatan in saba umarnin
ku mama, amma ina rokon alfarma ki ban izini
in cikawa sakeena alkawarin da daukar mata.
Zan tafi samun nutsuwa, idan ina kallonta a
matsayin mata ta kowane irin yanayin take. Ina
rokon ki Mami ki taimaka min. Ya jingina
goshinsa bisa kafadar ta, ya matse hawayensa
tare da ajiyar zuciya mai karfin gaske. Haka
maminsa ke cikin irin wannan yanain. Ta jima
shiru tana tunanin zuci, tana son gaya masa
gaskiyya, amma bakinta ba xai iya furtawa ba,
saboda tausayin dan tilon dan ta. Ta yi ajiyar
zuciya. Tace, nayi maka Umarni akan duk
abinda yafi xama alkhairi Al-ameen. Mike ka je
kayi sallah kaci abinci. Ya dubeta yana share
kwalla. Yace, nagode Mami. Ta danyi murmushin
dole. Jeka yi sallah. Ya tashi da sauri ya dauki
jakarsa, ya fice. Mami ta raka shi da kallo,
hannunta a kunci. Ta nunfasa kafin tace, Allah
gamu gareka. Yana shiga, bangarensa ya isa ya
yar da jakar hannunsa ya xauna gefen gado Ya
kama kai hannayensa 2 yana yiwa Allah tasbihi.
Jim kdan ya tura hannu aljihunsa, ya xao wallet
dinsa ya bude ya xurawa dan karamin hoton
Mama ido, nan da nan hwaye suka goce masa,
bai ma san tsaninin kukan da yake ba har da
shassheka, kamar xuciyarsa zata tsago kirjinsa.
Allah da ikonsa, tamkar mami na da masaniya ta
taso ta biyo shi dakin, don ganin a wane yanayin
yake? Da sauri ta karaso ta zauna kusa ta shi ta
rungumo abinta, idanuwan na tara kwalla. Komai
ya sami bawa daga Allah ne Al- ameen, bai
kamata ka xauna ka rinka kuka ba! Jin muryarta
yasa hankalinsa ya dawo jikinsa, sannu-sannu
hawayensa ya tsane. Ya dago ido jajur! Ya dubi
Mami, yace mami ki amince min inje in dubo
sakeena Yanxun. Ta goge masa guntun kwallan
dake bisa kuncinsa. Tace, na baka izini Al-
ameen, fargaba na kawai dare. Yace, kar ki
damu Mami. Allah xai tsare. Shikenan, Ubangiji
Allah ya sa ganinka ya xama waraka gareta,
hankalin kowa yakwanta. Yace, Ameen Mami.
Tace , To kayi sallah Maza-maza, don Allah kar
ka zauna dogon tunani. Yanxun xan fito Insha
Allahu. Ta mike ta bar dakin. Al-ameen Ya
sauke numfashi, shima ya mike ya fada bayi,
nan da nan ya watso ruwa ya dauro alwala ya
fito. Bayan yayi sallah ya kimtsa, ya fito Mama
ta matsa yaci wani abu, amma bai iya zama ba,
gaba daya hankalimsa ya koma Fandogari. Sai
dai ya sha Mamaki daya ga Mami ta nace dole
ya tafi da direbanya, bai yi musu ba. Kai tsaye
ya shiga mota direba ya ja shi suka dauki hanya
suka bar Mami cike da damuwa tare da tunanin
yaya al'amarin zai kasance idan Mama ta juya
wa Al-ameen Baya?
BAKIN CIKI 2*** 8 Ba su ido Fandogari ba, sai
karfe 8pm, babu bata tym gidan Uban dawaki
suka dosa. Ya shige sassan sa tare da sallama.
Umma ta amsa ba tare da ankara da mai muryar
ba. Sannu Umma. Ta dube shi da kyau, gaban ta
yayi mugun faduwa, ta mike tsaye tana fadin,
Al- ameen! Saukar yaushe? Yace, yau din nan
Umma. Ikon Allah. Sannu da xuwa! Zauna mana,
ya zauna yana amsawa. Kafin yace, ina yini
Umma? Ta amsa, lfya lau ya karatu? Mun gode
Allah, ya jikin sakeena? Tayi dan shiru, kafin
tace wani abu. Abba yayi sallama ya shigo, duk
suka amsa amsa Abba! Yace, ah! Al-ameen!
Saukan yaushe? Yace daxun da la'asar Abba. Ya
xauna suka gaisa, sannan ya sake tambayar jikin
mama. Abba yace ciwo na nan Al-ameen. Halima
kawo masa abinci ya ci, kafin muyi magana.
Abba bana jin yunwa, domin na riga na saba da
ita, tun tym din na sami labarin tashin hankalin
da kuke ciki. Abin daya hana ni jurewa kenan,
nace dole in xo inga halin da Mama take ciki.
Abba yace, gaskiyya ne. Mama na nan cikin
lularar da ta sameta sai dai al'amuran zai ba ka
mamaki idan na gaya maka alabari ya sha
bambam Al-ameen, nasan an boye maka komai
coz of karatunka, amma yanxun dole ka sani,
tunda ka zo. Jikinsa ya kara sanyi, yayi xuru
yana sauraron abba, al-ameen rayuwa ta
sauyawa mama, wanda muke ganin sa tamkar a
mafarki, daga ni har 'yan uwanta kaf! Babu
wanda ba shi ckin alhinin wannan abu. Balle
kuma kai da soyayyah ta hada ka Mama, kuma
ita da kanta takwo mana kai cikin gidan nan. Shi
yasa nayi rantsuwa, idan mama xata mutu, sai
dai ta mutu a dakin ka tunda tun farko ita ta
kawo ka. Ashe kuwa babu wani dalili ko uzuuri
da xata kawo mana mu saurare ta. Nasan har
yanxun kana jina a hagunce ne, baka gane inda
na dosa ba. To bari na fito maka a mutum kada
ka wahalar da kanka, Magana daya ce, mama ta
gano wani kuma idanuwanta sun rufe ta manta
cewar tayi xafin farko kuma na karshe a
swajena. Ka fahimce ni? Gaba daya kansa ya
kunce, daga yadda yayi kuri idanuwan sa kafe
yana kallon Abba, suka gane bai fahimci su ba.
Saboda haka yace, dole ka shiga rudu fiye da
wanda ka shuga a baya, amma ina so ka sani,
mu muna tare da kai, ba mu san kowa ba face
kai, ba don komai ba sai don tun farko kai tafara
kawo mana. Abinda nake son ka gane shi ne,
xuwanka ya sanya ni farin ciki. Domin kai kadai
nake jira in tabbatar wa Mama cewa lallai ni ba
tsohon banxa bane, kuma bana magana 2. Ina
mai tabbatar maka ba xaka koma ba sai na
daura auranka da sakeena da yardan Allah. Na
gama magana ta, ka tashi hankalinka kwance,
kashiga wajenta tana nan cikin dakinta. Ya mike
ya bar falon. Umma ta dube shi tace, Al-ameen!
Murya dishe ya amsa, na'am Umma tace kayi
hkr, ka kwantar da hankalinka. Mama bata isa ta
xubar mana da mtunci ba. Kai zata aura da
yardar Allah, domin da kai ne akayi mata baiko.
Tashi ka shiga wajenta ku fahimci juna. Ta mike
tabashi guri, don yaji dadin tashi......... Me
kunnuwan Al-ameen ke ji yau? Ya runtse ido
tamau! Ya girgiza kai wai ko barci yakeyi ne?
Abba ya xo masa a mafarki. Ya bude idanuwan
ya ware su sosai, tabbas zaune yake cikin falon
su Mama. Kenan dagaske ne maganganun da
Abba ya gaya masa? Kirjinsa ya soma bugawa ji
yake kiris! Yarage ya zare masa rai, saboda wani
gagarumin ciwo da yaji cikin xuciyarsa, nan take
ya kama shi. Motsin kirki ya kasa yi har Umma
ta sake fitowa da nufin dauko wa Abba
abincinsa. Ta danyi jim, tana masa kallon
tausayi, sannan ta matso tayi kiransa, ya dubeta
firgigi idanuwa sun juye jajur! Tace, ka na xaune,
baka shiga ba? Tashi ka shiga mana, ka kwantar
da hankalinka, komai xai wuce Insha Allah, ya
mike a kasale, ya nufi dakin ba tare da yasan me
xai je yayi ba. Tana zaune tsakar daki ba ta hade
kai da guiwa, tsiyayar hawaye kawai takeyi,
domin tana jin duk kalaman da Abba ke fadi.
Daf! Da ita ya tsugnna, bai san lokacin da yasa
hannu ya dago fuskarta ba. Sukayi wa juna xuru
tsawon lokaci kafin yace, kin ganeni sakeena?
Al-ameen ne, kin gane ni? Ta kau da kai abinta.
Da sauri ya kara juyo da ita, kiyi min magana
sakeena ko na sami nutsuwa saboda ke na dawo
kasar nan, don na duba jikin ki. Ina can tunani
da xulimmi sun addabe ni, idan kin gane ni, ki
amsa min, ya jikin ki? Ta watso masa harara,
hawaye na kwarara. Tace waya gaya maka banda
lfya? Yace, haka kowa ke gaya min tun tym din
da na daina jin muryarki a waya, komai nawa ya
tsaya sakeena, radadin ciwon daya sameki, ya
hanani sukuni. Ina fatan gani na ya zama
sanadin samun saukin ki. Ta goge kwalla. Tace
duk wanda ya gaya maka banda lfya, ya maka
karya, kalau nake, gani kuma kana kallo na
xaune, sai dai na tabbata dawowar ka zata iya
zame min cuta! Ya kara xura mata ido , kina
nufin abinda Abba ya gaya min yanxun gaskiyya
ne? Tace ka daina kokwanto. Ya langwabe kai
gwanin ban tausayi. Yace dole nai kokwanto
sakeena, don nasan akwai alkawarin a tsakanin
mu, kuma bana tunanin zaki yaudare ni, wannan
ya tabbatar min da tsantsan son da kike min.
Ban taba kallonki da xuciya 2 ba sakeena.
Shiyasa har halin yanxun da nake magana dake
ban yarda kin karya alkawarin mu ba. Ta kalle
shi a dage, ta watsar tace, ya kamata ka amince,
tunda gashi da bakina ina gaya maka, tsutsun
soyayyarka yayi fiffike yayi dogon tashi. Ya dafe
kirjinsa a natse idanuwansa tam! Da wahaye,
yace, bai tashi ba sakeena, nayi rantsuwa kina
so na. Akwai miskhila dai a wani wuri, ki gaya
min laifin da nayi miki. Wlh da kaina xan
hukunta kaina, koda da jinin jikina ne xuba, idan
har zai zama fansar tarin laifin da nayi miki.
Gaya min da sauri inji. Ta ya mutsa fuska,
hawayen ta ya bushe tace, Al-ameen ka farka
daga barcin da kakeyi ka saurareni, ni sakeena
na gaya maka a da naso ka, amma yanxun ban
son ka, ba kuma zan aure ka ba, idan sama da
kasa za su hade! Kaji ni ko? Sai na maimaita?
Ya matse ido, kwalla masu zafi suka yo waje da
gudu, ya dan kada kai murya shke yace, kin
xuba min dafi, kin xuba min dafi sakeena. Baki
tunanin amana? Yasa hannu ya kamo yatsunta,
ya kura wa zobensa ido, ya ciga, baki kallon
zoben alkawarin mu? Me yasa kika mance da
dimbin kalaman da kika sha gaya min? Wadanda
suka jaddada imani na akan son da kike min? Ta
kwace yatsunta a hankali ta zare xoben, ta jefa
masa, ga tsiyarka nan, idan shi kake kallo a
matsayin alkawari, ni ma cire min nawa ka bani.
Yaci gaba da kallonta, kafin ya dauko zoben
yace, kiyiwa Girman Allah ki maida zoben nan
sakeena.... Bazan karba ba! Idan ma ka aje shi,
zan jefa shi masai! Kuma nima dole ka ban
nawa! Yace sai dai ki kashe ni, sannan ki zare
shi, wannan din ma zan ciga da boye shi, har
xuwa tym din zaki sami nutsuwa dakin auranmu.
Ta kwada masa harara, sannan tayi wani dan
murmushi na kaico, ta kauda fuska, y mika
hannu ya kamo habarta, ta sa nata da karfi ta
doke nasa, kafin tace, karka sake tabani, idan ba
haka ba kuma sai na kurma maka ihun dan iska!
Ta mike da sauri ta bar wajen, kai tsaye bayi ta
shige, ta maida mukulli ta kulle. Yayin da Al-
ameen ke cigaba da kiranta. Ya tashi ya tsaya
kofar bayin yana fadin, ki fito ki saurare ni
sakeena, ya kamata mu fuskanci juna, mu gane
inda matsalar mu take. A zatona har duniya ta
nade ba zaki taba juya min baya ba! Tana daga
ciki ta amsa, bazan fito ba. Daman kasan inda
dare yayi maka, yace ki tuna alkawari sakeena,
don Allah karki bari ayi min dariya. Idan na
rasaki zan iya rasa komai nawa, ki tausaya min
sakeena, kar damuwa ta kasheni. Tace, kan ka
akeji! Ni na gama magana da kai. Ko za'a kashe
ni ba xan sauya ba, dama ka kama gabanka zai
fiye maka alkhairi. Ya tsaya jim, shiru goshin sa
jingine da kofar ya rasa inda zai tsoma ransa
yaji dadi. A hankali ya soma karannto Innalillahi
Wa inna ilaihir Rajiu'un. Ya fi 10mins tsaye.
Sannan ya juyo da sauri ya fito yana share fuska
da hankaci. Kawai arba yayi da su Abba zaune
falon. Ya rage sauri ya nufi gunsu ya tsugunna,
abba zan koma. Gab dayan su ido suka xuba
masa, jim Abba yace, amma dai ba minna zaka
nufa ba yanxu ko? Ya dan kada yace, kuma ka
kwantar da hankalinka Insha Allahu Mama matar
kace. Kar ma ka bata tym din wajen xuwa goben,
kai tsaye ka wuce gida, ka gayawa Marafa ina
tafe da kaina, muyi magana. Yace to, Abba na
barku lfya. Ya mike ya fice suka raka shi da
kallo. Ummma kam bata sami cewa komai ba,
saboda tsabar tausayinsa. Yana fitowa Gambo
direba ya balle murfin mota ya fito, ya tarbe shi
ganin ogansa na ta share fuska, yaya jikin nata?
Ya dube shi ido jajur yace ba sauki Gambo. Mu
shiga mota, ka maidani gida. Yace yallabai ai
dare yayi sosai, nayi zaton gidan gwaggo xamu
kwana. Ya miko hannu yace bani keys, kai ka
wuce gidan Gwaggon ka kwana! Ya dan sunkuyar
da kai, yace yi hkr yallabai Allah ya sauke mu
lfya. Shi tuni ya bude gidan gaba ya fada.
Gambo ya xauna mazauninsa da sunan Allah ya
murza mukulli yaja suka wuce, a tym din agogon
motar yana nuna 09:45pm. A daren nan nake son
ganin Dady na. Gambo yace Allah ya yarda
mana, ita kuma Allah ya bata lfya. Ya kama kai
ya runtse ido, ya jingina sosai da kujera yana
fadin amin Gambo. Direba na ta tsula gudu cikin
dare. Shi kuwa Al-ameen kurwarsa na can cikin
tunanin baya. Itin tsantsan son da Mama ke
masa, shi yake gani cikin idanuwansa, har xuwa
ranar da ya xo sallama da ita a sch, kawai
gambo ji yayi Al-ameen na sambatu, sosai
kikace kina sona sakeena, dama yaudara ce? Me
yasa sakeena? Me yasa? Hnkalin Gambo ya
koma gunsa yayi kiransa sau uku, kafin yaji
kiran. Ya xuba masa ido yayi da direba ke fadin,
kayi hkr yallabai, yace sakeena ta yaudareni
Gambo, ta xuba min dafin da xai wuya na sami
maganinsa. Xan iya mutuwa Gambo, domin gaba
daya na sallama kaina gareta. Ko kasan inda
nake da mishkila ka gaya min in gyara? Gaba
daya tausayin sa ya lullube gambo, ya kada kai
da sauri, yace babu inda kake da mishkila
Yallabai, sai dai ko ajizanci na dan adam. Ni
kaina ban yarda sakeena bata sonka ba,
watakila ciwo ne rudata yace, kai ma ka yarda
bata da lfya ko? Amma kowa yace kalau take, ni
nasan sakeena bazata ki ni haka kawai ba,
zuciya na wasi-wasi. Gambo yace , kar ka damu
Yallabai, Allah zai warware komai, sakeena zata
zama matarka. Ya sauke numfashi mai karfi
yace, wannan shine babban burina a duniya,
komai Allah ya bani na gode masa, saura
wannan burin ya rage min. Shima zaka sameshi
Insha Allahu. Yayi dan shiru, sannan ya kada kai
yace, laifi nane, rashin kasancewa ta kusa da
sakeena, shi ya jawo shaidani ya shiga tsakanin
mu. Lallai mata na da rauni Gambo, ba taba
tunanin sakeena zata iya hango wani har ya
rikita ta amince dukkan amanar da muka damka
ma juna. Al'amarin na daure min kai, na rasa
yadda xan fassara shi. Yace, haka ne yallabai,
amma idan ka barwa Allah komi na tabbata xai
maka zabin alkhairi. Ka sani ko wata jarabawa
ce Ubangiji yake yi ma don ya gwada imanin ka.
Kar ka damu Yallabai, Allah ba zai hana ka
sakeena ba, idan har kayi imani shine mai
hanawa da badawa. Ya sake jingina da kujera,
ya runtse ido ka fadi gaskiyya Gambo, na gode.
Bai sake tankaea ba haka kuma bai daina
tunanin xuci ba, ma'ana sakeena bata daina
xuwa cikin idanuwan sa dauke da lallausan
murmushinta mai sanyaya masa rai, tana tura
hularasa gaban goshi bakinta na fadin, so much!
Shi ya sa baya aikin komai face ajiya xuciya.
Gambo na jinsa tausayinsa nakara zama cikin
ransa. Karfe daya dai-dai na dare motarsu na
tsayuwa kofar gate din gidansu. Gambo yayi
hon, nan da nan Mai gadi ya shaida hon din
motar mami ne, ya taso a guje ya bude kofar,
motar ta shige kai tsaye kofar shiga ya tsaya.
Al-ameen ya fito, sannan ya wuce ma'ajiya
motaci. Tun kafin ya kwankwasa, yaji ana
kokarin budewa, don haka ya dakata hannayensa
biyu cikin aljihu. Marafa ne da kansa ya bude
kofar, suka zuba juna ido, daga bisani ne mami
ta bayyana wajen har ta riga marafa magana, Al-
ameen . Idanuwansa suka yi tam da kwalla, ta yi
azama ta jawo shi ciki, daddynsa ya maida kofar
ya rufe. Don me ka iyo daren nan Al-ameen? Sai
kace babu inda zaka raba ka kwana! Ya zauna
dabas! Ya kama hannaye biyu, Marafa ya xauna
kusa shi. Ya rungumo kafadunsa, yace baka
kyauta min ba Al-ameen, da ka dauko hanya
cikin daren nan dan kuskure kadan za'asamu,
shikenan ka ajwo mana tashin hankali, karfa ka
manta, kai ke nan guda daya muke kallo zukatan
mu na wankewa daga radadin rashin da. Ya dube
shi ido jajur! Yayin da Mami itama ta xauna daya
gefen suka sanya shi tsakiya. Yace, na kosa in
ganka Dady, sakon Abba xan gaya maka, yace
gobe yana nan tafe maganar aure na sakeena,
kafin in koma yake so a daura shi. Mami tace,
kun daidaita da sakeenar ne? Ya dan kada kai
yace, sakeena ba warke ba Mami, hasalima bata
gane ni ba, shiyasa tun farko nace a kaita
asibiti, kowa yaki amincea da ni, ga shi nan
kwakwalwarta ta tabu. Sakeena ta kasa ganeni
Mami, ni kuma bazan fasa auran ta ba, domin
shine babban buri na a duniya. Su abba sun goya
min baya, kuma ku taimaka min buri na ya cika
don girman Allah. Gaba daya ya kara daga musu
hankali babu kamar Marafa da ko alama baya
kaunar yaga dansa na kukan neman wani abu,
shi yasa nan take ya ji ko ana ba maza ha mata,
sai Al-ameen ya auri mama. Amma ita Mami
bata an ta dosa ba, don haka tace. Al-ameen
bania ron hankalin kanan, na ga alama baka
yarda Sakeena lfy lau take ba.... Ku kuka gaya
min ai Mami... Yanxun kuma ni na gaya maka
lfya, kawai cin amanar ka tayi, tunda kaje bata
saurare ka ba, kai ma ka manta da ita kawai, ka
roki Allah ya musanya maka da mafi alkahiri.
Bafa sakeena kadai ce ta yalwatu da dukkan
abubuwan da kake so ba. Saboda haka ka kama
kanka, ka nutsu ka gane cewa ko an daura
auran, ba zaku zauna lfya ba, tunda idon ta ya
bude, tana takamar tana da kyau, kowa na
kallonta, kajini? Ya girgiza kai, idonsa xuru yana
kallonta, tace au baka ji ni ba? Menene nufinka?
Marafa ya amshe don Allah, don Annabi ki kyale
shi, ba yace Uban dawaki na taf ba? Allah ya
kaimu goben lfya, shi aure ai nufi ne na Allah.
Yanun kaje ka kwanta mu saurari goben, kaji?
Yace naji dady, don Allah ku tayni da addu'a
sakeena kadai nake so. Yace na sani, addua
kuwa kullum munayi, kayi alwala ka sami koda
raka'a 2 ne kafin ka kwanta, na tabbata zaka
sami nutsuwa ok? Ya amsa da kai ya dan
bubbuga kafadarsa yace, yau dan Dady, Allah ya
bamu alkhairi. Bai dai tanka ba, ya mike ya bar
falon. Mami ta cire tagumi tace, sai Allah yayi
wa yaron nan sakayya! Yadda tai masa haka
Allah zai mata. In banda idon Al-ameen ya rufe a
kanta, me zaici da ita? Yarinyar da gwaggo tace
shagon saurayi take su raba dare suna.... Marafa
ya katse ta, don son Annabi, ki bar wannan
magana haba. Ki yi masa fatan alkkhairi kawai.
Cikin bacin rai ta mike ta koma daki. BAKIN
CIKI kamar ya kasheta. Shi kuwa Al-ameen yana
can yana nafilfili kamar yadda dadinsa ya
umarce shi. Da safe ya fito gaba daya ya zabge,
kallo daya za kai masa ka tabbatar da hakan.
Gaban mami ya fadi ta kwala wa Ladi kira ta zo
a gigice. Tace, to hajiya. Ta juya da sauri ta fice.
Mami ta dube shi tace, matso nan kusa da ni. Ya
kara matsowa yace, ina kwana? Ta amsa tana
shafar kansa. Ina dadina, bai tashi bane? Tace,
kwana yayi baiyi barci ba, sai bayan sallahr
asuba barcin ya sace shi. Tana rufe baki ladi na
sallama da tiran abinci ta dire gabansu. Tace ga
shi hajiya dr, Iya tace in gaida ka, yanxun xata
shigo. Yace ina amsawa. Ta fita ta bar dakin.
Mami ta jawo tiren ta hada masu shayi ta mika
masa, ungo nan dan iya. Daute ka sha kaji karfin
jikinka. Ya sanya kofi a baki ya kurba kadan.
Wlh daci mami ba xan iya sha ba. Tace don me?
Ka cigaba da sha za kaji bakin ya washe. Ga
kuma farfesun, bude bakin in xuba maka. Ya
bude 'yar kular ta debo a cokali ta mika masa,
karbi ka gani mana. Ya bude bakin ta xuba masa
tace, yauwa ko kai fah? Yanxun idan Abba ya zo
maganar auranta kankama, haka za'a ga ango a
rame? Dadi ya lullubeshi yayi wani lallausan
murmushi yace, mami na rame ko? Kai baka ji
ajikin ka ba? Bana so kayi angwanci a rame, don
haka ma za ka kama abinci ka ci. Nan da nan ta
ga ya gyara zama ya hau shan farfesu yana
kurban shayi, kinsan wani abu Mami? Sai ka
fadi, shayin nan ya daian min daci. To yi sauri
ka shannye. Ya kuraba ya sake kallonta, yanxu
Mami idan aka daura auran anan xan barta? Eh
mana, ko ba xan iya kula da ita bane? Yayi dan
murmushi, a'a mami na, amma ni na fison mu
tafi tare can, kin ga kafin mu dawo ta mance da
sakaran Yaron da ya hure mata kunne. Ko ma
muyi xaman mu can tana karatunta ina aiki na,
ko kuwa? Ta dafa kafadarsa, gaskiyya ne, ina
goyan bayanka, sai dai in ta haihu ka kawo min
maigida ko kishiya. Ya kyalkyale da dariya,
kwalla suka cika idanuwan mami ta bisi da kallo
tana gyada kai. Yayi gyatsa kafin yace, ina son
twins mami, ko? Sai dai an mai son su baya
samun su? Da sauki ya katse ta, no duk canfi ne
Mami, ni dai ina so kuma Allah xai bani ameer
da ameera. Tayi 'yar dariya tace, duk naji, idan
ma 'yan hudu ne Allah ya kawo masu albarka,
yanxun tunda ka koshi, kaje ka yi wanka kafin
dadin ka ya tashi. Xai ji dadi idan ya ga ango
shar! Yace haka ne mamina. Ina xuwa, ya tashi
da sauri ya fice. Mami ta ta tallafe kunci ta ce
nikam tawa.... Nikam tawa ta sameni, ni Ya su,
Allah ka duba mana. A bakin kofa suka hadu da
iya suka gaisa. Sannan ya wuce bangarens, ya
fada bayi ya sheko wanka, ya kimtsa jikinsa da
wani lafiyayyen farin boyel mai taushin gaske.
Ya fesa turare, ya dawo dakin Mami, ita ma
wanka yi ta sauya kaya. Ta dube shi tana fara'a
tace, haba yanxu na ga daidai. Ina ganin ma dai
daga yau aka angwancin nan. Ya xauna kusa da
ita yana dariya. Tsokanata kike sonyi Mami, me
kika gani yanxun? Sai ma ranar kenan. Ki gane
Mamina, ranar ba zaki shaida ni ba. Ta ware ido
tana 'yar dariya zai hana? Sai dai ko amarya ta
kasa shaida kai, amma ina mami zata mance da
dan tilon dan ta. Dadi ya kara lullube shi, ya
rungumo ta yana fadin Allah sarki mamina, Allah
ya bar min ke tare da Dady na. Dadin ne kansa
ya amsa, amin amin. Ya kara sa shigowa suna
masuayar fara'a. Dadyna ya tashi lfya? Na tashi
lfy Doktna. Suka gaishe shi cikin annushuwa,
duk da bai san sirrin ba, xuciyarsa tayi masa
dadi. Don haka ya xauna aka kawo masa
abincinsa su ka fara ci tare suna kara kwantar
masa da hankalin. Sosai kuwa hankalinsa ya
kwanta, yana ganin tamkar an daura auransa da
mama, tunda yana da magoya baya ta kowanne
bangare

BAKIN CIKI 2***9 Abba bai ga ta zama ba, 7:30
suka kama hanyar minna shida Alh. Adamu tare
da Umma, domin ita tana bukatar ganin likita.
Saboda ha ane aka tafi da Inna saude don ta
rinka taimaka mata. Basu iske abdulkareem a
gida ba, ya riga ya fita aiki. Hankalin Aunty Rabi
ya dugunxuma nan da nan ta dauki waya ta kita
wayar ofis dince, Yaya abdul yaji kamar zai
mutu, saboda tsabar bacin rai, amma ba yadda
zaiyi ya fito saboda tsarin aiki irin na banki.
Daga nana aunty amina ta kira, itama ta shaida
mata, kafin ayi haka labari ya gauraye ko'ina.
Asibiti suka fara aje Umma tare da inna saude.
Aunty Rabi itace jagora domin asibitin da banki
ke da reg da su ne. Daga can da Abba da alh.
Adamu suka dumfari gidan marafa. Da ganin su,
gaban Mami ya fadi, fara'ar karfin hali kawai
takeyi. Bayan su natsu a falo. Abba ya tambayi
marafa? Tace, ai kuwa yayi sammako ya tafi
Lafai, don shaidawa mutannan gida maganar
daurin auren, shi kuwa ango na san ya ma kai
zariya yanxun Insha Allahu. Kasan a can
yawancin abokansa suke saboda can yayi krt.
Ina fatan lfya? Ya sauke numfashi idanuwan sa
suka kara juyewa yace, babu lfya Hjya, Ki
Innalillahi Wa inna ilaihir raji'un! Alh. Adamu ya
gaya mata. Ya gayara xama, yace hajiya
wannnan al'amari babu dadin ji, a takaice dai
sakeena ta gudu tun jiya har yanxu ba mu san
inda take ba. Tsaye ta mike dafe da kirji, ta yi
me? Ta kame a hakan bata iya kara komai ba.
Abba yace, nayi iya yina Hajiya, amma mama ta
nuna min ta karfina, hanyar da zabarwa kanta ta
wuce da sani nan. Kuyi hkr hajiya, ni ban ma san
da kalmar da xan gaya maku ba. Ta koma a
hankali ta zauna cikin kasala tace, ai shikenan,
duk abinda Allah yayi daidai ne, mu mun hkr,
Allah ya musanya wa Al- ameen da mafi
alkhairi, sukayi ji. Shiru kafin Abba yace mu na
nan garin nasan har Alhji ya dawo. Itama hajiya
tana nan na kawo ta asibiti tun jiya ciwon ta ya
tashi abin sai yadda Allah yayi. Ta maida tagumi
tace, dole Umma tayi ciwo, ubangiji Allah ya
bata sauki ya kuma shirya mana zuri'a, suka
amsa amin. Suka mike sukayi mata sallama
suka tafi. Hawaye suka kubcewa mami, hannunta
a kunci tace, ta faru ta kare kowa sai ya hkr!
Tab, wannan yarinya ta daure min kai. Allah
kayiwa Al-ameen sakayya! Iya da ladi suka jiyo
hajiya na sambatu, suka fito suka taushi
xuciyarta, babu bata tym ta sa driver ya kaita
Lafai. Gado aka ba Umma, saboda yanayin jikin
nata, yana bukatar kulawar likita sosai domin
jininta ya hau, har ya haye yadda ko alama ba 'a
so. Anan su abba suka ci gaba da zama har
karfe 4. Yaya abdulkrm ya samu ya baro ofis.
Kai tsayr asibitin ya nufa a sukwane. Da ka dube
shi, kasan ransa a nbace yake, yana ganin
Umma kuma al'amarin ya kara gigita shi. Ya
dubi Abba ido jajur! Yace, yanxun wane mataki
aka dauka? Abba yace, ni na sallama mama,
tunda ta iya toazarta ni haka. Na kuma je gidan
su Al-ameen, matslar kawai ban same su bam
duk sun tafi raba goron gayyata, sai hajiya na
samu shaida mata. Alh. Adamu yace amma ni
ina ganin zai fi kyau abada cigiyar a gidajen
Radio da Tv. Abba ya amshe, da kudin wa?
Saceta akayi? Ba xan kara asara ba, yadda ta sa
kafa ta bar gidana, ta tozarta ni, ta wulaknata
ni, ta nuna min ban isa da ita ba. Wlh ni ma na
hkr da ita. Ba xan yi mata baki ba, dan ko bance
wani abu, tabbas ita da kanta ta kai kanta
mkrntar koyo hankali. Za ku ce na gaya maku.
Taje duniya cem ta ishi kowa riga da wando har
da mayafin yafawa. Ya abdulkrm ya numfasa,
yace ta yiwa knata, Allah ya shiryar da ita, yasa
ta gane, suka amsa da amin. Jimawa kadan ya
ba Aunty Rabi mukullin mota ta wuce dauko su
Ameera daga sch. Kai tsaye ta wuce da su gida.
Ta kama hidimar shirya abinci. Tana gamawa ta
kwashe gaba daya da yaran suka koma asibiti.
Ta iske kofar dkin da Umma take dankam! Da
Jam'a, ashe bayan tafiyarta kadan su ya Abdul
kadir da abdulrhmn suka iso. Can kuma sai ga
dady da mami. Al-ameen ne kadai bai dawo ba.
Duk tabisu ta gaida su. Dady kam yama rasa
yadda xai fassara al'amarin Allah ya sa bai riga
ya yayyada xancen ba ko 'ina, iyakar sa cikin
babban gidansu. Allah ya kawo Mami tayi masa
birki. Shi kansa yadda yakeji a tym din, idan
xa'a gwada jininsa dole ace ya hau, amma daya
iso ya dubi halin da iyayen Mama ke ciki sai
yaga ashe shi nafila ne, tashin hankali na inda
yake. Shi yasa ya nutsu sukayi magana ta
fahimta da abba...... Ya Dubi halin da Iyayen
Mama ke ciki sai ya ga ashe shi nafila ne, tashin
hankali na inda yake. Shi yasa ya nutsu sukayi
magana ta fahimta da Abba. Suka dauki komai
suka barwa Allah tare da rokon Abba daya
amince ya bawa mama wanda ta sake xaba.
Abba bai ce komai ba anan. Don baya jin zai iya
ba Danliti 'yarsa su hada zuri'a da mutuncin sa
da komai a gari. Yanxun tunaninsu dan gogan.
Yaya al'amarain zai kasance? Bayan abba ya
kauda masa duk wani shakku, ya bashi tabbacin
babu wani face shi, shi ya kara karfafa masa
gwiuwa har ya sami kafar tafiya gayyato abokan
taya shi murnar angwanci? Wannan amsa sai
wanda ya gani da idanuwansa. Gab! Da kiran
sallah magriba duk suka bar asibitin, aka bar
Inna saude ita kadai tare da Umman, wacce har
yanxun barci takeyi, domin allurar da akayi mata
mai karfi ce sosai, saboda ana son ta samu hutu
kwarai da gaske. Su dady na isa gida, kamar
tare suke da Al-ameen. Bai fhimci komai a
fuskokinsu ba, don basu yarda yaga sauyi ba ya
baje a kujera yace, wsh! Ai fah an fara kenanm
kinji yadda naga ji Mami? Ta danyi murmushi
tace, dan Iya kena, to abinda ya kamata ka
hanzarta yin wanke ne, don gab ake da kiran
magriba. Haka za'ayi Mami na, dadi ya aka baro
mutanan Lafai? Ina fatan zaka jaddada musu su
taso da wuri? Wannan ai dole ne, kama san
kawunka ba shi da wasa. Yana ta far'a gaskiyya
ne ni ma frnds dina ne ce masu kai tsaye su
wuce Fandagori, ai gidan Uban dawaki ba
boyayye bane, suna tambaya za'a nunna masu.
Dadi yace, kayi daidai, yanxun tashi ka shiga
wankan nnima shi xanyi aga wanda xai riga
fitowa cin abinci. Ya mike xumbur! Yana dariya
ni ne xan riga Dadi, to shikenan, mami ki na ji
ko? Idan kuma na riga shi bulala tara, tace ni
kuma xan cikashe dayar, su zama goma. Na
yada. Bai jira komai ba ya kwasa da gudu, ya
shige bangarensa. Mami ta bishi da kallo. Dadi
ya sa hannu ya cire mata tagumi yace, ke ma
tashi ki daina damuwa. Ta sauke numfashi,
amma ba tace komai ba, ta yunkura ya taimaka
mata ta tashi suka wuce. Kowa ya shige
dakinsa. Al- ameen ya fara fitowa falon, ya nufi
gefen tebur inda ya hangi ladi na jera abinci. Ya
isa wajen yana fadin, angaida Maman abinci.
Tayi dan murmushi. Tace ni ma na gaida dr.
Yace na kusa dina cin abincinki Ladi, ina ganin
daga yau nai masa bye bye. Tayi 'yar dariya, to
aci gaba ne dr. Amma ina ganin akwai gobe
kafin amaryar ta iso ko? Ya gyada kai, yana dan
murmushi, wa ya gaya miki xan dawo ni kadai?
Tana 'yar dariya ta amsa, au can xaka zauna?
Kafata, kafarta, zata sake magana, ya dakatar
da ita, shisshhh... Tayi tsit! Tana kallon sa yana
boyewa bayan kujeru. Dadi ya fito mami na biye
dashi, madalla, kinga bulala ta hau kan danki,
kira shi na tsatstsala masa. Tace, yanxunn nan
ma xaka ganshi a sukwane, kwai ganin sa sukayi
yana gyara xaman kujera xai xauna. Gaba daya
suka kwashe da dariya. Ladi na tasya su sannan
ta bar wajen. Dady yace, gaskiyya ba haka ake yi
ba, ai dai sai ya bari mu fito tare ko mami?
Dariyar Al-ameen ta karu, yayin da Mami ke
fadun, kaji wayau! Ta xuba wa kowa abinci yaci,
suka kashi suna ta biye masa, suna labarin biki.
Bukatarsu ya cika cikinsa, kuma ya ci sosai.
Bayan su kammala Dady ne ya fara barin tebur
din Al-ameen ya byi shi xasu yi wata magana,
nan da nan ya mike ya bi bayansa. Mami ta
kwala wa Ladi kira tace ta gyara kan tebur din,
ita ma kai tsaye ta wuce, ta iske su xaune bisa
kafet. Dayan gefen ta xauna, suka sanya shi
tsakiya. Dadi yayi gyarn murya yace, wasu 'yan
tamnbayoyi xan yi maka Al- ameen, ina fatan
xaka nutsu ka bani amsa shakikiya. Da farko dai
shin Al-ameen wa yake badawa, wa yake
hanawa? Yace, Allah. To idan ya baka, sannan
ya dawo ya karba, me yakamata kayi? Ya amsa,
nayi masa gdya, watakila ya musanya min da
alkhairi, ko Mami? Tace, Gaskiyya ne! Dadi
yace, Madalla, abinda nake ka sanya wa ranka
kenan. Idan har ka tabbata tsakanin ka da Allah
ka amsa min tambayoyi na. Ka kuma san imani
shine cikar dan musulmi, ko ba haka ba? A
salube yace, sosai dady. Yauwa, to kayi hkr
maganar da xan gaya maka. Nasan ka na son
sakeena, sannan kayi imani Allah ne ya hadu ku
ya sanya maka sonta, a da mu na ganin kamar
itama tana sonka, kamar yarda kake sonta.
Amma yanxun ta nuna yaudara ce kawai, saboda
haka ka hkr da ita. Kamar yadda kace Allah xai
musanya maka alkhairi. Ya dubi Mami, ya juya
ya dube shi, Dady ban fahimce ka ba, ai sakeena
na so na, xuga ce kawai kuma na tabbata da
xarar aka daura auranmu, ni masan yadda xan da
hankalinta gareni. Dady ya ka kada kai, maganar
ka dawo da hankalinta gareka duk ya kau. Al-
ameen sakeena ta gudu tun jiya babu wanda
yasan inda take saboda haka nake rokonka
arziki da ka kwantar da hankalinka, kayi imani
da furucin da kayi daxu, Allah ba xai bari kasha
wuya ba. Ya Dubi Mami fuska kunshe da tashin
hakali yace mami ban fahimci ta gudu ba? Me
dady yake nufi? Tace iyakar kiyayya sakeena ta
nuna maka, tunda ta xabi ta dauki akwatinta ta
bar gidan iyayen ta ada ace ta aure ka. Ta xabi
ta ci mutuncin mahaifanta akan auranka.
Wulakanci ya kai makura Al-ameen, ya kamata
ka nuna mana ka haihu dan halas, kace kai ma
ka hkr da sakeena. Ya xura mata ido, du sun
kadu, mami kina nufin an fasa daura auran
gobe? Tace abinda Abbanta yayi sammakon
xuwa shaida mana kenan, ia ske ba ku nan kun
riga kun tafi gayyata, ni na bi dadynka Lafai na
dakatar da shi. Kai ma ina so ka dauki waya ka
kira abokin ka dr. Lawal ka gaya masa an fasa,
don ya gaya wa saura kar su yi wahala. Ya kada
kai yace, baxan iya ba mami, na rantse da Allah
sakeena na so na, ina xata gudu taje? Ban yarda
ba mami sace min ita kayi, don a raba mu....
Rufe min baki! Mami ta daka masa tasawa mai
karfi, daga nan ta balle da masifa, kar ka yarda
Al-ameen, amma ina son ka sani, babu maganar
auranka gobe da sakeena! Idan kuma ka sake
tak a wurin nan sai na tsinka mata mari, don ka
gane ba wasa muke yi da kai ba! Yaya ana
rarrashinka ana numaka gaskiyyar magana ka
naso ka akrya ta mu? Sakeenar banxa sakeenan
wofi? Ita kadaice mace a duniya? In sake jin
xancen ta abakin ka sai na saba maka! Ku ma
ka sani, daga daren yau ka fara shiri gobe xuwa
jibi xaka koma sch! Kaji ko baka ji ni ba? Ya aje
kai kasa. Dadi yasa hannu ya dago fuskarsa.
Tuni hawaye suka wanke masa kunci, shi ya fara
fadin, me yasa zata gudu ta barni Dady? Ko
baxan hkr da ita ba, ai bai kamata ta gudu ba,
hatsari ne babba ga diya mace, wa ya san hannu
da take yanxun? Mami tayi caraf? Ta cafke, tana
hannun wanda take so. Dama ka daina bata
hawayenka a banxa. Sannan kama kunnunwanka
da kyau ka ji ni, tun daga ranar da ka daina jin
muryar sakeena awaya ta daina sonka, ta mance
da kai, ta share ka a rayuwarta. Saboda kin da
ta ke ma. Sakeena ta diro daga mota, da abin ya
zo da karar kwana da yanxun an kusa mata
sadakar arba'in. Sakeena tayi kwana da kwanaki
tana yajin cin abinci, tayi ta suma ana mata
karin ruwa a asibiti. Kai saboda kiyayyar ka,
gabada dabi'iun sakeena suka sauya, bata
gannin kowa da daraja, nballe ta saurari fada, da
iayeynta da 'yanuwanta ke mata ba dare ba rana.
A karshe sakeena ta aikata abinda yafi komi
muni akan diya mace. Duk saboda bata sonka,
ashe ya kamata ka hankalta kasan halin da kake
ciki, don kai ba yaro bane, kuma ba alfahari ba,
ilimi muhammadiya da boko sai dai a yiwa wani
gori ba dai kai ba Al-ameen, duk kuma wanda
yayi imani da kaddara, baya tabewa Al-ameen.
Ka maida al-amarin ka wajen Allah shi xai maka
magani. Ya dube su daidai tamkar karamin yaro,
murya na rawa yace, gaskiyya ne Mami, duk
abinda ki ka fadi na yarda, kuma na hkr da
sakeena, sai dai son ta ba xan iya cire shi cikin
raina ba, saboda ba ni na aje shi ba, kuyi hkr, ku
yafe ni, idan furuncin danayi ya muku xafi,
sannan ina rokon ku don Allah da son Manxonsa,
kar ku kullaci sakeena cikin xukatan ku akan
wannan maganar. Wlh har yanxu ina ji ajikna
sakeenna tawace. Dady ya rungumo kafadunsa
yace, shikenan,ya Isa, munji rokonka mun amsa.
Zamu cigaba da taya ka addu'. Yanxun abinda
nake sonka da shi shine, ka kira Dr. Lawal ka
gaya masa, don su sani. Sai dai in baka
lambobin ka kira shi dady, bakina ba xai iya
furta mummunan labarin nan ba. Ya mike ya jao
durowar dadi ya dauki biro da paper ya rubuta ya
bashi, ya mike xai fice, ya kusan kaiwa kofa
mamy ta kira shi, ya juyo tace kayi nafilfilu cikn
dare. Allah zai saurareka, ya nisa kafin yace
xanyi mami. Ya sa kai ya fice. Mami ta dubi
dady ta hadiye hawayenta, tace gobe in Allah ya
kaimu xan koma Lafai wajen baba liman in samo
masa ruwan addu'a ya sha ya sami sanyi cikin
ransa. Yace hakan ma yayi, Allah ya sa mu
dace. Tace amin. Ta jawo wa dady kan waya ya
nemi Dr. Lawal, ya sanar masa. Yace an fasa?
Subhanallahi? Wannan abu baiyi dadi ba. Don
girman Allah dady a samu a daidaita, wlh Al-
ameen yana son yarinyar nan ba kadan ba. Ya ce
ba sai ka rantse ba Lawal, ni kaina nasan hakan,
amma fadan da ya fi karfinka dole ka maida shi
wasa. Mu nan muna ta addu'a Allah ya zaba
mafi alkhairi. Ya numfasa, yace amin. Ina Dr.
Yake? Ai sai da ka neme shi xuwa gobe, yanxun
kam babu sukuni yana dakinsa. Yayi dan jim,
kafin yace Allah shi kyauta, amma ayi kokari
Dadi idan xai yuwu a sasanta. Ba komai mun
gode a gaida Iyali. Zasuji, ya aje wayar tare da
tsananin mamakin wannan abu? Me ya faru haka
da xafi? Haka ya kwana da tambayar kansa, don
babu alamar wata mishkila a tattare da soyayyar
abokinsa da sakeena, ko daya zo sanar da
xancen auran ma babu alamat akwai matsala
babba. Labarin barci dai babu shi a wajen Al-
ameen kuma xuciyarsa bata daina karyata masa
xancan ba. Ko alama ta ki amsar sakon, saboda
tsabar shakkun da yake ciki, wai sakeena taci
amanarsa? Har 8am yana kan sallaya, ba don
wai yana sallah ba, a'a kasala ce ta hana masa
tashi. Mami tayi sallama ta shigo da tiran kayan
karin safe. Ya xubo mata ido. Mami tayi sallama
ta shigo da tiran abinci, ya xubo mata ido, ta aje
a agbnsa, ta xauna gefe, sannan yace, ina kwana
mami? Lfya lau, ina fatan ba ka tsananta wa kan
tunani ba? Ya kada kai, ya xanyi mami? Kin san
ba yin kaina bane? Ta dafa shi a sanyaye, kllm
ina kara gaya maka Al-ameen, kai kadai ne
garemu, kuma ka zama tamkar dubu, ba gare mu
kadai ba, gabadaya al'umma za su so rayuwarka
ta daure cikin fciki da walwala, saboda
muhimmancinta, ina so ka san wani abu yau.
Wlh na yi maka rantsuwar da ba kaffara da
rayuwarka ta salwanta, gara ni in mutu, don
na..... Ya rufe bakinta, a hankali, idanuwansa
taf, da hawaye yace, kiyi shiru mamina! Da ni
dake zamu rayu da yardar Allah cikin farinciki da
kwanciyar hankali. Har ga Allah na hkra da
sakeena mami, kawai ciwon fitar son ta ke
azabtar da ni. Ka kwantar da hankalinki mamina,
a hankali zaki gan ni yadda kike so. Tayi dan
murmushi tace, Allah yayi ma albarka! Da sauri
ya kwanta a kafadarta yana fadin amin mamina.
Zauna da kyau na hada maka brkfst. Kaga masa
na sa iya ta shirya maka da sassafe, na san
kana so kuma kana kewarta, don ba'a samu a
Rasha. Ya bita da kallo dauke da tausayi. Yace
nagode mamina, amma tare xamu ci ko? Ta jawo
fileta tana fadi ah! Me zai hana? Bari ka gani. Ta
loda waina a plate tana xuba miya ya ware ido,
yace mami kin cika abincin nan! Ita ma ta ware
idon tace injiwa? Ni da kaine fa? Sa hannu ka
gani ko asa man shanu? Ya kada kai, a'a kinsa
banso kayan karni. Ka bar dadi yaro. Yayi 'yar
dariya yace Allah ko? Ta tura masa a baki tace,
haba ai ba sai na fadi ba. Dady yai sallama
dakin ya karaso da sauri yana cewa iye! Masa
kuke ci kuka nuna min 'yan ubanci? Gaskiya ba
ha akeyi ba, ai sai ku kira ni ko? Ya tambaya
yana kallon al-ameen cikin ido. Ya gayara masa
wwuri, yace laifin mami ne, xauna abinka
Dadyna. Ya xauna yasa hannu ciki, yace ai mami
akwai rowa, Allah dai ya tsaga da rabona. Suna
dariya ta bashi amsa, ka san kuwa da na kawai,
na aka yi ma. Kaji ko? Tafi son ka akaina. Yayi
wuf ya rike hannu da yake kokarin kai loma
yace, ba xaka ci ba sai ka fadi! Gaya min, mami
ta hau dariya shima ita yake yi. Dady na ga dai
da ta rikice kanka. Tace babu wani sai kai,
sannan aka sameni, ko ba haka bane mami?
Tace ni xaka tambaya? Dady ya karbe yanki
wainar daga hannunsa ya tura masa baki, yace
cinye dana, ka bani amsa daidai. Bai gama
cinyewa ba ya dauko cinyar kaza ya tura msa, ka
ra da wannan kayi brush! Duk suka sa dariya,
ganin al-ameen na neman kwarewa, kan kace
kwabo sun yaudari Al-ameen ya cinye wainar da
mami ta zo da ita, domin dai shi suka yi ta
turawa da wasa da dariya ya take cikinsa. Bayan
sun kare, mami ta dube shi tace yanxun ka tashi
ka shiga wanka ka kimtsa, muje asibiti ka gaida
Umma.... Umma? Me ya sameta? Tashin hankali
ya sa ta sami hawan jini tuntuni, maganar jiya
kuma ta kara birkita ta jininta yayi mugun hawa.
Tana nan asibitin sun bata gado. Jiyan abba ya
taho da ita. Ya marairaice yace, Umma na asibiti
tun jiya baku gaya min ba? Ban dadin hakan ba,
dady yace kayi hrk, ganin kai ma baka da sukuni
ya sa muka kyaleka, kaji da guda 1. Ya mike
yace ba sai nayi wanka ba, yanxun xan tafi, idan
na dawo nayi, bai saurara ba ya wuce ya jawo
dirowa ya dauko key ya fice. Mami ta biyo shi
tace Al-ameen, ya tsaya cak! yana dubanta, ta
matsi sosai ta dafa shi, ka tafi a hankali, idan
kaje kace ina gaishe ta, ni ma xan biyo in na
dawo daga Lafai, ya dan lumshi ido, ya bude
yace xan kula mami, amma me xaki je yi Lafai?
Tace uzurina xai kaini. Allah ya kiyaye hanya, ta
amsa amin. Ya daga kai dubi dady dake tsaye
yace, sai na dawo dady, to ina jin ma xan
sameka asibitin. Yace shikenan sai kazo. Ya juya
yayi waje, su iya na kokarin fitowa su gaisa.
Amma ina saurin da yakeyi, ya hana su su same
shi falon, tuni ya kai ma'ajiyar motocin, ya
murza ya bar gidan. Umma na xaune an jera
mata filo, ruwan lipton kawai ta iya kurba, ya
xuna cikinta. Likitan ne yace ta dan jingina
kadan ta huta. Duk 'ya'yan sun kewayeta, abba
na xaune gabanta bisa kujera. Gaba daya tausar
xuciyarta suke yi don ta fidda abin a aranta.
Sallamar al-ameen cikin dakin ita ta dauki
hankalin kowa, suka amsa kona masa duban
tausayi, ganin yadda ya xabge kamar mai ciwo,
wai don ma su mami na yin iya kokarinsa
akansa. Ya bisu daidai sukayi musabaha, sannan
ya tsugguna gaban Abba suka gaisa. Tuni
ganinsa ya sa hawayen Umma suka tsinke, yayi
shiru a tsugunne. Abba ya dafa shi, yace sai ka
dawo ka sami labari maras dadi? To ina so ka
kwantar da hankalinka kayi imani da kaddara, ka
sani yau da ace mama na da 'yar uwa xan baka
ita, don in nuna maka iya kaunar da muke maka.
Mama ta zabi ta wulakanta mu, shi yasa na ke
son kowa ya cireta a ransa, mu manta da ita mu
kyaleta duniya ta hora ta. Kayi hkr kaji? Ya goge
kwalla yace naji abba, kuma nagode akan iya
kokarin da kukayi min, amma abba ina rokon ka,
don girman Allah ku ya fe mata, sannan ku
sanya mata albarka, a auran da xatayi. Duk
sukayi shiru, kowa ya xuba masa ido. Tausayin
sa na ratsa su, umma ta goge kwalla. Tace
Mama ba abar tausayi bace Al- ameen, don haka
ka daina rokon ayi mata afuwa laifin data aikata.
Ya kata matsowa gaban gadon yace, ba haka
bane Umma, ki san sharrin shaidan, sannan
xuciya bata da kashi, ba 'a son ran mama zata
aikiata wannan abin ba, xuciya ce ta saka mata,
na tabbata duk ranar da ta nutsu tayi tunani
xata gane lallai bata kyauta ba. Don Allah Umma
ko ina nan ko ba nan, idan Mama ta dawo ku
amshe ta hannu 2, ku samata albarka. Insha
Allahu shaidanin daya rinjaye xuciyarta, xai
kyaleta, ta dawo diya ta gari kamar yadda take
da. Abba ya kara dafa shi, yace idonka ya riga
ya rufe a son mama, shi ya sa baka kallon
girman laifin da ta aikata. Ya juya ya dube shi,
ba haka bane Abba nasan ina son mama kuma
har na mutu ba xan daina son ta ba, amma ku
yafe mata, don rayuwar ta, tayi kyau nan gaba,
ba farin cikin mu bane ace mama ta lalace tabi
duniya, tunda gaba dayan mu nan, muna son ta.
Kun yafe mata ko Umma? Tace kayi hkr Al-
ameen ba xan iya cewa komai ba tukunna, ya
abdulqadeer yace, ko mu bamu goyi bayan su
Umma suyi afuwa gareta ba, har sai ta sauya
zabin da tayi da. Tunda tace ba kai ba, to ka
kawo wani dan mutunci tamkar kai, amma ba
Dan liti ba. Wanna itace shawarar da muka
yanke. Yana rufe baki dadi ya turo kofar ya
shigo tare da gaishe-gaishe. Ya dubi al-ameen
yace, dr na jiranka. Da mamai ya dube shi, dr.
Lawal? Yaushe ya zo? Bai dade ba, muna shirin
fitowa, sai gashi shine nace ya xauna xan biyo
na gaya maka. Ya mike yayi sallama da su ya
bar asibitin. Bai sami mami ba, don itama driver
ya wuce da ita lfya. Dr. Lawal na babban falon
gidansu, ladi sun adana shi da kayan kusa da
baka, amma da ka dube shu kasan baya cikin
sukuni. Yana shigowa ya mike da sauri ya tarbe
shi suka kama juna. Dr. Lafai! Yace banyi xanton
xaka xo ba. Dole na xo, wannnan mummanan
labari ya hanani barci jiya. Yayi dan yake, kai
dai bari, mu xauna aboki na. Suka zauna kujera
daya, dr lawal yace, me yayi zafi likita?
Idanuwansa suka kada yace, bansan me ke
faruwa ba dr sama da sati 4 ina can na daina jin
wayar sakeena, aka ce min bata da lfya ne,
dalilin da yasa na dawo kenan don hankalina
yaki kwanciya ita kawai nake son gani. Ina xuwa
na iske labari ya sha bambam, wai sakeena ta
sami wani ya hure mata kunne, har ta mance da
manyan alkawuran da ta daukat min. Kowa yayi
iya kokarinsa wajen nuna mata gaskiyya, amma
sam tace ba san wannan ba. Abban ta kuwa ya
sha alwashin ni da ta fara kawowa akayi mana
baiko, ya sani ba xai daura mata aure da kowa
ba, face ni don haka yace ba xan koma sai an
daura auran. So da kaunar da nakewa sakeena
yasa bana tunanin komai Illa xumudin a daura
mana auran, shi yasa koda naje jiya bana nuna
maka komai ba.a xato na bai kamata in tona
kwanne sirri na sakeena ba, do kar a zage ta
matsayin maci amana, ina ganin kamar idan
muka kebe matsayin miji da mata, xan iya
rinjayar ta. Son da take take min ya sake
dawowa xuciyarta. Ashe duk abin da nake zato
ya wuce nan dr.lawal kawai na dawo jiyan su
dady ke gaya min sakeena ta gudu cikin dare ba
a san inda take ba. Al-ameen ya jingina da
kujera ya runtse ido sai hawaye shar... Na
malala, hankalin dr. Lawal ya kara tashim ya
xura masa ido jim sannan ya sauke numfashi ya
dafa shi, yace, kana cikin tashin hankali aboki
na amma Allah yace duk inda tsanani yakem to
tabbas da akwai sauki. Pls ka zama jarumi a
cikin jarabawar nan, ka bari hkr ya xama
sanadin samun saukin tashin hankalin nan. Ya
bude ido taf da kwalla, yace inason sakeena Dr.
Kai kasan hakan, yace kwarai da na sani kuma
xato na itama tana tsananin sonka. Ya matso shi
sosai yace haka ne, wlh sakeena tana sona, to
me yasa ta kini tym 1? Yace mata kenan Dr.
Lafai. Balle sakeenna na da kyau da xata iya
wasa da hankalin kowane da namiji. Watakila
kuma wancan yafi ka duk abubuwan da take
bukta. Dan wani minister ne a abja? Yace ban
nemi sani ba, a yau ne nake jin sunansa bakin
yaanta wai shi Danliti, danliti? Daga jin sunan
kasan ba wani bane. Da sauri ya amsa ai kuwa
wani ne.... (Hahaha Allah sarki lazy Dr.) tunda
ya sace min sakeena. Ko da kuwa kwara masai
yake yi. Inda ace xan gan shi xan iya durkuwa
gwiuwa 2 in roke shi, ya bar min sakeena ta.
Wlh itace rayuwata dr. Ya kada kai yace, ka
daina fadar haka Dr. Lafao kar fa ka mance wani
hani ga Allah baiwa ne, xa iya kasancewa
sakeena kyan dan miciji gareta.... Ya dakatar da
shi ta hanyar daga masa hannu.... Yace gaya
min kowace kalma dr. Amma kar ka aibata min
sakeena, ba xan taba ganin farinka ba. Ya xura
masa ido, kunshe da mamaki, kafin yace, ba nufi
nake nan ba aboki na, ina so ka gane cewar
bakomai da kake bane yake kasancewa alkhairi a
gareka, shi ya sa kullum ake son bawa ya roki
alkhairi wajen Allah. Yace sakeen alkhairi ce
gareni, tuni mafarkai na suke nuna min hakan,
har xuwa yanxun kuma jiki na yana bani sakeena
tawa ce, mishkila aka samu wani wurin, bana so
musu da su Dady ne kawai, shi ya sa nake nuna
musu na hkr da ita. Yace to idan baka hkr ba,
yaya xakayi yi? Tunda batayi da kai? Babu
abinda
BAKIN CIKI 2***10 Amma nan da iya shkrun da
xanyia duniya ba xan daina son ta ba har na
koma Ubangiji. Ya xura masa ido, yace Al-
ameen kar ka manta akwai gagaruminn aiki
gabanka wanda kowa ya xura ido don ganin
rawar da xaka taka, kasancewar kai kadai ake
tunanin xaka iya taka ta kuma mutanenan arewa
suna jiran daya tamakar dubu ya dawo masu da
abin alafahrin a duniya baki daya. Ina ka sami
nutsiwa ka fuskanci abinda ke gabanka ka tare
da jadda imani a cikin ranka, lallai Allah xai iya
baka wata. Ina fatan xuwa na ba xai xama abnxa
ba ba, kuma addu'ar duk masoyanka a zariya ba
zata fadi kasa banxa ba. Kowa yace Allah ya
musanya maka da lakhairi, na tabbata Allah xai
duba ya kawo sauyi na fadi daidai? Ya numfasa
yace ka fadi daidai abokina na, na gode ma kowa
bisa addu'ar da suka yi min. Xan koma rasha da
yardar Allah cikin yardarsa xan dage na fidda
kowa kunya. Sai dai abinda nake so ka sani har
in mutu ina son sakeena. Yace tuni na sani,
sannan ina da ilimin xuciya daya gareka, duk
abinda Allah ya xuba cikin ta, babu me iya
dauke shi. Ya koma ya jingina da kujrea,
rungume da hannayensa, ya dan numfasa ya
kada kai, dr. Lawal ya bubbuga kafadarsa ya
sake fadin, ka manta kawai abokina, ya wuce,
ya bishi da kallo kawai baice komai ba su dade
tare. Dr. Lawal na kara kwantar masa da hanakili
tare da nuna masa mahimmancinsa ga al-
aumma. Bayan azahar suke asibiti ya gaida
Umma, daga can ya wuce zariya, shi kuwa Al-
ameen gida ya dawo, don shima ba ya son yana
ganin Umma kwance tausayinta yana kara karya
masa xuciya. Ya rinka jin kamar su abba ba xa
su yafe wa sakeena ba. Wannan shine babban
tashin hankalin sa. La'asar ta kawo jiki yana
xaune shi kadai bisa gadonsa, tym-tym ya kan
dauki hoton da ke bisa kirjinsa ya duba. Hotonsu
ne shi da mama wanda sukayi a dakin Mami,
xuwan ta farko gidan. Karo barkatai kenan daya
daga hoton ya xura masa ido tsawon lokaci,
sannan ya mike ya sake kife shi. Ya laluba
aljihunsa ya dauko xoben da Mama da dawo
masa dashi, ya xare na hannunsa ya hada su
waje daya, ya xura masa ido. Sannan ahankali
yake wasa da su, ya rike kowanne yana hada su
karo. Cikin idanuwansa yake ganin ita ke rike da
wanda ya bata, suke karawa juna. Wannan karon
da karfinsa ya kara mata, na hannunta ya karye
nan da nan ta shagwabe, gaskiya ba hake ake yi
ba! Ba haka ake ba Dr. Al- ameen! Al-ameen
tsananin kiran ya dawo da shi tunaninsa duniya.
A firgice ya dubi Mami dake gabansa xaune. Ba
xai iya cewa ga tym da ta shigo ba, don haka
yake mata kallon mamaki, haka itama ta xura
masa ido mai dauke da questions. Mami! Yaushe
kika dawo? Ta sauke numfashi ta kada kai,
kafin tace, tsoron na Allah tsorona kar ka xaunce
al-ameen ka dawo cikin hankalinka mana! Yai
sauri ya runtse ido yana fadin Hasbunnallu wa ni
Imal wakil, Allahuma ajirni fi musibati wa
akhlifini khairan minha. Ya bnude ido jajur ya
dubeta, kiyi hrk mami.... Takatshe shi ba xan
bari rayuwar ka ta salwanta ba Al-ameen sai
inda karfi na ya kare, Allah na gani yarinyar nan
ta xalunce ni. Kafin yace wani abu, ta mike da
sauri tai waje, ya bita yana kira, ba su hadu ba
sai a dakinta... Mami.... Ta daga masa hannu.
Ban son jin komai, ta mika masa wani ruwa da
ke hannunta tace shnaye shi ka bani kofi. Yace
na menen? Ban son tambaya ni na umarce ka
kashanye, ka bani kofin. Ya daga kofin da sunan
Allah, ya kafa aabki ya kwankwade. Ta karbi
kofin ta aje gefe. Ya sake tambaya mami ruwan
me nasha? Tace baba liman ya bani taimako na
kawo maka, anjima zaka sake sha, gobe ka kara
da safe da yamma. Jibi in Allah ya kaimu lfya
za ka koma sch, domin fitar da dadin ka yayi
bookin ya je maka, ina fatan kajini? Jikinsa yai
sanyi, ya kamo hannnayenta 2 ya ja suka xauna
bisa kujera yace Allah sarki mamina. Allah bar
min ke. Nagode da karfafa min gwiuwar da
kukeyi. Idanuwanta taf da hawaye tace,
hankalina bai taba tashi ba irin na yau. Ban taba
jin faduwar gaba ba irin ta yaukai da zobuna
kake hira kana dariya, Al- ameen ban same xai
faru ba nan gaba. Kafadunta 2 ya dafa yace sai
alkhairi mamina, kawai xancen xuci ne ya fito
fili mami... Tace daga haka sai tabin hakali al-
ameen , yayi dan murmushi yace Allah ba xai sa
ba mamina, ya san ni kadai ya baki, kuma shi
mai tsananin tausayi ne. Allah sa ruwan da kika
bani ba wanda xai cire min son sakeena bane. Ta
xura masa ido cikin xafi tace, shine Al-ameen
Insha Allahu sakeena ba xata zama ajalinka ba,
ya numfasa yana murmushi da bai kai ciki ba
mami kenan, wa ya gaya miki sakeena xata
kashe miki tilon danki? Kuma wa ya gaya miki
danki xai ji dadin rayuwa ba tare da soayyar
sakeena ciknin xuciyarsa ba? Duka 2 tafiya suke
kafada da kafada mami, Allah yayi hukuncinsa,
don haka ban ji Baba liman xai iya cirewa. Bayin
kaina bane, kiyi hkr mami. Tayi masa xuru duk
jikinta ya mutu a hankali ta ce ko bai fita ba
xaka ji sanyi cikin ranka. Tunaninn ka xai
daidaitu da aikin kwakwalwar ka ta yadda xaka
yi mu'amula kamar sauran mutane. Wannan
shine farinciknm. Yace, Allah ya taimake ku
akan burin ku. Nima ya taimakeni akan nawa.....
Tace xamu ci gaba dayi da fada idan har kana
gaya min irin wadannan kalaman. Ya kada kai ba
xa muyi ba mami. To ka daina. Ya lumshe ido,
ya bude yace na daina, Allah yayi maka albarka.
Ya dora kansa kafadarta ya amsa da amin. Ta
ciga da yi ma nasiha yana sauraronta sai dai can
kasar xuciyarsa cike yake da xulumi, Allah ya sa
ruwan da mami ta ba shi ya sha ba wanda xai sa
ya mance da sakeena bane. Da wannan xulumin
ya tafi yin sallah la'asar hankalinsa bai kwanta
ba, sai da ya tura yatsansa ya arce
makogwaronsa ya kirkiro wa kansa aman dole.
Bayan sallar magriba dady ya shigo ya tsare shi
yaci abinci. Sannan mami ta debo ruwan
addu'arta ta mika masa, ya shanye. Allah Allah
yake yi tashi ya koma dakinsa ya jawo aman,
amma kmar dady ya sano ya ki barinsa tashi.
Yayi ta jansa da hirarrakin duniya, wai don ya
rage tunanu. Kafin ya bar wajen ya kwashe awoyi
sama da 2 takaice ya ishe shi, don ya tabbata
ruwn nan ya gama bin jininsa. Wannan karon bai
nemi yin aman ba, gado ya fada ya fara tunanin
iska, har bacci ya samuyi, da alama an fara
samun nasara. Shi kansa yayi mamakin irin
barcin da yayi bugu da kari ya rage jin xugin
xuciyarsa ke y, hankali kwance suka yi karin
safe. Mami ta kara bulbuo ruwan addu'ar ta a
gora, ta mika masa. Ya kwankwada duk ba a son
ransa yake sha ba, a yau takardun komawarsa
Rasha xasu kammalu, haka dady ya gaya masa.
Saboda haka ya umarce shi daya kasance cikin
shiri koda yaushe xa'a iya basu tym din tashi.
Jikinsa babu kasala ya koma bangarensa ya jwo
jakar kayansa yayi ta lda kaya har da wadanda
ya dade bai anfani da su ba. Ya wuce dirowar
madubinsa ya jawo ya kashe takardun cikin kaf,
dinsu ya dauko xai xuba jaka, wata ambula ta
fado duk hotuna ciki suka watse bisa kafet
daidadi shigowar mami dakin. Ya aje takardun
gefen gadon yana amsa sallamarta, sannan ya
tsugunna ya kwashe hotunan, akasarinsa duk na
mama ne, sai kalilan wanda suke tare. Tayi tsye
tana kallon katuwar jakar da yake lodawa kaya,
ya akayi mami na? Tace kamar bada jakar nan
ka xo ba? Ya mike dauke da hotunan a hannunsa
yana amsawa, xan kara wasu kayan ne, shi yasa
na sauya jaka. Ya matsya xai cusa hotunan, tayi
wuf ta karbe ina xaka da dasu? Ai wadannan
hotunan wuta ya kamata ka cinna musu. Wuta
mami? Me ya san xan sa wa sakeena wuta?
Saboda nan gaba xata xama matar wani, ka ga
haramun ne gareka kallon hotonta. Ina fatan ka
gamsu? Yayi shiru na 'yan dakikai kafin ya
numfsa, ya dubeta idanuwan har sun kada, yace
kin fadi gaskiyya mami, amma baxan iya cinna
wa jikin sakeena wuta ba, sai dai ina rokonki
dan girman Allah ki adana min su har xuwa tym
din da xata halasta gareni. Tayi masa xuru tana
shakku cikin ranta, addu'ar Baba liman batayi
tasiri bane ko kuwa bata fara aiki bane tkunna?
Ta kada kai ta dubi hotunan ta sake dubansa,
amma shi ya riga ta magana. Mami pls ki ajeye
min su inda ba xa su salwanta ba. Ta sauke
numfashi, xan boye maka sun tunda kafi son
hakan, gwaggo ce ta xo tana daki na. Ya ware
ido sosai. Gwaggo? Da sasssafen nan? Dole tayo
sammako, hankalinta a tashe yake, ka fito tana
daki.Tayi waje da ambulan din a hannunta,
shima ya biyo bayanta. Tana xaune a shimfida
bisa kafet ya xube gabannta dauke da murmushi,
uwargida ran fida, kuma sai ki bugo min
sammako kamar ban aika da cefane ba? Duban
tausayi take masa, ta dafa kafadarsa tace dole
nai sammako, in xo in ga halin da kake ciki. Ina
fatan xaka sanya dangana cikin ranka. Ka mance
da yarinyar nan, domin dai.... Ya katse ta, ya
kamata mu gaisa gwaggo kinxo lfya? Ya tsufa?
Tace tsufa na nan kuma lfya lau na xo. Amma
me yasa ka katse min magana? Babu komai gani
nayi bamu ko gaisa ba, alhalin ya dace na fara
gaisheki. Haka ne to ina fatan duk shawarwarin
da kowa ke ba, kana ji ka kuma dauka? Ka
manta sakeena... Da sauri ya katse gwaggo tuni
na hkr da ita, hasalima yau ko geb xan koma
sch. Ban xan dalilin katseni ba Al- ameen akwai
abinda baka so na fadi. Mami ta amshe, sosai
kuwa kina so ya mance da sakeena,
kunnunwansa ba sa son ji, shi yasa yake
katseki. Tace oho, to wahalar banxa kakeyi,
domin dai labari ya tabbata tare da shashashan
saurayinta suka tafi, kaga kuwa sai abinda Allah
yayi. Gara ka kama kanka ka san inda ke maka
ciwo. 'yan mata dai ga su nan birjik duk wacce
kace kule xata ce cas. Rayuwa kawai sakeena ta
xaba, don na tabbata yaron nan baxai aureta ba,
nawa ya lalata, ya watsar tana gani kuma ta
bishi, inm banda ita ma, rayuwarka ta sha
banban da wacce sakeena ta dauka, kaga kuwa
tafiyarka ba xata xama daidai da tata ba. Ka
fahimce ni? Wasu kwalla masu xafi suka sauka
bisa kuncinsa, hakan ya jawo mamaki ga
gwaggo da Mami suka xuba masa ido baki sake.
Xugum sukayi, daga bisani mami ta numfasa
tace ikon Allah! Gwaggo ta xare tagumi tace,
akwai sauran aiki, kuma ina mai tabbatar maka
, bata tym dinka kakeyi. Ya jawo hankaci ya
share fuska, yace, ko kadan gwaggo, labarin ki
tsananin tausayin sakeena ya cusa min, sakeena
ba haka take ba, nayi rayuwa da ita sosai na
fahimci halayenta, xan iya cewa nafi kowa
saninta, na fahimci halinta. ,Zan iya cewa nafi
kowa sanin ta hakika ya zalunce ta tunda ya
sauyamata rayuwa ya bata tarbiyarta ya gurbata
mu'amalarta da iyayenta da yan uwanta ya datse
tasananin soyayyar dake tsakaninmu ka ALLAH
bazai kyale shi ba ta ko wace hanya ya bi yayi
nasa a kanta sai ya ga sakayya,"ya mike da
sauri zai bar dakin gwaggo ta kwala masa kira
ya tsaya bakin kofa yana goge kwalla tace dawo
ka zauna ai ban gama magana da kai ba yana
daga tsaye gaskiya gwaggo kunnuwa na ba za Su
iya sauraron irin wadannan labarurrukan akan
sakeena ba,tausayin ta bazai barni sukuni ba
gara a bar ni cikin bakin duhu ina laluben inda
ALLAH zai sake hada fuskokin mu har ta zama
mata a gare ni," jikin gwaggo yayi mugun sanyi
tace dawo zauna nan ya dawo ya zauna gefenta
ya hade kai da guiwa ta dafa kansa tace idan
nayi kuskure kayi min afuwa amma ba laifi na
bane ka sani ko wace uwa tana kishin danta
kuma abinda ya faru da kai dole mai kaunarka
yayi bakin ciki balle mu da muka fi kowa kusa
da kai, na san kana son sakeena sai dai ba na
son idon ka ya rufe ka kasa ganin aika aikar da
ta aikata a garemu, ya cire kai ya dube ta ni
kuwa hakan na fi so gwaggo domin na yi imanin
ba yin kanta bane sace min ita akayi hure mata
kunne akayi da kalmomin shaidan addu'a zatayi
maganin abin, da zaki taimake ni da ita ma zan
fi farin ciki akan wadannan labaran da ki ke son
bani," gwaggo " mami ta karbe za a yi maka in
dai addu'a ce ka samu tashi kaje kaci gaba da
shirinka bai tofa komai ba ya yunkura ya bar
dakin,kamar daman can ya kosa ya
barshi,"gwaggo ta dubi mami hankali tashe tace
bai kamata ku kyale yaron nan ya koma haka
kawai ba tare da wani taimako ba tace tun jiya
na je lafai na samo masa wajan baba liman wai
nan yama sha ruwan addu'ar ke nan tafdijan ki
na kallo fa ko laifinta baya son a fadi wannan so
yayi yawa gara ma da auran bai yuwu ba da
muna kallo zai zama mijin ta ce,abin haushi
nama na jan kare, mami tace me ki ka gani
gwaggo?ALLAH dai ya zaba alkairi abin cewa ke
nan anan gwaggo ta wuni, Shi kuwa Alameen a
dakinsa ya wuni don baya son ana daga masa
hankali da labaran sakkena kazantar da baka
gani ba tsafta ce,kai a yadda yake jin mama
cikin ransa koda ya ga kazantar da idanuwansa
zuciyarsa ba za ta amince masa ba bai fito ba
sai da gwaggo zata koma suka yi sallama daga
nan dakin iya ya shige ya kudundune kamar
maraya sama da awa guda tana tausar zuciyar
sa da kalamai masu dadi,ya kuwa ji dadin cikin
ransa saboda kalaman iya sunfi rinjaye ga. Bashi
tabbacin idan sakeena matarsa ce duk rintsi duk
wuya sai ya aure ta karfe shidda dai dai dady ya
dawo masa da takardun tafiyarsa sun kammalu
kuma gobe da yardar ALLAH sha biyu ranan zasu
tashi don haka yana gama cin abincin dare mami
ta ba shi ruwan addu'a ya kwankwada kai tsaye
asibiti ya wuce don yin sallama dasu abba,kowa
yayi masa nasiha kuma sun jaddada masa ya
maida hankalinsa akan anibda ya kaishi kar ya
tsaya bata lokacinsa. Akan tunanin iska wanda
ba zai fisheshi ba,sai dai abin yana basu
mamaki yadda lafuzzan alameen ke nuni da
tsantsan son mama a zuciyarsa. Wanda ko alama
na bayyana har yanzu bai yarda sakeena. Taci
amanarsa ba, akwai mishkila wani wuri shiyasa
yake ta rokansu dasu taya shi addu'a ALLAH
yasa wata rana sakeena ra zama mata a gare
shi,gaba daya ya kwabe masu guiwa har suka yi
masa alkawarin yin yafiya a gareta idan har ta
dawo ta nemi gafara,kowa ya dubi alameen sai
ya ji tarin kwalla cikin iadanuwansa lokacin da
yake barin asibitin yana gugar fuska shi kansa
yaya soja a yau zuciyarsa ta karaya,tausayi ya
kwarara cikin jikinsa ya nemi haddasa masa
abin mamaki domin kwalla ya ji tam da
idanuwansa suna zubowa da saurinsa ya bar
wajan bai gama ganin wucewar alameen ba
AKIN CIKI 2*** 11 Karfe 8am suka dauki hanyar
abj tare da mami. Hankalinsu bai gama tashi ba,
sai da tym ya cika aka kira passengers. Al-
ameen ya rungume su, idanuwan sa cike da
hawaye, bakinsa na son yin magana amma kasa,
haka su ma Allah ya doro masu nauyin baki,
kallon juna sukeyi. Da sauri ya juya ya wuce,
yana goge fuska da hankici. Shi yasa suke tafe
cikin mota kowa shiru. Mami dauke da
taguminta. Tunaninta yay rayuwar dan nata xata
kasance a kasar da babu wanda ya damu da
wani balle ya sami wata kulawa ta musamman.
Dadi yayi tana share hawaye ya dan dube ta,
kada kai. Amma bai iya cewa komai ba don ya
san mami tana mukatar zubda hawaye ko ta ji
dadi cikin ranta, amma da ya ga abin yaki
karewa, dole ya tanka, ina ganin bai dace ki ci
gaba da bata ranki ba, wanda kika yi ai ya isa,
ko sai ya jefa ki wani hali ni in rasa da wanda
xanji? Ta goge kwalla, tace Alh. Ba haka bane
ganin Al-ameen na da abin fadi, amma yakasa
ya wuce da damuwar cikin ransa? Wa zai gaya
mawa a can? Kai tsaye ya bata amsa, Allah zai
gaya mawa, kin kuwa san ya fini, ya fiki, yafi
duk wanda kike tunani zai ba Al-ameen wanni
taimako, saboda haka ki bar shi da buwayin
sarki, shine xai masa dukkan gudunmawa. Ta
zare tagumi ta numfasa, haka ne, Allah ya
taimake shi, to amin kuma na tabbatar zai
taimakeni shin, tunda kika furta, addu'ar uwar
yankan wuka ne, don haka ki kwantar da
hankalinki. Ina fatan kin ji ni. Tace, naji alh.
Allah ya shige mana gaba, yace amin. Daga nan
Mami ta saki jikinta suka ci gaba da hira. Suna
shigowa gari, asibiti suka wuce gano jikin
Umma. Alhmdlh, Umma na samun sauki,
watakila ma xuwa gobe a sallameta. Ba su iske
yaya abdulkadeer da Abdul- rahman ba, duk sun
koma a wannan yammacin. Sun dan jima
asibitin, sannan suka dawo gida. Mami ta dukufa
rokon Allah cikin sallolinta, Allah ya sanyaya wa
Al-ameen xuciyarsa, ya cire masa wannan
makahon so sa ya ke wa Mama. Haka ta kwana
tunaninsa har barci tayi mafarkinsa xaune yana
wasa da xobunan guda 2. Shiyasa da ta fara tayi
ta da na sanin da ta raba shi da zobunan kafin
ya tafi. Suna karin safe karfe 8:30, waya ta
dauki kuka, mami ta baro tebur ta zo duka tayi
sallama. Muryar dan lelenta taji ya amsa. Farin
ciki ya lallube ta tace, Allah sarki Dr. An sauka
lfya? Yace lfya lau Mami, ina dadina? Ga shi
nan, ya taso ya ji kaini, ina fatan ba matsala?
Babu mami, na ma iske time table din jarabawar
mu ya fito, karatu kawai xa mu fuskanta, ni da
abokan karatuna. Dadi ya tsaya wajen tana
fadin, kai naji dadi sosai, to Allah ya baku sa'a
baki daya. Ga dadinka. Ya ce, to nagode Mami.
Dadi ya amsa suka gaisa. Dady time table ya
fito a taya mu addu'a. Yace kullum a cikinta
muke, amma xa mu kara kaimi. Ubangiji Allah
ya taimako. Yace amin. To xan wuce cikin sch,
sai kun sake jina. Yace, yayi kyau, all d bst!
Cike da fara'a ya amsa. Nagode Dadina. Ya aje
waya ya dubi mami yace hankalinki ya kwanta?
Bakinta har kunne ta amsa. Kai bari Allah ya
kara masa hkr. Yace amin, muje muci abinci ko?
Suka koma tebur. Mami tace abinci hankalinta
kwance. Ba Haka al'amarin yake wajensu Umma
ba, domin yau sun koma Fandagori sun iske da
kuara da suka bari baya. Hankulansu su kara
tashi yadda xance ke ta yamadidi a agari. Zagi
iri-iri babi irn wanda ba'ayi ba wasu suna ba
iyayen Mama laifi, amma da dama sunfi zargin
mama akan rashin hankali da ta aikata. Wani
abinda yafi daga wa Ubandawaki hankali shine,
wai gaba daya gundarin labarin daga bakin 'yan
uwansa da matayensu ya fara fitowa. Bayan
gaskiyya ga tarin karya da karairayin da suka
yiwa labarin kawanya, don haka ya tara su falon
sa bayan sallar isha'i. Wannan shine karo na 2
da na tara ku akan wasu maganganu na batanci
da suke fitowa daga gareku. A zatona ku masu
rufa min asiri ne ko bayan raina a matsayin ku
na 'yan uwana da muka fito ciki daya. Amma
bansan abinda nayi muku ba kuke min bita da
kulli, ko kuma ince kuke farinciki don wannan
abin ya sameni. To abinda nake so ku gane
shine, da frko dai bamu mukayi kanmu ba. Allah
ne yayi mu, mu kuma shi ya rubuta duk abinda
zai faru da mu. Babu wanda yasan kaddarar
mu2m bnalle ya share masa mummuna kafin
tazo. Da anayi da na gogewa Mama, don na duk
fadin duniyar babu wanda zai kaini BAKIN CIKI,
sai kuwa mahaifyar ta. Idan kuwa hakane, bai
kamata ace ku da matayenku, ku dauki wannan
al'amarin ya zamar maku abin hira a gari ba.
Kaddara na kowa, idan baku duba kusancin mu
ba, ya kamata ku duba wannan. Allah yai sani
ban zalunci kowa ba cikin ku ba, haka ban
xalunci mama ba, kamar yadda kuke yadawa
cewar mu ne muka dage sai mai kudi xata aura,
alhalin kun san komai a game da alkawarin
auran ta da Al-ameen. Kun fi kowa sanin
gaskiyya, amma kuka boye ta, saboda son rai to
na bar kowa da Allah, yayi min sakayya, Da
yardar Allah BAKIN CIKIN Mama bazai kashe mu
ba, haka zalika ina mata fatana shiriyar koda
yaushe. Mai surutu da dariya kuma Allah ya
bashi sa'ar yi. Amma kar ya mance kaddara bata
fatan shiryar kowa! Yana sa aya, ya mike ya bar
falon ba tare da wani yayi magana ba, ita ma
umma tashi tayi ta bi bayansa, yayi sauran ke
mazuran rashin gaskiya. Haj. Gaje ta buga tsaki,
ta bar falon. Daga bisani Haj. Hajjo ta lallaba ta
sulale, Alh. Basiru ya dubi Alh. Adamu. Yace
mutane munafukai ne, wai daga dawowarsa, an
sami wani kusugurmin ya feshe shi, don neman
fada. Alh. Adam yace, wai me akace? Au ya faru
ba za'a maida yadda akayi ba? Me za'a baoye
bayan ta gudun kowa kuma ya sani tare da
shegen yaron nan suka tafi! Ai ko ba 'a fada ba,
amsar a bayyane take. Tace, bata so, ba sai a
kyale ta ba, ta auri dan iskan da ake ganin ba
shi da asali ba, ba ita zata zauna da shi ba?
Wahalar tace tunda tasan halinsa. Tace sai shi.
Wai kuma mu ake ganin laifin mu, don fin karfi!
Mts.... Ya ja tsaki yayi waje abin sa. Alh. Basiru
ya mike yana kada kai, shi ma ya fice. Zaman
doya da maja yaci gaba da yaduwa cikin gidan,
duk da ba gaba daya sukeyi ba, amma babu wata
kyakkaywar fahimta atsakninsu. Shi uban dawaki
yana ganin ya kamata su ba shi hkr a
matsayinsa na babban su, sannan yana gani sun
yi masa laifi, don sun bada labarin yadda akayi
mama ta gudu, tunda ba su suka xuga ta ba,
komai ya kwana gidan sauki saboda haka basu
ga dalilin da xai sa Uban dawaki Ya dauki dalan
laifi ya dora masu ba har ya rinka jiran kalaman
tubansu. Su ma fah yanxun ba yara bane, girman
'ya'yan su ya kai, ya gane shekarun su sun cika
daidai matsayin masu 'yanci. Zuwan Ali da Ya
saed don duba jikin Umma da kuma jin labarin
Mama ko ta bayyana, Al-amarin bai yi musu
dadi ba, ganin Yadda iyayen su suka ware
ubandawaki suna masa yankar baya. Musamman
Ya ali, hankalinsa yayi mummunan tashi, babu
bata tym ya gurfana gaban abba yana bashi hkr.
Daga bisani Ya saeed ya shigo falon. Ya ali Yayi
rantsuwa da ace mama zata dawo ta amince da
auransa, maimakon Danliti, a shirye yake a
daura masu aure. Ko a gaban iyayen sa haka ya
maida zancansa. Haj. Hajjo ta rufe shi da bala'i
Allah wadarn wannan so kuwa, tunda yake hana
ka kishin kanka. To idan ma mafarki kake yi, ka
wanke idon ka, ka saurareni, idan har ni na
haifeka, ba xaka auri ragowar Danliti ba. Wannan
kalma tayi masa ciwo, bai san tym daya tasshi
ya tabbatar wa su Haj. Hajo cewa kashe miciji
sukeyi basa sare kansa. Domin ko banza sun
kwana da mamakin Ya ali da yayi tafiyarsa,
daga magana, shima ya gudun kenan? Ko mene
nufinsa? Muna iya cewa matsalarsu ce, ko dama
abba ya fadi kaddara na kan kowa....... Inna
saude ke xaune gefen gadon tana mata fifita.
Kallo daya zakayi mata, ka gane cewa ta jima
tana fama da ciwon tsananin damuwa, domin dai
ta fyade ta fita kamanninta. Amma hakan bai
hana ragargazar shagalin bikin da akeyi cikin
gidan ba. Nasan xakuyi mamaki, idan na gaya
musu cewar bikin yaya Ali da Ya Sa'ed akeyi.
Iyayeyn sun hur masu wuta, tun tym din da suka
lura da take taken shi Ya alin, sam hankalinsa
ba shi akan abinda zai fishshe shi. Shi yasa
suka matsa kwarai da gaske akn ya fiddo matar
aure ko su su fidda masa, ya kuwa tabbatar da
mahaifiya sa xata ita. Gudun kar ta manna masa
alakakai ya sa ya fito da yarinyar da ta dade
tana sonsa a birnin gwari. Amina sunanta, kuma
makwabtansa ne a gidan daya ke xaune. Sa'ed
tuni yake tare da Hassana a kd. A yau ne maza
suka daura auran 11am. Daga can suka wuce kd,
inda xa'a daura na sa'ed bayan azahar. 8pm
wannan rana motocin amare ke shigowa layin
gidan angwayensu, haka daidai wannan tym
motar Danliti parkn a kofar shagon sa dauke da
tasa amaryar. Cike da mamki ayuba ya taso, ya
bude kofar yana fadin, wa nake gani kamar
amafarki? Wai dama kuna tunanin gida? Dan liti
ya fito yayi doguwar miki, yana dariya, yace ah
gamu kuma mun dawo, ya juya cikin mota ya
cigaba da fadin, ya Gimbiya anan zaki sauko ko
na karasa dae gida? Ta kada kai, tace, naji tsoro
ya kamani Danliti, bansan yadda xanyi ba? Yayi
'yar dariya. Yace tsoro kuma? To me xa suyi
miki? Ta kada kai bari dai na sauka nan, canm
ajima na karasa gidan. Ya kace da dariya. Amma
ke shirmen ki yayi yawa, to fito ki shiga ciki. Ta
ballo murfin ta fito, kai! Anya kuwa Mama ce?
Tayi wata shegiyar kiba ta kara ja, ina ganin shi
yasa Ayuba ya xura mata ido, tym din da take
mika masa gaisuwa. Danliti ya bude but suka
ciro manyan jakunkuna guda 2 da kit, sai manya
ledoji guda 3. Ayuba ya taimaka suke shige da
su cikin shago. Kai tsaye dakinta shige ta xube a
katifa. Duk suka biyo bayanta. Danliti ya xauna
kusa da ita. Yace kin gaji ko? Tace kai dai bari,
kamar in kwanta inyi ta barci wlh. To ki kwanta
mana, ai ba kya jin yunwa ko kinaji? Ta kada
kai, banji, to ki kwnta ki huta ne, xuwa karfe
goma sai in tashe ki, ki koma gida. Haka za'ayi,
ta jawo filo ta yada kai, suna kallon juna suna
musayar murmushi. Ya lukuce mata hanci, yace
baby na kenan. Ta juya gefe tana 'ya dariya. Ya
mike ya dubi ayuba yace, to muje dogari. Ya
juya yana murmushi, ina tsarabata? Yace yauwa
ka tuna min, ya suri jakar leda suka fice da ita.
Ya xauna bisa kujera ayuba na kan tabarma, ya
zazzzage kayan kedar a gabansa. Gaba daya
kayan sawa ne. Na gayu ya siyo masa, ya dube
shi suka hada ido, yace ga tsarabar legos nan.
Baki sake yace babu wai, har ma ga tsaraba nan
duka naka ne. Ya washe baki m amma na gode,
watau shi ya sana kunyi jajur abinku, ashe kuna
bakin teku. Yace, hutu ba karya bane ayuba, ga
kuma lafiyayyar bebi na, nake gaya ma. Yayi
shiru yana kallon sa, fuskarsa gaba daya
tabayyana babu abinda bai faru ba. Ya numfas
duk jikinsa ya mutu yace, bakaji Danliti. Me nayi
ma tukunna? Ko kaji surutu ne a gari? Ya gyara
zama yace ba'a tonawa Danliti, abinda nake son
ka da shi, ku sasanta ka aureta kawai, ka ba
masu surutu kunya, donn sunce ba auranta
zakayi ba, tayi saki reshe ne, ta kama ganye, ya
shafa habarasa yace, ko? To ai ba suyi karya ba,
shagali kuma basu ga komai ba daga nan ma
illa masha Allah ba za mu daina ba. Ya kada kai
yace, meye nawa a ciki? Idan ka huta ko xuwa
gobe mayi lissafi. Yace ina fatan akwai kudi
sosai, don wanda na tafi da su naci uabansu, ya
amsa ciniki na na ba laifi, sati biyu ma da suka
wuce na je kno na karo kaya da cinikin yafi
haka. Da kyau mutumina, shi yasa nke sonka
wlh. Yayi 'yar dariya yana daga kayan da aka
kawo masa, ni kuma ina sonka da nutsuwa ba
amma kakiji. Ya mike ya nufi daki yana cewa,
kai ka fiye surutu, bari in baka wuri. Ya shige
dakin ya bar ayuba da kallonsa. Ya kada kai
yace aransa, Allah ka shiryemu. Shi kuwa Danliti
komawa yayi ya hana mama barcin. Karfe 10 ta
dan gota, dan liti ya umarci Mama da ta koma
gidan iyayenta, su san ta dawo, dan su san
matakin karshe da zau dauka. Watakila hakan su
ta cimma ruwa. Watau su amince da auransu
cewarsa madugu uban tafiyar. Ya hado mata
kayanta taf! Da katuwar jaka, tana xaune tana
kallonsa, kafin tace gaskiyya ba xan dauki jakar
nan ba, guda uku kawai dauka cikin kit, in tafi
dasu. Ido waje ya tambaya, sabda me? Ka sani
ko su koroni? Ka bari tukunna mu gani, idan
suka kyale ni, sai in dawo in kwashe sauran.
Idan basu kyaleki ba fah? Sai na dawo nan ka
yanke hukunci duk da zaka yanke. Ya xura mata
do, ai iyayenki na san ba su ki karbarki ba,
hasalima ai laifin su ne, na tabbata yanxun sun
gane kuskurensu, dole su lallabaki. Ta doke
kafadarsa tana dariya, har ma kasan dole su
lallabani? Kai dai ka yi fatan su amince da
auranmu. Yace shikenan, yanxun ki dauki abinda
xaki dauka na rakaki, dare nakara yi. Ta bude kit
ta xuba kaya kala 3, yasa hannu ya dauko wata
'yar karamar doguwar riga yace..... Yace ba xaki
dauki wannan rigar ba? Tace wannan shegiyar
rigar? Shegiya? Lallai ba ki san yadda take mi ki
kyau bane, a'a ka dai barta anan, sanin kanka
ne, su Abba bna za su barni na sanya taba cikin
gidansu. An wuce wurin, ki barta kyasa a gidana.
Ta yada kai kan kafadarsa tace ashe ka gane. Ya
tsikare ta, ta mike xumbur! Ban fa so Danliti
banso! Ta figi kit dinta, tayi waje baki a ture. Ya
kwaso mata gyale da takalmi ya biyota yana
fadin sorry 'yar bebi na! Taja ta tsya tana
haraarsa, ya yafa mata gyalen, ya aje takalmin
gabanta ya jawo kafufuwanta, sa abinki mu tafi.
Ta xura kafar tace wa Ayuba, sai da safe. Yake
yayi ya amsa, Allah ya kaimu. Suka fice, Danliti
na cewa, har kin tabbatar da xamanki a gidan ne
kike ce masa sai da safe? Tace gane min hanya
wai, makaho ya so gulma. Ya ci gaba da dariya,
suna tafe suna hira. Gab da gidan, ya tsaya
sukayi sallama, idan kuma ya gan ta ta dawo
shikenan. Y koma ita kuma taci gaba da tafiya
hankalinta kwance yake, don bata saka komai
illa in su koroto, ta koma inda ta fito. Daga
bisani ma wata dabara ta fado mata. Tana
dosowa kofar gidan, ta hangi kamar ana hada
hadar jama'a, duk da dare ya fara yi, kana iya
gane wa ana sha'ani a gidan. Bata yi wa kowa
magana ba,a haka suma babu wanda ya
shaidata. Sai da ta shige xauran karshe ta aje kit
dinta, ta xauna akai ta hade kai da guiwa ta
kirkiro kukan dole ta shiga yinsa har da
shesheka, sannan hankulan masu wucewa ya
fara xuwa gunta kuma, Ya ali shine mutum na
farko daya fara dosar ta da tambaya, wai wacece
xaune? Gida kike son komawa? A zata son cikin
'yan kawo amare ne, yayi dan murmushi, don ta
bashi dariya. Da girmanki da komai kike
kauyanci? Dan Allah tashi ki koma cikin gida
tun kafain yara su fara miki dariya. Ko an yi miki
wani abu ne? Daga ji ta gane mai magana, shi
yasa ta dago sosai ta dube shi, kawai batare da
tayi magana ba. Gabansa ya tsinke ya fadi
xuciyarsa ke ambato sunan, mama? Sannan ya
tsugunna gabanta ya furta a hankali, mama!
Hawayenta suka kara tsunkewa, ta sadda kai,
tana gogewa da bayan hannu. Innalillahi wa Inna
illaihir raju'un! Ya waiwaiga babu mai kallonsa
yayi sauri ya ja mayafinta ya rufe fuskarta, yace,
taso muje, kar ki bari kowa ya ganki. Ya ja
hannunta suka sulale dakinsy Danlami. Babu
kowa cikinsa, duk suna can wajen fatin da
sukeyi da abokansa. Ya xaunar da ita gefen gado
ya tsugguna. Yace, yaushe kika dawo mama?
Baki na rawa ta amsa, yanxun, idanuwansa suka
kawo kwalla a raunane. Yace abinda kikayi kin
kyauta kenan mama? Da mtuncin ki da komai?
Iyayen mu masu girma da daraja a gurin jama'a,
kika tozarta su? Haba mama, kamar baki sami
tarbiya ba? Ta goge kwalla. Tace, ba haka bane,
Ya ali me yasa zaku rinka ganin laifi na ni
kadai? Nace ga wanda nake so, ba sai a ba ni
shi ba. Ina ruwan kowa da rashin asalinsa? Ai
dai ba daga sama ya fado ba, da uwarsa da
ubansa. Yace, Maganar banza ce wannan mama,
don na tabbata Daliti bai fi miki iyayenki ba. Kin
kuwa san halin da umma ke ciki tun ranar da
kika sa kafa kika bar gidan nan? Kin daure min
kai, ban taba xataon zaki aikata irin wanan
mummuna aiki ba. Tace hakan kadai xai memin
mafita kuma akan bakana na dawo ko Danliti, ko
su rasa ni baki daya. Ya xura mata ido, yana
kada kai. Afuwa ya kamata ki nema ku sulhunta
da iyayenki, su sa miki albarka, ko kin ga
rayuwa mai kyau da anfani nan gaba. Saboda
haka ki xauna anan ki jirani, xan shiga wajensu
in kwantar musu da hankali tukina, gaskiyya
bana so ayi miki taratsi cikin jama'a, kuma
gidan cike yake da baki. Baki? Me akeyi a
gidan? Ya amsa, biki na akeyi dana seed. Kana
nufin kunyi aure? To Ya xanyi, tunda kinki ni
Mama? Akan dole na yi auaran nan, su Baba sun
matsa min. Ina muku murna, nima Allah yasa ni
a danshinku. Ya xura mata ido gwanin tausayi.
Yace, nasan ba xaki ji komai a ranki ba, tunda
ba so na kike ba, amma ni har kwanan gobe ina
sonki, shi ya sa abinda ke faruwa da ke ya xame
min ciwon cikin raina, ki yiwa girman Allah
mama ki sanya tunanin ki dawo sak! Yadda
kowa ya sanki. Karka damu dani Ya Ali, ko da
yaushe ina gaya ma kai dan uwana ne, kauanar
mu ta jini ce mai asali. Kwanciyar hnakalina
kuwa Danliti ya zama mijina. Ina fatan iyayen
Al-ameen sunyi xuciya su fasa? Ko baka ji
komai akai ba? Ya xuba mata ido yana
mamakinta, ya jima bai amsa ba, kafin yace, Al-
ameen ya koma Rasha da ciwon xuciya Mama.....
Ta katse shi ido rufe ta dafe kirji. Tace, nagode
Allah! Har naji sanyi cikin raina. Ya kada kai
yana kallonta. Yace, baki masa adalci ba, baki
tsoron amanarsa ta ciki? Akan me? Bafa dole
bane na aure shi, ina son kowa ya gane wannan,
kawai kaje ka gaya masu na dawo din, kaji me
xasu ce? Yace ni ne nayi niyyar yin hakan, ba
sai kin bani umarni ba. Yi hkr Yaya, bai tanka
ba, ya tashi ya five, ta bi bayansa da kallo tana
fadin cikin ranta, je ka dawo, duk na kosa in san
babin da nake. Cikin dakin yayi sallama, abba
ya amsa masa yana kokarin hadawa Umma shayi
ta samu ta dan sha, ya akayi Ali? Ya xauna gefe
kusa da shi, yace babu komai abba, wata
alfarma naxo nema wajenku. Hankalin abba ya
dawo gare shi, yace ina jinka. Allah ya sa batafi
karfi na ba. Ya kada kai ya amsa, bata fi ba
Abba, duk mai laifi idan ya nemi afuwa, me
yakamata ayi masa? Ya dube shi da kyau da
mamaki yace, ayi masa afuwar, domin Allah
yana son masu yafiya ga bayinsa. Su kuma masu
laifin su yi alakwarin ba xasu sake komawa ga
wancanm laifin ba. Laifin me kayi? Ya amsa,
laifin mai girma ne Abba, a misali Mama ta
dawo ta nemi gafara, abba xa ka karbi tubanta?
Ba abba kadai ba harda Umma dake kwance ta
xubo masa ido, abba ya jima kafin ya numfasa.
Yace Bansan dalilin da yasa ka min tambayar
nan ba, amma ina so ka sani, mama ta aikata
laifi mafi muni a shafin tarihin gidan nan, da mu
karbeta da kar mu karbeta, bakin fentin da ta
shafa mana yana nan baxai goge ba, ina so ka
sani Ali, xaiyi wuya a fadin gari na Mama ta
sami wani mijin, face katon daya dauke ta ya
boye wani wuri tsowon watanni 3. Abu na karshe
da nake so ka snai, shine bai kai kadai ka rokeni
ba. Al-ameen ma ya rokar mata gafara kuma
nayi masa tare da alakwarin ba xanki karbarta
ba. Saboda haka ka kwantar da hankalinka,
muddin Mamma ta dawo gidan nan, ba xan ce ta
koma ba, haka xalika idan bata sauya ra'ayinta
ba, ba xan ce mata a'a ba, Allah na kallo, nayi
kokarin na, don nuna mata hanyar kwarai da
samun abokin zama na kirki mai kyan asali. Ko
duniya ta zageni, alhakin Na suka duka kuma
zamuyi shari'a da su gobe kiyama. Kawai ji yayi
kwallah na xubo masa, saboda tausayin Abba,
yasa hannu ya goge, abba ya riga shi sake
magana, ka daina kuka Ali, kaddara ce, tashin
hankalina daya, mahaifiyarta da ta kasa samun
nutsuwa. Ina jin tsoron kar ciwon xuciya ya
kamata kamar yadda likitocin da ke duba ta
suke gargadin ta kullum. Dalilin da yasa kenan
nake fatan Allah ya sa mama ta dawo, watakila
ya zama waraka ga mahaifiyarta. Na tabbata
hankalinta xaifi kwanciya idan tana ganin ta
koda a dakin auran Danliti ne. Ya Ali ya gyara
xama yace, gaskiyya ne abba, kuma naji dadin
bayanan ka. Saboda haka ina mai farin cikin
shaida maku cewar mama na nan ta dawo. Abba
ya xura masa ido. Umma kuwa ciccibawa tayi ta
tashi xaune. Ba fahimce ka ba Ali? Inji Abba,
yace Mama na nan a cikin gidan nan, idan kun
ban izini, zan shigo da ita ta roki gafararku.
Suka dubi juna shi da Umma baki sake, tuni
hawaye suka tsinke mata, tana kada kai tare da
salatin Manzo. Abba ya dube shi yace, je ka
ashigo da ita Ali. Har ya mike ya sake komawa
ya xauana, yace Abba ina fatan ba xaku daga
mata murya ba, kasan gidan na cike yake da
baki. Yace Insha Allahu, ba xan daga mata ba.
Yace nagde abba. Ya mike ya wuce, abba ya
bishi da kallon, sannan ya dubi Umma, ashe
haka Ali ke da hankali? Nayi kuskuran hana
masa auran Mama tunda farko. Umma ta goge
hwaye tace, hakika mama tayi asara masoya 2.
Haka Allah ya so, ba mu da abinyi, dai yi masa
godiya, abba ya sauke numfashi, sukayi xugum
suna sauraron ta yadda mama xata bayyana
garesu. Jimawa kadan suka tsinkayi muryar Ya
Ali yana fadin ki shigo mana! Na gaya miki
komai ya wuce, ki shigo kawai. Make-maken
munafurci takeyi ba wai ainihin tsoron bane cikin
ranta, da su abba xa suyi kuskuran cewa ta juya,
fes! Zata juya babu waiwaye sukayi sallama
dakin. Ya ali na dauke da kit dinta. Ta toge
bakin kofa, yasa hannun ya janyo ta har
gabansu abba dake sake da baki suna kallon
abin al-ajabi. Gata abba, umma ga Mama, ku
mance da abinda ya faru, ku amince da xabanta,
ku sa musu albarka, sai kuka ga Allah ya basu
zuri'a abin alfahari. Mama ki durkusa ki roke su
gafara. Ko dama a durkushen take kuma tuni
hawayen suka tsunke mata, murya na rawa,
tace..
BAKIN CIKI 2***12 Abba kuyi hrk, Umma ki yafe
min. Abba ya numfasa yana kada kai. Ya ce a
rayuwata gaba daya Mama ba tba xataon xaki
min irin wannan mugun butulcin ba. Na dauke ki
'yar da na dauki burin duniya na dora a kanki.
Kece kika bambamta da kowa cikin xuciyata,
kuma na nuna miki dukkan gata amma dare
daya, kika numa mana akwai wanda ya fi mu
muhimmaci a rayuwarki. Tabbas na yarda da
hakan, don a tunani na xan ga kin dawo kin
bushe a lalace saboda tunanin kin barmu cin
BAKIN CIKI sai gaki Fes! Kinyi kiba. Ban miki
baki ba, ba kuma xan miki ba, amma ina mai
tabbatar miki in rasa masoyi, kin rasa mai
tsanin kaunar ki tsakani da Allah, kuma a yau na
kara nadamar hana Ali auaranki tun farko.
Maganata karshe itace, tunda kin nace sai
Danliti to ki gaya masa ya turo magabatansa,
muyi magana, sannan kiyi wa Yayanki Ali
godiya, domin yayi miki dukkan taimako.
Zaciyarta fara sol! Jin Abba ya ambato Danliti ya
turo. Ta kara dukawa tana goge kwalla. Tace,
ngde abba, kuma ina kara baku hkr, don Allah
ku yafe min. Ta rarrafa gun Umma ta cusa kanta
jikinta, umma kiyi hkr! Ta share hwaye tace ai ya
wuce Mama, kinci albarkacin al-ameen da ali.
Amma gyara kayanka, ai baya zama sauke mu
raba ba. Ki bi duniya a sannu, domin ita duniya
budurwa ce mai kyale-kyale da yawa, da zarar ka
biye mata, to ka bace ka kuma shiga uku ka
lalace. Ban da abin kari a gareki, don nasiha
anyi miki, amma kin rushe saboda batan basira.
Allah ya ganar da ke, ya sa ki a hanya
madaidaiciya. Ya ali ya amsa da amin, yayin da
mama ke ci gaba da gugar hawaye. Alin ne ya
cigaba da cewa, don Allah abba karku nuna
kowa ta dawo har tym din bakin nan xasu koma.
Ko su Baba a kyale su tukuna. Ke mama ina son
ki cigaba da xama cikin dakinku dan Allah, na
san xuwa gobe da yamma kowa xai watse, sai a
kam magana ta gaba, kinji? Ta amsa da kai,
Abba yace shikenan Ali, kana son ka rufawa 'yar
uwarka asiri, asirin kuwa da ya riga ya tonu.
Yace kayi hkr dai abba, yace babu komai, ta
tashi ta koma dakinta, idan tana jin yunwa,
akwai abinci, yace xaki ci abinci ne? Ta kada
kai, to taso na raka ki dakinki. Umma mun gode,
tace Allah yayi albarka, ya amsa da amin. Tare
suka mike suka bar dakin. Umma ta tafa hannu
tana salati, sannan ta buga tagumi. Yanxun alh.
Danliti xata aura? Yace, t ya xamuyi, wa kike
ganin xai fito neman auranta, bayan ya san
wannan kwamacala? Haka nan xamu hkr da
abinda Allah ya kaddaro, yanxun dai bana ce ya
turo ba? Sai mu sa ido mu ga wadanda xai turo
din. Ta numfasa, tace Allah shi kyauta yace
amin. Ke dai ki kwantar da hankalinki, ki daina
xa damuwa a ranki don Allah. Tace naji alh. Ya
ciga ba hada mata shayin suna tattaunawa.
Kamar yadda ake tattaunaea da mama da Ya Ali.
Shawarwari kawai yake bata, tana sauraronsa
kamar gaske. Har kusan sha daya da rabi suna
tare. Dagab bisani yayi mata sallama ya barya
cike da farin ciki da baya misaltuwa. Nan da nan
ta fada bayi tayi wanka, ta kintsa jikinta ta
kwanta. Kewar Danliti ta lullube ta, fadi take
cikin ranta, ba dan dare yayi ba da naje yiwa
sweety Na albishir. Da kyar barci ya sace ta
saboda murna. Washe gari hidima taci gaba,
mama na cikin dakin na kulle babu wanda ya
san ta dawo, daga Ya Ali sai su Umma. Kuma
anyi sa'a taji maganar Ya Ali batayi marmarin
fitowa ba, sai shi ne ma ya kan saci jiki ya
shiga wajenta, ya ganta yaji dan ji sanyi aransa.
Allah sarki! Garin dadi na newa, iska na ta
wahalar da mai kayan kara, bayan sallahr la'asar
baki suka koma muhallin su aka bar amare da
angwayensu. Shi kuwa Ubandawaki 'yan uwansa
ya tara falon baki yace, naki ku ne a matsayin
ku na kannena na in shaida muku cewar Mama
ta dawo daren jiya, kuma har na yanke hukuncin
ta gayawa Danlitin ya turo magabatansa, muyi
maganar aure. Ban san yadda zaku karbi abin
ba, ko da mahimmanci ko ya zama abin dariya a
gareku, duk daya ne, ni dai na fita hakkinku.
Suka dubi juna cikin sigar tsarguwa, sannan
Alh.basir yace, ai shikenan yaya, amma banji
dadin yadda kayi mana fassara ba, ya kamata
kayi mana uxuri tunda mun ce maganar nan
bada wata manufa muka fadeta ba. Amma ace
mama ta dawo tun jiya, sai yanxun mukeji? Ba
komai. Alh. Adam ya cage, tabbas naga Danliti a
shagonsa, sai dain banyi tunani tare suka dawo
ba, tunda banji labarin ba a cikin gida. Sai dai
Yaya a gaskiyya muna so mu ganar da kai cewa
ba farinciki mukeyi da abinda ya sami mama ba,
mutuncin gidan nan, ai duk namune, me zai sa
muyi murna da rugujewarsa? Abba yace duk naji,
magana ta gaskiyya, Allah kadai yasanta, don
shine masanin sirrin xukata. Abinda ya sa bau
san Mama ta dawo ba, sai yanxun. Ali ne ya fara
ganinta kuma ya xo ya sameni guiwa 2 ya roke
ni da kyale mama kar in daga murya, saboda
baki fa ke cikin gidan nan. Idan sun tafi ayi su
wacce xa ayi. To maga ma ta kare, nacewa
Danliti ya fito a daura musu auran, su karata.
Allah dai ya gani ba da son raina bane. Fuska Ya
mutse Alh. Basir ke cewa, Dan liti xata aura?
Yace bamu da abinyi, haka Allah ya so, sai dai
muyi mata fatan alkhairi. Saboda haka bana son
abin yayi tsawo, yana turo sai aure. Ya turowa
za'a sa rana kuma ba zata wuce sati 3-4 ba duk
abinda Allah ya hore min shi xa'a kai mata. Ita
kenan maganara, kowa na iya tafiya harkokinsa,
mu saurari xuwan magabatan nasa shikenan,
Allah ya nuna mana. Haka suka fadi baki
dayansu. Abba ya amsa da amin, suka bar falon
ba yabo ba fallasa, cikin xukatansu, ma'ana
intayi ruwa rijiya in ba tai ba masai. Suna shuga
sasan su, suka bajewa iyalensu babu bata tym
suka fara xuba sharhi. Haj. Gake kuwa har da
guda. Daga bisani suka baxama sassan Uban
dawaki, don gain Mama tare da yiwa Umma
murna dawowar Mama fida, amma a zahiri a
cikin xukantasu yanayin Maman suke son gani.
Suka kwarara sallama, umma ta amsa, sai
mukaji daddadan labari! Ina maman? Inji Haj.
Hajjo, tana dakinta, gaba daya sukace Allah shi
kyauta na gaba. Yanxun da Danliti xa'ayi auran?
Tace, nufi ne Allah, duk abinda ya rubuta bamu
isa mu goge Ba. Haj. Hajjo tace gaskiyya ba
haka muka so ba. Sai dai hkr kwai. Haj. Gaje ta
tabe baki tace, ya xama dole, amma a hakikanin
gaskiyya mama ta bamu kunya. Ajin ai ba daya
bane in banda batan basira. Koda yake ance so
mako ne. Allah ya sanya alkhairi. Sukayi dan
shiru, kafin suka nufi dakin Mama, ina kike?
Kina jin mu amma ba xaki fito ki gaishemu ba?
Tana xaune gefen gado, ta fesa ado kyanta ya
kara bayanna, banda haka da ibar da ta kara
suka kalli juna sabe da haba, kafin Haj. Gaje ta
soma xuba, lallai Mama, watau hankalinki a
kwnace kika je, ki ka dawo! Wannan kiba haka?
To Allah yasa ki sami irin wannan a gidansa.
Haj. Hajjo ta amshe amin dai, kin dai riga
kinsan halinsa, komai yayi miki sai ki hadiyewa
cikinki, kar ki doshi kowa, tunda kin nace shi
kike so! Ko kuwa gaje? Tace haka yake yaya, ai
kowa ya sayi rariya yasan zata xubda ruwa.
Mayafinta dake bisa filo ta figo ta mike tsaye ta
xura takalmanta tayo waje tana yafa gyelenta, ta
barsu anan sake da baki, suna kallon juna. Ko
kinga dibar albarka? Inji Haj. Hajjo, Haj. Gaje
tace, mamaki kikeyi Yaya? Karfa ki manta
watanni 3 ta shafe a bariki, an kuwa ce xama da
madaukin kanwa, shike kawo farin kai. Mu meye
namu? Ta malam ai bata wuce amin. Can suka
sameta dakin Umma tana neman izinin zuwa
wajen Danliti, don ta shaida masa sakon abba,
suna isowa, umm ana fadin bance kije ki xauna
ba, mutunciki shine ya biyo ki nan kofar
gidanku. Saboda haka daga yau kar na sake jin
kin koma shagonsa. Tace, to Umma, insha Allah
yanxun xan dawo. Ta sa kai ta fice, ba tare da
Umma ta kara wani abu ba. Nan su Haj. Hajjo
suka xauna suka cigaba da kwasar tsegumi, ita
kuwa tana fitowa xauran farko, angwaye ta ci
karo dasu, saeed Ya maka mata harara, ya wuce
abinsa cikin gida. Ta dubi ya Ali, tace me nayi
masa? Yace kin fi kowa sani. Taja dogon tsaki,
aikin banxa, to shinme me? Don ya ki min
magana? Yace, kin baci da Rashin K mama, me
yasa? Da ba haka kike ba. Ta dan tabne baki
tace, ni ina da wurin xauwa, ba na fito magana
da Ya Saeed bane. Yace amma ba kije kinga
amare ba. Xanje ai, so nake in sauke wannan
nauyin ko ni,a na kama dahir. Yayi dan
murmushi yana kllonta, mama kenan, to a dawo
lfya, nasan sakon bai wuce na Danliti ba. Tayi
'yar dariya. Shi ysa nake sonka Yayana, bari dai
in dawo amaryarka ka xan fara xuwa na in gani.
Ta wuce tana cigaba da dariya, ganin yadda yayi
tsaye duk jikinsa ya mutu. Ya bita da kallo,
sannan ya kada kai, yace, ni ma ina mutuwar
sonki Mama. Ina ma ace hankalinki xai dawo
gareni? Ya sauke numfashi ya shige wajen
amaryarsa. Bakinta har kunne take sallama kofar
shagon, ayuba ta gani xaune ckin shagon ya
amsa mata cike da fara'a amaryarmu kenan, ya
gajiyar tfya? Tace tabi lfya, ina mutumin? Ya
amsa yana ciki tun azahar yake barci saboda
ragwanci. Ta fara dariya, lallai kuwa ragwanci,
barin inshiga dole ya tashi ya bani goron
albshiri. Ta wuce ciki, ayuba na fadin, ya dai
kamata ya tashi ko salla ya samuyi. Kan tsaye
bisa katifar ta fada, ta dada masa duka cinya,
don Allah tashi rago! Ka wani baje kana gugar
barci, ni ina can ina tunaninka. Ya bude ido
firgigi yana kallon ta jim, sannan yayi dan
gajeran tsaki. Yace kash! Wlh ba don ke bace,
marin Mutum zanyi. Kin ji dadin barcin kuwa?
Tayi far da ido, tace ko? To ka tashi, na tabbata
dadin barcin bai kai albishir din baki na ba. Ya
xuba mata ido yace fadi ina jinki. Idan kuma bai
fi ba, kinsan Allah sai na sanya ki kuka, ai kin
san gamuwar mu babu tausayi. Tayi 'yar dariya,
tace, haba duk wannan kukan wasa nakeyi,
kama daina hura hanci. Yayi murmushi, haka
kikace? To shiknen, fadi ina jinki. Ta gyara xama
albishirnka? Yamasa goro. Xaka bani Ah! Me xai
hana? Ke dai gaya min inji. Abba yace in fada
maka ka turo, ranar auren mu za a sanya. Ya
xuba mata ido, ya kasa ko motsi, kayi shiru? Ya
sa hannu 2 ya mutsutsuke idanuwansa yace, dan
Allah karki xalayeni! Ta ware ido, kana nufin
baka yarda ba? Gaskiyya ban yarda ba, yaushe
Abba xai yarda ya bani ke, bayan ya san bani da
kowa a garin nan? Sannan suna min kallon dan...
Tayi wuf ta rufe bakinsa, sau nawa xan gaya
maka ka daina dorawa kanka maraici? Ina sonka
Danliti..... su abba kuma sun amince ka turo asa
mana rana da gaske na ke gaya maka maganar
nan ba wasa ba da sauri ya figo ta jikinsa yayi
wani irin ihu wai shi murna ayuba ya kwaso a
guje ya fado dakin ya same si kankame da juna
dan haka. Bai tsaya tambayar komai ba ya juya
ya fita yana kada kai cikin ransa yana fadin
"Danliti akwai dan iska"ya jima bai kyale mama
taci gaba dayi masa bayani ba yanzu yaushe.
Zaka turo? Ya yunkura ya tashi zaune yace
bashine matsalar ba wadanda zan turar sune
matsalar ta dan bata fuska tace ai ba za ka
rasaba "Danliti ko yan dattijan daku ke gaisawa
sun isa su wakilce ka ko kuwa? Ya zura mata
ido duk sun juye, yace haka ne sai ki baru in gan
su mudaidaita tukunna sannan in gaya miki
ranar daza su zo ko" tace shi ke nan bari in
kwashe sauran kayana in koma gida ya kara
matsarta haba tun yanzu ?" Umma ta ce kar na
dade kuma tunda sun amince da kai ai zaka
rinka zuwa ne kan ka tsaye,"ya kankameta ya na
fadin haka ne amma ban so ki tafi yanzu sonki
kawai ke azabtar da ni ina kewarki da yawa jiya
da kyar nayi barci kinji yadda ki ke tashin
kamshi?gaya min dame dame ki ka shafa in karo
miki irinsu?"Bata iya bashi amsa ba don tun
tafiyar su yake koya mata irin wannan renon ya
gama da rayuwar ta gaba daya kai ALLAH ka
raba mu da sharrin masu sharri,magariba ta
wuce wadan da sukaje masallaci ma sun koma
gida yayin da mama ta fito daga shagon Danliti
jaye da katuwar jakar kayanta. -yar tafiya kadan
ya taka mata ya dawo abinsa bata sami dan
dakon da zai daukar mata kayanba ba don haka
da kanta tayi ta ja har gida abba da umma na
zaune a falo dauke da bakin ciki maras
misaltuwa mama ta turo kofa ta shigo sa
sallamar ta dauke da uwar jakar kaya babu
wanda ya amsa mata ta wuce ta gabansu ta
tsugunna tace sannu abba, wani irin kallo yayi
mata mai isar da sakon haushi da takaici kafin
yace daa ina kike?ta dan sunkuyar da kai tace
naje gaya wa Danliti sakon ka ne ai na gayawa
umma kafin na fita ko um..."Ya daka mata tsawa
rufe min baki don ALLaH shine zakije ki zauna
har bayan magariba kiji tsoran ALLAH mama ki
sani cewar mutuncinki ki ke zubarwa wannan
uwar jakar da kika shigo da ita tawace tukuna?
idanuwanta suka kawo kwalla ta fara rawar
murya na...nawa ne.. Kayan da...Danliti ya siya
min ne yace to ba a gidan nan ba idan yazo ki
maida masa kayansa ya baki can gidan sa,ai
kinji ni ko,?ta amsa da kai umma ta cire tagumi
ta kare mata kallo sannan tace Alhaji ya kamata
a tuhumi yarinyar nan idan idan tabada kanta
gareshi kasan istibira'i ya kamata, kafin a daura
auransu domin ni banyarda da mama ba a yadda
suke tare da yaron nan,ya numfasa ciki da bacin
rai yace ki na da gaskiya don ni ma wallhy ina
wasi wasi cikin raina ke mama ki gaya min
tsakaninki da ALLAH ki fi jin tsoran sa akan
komai na duniya ki gaya min gasjiyar abinda ke
tsakanin ki da Daliti kar kisa muyi kuskure da
gangan idan kin san da wani abu to ki gaya
mana mubi tsarin da ALLAH ya shimfida. -sosai
ta goce da kuka murya na rawa tace ALLAH abba
babu abinda ya shiga tsakanina da shi duk
sukayi shiru suna dubanta kamar sun gaskanta
ta kamar basu yarda ba amma dolensu yarda
tunda basu da wata hujjar kama ta don haka
abba ya daka mata tsawa ya isa don ALLAH tana
wani bare baki kamar mummuna tashi kiba mu
wuri kuma na gaya miki yana zuwa ki maida
masa jakar kayansa,ta goge hawaye ta dan
sunkuyar da kai tace yace ya gode insha ALLAH
zai turo din suka yi banza da ita shiyasa da dago
ido ta dube su uwar hararar da ta yi arba da ita
tilas tasa tayi saurin maida kanta kasa jim sun
kikara cewa komai yasa ta mike simi simi ta
janye jakar ta, ta wuce daki bakin nan tamkar na
agwagwa kai tsaye bayi tashige tayi wanka ta
dauro alwala ta fito ana ta kiran issha'i,don
haka tana yin magariba ta dora issha'i bayan ta
kammala ta fito neman abinci nan falo sukayi
kicibis da yaya ali wai me ki ke nufi baza kizo
kiga amarya ba?ta kama kugu hannu biyu tace
wannan amarya an damu nazo na ganta hala
tafini kyau ne ya kama dariya kafin yace soosai
kuwa tafi ki kyau muje ki ganta tace haka yake
amma duk kyanta dai ni aka fara so kifin ita
saboda haka a daga min kafa inci abinci
tukuna"kalamanta sun ruruta wutar zuciyarsa ba
kadan ba koda ganin yadda jikinsa ya saki
kasan ya fada wani yanayi ya zura mata ido
hannayensa rungume a kirjinsa murya sanyaye
ace zancan ki dutse yar uwata,.

BAKIN CIKI 2***13 hasalima rashinki yasa na
aure ta koda yaushe ki kace da ni kule da sauri
xan ce cas mama don son ki ya zauna a raina,
tayi yar dariya tace yaya ali ke nan kar kasa
amaryar ka ta tsane. Ni daga wasa sai ka hau
jera zance!ba haks nake nufi ba yaya ali muje
kawai naga amarya in na dawo na ci abincin
bata jira yace wani abuba ta yi gaba abinta tilas
ya biyo bayanta yana kada kai!Amare kam
masha ALLAH suna dauke da tasu baiwar da
ALLAH yayi masu musamman aminar yaya ali
har mama na masa tsiya wai ya kamata ya
maida sunan sa aminu dan su kara dacewa da
juna kallon ta kawai yake yi cikin ransa shi
yasan babu wacce tafi dacewa dashi face ita
kanta maman,bata wani dade ba ta dawo sasan
su ta dauko leda cike da kayan garar amare
bayan ta gama cin abinci ta zauna gaban madubi
tayi wa fuskar ta kwaskwarima tayi zaman jiran
Danliti har barci ya fara dibarta bataji aiken yaro
ba,ta kwana zullumi da juyayin abinda ya hana
Danliti zuwa alhalin ya sami izinin yin hakan ko
har yanzu bai amince wa ransa bane?ya gudun
kar yazo ya fuskanci wulakanci!wannan
tambayar taso ta hana ta barci domin ta kai
sama da karfe dayan dare bata sami barci ba,Da
sassafe ta tashi da ciwon kai wanda ya haddasa
mata jiri akai akai duk da haka ko karyawa bata
yiba karfe bakwai da rabi tasa kai ta fice babu
wanda ya sani ta nufi wajen Danliti dauke da
ledar kayan garar amaren da aka bata jiya ita ta
tashe shi barci ya tashi a gigice yana tambaya
lafiya kika bugo sammako haka?tace nayi zaton
zaka zo jiya hira me ya hana ka zuwa. ya ja
dogon tsaki ya kauda kai jim sannan ya juyo ya
dubeta wai me ke damun kine?ba kinzo nan ba
sai bayan magariba kika tafiba?to kuma me
zanje in yi maki saboda ALLAH ta zura masa ido
ya kare mata kwakwazo nan take idanuwanta
suka tara kwalla murya na rawa ta ba haba
Danliti laifi ne don ban gan kaba na biyo in duba
ko lafiya?ya bita da kallo tana ta gugar kwalla
ya kece da dariya kamar mahaukaci hakan yasa
ta daina hawaye ta zuba masa ido yayi dariya
mai isar sa sannan ya natsu shima ya bita da
kallo to meye abin kuka ni ina can ina ta billayin
neman mana waliyai ai banga ta zaman fira ba
sakeena"nan da nan ta hadiye tashin hankalinta
ta fara murmushi duk kin wani daga hankalinki
don baki ganni ba jiya kawai " kawai ne? In gaya
maka dai dai da sakwan daya bana son zama
babu kai,yayi wata budurwar dariya yace ko to
na kara baki tukuicin kaina ta kwanto masa tana
dariya kasan ALLAH da ciwon kai na tashi ga
wani jiri na diba na amma na kasa daurewa na
fito ko karyawa banyi ba, yace ai ya bebi na
sannu ko ya kamata mu karya ki sha magani
bari inzo. Ya fice ya bar ta kwance bisa katifar
wucewar minti ashirin ya dawo da soyayyun kwai
da naman kaza da doya itama hade da kwai ta
hada masu shayi suka batse cikinsu harda ayuba
anan ta yada kafada daga fira barci ya kwasheta
Danliti ya dawo shago ya zauna tare da ayuba ya
zura masa ido yace don ALLAH ka tasheta ta
koma gidan su yayi banza dashi ya fito yana
zuba fito kamar katon arne. -Ayuba ya kada kai
yace karshen alewa kasa Danliti idan an ciza a
rinka hurawa ya ballo masa harara ya ce ba
ruwanka malam ka kyale ni in ci lokacina ya
tabe baki yace na barka zaifi kyau suka yi shiru
kowa na harkan gabansa, a gida kuwa tunda
suka shafa babu mama a dakin ta suke ta
kwasar BAKIN CIKI don sun tabbata tana can
shagon Danliti karfe tara uban dawaki ya gama
shirin sa zai fita ko karyawa bai yi ba saboda
tsabar takaici yasa umma ta fito masa da jakar
kayan da mama ta shigo dasu ya sunkuta yayi
waje da ita kalla ya tarbe shi da sauri ya amsa
ya bude but ya saka Abba yace minna zasu tafi
amma zasu tsaya shagon Danliti, kalla yaja
mota suka wuce yayi fakin kofar shagon abba ya
umarci daya fito masa da jakar nan kai tsaye ya
wuce shagon lokacin da su Danliti ke ta
harkokinsu yayi tsaye babu sallama har
hankulansu suka juyo gareshi Danliti ya matso
yana fadin sannu alhaji ina kwana yace nasan
mama na nan tare da kai ina take baki sake yace
tazo amma ta tafi yayi jim yana kallonsa kafin
yace ba shi ya dame ni ba wannan ya rage kuda
ubangiji ina fatan. Ta gaya maka yace ta gaya
min kokarin da nakeyi ke nan na samu na turo
yace kar ka bata lokaci domin na kosa na kauda
kazantar da nake gani ya dan sunkuyar da kai
yana murmushin izgilanci naji abba in ALLAH ya
yarda zuwa anjima ko gobe zan turo yace shike
nan ina sauraronka amma ga kayan ka nan ka
aje idan ta tare gidanka sai ka bata ba na
bukatar komai daga gareka sai sadakin da
ALLAH ya wajabta ga jakar nan bai saurari wani
abu ba yasa kai ya bar shagon ya fada motarsa
kalla ya ja suka dauki hanya Ayuba ya matso
gare shi yace, Allah na tabaka dama, don ka
gyara kuskuran ka Danliti, kar ka bari ta subuce
maka, ka dawo kana cizo yatsa. Ya watsa masa
harara yace bana bukatar wa'azinka alaramma
karfa ka manta da ni da kai duk daya ne. Na ma
dai san abinyi, ayuba ya xuba masa ido ya rasa
ta cewa babu abinda ya sami Danliti, yasa
hannu ya dauki jaka ya shige da ita. Hannu 2 ya
rike kugu, yana kallon mama xucyarsa na masa
sake-sake. Kusan 5mins yana tsaye, sannan ta
tsugunna ya bubbugata. Ta farka tana yamutsa
fuska, menene? Tashi kiji? Ta yunkura ta tashi
xaune, yasa hannu ya kara janyo jakarta, don ta
ganta sosai. Cike da mamaki tace waya kawo ta?
Yace, abbanki mana! Wannan kadai ya tabbatar
min baya sona, baya kaunta. Bai dameni ba,
amma me yasa zai uzzura min dole sai na turo
magabata na yanxu-yanxu? Hankalinta ya tashi,
ta matso a hankali ta dafa kafadarsa. Don
girman Allah kar hankalinka yatashi Danliti....
Cikin sababi. Yace ki daina gaya min wannan
maganar! Kora da hali abba ke min, saboda
haka ki hkr, kije su baki wanda suke so! Tashi
ki bar dakin nan, kar kuma ki sake xuwa, ni
babu ruwana! Ta narke da kuka, murya na rawa
tace, karka yi min haka Danliti, ina mai tabbatar
maka xan kashe kaina idan ka juya min baya.
(Kuji banza mtsw :(). Ya cire hannunta daga
jikinsa yace, ni ban aikeki ba ya kamata ki gane
ki gane ba dole bane na aureki. Don me xa a
daga min hankali akan magabata? Banda su,
uban wa xanje na tura idan ban nema ba? Kinga
ki tshi kije ki gaya musu na fasa. Ta marairaice
kamar ranta xai fita ni ina sonka Danliti ba xan
iya rabuwa da kai ba, ai dai ni xa'a daurawa
aurenko? Xan gaya musu su kyaleka, sai ka
shirya. Shikenan? Ya kara murtue fuska, yana
kallonta bai tanka ba. Takara matsarsa sosai
taci gaba da fadin, muddin suka ki yarda da
uxurinka wlh na yi rantsuwa xasu sha mamaki
dan wlh nan xan dawo na tare..... Ok, ki sa a
daureni kenan? Tace wa xai daureka? Don Allah
ki kyaleni ni bana son surutu, tashi ki tafi kawai,
sai na nemeki! Dan..... Ya daga mata hannu,
idan baki so raina ya baci to ki tashi kawai ki
bar dakin nan! Ta cigaba da share hawaye, ta
xura takalmi ta dauki mayafi ta mike xata wuce,
amma ta kasa, tayi tsaye tana kallonsa, don
Allah kayi hkr Danliti. Ya dago ido ya dubeta,
hawaye keta ambaliya, yayi dan jim, kafin yace
nayi hkr, amma kije tukunna xan nemeki. Xaka
xo gidanmu? Eh xan xo ki share hawayen, ba
wani abu. Ta share da sauri ta duro bayansa,
Nagode Danliti na! To kayi dan murmushi mana
ko naji dadi mana. (mayya :() Ya banbare
hannayen ta ya mike tsaye, karki damu da
murmushina, muje in rakaki, kafin tace wani
abu, ya fice, dole ta biyo bayansa, bakin shagon
kawai ya tsaya, yace sai nazo ko? Tace, daga
nan xaka tsaya? Xan wuce neman wadanda xan
turo din ne. Nan da nan sanyi ya ratsa mata
xuciya, baki har kunne. Tace, Allah sarki nawan,
to sai mun hadu anjima. Ya daga gira yana
fadin, sai mun hadun, yana sakin tsaki. Tana
shigowa dakinta, ta shige, motsinta kawai Umma
ta jiyo ta biyo ta dakin, tana kokarin cire kaya,
don shiga wanka. Umma ta kare mata kallo, ta
kada kai, tace don girman Allah mama ki rinka
xama a gida. Tunda Danliti na sonki kuma
abbanki ya bashi dama ai shi xai biyoki. Kullum
inaga ya miki babu mutunci ga 'ya mace ta rinka
bin saurayi har makwancinsa. Ko bai aikata miki
komai ba jama'a ba za su dube ki da mutunci
ba. Me yasa Danlit ya sauya miki tarbiya.? Tayi
shiru tana ciccika tana batsewa, Umma tacigaba
ni rokonki nakeyi, ki taimakemu ki taimaki
kanki, don mu tsira da 'yar martabar da tareg
mana a idon jama'a. Kinji? Ta amsa da ka, kafin
tace, Umma idan abba ya dawo ki fada masa ya
daina matsawa Danliti akan turo
magabatansa...... Ta katseta kamar ya? To
umma tunda an gayama sa kuma ya amsa xai
turo din, ba sai asa masa ido ba? Ta mako mata
harara, bangane asa masa ido ba? Shi daman
can bai shirya auran ba, ya hanaki sauraron
wandan ya shirya? To baku isa ba, mu ba wasa
mukeyi ba, tunda ya hure miki kunne dole ya
gaugauta turowa, ya raba da mu da bakin ciki da
muke gani, kinji nagaya miki. Tayi ta tashi tana
fadin, to shikenan ai matsa masa ba shine xaisa
ya turo din ba. Me kikace? Ta shige bayi da sauri
ta rufe kofa. Mama ni kike wa rashin kunya?
Lallai kin rika, kina gab da tsinka min mari akan
Danliti. Sallamar da jiyo, shi yasa tayi shiru. Ta
mike ta fito tana amsawa. Inna saude ce da
Baraka, saude sannunku da xuwa. Duk suka
amsa, yayin da Baraka ta tsugunna ta cigaba da
gaisawa. Bayan sun nutsa a falon, inna saude
tace, tun jiya naso fitowa, wani axababben ciwon
kai ya addabeni. Tace ayya ina fatan yayi sauki.
A'a da sauki, ina maman? Tana ciki ta shiga
wanka.... Wai dama saboda ita kika zo? Ai da
kin yi kwanciyar ki kin huta, domin al'amarin
Mama ya zama jiki. Tace, ya xama dole in taso
yaya. BAKIN CIKI kuwa baya taba zama jiki sai
dai imani. Allah dai ya bamu ikon cinye
jarabawar, ta nisa tace amin. Tace, yanxun me
kuke ciki? Ta fada mata yadda al-amarin yake,
ta cire tagumi. Tace haka shi yafi dacewa, in ma
banda sakarci ba ita xata taimaka mana ya turo
da wurin a huta ba. Tace ina fa, ai ina mai
tabbatar miki tafi son shi akan mu. Allah dai shi
kyauta. Ta amsa da amin. Suka ci gaba da hira
har suka ji motsin fitowar Baraka ta tashi ta
shige dakin. Ba suyi wata hirar kirki ba, domin
ra'ayinsu yasha bambam yanxun. Duk mai zagin
Danliti Mama bata ganinsa da kima haka ta fada
ma baraka, shiyasa ta shiga taitayinta, tafito
daga dakin tace xata ganin amare. Mama dataga
shirinta can ta sameta dakin amaryar Ya Ali, nan
suka shantake, sama da 2hrs sai da Inna saude
ta shiryo tafiya tasameta can, ita ma bata yi ma
Mama maganar komai ba akan abinda ta aikata.
Domin a tunaninta babu wata bakuwar kalmar da
xa agaya mata wacce bata sani ba. A wannan
daren mama tasa ido taga xuwan Danliti shiru
kakeji yasa ta jin haushin rashin dawowar abba.
Al- amarin nata cizon ta taga ba xata daure ba,
karfe goma harta goa, ta fito ta bude kofar ta
fice abinta. Ko kafin Umma ta fito taga wanda
ya bude kofar mama har ta kai kofar gidan,
ganin bata a dakin ya tabbatarma da Umma ita
ta fita. Ta nemi kujera ta xauna hannunta a
kunci BAKIN CIKI ykamar ya kasheta. Take nan
taji xuciyarta na ciwo, wani abu dum! Cikin
kanta kamar xai makantar da ita, tasbihi ta
shiga jerawa ko ta samu saukin kan. Ita kuwa
mama Tunda ta kwashi sauri bata sausauta ba
sai da taje shagon mutumin nata ta ja birki.
Ayuba na xaune daga ciki, taga kanta ta shiga
tare da sallama. Ya amsa mata ta wuce tana
fadin sweetyna naciki ne? Da sauri ya amsa
mata ai bayana nan bai gaya miki bane? Ta
tsaya cak dauke mamaki, ina yaje? Ya amsa
gaskiya bai gaya min ba, cewa yayi xaiyi tafiya
kawai. Na xaci ya gaya miki daxun. Ta kada kai,
bai gaya min ba wlh, amma xai dawo gobe ko?
Yace watakila, ta danyi shiru sannan tace to
shikenan sai goben. Allah ya kaimu. Taga kanta
ta fice, ya bita da kallo. Duk tasuayinta ya lullbe
shi, aransa yace Allah ya kubutar dake daga
sharrin Danliti. To nima nace AMEEN! Da babbar
murya. Tana tafe tana sakar xuci, wai duk fushin
ne yasa Danliti yatfi ba sallama? Ina xansa
kaina idan kalaman Abba suka korar min
Danliti? Bata samo amsa ba taji ann fige
mayafinta, 'yammata ji mana! Firgigi ta waigo
hankalinta ta dubi gungun samarin da suka kai
kusan shida, kowanne su dauke yake da tabar
wiwi. Ta dora hannu bisa kai wayyo nashiga uku,
duk suka fashe da dariya, ina kika nufa mu
rakaki? Ta durkusa kuyi hkr dan Allah, dariya
kwai suke kyakyatawa, 2 daga cikinsu suka
kawo mata cafka. Ta xabura ta mike, Allah ya
taimaketa ta kutsa ta cikinsu ta xura aguje,
dawa Allah ya hada su ba da ita ba, ta watsar da
takalma, ko daman gyalen yana hannunsu, taci
gudun fitar rai, ta rufta cikin gida, yayin da alh.
Adamu, ke kokarin rufe gidan, bakara min figita
yayi ba, amma yayi axama ya maida kofar ya
jefa sakata. Mama kuwa tuni tana sassansu, ta
fadi warwas! Tana maida numfashi tamkar xata
mutu, Alh. Adamu ya biyota, ya isketa daidai
kasa, ya xura mata ido kafin yace, wai daman
mama ce kartin Maxan nan suka biyota? Me kike
a waje har 11pm? Umma tayo waje tana sallami,
ganin mama a kasa yasa ta dafe kirji lfy? Ya
dubeta ido waje, yace, yanxun saboda Allah me
yarinyar nan take a waje cikn duhu? Kinga kartin
da suka biyo sunyi su 10, wannan ai diban
albarka ne da iskanci. Jiri ya soma dibar Umma
tana fadin me? Innalillahi Wainna ilaihir raju'un
kasan Allah, Alh. Adamu har na rufe kofa naji
motsin fitarta, xaune nake kawai narasa inda
xansa kaina dan BAKIN CIKI! Ban san yadda
mama ta maida rayuwarta ba......... Tana rufe
baki, tayi kasa da dafe kirji, saboda ciwon da
yake tsananin yi mata. A hankali hawayenta ke
fita tana fadin, BAKIN CIKIN ki zai kashe ni
Mama.... Alh. Adamu ya daga murya yana
masifa, kin shiga 3 mama! Kin maida kanki 'yar
iska da karfi da yaji, to ki bi a hankali, muddin
kika bari BAKIN CIKI ya kashe mahaifanki, kin
buga babbar asara, tashi ki ba mutane wuri,
kafin in taka ruwan cikinki. Ta yunkura ta tashi
da kyar, amma ta kasa mikewa tsaye, a
duddauke ta shige falo a tym din har mutanen
gidan sun fara taruwa, don ji me ya faru, Alh
Adamu ke daga murya cikin dare? Nan take ya
maida yadda akayi har ya dora karya, wai kartin
har sun turmusheta, tsawat da yayi masu, yasa
suka gudu. Kowa tafa hannu yakeyi yana salati,
kusan 12am suna xuba magana. Sannan kowa ya
koma sasansu, aka bar Umma kwance da ciwon
abubuwa barkatai. Ya ali ne kadai bai tanka ba,
don BAKIN CIKIN sa na gaske ne, tamkar yadda
UMMa takeji cikin xuciyarta. Dakin amaryarsa ya
koma yana kuka da hawayensa. Amina tayi
rarrashinsa tana nuna masa addu'a Mama tafi
bukata ba kuka ba. Mts!.... Amina ba zata gane
ba, BAKIN CIKIN dake cin angonta ba xai iya
jurewa ba, tilas sai ya matse shi. Hasalima ba
zai iya zama yana kallon irin wadannan
abubuwan ba, gara ya koma bakin aiki ko ya
kauracewa idanuwansa ganin abinda ya fi komai
daga masa ciwon xuciya. Saboda haka yacewa
amina ta shirya kayansu gobe zasu koma birnin
gwari da yardar Allah. Al'amarin ya daure mata
kai, kuma tayi tambayoyin da bata sami
amsarsu ba. Washe gari da suke shirin tafiya,
taji fashin baki na bakin Haj. Hajjo. Eh lallai biri
yayi kama da mutum. Nan take kumallon mata
ya taso mata, ya dasa mata kyamar Mama cikin
ranta har tafi Ya ali kosawa su bar garin. 12pm
kuwa ya samo shatan mota suka damki hanya.
Mama bata ma san anayi ba, tana can tana
murkususun ciwon ciki ita kadai a daki. Don ko
daya shigo yin sallama da umma bai shiga
wajenta ba. Sai wajen azahar barci mai nauyi
gaske ya dauke ta. Haka ita ma Umma ke ta
gyangyadin takaici bisa kujera. Rabonta da
abincin kirki tun jiya da daddare motsi taji a falo
ana shigowa da kaya, ta taso da sauri ta leko
falon. Kalla ta gani da tsirin kwalaye ya aje gefe
yana gaisheta. Ta amsa da fara'a ta karfin hali.
Bai karasa ficewa ba, abba ya kawo ka falon
tilas ya rabe gefe ya bashi wuri ya shigo, sannan
ya fice. Alhajin yana fadin, agaida Iyali, yace
xasu ji. Kallo daya yayi wa Umma gabansa ya
fadi, ya amsa sannu da xuwan da tayi masa. Ya
xauna falo. Yayi da ta shiga kitchen dauko masa
ruwa ta kawo masa ta xauna gefe tana kara
masa sannu da xuwa. Bayan yasha ruwa ya
numfasa. Tace an dawo lfy? Ya amsa lfya lau,
duk suna gaisheki, ni ne har abuja, daga can na
xarce kd yau da safe. Tace, wai kunsha hanya,
ina fatan duk lfya ka baro su? Yace kalau,
amma sai naga kamar kin rame, ina fatan ba
ciwo ne ya tashi ba? Ta kada kai. Kai dai bari
Alhaji, ciwo na ba zai taba warkewa ba, idan ban
ga yarinyar nan dakin miji ba. Kaci abinci
tukunna, kaji abinda ya faru jiya. Yayi dan shiru
har ta mike xata dauko abinci kafi, yace ki gaya
min kawai Halima, nasan babu bacin ran da
xanji wanda ya wuce na baya. Ta dawo ta xauna
ta fede masa abinda ya faru. Ya kada kai. Yace
ya rage nata, ba burinta ta fita duk tym da ta ga
dama ba? Jikinta xai gaya mata, xata gane
akwai wadanda suka fita iskannci. Yanxun tana
ina? Tana daki, ni yau ko kalarta ban gani ba.
Bata xo ta gaisheki ba ke nan? Tace ni a suwa?
Bana ma bukatar gaisuwarta, amma tun jiyan na
gaya mata idan na mutu, ta sani BAKIN CIKIN
tane ya kasheni. Yace, ba xaki mutu ba Halima
da Yarda Allah mama ba zata salwantar min da
rayuwarki ba. Karki manta, su hudu kika haifa,
kuma Allah ya albarkace su dubi tsibin kwalayen
nan, duk sakonki ne, kowa na da sa nau'in
tsarabar, zabi kalar abubuwan da kika fiso.
Bayan haka, jibi asabar duk zasu hadu anan,
don su share mana hawayen kukan da Mama ta
samu. Don kuwa zau tsaya tsayin daka dole
Danliti ya turo wakilnsa a daura masu aure a
cikin satin nan. Saboda haka ki kwantar da
hankalinki, ki na dasauran 'yal3an da suke
bukatar ki kusa da su a koda yaushe. Kinji ni da
kyau? Ta goge 'yar kwallan da suka xubo mata,
tace naji alhji, Allah yayi musu albarka baki
dayansu. Yayi murmushi yana fadin, amin kina
iya dauko abincin yanxun. Ta tashi da saurinta,
ta wuce, ya raka da ido tausayinta ya kwarara
cikn ransa. Ya numfasa yace, mun gode maka
Allah da wannan jarabci. Ta fito masa da abin,
ya gaugauta ci, domin gab ake da kiran la'asar.
Ya kammalawa kuwa tym yayi, ya mike yana
fadin, ki shiga ki tasheta tayi sallah. Ta amsa da
to, ya wuce dakinsa. Umma ta kwashe kayan ta
maida kicin, sannan ta nufi dakin Mama, don
tashinta. Tana kife ruf da ciki, Umma ta dada
mata duka ta tashi a firgice. Umma ta xura mata
ido, tace, in kin ga dama ki tashi kiyi sallah!
Tayi waje ta bata wuri. Da kyar ta mike zaune,
kanta ya sara mata, ta dafe shi hannu biyu, gaba
daya miyan bakinta ya kafe. Makoshin ta ya
bushe. Tana daga xaune, amma jiri ne ke dibar
ta.... Idanuwanta na ganin duhu, don haka ta
runtse su tamau! Tana maida numfashi, ta wuce
minti sama da goma ahaka, sannan ta iya tashi
a daddafe ta shiga bayin. Tunaninta kawai tayi
wanka ko tafi jin dadin jikinta. Nan da nan ta
kwashi ruwa a bokiti ta fara wanka. Kamshin
sabulun( Joy) Ya gauraye bayin, ba xato ba
tsammani taji xuciyarta ta tsani kamshin, kan ka
ce kwabo ta goce da amai. Ta kwarara mai
isarta, wai don ma babu komi cikin nata. Tana
gamawa ta dauki bojitin ta juye ruwan ajikinta,
tun daga kai. Ta jefar da shi ta yayo xani ta
daura, ta banko kofa ta dawo daki, ta bar bayin
face face da amai. Ruf da ciki ta sake fadwa
gado fadi take, wash! Wayyo Allah xan mutu! Tun
daga tym din al'amura suka kwance mata, ta
rasa kanta ta rasa meke damunta tana rashin
son abinci da yawan tashin xuciya, ga wani cikin
safe da jiri wani tym din jikinta yayi xafi, don
kansa kuma ya sauka ba tare da tasha magani
ba. Duk ba wannan bace babbar Matsalarta ba,
Ina Danliti ya shiga kwana 2 babu labarinsa? Me
kuma yake nufi da tafiyarsa? Duk da cewar tasan
dole ya dawo, idanuwanta da xuciyarta sun gaza
jure rashin sa na 'yan kwanakin 2. Shi yasa koda
yaushe tana kunshe a dakin matsalolinta masu
yawa na neman xautar da ita. Umma da kanta
bata gane kanta ba, musamman rashin xuwanta
neman abinda xat ci. Amma yawan xaman daki
umma ta jingina da rashin ganin Danliti da ta
rataywa xuciyarta, balle ayi maganar jingina shi
da wanccan Matsalar. Ta kan kada kai, tace,
kaico! Abincin wani, gubar wani! Allah ka raba
mu da muguwar kaddara... A yau asabar ake sa
ran xuwan yayyin Mamma, ga shi babu magana
mai kwari ko kuma muce uban gayyar baya gari,
shi da kansa abba xaune yake shiru dakin ta
same shi, ta xauna gefensa tace, kana xaune
baka shiga wanka ba? Yayi gajeran tsaki, yace
maganar nan ke damuna, da yarinyar nan xata
gane da ta amince cewar Dalinti ba xai turo kowa
ba. Banda aikin rashin gaskiyya, menene na
kama hanya kabar gari, kai da aka ba damar ka
aiko a baka mallakar abinda kake so. Wane bata
tym xakayi saboda Allah? Ta numfasa, tace
yaushe xata fusknaci hakan yadda ta makance
gaba daya, bata ganin kowa sai shi? Ai na gaya
maka ko abinci bata ci, duk ta fige saboda
bala'i, ni yaran nan ma dasu wahala suke nake
tausayawa ba su gama warware gajiyar biki ba,
ga aikinsa mai dan banxan wahala, da da halin
da xa'a ce da su dakata, wlh da ance suyi
xamansu. Ya gyara xama kyale su suzo ko hira
mukayi, ai maji dadi, ko ba haka ba? Haka ne,
Allah ya kawo su lfya. Amin ke ki kira min
Mama ta zo yaushe, dan liti xai dawo? Ta mike
ta nufi daki Mama ta tura kofa kakarin amai ya
fara dibar hankalinta, cikin fargaba ta nufi kofar
bayin ta murda ta bude, Mama! Tana durkushe
kame da ciki, kamar xata mutu. Kan Umma ya
kara daurewa, domin bata taba ganin Mama na
kwarara amai haka ba. Ko rashin lfya takeyi,
bata amai, sai dai xafin xaxxabi. Don haka ta
nufe da sauri ta dafe ta, me xan gani haka
Mama, baki da lfya ne ko yaya ne? Bata iya
amsa mata ba, tana tsaye kame da haba, tagama
kakarinta, ta kuskure baki hade da fuska, tayo
waje abinta, ba tare da kula Umma ba. Bisa gado
ta fada ta datse ciki tana numfarfashi. Umma ta
biyo a fusace tasa hannu ta birkito ta, ba kyajin
ina magana ne? Nace lfya kike sheka amai? Ido
jajur! Cike da kwalla tace, cikina ke min ciwo,
tun yaushe? Yau 3days. Ta jawo ta waje cikin
haske sosai, ta kama hannayenta ta dudduba,
sannan ta gwale idanuwanta, ta duba cikinsu, a
tsorace ta tambayeta ke, kina yi al'ada kuwa?
Tayi shiru tana xaxxare ido, baki na rawa tace,
nima ban sani ba Umma. Ba ki sani ba? Ke xaki
gaya min ko sai na farfasa bakinki? Ta goce da
kuka, don ita ma ta kideme, ta mance rabonta
da a'alada. Umma ta xura mata ido, jinin ta na
kara hauhawa, da sauri ta wuce ta bar mama
tsaye. Dakin abba ta koma ta xauna, ta rike kai
tana maida salati. Me akayi? Tace alh. Magana
takare ka dauki mama ka kaita asibiti ayi mata
gwajegwaje! Gabansa ya fadi gwajegwaje? Name
kuma? Na komai Alh. Ina shiga na sameta tana
sheka amai a bayi, wai cikinta ke ciwo, amma
alamu a bayyane sun nuna Mama juna 2
gareta........ Tsaye ya mike tare da fadin me?
Hawaye suka kara tsunke mata, ya koma a
hankali ya xauna bakin sa na karanto salatin
Manxon rahma. Gaba dayansu tsit! Sukayi
tsawon lokaci sai Umma ke shatatar hawaye,
baiyi aune ba kawai ya ga ta dungura ta fadi a
sume. Ya xabura ya tarairayota, yana kiran
Halima! Halima!! Don girman Allah karki kara
min tsahin hankali akan wanda nake ciki, ya
jawo goran ruwa ya xuba a hannunsa, ya yarfa
mata, ya cigaba da shafa mata ruwan bisa
fuska, ahankali har ta dawo hayyacinta. Ta bude
ido, jim tana kallonsa, sannan ta sake fashewa
da kuka, nan take tausayinta, yasa kwallan
Ubandawaki suka fara sauka bisa kuncinsa.
BAKIN CIKI kamar ya aika shi barxahu. Kiyi hkr,
ki kwantar da hankalin ki Halima, wannan
jarabawa daga Allah Ubangiji take, babu wanda
ya isa ya kankare mana ita, bana son tsanin
damuwar nan da kikeyi, tana jefa ni mummunan
matsayi, ko dogara da Allah Halima shine xai
magance mana komai. Ta goge hawayenta tayi,
iyayinta don ta tashi xaune amma ta kasa. Yace
kar ki damu da sai kin tashi yanxu kiyi
kwanciyarki ki huta, bari in kwaso magungunan
ki in duba wanda ya dace kisha. Ya mike da
sauri wani duhu ya rufe masa idanuwansa, bai
ganin komai face wasu miliyoyin taurari kanana,
tilas ya dawo ya xauna ya fadin Hasbinallahu wa
nimal wakil. Yayi ta maxa ya sake mikewa.
Umma tace ka xauna Alhaji kar kaje ka fadi ka
nakasa. Bai tanka ba, ya fice. Jimawa kadan ya
dawo da kwanndon magungunan ta ya xauan
yana bincikawa, jikinsa na rawa saboda bacin
rai. Sallama sukayi daga falo kuma babu
tantama muryar Ya abdurahman ce, abba Ya
amsa, ya kara da fadin gamu nan, ku karaso
ciki. Ganinsu jugun2, Yaya take ya rasa
kuzarinsa. Yaya dai Abba? Jikin nata ne ya
tashi? Yace shine abdulrahman, nan da nan ya
xube gabanta, da dauko kanta ya dora bisa
cinyoyinsa, sannu Umma! Sannu! Ta matse
kwalla, ta dube shi, kaxo lfya? Ina safiyya? Ya
amsa lfya lau take, tace in gaisheki. Ina
amsawa, me yasa baka xo da ita ba? Ya goge
mata kwalla, tayi nauyi ne Umma bata jin dadi,
idan tayi doguwar tafiya, koda muka koma,
bayan daura aure sai da tayi xaxxabi. Ta dan
kada kai, tace Allah sarki, Allah ya raba su lfya.
Amin. Ya amsa sannan ya dubi Abba suka gaisa.
Kafin su kama wata maganar, muryar Manyan
yayin ta gauraye cikin falonm. Abba ya gaya
musu suna ciki, kowa ya shigo da kuzarinsa, ya
ga Umma a kwance sai yayi turus! Bayan sun
gaisa tasha magani. Abba ya kwashe abinda ke
faruwa kaf, ya gaya musu, kowa yayi shiru,
kawunansu sunkuye tsawon tym kafin Ya soja,
yace, yanxun Ina Maman take? Oho inji Abba,
gaba daya sukace oho? Ta bar gidan nne, Umma
tace tsakar gida na barya tsaye, ban sani ba ko
ta koma daki ko ta fice don ba sani xamuyi ba.
Duk tym din ta so fitarta, ficewa ta takeyi.

AKIN CIKI 2***14 Ya soja ya dubi Ya
abdulrahman, yace je ka kawo mana ita nan! Ya
miki cikin hanxari, ya nufi dakinta, tana kife bisa
gado aikin kuka kawai takeyi. Ya sa hannu ya
fisgota, ba karamin tsoro ya bata ba, ta kwala
ihu, wani BAKIN CIKI ya kara turnuke shi, bai
san tymda yasa hannu ya doke bakinta ba, yace
rufe mana baki shashasha. Da sauri ta kame
baki, wanda take kyautata xaton hakoranta xasu
iya xaxxagow idan bata dafe shi ba. Ahaka ya
ciga da jan ta har dakin abba. Gaban babban ya
direta, ta xube har tana karo da guiwarsa. Ya
xuro mata ido kamar zasu fado kasa. Yace
matsa kdaga kusa dani, xan iya tokarinki, ki
mutu idan baki matsa ba. Ta janye jikinta baya,
ahankali hawaye na ambaliya, sunfi minti 5 babu
wanda tanka saboda takaici, kafin Ya abdulkrm
yace, gaba daya kin rusa rayuwarki Mama kin
lalata cikar asalinki da martabar iyayenmu.
Yanxu wa ya isa ya kankare bakin fetin da kika
shafawa kanki? Wa ai daura miki aure da ciki?
Wa kuma xai jagoranci kisan kai? Wannan cikin
dole ki haife shi, domin yunkurin xubda shi, ya fi
yinsa barna da tarin xunubi. Kin ga tun daga nan
idan kinyi tunani cikin hankalinki, xaki gane
babu soyayysa tsankaninki da Danliti. Burinsa
dama ya ruguxa rayuwarki, burinsa kuma ya cika
tare da hadin kanki. Saboda haka dabara ta rage
wa mai shiga rijiya, sannan karki xargi Danliti,
idan ya tsallake auranki, gaba daya abinda yake
bukata ya samu, abinda yai saura shine ki haife
masa wannan ckin, in ya ga dama ya karbi dan,
idan bai yarda ba ya kyaleki da shi, ku wulaknta.
Dama wannan shine karshen son xuciya. Babu
uwar kudi balle riba ga mai cinikin son xuciya.
Kuma duk wanda ya hau motar kwadayi da son
xuciya, babu tantama tashar kunya da nadama
xata kaishi ta aje. A koda yaushe karshen
danasani, ina fatan wannan xai xama darasi
gareki, ki gane cewa abinda Babba ya hango,
yaro ko ya hau gwauron dutse ba xai hango ba.
Ya goge 'ya kwallan da suka xubo bisa kuncinsa
sannan ya sauke numfashi ya dubi sauran, yace
yanxun mene abinyi? Abba yace abinyi babu shi
abdulkrm, tunda maganar aure ta rushe a halin
yanxun. Ya Soja yace duk da haka, dole ya san
tana dauke da cikinsa, bayan ta haihu xa a daura
musu aure, su tare da yaronsu! Su karata can da
abin kunyarsu! Ya abdul rahman ya kara sanyaya
muryarsa mai taushi, yace wannan dole ne,
amma abu na farko shine, ina xata xauna? Ta
kula da kanta? Umma dai ba xata jure ganinta a
wannan yanayin ba, ya soja ya gyara zama yace,
gaskiya ne, kuma waje na ya kamata ta xauna,
sai dai ba xan iya daukarta ba saboda xan iya yi
mata dukan mutuwa yadda nake jin na tsani
ganinya. So a cikinku, wanda yake ganin xai iya
hkr da ita, yana iya tafiya da ita Allah ya
shiryeta, mu kuma kullum addu'a muke mata,
idan ta dauki wannan mtsayin darasi a gareta,
xamu fi kowa farin ciki. Ya Abdulrahman, yace ni
xan tafi da ita, no ka bari ni in wuce da ita
Minna. In ji Ya abdulkrm. Abba yace ba xata biki
ba nan da xata xauna... ban ce mata yin ku za
su yadda ta ba amman yau da gobe sai Allah.
gara ta zauna anan, domin anan ne suke aikata
abin kunyar u kun ga ganinta da juna biyu ba zai
girgiza kowa ba sanin cewar daman can
sakamkon da zai biyo baya kenan. in ba wani
gyaran Allah ba. saboda haka ku kwantar da
hankalinku kuci gaba da yi mata addua sannan
ku kwantar da hankalinku ku tallafa wa
mahaifiyar ku ta kowace fuska don ganin ciwon
BAKIN CIKIN bai tagayyara ta ba, dukkan su
suka jinjina kai alaman uban dawaki gaskia ne.
yaya soja yace da yardar Allah umma ba za ta
tagayyara ba, idan mama bata son ki mu bamu
da wacce ta fi ki. bamu da wani buri. da ya wuce
mu rayu tare da ke. kar bacin ran mama yasa
mu dakatar da dukkan farin cikin mu. mu ukkun
nan mun ishe ki kallo ki samu sanyi a ranki ko
umma? hawaye na suka malalo mata yaya abdul
yayi maza ya rungumota ya na share mata
hawayen ki daina kuka umma in kina kuka
mama ba zata taba ganin haske ba, duk adduar
da zamu mata tace ba komai wallahi bana
jayayya da ikon Allah amman ku sani BAKIN
CIKIN ba zai goge cikin raina ba, domin FARin
ciki da bakin ciki duk halitta ce cdaga Allah fata
na kawai Allah ya bamu ikon cinye jarabawarnan
Allah yayi maku albarka Kowa ya numfasa, yace
amin, abba ya dubi mama da hawayenta yaki
yankewa yace, ina fatan kin ji abubuwan da 'yan
uwanki suka fadi, idan kinyi anfani da su, ki ga
daidai, idan kuma kin ce ba haka ba, mu babu
abinda xamu iya yi, sai mu kyale ki, ki ci gaba
da rayuwar da kika xaba. Ko dama kin riga kin
ruguza ta, karashe ne kawai. Allah ya shiryeki,
ki na iya bamu wuri mu sha iska, ki jira dawowar
Danliti, amma ki sani auran ku ba shi yuwuwa,
sai bayan kin haihu. Tashi ki bamu wuri. Ta kara
makurewa, kukanta ya karu, duk suka xubo mata
ido. Ya soja yace wa yace kiyi kuka? Cewa akayi
mun gaji da ganinki, ki koma dakinki. Ta
yunkura kamar xata tashi, amma ta kasa, da
sauri ta rarrafa jikin Ya abdulrahman, ta
kudundune ta rushe da kuka. Nan da nan ta
karya masa xuciya, ko dama shi akwai sanyi da
saurin jin tausayin mutum. Idanuwansa suka cika
taf da kwalla, tun baya son kulata har ya kai
hannunsa, bisa knta muryarsa na rawa yake
fadin, imani kawai xai sa akalleki Mama, amma
ke ba abar tausayi bace, tunda baki tausaywa
kanki ba...... Ya soja ya katse shi, pls
abdulrahman, fita da ita, Umma tace sai ma ya
fita da ita? Gata kenan, ya kyaleta, ta tashi da
kanta ta wuce. Ya tarairayo ta suka mike tare,
ya janyo ta xuwa dakinta ya xaunar da ita bakin
gado. Ya tsugunna gabanta yace, dube ni Mama.
Da kyar ta dube shi, hawayen ta na xuba, yace
kukanki bai da wani anfani, muddin ba nayin
nadama bane. Nadamar ma ta gaskiyya, tsakani
da Allah. Saboda haka ina shwaratar ki da ki
kama kanki, wannan ya xama na farko kuma na
karshe. Ba soyyaya vace wannan, ki dauki jikinki
ki ba da ga namiji, daga ranar da ya sanki a
waje. Wlh kin gama yawo, duk wulaknci da ya ga
dama xaiyi miki, ko da kinyi sa'a ya aureki,
abanxa xai rika kallonki, sannan wulakanci ba
xai daina shi ba, a karshe ki ga auran ya
bantale, tun ba aje koina ba. Kuskure ne, kin
riga kin yi Mama, irin wanda bamu taba xato ba,
babu yadda xa muyi mu gyara shi, sai dai kiyi
tuba wajen Allah, sannan ki nemi afuwarsu Abba,
kin jini? Ta xura masa ido, hawaye na ta bulbula
ta kasa fadin komai, domin ita kanta bata san
ainihin abinda ke damunta ba, cikin ranta agame
da samun ciki ba tare da aure ba. Saboda haka,
sake fado masa tayi, ta kankame shi, kukan ta
kamar xai fasa xuciyarta. Ba karamin rikita shi
tayi ba, domin nan take ya goce da kukan shi
ma. Da kyar ya banbare ta ya mike da sauri ya
bar dakin, ya dawo falo ya cigaba da gugar
kwalla, xuciyarsa na masa ciwo. Kai! Sun
dandani BAKINCIKI, da akwai yadda xasuyi su
goge wa Mama wannan bakin fentin da sun goge
mata shi, ko da shi xasu rasa komai nasu. Sai
dai kash! Babu hali, shi ya sa ko abinci
tsakurarsa sukayi suka ci, ba don yayi musu dadi
a baki ba. Haka suka juya bayan sallar la'asar
makare da BAKIN CIKIN da baya misaltuwa.
Haka zalika sun bar Mama cikin wani yanayi na
kunci rayuwa, wanda ya wanxar mata da
cututtuka masu dama ajikinta. Kafin yamma ta
fadi, kamar ba ita ta dawo Legos dambasheshiya
ba. Sati 2 kenan yau babu labarin Danliti, yayin
da rashin lfyar mama ke cigaba da yaduwa
tamkar yadda labarin samun cikinta ya gama
baza gari, ta bakin Hajiya Gaje. Amma don
tsabar yaudara su suka matsawa Mazajensu su
akan su kai ta asibiti ko ta sami dan taimakon
da xai rage mata larurar jikinta. Da kyar abba ya
amince. Alh. Basir ya kaita babban asibiti da
garin Kagara. Suka ga likita, yayi gwaje gwajen
sa ya gano, lalurar shigar ciki ne ke wahalar da
ita. Saboda haka ya bata 'yan taimakon da xasu
rage abubuwan da take ji a jikinta, sauka dawo
gida. Sun wuce kofar shagon Danliti shi kuma
yana karasowa wajen. Yayi fakin ya fito tare da
yin daguwar mika mai isar da sakon gajiya.
Ayuba ya fito ya tarbe shi, sai dai fuskar sa
babu fara'a ko alama. Yaya dai mutumina? Naga
kamar kana ciwo? Ya numfasa, amma bai tanka
ba har suka shige shagon. Ya dube shi da kyau,
yace ina magana ka kyaleni, lfya nace? Ya kara
sauke numfashi. Yace ina fa lfya, magana ta
cika gari..... Ya katseshi Mama na da ciki ko?
Gabansa ya fadi ya saki baki yana masa kallon
Mamaki, Dan liti ya kece da dariya, kwalla na
gangara bisa kuncinsa kafin yace, shiege ni, dan
buzu mai shayi. Raina kama gaiyya, ka tabani ka
ga tsiya. Watau labari har ya bazu ko? Kaga
burina na farko ya cika, amma har yanxun akwai
saura, don na san dan xagin kalilan za'ayi mata.
Ido jajur! Ayuba yace, kaji tsoron Allah Danliti,
ka kyale yarinyar nan haka. Tunda ba xaka
aureta ba, ka barta taji da wannan bala'in! Ai ka
gama ruguzamata rayuwa, babu sauran
wulakanci da yafi wannan..... Ya ja Kujera ya
xauna, yace haka kake gani, nasan akwai saura,
sai dai ba xan shanye maka dadin labarin ba,
idon ka nake son ka gani kamar yadda ka ga
wannnan. Ya bishi da kallo, yana kada kai.
Murmushin keta Danliti yayi, ya sake fadin, babu
wani abu mutumina, kai kanka kasa ramuwar
gayya, tafi gayya xafi. Dadin abin a gabanka
mama ta xageni, ta xagi Mahaifina, ka manta
kawai! Yace wannan ba hujja bace Danliti, ina
gaya maka barnar da kakeyi tayi yawa. Allah ba
xai kyaleka ba. Ya ja dogon tsaki ya mike tsaye,
kai wannan ya dameka, ni yanxun gidan ma xani
kuma lfy lau xaka ga na dawo, see you! Ya juya
ya daga kanta ya fice abinsa, ayuba ya koma a
hankali, ya xauna ya dora tagumin mamaki da
takaici. Danliti ya sake gani ya dire masa bakar
leda tare da kwalin juice kato bisa kanta. Yace
ga sauran kazar da na ci a mota nan, idan ka
gama laulayin, ka ci. Ya juya ya wuce mota, yayi
tafiya sa ya bar shi da tagumi. Kansa tsaye yayi
fakin kofar gidan Uban dawaki, akwai yara gidan
suna wasa, don haka bai yi wahalat neman yaro
ba, take nan ya aika yana kiran Mama. Yarinyar
ta shiga, jim kadan ta fito ta gaya masa tana
xuwa. Yana nan jingine da mota yana kada
makullai. Abba ya fito. Nan da nan ya tsuguna
kai sunkuye, mummunin kare kenan. Yace, ah!
Sannu abba, ina yini? Abba ya bishi da kallo,
amma kash, ya kasa ganin bakinsa balle ya gaya
masa bakaken maganganu. Ya amsa gaisuwasa,
sannan yace mike ka biyoni. Ya wuce kofar falon
bakinsa, ya murda ta bude suka shiga, xauna, ya
nemi waje ya tankwashe kafafuwa. Abba ya
xauna ya dube shi da kyau yace, yanxun saboda
Allah Danliti abinda kayi, ka kyauta kenan? Me
ya sa duk abinda xakuyi baku sa tsoron Allah a
xukatanku? Ya xa kace kana son yarinya da
aure, sannan ka aikata mata abinda ba shine ba?
Danliti ya kara sunkuyar da kai, kamar xai tsaga
kafet din falon ya shige don gulma, abba ya ciga
da cewa, to ta faru takare, ahalin Yanuxn Mama
juna 2 gareta, kaga xancen auranku ya rushe
kenan dole tayi zaman istibra'i xuwa tym da xata
haihu. Wannan abu ya bani kunya kuma kun
xubar min da mutunci da kima a garin nan.
Hannaye 2 Danliti ysa ya rufe fuskarsa yayi
xugum, ko mtsi ba yayi. Abba ya numfasa ya
kada kai ya cigaba, ni bani da abinda da xan
iyayi, tunda kaddara ta riga fata, abinda kawai
nake soka sni, shari'a ce ta tsara haka, saboda
haka dole ku kauracewa juna, don gudun karku
kara maida hannun agogo baya. Ina fatan kaji?
Sai ka koma jira ranar da xata haifamaka danka,
kaga kun sami dan aike, ba sai kun nema ba.
Kana iya tfiya, mu jira abinda Allah xaiyi.
Shawara da xan baka kawai, ka nemi tuba wajen
Allah, domin ka saba masa, ka keta rigar
mutuncin yarainya. Shiru yayi ya kasa tashi,
abba yace tashi mana, ni nakare magana, ya
dago kai da kyar, amma bai kalli fuskar abba ba,
cikin sanyin murya yace, abba kayi hkr ka yafe
min? Wlh sharrin shaidan ne. Ya goge kwalla,
abba na kallonsa kafin yace, haka ne, amma
wani tym har da son xuciya. Si yasa nace ka
nemi tuba wajen Allah, don ta ni mai sauki ne.
Ya kara rankwafawa yace, je ka kawai. Ya tashi
simi simi ya fice babu ko waige. Abba ya raka
shi da ido, sannan ya numfasa ya kada kai, yace
Allah ya shirya mana. Shi kuwa Danliti yana fita
yayiwata 'yar girgiza ta jin dadi, ya wuce
motarsa cike da farin ciki ya koma shagonsa.
Ledar kazar da ya ajewa ayuba suna nan bisa
kantar bai taba ba. Wai don ya ba ayuba haushi
sai ya dage kantar kayan suka watse kasa.
Ayuba ya bishi da kallon kafin ya ce ni baka ban
haushi ba don ka xubar kudinka ne, ba nwa ba,
gaskiyya ce dai ba xan daina gaya maka ba,
watakila ma baiji shi ba, domin bai tsaya ya
saurare shi ba, cikin daki ya shigr. Yayi kwance
yana tunanin shirinsa na gaba akan mama. Abba
kuwa ys jima falon xaune yana tunani rayuwa
kawai. Sannan ya mike da kyar ya koma cikin
gida, ya maida wa Umma yadda sukayi da
Danliti ta kada kai tace , shikenan, Allah yasa ta
nutsu ta xauna gidan. Yace amin, amma ina mai
tabbatar miki muddin tace ba xata nutsu cikin
gida ba, xan bata mamaki, domin, dole ta xaba
ko mu ko shi. Umma tace gaskiyya ne, ace
wannan abu ya sameka, baka yi nadama, ai
kuwa sai a sallama mutum asa masa ido. Allah
yasa mu dace. Ya amsa da amin. Tunanin uwar
gayyar ba anan yake ba, domin kuwa jin ga
Danliti yana kiranta, ya tabbatar mata da cewar
ya dawo kuma taso ta ganshi, su Abba suka
taka mata birki. Duk da haka taji karfi a jikinta
kwarai da gaske, har wasu daga cikin
cuttuttukan da ke damunta suka yaye nan take.
Sai dai tana ganin babu adalci a hukuncin dasu
abba suka yanke. A zaton su zan iya zama
tsahon tym banga masoyina ba???????? Ta tabe
baki tana daga kwancw tace, ba xan iya ba
gaskiyya, sai dai suyi hkr wlh. Ai dai maga juna,
ya san halin da nake ciki, ya tausaya min. Ta
goge kwalla ta cigaba da sakar xuci. Ana ta
sallar magriba, tym ne da ita mama ta sami
damar satar jiki ta sulale ta isa shagon danliti.
Shi kuma kaida ke xaune cikin shagon. Ayuba ya
shiga sallah. Yana ganinta ya dafe kirji ya wani
lumshe ido. Yace wayyo Allah na gode maka! Ta
daga kanta ta shiga, ta nemi t barma ta zauna,
saboda bata jure tsayuwa. Tana xama ta hade
kai da guiwa ta fasa kuka ya kare mata kallo, a
dage yana dan murmushi, sannan ya taso ya
dawo gunta yace haba bebina! Meye abin kuka?
Ya xauna gefenta ya rungumota jikinsa, bana son
kukan hakan nan....... Ta cira kai da sauri ta
dube shi, ba xanyi kuka ba? Ciki fah gareni,
kowa ya tsaneni ana ta zagina. Shine xaka ce ba
xanyi kuka ba? Yayi dan murmushi yace, bebi
kenan, to don kowa ya tsaneki shine me?
Bayanni ina son ki kuma ina son ciki na! Kina so
yi kukan ne, wata kila kuma na dadi ne yayi
miki yawa. Ta mako masa harara tace, jin dadi?
A zageni, a tsaneni shine jin dadi? Son ka ne
kawai yake sawa bana damuwa, amma kai ina
ganin abin baya damunka, daya dame ka, da
baka wanke kafarka ka bar garin ba, tsawon sati
2, alhalin an ce ka turo a daura mana aure. Da
ka maida hankali ka turo din, ai da duk hakan
bata kasance ba, koda cikin xai bayyana
adakinka xai fito. Tunda ni ban ma taba nuna wa
akwai wani abu tskanin mu ba. Sannann.... Ya
da ka mata tsawa, ya ida don Allah! Haba!
Wannan maida xancen na menene? Ko kuwa turo
ki akayi ki zo ki batan rai? Ko dan kinga ina ta
rarrashinki? Babu fah dole, kin ganne? Abban ki
cewa yayi ba dole bane ya bani ke, ko bayan kin
haihu. So pls ki daina damu na da irin
wadannnan surutun banxan, ban son jinsu, idan
har kin son mu shirya! Kin gane? Ta xura masa
ido hawaye na xuba, ta ma rasa me zata ce?
Ayuba yayo sallama ya shigo ya riske su cikin
wannan halin. Shi ma yayi tsaye yana kallon su,
jim kadan Danliti ya buga tsaki ya tashi ya
shige daki ta goge hawayen itama ta tashi ta
bishi, ayuba yaa kada kai ya ja kujera ya xauna
yana fadin Allah ya kwaci yarinyar nan. Tana
shiga ido ya xubo mata. Yace au biyo ni kikayi?
To ranki xai baci kuwa, gara ki koma. Ta
marairaice tace, kayi hrk Danliti, ba don ranka
ya baci bane ya sa na gaya maka abinda ke
damuna. A xatona xaka tausaya min a halin da
nake ciki. Bani da wani gata wajen iyayena. Tun
ranar da na nuna kainake so Danliti, ka tausaya
min. Yayi lum da ido ya bude, ya cigaba da
kallonta tana tsiyayar hawaye kusan 3mins
sannnan ya yafito ta da hannu, yace xo nan! Da
sauri ta isa gunsa, ta fada jikinsa ta kara fashe
da kuka. A'a, kinga ni fa kukan ne bana so.
Yanxu menene damuwarki? Ta goge hawaye, tace
kullum in rinka samun kulawarka, hakan shi xai
tabbatar min da kana sona kana son abinda ke
cikina. Yayi dan murmushin nan nasa, ya kara
janyo ta jikinsa, yace, kin samu bebi, karewa ma
da kewarki na dawo. Kin ci abinci? Ta kada kai,
saboda me? Bana iyawa ne, jikina gaba daya ya
canza, sai amai kamar xai kasheni. Yace ayya
sorry ko? Amma duk da haka ba za a rasa
abinda kike sha-awa ba, gaya min in nemo shi,
na kosa in kore kishirwata. Ta mako masa
harara, ya kyalkyale da dariya, meye na harara
ta? Ko ke ma xaki min BAKIN CIKI ne, irin na
'yan sa ido? Masu shiga tsakanin masoya suna
son suga bayansu. Haushi su nake ji wlh. Tace ai
ko ni din ma haushin su nake ji, ah haba? Wlh
kaji na rantse. Ya cacume ta tana dariya tana
fadin, ban da lfya Danliti, bai saurare ta balle ya
tuna ya nemo mata abinda take son ci. Karfe 8
ya fito ya barta can kwance tana murkukusun
ciwon ciki, ya wuce waje wani mai suyan nama,
ya karbi danyan naman da yasa ya aje masa. Ya
dawo ya bade shi da magani, ya maida cikin leda
ya nade. Yana xaune bakin shgo bisa benci, yana
tunanin tafiya yayi wanka ko ya samu yayi
sallah. Mama ta fito tana yafa mayafinta, ya bita
da kallo yana murmushin keta, ya cikin? Tace
yayi sauki ni xan koma gida sai gobe. Haba haka
da wuri? Yanxun fa 8 ta wuce? Kar a neme ni ne.
Wa xai neme ki? Don Allah xaumna muyi hira, ba
wanda xai nemeki, bayan sun san kina nan. Bata
da xabi, don haka ta xauna kusa dashi, ya shiga
bata labaran banxa. Jimawa kadan wani kare ya
xo gilmawa nan take ya hau kiransa, tace me
xakayi da kare kake kiransa. Kasan karen
okundiri fada gareshi ko? Yace bai sami nama
bane don ubansa okundiiri, ya kece da dariya,
okundirin ne ubansa? Lallai ka samo shi. Yacee
to da waye ubansa? Kinga bude ledar nan nama
aciki dauko ki ba shi. Yana magana yana shafar
kan karen. Tace, taf ya cafke min hannu? Kai
dai ka bashi kai da ka siyo masa,don raka
asara. Yace karki bani kunya mana, me xai sa
ya cije ki, bayan yasan ke bebina ce, ko kare? Ai
ka santa ko? Sweetheart dina ce kar ka cije min
ita. Tuni kanta ya fasu, ya jawo leda ya bude ta
dauko katon yanka ta mika masa tana fadin,
abin har da yaji? Sangarta! Ya kwashe da dariya,
yace ina ruwanki? Ke dai mika masa gudan. Ta
dauko ta mika masa, ya cafke, Dan liti ya runtse
ido yace yes! Ya xarce da dairya. Ta xuba masa
ido tace, menene abin dariya har da wani cije
labe? Yace ji nayi kamar ya hade da hannunki ya
gartse. Takai masa bugu a kirji tace amma kai
mugu ne! Yace sosai ma ashe baki sani ba
yarinya, to tashi kije gida an gama hirar, kinga
karen yayi tafiyarsa. Ka gaida okundiri kaji? Ta
ci da kyakyata dariya. Yace, ah! Tashi karki sa
yarona ya fito yana fito yana kyakyatawa kamar
dolo. Ta shi kije gida sai safe. Don Allah kiyi
hkr, so nake nayi wanka inyi sallah. Ta fido lah
nima har ka tuna min banyi ko magriba ba. Ta
juya da sauri tana cewa, sai da safe! Yace Allah
ya kaimu. Ya bita da kallo, yace yarinya kin
gama yawo kin shiga 3 kin lalace, ya daga
murya ki fa sami abinci ki ci. Ta juyo ta amsa,
kar ka damu xanci. Suka ja hankalin mutane,
don haka yama didi ya biyo baya, masu tsinuwa
nayi, masu addu'ae shiriya nayi. A tsakar gida
ta iske su Abba na jiran dawowar ta, shi da su
Alh. Basiru. Tana shigowa tasha jinin jikinta, ta
shiga bin bango, tana so ta shige falo. Alh.
Basiru ya daka mata tsawa, ke dawo nan! Simi
simi ta matso gun su ta durkusa guiwa 2, batayi
aune ba, taji saukar wani wawan mari. Gaba
daya ya ratsa kanta, ya gigita ta, ta dunkule ta
fasa kuka. A cikin ba tace ga wanda ya xabga
mata wannan marin mai tsanannin xafi ba. Sai
dai taji muryar Abba na fadin wannan shine
gargadi na karshe da xanyi miki, shi ya sa na
tara kowa su xama shaida! Idan har ba xaki bi
umarni na, ki xauna a gida ba, to wlh sai dai ki
xaba, ko mu ko Danliti! BAKIN CIKIn nan ya ishe
mu mama. Gara in sallama ki, in tabbatar da
kinfi karfina xaman kanki kikeyi. Saboda haka
daga yau kika kara sa kafarki kika fita kikaje
gun yaron nan, to kar ki dawo, ki yi zaman ki
can wajensa ku sha shagalinku yadda kuke so.
Duniya ce Mama, mai dauke da axuxuwa babu
adadi! Ina fatan kinji kuma kowa ya shaida! Alh.
Basir ya karbe karuwa kike so ki xama ko? To
Allah ya baki sa'a, mu dai ba xa mu hana shi
ba, duk ranar da koreki. Alh. Adamu yace dama
saboda me xamu hana shi? Cikin shege ne fah
ajikinki, amma bai sa kinyi nadama ba, to me
xai sanya ki kuwa? Karkiji da wai, mun tsame
hannun a kanki, haka xuri'ar gidan nan kaf! Kar
ki ce kin san daya daga cikinsu, duk ranar da
wuya ta koro ki! Ta shi ki bace mana da gani
shashasha sakarya. Ta mike da gudu ta fada
dakinta, ta dasa kukanta, a fusace abba ya bar
wajen kowa ya kama gabanmsa, suka cigaba da
yada xancan a sasan su. Daren nan su ma Umma
basuyi barci ba, musamman Umma da tabbatar
wa kanta ciwon xuciya ya kamata. Da safe ta
atashi xuru-xuru baki daya idanuwanta sun
xurma, shi kansa Abba ya rame ta maxa kawai
yakeyi yana wa Umma fada kar ta salwantar da
rayuwarta akan Mama. Ita Mama ba wannan ta
aje ranta ba, kawau burinta kasance tare da
Danliti, don haka take ganin kowa ya tsangwame
ta saboda kiyayya. Kafin safiya ma ta mance
duk kalaman su Abba da kawunninta. Allah Allah
takyi ta sami saukin laulayin safe dake damunta
ta lababa taje ta gano Danlitin ta. Xuwa 12noon
ta iya shiga kicin, ta dan tsiyayi ruwan lipton, ta
dawo ta shanye. Xufa ta keto mata, danji dadi
ajikinta, kana ta shiga bayi tayi wanka da
sabulun wanki maras kamshi. Ta kimtsa, tsaf,
duk da tayi haske sosai, ta kuma rame kwarai,
kana iya gane kyanta na asali mai daukar
hankali. Ta koma ta kwanta yana kllon agogo
1:00 ta tashi tayo alwala tayi sallah, ta dauko
gyalemnta ta xura takalma ta leko falo bataji
motsin kowa ba, ta kwahi sauri ta fice abinta.
Yara suna ce mata sai kin dawo aunty Mama!
Jin haka yasa Umma yanke sallah, ta fito da
sauri ta tambayi yaran ina maman? Sukace
yanxun ta fita. Tabi xauran, yaran suka biyota ta
tura su tace, ku kira min ita. Yara suka fice da
gudu suna kwala mata kira, Aunty Mama, ki zo
Umma na kira! Haka suke ta gudu suna fadi har
suka isketa, ta dube su tace, sai na ci ubanku in
kuna kwala min kira haka! Ni sa'ar kuce don
Ubanku? Ku tafi ku ban wuri kafin in fallawa
yaro mari! Mts..... Taja tsaki, ta wuce abinta,
yara suka dawo a guje suka iske Umma a xaure
sukace, wai sai ta ci ubanmu idan muka sake
kiranta! Ta dafe kirji tace, ta kyauta, kuje wasan
ku. Ta dawo cikin gida a salube tare da mamakin
taurin kai irin na Mama, me take nufi kenan? Ta
xauna a falo tana juyayi. Da kyar ta sake mikewa
ta shiga dakin Abba, ta tashe shi barcin ramakon
da yakeyi. Ya farka yana kallonta...... Yace,
azahar tayi ko? Tace tayi alhaji. Ya yankura ya
tashi yace menene na ganki a salube? Tace
tasake fita, wa? Mama mana. Cike da mamaki
yace ta fita? Yanxun nan kuwa, kamar fako na
takeyi, har yaran nasa su kirata, ta dinga
kunduma musu xagi, taki dawowa. Ita Maman ta
zage su? Tayi murmushin takaici, tace kana
mamaki ne? Bai kamata kayi ba alhji. Ta kuwa
tafi kenan, kinsa Allah ba zata dawo ckin gidan
nan ba. Kiyi hkr, duk abinda ke ranki na so da
kaunar Mama, ki cire ki dangana da ita, nima na
hkr da ita. Umma ta fasa kuka, ta tashi da
asauri ta bar dakin. Hankalin Abba ya kara
tashi, ya taso ya biyota dakinta, tana xaune
bakin gado kukan kawai takeyi. Ya tsaya kanta,
yace saboda Allah ya kike so nayi Halima? Ta
cira kai murya na rawa. Tace har ga Allah ba
korar Mama ke sanya ni kuka ba, tausayin
rayuwarta ke bani, yadda ta ka sa gane cewar
mu ba tsangwamarta mukeyi ba, saboda tana son
Danliti. Yanxun shikenan ba xata gane cewar
alabarkar mu itace kwanciyar hankalinta ba, duk
tsananin son da Danliti ke mata, shikenan ta
xabi cigaba da xaman shashanci akan ta nutsu,
dn tym kankani a daura masu aure? Wannan
rayuawar tana cike da tausayi da ban Mamaki,
kamar Ya asirce Mama? Ta kada kai ta ciga, ba
haka Mamar mu take ba alhji, ta sauya saboda
soyayya, kenan ta fi son shi a kanmu? Ina xan
samo amsoshin nan Alhji? Ina xan..... Ya rufe
bakin da sauri, ya ace ya isa haka! Kar ki jefa
kanki damuwar da xata tada miki ciwo, ki kauda
kanki ki akan komai, sannan ki nisanta xuciyarki
ga irin wadannan tambayoyin da kike wa kanki.
Xaki xautu saboda yarinyar da bata damu da
lfyarki ba, xamani ne Allah ya kawo mu da yara
ke rufe idanuwan su akan abinda suke so. Suyi
ta fada da iyeyensu har xuciyoyin iyayen su fara
xargin asirce su akayi. Xan ji dadi da farin ciki
idan xa'a ce, duk wannan abubuwan da suke
faruwa, ki dauke shi amatsayin mafarki mai
wucewa, tamkar baki taba haihuwar wata mai
suna sakeena ba. Ta dube shi xai yuwu ko? Mai
hana? Idan har zaki dage da adduoi, ubangiji ba
xai barki haka ba, ta goge hawayenta ta sauke
gwauran numfashi tace, xan yi iya kokarina Alhji.
Ya jinjina kai. Yace haka nafiso sadiya, kin san
ina jin dadin xama dake, kuma tun ina saurayi
ban taba son wat 'ya mace ba sai ke. Ban fatan
abinda xai salwantar min da rayuwarki, ya
kasance wata kaddara tasa kin fara barina cikin
duniyar nan. Kullum nayi sallah, sai na roki Allah
ya fara daukar raina saboda ba xan iya ganin
gawarki ba halima. Idanuwanta suka kara tara
hawaye. Tace ka daina fadar maganar nan
Alhji..... Ya katse ta, ni ma ba ason raina na fadi
ba, domin sirri nane wanda nake xaton shi kdai
ne ban taba gaya miki ba, sai yau, dole ce ta
sanyani, don ina son ki sami nutsuwa sadiya. Ta
matse ido kwallatana suka kwararo ya mika
hannu ya goge mata yace, sha kurkuminki
Maman abdul 3, gwarazan samarin nan masu
takama da baiwar Allah. Ta numfasa tace, Allah
yayi masu albarka baki dayansu. Kina nufin har
da sakeena ko? Ta amsa da kai, kafin tace, ai
mu na mata fatan shiriya ko? Yace haka ne, toh
Allah ya shiryta. Amin ta amsa. Haka yayi ta
rarrashinta, ta samu nutsuwa, sannan sukayi
sallah suma mika kukan su ga Allah. Na san
kilan kuyi musu ko mamaki idan nagaya muku
Mama bata dawo gida ba, sai bayan sallar
magriba. Abu na farko da ta fara cin karo da shi
a kofar sasansu dake kulle, shine akwatin
kayanta. Taja cak! Ta tsya ta xura masa ido
tsawon tym, kana ta matsa ta tura kofar taji ga,!
A kulle. Ta tabe baki tare da jan tsaki, ta figi
akwatin ta juya tana fadin a ranta, sai aga na
kwana a titi. Kai tsaye Danliti ta dosa, yana
xaune kofar shagonsa, inda ta basa. Yana
hangota da akwati, ya mike ya shige daga ciki
yana gayawa Ayuba ga mutuniyar can tafe da
akwati, ko maganarta tace ta tabbata? Ayuba ya
murtuke fuska yace ni xaka tambaya? Au haushi
kaji? Amma dai kana ji na gaya mata kar ta
kuskura ta bari su koreta, don bani da wurin
ajeta, ko ban gaya mata ba? Yace oho! Wai kai
wani irin banxa ne? Yace Ni banxa bane, ai
rainin wayau yasa ka gaya mata hakan. Wa ke
jan ragamar rayuawarta, in ba kai ba? Ai sanin
bata da xabi shi yasa ka raina mata hankali. To
ya isa malam, sai gata tsaye gaban kanta, tana
kokarin dagawa, duk suka xubo mata ido, ta
karasa shigowa, ido waje ya dubi shirgegen
akwatin, ya ce ya dai? Bata saurare shi ba, kofar
dakin ta tasarmawa xata shige. Yayi azama ya
shawo gabanta, magana fa nake yi, kona kokarin
shigewa kamar gidanku? Ta xubo masa ido a
marairaice tace, me na gaya maka? Ni kuma me
na gaya miki? To yaya xanyi? Ina komawa na
iske akwatina akofar gida sun kulle gidansu. Ya
gayara tsayuwa, da yake kuma ke sakarya ce sai
kaka kamo hanya kika taho baki tsaya kika nemi
sulhu ba! Yanxun menene nufinki? Anan xaki
xauna? Cikin shago? Lallai kin cika dakikiya,
Jaka! Kuka sosai ya kwace mata, ta tsugunna ta
rungumi kafafwansa, murya na rawa tana fadin,
karkayi min Haka Danliti! Saboda kai suka
koreni, ina kake so naje, idan ba nan ba?
BAKIN CIKI 2***15 Ayuba ya daga kanta, ya fice
hankalinsa tashe, shi kuwa ko gezau beji ba
ajikinsa, a dage yake kallonta, tsawan tym
sannan ya fizge kafarsa ya kama hanya xai fita,
da sauri ta mike ta cukuikuyo rigarsa, fadi take,
kayi hrk don girman Allah. Wasu samari 2 suka
iso wajen siyen taba sigari, ai sai suka buge da
shari'a, kaya-kaya hayaniya har waje Danliti na
daga murya shi ba xai aje ta cikin shagonwa ba,
ta koma ta nemi sulhu da iayeynta. Kan ka ce
kwabo jama'a sun cika makil a gun. Kai Mama
ta sha zagi da la'anta, Allah shi kara kwando-
kwando. Kalilan ke cewa Allah ya shiryeta, Dan
liti ya gacciye banci kofar shagoin ya xauna yace
yaga uban da ya tsaya mata agarin nan, wnada
xai sashi ya ajeta. Baiwar Allah kuwa na tsugene
gaban akwatinta, tana ruasar kuka har karfe
10pm. 'yan ganin kwakwaf suka gaji suka koma
gidajen su dauke da labari mai ban al'ajabi.
Wasu suna ganin bai kamata Uban dawaki ya
koreta ba a matsayin sa na Uba, kuma babban
mutum mai sarauta, wasu kuwa suna ganin
hakan shine daidai, imna xai sa BAKIN CIKI?
Idan bai sallame ta ba, tunda ta tara masa, ya
cika masa xuciya, tana neman fashewa ta
hallakashi? Ai gara da ya sallamata duniya ta
koya mata hankali. Ga darasi na farko nan ta
fara gani, duk iskancin Danlitim yace baxai aje
taba. Alhalin saboda shi aka koreta. Wannnan ya
nuna a fili ita ta nace masa kamar sauran 'yan
mata marasa xuciya. Mutane na mamaki abinda
Danliti yake da shi wanda yake tsonewa 'yan
Mata ido. Su mutu cikin soyayyar sa. In bata ga
kyau me yake da shi? Shi babu hali babu
kwakkwaran asali. Amma duk wacce ta fada
tarkonsa sai gagari iyayenta. Ko don kudi da ya
ke kashe mus ne? Shiya sa suka dauki laifi
kacokan suka dorawa 'yan Matan masu biye
masa don kwadayi da kyalekyalen jikinsa. Wayyi,
kai bai san dawan garin ba, dai bai yi tunanin
kutsa kansa ciki ba. Tun ciki dare surutai kala-
kala suka fara baza gari. Shi kuwa gogan da ya
ga kowa ya watse sai ya matso ya xunguri Mama
da kafa, ta dago kai da sauri ta dube shi, matso
mana nan kiji, ta matsa gareshi, tana hawaye.
Ya dubeta da kyau yace, ke banxa ce wlh, shi ya
sa kika bani haushi. Nace ba xaki xauna anan
ba. In banda hauka irin naki, ya xa'ayi ki xauna
tare da mu cikin shago? To ina sane da abinda
nakeyi, kin gane? Saboda haka ki koma ki nemi
wani wurin ki xauna, ki bani nan da sati xan san
abinyi. Murya dushe tace, ni bansan inda xani
ba, a'a ko gidan 'yanwanku ba xaki je ba? Ko
baku da su ne? Sai dai inje gidan su Baraka,
yace ko gidan su Mubarak xaki, sai kinm dawo
matsalar kice. Amma ba xaki kwana shagon nan
ba. Yauwa, tashi ki sungumi akwatinki, ki wace
kar su kulle gidansu. Tace to nagode, sai da
safe, Allah ya kaimu 'ya bebine. Muyi fada mu
shirya ko? Kar ki damu xan ganki goben. Tayi
murmushi, dadi ya rufeta, ta mike tana kara
masa godiya, taja akwatinta ta nufi gidansu
Baraka. Ya mike janye da benci yana kyalkyala
dariya, ya shige shago. Kai mugu dan gidan buzu
mai shayi! Yayi wa kansa kirari ya shige daki.
Ayuba na kallonsa yana kada kai. Gidan su Bara
akulle yake, saboda sha dayan dare tayi ma. Ta
shiga bugawa har aka xo aka bude mahaifin
Baraka ke tsaye cikin xauran, ya dubeta da kyau
yace, Mama ce? Daga ina haka? Ta fara kuka
yace shigo shigo ciki! Ta wuce da uban akwati
ya maida kofa ya rufe. Tana gaba yana biye da
ita yana fadin, subhanalillahi! Dakin Inna saude
suka shiga tana tsaye tsakar daki, lfya? Ta xube
sharaf! Cikin kuka tace, abba ne ya koreni.....
Ina saude ta nemi waje ta xauna, yayin da
malam kasim ke fadin, me ya sa Uban dawaki
xaiyi hak? Inna saude tace BAKIN CIKIN ta ne ya
ishesu. Ace kamar Mama ta gagari kowa duk
abinda ya sameta da abinda ake gaya mata ba
su isheta nadama ba, idan ba su koreta ba me
kike so suyi miki? Ba shashanci kike sha'awar yi
ba? To sun baki hanya, meye kuma na kuka?
Mal. Kasim yace hakan ba hujja bace, duk
abinda xatayi, gara tana gabansu suna tsawata
mata, yau da gobe ana hada mata da addu'a, sai
Allah ya taimaketa ta gane illar abinda take
aikatawa. Saboda haka ta xauna, gobe Allah ya
kaimu lfya, xanje in ganshi. Ke kuma je ki
kwanta kiyi tunani, meye amfanin lalata
rayuwarki da kikeyi? Har jikokinki sai an yi musu
gori, wannnan abinda kika aikata! Kina da
babban laifi mama, sai kin tuba kin bi Allah kin
bi iyayenki sannnan xaki ga daidai a rayuwarki,
kinji ni? Ta amsa da kai, yace ta shi ki shiga
wajen 'yar uwarji kafin Allah ya kaimu goben. Ta
mike simi-simi ta ja akwatinta, inna saude ta
xuba mata ido tana mamakinta. Ta kada kai,
taca baka ce xata aikata ba, yarinya kyakkyawa,
ta lalata rayuwarta. Allah ya shirya mana, yace
amin albarkar annabi. Atsakar gida taga Baraka
tsaye tana share hwaye, ta matso ta kama mata
akwatin suka shiga dakin, kowacce ta nemi wuri
ta xauna bakin katifa. Baraka ta dubeta.........
Tace anya mama abubuwa da kike yi kanki
kalau? Ke bakijin kinya? Baki tunanin gaba daya
idanuwan garin nan sun dawo bisa kanki? Baki
da martaba da darajar Abba agarin nan? Haba
Mama, kamar ba tare muka taso ba? Tarbiyarmu
iri daya, nutsuwa da kamun kai, kowa na yabon
mu. Mutane na rububin mu, da son hada xuri'a
tagari. Ta daga kai sama, idanuwa cike da
hawaye ta cigaba, Allah ya isa tsakaninmu da
Danliti! Ta dube ta sukayi ma juna xuru kafin
Mama tace kar ki sake xagin Danliti Baraka,
alhakin sa xai kamaki, laifin mune? Tun tym din
da mukace muna son juna, ya kamata su Abba
su rungume mu hannu 2 amma suka ki, suka
gwammace in kwashe kayana in bishi. A tunanin
ki wane sakamako ya kamata su gani? Bayan
wannan dake jikina? Baki sake take kallonta,
kafin tace, maganar Banza ce, idan duka jina
kunnuwa ne xai taba sauraronki ba, wa kika
burge don kin aikiata wannnan sakarcin? Shi
kansa Danlitin adage yke kallonki. Kin dawo an
yi miki afuwa, cikin nman ya bayyana, duk sun
hkr, sun shanye, amma ki ntsu xuwa tym din da
xaki haihu, a daura maki aure, kar fa ki manta
xaman nan naki agida ibadane tunda Allah ya
shifida hakan, sai ki ga dalilin xaman, duk
xunubunku sun kankare, auran ku yayi karko tare
da xuria masu albarka. Ki kwanta kiyi tunani
mama, ko asiri Dan liti yayi miki, xakewar taki
tayi yawa. Ta sualala kafita ta kwanta, tace, na
kwanta shekiya Baraka, sai da safe ko? Ta bita
da kallo ta numfasa, tace Allah ya sa ki gane.
Amin, ta amsa da gatse ta juya baya abinta.
Baraka ta mike ta rufe daki ta dawo ta kwnta. Ta
jima bata sami barci ba, saboda juyayin halin da
'yar uwarta ta shiga. Da farar safiya M.kasim ya
usa gidan Ubban dawaki yasa aka yi masa
sallama da shi, jin cewa shine ke sallam ya sa
yace ya shigo cikin gida. Bayan su gaisa. Umma
ta fito suka gaisa. Sannan ya maida jawabinsa, a
karshe yace, alhaji kar bacin rai yasa ka yanke
wannan hukunci, ni ina ganin gara yarinyar nan
ta xauna agaban ku, kuna tsawata mata, sai
Allah ya taimakemu ya shiryar da ita. Don
girman Allah ka yafe mata dawo gida, tunda tayi
tunani taxo wajenmu, ta kawo mana kukanta.
Abba ya gyara xama yace, a tunanin ka a kashin
kanta, ta yanke shawara taje wajen ku? To ba
haka xancen yake ba, kila ba xaka sani ba ne,
saboda kuan cikin lungu. Amma ni tun jiya na
sami labarin wulakancin da yaron nan yayi mata,
ya tara mata jama'a, ya tozarta ta, ya kuma ce
ba xata xauna masa a shago ba, kaji dalilin
nemanku, amma ba nadama tayi ba. Yace, duk
da haka ina son ka duba girman da martabar ka
agarin nan. Kayi hkri ka amshi rokona, ba don ni
ba, sai don girman Allah da darajar iyaye. Ya
sunkuar da kai yana kadawa, kafin yace,
M.kasim ban ki ta taka ba, amma ba xan iya
xama da yarinyar da ban isa in bata umarni ta bi
ba. Ta fita tayo shashancinta, ta dawo min gida
ta wanke najasa ta kwanta. Mts! Ban jin
idanuwana xa su iya jure gainin wannan kaxanta.
Gara ta tafu su cikashe. Wlh na hkr da ita, kuma
ina rokon Allah ya sanya mana dangani nida
Mahaifiyarta, ba kuma xamu gaza ba wajen yi
mata addu-ar shiriya. Watakila wata rana taga
uwar bari, ta dawo da kanta ta neme mu. Kaga a
tym din xan tabbatar da tayi nadama. M. Kasim
yayi shiru, jawabin Uban dawaki na cike da
tausayi, ya numfasa, yace, na yarda da kai Alh.
Sai dai har yanxun ina rokonka, da ka sake bata
dama ta karshe, mu gani.idan bata daina ba, to
muma sai mu tsame hannayen mu. M. Kasim ya
cikwa Abba ido kwarai da gaske, ya jima kafin
ya numfasa, yace, shikenan ba komai nagode.
Yace nima nagode, Hajiya akara hkr, a bata
damar karshe, tace babu komai M. Kasim, Allah
saka da alkhairi. Yace amin, barin in koma in
turo saude ta dawo ita. Tace to ka tsaya kaga
abin kari akawo maka mana, ya mike cike da
fara'a, yana fadin alhmdlh, kar ki damu nagode,
to nabr ku lfya, Allah ya shige mana gaba, suka
amsa amin. Yaka hanya fice. Bayan tafiyarsa
kamar da hadin baki, jama'a sukayi ta xuwa
suna ba uban dawaki hrk tare da rokonsa ya
daure ya maida 'yarda gabasa xai fi kyau
agareshi. A cikin su har da abokansa da yaron
gidansa, watau kalla. Duk ya karbi rokonsu,
kuma yaji dadin kulawar jama'a gareshi tare da
tausaya masa akan kaddarar da ta fada wa
iyalinsa. Karfe Tara saura, Inna saude ta taso
Mama xuwa gida. Bata ma biyo da ita ta shagon
Danliti ba, balle ya gansu, haka suka taru da
matan gidan kamar zasu cinye ta danya, sannan
matza suka shigo suka dasa nasu. A gaban kowa
suka tilasta, ta dauki alkawarin ba xata sake
xuwa ko ina ba, kidan kuwa ta saba, to a yanke
mata hkunci da yafi wannan. Kwana 2 hatsaniyar
nan ta kwnata, mama na xaune cikin gida bata
fita daidai da tsakar gidan sasansu. Muna iya
cewa Danliti bai murda kambunsa bane haka?
Saboda haka xuciyar Mama ta sami 'ya nutsuwa.
Bata ita kadai ba, su abba ma sun sami 'ya
nutsuwa har tana debo 'ya'yan itatuwan da Abba
ya ka siyo ta kawo mata, tace ta sha saboda
rashin cin abinci da take fama da shi.....
***************** A wannan asabar din ma
abdulkrm ya xo daiyalinsa duka. Su ameera nata
murnar ganin auntynsum domin sun jima basu
ganta ba. Dr. Na ta dabo, yana son ya taka, sai
'yar banxar kuiyam shi ya sa yaki yarda Mama
ta daukeshi. Aunty Rabi ta tasa ta da nasihohi,
ayoyi, hadisan Manxo SAW akan ta dage ta yaki
xuciyarta ta dawo kan kanya, sannan ta nuna
mata wannan ba shine soyayya ba, duka
saurayin da ya nemi lalacewa da yarinyar da
yake so, a hakikanin gaskiyya ba son gaskiyya
yake mata ba. Sha'awar sassan jikinta kawai
yakeyi. Haka yayanta ta tsatsagge mata
gaskiyya, har yayi mata alkawarin idan ta nutsu
ta xauna gida kamar yadda aka umarceta, to
bayan ta haohu za'ayi bikinta, duk abinda take
so, shi xai sayo mata. Mama ta wani kuka tana
ba su ameera tausayi. Anann suka kwana,
washegari lhadi karfe 12noon suka juya. Su
ameera nata tambayar antyn su yaushe xata xo?
Tace kar su damu tana nan xuwa nan bada
dadewa ba, suna isa gida, yayan ya kira 'yan
uwansa, ya labarta musu abinda ya gani game
da Mama, idan har ya dore a hakan, alhmdlh!
Ana iya cewa an fara samun nasara. Kowa yayi
farin ciki jin wannan labarin da fatan Allah ya
shige mus gaba. Allah, da ikonsa a yammacin
yau din, tun bayan sallar la'asar mama ke cike
da kewar Danliti, kafin 5pm ra mance kaf! Da
alkawuran da dauka, babu abinda take so face
gain Danliti, kewarsa ta gigita kwakwalwarta, ta
birkita ta. Kamar an tsikare, kawai ta tashi ta
suri gyale da takalmi ta fito kanta tsaye ta fice
abinta. Dan gogan ta samun cikin dakin
barcinsu, tana shigowa yana xubawa wani
kaskon rushi ruwa, ya dago ido ya dubeta, yace
ba xan miki sannu da xuwa ba. Ta xaune gefensa
tana murmushi, saboda me? Ya xubo mata
harara, yace kwanaki nawa rabon ki da nan?
Sabo da nayi miki fada ko? Ta rungomoshi tana
dariya, ayya nawan ba haka bane, kowa yasa
min ido, sai surutai sukeyi kamar ni kadai na
fara soyayya agarin nan. Amma kana cikin raina,
kaima ka sani, bani da burin da wuce in kasanxe
tare da kai, ta bae baki yace tsarani, au baka
yarda ba? T yanxun ba ni na xo ba? Dana kiraki
ba? Ka kirani? Kamar ya? Ya ture kaskon ba
xaki gane. Sai dai na yarda kina sona, tunda
kika amsa kiran. Ta xura masa ido tace ngode,
tunda kasan hakan, me kake yi da kasko? Ke
duk xamanki a dakin nan baki taba ganinsa ba?
Da shi fah muke turaren daki. Kai amma wannan
bai hadu ba, kauri gare shi, kin kuwa san
tsadarsa? Ai ku maza ba gwabe bakin ku ake
wajen siyayya? Kabari xan kawo maka mai kyau,
idan ka sanya shi sai makwabta sun tambayeka
ina ka samo. Ko? To sai kin kawo din. Yanxun
mu ake maganar turare, ina kuka kwana da su
Abba? Ta tabe baki, me ma? Wai an bashi hkr
ya kyaleni, amma idan na sake xuwa nan, dole in
tafi. To kice kin karya doka, tunda gaki kin sake
xuwa, ni kuma da har nayi cinikin wani gida can
bayan tasha, ina fasa kenan? Bakinta har kunne,
tace ka fasa kuma? Ai xai mana anfani idan
munyi aure ko? Ya shafa kai, gaskiyya ne, xan
biya kudin in sa a gyara shi, ai sau muje ma ki
ganshi ko? Ya xama dole, yaushe xamu? Duk
tym din da kika shirya. Ko yanxumn a shirye
nake, mu tafi kenan? Bismillah. Ta sumbace ta
yace, amarya ta kenan, maman bebi! Ta rausaya
da kai tana dariya. Tare suka fito yana rike da
hannunta, har gaban motarsa. Ya bude mata ta
shige, ta dawo maxauninsa yaka suka tafi. Gidan
ginin kasa ne mai dauke da dakuna 2 kicin da
bayi, tsakar gidan turbayar kasa ce, haka ginin
babu digon siminti ko kadan, zallar kasar ce
kawai, illah iyaka cikin dakunan anyi masu dabe,
suna tsaye kafada da kafada, ya dubeta yace,
kinga gidan, ina fatan yayi miki? Ta yake baki
ta makalo wuyansa tace, ya fiye min kowannne
irin gida muddin da kai xan xauna cikinsa. Kar
wani abu ya dameka,a hankali na gyara shi,
kyau xaiyi fa, yayi dan murmushim ya falla ido
sannan yace, toh shikenan, tunda yayi maki, yau
din xan nemi dillalin in bashi kudin. Ta kara
kankame shi tace, ina tayaka murna. Ya xubo
mata ido yace ni xaki taya murna, ko ke xan
taya murna, gidan ki ne fa? Tayi dariya sosai. To
dukkan mu Congratulations! Ya sumbaci labbata,
tace thnk U! Sun jima cikin gidan suna
sharholiyar su, ana kiran magriba, suka fito, ya
kulle kwadaon gidan suka koma shago, maimako
ta koma gida sai ta rashe nan, tana nishadantar
da shi, kamar yadda ya bukata, ya siyo mata
abubuwan da take so, tace, tayi hani'an, kai
barci sace ta mana, ta yada kai bisa filo tai tayi
kuwa...... 11pm za su kulle hsago, ayuba yayi
juyin duniyan na Danliti ta tashe ta, ta tafi gida
amma yaki, ya kuma hana Ayuba ya tasheta. Da
ita suka kulle shago, ayuba ya kwana tsakar
shagon, shi kuwa dan gogan yana tare da
gimbiyar. Tsakar dare ta farka da ganta tare da
mutum. Ta tashi xaune ta bubbuga shi ya tashi,
menene? Tace dama ban tafi gida ba? Yace ga
shi nan kin gani, ai da ka sani ka tasheni
Danliti. Yace waya gaya miki ana tashin mai ciki
barci? Kiyi kwanciyarki kawai da safe kin koma,
Abba xai koro ni Danliti, yace akwai gida na biya
kudinsa, baki da haushin wannan. Idan kina
kwanciyarki, ki kwanta ida kuma yanxun xaki
fita 2am ga hanya nan babu ruwana. Bebi na
kawai nake ji. Ta watso masa harara ni banda ni
ko? To! Na ga kin wani hakikance ne, meye sabo
idan kin kwana anan? In banda gulma! Ta dare
ruwan cikinsa ta kai masa duka, ni ce
magulmaciya? Kai din fa? Todama mai neman
kuka ne aka jefa shi da kashi awaki, sai yaya?
Washegari, yadda bata sallaci magriba da isha
ba haka batayi asuba ba, karfe 7am ta dauko
hanya. Gata nan ga nan har gida, salalau-
salalau ta karaso ciki, ta iske duk sammakonta
Abba ya riga ta tara jama'am don haka tana
xuwa tsakar falo, tayi sanrada. Gwiuwa 2 ta xbe
ta fara kuka. Kowa ya saki baki yana kallonta,
M.kasin ya fara magana, yanxun saboda Allah
Mama duk maganganun da aka gaya miki ta
bayan kunnunwaki suka wuce? Ashe haka kike
da taurin kai? To mu babu ruwan mu, dama
rokonsa mukayi, ya ga girman mu ya hkr, tunda
ke baki gani ba. Shikenan ga hanya na, ki bi duk
wacce kika xaba. Abu yaya kamari har da
kwana? Ke Mama kiji tsoron Allah ki tausayawa
iyayenki. Ba xata suka ji tana magana, wlh Baba
bada niyyara kwana ba na fita, Danliti ne ya sayi
gida, yace muje na gani, mun dawo ina hutawa,
ban tym din da barci ya kwasheni ba, abba ya
xaburo yana fadin, kunaji Maganar Banxan da
take fadi ko? Kun tabbatar da cewa abinda nake
fadi gaskiyya ne? To ya isheni haka! Ya isheni
haka!! BAKIN CIKI ba xai akshe mu ba. Daga nan
ki juya ko koma, idan har ki na son kanki da
arxiki, wlh! Wlh!! Babu wanda ya ya sake roko
na in kyaleki cikin gidan nan! Duniya ce da fadi,
karki saurara wajen bin ta kwararo-kwararo har
ki gano iyakar ta! Tashi ki bace min da gani,
kafin in kusa kashe ki da duka. Gaba daya falon
yayi tsit, sai shasheshekar kukan Mama, jim
kadan muryar abba ta kara gauraye falon, kai
Jama'a! Ina xan kai takaici da BAKIN CIKI? Me
nxan yi wa yarinyar nan a dniya na huce, banda
in sallama ta, tamkar ban taba haihuwarta ba?
Ki tashi fice min nace, in daina ganinki a
gabana..... Ki ta... Kawai sai ya yanke jiki ya
fadi, gaba daya suka mike da sallalami sukayi
kansa...... Toh masu karatu, wannan fa shine
wasa farin girki. Nayi iya kar kokarina ace nayi
muku sallama anan. Amma ina abin ya faskara,
kuyi min hkr karshen badakalar wannan littafi
yana cikin 3, ku biyo ni, kada ku gajiya nayi
gaba....................THE END!!!

BAKIN CIKI 3***1 Ganin haka yasa Alh Adamu ya
figi wayar rediyo ya tsulawa mama "zaki kashe
mana shi ne? Ta mike a gigice ta yanka waje a
guje shima ya bita da gudun yana fadin fita!
Shegiya! Tsinanniya! Yar iska! Idan kin sake
dawowa gidan nan sai mun taru mun kasheki!
Har suka wuce kofar gida a guje sannan yaja ya
tsaya yana haki, yar banzar yarinya gantalalliya
maras mutunci! Ya dawo yana ta zage-zage yan
kallo suka fara kawo dauki ya fada cikin gidan
ya iske umma ma ta sume anata shafa musu
ruwa tare da firfita ya kutsa cikin yan
gudummawa. Abba kam ya farfado amma umma
abin yaci tura don haka gaba 1 aka debesu sai
minna inda zasu fi samun kulawa sosai sannan
yayansu susan halin da ake ciki. Al*amrin ya
daurewa Abdlkrm kai kwarai da gaske sanda ya
sami waya a office. Yaushe suka baro fandogarin
har wann abin ya faru? Dama mama bakan
kawai tayi tana jinsu tana kallonsu a dage?
Tirkashi! Ai dole su hakura da mama!
Hankulansu bai kama tashi ba saida suka zo
asibitin suka ga halin da umma ke ciki. Tun
isowarsu take sume Dr yace heart dinta ta riga ta
buga saidai suyita addua Allah yasa ta mike.
Kowa ka kalla dole ya baka tausayi musammn
Abba da yayi wata muguwar rama sbd zullumi. 3
days anata kai kawo akan umma abun yaki dadi
abdlkdr yace a basu ita su wuce Abj a daren aka
sallamesu suna jira gari ya waye su wuce. Karfe
3 na dare Abba na zaune a gaban gadon yaga
umma ta daina jan numfashi a zatonsa ta sami
sauki ne don hk yayiwa Allah godia ya leka ya
kira nurse yace tazo ta gani ko zasu cire mata
tukunyar gas din iska ta huta. Nos ta kalleta da
kyau tace tana zuwa cikin sassarfa ta fita ta kira
dr suka dawo tare ya gwada ta da kyau ya cire
duk injin dake jikinta ya rufeta da mayafi ruf!
Gaban Abba ya fadi ya tsurawa dr ido ya juyo ya
dubeshi... Alhaji..... Ya katseshi naga ka rufe
mata fuska me hakan yake nufi? Ya dafa
kafadarsa yace sai hakuri Alh kuyi imani da abnd
Allah yayi. Yasa kai ya fice. Abba yayi mutuwar
tsaye fadi yake Innalillahi.... .....!!! Nos dinnan
ce ta kamashi ta zaunar tana kwantar masa da
hnkli saidai zaiyi wuya idan yanajin ta ya dai
zauna ya zubawa gawa ido yana tasbihi. A haka
ya riki asubahi sannan ya tashi da kyar ya fito
masallaci yai salla. Yana fitowa su abdlkdr na
fakin har sun fito tafiya ya nufesu da sauri suka
yi saurin gaidashi ya jikin ummar? Yace jiki yayi
sauki ina fatar zakuyi hakuri ku dauki maraici.
Haka Allah yaso.... Ya wuce da sauri yana goge
kwalla ya barsu suna kallon juna kamar ba. Ya
jima yana kallon gawar umma tamkar a dream
sannan suka shigo yaya soja ke kan gaba ya
zauna ya bude fuskarta nan da nan abdlkrm ya
fice daga dakin yana kwalla da salatin Manzo
SAW. Shi kuwa soja zura mata ido yayi baya ko
kiftawa ganin haka yasa Abba yaja mayafin ya
rufeta sanna ya cira kai ya dubi Abba amma bai
iya firta komai ba idanuwansa kamar garwashi.
Abba ya dafashi yace ya kamata mu wuce gida
kuyi hakuri kaji?. Ya kada kai kwalla suka zuba
kuncinsa yasa hannu ya share nan da nan aka
fito musu da gawar aka sanya a mota suka tafi.
Anti rabi da inna saude suka gigice ta fasa kuka
ganin haka suma yaran suka hau kukan. Abba ya
rungumesu yana rarrashi yaya soja ya kira waya
abj ya shaidawa anti amina. Daga nan ya kira
abdrhmn yace su hadu a fandogari nan take suka
danko hanya shida ya saeed da matarsa suka
biya birnin gwari suka wuce da yaya Ali. Gida ya
barke da koke-koke kan kace kwabo rasuwar
tayi tambari a gari. Baraka da mahaifinta suka
garzayo gidan. Misalin 10am suka iso da gawar
kowa sai cewa yake mama ta kashe uwarta!
Hnklinta ya kwanta, babu bata lokaci aka
shiryata aka fito da ita jama'a kamar kasa suka
sallaceta suka kaita makabarta, uban dwk dai
karfin hali yake har suka sata a kabari shida
yayansa wanka zata fito lokcn danliti ya shigo
gidan a sukwane ina kike? ta karasa fitowa da
bocket a hannu gani nan wanka nayi. ya matso
ta yana fadin kina da lbr kuwa? tace name?kai
tsaye yace ummanki fa ta mutu yanzu aka wuce
da ita..... ta saki bokiti da kwandon soso ido
waje tace gane ba? yace ya hausar baki gane
ba? kije kisa riga kije gidan ki gani amma ni
tabbs haka naji ana fadin matar uban dawaki. ta
rasu ko yana da wata matar bayan ummanku? ta
fasa kuka ta ruga daki ta rarumi riga tasa ta fito
waje a guje ba takalmi ta kwasa da gudu. tana
salati hawaye na kwarara, danliti ya fito ya bita
da kallo cikin ransa yana fadin mahaukaciyar
banza ta wani kwasa da gudu kamar barinta
zasuyi zama a gidan. Shashahsa! yaja tsaki
yajawo kofar gidan yasa kwado. ita kuwa taci
gudu gidan ma nisa yayi mata tana isowa
motarsu Abba na tsayawa. Taja birki tana haki
kamar ranta zai fita ga hawaye na kwarara duk
suka fito suka zuba mata ido shi kuwa soja yana
fitowa ita ya dosa gadan-gadan idanuwansa
kawai ta hanga ta soma ja da baya kafin ya
karaso don kanta ta juya ta koma inda ta fito.
yace dakin tsaya mana in karaso! kiga yanda
zan kasheki da sauran kwananki! su M kassim
suka rikoshi suna bashi hakuri kwalla taf idonsa
yace in banda raini me zatazo nema bayan ta
kasheta? tunda wuri ku gaya mata idanta bari na
damketa saidai wata ba ita ba! akayi tabashi
haquri,yazauna cikin en uwansasunata karban
gaisuwa,inna saude da sauran matasun cika
falon umma.baraka kuwa hawayenta yaqi yatsaya
da zarar ta tuno mama sai taji kamar ta
sheqabarzamu da bakin ciki! Gidan dan liti
mama takomatana tafe tana kuka anata kallonta
tamkar mahaukaciya...tana isowa taga gidan a
rufe,tarasameke mata dadi....mutuwar umma ko
rashin makulli?tasake bin titi tadawo shago
tazauna akan benci kofarashagon dan liti na
kallonta bai tanka mata ba.ayubayace kace
tashigo ciki mana a ranafa take.......yacekasani
ko ranar tafiso?kyaleta tagama juyayin muma
haka mukayi muka bari.ayuba yace bakada
tausayidan liti,narasa inda imaninka yake,yace
to kaki filincigiya da sanarwa mana,sai su nemo
makashi.ayubayafita ya lallashi mama tadawo
shago tayi kukantaharta gaji,bacci ya
dauketa.danliti kuwa yaci gaba dacinikinsa
hankalinsa kwance..don yasan yasha gaban
kowa babu mai tinkararsa akan wani
magana.ammayamanta Allah nanan?kuma yana
kallonsa?baikulataba saida yagama cinikinsa,zai
kulle shagoyasameta zaune yace kitaso muje in
sauqeki indawoyau anan zan kwana,,,,,,tadubeshi
ido jazir tace anankuma?nikadai zan kwana
kenan?ya qara tsuke fuske yace ke!na aureki ne?
ina tambayarki...na aurekine?Daga taimako sai
ya zama tsiya?kuma shikenan saiin ringa kwana
dake,salon kisa mutane su zageni,acena ajiyeki
muna dadiro ko?......takada kai dasauri,tace a'a
wlh ba haka nake nufi ba,yi haquri,yacemeyasa
kikeson batamin rai?kinga nafasa kaiki tashi
mazaa ki kama kanki,ungo makulillin ki
wuce.tamarairaice tace kayi haquri katausayamin
dan litikaga dare yayi bayan tashan nan yan
shayeshayene.wulaqanci zasumin don Allah
kayihaquri.......ya zura mata ido fuska daure
yacemuminar qarya!da anyi magana ki
marairaice,ni tashi muje in ajiyeki indawo!iya
mike yayi wajeabinsa,canta sameshi cikin mota
ayuba dai bai iyakallontaba saboda tausayi
tunda tashiga baitankamataba duk lallashin
datake masa kuwa...hakata sauqa tana waigensa
yayi ribas ya figi mota yawuce tasa mukullai ta
bude kofan tashiga ta kulle da sakatagidan
bakikirin tayita laluba tashiga daki talalibo
ashana ta kyasta,,,ta hango inda fitilar kwaitake
tana kunnawa ko minti goma
baiyibayamuta,kalanzir din dake ciki ya
qare.........dole takwanta kusa da katifar da
danliti yasayo mata.takasabacci tarasa abunda
yake damunta...tsorone?fushin da danliti yakeyi
ne?ko rasuwar mahaifiyarta?saikusan asuba
tasamu bacci mai nauyi yadauketa. kwanaki uku
da rasuwar umma.a tsawonkwana ukun nan abba
baya barci,daka dubeshi zakagane yana wani
boyayyen ciwo dake
tsananindamunsa.idanuwansa sun
zurma,fuskarsa ta tsukekwarai da gaske,shisa
hankula yayansa yaketashe,abincin kirki babu
mai cinsa...sallar azahar aka kira kowa ya tashi
da nufin yin alwala,akaja sahu nanbisa tabarmi
malam qasim ke limanci tunda akafarazaman
makoki,,,,,,,,,,,,,,,a raka'an qarshe suka dagojiri
yadebi abba ya buga da qasa mutan biyu
dakegefen hagu da damansa su suka yanke
sallan,sukajanyeshi gefe suna masa firfita har
saura suka idar da sallah.yaransa suka rugo
gunsa tare da sauranmutane,,,,,masu shafasa
ruwa nayi masu firfita nayiharya farfado,sai dai
yanayin yanda yafarfado yafirgita kowa,gefen
damansa ya shanye,baki yakomagefe,gwanin ban
tausayi.labari yashiga cikin gidamata sukayi ta
fitowa suna koke koke ganin yanda akadauko
abban kaman gawa akasa a mota sukakaman
hanyan minna......har akayi bakwai abbanacikin
kaka nikayi.dole suka kasu,alh basiru da yaabdul
kareem suna tare da abba saura kuma sunawajen
karban gaisuwa..kai!sunga tashin
hankali,kukadai anyishi babu adadi,da yana
magani.daya magance matsalar data sauqa cikin
gidan uban dawaki.. Wasawasa abba ya kwashe
wata guda ana jelarasibitoci,daga minna aka
turasu k.d dagananzariya,akarshe ya abdulqadeer
ya daukeshi yadawodashi abuja,sukafara shirin
fita egypt cikin sati gudakomai ya
kammala,abdurah man da anty amina ne suka
tafi dashi saboda yanayin aikin sauran ammashi
yaya soja zai biyosu da zarar yasamu
umarnidaga ofis. andanga canji a cikin sati
biyun dayasamu yana ganin kwararren
likita,domin ansamu yanamagana kuma yana
amfani da hannunsa kadankadan,kafarce dai
bata aiki haryanxu.,...a sati nauku..akabasu
sallama tareda magunguna da zai ringaamfani
dasu.suna sauqa abuja.ya soja yawuce dashi
gida yace anan zai zauna yarinqa samun kulawan
dayadace..aka gyara masa daki,,,sannan yayi
masarijistan zuwa ganin likita lokaci lokaci,anty
aminatasha damarar kulawa dashi cikin hakuri
dagirmamawa Dan jikansa kuma malami yana
debemasa kewamusamman da yamma zaiturasa
akan kekensa sufito shan iska yana zagayawa
dashi cikingidan,wataranma harwaje dan yaga
gari,,,,kullam daresai sunyi tilawar alqur'ani mai
girma sannan sukebacc.haka kusan duk sati
yayansa ke zuwa dubashi danasu iyalan.har
safiya ta haifi ya mace,abdurahman yaso yasa
mata sunan umma,ammaabba yace tunda
akwaita yana roqon arziqin asamasasunan
mahaifiyarsa watoo sakeena tunda shi
yanxubaida mai sunan....abdurahman bai musa
masa badukda dai sunan bai kwanta masaba
yabi zabin abba,don ya faranta masa rai....komai
na abbayadawo qarqashin kulawan yaransa
hardagonakinsa,,,bayan wata biyu da haihuwar
sakeena. Bayan wata biyu da haihuwar sakeena
qarama yaaika da takardar murabus,,,aka nada
alh basiru amatsayin uban dawaki.zaman sa yayi
masa dadi agidan dansa hankalinsa kwance
dukda yana damuwada rashin umma...sai dai
imanin dayayi qokarintusawa kansa wajen maida
al'amuransa wajen ubangiji.illa iyaka yarakata
da addu'a tareda nemawamama shiriya. To
komai dai sai Allah yayi hattaasiririn dayayi
tasiri ajikin mama da izininsa ne,,,,donya jarabta
ta da iyayenta kuma yayi wa danliti
daurintalala.saboda fidda tsoron Allah a
zuciyarsa. Page 12:mama dai sharholiyanta
takeyi dukta mance abubuwan da suka
faru..domin ko alama bata ganinkowa a idonta
sai danliti.....shine mai sata shine maihanata
musamman yanxu data samu
lafiya,cikintayashiga wata 6 yana neman 7
batada watamatsala,batada abun dayake daga
mata hankali saifushin danliti.shikadai zata gani
yanxu tafita hayyacinta...tun mutan gari na
suru2 suna zaginta harabun yazama jiki bamai
kallonta......sau dayawa zakasameta cikin shago
ita ke siyar da kayan shagon saitazauna tun safe
har dare suna sakarci kalakala...gidan danliti
kuwa yanxu bata tsoronsa dukdare zatabi hanya
takoma takwanta,,,shiyasa ma inna saude
tadaina bin hanyar haka ma baraka ko saudaya
bata bari hanya ta hadasuba. A yan tsakanin ne
akasa ranar baraka da Muhd dinta 5mnths. Basu
baraka kadai ke gudun mama ba harda Ya Ali
shima idan yazo garin bai biyowa ta kofar
shagon ya gwammace yayi zagaye ta hanya mai
nisa, ya kanyi kuka shi kadai idan ya tuna halin
da mama take ciki baida abinyi face addua
kullum bata yankewa a bakinsa yakan jima bai
shigo garin badon kar ya shiga gida a rinka
bashi mummunan lbr masu jirkita masa tunani.
Kwanci tashi watan haihuwar Mama ya tsaya ta
kumbura dam! kamar ta fashe sbd hawan jini
bata sani ba, tunda ba awo take zuwa ba, amma
shegen dariya yake mata wai ta dawo alkubus.
Ita kadai a daki tsakar dare nakuda kamata ta
rasa inda zata tsoma ranta taji dadi tayi nan tayi
can tana ambaton Allah tare da tambayar kanta
wannan wane irin ciwone kuma? gab da asubah
jini ya goce mata idanuwanta suka raina fata
fadi take shikenan zan mutu! ta hau kuka tana
kiran zan mutu danliti ka taimakeni! garin Allah
ya waye 7am danliti baiga tazo shago ba alhalin
kullum 6am take zuwa wata zuciar tace yaje ya
ganota ya buga mota ya iso gidan ya iske a
kulle yayi ta bugu bata bude ba wasu samari
suka taimaka masa aka buge kofar ya shiga. a
zatonsa ma ta mutu ganin ta shame shame cikin
jini saida ya tabata ta motsa tace zan mutu ka
taimakeni. cak! ya daukota ya saka a mota sai
asibiti take sukace bazasu iya ba ya kaita
kagara, nan da nan ya buga mota yazo shago ya
kwashi kudi ya wuce yanata zage zage dama
haka takeso aci kudina tana jin ciewo tayi
zamanta bataje asibiti ba zata farfado ta hadu
dani kudin dana kashe saita biya su don ubanta
.......ayuba yayi tagumi yana juyayin karfa
mamatarasa ranta .yana isa asibiti a ka turata
emergencylikita yace tiyata za'a yi mata sunan
bukatar jiningaggawa. Babu yanda Danliti ya iya
dole yaceagwada nasa jinin a gani ko zaiyi daidai
Aka gwadaamma bai yi ba. Mai daukar jinin ke
gaya masa akwai wanda ya saba bada jininsa
ana biyansa, idan yayarda a kira shi au tsadance
ya biya. Ba ason ransaya amince ba nan da nan
aka kirashi, suka tsadance,ya biya shi dubu biyu
aka diba, ga kuma kudin aikidubu goma sha biyu
da dari bakwai da hamsin. Donhaushi kamar
yace bashi dasu wannan shiri Maimakon yaci
bulus ya dawo yana cacan kudi donneman
lafiyarta. Wucewar minti talatin aka fito da itada
jariri namiji. Santalele dashi ga kyau ga girma
shikansa likitan sai da yaji kamar ace babyn
nashi ne.Malaman jinya kuwa kamar su lashe
yaron. Ahi kuwaDanliti yake kawai yakeyi cikin
dan kankanin lokaci da bai wuce awa daya ba an
wawure masa kusandubu sha biyar, bai ma san
me zataci ba nan gaba namagungunan. Ya na
tsakar wannan tunanin watanurse tazo ta gaya
masa akawo kayan da za asawababy kudin
aljihunsa kaf sun kare sai da ya komaFandogari
rai bace. Ayuba yayita masa dariya yana masa
kirari, "angon karni angon karni!!", bai kulashiba
ya shiga ciki ya sake lalo wasu kudin ya fito
yakoma. A kagaran ya shiga wani shago, ya
sayo kayanjarirai kala hudu da rigar sanyi, sai
sabulu da Omonwanki ya koma asibiti ya kai
musu aka sayaron.Mama tana kwance bata
farfado ba tukuna. A ka kawo masa jariri ya
karba ya zura masa ido gaban saya fadi. Yace a
ransa "kaga shegen yaro kamar mudaya dashi?
Maimakon ka kwashi uwarka, sai kadebo ni? Tun
yanzu kenan ka nuna min baka dakunya". Ya
bawa kansa dariya ya shiga yi kamarsakarai"
kwana bakwai mama ta gyagije tare da taimakon
nurses da wasu masu jinya saboda karyarda
sukayi, wai daga nesa suke kuma iyayensu
basason aurensu, shi yasa babu wanda yazo
jinyarta.Babynsu sai kara kyau yakeyi, shi ya
kara jawo musufarin jini a wajen ma'aikatan
asibiti da masu sontaimaka musu. Ranar da ta
cika kwana 7,aka sallamesu likita yagindaya
mata sharudda banda aikin qarfi,sannan
tatabbata tana samun ishashen kayan qarin
jini....dantayi saurin maida jikinta.sati daya aka
basu su dawoakara duba lafiyarta sukayi sallama
da kowa cike dakewa,,,,don anriga ansaba
dasu.danliti ya kwashesu a mota suka kama
hanya. sunfara tafiya ta kallesa idokode tace
haryanxu banji kafadi sunan yaronba,kawaiqarya
nayi wa mutane ake kiransa adamu...jitayikawai
yamake mata baki..kar insake ji bakinki ya
kirawannan sunan.dama na kyaleki ne dan
ganinmutane,,don iskanci kirasa sunan da zakisa
wa shegen danki sai sunan ubana? Tuni take
rungume da baki ido waje takekallonsa,,tace
haba danliti!baka tausayina? dana sansunan
babanka ne zanfada?wlh zuwa kawai
sunanyamin nafada musu shiyasa ranan da kazo
da ayubasuke ta kiranka baban adamu... yasake
kawo matawani dukan,yace sake fadi kikayi??
wato raini ya shiga tsakaninmu koh? bakisan
cewa inajin haushinkiba ko?to kibi a
hankali,idan kina neman zaman lafiyadani,,idan
nasake jin adamu a bakinki sai na karyakiwlh.....
taguma ta doka tana kwalla tana kallonsa,Allahb
aka haquri danliti,yaron nan dai dankane,duk
sunanda kace akira dashi za'a na
kiransa.bannaso na bata maka rai danliti..amma
kai abu kadan sai fushi. yacebabu ruwana da
sunan yaro,,idan kinso ma kinakiransa BIRI ,duk
daya a wajena!tace Allah ya hucizuciyarka,,
maganar batakai hakaba,tunda ran talataaka
haifishi zamu na kiransa mai kudi...yadan
dubetakadan ya kauda kai yarage naki inkinso
ma kina kiransa miloniya wannan keya
dama..zatayi maganayadaga mata hannu banso
jin don Allah kimin shiru.tasunkuyar dakai tana
kallon yaron dayake jikintayanata bacci
abunsa.har suka iso gida,,basuyi wanimagana
ba.ya tsaya kofar gida tafito yatayata
kwashekaya..taron mutane nata kallonsu suna
mamakin wannan lamari..bai zaunaba yajuya
yana kokarin fitatace ya maganar abinci?zan
girka ne ko za'a na kawomin na sayarwa? Ya
kalleta sama da kasa yace,wai ke me
kikadaukeni?baki ganin kudin dana kashe a
asibiti? Koshagon kikeso ya rushe na tsugunna?
baga saurankayan tea a nanba?ki hada mana
kisha! Kedamaba'aso ki nannagi abu mai
nauyi.mtsssss..... Yajatsaki yayi waje,,,ta koma
gefen katifa tana tabe baki...a ranta tana fadin
Allah ya huci zuciyarka.tadangyara waje tamaida
kai ta kwanta ba'a jima ba bacciya dauketa...
Bayan sallar la'asar kukan yaro yatasheta.ta
tashi da sauri tabashi nono da ruwa..nandanan
yasake komawa barci.tafito tsakar gida
tanahamma tareda mikar yunwa..tayi dan
shawaginta a tsakar gida takoma daki..tajanyo
ledar kayan tea tazuba a kofi tajanyo fulas zata
tsoyayi ruwa taji baburuwan..tasaki tsaki ta nufi
kichen babu itace ko dayabare ta daura.haka
tadawo tasha tea da ruwansanyi..tasake
kwanciya dan babu abunda zatayi harqarfe taran
dare bataga danliti ba,,bare tasa ran wani abun
sanyawa a baka. Ga yunwa tana sha'awar
tacimai dan gishiri...nan take tayafa gyale ta
zura silifastadauki jariri taja kofa tayi waje ta
lallaba a hankalitayi wajen danliti.....yana
ganinta ya daurefuska,,,yayinda ayuba ya taso
ya karbi maikudi,,meya kawoki?inji danliti tace
naji shiru ne ga yunwa inaji.....ba akwai kayan
tea ba?we me kedamunki ne? Murya raunane
tace nasha wlh..dama ruwan sanyinasha babu
sauran ruwan zafi kuma babu itace...maidan
gishiri nake sha'awan ci kodan yayane! Ya
gyarazama nifa ba ubanki bane,bakuma
mijinkiba bare kinadauramin wannan
nauyin,,kingane koh?daga taimakosai ya zama
tsiya?ki dauki duk nauyinki ki dauramin? to bafa
zai yiyuwa kinjiko?karkisake biyoni shago
kicenabaki wani abu...abun da nasamu nabaki
basai kinmatsamin ba..karki sake dauko danki
kizominnan...idan kunne yaji..... Tace yi
haquri,,,yacewaayuba bata danta ta koma.ta
karbeshi tajuya zatawuce taji yana fadin bata
taliya daya taje tadafa karta cinyeni....ta karba
tana murna ya wurga mata nairaashirin tasaya
itacen..jikinta na rawa ta dauka hardagodiya ta
sabo yaronta takoma gida..sai yanxu matake
tunanin a ina zata samo icen dare yayi?ta
sauqenumfashi numfashi takoma takwanta
dayunwarta.dasafe da kanta taje ta nemo
itace,ta tafasa ruwa ta dura a filas,tayi wa danta
wanka itamatayi..tahada tea tasha da ragowar
biredi. Tayi wanka tayi wanki duka ita
kadai,,anjima kumadole ta bararraka taliyan da
zataci.ko ta ci gaba dashan shayi...aikin yamata
yawa ita daya shisa dakwantawarta zazzabi ya
rufeta. Maganar haihuwartakuwa naci gaba da
yaduwa a gari,wasu emmata masukarambani
haar suna zuwa mata barka.haka tci gaba da
manejin rayuwa sai abunda danliti yaga dama
yakekawo mata taci,a lokacin da kuma
yagadama! .......kwana 7 suka cika tayi masa
maganarkomawarsu asibiti,,,kai tsaye yace bai
zuwa,Allah daikonsa jikinta ya hade kamar yana
samun kyakkyawarkulawa.haka mai kudi yayi
bulele dashi alamun ruwan nonon dayake sha
yanada kyau...batadai zuwa koina,,,saboda
danliti yahana.komaisa oho?shi kadaiyasan
dalillin yin hakan. wannan satin shine ake bikin
baraka da muhddinta,mama na gida mai kudi
goye a bayanta.tunsafebatasa komai a
cikintaba,,,har zuwa yanxu da akaidar da sallan
la'asar.tagumi hannu bibbiyu tayi tunanitake
lafiya meyafaru da danliti baizoba?bata
samuamsarba taji tsayuwar motarsa. Farin ciki
ya lullubeta ta taso ta tarbesa.babu walwala ya
wuceta yashigedaki...t abiyo sa abaya tazauna
kusa dashi tanatambaya,,,waya tabamin cweethrt
dina?ko fushin netunna jiya? Ya ballo mata
harara yace kinason wanimarinko?to kici gaba
da tadamin wannanzancen,,tadan kada kai tana
murmushi tace sha kuruminka,indai maganar
aure ne bazan sakeyimakaba duk lokacin dakaga
ya dace saimuyi,,shiyasa bangankaba
tunsafe?.......ido zuruyana kallonta bansaniba!
tace yi haquri shalele mezanci yau?yace babu,ki
tashi kishirya kije gidan bikikici..tace bikinwa?
yace ke saboda sakarci ma bakisan ana bikin
yar uwarkiba?bikin yarinyar nanakeyi baraka...ta
ware ido ta washe baki,bikin barakaakeyi?to ina
zan sani ka hanani fita? Yayi matabanzan kallo
ai dama ni kike gani na hanaki fita?toubanwa
zakiyi a waje?kina samun ci kina
samunsha...kinfiso kirinqa yawo kwaroro kwaroro
da goyo ana nunaki?to shikenan tunda kinfison
hakan gahanya nan,,,,amma kisani kwayar dawa
bazan kawomiki gidan nan ba..da sauri ta
rungumeshi,Allah sarkidan litina,ba haka bane
,nima bana sha'awarfitan,tunda baka so.yanzu
bari in shirya ka saukeni agidan bikin...a razane
ya kalleta,wai ke meyasa jaka ce?kawai sai in
daukeki a mota in kaiki gidan biki anakallonmu?
idan ke mahaukaciya ne nida hankalinanasan
abun da nakeyi....
BAKIN CIKI 3***2 Yaja dogon tsaki ya tashi .da
sauri yatashi yafitayana fadin sakaryar yarinya
kullum sai ta bata wamutum rai!ta taso ta biyo
shi tana bashi haquri,baisauraretaba yafada
mota abinsa,,,,tadawo tanahawaye tana shirya
mai kudi.ta goyashi ta rufa gyaleta kulle
gidan...bata zame ko inaba sai gidansu
baraka.ana tsaka da biki kallo yadawo
kanta....dukyan uwa na kallonta a
wulaqance,tana gaishesu sunabasarwa.kai tsaye
inda inna saude take ta dosa,takuma zuba mata
ido harta qaraso gunta,,,sannu inna!Ta bita da
kallo daga ina?tace daga gida,yanxu danlitiyake
gayamin ashe auren baraka ake,nace ina nasani!
inna saude tace dama ya za'ayi ki sani?ke
kokunya bakijiba?kika ratso jama'ar nan da
goyo kikashigo?dubeki kamar ankoraki babu
mamaki ma bakiciabinciba. Duk baki ya wani
bushewa anya kuwamama...baza kiji magana
bako?wannan duniyarkagama da iyayenka lafiya
ma ya ka qare?belle ke kina kallo mahafiyarki
tafadi ta mutu saboda BAKINCIKi,,mahaifinki
nacan bisa keken nakasassu.ammaduk wannan
baisa kinyi nadama ba mama?ke kuwawata irin
iskar duniya ke kwasarki????? A marairaicetake
magana inna bai kamata ku ringa ganin laifina
bani kadai....ta katseta da sauri rufemin baki
sakarya! Da yana son aurenki da tuntuni baizo
yayi maganaba?tun yaushe kika haihu?ina
lissafi watanki biyarkenan! ya ajiyeki kawai kin
biye masa kunawatsewa..wa llahi ki guji
makomarki,,ki kuma gujiwalaqancin da
namiji.gashinan ai kinfara gani da hakakike?to
wlh ki kuka da kanki karma kice kin
sanni,,saboda haka juya ki koma inda kika fito!
Tace aidama shima dan liti yace inya shirya
zaizo yasameku a daura mana aure,ta watso
mata harara tajadogon tsaki zata wuce mama
tace banga amaryarbainna,ina take?ta juyo
tace,suna makwafta itadaqawayenta..tayi
tafiyarta sabgoginta.mama ta shigazabga
loma,rabonta da abinci da naman kaza harta
manta.tayi ta zabga tana zare ido gwanin
tausayi.kankace kwabo,ta tada shinkafar nan
cikin kwanotatas,ta kora ruwa da kunun aya tayi
gyatsa tayihamdala,sannan tajita aduniya..
Tananan tsuru kamarmujiya baraka tashigo cikin
gidan,inna ke gayamatamama tazo,,ta zagaya
bayan kicin din tasameta zaune tana bawa mai
kudi nono,,bakin ciki yaturnuketa kamar ta
hadiyi zuciya ta mutu.haka nan tacije ta qarasa
gunta fuska daure....amare!injimama,tace mama
kenan,ya kike?tace kuma dankowa ya gujeni
shine hardake koh baraka?zancenbikinma a
bakin danliti nakeji,,,banci arzikin da zakizo
kisameni ki gayaminba.ai kinsan inda nake.ta
kalletasama da qasa ni bansan inda
kikeba,,koda ma nasaniwannan ba gidan zuwana
bane..hasalima namantadake.bandan kinxo inna
tace kinanan ba wlh bazantaba tunawa dakeba.!
mama tace ba laifinkibane,,,,,,,ta rausayar dakai
tace thank god da kika gane ba laifina bane.bari
inkoma frnds dina na jirana.tajuya dasauri
tawuce ko kallon yaron batayiba.mama ta
tabebaki tace agayas mai qawaye,zakaran da
Allah yasoda cara,ko ana muzuru ga shaho sai
yayi.danliti nedai ba a kauna,nikuwa inason
kayana,bazan rabudashiba! yawwa! Ta mike ta
jefa mai kudi a baya ta goyeshi ta tafi neman
inna tasameta tace innazantafi,ta juyo ta
dubeta,bangane zaki tafi ba?bakijiabunda nace
bane?ko a zatonki wasa nake?nandanan ta
kumbura fuska.samu wuri ki zauna kafin nabata
miki rai!ta zauna gefen gado tana
kunkuni,kowana kallonta,masu taya inna fada
nayi........ana sallar magaruba gida ya gwaraye
da duhu sai inda aka ajiyefitulun kwai keda
haske.mama ta fakaici ido ta sulaleabunta ta
kullin wainar ta da miya,duk ta juye su
cikinleda.abincin dare ne da aka rabawa kowa
tajuye nataa leda,,ta cika wa zaninta iska ta
harba gida abinta.Hankalin inna bai dawo
garetaba,,sai da za'a wuce da amarya.ta nemi
mama sama ko kasa ta rasa.ta dokatagumi tana
sanar da Allah da manxonsa kafintace,kai
jama'a!wannan yarinyar tayi nisa batajin kira!
Allah ka shirya mana ni saude..sauran mutane
sukace amin!haka aka wuce da baraka tana
kukan BAKINCIKI!da takaicin yar uwarta.ita
kuwa mama tana can hankalinta kwance,ta juye
wainarta a kwano miyarkuwa taji tantakwashi
masu taunuwa,zatafara cikenan danliti yashigo
gidan ,ya tokare bakin kofayana kallonta,,,tace
saboda me?yace saboda naxokafin magruba
naga baki dawoba. Tayi dan murmushidanliti
kenan,bikinma badan kaikace najeba maizai
kaini?kaga maganar inki dawowa ma
baitasoba.yaqaraso yana fadin Allah
yasoki,dama bell dina nadawo induba,idan baki
dawoba inbiki hargidan indawodake,,sannan
inmiki shegen duka! kinganshi ko?, Tace Allah
sarki danliti bai kamata kanadukanaba,,,iyakar
biyayya inamaka,amma dankuskure kadan sai ka
hassala..!ya zauna kan tabarmayace,ke dai kiyi
shiru tunda Allah ya kwaceki yau,aiku mata sai
da haka,domin kwakwalwar kifi Allah yayimuku.
Ta sosa kai tana kallonsa,batace komai.danki
yayi barci ne?tace eh! Meye wannan kike ci?
tacewaina ce inna ta bani.yajanyo kwanon
gabansa yacedama kuwa yunwa nakeji..tace to
muci tare mana aitana da dan yawa.yace ni
bazanci dakeba miko filet inzuba miki.ta jawo
filet din roba ta miqa masa,ya jefamata guda
daya..tace guda daya nagani?......a fusace yace
wannan wani tambayar banza ce?don kinxo
dawaina zanci? shine kike min kurilla?watau
nawa nebanza!ga tsiyarki cinye dani kike
zancen,,,,ya turamata kwanon.da sauri ta maida
masa ta tarairayo shikamar na goye,tayi ta
rarrashinsa,sannan ya aminceda cin wainar.
Tarinqa bashi a baki,,ya taune qashin ya
batse.ita kuwa ko guda dayar bata ciba,bata ma
kokwatanta ci ba,don karya ransa ya baci.sai
dayagyatse,sannan ya gaya mata bibikon da
yake nanemanta...babu musu tabada kai bori ya
hau Haka rayuwar mama ta kasance tamkar
tadabbobi,,duk inda danliti ya kadata can
zatadosa.tsakaninta da Allah kafin maikudi ya
shekarabiyu ya zubda mata ciki sau uku kuma
kowanne babuwanda batasha wahalar
zubansaba.,,duk ta jeme tayiduhu fatar jikinta
yafara yaushi saboda wahala da ukuba.(Allah zai
i sarmata) ......tabbas hakane,tundamasu ganin
rashin jinta ne yajawo mata halin da takeciki
sunayi mata addu'a, mussamman abba kullum
yadaga hannu samu bashi da abun nema wajen
ubangijiface Allah ya dafa masa akan qaddarar
data sauqaaka sakeena,wanda hakan shi ke
hana yan uwanta zuwa fandogari...amma kannen
abba sukanxo abujasu dubashi.haka ya ali
musamman yake zuwa damatarsa su duba abba
su koma. Shekarunta qarashudewa suke tare da
qara dumulmulewar rayuwarmama cikin kunci da
talaucin dole...duk yansuturunsu sun mutu,ko da
yaushe busu busu zaka gansu,musamman
lokacin sanyi.babu manshafawa ,babu sabulun
wanka,balle na wanki,sau ukutana zuwa neman
taimako wajen inna tanahanata.tace muddin
bazata dawo cikin yan uwantatazaunaba,ko
kwandala bazata bataba......mama tagammace
hakan shiyasa ma tadaina zuwa.wani lokacin
tsirara zakaga mai kudi yana yawo sabodarashin
sutura.sai makwafta sunga Allah sunga
annabizasu kamashi su sanya masa kaya
sadaka,anya?kaicon wadanda imani yayi musu
karanci! BAYAN SHEKARU GOMA SHA BIYu.
Nasan maitausayi da imani zai daura hannu akai
yanakururuwa,idan yadubi halin da mama take
ciki dayaronta kai duniya!ina zaki damu?
shekarunta nahaihuwa talatin da biyu cif
cif.amma idan ka dubetazaka rantse da Allah ta
zarce hamsin.tsufa ya bayyana kuru kuru a
jikinta,badan takai shekaruntsufanba sai don
wahala. Sau da yawa tanayin rashinlafea babu
kulawar data dace,saboda zata kwantaciwo sai
ta kusa sati akwance kafin danliti yakaitaasibiti.
koya sayo mata magunguna.muddin kuwahakan
ya kasance to tabbaci idan ta warke sai ya
kirkiro mata laifin da bai taka kara ya
karyaba,don yajibgi kudinsa...a wasu lokuta idan
taje rokonsa ayubake tausaya mata ya dauka
cikin shagon yabata aranar kuwa zai bita gidan
ya narketa yandayaso,dataga hakan ba riba sai
ta fara neman wankaua makwafta tana samun
abincin da zasuci itada danta. A wannan hali
mai kudi yatashi yagamahaifiyarsa cikin ukuba
da azabar duka wajenbabansa,wanda shikansa
yagane randa yazogidan,sai yaga mahaifiyarsa
na kuka.tunyana matamaganar makaranta har
yadaina.ya fahimci cewabashida gatan xuwa
makaranta kamar sauran yara!!... Daka
dubeshi,kaga yaro mai kyau amma babugata.sai
dai abun mamaki a game dashi yana danitsuwa
kuma a koda yaushe yana taredamahaifiya
rsa.,musamman inyaga tana kuka,daya farakawo
qarfi sai yafara fita nema,shine yankan ciyawaya
siyar,shine neman kwalabe da fasassun robobi
da tsofaffun karafuna a bola,yana kaiwa inda
akesayarwa,ya siyar ya kawo mata kudin. A
haka tasamu da kudin datake wankau
tahada,tajajarin AWARa,tana rabin tiya tana
sayarwa a zaurengida.a haka take dan saya
musu kayan gwanjo masuarha.duk wannan halin
da mama take ciki gaba dayajama'a namata
kallon rashin biyayyar iyayece ta jawomata
hakan.shiyasa kalilan ke tausaya mata.itada
gidansu sai gani sai hange,,ko a hanya ba
dukkansuke magana da itaba,rayuwa tayiwa
mama tsauri dayawa,tsawon shekaru ashe dole
tayi tsufan qarfi dayaji........yamma tayi sosai
lokacin da mama kezaune gaban kaskon suyar
waranta a cikin zaure.yaranata shigowa suna
saye naira biyar biyar,goma ashirin,duk yanda
takama.muna iya cewa tanaciniki,don bata
tabayin kwantaiba.maikudi ya shigosabe da
buhun tarkacensa a kafada.kayan jikinsaduku
duku,kafa babu takalmi,ta cire kai cike da
fara'ata kallesa,yaro dan umma andawo?ya
zagaya gefentaya zauna.nadawo umma.tace
angaisheka.to kaje kayi wanka kayi sallah,akwai
dumamenka yananan atukunya,ka zubo kaci.yace
to ya mike ya sungumibuhun kayansa yashige
gida.yayi duk abunda taumurcesa.ya zubo
tuwunsa yadawo zauren gefentaya zauna. Ta
dubesa sai kaki ci saboda riba?kai nalura kafini
son kudi,,,,yayi yar dariya yace umma kenan
yanxu saboda Allah gabadaya ribar
nawakikesamu?tace mungode wa Allah ko nawa
ne,ammaai dole aci,dauki guda biyu to,yace
barin gama cintuwon tace gama idan kuma ta
qare ka huta. Ya sa hannu ya dauki guda biyu ya
ajiye a gefe,yaceban nuna miki ciwona ba,wani
tsohon kwano ya yankemin gefen kafa!ta kamo
qafar cikin sauri da tausayitace wayyo dan
umma,sannu,shiyasa na kosaingama tara maka
kudin takalma ka sayo,gamacintuwon inbaka
naira goma kasayo ja da yalo in rinqa barbada
maka yana saurin warkar da ciwosannu.....yace
to umma!sukayi shiru yanata cintuwonsa yana
gutsurar awaransa,jim kadan yaceumma wai ni
bani da wani suna ne sai mai kudi?tayidan
murmushi tace kana da shi mana...yace
aibantaba jin kin kirani bane,zura masa ido tayi
tace sunan kakanka gareka shisa bana kira
shima yabitada kallo yace kigayamin inji,gobe
idan munhadu daabokina in gayamasa,tace
sunanka adamu,ya sakibaki yana murmushi,yace
lalle ai sunan tsofi neamma inason sunan.tayi
yar dariya tace amma karkabari babanka yaji
yasan nafada maka dan baya so,yace saboda
me?bashi ya radamin ba?tace shineamma
saboda sunan babansa ne baiso ana kira.yatabe
baki yayi tsaki,yace bani kudin ja da
yalon,tamika masa naira goma yafita yana sude
hannu,tabishida kallo ta kada kai,domin ta
fahimci bayasonmaganar babansa,,,bai taba
yabonsa ba kuma bai damu da
al'amuransaba.bai dade ba yadawo
damaganin,ya zauna ya kakkabe kasar jikin
ciwon,yamika mata kafar tasanya masa garin
maganin.nansuka zauna sunata hirrasu har wara
ta qare,ya kwasomata kayayyakin yadawo mata
dasu gida,yayin da itake zaune tana qirga
kudin,gaba daya dari uku tayi ta ware uwar kudi
Ta ware uwar kudi,tasamu ribar naira tamanin,ta
cirenaira goma tabawa mai kudi tace jeka wurga
a cikinasusun takalminka,kayi sauri kayo mana
cefane danaira saba'in din,sannan ka auno min
wakensuya,rabin tiya mai gwangwani biyu....yace
to ya karbikudi yafice,itama ta mike ta ddebi
ruwa a bokiti ta dauki sabulunta yankan qusa,da
soso tayo wankatafito.injin oil dinta a yar
roba,,ta dauko ta shafa tacanxa tsumman
zaninta da wankakke, ta hada dawata kodaddiyar
t shirt,ta fito tashiga kicin ta doraruwan tuwo.
Sallamar mai kudi ta amsa ta leqo dagakofar
kicin din jirgi dan umma,shiyasa nake sonka
saboda babu wasa,,yana murmushi ya zube
matacefane,ta duba komai dai dai yasayo ya
laluba aljihuya ciro naira biyar ya miko mata ta
me ce ce?yacemai waken suyane yamin ragin
naira biyar,ta dafakansa,tace Allah sarki
mungode,amma kaima kajekasha minti,,,ya kada
kai,umma me zanyi da minti kamar qaramin
yaro......ta kece da dariya!iye lalle maikudi
angirma ko?to je kasha rake..yace umma ki
ajiyeko farin maggi kya saya ko kuma a xuba a
asusu...tazura masa ido tadan kada kai jeka tura
a asusun,,,yawuce taraka shi da kallo harya fito
tana tsaye batamotsaba mezan tayaki umma?
tace kaga ka zauna ka huta ai ka sha gararanba
dan umma,,,ya kamata kahuta,kaga rauni a
qafarka.yace to. Ya jawo tsohuwartabarma ya
kakkaba ya shimfida a kofar kicin
din,yakwanta.it a kuma tana ta hidimar mada
miyar kukakamar yadda yayo mata cefane,.
Bayan ta kammala,ta fito da robar gari
tanatankadewa tana fadin daga yau ma garin
tuwunmu yaqare,,,ya yunqura yatashi,yace ai
gara daya qare maumma.nagaji da cin tuwon
nan,ta dubeshi da kyautace yaro kenan!har ka
mance wata rana ma nemantuwon mike ido rufe?
bama samu?kadaina fadar haka komai Allah
yabaka kayi masa godiya sai ya qaramaka kaji
ko?yace naji umma amma kinsan waniabu?sai
ka fadi...yace in Allah yasa natara kudi dayawa
zanbaki mamaki.tana dariya tace aidamakasaba
bani mamaki yarona.....yace amma baki
tabaganin wannanba....kedai kiyimin addu'a
Allah yasa intara kaya da yawa,,,tace to Allah
yasa dan ummayace ameen..ya koma ya kwanta
yayi matashi dahannunsa.yana bata labari
tanashan dariya.ta qaregirkinta ana kiran
magrub..ta kwashe ta aje gefe gabadayansu
sukayi alwala sukayi salla,shiya dauko
musuabincin sukaci tare kamar yadda suka saba.
Bayan sallar isha'i ta koya masa karatun
alqurani kamaryadda suka saba haryakai
amma,mai kudi nason yinkrtu amma basu da
kudi shiyasa take koya masa dakanta.kullum
kafin su kwanta,,,musamman ranakunda
babansa bai xoba,,,shiyasa bayason
zuwansa.donyasan zuwansa baya haifar da
komai sai BAKIN CIKI .A Garesu Kwana uku
mama na ririta kudin da ke hannunta dankar dan
jarin da take taqama dashi ya qarye,,,gashidan
gogan yaqi waiwayarsu balle ya wurga masu
nairadarin datake samu tayi awo akai niqa,su
sami garintuwo....shikuma mai kudi yana can
kasuwa wajen yankyadi da tulin kayansa.. Daya
tara buhu buhu,,,kuma Allah da ikonsa wannan
karon yasamu manyan kayamusamman
karafa,aka auna kayansa sai gashi dakudi naira
dari bakwai da hamsin...kai farinciki kamarya
kasheshi,,,,nan da nan yafada
kasuwa.dafarkoshinkafa yasaya rabin tiya.......ya
wuce teburin mainama yasayi na dari da
hamsin,ya koma bangaren kayan miya aka hada
masa na naira dari,yabadamarkade,,,aka juye
masa aleda,,mai gwangwani biyuda maggi mai
tauraro dda fari,ya koma ya nemi wajeya nutsu
ya qirga ragowar kudinsa naira dari dasaba'in
yanade abinsa yamaida aljihu ya
kwasocefanensa ya dawo gida. Mama tasaki baki
tana kallonsa da ledodi,,,ina kasamo kaya haka?
yacedama nagaya miki zanbaki mamaki,kayan
da na tarane...ta bude ledodi tana fadin iye!
yanxu kayan nanharsun kai haka?yace naira dari
bakwai dahamsinfa...kinga harda canjin dari da
saba'in nakawomiki ki qara jari,,,,ta saki baki
tana kallonsa ya miko mata kudin,,,ta amsa
kina ta kallona umma ko bankyautabane?ta
janyo shi jikinta da sauri tace a'a
danumma..gani nayi ka kwashe kudinka ka
kashe,bakasayo wa kanka komaiba,,,,ai da
kasayo kodatakalmine,kaga wancan asusun sai
kaci gaba da zubamasa abunda yasamu
kawai.........yace babu komai umma,nima so
nake muci dadi yau,,rabonmu fa dashinkafa tun
na sunan maman fati kullum tuwo mukeci,,aiya
kamata mu canza,tunda nayi dabara
nasamukudin. Tayi dariya tana mamakin mai
kudi,,,,sannan tanumfasa,,gaskiyane,Allah yayi
maka albarka.ammaduk da haka kadauki saba'in
da biyr kasayosilifas,inyaso daga baya sai
kasayo dan dari biyu dahamsin din,,,yace umma
kibar maganan takalminnan,yanxu kawo talatin
nasayo itace,tace to tamiqa masa to maza kaje
ka dawo kayi wanka ko?yace toumma.ya fice
tana fadin haba ni inacan inata tunaninbanga
dan ummaba ashe yanacan yana kashe
managara.Allah sarki mai kudina!ta kwashe
kaya ta nufikicin ta hura wuta ta daura shinkafa
da sauranitacen,,,,yana kawo mata itacen tahadi
wani murhun,,,ta kama hidimar miya.shikuma
mai kudi yayiwanka ya sauya kaya ya fito ya
shimfida tabarma yazauna .ta miqa masa warar
data aje masa gudabiyu,ya karba yanaci suna
hira abinsu. Kafin kiranmagruba ,gida ya
hautsine da qamshin dage dage gashinkafa a
gefe,,,,,tuni ta sauketa gwangwani uku ta dafa ta
wadace su sosai .kawai tsayuwar mota sukajia
qofar gida,mai kudi yayi wuf
yatashizaune,,,gabansa ya yanke ya fadi,mama
da sauri taleko tace kamar tsayuwar motar
babanka?ya qaradaure fuska,,shine man..to
menene na bata rai?yayiwuf ya mike ya dauki
buta yafada bayi. Ku sakani a addua zan fara
exam, tnx.
BAKIN CIKI 3****3 Ta bishi da kallo tana kada
kai,,,,babu sallama yashigo.bakinta har
kunne..sannu da zuwa!ya kalletasama da qasa
hannaye cikin aljihu,yace tundagazaure nakejin
qamshi,na makwafta ne?ko a nangidan???ta
matso shi sosai ganin ba fara'a a fuskarsatace
wlh mai kudi ne yasayar da kayansa yayi mana
cefane harda nama,shiga ciki barin zubo
maka....yawatso mata idanuwa mai kudi?karki
mai dani wanisakarai mana.kinfara iskanci kina
samo kudi ko?dasauri ta katse shi,,iskanci dan
liti?ya daka matatsawa,rufe min baki ko in
farfasa miki kai,,,banxakawai ina magana kina
so ki qaryatani..ya wuce kicin din a fusace yaje
ya duba,,banda ke yar rainin hankalice mai kudi
ne zai samo miki kudin uban wannancefane?ina
mai kudin?ta durkusa gabansa ido tafhawaye
tace na rantse da Allah danliti bangaya
makaqaryaba,,anan yayi ta tara kayansa buhu
buhu ya fitadasu ya....ya isa haka don Allah!
mtss yaja tsaki ya wuceta tsugune. Tsakar gida
yatsaya yana dagamurya ina mai kudin?cikin
sanda yafito daga bayin,daganinsa dama can
kuka yakeyi,,,zonan danuwarka.ya matso
gabansa yana kokarin tsugunawayasa hannu ya
murde masa kunne miqe tsaye daniska!gidan
ubanwa kasamu kudin wannan cefanen? yayi
banxa dashi BAKIN CIKI ya hanasa
badaamsa...... Kafara sata ko?to saurareni
dakyau,,,duk ranarda aka kamakakayi sata daga
kai har uwartakamai goya maka baya karku
kuskurakuce kunsanni! kajiko?bai tankaba.illa
hawayensa da suka qaratsinkewa bace min
dagani shegebarawo yaruga bayan kicin
yatsuguna yana kuka,mama na tsayeta rasa nayi
itama hawayentakeyi,,,,yaja dogon tsaki ya
wucedaki.dole ta biyoshi badan rantayasoba sai
dan sanin batada yancinrarrashin danta
agabandanliti...........yana zaune gefenkatifa
tazauna a hankali tace kabanmamaki danliti
daka mancezamanka nakeyi a cikin
gidannan,,,,ya daga mata hannu bansonjin komai
dan Allah.tace to nazubomaka abincin?yace
kema kinsan baabincinku naxo ciba..tadannumf
asa kanta sunkuye gwanin bantausayi.....
...ankusa idar da sallarmagruba taje kicin ta
debo masaabinci cikin langa da nama
yakaiyanka hudu,,,,,,ta hado masa dakofin ruwa
ta ajiye agabansa.yanaci yana danqara
matamaganganu! bai kammala ba maikudi
yashigo gidan,,,waye yakemana sanda?ya amsa
da kyarnine,,to miye kakeyi wa mutanesanda?
yace ba sanda nakeyibamasallaci nadawo!yace
sannu dazuwa liman,ya koma can jikin kicinyayi
zamansa.ya qare cin abincinsannan ya dubeta
baki buqatarkomai tunda danki nakawo miki.
Kafin tace wani abu,ya miqe yanashirin barin
dakin,ta biyoshi tanahaba danliti!kwana nawa
rabondaka waiwayomu?kuma wannan
yarshinkafa kwana nawa zata mana?idocikin ido
yace bafa dolenabane,,,,ni ba mijinkiba ni
baubankibane,ko ban fadaba?.........tayi shiru
dan bataso ta qara waniabu dazai jawo mata
duka,,,sabodahaka ta kyaleshi,,,yasa kai ya
ficebai ko kalli inda mai kudiyakeba.....ta jima
tsaye tsakar dakisannan ta fito ta tsugunna
gabanmaikudi tadafa kansa kayi haquridan
umma!yace wai umma meyasakika auri wannan
mutumin?cikinfada take masa magana karka
sakemin wannan tambayar idan kanasomu shirya
dakai cikin gidan nan.yagoge kwalla da bayan
hannu kiyihaquri umma,dole nagayaa mikigaskia
natsani wannan mutuminnatsane sa.shiyasa
danayi sallahyanxu na roqi Allah ya kasheni
danbanaso na girma dashi. Ta xuramasa ido na
tsawon lokaci habadan umma karka daga min
hankalimana meyayi zafi?yace umma dukabunda
baba yake miki ina kallokuma inajin zafi,mesa
zaice minbarawo?bayan ni banasata...umma da
baba yayi minbaki inzama barawo gara na
mutuAllah! tace bazaka mutu ba danumma kuma
da yardar Allahbazaka zamo barawo ba.kai
yarone shisa kake gani babanka ya
cikafada.amma idanka girma zaka ganesauqin
kai gareshi.baka ganin harabinci na xuba masa
yaci?to aialbarka yasa maka.saboda haka
kakwantar da hankalinka komai zaiwuce da
yardar Allah kajiko?bariinyi salla inxo muci
abincinmu. Ta share masa hawaye ta tashitayo
wanka tadauro alwala tayisalla,lokacin ana kiran
isha'i,,,,donhaka tadaura gaba
daya,,,,shikuwamai kudi yanajin kiran
masallaciyatafi bayan ya dawo suka zaunacin
abincinsu.tanata lallashinsakafin tasamu
hankalinsa ya kwantatadaura masa karatu
sukakwanta......yau kwanansa hudu cifdayin
rauni a qafarsa yana tafeyana yawon neman
robobi dakwalabe amma bayajin
dadinjikinsa....wani irin sanyi yakeji gazazzabi
na neman kamashi hakayaketa yawo bashi
wannan bolabashi wancan,,,,,,har aka
kiraazahar,ya nufi wani masallaci danyin
sallah.ana idarwa yafito yadaukibuhun kayansa
yaci gaba,,,la'asart ayi,,,yanajin qira bai bata
lokaciba ya nufi masallaci,,yabada faraliAllah
kenan yaro qarami sai kaifinhankali shiyasa
yake bawa mutanemamaki harba mai iya daga
kaiyayi masa gori. Yana fitowamasallaci gida
yadawo sabodazazzabin qaruwa
yakeyi,,,mamanata yanka wara tana sawa a
cikinruwan gishiri.....yayi sallamayashigo tana
amsawa yau da wurihaka dan umma?ya jingina
buhunkayansa yadawo kusa da ita yazauna.yace
zazzabi nakejiumma..da sauri tajawo shi
jikintata cusa hannunta kasan wuyansataji zafi
rau..wai wai aikuwa gajikinka yayi zafi maikudi
meyasatuntuni baka dawoba? yace inatunanin
dan abunda zan samomana ne umma,,,kinga
bamudaabinci Ta rungumeshi,sosai ya
kwantajikinta,tace Allah sarki yaronakomai ai
sai da lafiya.bari inyisauri inje chemist insamo
makaparacetamol kasha....kwanta nan
kajirani.ta miqe tadauki naira ashirinta yafa
mayafi ta wuce.........ka fintadawo ya qarasa
yanka mata wararyazuba cikin ruwan
gishiri,,,,tazura masa ido maimakon kakwanta
mai kudi kaji zafin jikinkakuwa?yace natayaki
ne umma kobaki so?tace inaso Allah
yamakaalbartka ungo maganin barin debomaka
ruwa kasha guda biyu. Tadebo masa ruwa yasha
maganin tamatsa masa ya kwanta adaki,,,,amma
dayaso yafitar matada kayan suya zaure ya hura
matawuta....ai kuwa yana kwanciyabacci ya
kwasheshi.harta gama baifarka ba,tazo ta taba
jikinsa zafirau.hankalinta ya tashi kwarai
dagaske ta zura masa ido sannan taqirga kudin
dake gabanta,,,,kawaiabinda yazo ranta shine
takaishichemist a hada masa maganinmaleriya
.haka kuwa akayi baifarkaba sai da aka kira
magrub.kaitsaye alwala yayi yakama
hanyazaifice,ina zaka mai kudi?yacemasallaci
mana umma!tace kayi agida tunda bakajin
dadi.....yacenafiso inje masallaci umma
taceadawo lafiya,yawuce yanaamin.yana dawowa
tariqehannunsa har chemist aka hadamasa
maganin maleriya takashedari uku suka
dawo,,,takawo masasauran tuwon datayi da
ranasukaci,,,,tabashi magugunayasha,,,yana
sallar isha'i wanibaccin yasake kamasa. Cikin
dare taji yana ta rawansanyi,,ko ina jikinsa
rawayake,takwaso duk tsummanzannuwanta ta
rufa masa.amma abanxa haka suka kwana
zaunekamar bazaiyi raiba...hankalinmama
yatashi kwarai ganin yaumaikudi ko sallah
yakasa tashiyayi.don haka tana sallame sallahta
figi gyale sai shagon danliti.Ayuba ke alwala
kofar shagon bisabenci..ya dubeta afujajan
kwalla tafidanta yace lafea sakeena?tacemaikudi
baida lafiya ayuba jiyabamuyi bacci ba.danliti
yananan? yace yananan baima
tashiba.......tawuce ciki tuni hawayenta sukafara
zuba tausayi yakama ayubadomin ya hango
matawalakanci,,,,danliti na bacci zatatashe shi?
haka kawai ma ya akaqare? ya kada kai
yarasanayi,,,,yana kwance dai dai akankatifa ta
tsugunna ta tanbubbugashi.ya bude ido
yamutseya zuba mata ido baitankaba....hakan
yabata damarfadin abunda ke tafe da ita.
Maikudi babu lafiya kamar zai mutudanliti don
Allah kazo ka taimakaakaishi asibiti.....nakaishi
kemisanbashi magunguna amma baiyibako
barci......ke ya isheni haka!haba!ke sakaryar
inace wai?tukunama banhanaki zuwa shagon
nanba?kin raina ni koh?har ina bacci
kizokitashen...nina samasa ciwon?iye?ina
tambayarki? Da gudu hawayenta ke kwarara!
takada kai murya na rawa tacebakaga halin
dayake ciki banedanliti.don girman Allah
kataimakaka kaishi asibiti..wallahi
sukenankudadena duk na tattara na
kaishichemist Idanuwa sunkafe,,,,,ta yada
mayafita doka salati ta tarairayoshi...tanakira
amma ya gagaretadagawa,,saboda duk
gabobinsa sunmimmike ta koma kicin
takandamo ruwa tazo tana shafamasa bakinta na
fadin nashiga ukuyau me zangani me kudi?
Hawayenta yaci gabada kwararatsawon lokaci
batare datasanadadinsaba kawai hango rana
tayiyafito ba danliti ba alamansa.tafitokofar daki
idanuwanta duk sunkumbure tarasa yanda zatayi
taceto rayuar danta mai tsananintausayi
nta....batasan lokacin datafada gidan maman
fati ba. afiya maman maikudi?ta durqusaa
gabanta baki na rawa kitaimakenimaman
fati,,,,mai kudi zai mutu!maikudi zaimutu
maman fati!meyasameshi? daga zazzabi sai
sumayakeyi....kitaimakeni da kudiinkaishi asibiti
inmundawo zantayimiki wanki har kudinki
yaqare....dan Allah kitaimakenimama n fati. Naje
nagayawa babansa yaqizuwa....tausayi yakamata
tanumfasa tace nima maigidan bayagari ne
maman maikudi.ammabarin dubo miki
abundayasamu.tashiga daki tafito mata dakudi
yan dari bibbiyu. Ta mikamata ungo nan dubu
daya cekawai!nasan bazasu ishekiba ammakiyi
kudin mota xuwa kagara sai kinemi taimako.idan
kuma babannasa yaga dama yajeshikenan.Allah
ya sauwaka. Takoma dakin tasameshi
yanananyanda tabarshi...ta sake baxamatasha
neman mota suka tsadanceakan dari takwas dan
sun tausayamata....tadauko mai motar harkofar
gida....sannan tace yashigoyataimaka mata da
maralafiyar...yayi sallama yashigodakin.me
direba zaigani?dafara ngangara gefen bakin
maikudi dasauri ya tabashi ya jujjuya ya
dubimama dake tsaye idanu waje. Yace
uwargida,ai ina ganin yaronnan babushi!ta qara
zaro ido tanafadin a'a malam babu
ruwankadashi...kasanya minshi a motakawai
tunda nace biyankazanyi....yace uwargida haquri
fazakiyi ko kinje asibiti wahalar kawaizakisha
dole kidawo dashi,,,dominbabu abunda zasu iya
masa...kiyihaquri kawai Allah yajikiansa.yasakai
yafice cikin alhiniyaja motansa yakoma tasha.
Mama ta zubawa mai kudiido..ahankali ta zube
gabansa takamo hannayensa taci
gabadakallonsa hawaye na zuba
kamarfamfo..shikenan anyi angama?dagazazzabi
kwana daya?haka zuciyartataketa wasi
wasi.haqiqanin gaskiyakuwa ciwon maikudi tun
ranardayaji rauni a bola tetanus
yashigeshi.rashin kulawa kuma yakaishi garasa
ransa..kokuma mucekwanansa ya qare ya huta
dagwagwarmaya. Tamkar a mafarki mama ke
ganinabun,,,shiyasa take zaune bataredatasan
meya dace tayiba.kawaimurya taji bisa
kanta.kitaso mutafiasibitin in ajiyeku sauri
nakeyiinada wurin zuwa.!taciree kai tadubeshi
ido yayi jawur wasuhawayen suka qara tsunkowa
bakina rawa tace yamutu...yacebangane ya
mutuba? Mama ta zubawa mai kudi
ido..ahankali ta zubegabansa ta kamo
hannayensa taci gabada kallonsahawaye na zuba
kamar famfo..shikenan anyiangama?daga
zazzabi kwana daya?haka zuciyartataketa wasi
wasi.haqiqanin gaskiya kuwa ciwonmaikudi tun
ranarda yaji rauni a bola tetanus yashige
shi.rashin kulawa kuma yakaishi ga
rasaransa..kokuma muce kwanansa ya qare ya
huta dagwagwarmaya.Kan dole ta tsagaita da
kukanta...amma hawayentayaqi yanke.jimawa
kadan ayuba yazo tare da abokandanliti mutum
hudu,,,,daya daga cikinsune ma yatahoda
likkafani.ayuba yayi masa wanka...ya kintsa
shisuka nadoshi a tabarma sika fito
dashi.kowannensuyayi alwala suka sallaceshi
tare da tsirarun mutane masu wucewa, Sannan
suka tafi kaishi suna bada baya maman fatita
shigo tasami mama tana ta kuka.tazauna
tayitararrashinta harta sami yar nutsuwa.ta
dauko kudinmaman fati tabata tace nabarmiki
mama.nidai fatanakokuma ince roqona gareki
shine Allah yasa kiganewannan zama bayida
wata fa'ida ga dan musulmi. Tausayi rayuwarki
kebani,,,saboda duk wanda yahaihu baikamata
yazauna yana aibanta waniba.donyaganshi a
wani hali marar kyau.don Allah kirinqa yinaddu'a
kina rokon Allah ya kore miki wannanshaidanin
daya dabai bayeki miki ziciyarki.saifa kindage
kin yaqi zuciyarki sannan Allah zai taimakeki
kinji? kiyi haquri ni zankoma Allah
yajikansa.....tashare kwalla tace ameen ngd
maman fati kumaazanyi addu'a kamar yadda
kikace..tace toshikenan.ta taso tabaro gidan cike
da tausayinta Suna dawowa maqabarta shago
kawai ya wucedasu.yan rakiya kowa ya kama
gabansa..ayubayazauna yanata juyayin mutuwan
maikudi.shikuwagogan cikin shago yashige ya
kwanta.baza ace gaabinda yake tinani ba.domin
zuciyar danliti sai Allahkawai.ita kuwa mama
zaune take idanuwanta na kallon sama,,,hawaye
nata sauqa bisakuncinta.maganganun mai kudi
ke yawo cikinranta.kiyi hauri umma"!yazama
dole ingayamikigaskia!natsani mutumin nan na
tsanesa umma!shiyasa danayi salla yanxu na
roqi Allah ya kashenidan banso na girma tare
dashi.Tayada kai bisa filo tagoce da
kuka,,meyasa ka rokimutuwa maikudi?tayi
kukan daya isheta babu mairarrashinta har akayi
kiran azhar.sannan ta fito kantasosai yake ciwo
haka kuma batajin yunwarcikinta.dukda cewar
rabonta da abinci tunjiya.ta zubaruwaa abuta
tashiga bayi tadawo tazauna tana alwala.karaf!
idanunta suka sauqa akan buhuntarkacen
maikudi.buhun yananan inda ya
jingineshi.tazubawa wajen ido tana kallon
shigowansa da dukkanabunda yamata jiyan kafin
yakwanta.nantake kukantayadawo sabo tana
alwala tanayi.tashiga sallahhawaye na zuba
harta qare.karo na farko da Allah yafara bata
ikon daga hannu tayi addu'a.Allah
kajiqanadamu!Allah kasanyamin haquri da
dangana!Allah kakoremin sheidanin daya
dabaibaye zuciyata!Allah kataimakeni!tasauqe
hannu tana goge kwalla takomagefen katifa ta
zauna
BAKIN CIKI 3***4 Kun jini shuru ko wlh sub dina
ne yayi expired da kuma exam da nakeyi kuyi
hakuri Zamanta keda wuya almajirin maman
fatee yayisallama...yashigo dauke da kwano a
hannunsa..bayanyayi mata gaisuwa yace wai
gashi inji mamanfati.tafito ta dauko kwano a
kicin ta juye dafadukanshinkafa da manja da
bushassen kifi.kace matangd.yafice yana fadin
to.tajima bata iya cin abincin ba daga baya ta
daure ta tuttura badan yamata dadinciba.haka
takasance cikin kadaici da kewar dantakwana
uku batare da danliti ya
waiwayetaba...saimaman fati ke aiko mata
abinci sau biyuarana..shiyasa dubu dayanta bata
tababa.waniabunda ke qara mata qarfin zuciya
shine tun mutuwar maikudi takoyi addu'a.kuma
bakinta ke maimatakalaman maman fatee Allah
ya kore shedanin dayakecikin zuciyarta, Ita kanta
batasan lokacin da kalamin
kezuwabakintaba.fadi kawai takeyi.amma duk da
hakamutuwar maikudi yadasa mata ciwo
acikinzuciyarta.wanda yake hana mata duk wani
kuzari naaikata wasu aikace aikace kamar
yaddatasaba.kullum zaune take shiru.a cikin
wannan yanayin danliti ya risketa.yau kwana
hudu darasuwar.ta zuba masa ido bata tankaba
haryaja yarkujera ya zauna.haka shima yayita
kallonta kafin yajadogon tsaki.yace ke!bakiga
shigowata bane?tadubeshi ido cikin ido tace me
kakeso incemaka? Yace gaskiyane,,,da alama
haushi kikeji dankiyamutu.to ai bani na
kashekiba.ta kalleshi koba kaibane kaine
sila..yace saboda kinkirani banxo akanlokaciba?
aiba tsoronki nakejiba.tace nidama bancekaji
tsoronaba kadai ji tsoron Allah.kasani duk
abundayasamemu nida maikudi alhaki nakanka
donkai ka ajiyemu. Yadaga mata hannu tare da
tsawa.tsaya anan!yadanjima yana kallonta kafin
yace da alama wuyanki yaisa yanka.toki tsaya
anan tunkafin in hassala inhadamiki zafi
biyu.dan zan iya farfasa bakinki.sannankibar
gidannan yanxu domin dai bana uban
dawakibane,,na buxu mai shayine.kuma axatona
bakida gadonsa ko kina dashi?tayi shiru tana
kallonsa.yacigabada fadin duk ranarda kika sake
gayamin maganamakamanciyar wannan,zaki
fuskanci tashin hankalinda harki mutu baxaki
mantaba.ya miqe a fusaceyadaga kujerar dayake
kai ya makata da qasa takarairaye.ya dubeta ido
waje yace sakamakonki daya da wannan kujerar
duk ranar da bakinki yayi gigingayamin maganar
banxa.yasa kai yafice tamatsekwalla tarasa
abinda ke mata dadi,Kullum kuma a rashin jin
dadin take tsawon lokacisati uku itake ciyar da
kanta.domin dai danliti yaqiwaiwayarta,,tun
wancan xuwanda yayi.yankudinhannunta gaba
daya sunqare.saboda warar matadaina.tun
rasuwar maikudi kuzarinta ya qare.yaukam tura
takai bango rabon mama da abinci tundan saura
dumamen taliyar hausar jiya da daddare
.la'asarta wuce sosai lokacin tafito baki
bususu.dun rabontada wanka kwana biyu
kenan.balle wanki tayo alwalaamma sallah ta
gagareta a tsare jiri ke dibarta.daalama bayan
yunwa dayake damunta akwai rashinlafea a tare
da ita.da kyar ta idar da sallah ta raarafa katifa
takwanta.bata jimaba baccin wuya
yakwasheta..jitayi ana bubbugata tayi firgititi ta
tashitabishi da kallo.yana zaune kusa da ita ta
tashi tazauna jikin bango.taja doguwar hamma
hartanakwalla,,sannan tasake kallonsa sannu da
xuwa!yacekema sannu kinajin dadinki la'asar
sakaliya kina bacci to gani naxo. Tadubeshi da
kyau tace yinme?baki sake yakekallonsa kafin
yace kinfi kowa sani .takauda kai shirubata
tankaba,karki batamin lokaci inada
wajenxuwa.takada kai fuska yamutse batare data
kallesabagaskia banda lafiya.danliti kuma yunwa
nakeji.rabonada abinci tunjiya. Ya mako mata
harara me kike nufi? tayi shiru...ya numfasa
yace hu'un!lalle nayi sake dayawa ba laifinki
bane.tadago ido takalleshi wannanmatsalark
ace.Ita kanta batasan lokacin da kalmar
tafitobakintaba..saida gabansa yafadi ya qara
zaro idoyace mene?me kikace?ta sunkuyar dakai
tayi shiruhawayenta suka fara zuba.yasa hannu
yazaretakalminsa ya lafta mata aka.yadaka mata
tsawa mekikace?nikike gayawa wannan
maganar?yasake lafta mata..iye? To saurareni
kiji kinshiga uku kinlalace...zaki ci gaba da
dandanan axaba a gidannan.tabbas zan nuna
miki nidan gidan buxu mai shayine,,,,kwarton
nan daya mutu wajen kwartanci.kinmance ko
haryanxu tarihin yananan cikin xuciyarki?
(kalman da ya jefa mama cikin halin datake ciki
kenan inbaku mantaba)taci gaba da kuka bata
tankamasaba, Yasa takalmin ya dago
habarta,,sakeena kenan maikyau yar asali jikar
asali!yanxu ina asalin da gatanyake?dalili daya
yasa nake rangwanta miki sabodakina gamsar
dani yayi dan murmushi.yakada kaizandawo
anjima zankawo miki abunda xakici kitabbatar
da kinyi wanka dan wari kawai kike kinji?ta zuba
masa ido bata tankaba ya marmari kumatuntada
takalmin yasake fadin kiyi wankafa!kinsan
bansonhamami.(dan iska).ya mike ya xura
takalminsa zaifice.. Tabishi da kallo DANLITI ya
tsaya cak.kafin yajuyoya zuba mata ido.ta goge
kwalla murya na rawa tacenaji duk abunda
kace,,,amma ina rokon Allah idanxaman da muke
banida haqqinka ubangiji Allah yayimin sakayya!
ya matso ya wanketa da mari yanunatada yasta
nikikewa Allah ya isa?gaskia ne tabbas ba
laifinki bane,amma xangyara.yasa kai a fusace
yabargidan.mama na xuba kuka abun tausayi.a
fusace yaisa shago ya nemi wuri kawai ya zauna
yana hucikamar mesa, Ayuba ya xura masa ido
tsawon lokaci kafin yacelafiya?ya kada kai ido
jawir inafa lafiya...ni sakeenakewa Allah ya isa?
lalle nayi sakaci ba kadanba.wanidadi ya ratsa
zuciyar ayuba cikeda fara'a yace kayisakaci? Ko
kuma tafiya ce tayi tafiya?ko kanatsammanin
har abada zaluncika zai dore?towlh ka farka
barci kasan yanayin da kake ciki.ko
kasanwaccan juma'ar danaje masallaci akan
zalunci darashin adalci liman yayi huduba.Anan
naji cewa addu'ar wanda aka zalunta
tamkaryankan wuqa take.kuma batada hijabi
daubangiji.anayinta kai tsaye Allah zai
amsa.sabodahaka ka kiyaye danliti.kasani
shekarunmu sunyinisa.gaba dayanmu yakamata
ace munadaiyali.amma muna zaune cikin
shagoana mana kallon yan iska..ya watso masa
harara yaja dogon tsaki.kaiwannan yadama.Allah
ya isan sakena bai isa yaminkomaiba.kuma kasa
ido kayi kallo aure kuma ninahanakayi?ni banda
ra'yi inkanadashi ga hanya kajekayi man... Yace
baka hananiba.amma bakin halinmu ya
hanaabani.kana gani har kauyuka bansamuba
sabodakowa kanyabada yarsa zaiyi
binciki.danliti yaja tsakikaikaso amaka binciken
ni dan uban mutum inya isayaxo yamin maganar
banxa.yagani idan banyimaganinsaba dagashi
har diyarsa.kuma a zatonka sakeena taci banxa
ne? wlh bataciba munanan mutukaraba takalmin
kaxa.kahada min lissafi kafabundake hannu
zanyi tafiya gobe. Yaja tsaki yatashiyashige
dakin baccinsu, Mama kuwa na shimfide gafda
magruba. Almajirinmaman fati yshigo da kwanon
sameera yace injimaman fatin.ta bude kwanon
shaqe yake da tuwonmasara miyann
ayayo.jikinta na rawa ta tashi tajuye.ta wanke
mata kwanon tabashi tanata zubagodiya.tanemi
roba tayanki tuwon ta adana sauran. Ta zauna ta
cinye tas.tasha ruwa.zufa yaketo mata
tayigodiya ga Allah.abincin ya tsirga mata ta
tashi tayisallah.tajira isha'i tayi tarufe ko ina ta
kwanta.tunaninmaikudi ya lullube zuciyarta,,,,ba
tasan lokacin dabacci ya sace taba.dasafe
ragowar tuwon ta dumam,ataci tafito ta nufi
neman wankau gun maman fati. Shikuwa danliti
a wannan lokacin yadade da
barinfandogari.ayuba keta hada hadar shagon
kamar yaddayasaba.amma zuciyarsa na cike da
mamakin danlitiyadda yakasayin nadamar
abubuwan dayakeaikatawa.kuma yana mamakin
yanda yakasa rabuuwadashi.alhalin yasan cewa
halin abokinsa bamai kyaubane.karfe daya da
rabi dai dai wata daf tayiparking bakin titi
danliti yafito daga cikinta da alamaragajiye
yake.saida ya matso kusa
akaganefuskarsa.dukta kumbure.musamman
gefen bakinsadana idonsa..mai mota yaja yayi
gabaabunsa.shikuma ya qaraso shago yana
dingishi, Ayuba a tsorace yake tambaya lafiya
danliti?baiamsaba harsai da yakwanta akan
katifa.yace wlhyanfashi saida naxo daidai
buruku.na iske suntarehanya.in gayamaka
dagani sai yar wannan wayan natsira sunkwace
mai tsadar.ido waje yace kana nufinsun kwace
har motar?yace bar maganan ayuba nikaina
bakaga yadda suka maida niba?ai mutanennan
yan iskane mutum da kayansa..amma suyitaduka
kamar Allah ne ya aikosu...Ayuba ya numfasa
yace ai amma gode tunda basuharbekaba basu
da imani..sannu!ya nxu me za'a sayomaka
kasha?yace barin huta sai inje
kemisdakaina.yakwanta a hankali yana fadin
wash.ayubayadawo cikin shaghon ya qaleshi
harbacciyadaukeshi.akwai alamar tambaya
acikin wannan lamari.danliti dazai gane daya
saduda...ammakash.bazai ganeba.shikadai
yaketa saqe saqensacikin ransa.shikuwa danliti
cikin baccinsa yayi mafarkisuna ganawa da
bokansa.shiyasa bayan la'asar yanafarkawa
yakirasa yana shaida masa abundayafaru.sh
ikuma yabashi tabbacin ya kwantar da
hankalinsa za'aga motar.sakeena kuwa har
abadaragamar rayuwarta na hannunsa. Hankalin
danliti yakwanta yaci gabada jinya yanashan
magungunandaya amso a chemist,,,haka
kumabai waiwayi mamaba.danta masalaifi saita
kurxu da yunwatukuna.ganinsa dan abunda
yakebata shitaketa ci kodayake yasantanashan
wahala sosai.sati biyubabu mota ba
labarinta.sabodahaka ya qulla a ransa gobe ya
tafiwajen bokansa suyi magana gabada gaba.a
wannan daren sunkwanta babu wutan nepa. Can
cikindare nefa suka kawo wuta maiqarfin
gaske.ba hawa ba sauqakawai shagon danliti
yakama dawuta.da kyar sukasha
shidaayuba.kowannensu dagashi saikayan
jikinsa sai yar wayardanlitidake cikin
aljihunrigarsa. itama rabon zaifita daitane.yasa
yamanta bai cireba Sunata kururuwa wuta!duk
jama'asukayo waje.amma duk iyakokarinsu basu
iya kashewutanba.sai da ta cinye tas koallura
bata bariba.danliti kamarzaiyi hauka.gaba daya
ya gigiceyanata zuba sambatu har gari
yawaye.kofar shagon yacika dankamda jama'a
anata musu jaje,,,dadama na tambaya yaushema
akayimasa fashi?mutane na hasashenhalin
danliti ne.ba mamaki danmasifa ta afka
masa.domin damaabunda mutum yashuka
shizaigirba.komai daren dadewa kuwa Suna
zaune jugum danliti yayi baqikamar bashine dan
kwalisan nanba.mama ta iso wajen fuskasharkaf
da hawaye.tayi tsaye tanakallon yadda wuta ya
cinyeshagon..tace nashiga uku danlitigarin yaya
wannan abu yafaruhaka?ya kauda kai
baitankaba.ayuba ne yabataamsa.Allah ne kadai
yasani mudaimuna bacci mukaji
numfashinmubaya fita imgaya mudai
munbudeido ne munga wuta takoina.sannan
kwananmu kegababamuda rabon wahala shisa
mukafito Taci gaba da tafa hannu
tanasalallami.kafin tace nima inanasani?kawai
yanxu nashigamakwafta neman wanki
shinesukemin jaje.wai ashe abundayafaru kenan?
ni wlh cewa ma naketun maganan fashin nan
ne....dasauri danliti yadaka mata tsawa danAllah
malama kiwa mutaneshiru...bamu san surutu.ta
zubamasa ido tace Allah baka
haquridanliti.ayuba sai anjima.Allah yamayar da
alheri. Yace ameen.tajuya zata tafi danliti yace
dama kikwashe komatsanki kibarmin gidanima
ciki zandawo. Tadawo ta tsaya cak,,,ta
xubamasa ido a marairaice tace inakakeso naje
danliti?yace kekikasani wannan ba
damuwatabane,,,kawai abunda nasani
inasondaganan xuwa dare kibarmingidana.ta
goce da kuka ta dubiayuba ina yakeso inje
ayuba?donAllah ka rokeshi ya rufamin
asiri.Bansan inda zaniba ayuba....yaceko ma
gidan babu komai zanyi masamagana.ta goge
kwalla ta wuceabun tausayi danliti
yahadafuska.duk irin maganganun dadanliti yake
masa babu wadda yayarda da ita..shiyasa ma
baitankaba.abinda ya ajewa ransa yaukomai
dare sai tabar masa gida Saboda haka yaci gaba
dabilayinsa,,,bashi kasan wancanbishiya,bashi
kofar shagonmutane.sudin nema masu sayamusu
abinci suci tare.abin duniyaya jagulewa
danliti.BAKIN CIKIKamar ya kashesa.idan ya
dubishagonsa.ya tuna dukiyar dakeciki,zuwa
la'asar yaga bazai iyajurewa ba shagon
okundiri.yajeyaci bashin kati yasawa
wayansayakoma gefe ya kirabokansa.yasanar
dashi abunda kefaruwa.sunjima suna adawo ya
zauna shiru.a qasanwata bishiya.ayuba yafito
dagamasallaci yace danliti kaje kayisallah kaga
ko asuba bakayiba.yaceina kai kayi?yace nayi
mana yace toAllah ya karba.yace kana
nufinbazakayiba kenan?fuska yamutse yaamsa
dan Allah ka kyaleni ayuba kakyaleni najida
abunda nakeji.ayubaya numfasa na kyaleka
tundabakason gaskia.yaja tsaki ya tashiyabar
wajen. Karfe takwassuka tafi gidan dan basuda
wajenzuwa daya wuce candin.mama nazaune a
tsakar gida tana tunaninidan danliti ya koreta
ina zata?sallamar ayuba tamaidata
cikinhankalinta.tayi wuf tamiqe
tanaamsaw.inafata kinhada komatsanki?ayuba
ya cafe haba danliti asheduk maganar dana
maka bakajibakoh?ina kakeso taje adaran nan?
yace bansaniba.duk inda taga damataje gida
sayar dashi zanyi. Insakebude wani shagon.ko
kuwa inadakadara sai inxauna haka saboda
gashafaffiya da mai tana zaune agida?to bazai
yiwuba!maza kamahanya kisan nayi a durkusa
amma kafin tayimagana ayuba ya rigata
kayiwagirman Allah ka kyaleta zuwa gobenida
kaina zan nema mata wajenzama ko kuma ka
bata izini takoma gidan iyayenta,,yace
ninahanata zama gidansu?yace kainemana
aikasan yanda zakayi takomagidansu......ya
katseshi ya ishekahaka ayuba!ko kuma idan
zaka iyakamaidata gidan nasu mana.yakada kai
yace kasan bazan iya baneshisa.roqonka nakeyi
dan turafatakai bango dazaka fahimcihakan.yaja
tsaki ya shige dakiabinsa.ayuba ya dubeta
miqesakeena ki gyara wancan dakin kikwanta
xuwa safiya.koda zai sayarda gidan nasan
abinda zanyi a juya ya bishi dakin itakuma
tasaaci bal bal ta share daya dakin tasata baxa
keson tabalma.ta kwasotsummokaranta ta kulle
tayimatashin kai ta kwanta cike datunani.sha
biyun dare ta gotalokacin da danliti ya tsinkayi
ayubayanata minshari barcin ramako dagajiya ya
saceshi.yayi wuf ya tashiya sulale yabar
gidan..kamar yaddabokansa ya umarcesa dayayi
amfanida akuya a wannan daren kafin gariya
waye yasaida gidan sa yasakebude shago zaiga
kudi yana zuwakota ina.kai tsaye kasuwan ya
nufadan awakin da sukayi batan kaidare yayi
musu basa gane gida cansuke kwana Yana zuwa
yasamu qatuwar ciki yaturmusheta tareda
matsebakinta.kaya kaya harya biyabukatansa
(yayi releasing) farin cikayakamasa ashe banan
gixo kesakarba.yayi yayi ya rabu da jikinakuyan
nan abu ya gagara..tunyanaiya riqe akuya hartafi
qarfinsa tazabura aguje tarinqa wasan kuradashi
a cikin kasuwa.duk sauranawakan suka
watse.can yasamutadan tsaya.zafi da wuya
kamar sukasheshi.idanuwansa suka farahawaye
ya lalubo waya yana kukaakuya nayi da nufin
yagawabokansa ya nemo masamafita.kamar
ansake fincikar akuyata zabura wayarta fadi!
shikansabaisan inda tayi ba.kai danliti
yagawuyar duniya...kafin asuba yayibusu busu da
kura..yafitahayyacinsa
HAUSA Novels BOOK
BAKIN CIKI 3***5 Gaba daya qarfinsa ya qare.duk
inda akuyar tayi canzai nufa.suna manne
gagam.inda tayi gudu yatafi dagudun inta tsaya
ya tsaya.inta baje a qasa shimahaka zai baje a
qasan.akuyar kanta ta galabaita harkukanta
baya fita sosai.gari yafara shaa zai wayemasu
dawowa daga masallaci suka fara ganin wannan
abun al'ajabin.domin dai akuya takawo danliti
harbakin titi.mutane sukayo caa dan ganin waye
maiwannan aika aikar... Motsinsu ya qara firgitar
da akuyar nan.ta zabura tafada titi.dai dai wata
tirela takawo kai.Allah yasatashin motan
kenan.aikuwa nan take ta
hankadasukwalbati...kankace kwabo jama'a
ancika danqam akacirosu.mutane nata kallo ikon
Allah tare da hasashenwai wanene dubunsa ta
cika haka?gari ya waye tangaram,ana zubawa
danliti ruwa sannan yafarfado,,aka zuba masa
ruwa ya wanke fuskansaqurar data wanke masa
fuska ta bude.nantakemutane suka
shaidashi.wannan ai danliti ne,,,danliti?kowa ya
dauka guri ya dauki sallallami.tafdi!
muxuraikawai yakeyi.yana kallon jama'ar dake
kansa.yansanda suka iso dan ganin meke
faruwa.Cikin masu kallo kuwa harda malam
qaseem mijininna saude,,,kowa ya tsaya cirko
cirko anrasa yaddaza'ayi dashi.shikuwa nunawa
yake abashi ruwa.wanidan cuwa cuwa ya bula
pure wata yana tsiyaya masarabi a qasa rabi a
baki.can saiga ayuba yafito nemandanliti.don
tunda yatashi bacci bai gansba.Tun kafin ya
qarasa yasamu labarin,,,don haka yakutso ya
ganewa idonsa.tamkar zai suma
yakeji,,,yatsugunna gabansa ya ce mezan gani
dan liti?meyajawo maka wannan aikin?ya kada
kai da kyar yaceayuba wlh bantaba ba.alhakin
sakeena neyakamani.nina san alhakintane
kawai.don nasan na cutar da ita.kuma inason
yau kowa yasani.dukabunda sakeena tayi a garin
nan sharrinane,,,,asirinayi mata mugun asiri
kuwa..wanda ya dabaibayezuciyar kowa bamai
ganin aibuna.balle a tuhumeninasa andaure
bakin kowa harda naka ayuba tayandazanci
karena ba babbaka.. Dafarko ruwan maniyyi na
na bayar aka hada min dawasu ayoyi da garin
magani wanda idan na turara shiduk inda
sakeena take sai taxo.daganan aka baniwani
magani na badeshi da nama da hannunta
tabawakare yaci duk wulaqancin dazan mata
bazata tabarabuwa daniba.kuma baza taji
maganan kowaba sai nawa....nayi haka ne kawai
dan inci zaarafin sakeenasaboda walaqancin
datayimin.haqiqa na wuce makadida rawa kuma
ayuba nagayamin.amma banjiba.sai dayanxu
nagane duk masifar data samen
sakamakonabunda na aikatane.don Allah
kuyafen.ayuba kakiramin sakeena na roqi
gafararta.insami sauqin masifar danake ciki!sa'a
ce malamina yabani bantababin akuyaba,Labari
har gidan ubandawaki...don haka suka
garzayoakan idonsu danliti ya qarasa
labarinsa.kuma yakemagiya akira mama taxo ta
yafe masa.tuni wani danmatashin saurayi wanda
shekarunsa baxasu wucesha takwas ba ya sheqa
da gudu kiran mama,,,bamama kadaiba hatta
malam qaseem ya aika a kira masa inna
saude.ayuba yarasa abunyi hawaye kawaike
zuba.yayinda samari ke cewa abari su kasheshi!
jininka ya hallata danliti ayar Allah ka
wulaqanta...yansanda suke bakin qoqarinsu don
ganin samari basudauki doka a hannuba, Ana
cikin wannan hatsaniya akuya tace ga
garinkunan.Allah da ikonsa tana mutuwa jikin
danliti yafgitadaga duburar akuyar nan.can saiga
mama a guje batako ganin inda take jefa
qafarta.tana kawo bakin titiwani mai mashin
shima yanaso yaxo yaga taron meake...?yayi
awon gaba da ita.duk suka watse bakin titi.dai
dai lokacin inna saude nakawo kai
itama,,yuuwasu jama'a suka koma inda hatsarin
yafaru.kowafadi yake sakeena ce,,,,Allah sarki
sakeenance.jinhaka inna saude da sauran yan
uwan sukayikanta.asume take sai dai babu
alamun wani ciwoajikinta....ruwaa aketa zuba
mata yayinda yansanda biyu suka wuce da
danliti ofishinsu.daya kuma yatsaya a wajen
hadarin daya samu mama... Da akaga tajima
bata farfadoba,,,,sai akasakata amota da
dansanda daya aka wuce da ita
asibitinkagara..suka bar mutanen gari da
mamakin wannanabu mai kamada
almara.shikuwa ayuba sulalewa yayiyasamu
babbar mota ya bisu kudu.dauke da nadamamai
tarin yawa.tamkar shiya aikata wannan sabon.a
babban asibitin kagara kuwa..tuni anbawa
mamagado.kuma su alh basiru sunkira waya
abuja.,donbasu wannan labari mai ban
al'ajabi...ba abujakadaiba.duk yan uwan mama
sunsami labari...innasaude ma bata bata
lokaciba...ta garzaya gidanbaraka amma bata
samu kowaba duk suntafi aiki...domin tuni
baraka ta fadada iliminta a fceminna.kuma
tasamu koyarwa a l.e.a tana amsaralbashinta
,Yaranta biyar duk suna makaranta....da
albashintatasawa inna waya.sai dai yau wayar
bata jikinta baretakira baraka da tambaya tagane
makarantar dabaraka take koyarwa...ganin
innarta yasa gabantayafadi.kwarai da gaske basu
ko gaisaba inna ta sanarda ita halin da ake
ciki.jikin baraka yadauki rawa idanunta ya kada
tace haba!wannan lamari akwaidaure kai.Allah
ya isa tsakaninmu dashitambadadde.kotu ce zata
rabamu ina zuwa inna.Ta sheqa ofishin shugaban
makarantar ta nemi iziniankawo yar uwarta
magashiyan asibiti.take aka bataizinin
tafiya.suka rankaya da inna saude.baraka
tanakallon mama tafara hawaye saida inna
tayitararrashinta.tayi shiru.sunanan zaune jugum
jugum hartym din sallah yayi dake ranar juma'a
ce.duk maza suka dunguma sallar juma'a.basu
wani dade sossaida tafiyaba mama ta bude ido
tana kallon silin.innazoki gani ta bude ido inji
baraka.ta taso da sauri!ta isawajen gadon
mama!duk suka kirata.a hankali ta juyoda
fuskarta garesu.ta zura musu ido quri babu
koqiftawa.wucewar minti uku kafin tace inna!
Jiki na rawa tace naam sakeena!kingane wannan
yaruwarki ne?ta zura mata ido tace baraka tace
naammama.alhmdulillahi mungode Allah.tasake
kalle kalletace inna a ina nake?tace asibiti ne
mama,,,,tacemeya sameni?tace babu komai taci
gaba da kallonjikinta kaya dukun dukun gata
cikin tsumma farce kaman na makaniki takara
zare ido taceinna.haukacewa nayi koh?ina abba
nah?ina ummanaha?tayu wuf zata sauqo duk
suka riqeta hawaye naxuba musu.inna tace
kwanta mama ba haukakikayiba.ki nitsu!amma
inaso ki nutsu cikin hankalinkizaki iya tuna
meke tsakaninki da danliti?Idanuwanta suka qara
yo waje tace danliti?ta koma takwanta ta runtse
ido tamau! komai yana xuwa matakamar a
mafarki.zuciyarta ta soma zarya.kirjinta
nabugawa dasauri.kafin su ankara ta dirqo daga
gadontafita aguje.fadi take inna lillahi wa inna
ilaihiraji'un.suka biyo ta suna kira hankalin
mutane yadawo kansu daidai lokacin ya ali yake
isowa barandar zuwansafandogari kenan.inna
fadi take riqe min ita ali.ai kokafin ta qaraso
gunsa ta yanki jiki ta fadi..da gudunsaya qaraso
ya ciccibeta.ya riqe hannu biyu tamau!
tanaqoqarin kwacewa batare datasan ko a
hannunwatakeba.shiko fadi yake nitsu ki
saurareni dubeni mama!nace ki nitsu,Nitsu ki
sauraren,,,dubeni mama dubeni nace!
dakyaryasamu ta nutsu tana kallonsa jikinta
yaqara sanyi.tazura masa ido murya na rawa
tace yaya ali kana kallonadawo haka?tuni
hawaye sukafara zuba masa yacekwantar da
hankalinki mama! Abunda Allah yaqaddaro babu
wanda ya isa ya hanashi...zomuje ki kwanta ki
huta...ta kada kai .nibazan komaba.wajenumma
na zani.yace mama umma ta dade da rasuwatace
nasani dakinta zanje.ku kira min
abbainganshi.yace tuni aka kirashi kinsan yana
abuja nesuna hanya insha Allahu.kiyi haquri
likita yabakisallama tukun. Ta zube nan tace
atafau bazata komaba.inna saude tace a jira su
alh sufito sallah asan abinyi.ba'a dadeba suka
fito sallah suka iskesu waje..mama nata faman
kuka baraka na tayata.babu wanda bai tausaya
mata.jin kalamin dake fitowa bakinta.suna kallo
ta walakanta haka?duk wanda ta kalla irin
tambayar take masa.ganin ta kafe bazata zauna
a asibitiba yasa alh basiru yanemi sallama.daga
asibiti gidan baraka aka wuce da ita.sukuma
sukayi fandogari.nanda nan baraka tasa ruwan
xafi a hita.kafin wani lokaci yayi zafi.tare suka
shiga bayin ta surka mata.ta zuba mata wani
abuta..tace idan tagama na sabulu tayi na tsarki,
Wasu hawayen suka qara goce mata ta zurawa
baraka ido...na tsani kaina baraka.dan Allah ki
gayamin wani irin xama mukayi da danliti?ni
bangaskata abunda tunani na ke nuna minba.ta
dafata tace mama sanin irin xamanku da danliti
bazai haifar miki da komaiba sai bakin ciki..ki
dangana da qaddara!sannan kiyiwa Allah godiya
daya kubutar dake tsawon shekara goma sha uku
kina wahala.ta qara zaro ido sha uku?ashe
dagaskene?yaron danake gani nina haifeshi
dagaske ne ko baraka?Itama ta goce da kuka
tana fadin mama kidaina fadi nace?kiyi wanka ki
tsaftace jikinki kiyi sallah kiyiwa Allah
godiya.kinji?tafita da sauri ta janyo mata
kofar.ta kama kai kuknta ya tsananta.amma
tana dirza jikinta da soso da sabulu tayi ta dirza
saida sabulu guda ya qara...ruwan zafi ya qare
ta bude famfo ruwan sanyi.yi take da soso
hakanan.tanayi tana kuka.ta figi buta tayi
wankan tsarki...ta sake maida soso dirza takeyi
sama da awa daya watsa ruwa kawai sukeji
shaaa.kamar ana ruwan sama.inna saude tace
babu lafiya wannan wanka.ta tashi tabita
bayin.tayi biji biji da wuri inna ta kwace soson
ta dauraye mata jikin,ta warware sabon zanin da
baraka ta bayar aka rufa mata tace daura muje!
Ta xubo mata idanu jajur batace komaiba.inna ta
qara fadin ai kinfita mama kin wanke duk wani
datti.kisani Allah bazai kamakiba,,,karki
matsawa kanki.daura zaninki kiyi alwala muje
kiyi sallah.ta goge hawaye tadaura zanin tayi
alwala.inna ta kamo hannunta suka fito.tace ga
sallaya nan.gamai kifara shafawa ki sanya
riga.ga hajjabi kihau sallayar kiyi salla.dakai
take amsawa duk abinda inna tace.tahau sallaya
tafara sallah.kafin ta idar abincinta dana sha
suna gefe.Ta daga hannu sama fiye da minti
shabiyr tana addu'a tana kai kukanta ga Allah
tareda zuba godiya agaresa.hawayenta bai
yankeba saida tasauqe hannuwanta qasa baraka
tashigo ta matso mata da abincin.tasa hannu ta
share mata hawayen tace ga abincinki nan.ki
daure kici.hakan shi zai qara nuna godiyarki ga
Allah.tace banajin yunwa baraka.bana sha'awar
komai naci kosha..bazan gane menake ciba.tace
to zankira miki inna......tace a'a baraka bawai
kema baki isa kisani cibane kawai banajin
cine..na qosa inshiga dakin umma.na qosa inga
abba da yayyina.baraka kigayamin kadan daga
labarin al'ameen kozan daina jin kuna cikin
raina.Baraka ta qara matsowa ta riqe yatsunta
mama ban san komaiba game da al'ameen.tun
lokacin daya dawo kika qishi.yanaji yana gani ya
haqura da aurenki.ance yasake komawa rasha
daganan,bansake jin duriyarsaba.amma nasan
kakarsa goggo hassu ta rasu.kamar anbude
famfo bisa kuncinta....murya na rawa tace wlh
baraka banqishiba...al'ameen kadai nakeso ke
kinsani..meyasa baki gayawa su abba ba adaura
min aure dashi dan dole ba?tace haka abba yaso
amma kika kwashe kayanki kuka gudu da
danliti.aka nemeki aka rasa. Ido waje tace nidin
baraka?ke kuwa mama..sai da kuka kwashe wata
uku baku dawoba.....ta toshe kunnuwanta tana
fadin.kidaina gayamin baraka!kidaina!tamiqe da
sauri tayi falo..taci gaba da maimaitawa baraka
ta biyota su inna suka mike.suka tarbeta...ta
zube jikin inna kidaina gayamin kidaina gayamin
nace.inna ta rungumota me kike gaya mata
baraka?don Allah ki dena daga mata
hankali.tace inna ita ta tambayeni labarin
al'ameen.inna ta numfasa tace ya isa,duk
maganar nan abarta taci abinci? bataciba. Jeki
dauko mata ta juya tadauko...su hajiya hajjo ba
baka sai kunne.tagumi kawai suka doka suna
ganin ikon Allah.addu'a suke kar mama taji
magana daya acikin wanda suka yayata.inna ta
tasa mata abinci tace ci abinci mu wuce kinga
yamma tayi.ki kwantar da hankalinki.irin
walaqancin da danliti yagani yau.dakin ganshi ke
kanki zaki gane Allah ba axxalumin bawa
bane.daure ko cokali uku kici.tasa hannu tdauki
cokali tafaraci kamar mecin magani ido na zubar
da ruwa. ***page 60:sun iso fandogari.la'asar
sakaliya golf din da ta kwasosu ta ajesu kofar
gida mama ta balle murfin mota.ta tsaya ta
qarewa gidan kallo.wasu abubuwa nadawo wa
cikin tunaninta.qarara take ganinta ta kwaso a
guje alh adamu ya biyota da bulala a
guje.takenan ta zube bisa guiwa.ta qara fasa
kuka.ciwo zai kamaki mama wannan kuka yayi
yawa kiyi haquri mana Inji hajiya hajjo duk
maxan gidan suka fito.suka tarbesu.sukaja
mama zuwa cikin gida.sunaa isowa kofar
sasansu,,taja ta tsaya tace ku budemin inshiga
wajen umma na!hajiya hajjo ta ruga daki ta
dauko dan makulli.alh basiru ya amsa da kansa
yabude.ta shiga suka take mata baya.ta kalli nan
takalli can.harya bude qofar falon yace shigo!
yajawo hannunta...ta shiga falon.da gudu ta nufi
dakin umma ta murda ya bude.cikin sanda take
shigowa.tunaninta ya koma baya lokacin da
danliti yake gayamata rasuwar umma.da gudun
da tayo zuwa gida.haduwarta da yanuwanta suka
hanata shiga.jiri ke dibarta...basu luraba.sai ta
zube qasa a sume.take nan tasamu taimako ta
farfado.ta fasa kuka tana fadin.umma kiyafemin
kiyafemin umma! Kai ya ali bazai iya jure ganin
mama ba cikin wannan yanayi.don haka yayi
waje yana share kwalla.yana zama ya abdul
rahman na sawo kai.ali yace sannu da zuwa
yaya!yace wai da gaske ne abinda naji?yace
gaskia ne yaya tana cikin dakin umma.yayi
azama yatafi dakin tun kafin yaqarasa yakejin
kukanta.yadannada gudu ya qaraso tana kife kan
cinyan inna saude.kowa kukan yakeyi tamkar
yau umma ta rasu.yasa hanna ya dagota.tadago
kai ta dubeshi haba tuni ta tashi ta
rungumesa..wanisabon kukan ya balle.ai shima
baisan lokacin danasa yafara zubaba.tsawon
lokaci suka kwashe kafin ya dagota ya share
mata hawaye.kidaina kuka haka mama!murya na
rawa tace yaya kuna kallo aka maidani haka?
kuna kallo aka haukatar ni?aka rabani da
gatana? Ya rufe bakinta ya girgixa kai.yace ba
haka bane mama munyi iya yinmu.amma bamu
nasaraba! sabodaAllah ya nufa sai dan
liti.yaxamo jarabci agareki.amma bamu gaxaba
wajen yimiki addu'a kuma nayi imanin addu'oin
ne suka taimaka wajen kwato ki daga hannun
mummunan halin da danliti yajefaki.kiyi haquri
kinji?kimaida al'amuranki gurin Allah.kiyi masa
godiya daya ku buto dake.share hawayen ya isa
haka.yaci gaba da share mata.tace wai yaushe
su abba zasu xo? yace munyi waya yace min
yataso amma abdulkareem sai gobe.kinsan yabar
minna anmaidashi legos,,shekara uku dasuka
wuce....tace Allah sarki yaya.tagoge kwallan
daya digo mata tace...kowa nananko?yara duk
sun girma?yace kowa nanan mama.yara kuwa
wadanda kika sanima baxaki ganesuba.naso
xuwa da nawa saboda mkrnta gobe weekend
direba zai kawosu da mamansu.
IN CIKI 3***6 Nagodai da adduar ku, bari na
dan taba muku kadan idai kunji shuru to exam
ne ya rike ni Kai ya ali bazai iya jure ganin
mama ba cikin wannan yanayi.don haka yayi
waje yana share kwalla.yana zama ya abdul
rahman na sawo kai.ali yace sannu da zuwa
yaya!yace wai da gaske ne abinda naji?yace
gaskia ne yaya tana cikin dakin umma.yayi
azama yatafi dakin tun kafin yaqarasa yakejin
kukanta.yadannada gudu ya qaraso tana kife kan
cinyan inna saude.kowa kukan yakeyi tamkar
yau umma ta rasu.yasa hanna ya dagota.tadago
kai ta dubeshi haba tuni ta tashi ta
rungumesa..wanisabon kukan ya balle.ai shima
baisan lokacin danasa yafara zubaba.tsawon
lokaci suka kwashe kafin ya dagota ya share
mata hawaye.kidaina kuka haka mama!murya na
rawa tace yaya kuna kallo aka maidani haka?
kuna kallo aka haukatar ni?aka rabani da
gatana? Ya rufe bakinta ya girgixa kai.yace ba
haka bane mama munyi iya yinmu.amma bamu
nasaraba! sabodaAllah ya nufa sai dan
liti.yaxamo jarabci agareki.amma bamu gaxaba
wajen yimiki addu'a kuma nayi imanin addu'oin
ne suka taimaka wajen kwato ki daga hannun
mummunan halin da danliti yajefaki.kiyi haquri
kinji?kimaida al'amuranki gurin Allah.kiyi masa
godiya daya ku buto dake.share hawayen ya isa
haka.yaci gaba da share mata.tace wai yaushe
su abba zasu xo? yace munyi waya yace min
yataso amma abdulkareem sai gobe.kinsan yabar
minna anmaidashi legos,,shekara uku dasuka
wuce....tace Allah sarki yaya.tagoge kwallan
daya digo mata tace...kowa nananko?yara duk
sun girma?yace kowa nanan mama.yara kuwa
wadanda kika sanima baxaki ganesuba.naso
xuwa da nawa saboda mkrnta gobe weekend
direba zai kawosu da mamansu. Su nawa ne
yaya?yace su uku nee.harda takwararki..itace
tafari.ido waje tace kana nufin sakeena sunan
yarka ta farko?ya amsa sosai ma abba ne yace
asamata.ta runtse ido abba nah kaxo
inganka.hawaye shar bisa kuncinta.ganin
yayanta kusa da ita yasa ta saki jiki tarinqa
tambayar abubuwan dabata saniba,tare da
tambayan yanuwanta da bata gansuba..da
yawansu suna skul.danlami kuwa yana aiki a
sakkwato harda matarsa da yaransa
biyu.daganan suka fara amsa sallamar mutanen
gari masu zuwa musu murna da jaje,,,ciki kuwa
harda maman fati saida tayi kuka dataga mama
acikin danginta.meya fi wannan dadi?tajima
tana maida abubuwan data sani game da zaman
quncin da mama ta fuskanta.sannantatafi itace
baquwa ta farko da mama tayiwa rakiya.don
baxata mance gudumawar data bataba.anyi sallar
isha su hajiya hajo suka gabatar da abinci.mama
na kwance lamo kamar mai bacci gefen
yayanta.malami suka gani yayi sallama yashigo
yazama qaton saurayi yanata karatunsa a n.d.a
kaduna. Su suka biya suka daukeshi.duk suka
miqe malami kun iso?yace mun iso kawu.ina
anty maman?tana zaune jugum takasa motsi jin
cewa abbanta ya iso.idanuwanta tuni suka fara
tara kwalla.gabanta na faduwa !malam.ta
kirashi.yayindaake nuna masa ita.kai ina
baiyarda.duk da yafara manta kamanninta yasan
anty maman sa.kyakkyawar gaske ce mai
kwarjini wanda yake burge manya da yara.dan
takaitaccen tarihin da yaji a mota yasa duk
tausayinta yamasa bargo.idonsa ya cika da
kwalla.ta mike tana fadin kunxo min da abba
na? ya kamo hannunta gasu nan a waje.zo muje
ki tarboshi.sukabibayan sauran ayarin dasukayi
gaba.suna kawo kai zauren farko ana turasa a
keke.anan ta qame suka xubawa juna
ido.abbanta ne a keke?duk tsufa ya mamayesa?
zuciyarta taci gaba da bugawa shiko tasbihi
yakewa ubangiji wanda yayi nufin sake hada
fuskarsa da diyarsa.shi sauyin kamanninta bai
damesaba ganinta yadanne duk abunda ke cikin
xuciyarsa Batasan malami najantaba.ita dai
ganinta tayi daf da keken abba.muryarsa dataji
ya qirata yasa tayi lau zata xube.amma ina yan
uwanta.basu bariba.caraf!suka cafketa.yaya soja
ya amshe yasa hannu biyu ya girgizata.mama!ke
mama!ya ali ya miqo kofin ruwa.ga ruwa yaya.ya
zuba masa a hannu ya shafa mata a fuska.tayi
ajiyar xuciya..tafara kuka abbana!da dorata
jikinsa ya rungumeta.irin kukan datayi sai da
tabawa kowa tsoro.domin ji sukayi dif babu
rai.daukarta sukayi cak sukayi cikin gida da
ita.babu abunda BAKIN CIKI Baya bayarwa.haka
zalika FARIN CIKI!dan saiya gigita mutum take
nan har ya iya fadawa wani hali.mama kam farin
ciki yasa sai da yan uwanta sukayi da gaske ta
farfado.tadawo hayyacinta ta bude ido taganta
kwance jikin abba.ta zura masa ido yakada kai
yace mama ki taima keni kar farin ciki ysa ki
sake jefamu a yanayin da muke sallama dashi Ta
hadiye miyau da kyar tace har yanxu cikin BAKIN
CIKI nake.abba.na kuma tabbata bazan taba
fitaba daga cikinsaba.menayiwa danliti ya
lalatamin rayuwa?menayi masa dazaya karya
dukkan gabobin tatbiya ta da kima ta da
asalina...sannan yawargaza dangantaka ta da
iyayena,,,ya rabasu da komai najin dadi...har
umma tabar gidan duniya?yaya soja kana kallo
duk hakan ta kasance?meyasa baka jefani gadi
rum ka rufeba?meyasa baka hadani da sojoji
sukayi ta dukana harna mutuba?dukknku kuna
nan?kun san wanda nakeso kunsan zabi
na,,,amma kuka barshi yatafi maimakon ku
tilasta inbishi duk. Yaya soja ya rufe
bakinta,,mama ya kamata kiyi shiru
haka.zuciyarki zata buga.idan kina fadin irin
wadannan kalaman.ni yadda nake gani ma ke
baki ga BAKIN CIKI Ba tamkar yadda muka
ganshi kiri kiri.amma bamuda maganinsa.kisani
duk abubuwan da kika lissafa babu wanda bamu
kwatanta akankiba.sai dai abin ya
faskara.saboda anriga an mallaki zuciyarki
mama.karki danganta laifin akan kowa.don babu
wanda yasan gaibu sai Allah.shidin kuwa mukayi
ta roko ya warware mana abunda ke boye.agame
da lamarinki.ina ganin yakamata ki kalli
uzirinmu.kiganecewar munyi iya kokarinmu.
Hargashi Allah ya shige mana gaba ya kwato
mana ke.ayanzu mukeda damar nunawa danliti
cewar lalle ya debo ruwan dafa kansa.dazai
kaisa har lahira.ki kuma sa ido kigani. Da sauri
tadawo wajensa shima ta rungumeshi murya na
rawa take cewa karka barshi da rai yaya!kasa a
masa azaba mafi radadi harya mutu.ya lafe
kanta a kirjinsa zuciyar maxa ta motsa.idanuwa
suka qara jirkita.kawai gani sukayi yasaketa ya
miqe cikin hanxari zaiyi waje,,,abba yayi azama
yace ku riqo minshi don Allah!su alh basiru suka
cafke hannayensa.dawo ciki ka zauna ya qame a
tsaye suna ganin yanda jikinsa ke rawa.namansa
na girgiza saboda fishi.alh adamu yace alh ne
zaiyi magana dakai..abba ya daga murya yace
abduqadeer dawonan ka zauna!a hankali fishin
yarinqa sauqa sannan su alh basiru suka dawo
dashi ya zauna.yayinda mama tasake baro jikin
abba tadawo gunsa ta zauna. Abba ya numfasa
dukkanmu musulmai ne,,kuma munyi imani!da
ko waccw qaddara ce.ina ganin fushin farko
banamu bane.kar zuciya tasa mu aikata aikin
nadama.yaya soja ya kasheshi babu nadama dan
an harbe azzalumi macuci.irin danliti.karka
manta muya fesa mana gubar mutuwa.mun
shaqa harta shige mana da ginshikin gidan nan
abba,!bazamu yafewa danliti ba abba.koza a
kasheni saina harbeashi.abba yace kenan bamu
godewa ubangiji ba daya nuna mana wannan
ranar?wanda yace muyi afuwa a
tsakaninmu.domin shi yanason masu yafiya.ko
bamuyi fansa a gun danliti ba.nayi rantsuwa
Allah bai gama walaqanta shiba.tunda ya
walaqanta ayoyin alqur'an.inaso mugane
wannan.ba haqqin mama kadai ke wuyansaba.
Banajin akwai hukuncin dazamu yankemasa face
mu qyaleshi da wanda yabasa ikon aikata
wannan aiki akan mama.na tabbata bazai
qyaleshiba yaci bulus!ba.ina roqonku da muyi
haquri.mu sadauqar da yafiyarmu a matsayin
godiya ga Allah daya musanya mana bakin ciki
da farin ciki.ina fatan yaya soja zaibi umarni
na? jikinsa yayi sanyi yadan kada kai..yace ya
wuce abba yayi dan murmushi. Yace nagode!
mama zonan...!ta rarrafo ta dawo jikinsa ya
jawota. Yace ki nitsu nasan kinrasa komai na
tsarin rayuwarki yanda kika shirya....saidai inaso
ki gane cewar shirin Allah shine gaba da
komai...saboda haka ki rokesa sabon rayuwa mai
albarka.muma zamu tayaki zakiga kamar
wannan abun bai faruda rayuwarki ba.ki sani har
ummanki ta rasu bata taba yi miki baki
ba.kullum addu'arta Allah shiyaki.idan zatasa
albarka tare takesa muku da sauran yayunki.don
haka tsakaninku adda'a ne kawai. Na tabbata
hasken addu'arki zaije gareta.harta gane cewa
lallai albarkar ta na tare dake kinji mama?ta
dubeshi kwalla na zuba tace naji abba.don Allah
kayafemin ya goge mata hawaye yace baki min
komaiba mamana.ayau nagane baki da laifi ko
kankani saboda haka ki saki jikinki.tace nagode
abba intambayeka abba?yace tambayeni
mamana.ta karya wuya gefe tace al'ameen fa?ya
kada kai yace allahu akbar!alkairi Allah yakai
mas duk inda yake.haqiqa bantaba ganin tashin
hankaliba irin wanda nagani a fuskar
al'ameen..saboda rashinki mama kiris yarage ya
zautu amma qarfin adda'a ya miqar da imaninsa
zuciyarsa ta daidaitu bisa shirin ubangiji.ya
rungumi qaddara yawuce da ita rasha.gaskia
bansake jin duriyarsa ba haryau din nan danake
magana dake...kuma hulda ta yanke
tsakaninmu.ni kaina bansan daliliba.watakila
iyayensa sun nisancemu don qara nesanta
rayuwar dansu ga tinaninki.hasashe nayi amma
bansan musabbabinba.
BAKIN CIKI 3***7 Tacire kai ta dubesa kwalla na
zuba tace tabbas zai iya zama hakan abba!nima
nayi alqawarin zanyi masa addu'a Allah qara
nesantamu.ya mance ya taba sanina a duniya..ko
a hanya kar Allah ya qara hadamu.abba yashafa
kanta Allah ya shige miki gaba.yayi miki jagora
a sabuwar rayuwar dazaki fuskanta nan
gaba.kowa yace ameen yace muyi addu'a.sun
raba dare a falo suna hirarrakin duniya abba yace
aje a kwanta a huta.mama ta turashi a kekensa
zuwa dakinsa wanda tuni anty amina ta dade da
gyarawa.suka kamasa yakwanta a gado.sannan
sukayi sallama takoma dakin umma!inda anty
amina da baraka suke. Kowa ya kwanta barci ya
kwasheshi.amma mama ta kasa.kawai tunanin
yanda tayi cudanya da danliti take.nan da nan ta
ji kyaman kanta ta kamata.tafara sunsuna
jikinta.hankalinta tashe batasan lokacin data
diro tashige bayiba.ruwan sanyi ne a bokiti da
anty amina ta dibo.mama ta duba ba soso ba
sabulu.haka nan tahau kwara ruwan sanyi
ajikinta.tana dirjewa da hannu hawaye na
xuba.ruwan ya qare ta dauki bokoti ta kwarara
sauran. Tadauki bokitin takwara sauran ruwan
gaba daya.haushin qarewar ruwan
yakamata.tasanya kayanta ta figi bokitin da
nufin taje tsakar gida ta debo a rijiya.su anty
amina da baraka tagani cirko cirko abakin
bayin.tawuce abinta ta doshi kofar.yayinda anty
ameena kefadin haba mama! ashe bakiyi
bacciba?yakamata kimanta komai karki zautu a
banxa da wofi.ta zuba mata ido kwalla na xuba
wari nake anty ku bakuji?babu wani warin da
kike mama!tunaninki yagaya miki
qarya.yakamata kisamu bacci ko kwakwalwarki
zata huta.ta dubi baraka taga hawaye itama
take,,,tace saboda Allah baraka bakiji warin
danake ba?sunsuna fa kiji....takara mata hannu
a hanci baraka ta goce da kuka ganin haka jikin
mama yayi sanyi ta zube qasa dabas takama
kai.wayyo Allah na!suka kamota sukayi ta
rarrashinta.tadan nutsu.amma barcin da basu
komaba kenan gabadayansu Washegari kowa ya
hallara da iyalansa.ya abdulkareem da anty rabi
kamar su hadiye mama sukeji.sun xubda hawaye
saboda murna.ta dubi girman ameer da ameera
kawai sai ta kada kai.tana tuna al'ameen
shikansa docta yazama saurayi.ta zura masa
ido,,,hannayenta bisa kafadunsa ta matse
ido.hawaye suka kwararo..jitayiyana share mata
hawayen tayi wuf! ta bishi da kallo.bakinta na
rawa tace al'ameen momy nagayama inasonka??
ta taba gayamaka? ya juya ya kalli
mominsa.yamaidoda kansa gareta ya girgiza
kai.bata gaya maka ba?amma momy bata
kyautaba.tasanfa yadda nake sonka Allah tasani
boyema tayi togayamin kana sona? yadaga kai
alamar eh.ta rungumeshi tana fadin nima
inasonka dokta. Anty rabi ta taso ta dafata.ta
dago kai ta dubeta kwalla na xuba mama!ki
kwantar da hankalinki na tabbata Allah baxai
barki hakaba.zai musanya miki mafi alheri wata
qilama fiye da al'ameen.tayadd a rayuwarki zata
daidaita tamkar da. Ta miqe a hankali ta
fuskanceta tace hakane.nasan babu abunda zai
gagari Allah.amma dokto shine farko shine
qarshe.ta wuce ta murda kofar dakinta.ta qare
masa kallo inba qarya idonta ke gayamata
ba.kamar ta taba ganin al'ameen tsugunne a
wajen data qurawa ido.dukda takasa tuna
kalaman dayake fadi.idanuwantana nuna mata
zubar kwallansa.tayi wuf!ta cafke yatsunta ta
runtse su tamau.tana tambayar kanta ina zobe
na?ina na ajeshi?ta wuce a hankali bakin gado
ta zauna tayi shiru tana tuna kalaman dayake
fadi idanunta na zubda hawaye.kai al'amarin
mama qara sukurkucewa yake dalilin dayasa
abba yace subar garin wataqila tafi samun
nutsuwa.nanda nan suka fara shiri.kafin wani
lokaci kowa ya kimtsa abba ya sallami en uwa
da abokan arziki.su hajiya hajo sunata neman
gafara wajen abba da mama.motoci suka
kwashesu kowa da iyalansa suka miqe
hanya.suka bar danliti hannun hukuma.duk
abinda yakamata su masa A kagara suka sauqe
baraka tukuna suka dau hanya.minna suka yada
zango gidan ya abdulkareem.ko anan dinma
al'amarin bai sauyaba.haka suka kwana ba barci
a idon mama.washegari suka kimtsa masu tafiya
abuja suka dau hanya.ya abdulrahman yayi
kaduna da iyalansa da malami.shikuwa
abdulkareem jirgin shabiyu sukabi zuwa
legos.yan abuja suna dira gida wanka mama
tafarayi.wannan wanka yafara damun yan
uwanta.su wanka ma kawai suke gani basusan
yanda taga dare haka take ganin ranaba!akwai
fargaban rashin bacci zai mata illa.idan ba'ayi
gaggawar daukan matakiba.towayasani bare ayi
mata magani? shiyasa kafin sati ta birkice gaba
daya.ga zama shiru ga sunsune sunsunen
jikinta.wanka kuwa ba'a maganarsa.saidai in
danliti bai fado mataba.nan da nan tafara mura
zazzabi mai zafi ya rufeta.hankalinanty amina
yatashi.data shigo dakin tasameta nade cikin
bargo sanyi na kadata.cikin sassarfa tasamu
abba.ta durqusa a hankali tace abba idan ba'a
dau matakiba mama zata kashe kanta da yawan
wankan nan. Mama zata kashe kanta da yawan
wankan nan.gatacan jikn kamar wuta sai rawar
sanyi take.yakamata asan abinyi cikin
gaggawa.nanda nan ya latsa control din kekensa
yawuce ya nufi dakin yana fadin kira yayanta a
waya.kuma fa yau dinnan naji yana fadin sun
gama magana da yan uwansa egypt zasu wuce
da ita asibitin dana kwanta. Su duba lafiyarta!
tace nima yagayamin amma duk da haka
yakamata afara kaita nan tafara samun
taimakon farko.yana kutsa kai dakin yana fadin
gaskia ne.kirashi din ki kara gaya masa.ta juya
shiya shige dakin yasamu mama sai kyarma take
cikin bargo.kwananta biyu a asibiti basu gane
ainihin matsalartaba.amma taimakon dasuke
bata yataimaka kwarai wajen sanyata bacci.tana
samun hutu.duk takardar tafiyarsu masar sun
kammala itada yayanta wato soja.a ranar basu
kwana ko inaba sai egypt .acan bincike ya
tsananta.don babu irin gwaje gwajen da bata
samuba.hoton kwakwalwa hiv aids,,ciwon sanyi
da sauran ciwuka dakan kama mutum
sakamakon shiga wahala mai tsanani.Ba a
sameta da wata matsalaba sai hawanjini da
rashin bacci.kamar dai yadda likitotin nigeria
suka ce amma su abba basu yaddaba dan gani
suke kamar hauka mama keda niyyan yi.sai dai
Allah da ikonsa likitotin masar suna kokarin
shawo kan matsalarta.da magunguna da
shawarwari.don cire mata damuwa wanda
gabadaya ita ummul aba isin komai.to muma
bari mubarta ta huta. A lokacin da mama ke
kwasar hutu damagunguna akasar masar.shi
danliti yashe yake aofishin yan sanda.yanata
hauhawa kamarfarashi.gaba daya fuskarsa ta
aune ta kumburasundum.sukansu yan sanda sun
gaji da saya masagarin rogo yanasha..babu mai
belinsa.tsawon kwana biyar dama ayuba ne yake
zaton ziyi belinsa to shimatunda yaga ayar Allah
ta sauqa.don haka yayi wakansa alqawarin tuba
daga nasa laifukan zinacezinace dayake
aikatawa.babbar mota yabi sai indamai
yaqare.wajen neman halal.to Allah ya
karbitubansa.shikuwa dan goga yarasa tudun
dafawa ga ciwo ga masifar yansanda.ranar daya
cika kwanashida.sukace zasu sakeshi yatafi
yanemilafiyarsa.idan yaga dama ya gyara
halayensa ko yacigaba da lalacewarsa..shidai
yana kuka yana roqonsusu barshi dare yayi su
sakeshi saboda kunya kunjidan iska ashe yanada
kunyan?kuma da tsoron kar jama'a suganshi su
sake rufar masa da duka,Yansanda suka amince
hakan amma baxasu bashiabinciba.h aka
yazauna da yunwa har qarfe gomandare.suka
tarkata shi suka tura waje.a hankaliyasamu ya
sulale yakoma gidansa ya kwana.yanatunan in
mafita da da hali gidansa zai sayar a darannan
yahada kudinsa yatafi neman magani.sai dai
kash takardun sun kone a shago lokacin
gobara.meyeabunyi yanxu?bai runtsa ba kamar
sauran dararendasika shude.yana wahala da
ransa.sai dole yakaudakunya ya nemi wasu
takardun yasaida gidan danbashida wata mafita
data wuce wannan.idan yanasoya tsira da sauran
mutuncinsa duk inda zashi..haka kuwa akayi da
sassafe ya lallaba gidan maianguwa.baiko dawo
masallaci ba.ya zauna yajirashi.ya gurfana
gabansa yayita roqon gafara.sannanya miqa
masa kukansa.mai anguwa bai bata lokacibaya
amince domin shima zaiyi farin ciki idan
danlitiyabar garin fandogari.saboda haka nantake
yakawo takarda da biro suka rubuta wani
takadda.dakansayanemo shaidu uku sukasa
hannu.kuma yasa akanemo dillalai sukayi wa
gidan kudi yace shi zai Saya,Gaba daya dubu
dari biyu cinikin ya kaya.danliti yasallama ya
karbi kudinsa a hannu.kafin qarfe goma nasafiya
ya tattara yabar gari.gashi nan gashinan harwani
kauye da ke tsakanin zariya zuwa kura
jaharkano.da la'asar sakaliya.kofar gidan daya
dosa cikeyafe fal!da jama'a anata alwala.a
raunane yayi musu sallama.suka amsa ya
tambaya..ko lafiya kofar gidanmalam?daya daga
ciki yabashi amsa ai malam wa'adiyayi.shirin
yimasa sutura ake.danliti ya dora hannuaka yace
ciwo yayi? yace to ciwon ajali ne.kwanansabiyu
kacal a kwance.ya nemi waje a qasa ya
zaunahankalinsa ya qara tashi..wanda ke bashi
amsa yamiko masa buta yana fadin hala kaima
cikinalmajiransane?yace aytoo harda neman
taimakoma.Allah sarki malam Allah jiqansa.yace
amin yialwala yanxu za'a fito dashi.jiki babu
kwari yafaraalwala.ya na kammalawa ana fito
dashi.daganan sukadiba zuwa makabarta..ga
kabarin malam an haqa duk abunda ake anyi
akasakasa a kabari aka maida qasaakarufe
iyalansa nata kuka harda danliti,Daga nan aka
dan jira ayi masa addu'a kawai ganingawar
malam akayi ta bulloqo waje,subhanallah!
mekefaruwa ne? tashin farko jama'ar wajen suka
watse.kafainbak iyi kibani waje musamman
danliti.daya riga kowaficewa daga wajen.daga
bisani liman yasa aka tattaromasa mutane suka
dawo.danliti nacan baya yana rarraba
idanu.liman yadaga murya yace innalillahiwainna
ilaihi rajiun.! jama'a wannan al'amari fa
banagudu bane.! wata ayace dake bukatar
bincike.matsayin malam agarin nan wannan zai
iya zama abin kuka agaremu.domin mu a zahiri
munsan malam mai iliminaddini ne,,wanda ya
koyar da almajire da yawa.wanda yake wakilta
na lokutan danake da uzuri.sai dai ahalin yanxu
wannan abun yanuna mana akwaiboyayyen laifi
agareshi!ina rokonku dan girman Allahku tsaya
muyi masa addu'a.mu roqa masa
rahamarubangiji.alfarmar annabi muhammad
(s.a.w) Yayi kabbara sau uku jama'a na
amsawa.iyalanmalam kuka da firgici yaci
qarfinsu labari kuwa tuniyabaza kauye.har
wadanda wani uxiri yahanasu xuwasun sheqo
aguje.shiyasa makabarta taqara cikamakil.liman
ya jagoranci addu'a mai tsawo.sannanaka qara
haqa kabari aka sakasa.shikansa liman kuka
yake da hawayensa saboda ganin wannantashin
hankalin.bayan anmaida qasa an rufe .sukasake
tsugunnawa dan nema masa gafara.ai sai
gagawa tayo waje.ana salatin annabi da tasbihi
daistigifari akasake mai dashi.amma ba'a gama
maidaqasar ba gawa tasake bullowa waje.liman
ya dubi babban dan malam.ya tambaya!meka
sani agame damalam wanda mu bamu sani ba?
gashi ubangiji yananuna ishara gamasu yi su
tuba su daina.ya gogekwalla yace wlh bansan
komaiba,,,bantaba lura dawani aiki na assha
atare dashiba.dana sani wlh danafadi sai dai ko
aje atambayi mata a gida, LLiman ya numfasa
duk guri yayi tsit!kawai sai ganindanliti akayi a
gaban liman ya tsugunna Allah gafartamalam ni
nasani.na kasance ina daya daga cikinmasu
zuwa gun malam.neman taimako akanabubuwan
dasuka damemu ko ince nemanduniya.bansan
irin shirin dayake wa sauranba amma nida kaina.
Nasha kawo ruwan..........ruwan maniyyinayana
rubuta ayoyin Allah dashi.yana
hadaminmagunguna danake buqata.ina bashi
maqudankudade.tahanyar malam mun cutar da
bayi Allahwadanda basujiba basu ganiba.ba
malam kadai kebuqatar addu'a ba harda ni.Allah
gafartawa malam.wuri ya kaure da sallami.wasu
sukafarazungurar dan liti suna la'antarsa.liman
yatsawatar.yace a saurara.tsarki ya tabbata ga
ubangijindukkan halittu.jama'a kunji wannan
mummunan tashinhankali?toga aya ta
tabbata.ina ganin ta ishemutsoron Allah.ta
ishemu mu gane komai ka boye wa mutane
bazaka boye wa Allah ba..kuma ko ba dadekoba
jima zaka koma gareshi.bamu da abinyi a
halinyanxu dan hukunci yakoma gunsa. Ya daga
hannunsa sama yaci gaba da fadin yaubangiji
muna tawassali da sunayenka guda casa'inda
tara,,,ka taimakemu ka amshi wannan bawa
nakadan kar warin gawansa yazama guba ga
bayinkasalahai!ya Allah ka sauqar da rahamarka
cikinkabarinsa badon halinsaba.badon
halinmuba.badon ayyukanmu ba sai don monxon
mu annabimohammad (s.a.w)suka qarasa tare
da muryoyinmutane dake cike maqil.kai tsaye
liman yace akamaa maidashi.kankace kwabo
ansakasa a rami anrufeakayi zuru! ana jiran ikon
Allah.amma tsawon mintocishabiyar. Babu
abunda yafaru.aka soma qabbara.liman kuwa
fadi yake jama'a muji tsoronAllah.muji tsoron
Allah ya al'umman musulmai.kodada nliti yaga
haka saiya fakaici idon mutane tuni yasulale ya
tsere kar yasha dukan banxa gun wadannanyan
kauyen.A gigice yashiga kano cikin dare da
kullin kudinsayanufi inda yasaba sauqa,,,,,zuwa
safiya yayi amfanida kudinsa danyin wata
sana'ar don riqekansa.washegari yashiga kasuwa
yin sari wani mutumya bangajeshi ya wuce.saida
aka hada masa kayandubu dari da hamsin.ya
laluba kudi sukace daukarmu inda ka
ajiyemu..nanda nan ya firgice.ya tubekayansa
tsundur yana dube dube....ina kudin suke?anan
fa na ajiyesu...masu shago sukayi zuru
sunakallonsa.am ma dasukaga abin nasa babu
hankali aciki sai suka turasa waje.ga ganin
wannan mugun nufine yakawo sa Allah
yakamashi.yakama haukan qarya.haka masu
shagon da jama'ar wajen ketafadi.danliti kuwa
ya rinqa bi kwararo kwararo akasuwayanata
surutai.fadi yake...wannan bala'in
yayiyawa..wata tsiyar ma sai anmutu.lalle lahira
dakallo.toni wama zan kalla?aini ne zanxama
abinkallo.da dama idan sukaji dariya suke.wasu
kuma al'amarin yabasu tausayi.ga mutum har
mutum daganiya aje iyali amma ba saiti,Bayan
watanni hudu har mutan fandogari
sunfaramantawa da abin mamakin daya
faru...wanda ya ajetarihi musamman ga yan
jarida ta yadda..suka rinqawatsa labaru.cikin
shafukansu.na abin al'ajabindayafaru a kauyen
dunduta.ba xato ba tsammanikawai sukaga
danliti ya keto titi a kafa da rana face face.yayi
bakikirin.gashi n kansa cunkus hade
daqasumba.harda furfura.dafarko basu shaida
shibasaida yayi sawu uku.nanda nan labari yayi
tambari harkunnen su abba cewa danliti ya
HAUKACE.Allah daikonsa,tunda ya iso fandogari
bai qara gaba ba.nanyaketa bilayinsa.qafafu duk
sun kumbura.wani lokacinma kasa tafiya
yakeyi.kaganshi kwance cikinrana quda na
binsa.idanyaji yinwa yayi tabin gungunmutane
yana bara.asiya masa abinci.kai jama'a
muceALLAHU AKBAR! **A watannan hudu,,ita
mama sauyi sosaitasamu.domin tasamu matuqar
kulawa a sati ukundatayi a masar.tacci gaba da
samun kulawar yanuwanta.suna nuna mata gata
fiyeda wanda tasamuada.tadawo sakeenarta.sai
dai dan qara manyanta dafuskarta tayi.ayau suke
sa ran dawowarta daga umara!inda tasami sati
biyu a saudiyya tana ziyararka'aba.tana samun
nutsuwa tare da miqa addu'ol daneman buqatu
na alheri.sai dai bata sauqa abuja ba alegos ta
yada zango.anty rabi dasu ameera sukadaukota a
filin jirgi tayi bulbul. Abinta
gwaninsha'awa.dokta yafi kowa tsaraba masu
tsada.bayan taci abinci ta huta ta kira wayan
abba.ya dauka tayimasa sallama kafin yace haba
mama na! watau dagaske kike a legos din kika
sauqa? tayi murmushitace yi haquri abba.ai
bazan dadeba zandawo kwanauku kawai
zanyi,Yace sunyi yawa mamana!kiyi kwana biyu
na tabbatasun isheki warware gajiya.akwai
magana muhimmiyadanake so muyi.tace
shikenan abba Insha Allah jibinzanbiyo jirgi
inade ya soja baiyi fishiba?yace yayiamma ya
huce tunda yayan legos din yabada
haquriinkindawo jibin kinqara wanke kanki.ta
qara murmusawa tace nima na qosa in ganka
abba dukkewarka tadamen.yayi yar
dariya,,,mamana kenan tomuna sauraronki
jibin.sai munsake waya tace toyanxuma zankira
any amina mu gaisa. Toyayikyau.ace ina gaida
halima.zangayamata.sukayisallama takashe
wayan tasake kiran yayanta.sannan ta kira anty
amina duk suka gaisa.tagaya musu inshaAllah
jibi zasu iso abuja.daganan kaduna ta bugasuma
suka gaisa.bayan tagama wayan duk indatakeson
kira ta dubi dokto.dake liqe jikinta.kanatakallona
na fiye surutu koh?yayi yar dariya yace
nibanceba anty.taja habarsa tace ai nasan
bazaka ceba.kai din waya kaika surutu?yaware
ido kamarnata yace ni anty?ko a skul gentle man
antynmu kecemen saboda banda surutu da
yawa.Ta zura masa ido fuskarta cike da
murmushi taceuhm.....yabon kai adai rage dokto
saboda gobe yacemai zan rage?tace qarya!yadan
cunno bakin takamatana dariya.toyi haquri
gettlemen ai nima nasan kaigentle ne.akwai
wasu cakulate a jakata miqominnaqara maka
sunfi ta dazu dadi.yamiqe da gudu yadauko mata
bisa madubi.ta bude ta kwasomasa.tadauki daya
ta bare tace bude bakin insanyamaka...kunya
takamasa.ya tsaya yana kallonta
yanamurmushi.lah!kunya?dan kyauye bude
mana.yakasabudewa sai rufe fuska yake ba zato
tafara fadin bahaka akeyiba...gaskia ba haka
akeyiba dokto!ka bude bakin insaka maka.anty
rabi ta kyalkyale dadariya.sannan mama tagane
tashigo dakin.tadubeta afirgigi.lah anty labe kike
mana?ni yasu mezanyi walabe a sha'anin uwada
danta?akwai dai son kai danbashi kadai bane
dan.amma ankilliceshi shikadaianabasa
gara.adai rinqa adalci...... Tayi dariya sosai tace
kaji hassada,,bude bakinkamubasu haushi.ya
bude tasanya masachocolate.suna ta masa
dariya.ta jawosa jikinta tarungume..anty rabi
tazauna gefen gadon sukaci gabada hira.da
daddare ma bayan cin abinci haka sukataru.a
falo suna kallo suna hira.da yayanta.washegari
bayan cin abincin rana.suna kebe cikin daki da
antyrabi..suna hira.mama tace anty nikuwa
tuntuni nakeson tambayanki wani abu amma
inajin nauyi.tazubamata ido menene shi? tace
don Allah ko kinadatsofaffin hutunan su ameera
da al'ameen?tayimurmushi mama kenan!inbanda
abinki waya isa yarabaki da al'ameen balle
yahanaki ganin hotonsaharda zaki rinqa jin
nauyin tambaya?ni wlh bakiji dadindanake jiba
innaga yanda kike hira da al'ameen dankisai
inrinqa ganin kaman a'ameen dinkine.yanzu
zanbinciko miki nasan dai suna nesa cikin
tsofaffinalbum. Tayi murmushi to nagode!tamiqe
tayita sauqe kaya tazakulo album din tadawo
dashi inda mama kezaune.ta miqa mata tace
gashi duba,,tafara budewatana kallon tsofaffin
hotunansu harta kawo wandaal'ameen yadauka
dasu ameera.yana tsakiyarsu duksuna dauke da
wadataccen murmushi!gabanta yafadi ta bude
ledar ta dauko hoton tazuba masa ido.dagacan
tajiyo muryar anty rabi na fadin nidai
mamatsorona daya kar ganin hoton nan yasake
jefaki waniyanayin da bama fata.kinsan abba
bazaiji dadiba.tanumfasa ta dubeta anty rabi
nayi rashi tace nasani!nakuma tabbata shima
bazai taba mantawa dakeba.tace zai manta idan
haryasamu labarin mummunan halindanake
ciki......takada kai nikuwa banjin wannanaraina
saboda shine mutum na farko dayaqi yardacewar
akan ra'ayinki kika canxa.kullum fadi yakeyasan
kina sonsa..lalle akwai rashin sani a
waniwaje.kowa yayi biris!da zancensa.dan
anaganin zautuwar sanki ne.ta gigitashi.kinga
kuwa banjinakwai wani abu dazai goge sonki
aransa. Ta goge kwallan daya zuba mata.anty
rabi tacekingani koh?gaskia bazan baki hoton
nanba.kisa inyilaifi gurin kowa.tagoge da sauri
tace bawani abu antyrabi kinsan Allah?zuciyata
adake take kanal'ameen.kuma nasan narasa sa
har abada.kuma nikaina bana fatan mu hadu.ina
mai tabbatar miki a gaban ka'aba nayi wannan
rokon wajen Allah.fatanaya amshi rokona.saboda
haka kar hankalinkiyatashi.donkinga ina hawaye
bazan iya hanasuzubowa bane..tunda sun taho
sanadin farin ciki.tacegaskia ne.to Allah zaba
mafi alheri.taceameen.intambayeki mana...waiya
kikaji da akace miki danliti ya haukace?tayi
murmushi ta kada kai tacemaizanji kuwa anty?ai
qarshen alawa qasa kuma dukwanda yataba
qur'ani.bazai shaba anty.Allah yayigaskia
dayace qurani nashi ne kuma shi zai bashikariya!
kinga kuwa danliti yadebota da zafi.wata qilada
haqqina kadai yadauka abin yazo masa da
sauqi.Allah ya shiryi zukatanmu baki daya.ta
amsa daameen tana mata kallon tausayi,80.....
.jirgin safe tabi xuwa abuja tana zaunecikin jirgi
tunanin maganan anty rabi kawaitake.tabude
jaka ta zaro hoton ta zura masaido,,,salon
soyayyar dayake mata take karantowa.tasauqe
numfashi cikin ranta tace inasonka
al'ameenamma bana fatan sake haduwarmu
dakai.tamaida hoton cikin jaka takoma ta
jingina da kujera.taci gabadayiwa Allah tasbihi
har suka iso abuja.tana fitowaharabar taran
fasinjoji ta hangi anty amina a tsaye.Suka
rungume juna zuwa inda tayi parking.suka
shigemota anty amina tajasu zuwa gida.a guje
tashigegidan cikin falo ta iske abba zaune kan
kekensa ta zube jikinsa cike da murna..abba
nah!mamana kenan! andawo lafiya? ta dago kai
tadubeshi lafiya lau.yacenayarda saudi ta
amsheki kinga kumatunki kuwa? tayidariya kai
abba harda zolaya? yace aiba zolayabacekowa
yaganki zai shaida hakan.anty amina tace
nimadai haka nagani.tace to ai hakan akeso ko?
yace kwarai kuwa bakiji dadin danajiba.toya
mutan legos?tace qalau suke suna gaidaku.ina
amsawa.anty aminatace nizan haura sama.Anty
amina tace ni zan haura sama..duk abindakikeso
naci akwai a kicin.tace to anty sai na
hayosaman.tajuya ta haye saman tabasu gu su
gana.abbayace kije kisamu abunda zakici..tace
aibanjin yunwaabba karfe 12 ne yanxu akwai
sauran lokaci.yacekodan ruwa mamana.?tayi
murmushi ta miqe barin dauko abba..ta ajiye
mayafinta tawuce kicin ta zuboabinci filet tanaci
suna yan hiransu.tana bashi labarinumara har
aka kira azahar.takaishi dakinsa
yayisallah.itama taje tayi tasawo tasamesa yana
cinabincinsa gefensa ta zauna ta qara yawan
abincinsunaci tare abba kace zamuyi
magana..amma bakace min komaiba?yace ina
sane inasone ki qaranitsuwa.tace a nitse nake
abba...kagayamin nimainada nawa
maganan.yace toki saurarenidakyau.bayan
tafiyarki umara kawunki alh basiru yabugamin
waya wai mutane sunata zuwa nemanaurenki...
..aurena?yace wlh kuwa kuma abin mamaki duk
yan fandogari ne..bangama nazarin
maganarba..saiga wata wayar tasameni aranar
dakika sauqalegos,,,ake gayamin ko yar gida
zamuyi, Domin yayanki ali yadawo da
maganarku tabaya.nace duk sumin uxiri kidawo
muji tabakinki..nanda nan fuskarta ta sauya
tashin hankaliyabayyana a fuskarta..abba ya
zura mata ido kafinyace..yanaga hankalinki
yatashi?hawaye suka gocemata tace dole
hankalina yatashi abba nah!don ka kawo min
maganar dana jingineta a
babinrayuwata.....kamar ya mamana? aini
addu'ata kenanAllah fidda miki miji nagari kuyi
aurenku.hankalinkowa yakwanta..kuma Allah ya
amsa ganin gamanema Allah ya turasu..ko baki
zabi kowaba inakyautata zaton bazaki qi zaben
dan uwankiba.domin aliyu yacika dan halas
kuma masoyi na haqiqa. aliyuna daya daga cikin
mutanen da bazanmantaba.saboda shine mutum
na biyu daya roqe ninayi afuwa a gareki duk
ranar da kika dawo gidalokacin dakika bi danliti
kuka gudu.al'ameen shine nafarko sai ali.haka
bana manta ranar daya kamo hannunki yakawo
minke.ya durqusa yanema miki,Kuma ya hana
mu daga miki murya saboda baqi
cikingidan.aliyu ya jima yana zubda hawayensa
akanBAKIN CIKIN Qaddarar data sameki.ba
qaramin maisonki bane zai nuna maka irin
wannan yardabamamana.a yanxu kinga zahiri ali
mai qaunar ki ne.donAllah mamana kar kice
bazakiyi aureba! saboda wani dalili nikam
ayanxu banida wani buri face nagankidakin
mijinki.ta kada kai tana share hawaye
wannanbashi ne burinka akaina ba abba,,,tun
banda wayaukagayamin burinka akaina amma
yarinta yasanamaka musu.na sauya maka
tunani.akan dolekadauki zabina.bansani ba
wataqila musun dana maka ne yazamemin
matsala.abba yanxu nayihankali burinka shine
nawa,,,yadda kake sha'awar yamace likita insha
Allahu Allah zai nuna maka ni amatsayin
likita.kamar yadda kake burin hakan tunasali.da
wannan tunanin nadawo umara.kuma
itacemaganar danace zamuyi.don Allah abba
kagoyamin baya akan rayuwar danake ganin
itace zaman lafiyada kwanciyar hankalina,Kuka
sosai takeyi hankalin abba yayi mugun tashiyace
saurara mamana sanin kanki ne idan na
goyamiki baya kikaqi aure,,haqiqa nabi son
raina.ni aganina ai auran bazai hanaki karatu
ba.idan banmantaba hakan kuka shirya da
al'ameen.Allah ne bainufaba inkuwa hakane
mezaisa ki fasa mamana?tace abba a fuska
faram faram,amma zuciya saiAllah.inada abin
gori ajikina wanda yazame mini adolena nesanta
kaina da kowa.don tsira damutumcina.abba na
tabbata ka gane nufina.dangirman Allah kaban
izini nakama karatu.ya kada kaicikin
damuwa.mamana ko wani zai miki gori kamar
yadda kike hasashe na tabbata aliyu dan
uwankibazai miki gori ba.ki sadauqar masa da
kanki kamaryadda ya miki halacci lokacin da
kowa yakyamaceki.tace zan iya yiwa ya ali
komai muddin inadashi har qarshen rayuwata
amma bazan iyaaurensaba.tu nda yanada
mata.kubashi haquri yaci gaba da juriya da
kulawa da iyalinsa yadda yadace.tayunqura ta
tashi tayi waje.abba yabita da kallo
yanasoyakirata amma ya kasa saboda
tausayinta. ana fitowa ta hadu da yayanta yana
shigowa.ta rugata rungume shi yace menene?
takasabashi amsa yajata suka koma dakin abban
yanazaune shiru yana juyayi,,abba meya faru ne?
sukazauna kusa da abban yace ba'ayi komaiba
akan maganar nan ne dana gaya maka masu
sonta daaure.shine tace karatu zatayi amma ban
yarda dahujjojintaba.ina ganin aurenta zai zamo
mata garkuwaaduk inda zata neman ilimin.yaya
soja yace gaskia nesai dai inbata aminceba
akwai matsala dan ita bayarinya bace.tasan
abinda take hangowa kanta,,,so pls abba..idan
bazaka damuba a madadin sauran yanuwana
muna roqonka kabar autanmu ta
nemiilimi.ahankali zata gane aurenma
yanadamuhimmanci.dakanta zata kawo maganar
cikin gidannan so please abba!please!!ya tallafe
goshi shiru jim!Ya dubesu yace.shikenan Allah
yasa hakan shine mafi alheri matsalata kawai
bansan mezan cewa aliba.inajin nauyin yaron
nan.farin ciki ya mamaye matazuciya.yayin da
ya soja ke fadin yayi haquri.Ai ali ya girma babu
wannan haukan yarinta a taredashi kamar
da.kekuma dole kiyi taka tsan tsan andaishaki
kin warke.rayuwa ta zarce duk yadda kikezatonta
saboda haka ki kiyaye.tayi murmushin farinciki
ta matsa kusa da abba nagode abba,,kuma
dayardar Allah zan kiyaye.yadafa kanta yace
Allah yayi miki albarka tace amin.yaya
nagode.yace inatsarabata?kinje kin rabeta a
legos ko?kin kai wa lazydokto.ta rufe baki hannu
biyu lah yaya me kake nufi?ya damki bayan
wuyanta yace are u askin me? aiangayamin
kayan al'ameen yafi tsada da yawa.taceok nasan
magulmaciyar ameera ce babbar kwabo batada
abokin kishi sai al'ameen.sukayi dariya
abbayace umman takice mai gulma?lalle ya ta
riqa.tacigaba da dariya tana cewa ni ummata
bata kishi dakowa.Allah ya jiqanta amin.anty
amina tayi sallama tashigo ta zauna cikinsu
abba yace mutuniyarki taqiyarda.yayanta kuma
yace abarta tayi karatu.tayi murmushi kayi
haquri akan hakan abba Allah saalherine.yace
amin haka nake fata.hira ta tsunke ananya soja
yaci abinci.
BAKIN CIKI 3***8 Ai ali ya girma babu wannan
haukan yarinta a taredashi kamar da.kekuma
dole kiyi taka tsan tsan andaishaki kin
warke.rayuwa ta zarce duk yadda kikezatonta
saboda haka ki kiyaye.tayi murmushin farinciki
ta matsa kusa da abba nagode abba,,kuma
dayardar Allah zan kiyaye.yadafa kanta yace
Allah yayi miki albarka tace amin.yaya
nagode.yace inatsarabata?kinje kin rabeta a
legos ko?kin kai wa lazydokto.ta rufe baki hannu
biyu lah yaya me kake nufi?ya damki bayan
wuyanta yace are u askin me? aiangayamin
kayan al'ameen yafi tsada da yawa.taceok nasan
magulmaciyar ameera ce babbar kwabo batada
abokin kishi sai al'ameen.sukayi dariya
abbayace umman takice mai gulma?lalle ya ta
riqa.tacigaba da dariya tana cewa ni ummata
bata kishi dakowa.Allah ya jiqanta amin.anty
amina tayi sallama tashigo ta zauna cikinsu
abba yace mutuniyarki taqiyarda.yayanta kuma
yace abarta tayi karatu.tayi murmushi kayi
haquri akan hakan abba Allah saalherine.yace
amin haka nake fata.hira ta tsunke ananya soja
yaci abinci.Basu tashiba sai la'asar kowa yaje
sallah.bayan taidar da sallah ta haye gado
tasaka (ear piece)tanasauraren karatun
qur'ani.wucewar minti talatin tanasaurare
dadinsa na ratsata.tashi guda karatun yayanke
adalilin kiran daya shigo.ta duba allon wayandan
ganin waye sunan ya ali ya bayyana.gabanta
yafadi amma ta daure ta danna ok' ta dauka
kawaitaci gaba da saurare.da sallama ta fara.ya
amsadawata muryar dabata saba jiba.tace yaya
ali dangirman Allah......ya katseta da sauri yace
karki hadanida Allah ki cuceni mama!meyasa
baki tausayina newai?ta numfasa idanu suka
kawo kwalla.tace bazaka fahimceni bane ya ali
.....yace babu abinda zanfahimta mama,,,ai
dama kin dade kina azabtardani.axatona yanxu
tunda babu al'ameen zaki iyamaye gurbinsa
dani.ashe bazaki iyaba? wannan yanatabbatar
min ko alama can zuciyarki bata
sonamama.mesa?ta kada kai tace yaya ali ba
haka bane nasan ada al'ameen kadai naso amma
ayanxu hardakai kashiga raina.saboda halaccin
dakamin.wlh dazaniya aure kai zan aura Sai dai
bazan iyaba don girman Allah kayi
haquri..yayiajiyar zuciya yace mesa mama?
kinkuwa san yandatausayinki ya ke bin jinin
jikina?bani da wani buri dayawuce kizama
matata mama don inshare mikihawaye.kimanta
rayuwar wahalar dakika sha canbaya.kiyi tunani
zanbaki lokaci karatu kuwa na miki alqawarin ko
ina kikeso zakije indai kinxama mataagareni.kai
tsaye tace bana buqatar lokaci yaya
ali.ainagama yankewa kaina hukunci..kariqe
matarka zaifima kyau yaya ali..idan kuwa qari
kake sha'awakanemi maras tabo ka aura.tabo?
ban fahimceki bamama.tace bazan jure goriba.ka
kuwa san yauda gobe sai Allah.ba daga gareka
nakejiba ina nufinkishiya da kaidinta.zan iya
mutuwa saboda BAKINCIKI.Duk ranar da matarka
ta gorantamin.wani abudaga rayuwata.kasani ba
ruwan kishiya da asiri idantaso musguna maka
zata iya maka sharri zata iyarufe komai ta
musguna maka da gangan.Yaja dogon tsaki
wannan ne hujjarki mama?ni bankarbetaba dan
nasan amina bazatayi mikihakaba.idan kuwa
harta kuskura zan nuna matabayan tsananin
sonda nake miki zan nuna mata keyar uwata ce
ta jini.saboda haka bake zatayi wagoriba ni
zatayiwa.tace nagode Allah da bakinka ka furta
wannan.ni bazan zama sanadin rabuwarka dayar
uwarkaba yara biyar ba wasa bane yaya
ali.Allahyamin tsari dashiga wannan
tsakanin.kayi haqurikayafemin kullum nayi
sallah zanmaka addu'ar fatanalheri yazama
sakamakon halaccin dakamin.nagode.jitayi
shuuuu!ya kashe wayar karatunda takeji yaci
gaba.ta sauqe numfashi bakaiba ya ali ko
al'ameen neyadawo yanxu bazan auresaba.ku
kyaleni BAKINCIKI Yazamo tarihi a rayuwata.taci
gaba da sauraronkaratunta hankalinta na qara
kwanciya.da zamandakin ya isheta tafito tasamu
anty amina a kicinsukaci gaba da aikin abinci
har suka gama aka kira magaruba sukaje sukayi
sallah.bayan cin abinci dareda hirarraki kowa
yakoma dakinsa.don kwanciya tayizuru tana
kallon hoton dake hannunta .Tsawon lokaci ta
rufe ido tana kallonsa yana matalabarai ta bude
ido a hankali tayi murmushi tana kadakai
tamaida hoton cikin jakarta.tagyara kwanciya
tayiaddu'oi ba a jima ba bacci yadauketa.bayan
kwanabiyu suka samu labarin haihuwar baraka
mamatasami zuwa sunan.saboda tasamu takwara
harta kwana biyu acanma.inna saude ta matsa
tana songaninta don rabonsu da juna tun
dawowanta dagamasar.direban dayakawota
yasake daukanta sukayifandogari.inna tayi farin
cikin ganinta fes kamarbalarabiya yar hutu.daga
can tace akaita gida tagaidasu hajiya hajjo.suna
gangarowa babban layinsu saiga danliti yana ta
hauka afajajan.ya wuce cikin sauriwando a
hannu yanata zamulowa tabishi da kallo arazane
saidata juya sannan ta nutsu!tana kada
kaihawaye suka cika idonta ta matse su tayi
sauri tashare tace Allah sarki duniya. Kamar su
hadiyetacikin gidan sunata kawo mata cima kala
kala.bayan sun gaisa hajiya hajjo tace haba
mama.meyasazakice bazakiyi aureba?ga dan
uwanki kamar yayihauka akanki.yakamata ki
duba. Duk yayi baqin jini gun matarsa dagaji ana
maganartahau fishi ba gaira ba dalili,,don Allah
mama kiyitunani akai.aliyu yadade yanasonki.ta
sunkuyar dakaitace inna ai matarsa tana
sonsa,bai kamata yajawoabinda zai tarwatsa
gidansaba.ni wlh tawa mai sauqice tunda amina
bataso kawai ya haqura..hajiya gaje tace bazai
haqura ba.tunda Allah bai haramta masabaki
amince masa kisha mamaki.tadan kada kai
kudaiyihaquri inna!yaya ali nawa ne ko ban
auresaba.kidaiyitunani kinji mama?zamuyi farin
ciki idan kin amince!tace to.nan tayi sallar
la'asar suka kama hanya dadirebanta.haka suka
qara ganin danliti yanata bilayi.tsince tsince kan
titi.duniya kenan.babbarmakaranta.suka
wuceshi.kafin takwas da rabi na daresuna abuja!
Harya zuwa yanxu da mama tayi nisa a zariya ya
alibai daina damunta da magiya ba.kusan kullum
saiyakirata yagaya mata kalaman dayake ganin
zaisatasamu nutsuwa dashi.itakuwa karatunta
batawaiwaye.haka bata damu tasan kowaba
indai bamaganar karatuba.matar aure sak!kowa
yadauketa domin jikin littafanta da hand out duk
(mrsal'ameen)tasanya saida tashafe shekara
daya batadaqawa ta zama ayi hira.mutane
dayawa sun buqacineman aurenta,amma in suka
bincika sai a gayamusutana da aure.saboda iya
takunta.yanxu suna shekarata biyu kuma suna
tare da wata zainab gida daya.amma ko wacce
da dakinta Allah yasani duktsawon lokacin
zainab na matuqar kaunar mama.dukda cewar
tasan ta girmeta saidai rashin samun hadinkan
mama yasata cijewa.illa iyaka su gaisa yar
asalinkatsina ce tanada kokarin kamun
kai.saudayawatanazuwa aron text books.din
mama don zumunci ya qullu amma ina!mama
bata maida hankaliba.Yau litinin sunada
masaniyar zasu (practical)ofishinbabban likita a
fannin da suke karantawa.wataucutattukan
dasuka shafi kai.duk sun hallara acikinclinic din
dake cikin babban asibitin koyarwa nashika.su
goma sha biyu ne cif!amma likita bai riga
yaisoba.saboda haka mama tace zataje takai
wani (assignment) kafin likitan yaxo.zainab tace
karki tafikusha bam bam sakeena.kinsan doctors
dinnan basuda sauqi.balle wannan bamu taba
ganinsaba.tacekarki damu zainab bazan
dadeba.kin karba idanlokacin yawuce ta juya ta
fita ta wata kofar.kamarhadin baki ya bayyana
ta kofar gabansu.ya wuce su zainab yafada ofis
din.wannan ya tabbatar musushine DR
SAIFULLAHI.Da aka turasu gunsa.nandanan
hankalin zainab yatashi gashi batada
numbanmama bare taqirata.hakanan tabi ayari
suka shige ofisdin sukayi gaisuwa.ya sauqe gilas
yaqare musu kallosannunku fa likitoti.duk suka
fara murmushi gabansu ya rage faduwa da alama
zaiyi sauqin kai.amma dukda haka hankalin
zainab tashe yake. Ya miqo musu farar takarda
yace musu write urnames here!wato su rubuta
sunayensu.nafarko yaamsa yarubuta ya miqa wa
dan uwansa amma mamabata dawoba.ya karbi
takardar ya duba yana shirinajiyewa zainab tace
sorry sir!akwai sauran daya batashigo ba.taje
kai assignment sir.yadan tabe baki yace ko?may
b assignment yafi mata wannan
muhimmancishisa bata damuba.jiki na rawa tace
no sir!yanxu zatadawo.mujirata kenan?tadan
sunkuyar dakai tace sorrysir! Ya numfasa yace
well mu bama jira haka qa'idartake.saboda mu
masu ceton raine mai ceton rai kuwabaya jiran
kowa kuna iya zama.kowa ya nemi wajen zama
suka kewayesa yafara daga (files) kenan
mamata murda kofar cikin sanda da tsarguwa
tashigo.zainab taruntse ido tace thank god.!ta
tako ahankali ta tsaya a gaban tebur din tace
morning sir!yadago a hankali ya dubeta.kai!ta
maza kawai yayiamma jiyake kamar zai zube a
qasa,Ya zura mata ido,,tamkar yadda ta daskare
a tsayesai dai iya takun mama yasa tayu kamar
bata tabaganinsaba.tayi dan yaqe sorry sir!nakai
assignmentne,pls sorry sir!ya wani sauqe
numfashi bironsa nacoge bisa kuncinsa yace
gaskia ba haka akeyi ba!bahaka akeyiba ni
yakamata ki fara gani kafin ki tafi!.tace sorry
sir! yace zauna takoma kusa da zainabtazauna
tace nagode!sauran students na mamakinabunda
yafaru.kalamansa na farko kwarai yabasudariya
sai dai ba'ayi wa oga dariya.shiyasa
suketayiacikin cikinsu.zainab ta rada mata anfa
rubutasunaye.don haka suna miqewa tace sir!ni
ban rubuta sunana ba ya zuba mata ido yace
nasani ki zaunakawai.ta zauna a sanyaye.aka
fara kiran masu ganinlikita kowacce tambaya sai
yace makararriya bamuamsa!ya kuwa ji
amsa.dan ko ajikinta fes take budebaki ta
turance shi.duk yadda yaso ya rikirkitata.har
akafara musu dariya.anan suka kai qarfe dayan
rana lokacin tafiyansu yayi.Mama tasake fadin
sir!my name...yace owk myname? AL'AMEEN
SAIFULLAHI LAFAI.Tace sir inanufin bansa
sunanaba.yace bazaki rubuta sunankibakinxo
latti wannan shine horonki kinxo latti.ya
juyakujera yace zaku iya tafiya.duk suka fice
zainab tarada mata karta fito ta tsaya ta bashi
haquri su gyarota.yasan duk sun fita amma
yanaji cikinxuciyarsa tana nan.yasake wawan
numfashi ya juyosuka xubawa juna ido..kafin
yace mafarki nake kogaske sakina?idanunta
suka tara kwalla.damuwa tabayyana qarara a
fuskarta.kuma ta rasa yadda zatayikawai saita
juya zata fita.ya sanyaya murya ya kirata
sakeena?ta tsaya kyan !kafin ta juyo fuskar nan
babuannuri.yace zoki rubuta sunanki.ta tako a
hankali tatsaya a gaban teburin ta rubuta sannan
tafice cikinsauri.ya lalubi kujera a hankali ya
zauna fadi yakecikin ransa mafarki ko wasa?
yadauko takardarsunayensu.sakeena uwais
malami! Ya runtse ido tamau..kirjinsa yaci gaba
da dokawainnalillahi wainna ilaihi
rajiun.sakeena? yatashi da sauriyabar ofis din ya
shiga wani ya murda kofa.da lawalke zaune shi
kadai yana rubuce rubuce..ya dubeshi
famurmushi kai likita ya akayi ne?ya zauna
hankalitashe idanuwa sun kada yace yau naga
abun mamaki dr lawal!ya zura masa ido cikin
patients da akaturama?yace students aka
turamin yau kuma nagasakeena acikinsu!
shikansa saida ya girgizasakinarka?ita dr lawal
gaba daya na rude ta maxanayi kar yaran su
gano ni.amma bakaji bugunxuciyataba .yace
dakata!a wani yanayi kaganta?da alamar akwai
aure?yace matsalata kenan.bansankoda
aurenba.wani abin mamaki yanda ta nunatamkar
bata taba ganina ba.dan Allah?yace wlh todaaure
kenan.ya yamutsa fuska kadaina gayamin
drlawal please!ya zura masa ido baki sake kafin
yacekai likita ka nutsu kanada abun yi ne
intanada auren? ya dubi zoben alqawarinsu yace
zan bincika da alamasa'a ce tadawo dani qasar
nan sha Allahu sakeenatadawo gareni.Dr lawal ya
numfasa!yace to Allah yasa idan kumatabada
aurenta muke wannan maganar astagafurullah!
katashi ne?bai amsaba yaga ya miqe yabar ofis
dinyabishi da kallo ya xabga tagumi a ransa
yace munshiga uku!meya dawo da yarinyar nan
zata wargazamana oga?ofis dinsa yakoma
tunani ya isheshi.yazanyi da rayuwata yau idan
sakeena nadaaure?menene yasa ta nuna min
halin ko inkula?hakanyanuna tanada aure?yayi
saurin kauda wannantunanin no ba haka bane ai
hawaye ya taru a idontame wannan yake nufi?
yakada kai gaskia bansani ba aina zansamo
gaskiayar lamarin?abufa yarikicewa al'ameen
yakasa sukuni gida da ofis.har cikin bacciyake
ganin mama gaban teburinsa tana fadin
morningsir!kafin sati ya zagayo ya
sukurkuce.haka al'amarinyake gun mama.gaba
daya nutsuwa ta matatsuntsu.tun aninta yaya
zatayi da al'ameen takaudaduk wani alaqa
dazata shiga tsakaninsu inbata karatuba? Haka
kuma abin na bata mamaki ganin har a
ka'abatayi addu'a karya sake hadata dashi gashi
sun hadunme hakan ke nufi?tambayar na hanata
bacci.hakakota dauko hotonsa take kasa kallo
saboda tsoronkarya bata amsa.zainab kanta ta
lura sakeenanadauke da wata damuwa.a yan
tsakanin nan tana yawan zama shiru cikin mota
kafin ta qaraso gida.kocikin aji tarage bada
yawan amsoshin da datakebayarwa.abin
yadameta sai dai bazata iya tunkararsakeenaba
ganin ba fuska.kuma tana kwarjini.kamarko
wacce litinin yau ma tazagayo clinic din
masufama da larurin kai qananan yara.ranta
bace tashigo gun.zainab na lura da ita.tunda
suka shigo bata yardasun hada ido da al'ameen
ba.dan ko gaisuwardasukayi cikin jam'i bata
tankaba.ya tura musutakarda yace kowa yasa
hannu wato signing Bayan sun kammala aka fara
shigo da masu jinyayariyar sunanta sakeena
ahmad file nata na tsakiayasa aka dawo dashi
sama albarkan sunan akafarakiranta bayan
mahaifiyar yarinyar taqare bayanintaakan ciwon
yar(convosion) kasen cewar zuwansuclinic
nafarko.sunja tsawon lokaci tana amsa
tambayoyi daga dr.tashin farko mama yafara
jefawatambaya,sakeena tunda sunanku daya
kezaki faracewa wani abu!karo na farko datayi
masa duba tadauke kanta.da turanci suke
magana.ki bayyanamana me ake nufi da suma?
da abinda ke kawota?tayishiru kamar bazata
tankaba bawai dan bata saniba sai dan jin
haushin fara kiranta da yayi.ganin ya zubamata
ido yasa tafara zazzago masa bayanai yadda
yakamata.yace bai gamsuba.wazaiyi bayani
wandayawuce na mama?ya kallesu daya bayan
daya inafatadai da likitoti nake magana?93-duk
suka amsa yes sir"banda mama yace to
kuyimagana mana kuna nufin kunfi yarda da
sakeena?Suka fara sosa keya suna kallon juna
ya tabe bakiyace wannan son kai ne'su kayi yar
dariya mama takirne zainab ta daga hannu tace
sir zan dan kara yacego ahead ta kara wasu yan
bayanan masu kama dana mama ya dube ta yace
muntafi mun dawo ke nan kunfini gaskiya to bari
mu ci gaba kar mu bata lokaci ko?yaci gaba da
bayanai da tambayoyi har lokacin tashiya yi
karfe daya daidai suka sallame shi tare dayimasa
godiya cikin karfin hali ya nuna zainab yace
tatsaya yana son ganinta na minti daya kawai
duk suka fice suka barta tana yan mazurai gaban
ta nafaduwa.sun dan jima shiru yana wasu yan
nazari kafinya dubeta yace ke ce zainab tace yes
sir yaceuhm...ko kina da alaka da sakeena tace
eh sir gidanda muke ma daya ne,94-yace good
don Allah ko kin san tana da aure kobata da shi?
tace uhmm..toni dai gaskiya ban sankomai game
da ita ba amman da alamu tana da auredon jikin
littattafan ta ma ni kan ga tana rubutawakoga
wannan pharmacology din ma na ta ne"ta
mikamasa ya bude shafin farko ya duba "mrs al-
amin? Ya tambayi kansa ya dube ta da sauri kin
taba ganinsaya zo gunta tace wallhy ban sani ba
ta kan sami bakiamma da yake ba wata
mu'amala take da kowa bashiya sa ba zan iya
tantancewa ba ko yana zuwa yasauke numfashi
yace zainab idan bazaki damu ba kigaya min
inda kuke ki kuma bar min littafin nan tace shi
ke nan sir nan take taba shi adirea ta bar
masalittafin ta fice dauke da wasi wasi mai yawa
cikinranta,ta tabbata oga ya kamu ne to amma
zai shaguduma muddin ya tinkari sakeena
fargabar ta dayace karbar littafin nan a hannunta
mece ce manufarhakan?Allah yasa ba amfani zai
yi dashi ta wata hanyar ba don ya cimma burinsa
yasa jawo matabakin jini su daina gaisawa da
sakeena babu abindabata sakawa ranta ba. Haka
mama ta sha jinin jikintatunda taga. al-ameen
ya tsaida zainab sai dai batafargaban komai don
ta san zainab bata san kamai baa game da ita ba
shi yasa hankalinta kwance ta isa gida tayi fakin
motar ta cikin inuwa ta fito ta budebangarenta
ta shige ta mayar da kofa ta kulle bayangabatar
da sallah ta danci abinci ta maida kai bisa
filotana ta sakar zuci game da sake haduwar ta
da al-ameen, a haka barci ya sace ta har zuwa
uku da rabita farka ta nufi bayi ta fito da alwala
ta gabatar da la'asar daga nan ta kawo azkar ta
dora kai tsayelittatafanta ta kwaso don yin wasu
aiyukan gida daaka basu cikin wayar ta take. Ta
birauzin ta yanargizo duk ta kosa ta gama don
karfe biyar take dawata lakcar Babu zato taji an
kwankwasa kofar ta ta dago kaita dubi kofar
tace ana zuwa ta karasa dan rubutun datake yi
ta taso ta murda makulli ta bude kofa gaban
taya yanke ya fadi tabi mutumin dake tasye da
kallo tadafe kirji tace inna-lillahi wa inna ilaihir
raju'un tace niya ce ni kuma nace Assalamu
alaikum ta hadiye miyau da kyar taamsa sallama
dole yace zan iyashigowa? Ta tsaya jim kafin ta
koma gefe ta bashiwuri ya shigo ita kuwa tana
daga tsaye a bakin kofabata motsa ba shi ma bai
zaunaba ya zuba mata idoyace ya karatu tace
lafiya yayi dan murmushi yace ".mrs al-ameen
ke nan ta kara dubansa a razane amma ta kasa
cewa komai ya kara matso ta ya sake fadinkin
taba ganin aure babu zoben alkawari? Ya nuna
nayatsan sa kinga nawa nan bai taba rabuwa da
yatsanan ba saboda muhimmancinsa sannan ban
tabaganin inda mata ke gudun mijin bs idan da
amana airuwa za zai dafa kifi ba mama ya
kamata ki maida zoben ki kafin mu ci gaba da
tambayar bayan rabuwa!Ya laluba aljihun sa ya
fiddo shi cikin gidan sa yabude ya ciro shi tun
daga lokacin. Idanuwan ta sukafara tara kwalla
kirjinta kamar zai tsage tana tsayesototo har ya
kamo yatsunta da zoben yake ya maidashi
mazauninsa shi kan sa kwallan ne cikin idonsa
yayi ta maza ya hadiye su yayi murmushi
yacegodiya ta tabbata ga Allah daya nuna min
wannanrana amma zai fi kyau ki zauna sakeena
inji kalamanbakin ki, tace Al-ameen kazo ka tafi
yace in tafi waisakeena laifin me nai miki ki ka
daina so na ne tacenace ka zo ka tafi yace
bazan tafi ba sakeena sai kin gaya min dalilin da
yasa ki ke amfani da suna na amatsayin mijinki
alhalin ba kya sona ki gaya min inji, ta zuro
masa ido kwalla suka fara zuba" ni nayiamfani
da sunanka?ya daga littafin dake
hannunsashafin farko yace mene ne wannan?
Idan kuma kinamusu ki kwaso gaba daya (texs
book) din ki dahandout a duba takara razana
rashin gaskiyarta yabayyana karara bakinta ya
mutu kwalla suka ci gaba da zubo mata ya
sanyaya murya yace. Sakeena kinsan ina sonki
munyi wa juna alkawurra masu damaban taba
tunanin zaki yaudareni ba har kwanan gobekuwa
ba na kawo hakan a raina ni na san yanzu
kinwarke kin dawo cikin hayyacinki sosai tunda
har ki kagane ni ne mijinki,amma me yasa da
aurenki ya mutu ba ki nemeni ba ki ka barni ina
wahala? Nayi rantsuwako ki duke saboda
tsufanki sonki bazai shafezuciyata ba kuma zan
karbe ki a matsayin matardana fi so a rayuwata.
Dubi. Zoben nan sakeenagirman dana karayi yasa
ya yi min kadan ammasaboda ba zan iya rabuwa
dashi ba na kai shi aka yanka min na kara bude
shi ina sa shi a haka dubenisakeena har yanzu
al-ameen dinki ne sak babuabinda ya sauya kar
kiji nauyi ko kunya kin kini abaya wallahi ban
daukeshi a matsayin laifi ba muddinki ka amince
min zan baki mamaki!, Ta goge kwallata ce
banyi aure ba al-ameen karuwanci nayi kuma da
diro har ciki na haihu cikin dana zubar kuwa ban
sanadadinsu ba me za kayi dani me zai sa in ne
mekabayan cin amanarka,amanarka kuma ta cini
me zakayi da kazama irina? Ni abar kyama ce ni
kaina nasan ni najasa ce balle wani,koba ka jin
warin.... Ya daka mata tsawa ya isa haka
sakeena ta cebai isa ba dole in bayyana maka ko
ni wace ce don katabbatar da cewa babu abin
sha'awa a tattare danikyan dan maciji gareni
idan kai ba ka jin warin danake ji ni na san ina
yi kuma....bai san lokacin da yaciro hannunsa ba
ya dalla mata mari duk suka dauke wuta ita da
shi,tana tallabe da kunci ta zuba masa idoya
nuna mata yatsa fuskar nan kaman gobara yace
kidaina ci min fuska sakeena....!ya kasa kara
komai saiya kama hanya ya fice cikin sauri ta
sulale kasa batasan lokaci da ta fasa kuka ba ji
tayi an rungumeta tamurya mai sanyi na fadin
sakeena! Sakeena mene ne ta cira kai ta dubi
mai magana Zainab ce ke tallabe daita ta kasa
magana sai kuka takeyi hankalin zainabyayi
mummunan tashi don taga shigowa da fitar Dr
al-ameen cikin ranta. Tace na shiga uku Allah
yasa bani na haddasa wannan fitinar ba hakan
yasa ta damukwarai taji musabbabin kukan da
mama takeyi, ta kwashi lokaci tana rarrashinta
kafin ta shawo kantatayi shiru amma hawaye
basu daina sauka basakeena kina cikin damuwa
ni tuntuni na san hakaamma Allah ya zuba miki
zufin ciki na kasance inamatukar kaunarki
sakeena zan si ki gaya min keketsakaninki da
Dokta yake neman wasu bayanai da suka shafe
ki, Ta goge kwalla ta kadai kai tace ke
yatambaya tace gaskiya ni ce amma na gaya
masa kinada aure harna bashi littafinki da ki ke
rubuta sunanmijinki don ya tabbatar kiyi hakuri
in ni na haddasamiki wannan fitinar sakeena
banyi zaton zai zoba donna tabbata gaskiya na
gaya masa tace bakiyi laifi ba zainab hasalima
shi ne al-ameen din....98-Ta kara dubanta a
razane what? Nan da nan tagaggauta tuna baya
ranar da ta fara shigowa ofishinirin razanar da
suka yi na ganin juna da yaddasunanta ya zauna
bakin sa haka tabbas ya fadicikakken sunansa
sunji, ta sake dubanta tace damaoga ne mijinki
sakeena ? Kai amma kinyi sa'a me yasa ki ke
gudunsa kuma da alama kun dade rabonkuda
juna tace ban aure shi ba zaina amma
munyisoyayya ta ban mamaki mishkilar da aka
samu ita ceboyayyen labarina wanda ya tilasta
min maida kainadodanniya ga kowa musamman
da namiji, cikintausayi tace Ayya koda ban sani
ba na tausaya maku ta goge hawaye haka idan
kika ji baza ki so in rabikowa ba rayuwa ta za
tafi min kyau ni kadai dongudun abinda kaje ya
dawo" ta kara rungumota tace kidaina kuka
sakeena rayuwa ita shirin Allah ce dukyadda ya
tsaro maka baka iya tsallakewa yanzu bagashi
ya wuce ba? Tace ai ya dawo tunda al-ameen ya
dawo rayuwa ta ni kuma bazan iya auren sa ba
ke kosabo dame shi ya miki laifin? Ta kada kai
bari kiji agurguje take nan ta bayyana mata
yadda rayuwarta takasance a baya Tuni zainab
ke kuka har da shashekatace sakeena kinga
rayuwa Allah ka rabamu dasharrin mutun da
aljan tace amin zainab to kin ga ina ni ina aure?
ba komai nake gudu ba gori yanzu al- ameen ya
daukeni ya hada da matarsa idanbatakwarai
bace duk ta yadda zatayi ta binciko asalinazata
yi don ta muzguna min ba zai yuwu ba zaina
bazan iya jurewa ba dole in nemi.
BAKIN CIKI 3***9 yace karki damu zainab duk
inda take yau zandawo da ita bazatabar
karatunta saboda ni ba!ya juyaya fada mota kai
tsaye ya dauki hanyar kaduna yatabbata bata
wuce gidan yayanta Abdurrahman ko datambaya
zai kai kansa gidan tunda yasan anguwar.
Awannan lokacin ita mama ke shiga get din
gidan yayi fakin ta fito jaye da jakarta ta
kwankwasa kofa akabude takwararta ce tabude
nan da nan ta rungumetaanti mama oyoyo tace
oyoyo name sake ina su ihsansai gasu sun
kwaso a guje suka rungumeta dukkansukayan
islamiyyar da suke zuwa ne a jikin su tace
haladaga ismaliya kuka dawo yanzu suka amsa
eh safiyya ta fito daga kicin ta tarbeta maraba
da doktakece haka da almuru ina fatan dai lafiya
tace qalaumatar yaya suka wuce da jakarta cikn
daki basugama gaisawaba aka kira sallah duk
suka tashi yinalwala ta kai raka'a daya ta jiyo
muryar yayanta yanafadin naga motar mama a
waje ta zone safiyya ta amsa ta zo gab da
magariba magariba lafiya tacehaka dai tace wai
gobe ma abuja zata wuce yayi danmurmushi
yace mama manya kwadayin ganin abbane ya
motsa tana ina tace tana sallah ne suka
wuceshima yayi alwala yayi sallar ya fito ya
samu mama afalo da y'ayanta bayan sun gaisa
ya tambayeta babu karatue kika baro school tace
eh dan break mukasamu gobe da jibi shine nace
bari inje inga Abba yacekin kyauta amma abba
ya hanaki ki tuko mata zuwawani gari ko?me
yasa baki kira an turo miki direbaba?kuma ance
gab da magariba kika iso tace sorryyaya na kosa
in taho ne yau din don in kwana biyu a can, 104-
yayi yar dariya yace to Allah ya kaimun
gobenlafiya sai in nemi mai tuka miki motar
muje cin abinciko duk suka nufi tebur inda
safiyya ta shirya gara kalakala suna cin abinci
suna hira mai gadi yayi sallamaya shigo yace
ana sallama da mai gidan babu batalokaci ya aje
cokali ya fita yana tsaye jikin motar sa daga
wajen gate yaya Abdul rahman yayi sallama
yaamsa ya dan zura masa ido kamar ya taba
ganinfuskar ka gane ni yayayace kamar na san
fuskar dadaewa yayi dan murmushi yace al
ameen ne ya kamabaki kana nufin dokta. Ni ne
yaya yace ikon AllahAllah bisimillah shigo da
motar yace kafin nan yaya ina fatan sakeena na
nan gidan? ya numfasa yace tananan shigo,yasa
mai gadi yabude get ya shigo da motarsa.ya
jagoranceshi zuwafalon gidan.gaba daya suka
shigo da sallama.hankalinsu ya koma kan
bako.zumbur mama ta miqe dafe daqirji ta zaro
masa ido jim! Sannan ta zura da gududaki
hawaye na fita.safiya ta cika da mamaki.a haka
suka wa baqon sannu da zuwa suka gaisa.yara
masuka gaisheshi.suka dauki abincinsu suka
wucedakinsu.ita kuwa safiya kicin tashiga ta
hado wa bakokayan kusa da baka.yayinda suke
gaisawa da yayaabdulrahman.amma mamaki ya
ishen fa.wai yaya ne?takenan ya fede masa biri
har wutsiya.yayan yace Allah mai girma da
daukaka.tsarkakakken sarki maishirya yadda
yaso.inbanda abin mama meye na boyemin?zan
mata dole ne?saidai in nuna mata
abundayakamata idan ta dauka ya yi mata
kyau.idan batadauka ba laba'asa.amma zancen
tabar karatu mabaitasoba.105.Yace nima abinda
nagani kenan.don me zatabarkaratunta?
hankalina yatashi dana koma akace
tataho.shiyasa nabiyota inbata haquri.ta
komamakaranta bazan zama sanadiyyar rasa
komainataba.nasan ina matuqar sonta zanci
gaba da jurewakuma bazanyi dana sani ba!idan
na mutu akan sonta.pls yaya ka kirata na
roketa,tazo mukoma kardare yayi.gobe in Allah
yakaimu taje lakcasdinta.bana ma so abba
yaji.maganarnan .don karya cezai tilasta
mata.yaya yayi shiru jim! ya sauqenumfashi ina
zuwa.ya miqe ya bita dakin.tana ta rusakuka
kamar an aiko mata da mutuwa.duk ta dagawa
safiyya hankali ta riqeta tanaso tamata bayani
ma yagagara.sai fadi take ni bazan aureshi
ba.yazaunagefenta yace to wayace dole ki
aureshi?da kikazo nankika rufe min abinda
yafaru.kina ganin shinemafitarki?to shima baya
biyoki bane donya tilastamiki aurensa!soyake
yamai dake makaranta.kici gabada
karatunki.saboda haka kitashi kije ki sauraribaya
ninsa..idan harkika yarda kika koma
makarantanamiki alqawarin ko abba bazaiji
maganar nan,Na miki alqawarin ko abba bazaiji
maganarba.balleyasan al'ameen na
numfashi.tashi kije sharehawayenki.safiya ta
goge mata tace dama wannan nematsalar?to ta
wuce tunda shima ya haqura.miqe kijekarki
barshi zaune.ta yunqura da kyar ta mike
sukabita da kallo.yayanta ya numfasa ya dubi
safiyya data zabga tagumi yace idan kuwa har
mama bata yarda taauri al'ameen ba lalle babu
wanda zata aura aduniyarnan!tace ko?yace
gaskia safiya yadda mamataso al'ameen banjin
antaba soyayya irin tasu.keqarshen abin dubi
yanda akemata kallon ta lalaceshibai
damuba.zanso su daidaita da al'ameen saboda
ina sha'awarsu tare.tace ubangiji ya sa
hankalintayadawo jikinta tagane muhimmancin
auren da zatayiya amsa da amin.salalau salalau
tashiga falon tayitsaye kanta na qasa tana share
hawaye.ya zuba mataido jim!kafin yace ki zauna
mana. Yace nima abinda nagani kenan.don me
zatabarkaratunta?hankalina yatashi dana koma
akace tataho.shiyasa nabiyota inbata haquri.ta
komamakaranta bazan zama sanadiyyar rasa
komainataba.nasan ina matuqar sonta zanci
gaba da jurewakuma bazanyi dana sani ba!idan
na mutu akan sonta.pls yaya ka kirata na
roketa,tazo mukoma kardare yayi.gobe in Allah
yakaimu taje lakcasdinta.bana ma so abba
yaji.maganarnan.don karya cezai tilasta
mata.yaya yayi shiru jim!ya sauqenumfashi ina
zuwa.ya miqe ya bita dakin.tana ta rusakuka
kamar an aiko mata da mutuwa.duk ta dagawa
safiyya hankali ta riqeta tanaso tamata bayani
ma yagagara.sai fadi take ni bazan aureshi
ba.yazaunagefenta yace to wayace dole ki
aureshi?da kikazo nankika rufe min abinda
yafaru.kina ganin shinemafitarki?to shima baya
biyoki bane donya tilastamiki aurensa!soyake
yamai dake makaranta.kici gabada
karatunki.saboda haka kitashi kije ki sauraribaya
ninsa..idan harkika yarda kika koma
makarantanamiki alqawarin ko abba bazaiji
maganar nanba.Na miki alqawarin ko abba
bazaiji maganarba.balleyasan al'ameen na
numfashi.tashi kije sharehawayenki.safiya ta
goge mata tace dama wannan nematsalar?to ta
wuce tunda shima ya haqura.miqe kijekarki
barshi zaune.ta yunqura da kyar ta mike
sukabita da kallo.yayanta ya numfasa ya dubi
safiyya data zabga tagumi yace idan kuwa har
mama bata yarda taauri al'ameen ba lalle babu
wanda zata aura aduniyarnan!tace ko?yace
gaskia safiya yadda mamataso al'ameen banjin
antaba soyayya irin tasu.keqarshen abin dubi
yanda akemata kallon ta lalaceshibai
damuba.zanso su daidaita da al'ameen saboda
ina sha'awarsu tare.tace ubangiji ya sa
hankalintayadawo jikinta tagane muhimmancin
auren da zatayiya amsa da amin.salalau salalau
tashiga falon tayitsaye kanta na qasa tana share
hawaye.ya zuba mataido jim!kafin yace ki zauna
mana.106-Ta nemi wuri ta zauna ya numfasa ya
karamatsowa gareta ya sanyaya murya yace
sakeena nasan na tafka kuskuren daukar hannu
na mareki inarokonki ki yafe min kuskuren
danayi amma ina so kisanu ba laifi na bane
miyagun kalaman da ki ke jifarkanki dasu sune
kunnuwa na baza su iya ji ba, zuciya ta baza ta
iya daukar girman kalaman da bakinki
yakefurtawa ba maganganun sunyi muni a ido
sakeenadon girman Allah kar ki sake danganta
kanki da irinwadannan kalaman don ba su
kamace ki ba maganata gaba da nake so ki sani
sakeena itace tun farko nine nayi sanadiyyar
rushewar komai naki burin ki dana iyayenki shine
ki zama likita Amma na cusa miki sona ki ka
dauki dukkan ra'ayinaki ka bar wanda su abba
suka shirya miki ba ki dawani buri face aure na
nayi ruwa nayi tsaki dole kikirani in dawo muyi
aure kafin ki fara karatunki ki kaamince min a
karshe wani ya sami damar dagulalissafinki ya
rushe komai ya lalace ni ne silar rugujewar
komai naki sakeena saboda haka a yanzuba zan
sake zama sanadiyyar barin karatun ki ba.Ta
goge kwalla ta dube shi na yan sakwanni
kafintace na amince ya sauke numfashi yace na
godeamma ina so in roki alfarma guda biyu bata
dainakallonsa ba tace zan amsa maka idan masu
yuwuane yace ki amince zaki bar zobe na a
yatsanki kiamince zaki ci gaba da amfani da
suna na a matayin mijinki da gudu wani hawayen
suka zubo bisakuncinta ita kanta bata san dalili
ba haka murya takerawa tana fadin suma na
amince maka idan har bazaka taba nuna kai ne
al-ameen ba da sauri ya amsabazan nuna ba i
promise yau babu wanda zai sani drlawal ne
kadai. Ya sani kuma zan kwabe shi ya rike min
sirri amana,108-tace shike nan", zamu iya tafiya
yanzu tace bariin tambayi yaya suka mike tare
shi ya zauna a kujeraita ta wuce kiran yaya.
Yaya abdul-rahman yaso sukwana da sassafe
suyi sammako amma al- ameen yanuna ya fison
su tafi saboda haka dole ta bar motar tagoben
direbansa zai kawo mata suka kama hanya karfe
takwas saura yan mintoci sun jima shiru a
motababu wanda ya tanka shi al-ameen bakin
ciki ne yacunkushe zuciyarsa yana tunanin yadda
zai sarrafarayuwar ba tare da abinda yake so ba
alhalin yanaganinta kusa dashi ita kuwa mama
tausayinsa ne yahana mata magana harga Allah
ta san al-ameen karfin hali yake yi kawai
shiyasa bata so sake haduwarsuba sauke
numfashin da yayi shi yaja hankalintazuwa
gareshi ta dubeshi yana kada kai gwanintausayi
jikinta ya kara sanyi tayi shiru tana tunaninme
zata ce masa? Ya dan sanyaya ransa jim
kadanta sake dubansa tace yaranka nawa kamar
daga sama ya ji tambayar don haka ya dan
dubeta sukahada ido ta yi dan murmushi shi
yasa shima ya daukekansa yana murmusawa
kafin yace yarana dozin Ido waje take kallon sa
kai dokta dozin fa ka ce ?sunyi yawa ne tayi yar
dariya tace naji abin ne kamarna debo su a
kasuwa don Allah yaranka nawa yacebiyu ne....ta
yi fit ta katse shi Ameer da Ameera ko?Ya dan
dubeta ya kadai kai waleed da waleeda tace
azatona mafarkinka kullun ka sami ameer da
ameera me yasa ka sauya ra'ayi tai masa susan
inda yakemasa kaikayi kai tsaye yace kin san
yadda mafarkiyake. Ba kasafai yake zama
gaskiya ba,109.Ta sunkuyar dakai shiru shima
shirun yayi kamarbazai tankaba.sannan yace tun
ranar dana daina jinmuryarki a waya na tsinci
kaina cikin wani hali dabazan iya misaltawaba
sakeena!da taimakon Allah dataimakon mamina
nasamu yar nutsuwa.hankalina yadaidaitu akan
qaddarar data sauqo min.bayan narasa ki
nakoma rasha.can na kwashe shekara hudu
banwaiwayi gidaba.sai dai inkira waya.a cikin
shekara tabiyar goggo ta rasu mafarin zuwa na
gida kena(inbakumanta ba goggo itace kakarsa
daya fara haduwa damama a kofar gidanta
farkon littafin)shima saidan nakwashe sati biyu
nasamu zuwa.iyakata minna wajensu daddy nayi
sati daya adaddafe nacezankoma.mami tace
bazan komaba saina fidda mataraure.nace banda
wadda nakeso alokacin suyi minuzuri zuwa wani
lokacin.109-ta sunkuyar da kai shiru shima
shirun yayi kamarbazai kara tankawaba sannan
ya ci gaba tun ranardana daina jin muryanki a
waya na tsinci kaina cikinwani hali da bazan iya
kwatanta shi ba sakeena dataimakon Allah da
taimakon mamina na sami yarnatsuwa hankalina
ya daidaitu akan rungumar kaddarar da ta sauko
min bayan na rasaki na komarasha can na
kwashe shekaru dudu ban waiwayi gidaba sai dai
in kira waya acikin she kara ta biyar Allahya
dauki ran gwaggo mafarin zuwana gida ke
nanshima sai da ta kwashe sati biyu na sami
zuwa iyakata minna wajen su dadi nayi sati daya
a daddafe nace zan koma mami tace bazan koma
ba idan har banfidda matar aure ba nace banda
wacce nake so alokacin suyi min hakuri zuwa
wani lokaci Duk suka hade min kai sukace
atabau basuyardaba.akan dole na basu zabi,,dan
na farantamusu.ba ayi kwana ukuba dady
yasamo min yarabokin kasuwancinsa a suleja
sunantaruqayya.dakansa yadaukeni yakai ni
gidan.tsakani daAllah ruqayya batada makusa
amma saboda hankalina ba a kanta yakeba naji
raina yanabaci.zucita namin sake sake akan
alqawuran danadauka miki.wlh sakeena bantaba
kawo wa rainakindena sonaba cikin
raina.shiyasa nakasa kallonruqayya a matsayin
matar dazan aura.saidai bandenabin umarnin su
daddy ba har akasa mana rana.cikin watanni
biyu aka daura aure.batare da
munfahimcijunaba.saboda rashin kulawa irin
nawa.dukda nasanita ruqayya nasona.kumatana
iya qoqarinta wajennunamin ta amince dani
bawai hadamuakayiba.tausayi takeban idan na
kalleta na tuno babualamar sonta cikin
zuciyata.110 Bawai rashin sobane yahanani
rabarta a matsayinmatata ta sunna ba.a a
tausayin danakeji shikehanani aganina ban mata
adalciba.idan natabata alhalibabu soyayyarta a
zuciyata.abun yadamen kamaryadda na lura
itama tanada damuwa cikinzuciyarta.amma son
xuciya ya hanani magance matsalar.ruqayya
nada kunya kuma duk abinda ta lurainaso zata
ce gashi basai na tambaya ba.munkwashe sati
biyu a haka nafara shirye shiryenkomawata
rasha.saidai su mami sunce inbar musu itaanan
dan indinga waiwayen gida akai akai.darendazan
koma bansa ruqayya a idonaba.amma naga duka
kayana ta kimtsa min cikin jaka sai da jikinayayi
sanyi danaga jakan tsaf ashirye.Na fita naje
wajen su mami nayo hira na dawo misalintara da
rabi na iske ruqayya tanata rusar kuka
cikindakin,duk iya sallamata bataji shigowata
ba.nimaganin banji motsintaba yasa na tura
qofar naleqa.gaskia gabana yaafadi ayadda
naganta.dasaurina qarasa na zauna gefen gadon
nayi kiranta ruqayya! take naga ta dauke wuta
taqara tusa kai a filo nacemeyafaru? ta amsa ba
komai.nace babu komai ayitarafsa komai?
kigayamin danna tabbatar bani na
batamikiba..tayi shiru nace tashi ki zauna.nanda
nan tabiumarni na.gayamin abunda yasaki
kuka.ta sunkuyardakai idan ka tafi yaushe zaka
dawo?na zura mata ido saboda mamakin wai
tafiyata ce tasata kuka.atunani na da xama na
da rashinsa duk zai iya zamadaya agunta ashe
ba haka bane. To mezaisa nakasazama adali
agareta? Tausayinta ya lullubeni idanuwa na
suka tarakwalla bansan lokacin danakai hannu
na kamotabanace ruqayya!ta dibeni da kyar
muka zurawa juna idotsawon lokaci kafin ince
shi ne kadai matsalarki?taamsa dakai.nayi
murmushi nace ai bazan dadeba komutafi tare?
tace aiba ka shirya hakanba ko?nace hakane kiyi
haquri sai na sake dawowa.kinji?ta
kallenitanadan murmushi tace nayi!tundaga
lokacin natabbatarwa ruqayya cewa kyakkyawar
tarbiyarta tajawo mata wani matsayi a zuciyata!
daren dazan tafiyazama daren da ban taba
mafarkinsaba da ita.natafinabarta cikin wani
yanayi da bazan iya gayamiki ba.ko ni na dade
ina juyayi nakasa mance ruqayya daalherin dake
tattare da ita.amma duk sanda na runtseido ke
nake gani.wata guda bayan tafiyata
ruqayyatafara rashin lafiya gwaje gwaje ya
tabbatar tanadauke da juna biyu.al'amarin
yadaure min kai ikonAllah kenan.zuciyata ta
qara sanyi akan qaddarar al'amarinmu.kuma na
tabbata su mami na rokon Allahakaina.cikinta na
wata shidda .112.Taqi samun lafiya saboda haka
na wuce da itarasha.tasami ishasshen binciken
da sakamakonsayadagawa kowa hankali.cancer
aka samu amahaifarta nida kaina saida na zubda
kwalla.sabodatausayinta.nan na barta a asibitin
danake aiki hartahaihu gaban kwararrun
malamaina.dukda haka dakyar aka samo
ranta.babynmu kuwa qaton gaske ba indayabaro
ni sakeena.ta waya mukayi maganar sunadasu
mami nace sunan yaro abdulrasheed.su
nanmahaifin ruqayya.abin yabasu mamaki saida
mami tatambaya donme bansa sunan dadyba?na
nuna matakawaici nayi dan faranta mata
rai.bayan ta warware a asibiti muka dawo gida
nigeria akayi shagalinsuna.aikuwa iyayenta sunyi
murna akan sunandanasa kaya akwati akwti
abbanta yayo masa nannabarsa nakoma
rasha.tana samun kulawa a gidansutare da shan
magunan cutar dake jikinta.wanda likitotidani
kaina na tabbatar hatsari ne sake haihuwarta
nan gaba dalilin dayasa kenan muka shirya
planning doledan ceto lafiyarta.bamu rasha
bamu nigeria sabodakwarewata a fannin daya
shafi kai,Ko'ina ana gayyata ta muna zamanmu
lafiya daruqayya tsawon shekaru takwas ba a
yiwa waleedkani ba saboda tasoron abinda kaje
ya dawo kuma balaifi kulawar da take samu ya
taimaka kwarai wajeninganta lafiyar ta a gaskiya
ruqayya mace ce takwarai saboda a dalilinta ne
na gane hali yana sawa a so mutum ko a tsane
shi zama na da ita ta samar mindukkan farin ciki
iyakar kokarinta kuma na gamsu datarbiyarta
amma koda sau daya na kasa furta kalmarso
gareta duk lokacin dana dubi fuskarta da
nufintabbatar mata da soyayyata gareta sai in ga
fuskarbata wadda nake mafarki kullun
bace,kwatsam cikin wani hukuncin na ubangiji
wani cikin ya bayyana ajikin ruqayya,tun kowa
bai sani ba daga ni sai ita nacea zubar dashi don
kar sa mi matsala nan gaba ammamezai faru
ruqayya tace atabau bata san wannanzancen ba
raina ya baci a zatona hakan zai sa ta barina
aiwatar da abinda nake ganin zai tsirar da lafiyar
ta Sai daii abun mamaki Ranar dana diro kasar
na sha fada wajen mami kwaraita nuna min
bacin ranta saboda halin ko in kula da nanunawa
ruqayya dalilin da yasa kenan dana koma nakira
ta daki na ta sameni ta zauna bakin gado
gadadaya ta rame sai katon ciki gabanta na kare
matakallo na kada ka nace saboda Allah ruqayya
kin ga yadda ki ka dawo kiri kiri ki yi wasa da
rayuwarsaboda me? Ta kare min kallo kafin tace
me zai saAllah ya bamu kyauta muce ba ma so
me yasa zakudage akan cewa wannan cikin zai
iya zama ajalinakuna nufin kun fi wanda ya bani
cikin sanin abinda yadace,114-da sauri na
katseta ruqayya...."Itama ta katse nizan mutu
koda cikin nan koba bu shi muddin kwanakina
suka kare dokta amman ka dauki karan tsana
kadora min akan laifin da bani nayi shiba nayi
zatonzaka tausayamin ka dauki laifin ka dora wa
kankaganin komai ya faru daga gareka ya fito
sai ka juya bin baya ka nuna min tabbas hadamu
akayi Allah yayi aurenmu badan ka so ba,, ban
san lokacin da narufe bakin ta ba nace ba haka
bane ruqayya pleasekar ki dauki maganar nan ki
kai ta in da bai dace banasan nayi kuskure ki
yafe min don Allah idonta yacika da kwalla tace
ya wuce dokta kullum burina in faranta maka rai
don kar kogin soyayyar da yacinyeka ya samu
damar hallaka rayuwarka gaba dayana zura mata
ido dauke da mamaki na ce ya akayikika sani?
Tace iya taban labari tun lokacin zamantaa waje
na jegon waleed tun daga ranar na kara
azamabana fashi kuma ba na sanya akan duk
wani Bakin ciki daka shiga Barin cikin nan yana
daya daga cikinhanyoyin. Dana zaba na faranta
ranka dokta na sankona mutu idan ka kalli
abinda na bari zakaji dadi harka tuna yi min
addu'a ka taso kai kadai cikin gidankubai
kamata ace kaima ka rayu da Da kwaya daya
batace ina ji ina gani a kashe maka karin da
Allah ya baka ina fatan kaima zaka dubi uzurina
ka dainaganin laifina? Kai ban taba jin kalaman
da suka ratsani ba tun rabuwar mu dake sai a
ranar ban san tsawonlokacin dana kasance
rungume da ruqayya ba idokuwa taf da hawaye
kaunarta na ratsa ko'ina a jiki naduk da ban iya
furta mata ba na tabbata son ta ya kamani baki
na ne kawai ya kasa fadi,115-mun raba dare
muna. Faranta wa juna rai washegari nayi shirin
tafiya. Sakkwato in da zan gudanar dawasu aikin
fida cikin kai burina in hanzarta
kammalaayyukan da zanyi a nan sai in dauketa
mu komarasha tare don ta haihu a can wata kila
a dace tatsallake siradi, sai dai shirin ubangiji
yana gaba da mu a ranar da na wuce sakkwato a
daren na sami wayana kai ta asibiti nakuda ta
zo hankalina ya tashikwarai da gaske ga shi
tiyata biyu ke gaba na daya adaren zamu shiga
dayan kuwa sai da safe ni dai aikinnan nayi ne
kawai Allah dai ya bada sa'a bamu fito basai
karfen biyun dare ina fitowa na kunna waya ta
mami na fara nema cikin daran nan jim kadan
naji tadauka nace mami yaya ruqayy,?tace
ruqyyaalhamdulilahi ta haifi ya mace wajan sha
biyun dare tadai ji jiki amma an gode Allah
tunda da gata a kwancetaba bacci na sauke
numfashi nace lallai Allah abingodiya ne to Allah
ya kara mata lafiya ya amfana abinda aka samu
tace amin yaushe. Zaka dawo na cein sha Allahu
gobe zan dawo muna fitowa aikin dazamuyi tayi
min kyakkywar addu'a muka kashe wayana
kwanta na kasa barci ina tunanin kalaman
ruqayyaina sallar asuba na sake kira mami ta
hadani da itamuryar ta a shake tayi min sallama
na ansa cike da fara'a mai jego to ya jikin ki
tace lafiya lau kintabbata? Tace zazzabi ne
kawai ke damuna nace zaibari in sha Allahu ya
bebina ina fatan dani take kamatace kuma shi
ke nan kai kadai zaka cinye gidan?Nayi dariya
sosai nace kina kishi ke nan to ya zakiyiidan na
cinye gidan.... tace me kuwa amma idan aka
raba ai zai fi amisali in na mutu baza ka rinka
ganin me kama daniba Nace yanzu me ya kawo
maganar mutuwa bayankin fimu gaskiya Allah ya
nuna mana ikonsa tayimurmushi tace hakane to
yaushe zaka dawo naceyau yau din nan da yardar
Allah badan ma aikin gaggawa zamuyi ba dana
biyo jirgin karfe bakwainazo na ganku tace Allah
ya kawo ka lafiya na amsada amin mun jima
muna waya ta ita tana min dariyawai. Bebyn tayi
kama da ita,karfe takwas muka shigatiyata
banmance wa akwai wani mutum ne da
wasujijiyoyinsa ke hardewa ta bayan ke yarsa
suka dinga haifar masa da matsaloli masu yawa
awowi bakwaimukayi kansa muna aiki don bamu
fito ba sai karfeuku na yamma na hanzarta sallar
azahar na dan kirala'asar ta karasa yi itama na
mika ta kai tsaye wayata na zaro na kunna na
nemo lambobin ruqayya najitaa kashe saboda
haka ns nemo ta mami hankalinta a. Tashi naji
muryarta kamar mai kuka tace al-ameentun dazu
nake neman wayarka a rufe ya mata ka tahojikin
ruqayya ya rikice bata san halin da take ciki
ba,jiki na ya dauki rawa nan da nan zufa ta fara
ketojikina ban jin na cewa mami wani abu ba
kashe wayarkawai nayi na bazama wajan abokan
aiki na na gaya musu halin da iyalina ke ciki
take nan suka kai ni filinjirgi yan mintoci ya rage
jirgin danayi bukin ya tashilokacin na cika ya
kwashe mu ya aje minna ya wuceabuja tundaga
nan na dauki shata har asibitin inatambaya aka
nuna min dakin haihuwa na doshi dakingaba na
bai daina faduwa ba da ka ganni kasan bana
cikin natsuwa mami na fara hangowa,117-kamar
kuka take yi na rage sauri ina zare idosannan na
gane kowa na wajen kuka yakeyi na matsana
zurawa mami id nace mami da dago ido ta dube
nita kara fashewa da kuka ya jikinta sai ga dadi
tare daabban ta suka fito daga dakin na nufi
gunsu inatambaya don su ma babu alamar
natsuwa a jikin su abban ruqayya ya kamo
kafada ta ya jawo ni gefeyace kayi hakuri al-
ameen ruqayya babu ita kaina yasara yayi
gingirin duk da na saba ganin mutuwa iri irisai
yau naji ta sabuwa zuciyata ta buga komai
nawaya daina aiki tsawon lokaci ina kallon
abban ta bancekomai shi yaja hannu na. Zuwa
dakin dadi ya biyo bayan mu tana rufe bisa
gadon ta yasa hannu yabude min fuskarta na
kafa mata ido yanzun nan tacika da kalmar
shahada al-ameen don Allah kayihakuri kayi
imani da hukuncin ubangiji Inji
abbanta,,innalillahi wa inna ilaihi
rajiun..gabadayanarikice kamar ba likita ba.nidai
bansan yaddaakayiba aka dawo da gawar gida
nakasa mata wankakamar yadda shariah taso sai
su mami ne sukamata.ina rungume da
waleed,shima kukayakeyi.mami tace inje inyi
mata addua kafin afita da ita.nashiga dakin
nasameta tsaf cikin likkafanintatamkar ka kirata
ta amsa.nadauki kanta nadaura bisacinyoyina
nafara addua.muryata na rawa ido na
zubdahawaye.bansan lokacin dana goce da
sumbatu ba,fadinake haba ruqayya,meyasa
zakimin haka?saidanafara sonki zaki tafi ki
barni? kinmin adalci kenan? yanxu ya kikeso
nayi da raina?dady ya dafani yacekayi shiru da
bakinka al'amin.taso haka ya isa!nadubeshi
hawaye na sauqa nace haba dady wannanwani
irin abune? narasa sakeena sannan
narasaruqayya ma kenan?ku tausayamin
mana.118Baice komaiba yadauke kanta daga
jikina yanadeta waje daya,sannan yakamoni ya
fiddo niwaje,yatura aka fito da gawar.mutane
maqil!sukasallaceta nadauketa da hannuna nasa
akabari akabinne abinda nakasa mantawa
kenan.ya rinqa firgitaniidan natuna dasafe munyi
waya da ita.nakasa kallon jinjirar data bari ga
waleed naqara raunana min xuciyada
tambayoyinsa.su nanta aka maidawa bebin
danhaka muke kiranta waleeda.babu inda
tabarmahaifiyarta.tananan yanxu shekararta daya
darabi,nikuwa tun lokacin nakoma rasha nabar
waleedwajen mami.ita kuwa waleeda tana
hannun umman ruqayya.idan kinganni nigeria to
gayyotani akayi waniaikin dabazan wuce sati
biyu ko wata guda ba.gabadaya nasamu rauni
acikin xuciyata agame damaganar aure ko
soyayya.dukda nasan nafaramanyanta yakamata
nasake aje mata.amma banatunanin hakan.abisa
dalilin dani kaina nasan ba hujjabace a wajen
ubangiji,119Amma Allah yagani na jarabtu wajen
kewarruqayya.da kayan sonki danakasa sauqewa
shekarada shekaru.kuma inayin addua ina rokon
Allah idanyasake bani mata yabani wacce
zuciyata zatasotakarna sake tafka kuskuren
danayiwa ruqayya.saibayan ta mutu nake
gayamata kalmar so.kwatsam! Nasami takardar
gayyata indawo inyi aikin wata shidaanan
asibitin zariya.musamman saboda ku yan
koyonaikin dakuma yawan samun matsaloli
lalurar datashafi kwakwalwar yara.bantaba
tsammanin zansakehaduwa dakeba
sakena.saigashi cikin satin farkodana shiga
office.Allah yahadani dake.nayi murna da
farincikin dana manta rabon da inyi irinsa.don
azatonaAllah yakarbi adduata.saboda yasan
babu macendanakeso tamkarki..ya numfasa
tareda shafa zufardata karyo masa,yaci gaba da
fadin.koda yake nayiimanin bakomai kakeso
yake zama alheriba.wata qilaakwai abunda Allah
yaboye agame damu shisa nakasa samun
aurenki.nagode Allah tunda ya tsamoki daga
qangin sharri.ubangiji yadada tsaremu
dagasharrin masu sharri. Ya dubeta tana share
kwalla yace kukan me kikeyi?tace mutuwar
ruqayya naji tamkar nasanta.Allahyajikanta.yace
amin summa amin! tace haryanxuwaleeda tana
suleja?yace tana can waleed ma yanazuwa hutu
yadade acan har hutun yaqare.ta numfasatace
Allah amfanasu yace ameen.sukayi shiru suna
ratsa tsakiyar zariya haryakawo gida.yayi
fakin.tadubeshi daidai lokacin dashima ya
dubeta.tacenagode ina fatan zaka yafemin.yace
me kika min?tace shikenan saida safe.ta bude
murfin motar tafitoyana kallonta bai iya tankawa
ba.yabude nasa murfinyafito yasake dubanta
yace dazaki ban numbarki dakin taimakamin ko
gaisuwa mudinga yi.tagyaratsayuwa tace kada
muyi hakadakai babanwaleed.alfarma biyu ka
nema.kakuma gayamin naamince.toyanxu zaka
karya alqawari.ya kada kai yacesakeena.....ta
katse shi saida safe baban waleed tajajakarta ta
tura get ta shiga ta nufi bangarenta tana budewa
zainab ta tura qofar ta shigo.sakeena
kindawone?tadub eta da murmushi bake kika
turamin dr ba?yana iya daku!ta tura qofa
tashige,120.zainab tana dariya to ko kefa?
saboda Allahakanme zaki bar karatunki?ta jefar
da jaka tazaunagefen gado bazaki gane bane
zainab.medaki shiyasaninda yake masa
yoyo.nisanta ta da dr shine
zamanlafiyata.tazauna kusa da ita ta sanyaya
murya tacedon Allah intambayeki?tace tambaya
naji.tace tsakani da Allah bakison dokta?ta zura
mata ido jim kadantace meyasa zakimin
tambayar kurilla?kiban amsakai tsaye zan
fahimta sakeena.tace to aikobangayamiki ba
kinsan amsar tambayar zainab shinaso afarko
kuma shine a qarshe.idan kuwa
hakanebaikamata ki cutar da kanki ba.kimanta
da komai ki amince masa adaura muku aure.tace
zainab kenan tona gode da kulawarki.tamiqe tana
fadin don Allah kiyitunani karki bari dr yaqara
kubucemiki.Ta juya ta bar dakin mama tayi shiru
kanta sun kuyeduk gabobinta suka mutu,zainab
ta sake fadowadakin. Ta firgita sakeena haba
sakeena ki taimakibawan Allah nan koya sami
natsuwa ko kin san haryanzu yana waje ta kara
zaro ido banganeba doktayana waje kin kuwa
san zai iya kwana a nan don hankalinsa ba a
jikinsa yake ba ta sauke numfashitace na shiga
uku ta mike da sauri ta fita zainab tabita kansa
na kife bisa sitiyari ji kawai yayi an budemurfin
motar ya dago kai ya dube ta ya zura mata
idobaki sake ya kasa fadin komai ta gyara
tsayuwa tacebaka san dare ke kara yi ba Ta juya
tabar dakin,mama tayi shiru kantasunkuye.duk
gabobinta sun mutu.zainab tasakefadowa dakin
harta firgitata,sakeena!haba sakeena!kitaimaki
bawan Allah nan kozai samu nutsuwakinsan
haryanxu yana waje.ta qara zaro idobanganeba?
dokta yana waje.kinkuwa san zai iya kwana
anan,don hankalinsa baya
jikinsa.tasauqenumfashi tace na shiga uku!ta
miqe da sauri tafita.zainab tabita.kansa na kife
kan sitiyeri ,ji kawaiyayi anbude murfin
motar.yadago kai ya dubeta yazura mata ido
baki sake,yakasa fadin komai.tagyaratsayuwa
tace bakasan dare ke qarayiba?ya sauqe
numfashi yace zantafi.tace yakamata kasan
yanayingarin ko?yace hakane saida safe.tace
Allah yatashemu.ta rufe masa murfin mota ya
tayar yasakedubanta kamar yagayamata sirrin
zuciyarsa ya tunamata baya,amma yariga ya
dauki alqawari dan hakayadake kawai.yadaga
mata hannu ya wuce.itama tana daga masa
saida yabar haraban wajenm tadawo dakiba
kwari ajikinta.batama san tawuce zainab
tsayeba.Ta maida kofar ta rufe ganin haka yasa
zainab itamata wuce nata bangaren ta kyaleta
tayi tinani akanabinda take shirin
aikatawa.kwanciya tayi bisa gadotunani ya
isheta labarin daya bata kawai yakanta
cikinranta.ta tausaya masa ta lalubo hotonsa ta
zura masaido bata lokacin da kwalla ya zuba
mata ba daren nan bata runtsa ba saboda tsabar
tausayin al'ameen dayaransa.haka zalika
lamarin yake ga al'ameen tundaya koma gida
yakira wayar mami yasheda mata dukyadda
sukayi da mama.ita kanta ta girgiza.sai
daibatada abinyi illa tabashi haquri ya
dangana..tundayace bayaso abbanta yasani dan
karya takuramata.wanda hakan baisan abunda
zaijanyoba.haka yakwana yana juyi da
tinanetinane.kamar yabar garin yakeji.dasafe a
ofis ya iskemutumin dr lawal.yazauna shiru yana
kallonsa.drlawal yakada kai yace ai mukam mun
shiga uku!tundasakeena ta dawo mana!yanxu
shikenan haka zamu kasance a susuce?dafa ba
yanxubane kasanalameen din yanxu ba yaro
bane.122Yaja tsaki ina ruwan so da shekaru?
yace waitsaya baku daidaita bane?ko tana da
aurene?yacelabari ne mai tsawo ashe yaron nan
asiri yamatasaboda taqi yarda dashi ya lalata
mata rayuwartayakuma qi aurenta.ya rabata da
iyayenta.ya ajiyetakamar dadiro.cikin wahala da
kazantatciyar rayuwa abin babu dadin ji sai dai
Allah yakawo qarshenabin.asirin ya karye.ance
yananan yana hauka afandogari.amma ingaya
maka har haihuwa sukayidashi saida yaron
yashekara goma sha biyu yamutu.da wannn fa
take ganin ita abar kyamace.tagaggaya min
maganganu masu qona zuciya.wai harda tarkata
kayanta ta gudu tabar karatun.tagudu harkaduna
nabita na lallasota nace indan tanine tayihakuri
na haqura.ya ce haba!bai kamata kayi hakabaai
ita abar tausayi ce kuma dakai yadace ku
zaunazaman aure.don wancan BAKIN CIKIN
Yazama tarihi!
HAUSA Novels BOOK
BAKIN CIKI 3***10 Yace ita batayi wannan
nazarin ba.amma tunda hakane sai mu mutu
gwaraye!dr lawal yace a a Allahyasauqa kamutu
gwaro nizanje nasameta.da sauriyace karka je dr
lawal alqawari nadauka mata koabbanta
bazaijiba.to saboda me?bayan kana sonta?yace
bana so tabar karatunta dr lawal.kaga tunfarko
abbanta karatu yaso tayi nazo na tusa
matasoyayyata har wancan shirin ya
russhe.yanxu kumatayi nisa sai inqara rusa shi?
ka kyaleta kawai zandaure har zuwa lokacin
dazan koma abina.daga nanbazata sake
ganinaba.ina ganin hankalinta zai kwantataji
dadin karatunta.ya numfasa yace Allah yazaba
mana mafi alheri.yace amin zan qarasa
ofis.tosai kafito yamiqe yafita yabar dr lawal
yana girgizakai.kwana 7 suncika litinin tazagayo
wa al'ameen adaddafe.domin gani yake kamar
yashekara da zuwayanda nigeria tamasa
zafi.komai akan qarfin haliyakeyi.amma
hankalinsa nakan mama.ko yau da wuri yazo ofis
dan ya ganta kozaiji dadi aransa.kowa yazoya
tarar dashi ne azaune a ofis yanata fama da
(laptop),A hankali masu jinya suka cika wuri
masu raba(folder)suka rarraba kamar kullun
sababbin zuwa susuke ganin baban likita kuma
mutun hudu ake bokinko wane wata saboda
dadewar da ake wajan bincikeakan kwashe sama
da awa biyu ana ganin mutumdaya, dalibai suka
iso cikin ayari kaman yadda suka saba suka
kutsa kai ofishinsa. Bai iya dauke idon saga
kallon mama ba hasalima wani banzan kyau
tayimasa ga rigar likitocin ta kara mata kwarjini
bayansun gama sa hannu kowa ya zauna aka
fara karatugaba daya ya tasa mama da
tambayoyi kuma idonsabaya daukewa akan na ta
koda bada ita yake magana ba ma'ana dole ne
duk bayan yan sakwanni ya dubiinda take zaune
anan suka kai karfe daya kamaryadda suka saba
suka sallame shi kowa ya ficemama na tsaye
rungume da wani (file) a hannunta yazuro mata
ido jim kafin yace yaya dai ta matso ahankali ta
dora masa file din hannunta akan tebur ta juya
da sauri tabar ofis din ya bita da kallo ya rasa
mezaice har ta fice ya jawo file din ya bude ya
daddagetakardun dake ciki daya bayan daya ya
karanta kafdin su sakamakon gwaje gwajen da
aka yi mata ne aegypt kansa ya daure mene ne
nufinta na kawo masafile din yakasa warware
dalilin... -Amma a hakikanin gaskiya kai zan
kawo mawa don ka gani a matsayinka na mijin
da na yanke shawarar mika wa amanta Allah ya
tsare ni dokta ba'a sami cutar komai ba a jiki na
zaka iya hakuri dani a matsayin matarka ba tare
da tunanin na taba haihuwa a waje ba tsawon
sakwan biyar yayi zuru yana kallon a idanuwanta
jajur taf da kwalla murya dishe ya ce idan
zolayata ki keyi ki bari sakeena please kar ki yi
wasa da rayuwa ta kwalla suka zubo bisa
kuncinta tace ba wasa bane dokta zainab tayi
kokarinta ta gaya min gaskiya haka abokin ka dr
lawal zuwansa uku gidan nan yana jawo
hankalina akan abinda ya sameni ba hujja bace
ta kin yin aure na kuma tabba ta ko abba yaji
wannan maganar zai so mucika wa juna alkawari
shi yasa na hakura na yi niyya cikin raina da
yardar Allah baza mu mutu gwauraye ba muddin
zaka kare min mutuncina wajen danginka kayi
min alkawari ya dafe kirji idanuwansa sama
yake fadin Alhamdulillahi Allah na gode maka da
ka nuna min wanna rana dana dade ina mafarkin
zuwanta kawai gani tayi ya zaro waya ya nemo
wasau lambobi ya kara wa kunnensa tayi zuru
tana kallon sa dukkansu kwalla ke bin kuncin su
jimawa kadan ya fara fadin wa'alaikumus salam
mamina albishirinki sakeena ta amince mami
sakeena ta yarda zata aure ni tace godiya ta
tabbata ga Allah ka gaya mata muna godiya
yace zan gaya mata mami zan kira dadi in gaya
masa ya fara shiri tayi yar dariya tace Allah
sarki dan gidan dadi to shi ke nan sai mun
ganka ya kashe waya ya dubeta sukayi wa juna
kuri na tsawon lokaci yai dan murmushi yace
sakeena har,126Yace sakeena har abada asirinki
a rufe yake.kuma zaici gaba da zama a rufe har
qarshen rayuwarki.duk wanda ya nemi ya tona
miki sai naga iyakarsa.ina mai tabbatar miki
qarshen sa zai zama tamkar na danliti.karkiyi
kokanto ko kadan tunda ga fuska har zuciyaata
alameen dinki ne wanda kikasani.ta kada kai
tace bashi bane al'ameen dina saurayine,wannan
kuwa harda furfura!ya fashe da dariya yana
tambaya furfura?ina furfurar take? itama ta fara
dariya gatanan ina gani bisa kanka!Allah sarki
dr na ya tsufa!yace sakeenarfa?ai ita ma ta
canza.taci gaba dayi masa dariya.yana kallonta
kwalla suka taru masa ya numfasa yace Allah
nagode maka da dr lawal da zainab.dasuka dage
da farin ciki na ya dawo.sakeena kigayamin
ranar da za'a daura mana aure tun kafin a
tasheni daga baccin nan! 126Yace sakeena har
abada asirinki a rufe yake.kuma zaici gaba da
zama a rufe har qarshen rayuwarki.duk wanda ya
nemi ya tona miki sai naga iyakarsa.ina mai
tabbatar miki qarshen sa zai zama tamkar na
danliti.karkiyi kokanto ko kadan tunda ga fuska
har zuciyaata alameen dinki ne wanda
kikasani.ta kada kai tace bashi bane al'ameen
dina saurayine,wannan kuwa harda furfura!ya
fashe da dariya yana tambaya furfura?ina
furfurar take?itama ta fara dariya gatanan ina
gani bisa kanka!Allah sarki dr na ya tsufa! yace
sakeenarfa?ai ita ma ta canza.taci gaba dayi
masa dariya.yana kallonta kwalla suka taru
masa ya numfasa yace Allah nagode maka da dr
lawal da zainab.dasuka dage da farin ciki na ya
dawo.sakeena kigayamin ranar da za'a daura
mana aure tun kafin a tasheni daga baccin nan!
Yace sorry ba baraka yadace infara tambayaba
ya umma dasu ameera?tadanyi shiru jim kadan
ta dubeshi ido ya kawo kwalla tace umma ta
rasu dokta.....yace what?innalillahi wa inna ilaihi
rajiun.ciwo tayi?ta goge kwalla tace BAKIN CIKI
Ne yakasheta dokta!umma takasa jure ganin
halin qasqancin dana shiga.shisa bana son
tunata.hankalina tashi yake tun lokacin shima
abba yasamu matsalar paralise.andai samu
yanxu hannun yana dan aiki amma baya tafiya a
keke ake turashi.yace subhallahi Allah ya jikanta
ya mata rahama.ta amsa ameen.ya miqo mata
hankici share hawayenki kiyi haquri kinji?ta
share fuska yana qara bata hakuri.sundan jima
shiru kafin yace pls kidena damuwa insha Allahu
abba zai warke idan har akwai yiwuwar hakan
sai inda qarfina ya qare.ta numfasa nagode hira
ta tsunke labarin bayan rabuwa sukeyi.kiran
magruba dole ya miqe sukayi musayar
lamba,yafito ta tako masa zuwa gaban
motarsa.ya bude ya shiga,sannan yace to sai
munyi wayako?tace ina sauraronka.ya qara zuba
mata ido yace i love u! tace mee too!yace so
much?tayi murmushi ta tura hularsa gaban goshi
tace so much!ta juya tabar wajen tana
waigensa.bakinsa har kunne yabar wajen,
128.tana karasowa ta iske zainab tana mata
dariya.taja ta tsaya meyabaki dariya?ta daga
gira ta kama kugu hannu biyu so baya tsufa,sai
dai masoyan su tsufa kinga oganmu baki har
nan?ta nuna da hannayenta mama tayi murmushi
tana kada kai ke mayya ce zainab,wato ido
kikasa mana ta window? zangayamasa.tace
karki hadani da oga kisa ranar monday ya
kasheni da tambayoyi.tana dariya ta tura qofarta
tana fadin barinyi sallah.akwai abincifa kixo
muci,tace sai na shigo ina jiranki kowacce ta
nufi bangarenta.sannan suka hadu cin abincin
karo na farko da mama ta gayyoto zainab
saboda jin dadin shawarwarin data bata,har suka
taimaka wajen dawo mata da farin cikinta. Haka
al'amarin yake wajen dokta yana fitowa
masallaci wayan dr lawal ya kira yagaya masa
yana gida cikin yan mintoci dabasu fi ashirinba
ya isa gidan.yana fitowa yaga dr al'ameen ya
nufosa baki har kunne ya rungumesa.ya dubesa
yaya dai likita?yace Allah yasaka maka da
mafifi cin alheri!ya ware ido sosai yace amin
likita meya jawo min wannan kyakkyawar
addu'ar?yace ta amince dr sakeena ta amince
zata aureni!ah haba?yace gaskia nake gaya
maka,bansan irin godiyar dazan makaba dr
lawal.ya numfasa yace yazame mini dole in
taimaka maka.don na tabbata fadi kawai kake
bazaka iya haqura da itaba.nima ngd Allah data
dubi girmansa ta amshi rokona!nagaya mata
bakai kadai zata kasheba. Allah kadai yasan
mutanen dazasu mutu idan ta bari sonta ya
wargaza mana kai.ko ba gaskia ba?abin ya
dameni da yawa.koda kace kar insake mata
magana najika ne kawai amma tunani yana kan
yadda zanyika auri sakeena.muma hankalinmu
ya kwanta.so yaushe tace zamusha bikin?ya
rungumeshi yana fadin.bazan taba mantakaba a
rayuwa dr lawal.yace to nima nagode.suka dubi
juna fuskokinsu cike da annuri to yaushe
zamusha bikin?yace tace wata uku amma gaskia
yayi yawa munbarshi a sati uku.yayi dariya dr
love!watau ku kuka sanya wa kanku rana koh?
tsokanarka fa nake dakaji na tambayeka.ya zura
masa ido yana yar dariya.wlh madam na fama da
iya shegenka.to miye dan musa rana?ya tabe
baki hannayensa cikin aljihu babu komai sa'ido
ne kawai irin na lawal mushiga muci abinci.ko
sakeena ta baka?yace banceba dr lawal.karka
min sharri.suka shige ciki sunawa junansu
dariya.dr al'ameen na fadin ranar sati zamu
wajen abbanta a abuja shima sati uku zamu
gaya masa.bakuda kunya shima sai kun nuna
masa kun kosa?suka fado falo suna kyalkyala
dariya.ah madam kenan!ta yunkura ta tashi tana
murmushi oga ne dakansa?ashe yana dariya
haka abokin naka?tana tambayar mijinta dr
lawal.yace kingano kenan?ai sirrin zuciya a
tambayi fuska.ko?yace hakane mana ke me kika
fahimta kan fuskarsa?130.Tace wataqila sakeena
ta janye gudumar data daga!yace shisa nake
sonki mairo.akwai ganewa ingayamiki har
sunsanya wa kansu rana!tace ahaba dai!?kace
biki ya kusa.yace sati uku kinkuwa san akwai
sonkai aciki suna nufin sun kosa.takama baki
wai!maganar tafi qarfina.wannan tsakaninku
ne.dokta ka zauna akawo ruwa ko?yazauna yana
fadin kungama sharrin?toya yarana.tace suna
lafiya tun dazu suke sallah yace yayi kyau.tace
to congrats! muna murna Allah sa ayi damu yace
amin madam.ta wuce yayinda dr lawal ke zama
kusa dashi.kai mugun maasharranci ne wlh.yace
rantse da Allah baka kosaba?ya zura masa ido
yana dariya yace yo see! nasan bakada abin
cewa nidai ina roqon likita pls nd pls karka
manta wa wani almakashi acikin kai.arinqa ajiye
sakeena a kofar tiyata.ya bashi hannu suka tafa
suna kyayatawa kasamu ni dayawa dr
lawal.amma ba komai gidanka naxo.maryam ta
fito da tiren kayan abinci ta nufi tebur ta jera
musu.sunata yankar dr al'ameen.yazaiyi?sai
dariya kawai dan sunfishi baki.shiyasa yace wa
dr lawal duk ka bata madam da sharri Allah
shiryeku.ahaka suka gama cin abincin takwas da
rabi yabar gidan yakoma nasa.can yayi sallar
isha'i yayi wa Allah godiya ya rokesa daya nuna
masa ranar dazai ganshi da mama a matsayin
matarsa.yayi shiru ya rufe idonsa.wayarsa tayi
qara ya dauka dadinsa ne.yamayar masa yanda
akayi.dadi ya lullubesa.yasa musu albarka tare
da fatan Allah nuna musu wannan rana da zata
zamar musu abin tarihi a rayuwarsu.bai iya bacci
ba dan daya rufe ido mama yake gani tana tura
hularsa tana fada masa so much! ranar asabar
akan hanyarsu ta zuwa abuja.kaduna suka tsaya
makarantar da waleed yake (TURKISH
INTERNATIONAL SCHOOL.)inda yake karatunsa
makarantar kwana ce ta yaran masu kumbar
susa.suna zaune falon karbar baqi aka kawo
musu shi.ya rugo ya rungume babansa murna
kamar ta kasheshi.mama tayi zuru tana kallonsu
tana murmushi daka ganshi kaga al'ameen..ya
dago shi suka zurawa juna ido dady yaushe
kazo?yace banwani dade ba dama nace kar a
gayamaka sai naxo kaganni suprise ko?yace
amma kaje kaga waleeda?yace sau daya naje
Allah sau daya naje ya tura baki a shagwabe
gaskia ba haka akeyi ba .ba haka akeyi ba
dady.ya fara dariya ya kama kunnuwansa biyu
sorry.i'am very sorry abdul kayi?ya qara
rungumeshi i miss u dad.yace nima haka yarona!
ya dagoshi ya dubi mama ta zura musu ido tana
murmushi.har wasu kwallan da batasan
dalilinsuba suka taru.dadi wannan fa?ya dubeshi
ya numfasa mominku ce saura sati uku adaura
mana aure kana sonta?ya zura mata ido tamkar
yadda take kallonsa ina sonta dady wlh tanada
kyau kamar balarabiya! suka fashe da dariya
mama ta jawoshi jikinta ta rungumeshi.tace
nima inasonka kaima kayi kama da larabawan
my beloved son.ya kwashe da dariya yace harda
waleeda?tace sosaima.131Yace sister nane tana
can suleja wajen kakarmu.zakije ki ganta?tace
daganan can zamu wuce ya miqa mata yatsansa
promise?ta jawo shi ta rungume al'ameen ya
sauqe numfashi ya zura musu ido yana
murmushi..ta dago ta dubeshi to nagode tunda
kana sona kaga zamu zauna cikin farin ciki
kenan koh?ya amsa da kai dady kuzo ku dauken
ranar daurin auren.yace ai bakuyi hutu ba waleed
kasan makaranta bazata bariba.kayi haquri
inkunyi hutu kai tsaye zariya zan wuce dakai
wajenta.yace waleeda zataje bikin?yace wai
meyasa waleeda tazamo kishiyarka?to ita bazata
jeba shikenan? gaba dayanku sai anyi hutu
inkaiku.yadan saki fuska.mama tadauko wata
farar leda ta miqa masa duk wannan naka ne.ya
karba ya dudduba.kwalayen biskit da cukulet
kala kala wanda yakeso.ya dubeta yana dariya
momy na gode!tayi murmushi nima nagode.dr
al'ameen yace bari mu wuce koh? muna sauri
muje muga waleeda kar dare yayi sai
mundawo.sukayi sallama da waleed kamar zaiyi
kuka.hakanan suka tafi suka zuciyarsu cike da
tausayinsa.shiyasa mama tayi shiru a mota
tsawon lokaci sannan ta numfasa waleed kamar
kayi kaki dokta!133Yayi dan murmushi Allah ko?
tace har muryarku iri daya.ga shagwabar gado.ya
kyalkyale da dariya yace.haka kema zaki haifa
min ameer da ameera.ta watso masa harara,tace
kai ka sansu.yace ashe kingane.kullum na rufe
idona su nake gani.suna tumurmusani
uhm...mafarkina yakusa zama gaskia.Allah
kaban ameer da ameera ta tsatson sakeena
wannan shine babban burina.ta zura masa ido
harya tsargu yajuyo ya dubeta suka hada
ido.yayi murmushi yadauke kai.itama tahauyi
cikin ranta tana tayashi addu'ar Allah ya cika
masa burinsa.suna tafe suna hira nanda nan
suka iso suleja mama tana ganin yanda yadauki
babban titi tace ina zamu? yace wajen waleeda
mana!tace gaskia inajin kunya dokta.mu wuce
kawai watarana na ganta.yace kunya?ina
alqawarin dakika dauka wa waleed?tadan runtse
ido ya salam.ta dubeshi ta ci gaba sai kuma
muje kace musu ni wa?yace mominsu waleed
ofcourse!cike da damuwa tace aikaji.sai ace
banda kunya harna biyoka ganin yarka.ya
karkace kai yace salo!to idan baki biyoni ba
waza ki biyo?ta zura masa ido harya gaji yace
tsaya kiji karewa cemusu zanyi kece nafara so
rashinki yasa na auri ruqayya..tace kaga tun
anan ansami matsala kana fadi zanyi baqin jini.
Da dai....yanxu zakice bazakije kiga waleeda
bako? ta bishi da kallo haka shima yasa mata
ido jim! sukayi shiru kafin tace muje dokta
amma ka taimakeni dan Allah karka basu labarin
daya wuce.yayi dan murmushi yana tada mota
fuskarki kamar na mara tsoro can cikin zuciyarki
kamar farar kura.ga tsoro ga ban tsoro.tace muje
a tsoron aini nasan menakeyi.yace nine bansani
ba ko?tace wuuu! banfada ba Allah huci zuciyar
mai gida. Da wutsiyar ido ya kalleta in banda
abinki gidansu ruqayya ai gidan mune aminin
dady fa.yadda yake abbanta nima abba nane
tace nima abba nane.har kofar gidan kowa na
kokarin kare kansa yayi horn mai gadi yabude
suka gaisa ya ajiye motar a wajen ajiye
motoci.suna tsaye kofar gidan dr al'ameen yana
kwankwasawa yana mata dariya ganin yadda ta
tsaya tamkar marar gaskia.jimawa kadan aka
bude.ah! oyoyo dadin waleed yana murmushi
yace anti niima sauqar yaushe?tace dazu dazu
tafe kake da baquwa? yace wlh kuwa wai tanaso
tazo taga waleeda.bakinta har kunne tajawo
hannunta suka wuce ciki.tana mata sannu da
zuwa.har kujera takaita.tace zauna inkira
umma.suka zauna dr alameen yace antin ruqayya
ce tana aure a kano.tace akwai fara'a sai gasu
sundawo.anty ni'ima na riqe da hannun waleeda
tana taka qasa dabas dabas.saboda kiba,rugu
rugu!da ita.ga gashi kamar buzaye.mama ta zura
mata ido ai batasan lokacin data tashi ta
runguma yarinyarba saboda sha'awa data
bata.bayan angaisa anty ni'ima takawo musu
ababen sha.hajiyar ke tambaya hala wannan
itace sabuwar mominsu waleeda?Yana yar dariya
yace itace hajiya munje makaranta taga waleed
shine tace sai na kawota 135-wajen waleeda
hajiya tace madalla ya ya kyau Allah ya sanya
alkairi yace amin yayin da mama ta kara
sunkuyar da kai tanayi wa waleeda wasa ita
kuwa tamkar ta taba ganin ta fariya kawai takeyi
mata ya sunanta anti ni'ima ta tambaya yace
sakeena sunanta tace sakeena ta dan yi shiru ka
na ta kara fadin dadin waleeda ko dai sakeenar
da marigayiya ta taba ban labari ne duk suka
kalli juna sannan ya tambaya ta taba. Baki
labarin wata sakeena ce tace ya dade da ta gaya
min ka so wata yarinya sakeena amma Allah bai
yi auren ba ta auri wani itama iya ce ta bata
labarin irin son da kake mata haka ne? Yayi
murmushi yace haka ne anti ni'ima ga ta kuma
mun sake haduwa hajiya tace haka shirin
ubangiji yake matar mutun aka ce kabarinsa ina
fatan dai yanzu babu wani sai da na ko sakeena
taja mayafi ta rufe fuska suna ta mata dariya
kunya ta hana mama sakewa sha biyu rana suka
bar gidan da alheri mai yawa da hajiyar taba
mama waleeda kuwa harda kukanta da taga sun
shige mota sun tafi sun barta, suna tafe suna
labarin gidan irin kyakkyawar tarbar da akayi
mata abin ya faranta mata rai kwarai da gaske
bayan wucewa awa daya. Suka iso maitama gab
daza su shiga gidan take cewa kasan wani abu
ban fa gaya wa abba komai a kanka ba kamar
yaya tace kawai gaya masa nayi zan zo weekend
so na ke abba ya sha mamaki yace ai kuwa zai
sha mamaki na bazata ma kuwa ba shi kadai ba
kowa ma ya ganni zai saki baki yau , kin kyauta
da baki fadi yayi horn aka bude musu get suka
sulala ciki tace munyi sa'a yaya na gida ga
motocinsa nan a jiye yace good al-ameen sa'a
ke nan... mu je ciki asa mana rana yarinya
balarabiya ta bakin waleed" ta ballo masa harara
tace wace ce yarinyar yayi yar dariya ya bude
murfin yana fadin Allah na tuba duka kwaya
nawa kike ita ma ta fito gara dai da kace Allah
ka tuba ta wuce yabi bayanta yana dariya suka
tsaya bakin kofa tace ka tsaya anan zan dawo in
shigo da kai yace ba laifi ina jira ta shige tana
kwarara sallama duk suka amsa mata daga
babban falo can ta wuce da sauri suna mata
oyayo ta fada jikin abba da murna sanna ta juya.
Wajen yayanta da anti amina duk ta gaishesu
kana ta mike tsaye tace kun san wani abu duk
suka zuba mata ido abba ya bata amsa sai kin
fadi mama na tace duk ku rufe idanuwanku
akwai abin mamaki dana taho muku da shi
yayanta ya aje jarida yace idan kin ka nuna
mana shirme sai na balla kafarki tana dariya
tace na yarda to kun shirya mun shirya a rufe ido
ina zuwa ta fice suna mata dariya abba yace ai
sai mu rufe mu bude muga abin mamaki duk
suka rufe suna dariya jimawa kadan suka shigo
tare da al-ameen ya tsaya saitin daza su ganshi
sosai yana ta murmushi tace kuna iya budewa
duk suka bude kowa ya yi ido hudu da al-ameen
dif yake dauke wuta ya zubo masa ido anti
amina ce ta fara magana dokta ko ba shi bane
mama tace gashi nan dai abba wanene a tsaye
yaya ka gane shi yaya yace al-ameen abba ya
miko hannayensa biyu yace zo nan al-ameen zo
in taba ka in tabbatar da ba mafarki na ke yi ba
ya tako da sauri bakinsa har kunne ya zube,137-
gaban abba ya rungume shi yana fadin 鈥渢sarki ya
tabbata ga allah ashe zan sake ganinka al-
amin?鈥� Ya jima yana rungume da shi.sanna ya
dago shi suka duba juna. abba ya numfasa ya
sake fadin 鈥渉aba al- amin kuma sai zumunci ya
yanke? Babu kai babu labarin dadinka?鈥� Ya-ce
鈥渒a yi hakuri abba. Tunda na ba kasar nan ban
dawo ba. Sai da na kusan shekara biyar. Duk
abubuwan da suka faru ban dawo ba. Sake
haduwarmu da sakeena take gaya min har umma
Allah yayi mata rasuwa kai kuma ga lalurar da
ta same ka banji dadi ba Abba ubangiji Allah ya
jikanta yayi mata rahama hannayensa biyu bisa
kafadarsa ya amsa amin summa amin ina fatan
su alhaji duk suna nan lafiya ya juya suka gaisa
da yaya soja da anti amina yayi masu. Gaisuwar
umma nan da nan aka baibayeshi da kayan ciye
ciye dana sha kala kala ya jika mako shinsa da
ruwan sanyi yace ashe haka al'amura suka faru
abba wannan wane irin zaluncine da rashin
imani, Abba ya kada kai yace ka bari al-ameen
ai munga tashin hankali yarinyar nan ta dawo
tamkar mahaukaciya a gari kowa yana ganin
kamar rashin biyayya ce ta jawo mata lalacewa
da kaskanci ashe ba haka bane ka ganta nan
Allah ne yasa tana da sauran shan ruwa a duniya
hankalin al-ameen ya kara tashi yace
subahanallah Allah karabamu da sharrin shadan
suka amsa da amin yace shine wannan zai zama
dalilin da* tace ba zatayi aure ba sati uku muna
artabu abba da kyar abokin na ya shawi kanta.
Inda harna ce na hakura suka zuba mata ido
kafin abba yace haka ne kuma nima na kyale ta
ta zaba abinda tafiso dan hankalinta ya kwanta
sai dai tun lokacin na sani dole wannan kudirin
na ta ya tashi domin bani da wani buri da ya
wuce in cika maka alkawarin dana daukar maka
to Alhamdulilahi,138.tunda itama ta gane
gaskia,nakuma tabbatar batada wanda takeso
face kai.saboda haka duk lokacin daka shirya
kazo adaura auren dafatan bazaka samu matsala
da iyalinka dake gidaba.yayi murmushi yace ai
babu iyalin abba banganeba.ta rasu abba
shekara daya da rabi kenan.yace ayya Allah
yamata rahma yasa duk musulmi suna
kyakkyawar matsayi.yace amin abba.kowa yayi
masa gaisuwa,,,,,suna suka ci gaba da
tattaunawa.mama tace abba bakaga
yaronsaba.yakusa tsawona.al'amee n yasaki baki
yana kallonta,,yayinda abba ke fadin ah lalle ba
shakka,su nawa ne?tace su biyu ne,abdulrasheed
da ruqayya.sunan mamanta aka samata.abin
tausayi abba tana haihuwarta ta rasu.tausayi
yakama kowa sunata mata addu'a.al'ameen na
amsawa haka suka wuni hira salloli kawai ke
tadasu.dare yayi aka kai al'ameen masauqi.farin
ciki kamar ya kashesa.shine mutumin dazai iya
sharewa mama hawayenta.cikakken labarin
abinda yasameta dayaji ya qara masa tsantsar
sonta.bashida wani buri daya wuce ya mallaketa
ta hanyar sunna.don ya tabbatar mata da cewa
Allah baya zalunci kuma bayason mai
yinsa.washegari qarfe tara suka bar abuja dauke
da albarka mai tarin yawa daga wajen abba.suna
shigowa suleja mama ta tunada waleeda.tadan
dafa qirji Allah sarki waleeda kamar mu koma
mu daukota.yace kinsan rigimar waleeda kuwa?
bazaki iyaba nake gayamiki kukanta sai
hajiya.139.Tace haka kake gani,badon karatu ba
dana daukota.Allah taban sha'awa,jiya saidanayi
mafarkinta.kukan da take lokacin dazamu
tafi.yace ba waleeda kika gani ba ameera ce.ta
ballo masa harara yasan hararar yakesha
shiyasa yaqi waigowa ya rinqa yar dariya.ya
qirqiro waka.yana rerawa idan da rai da
rabo!.......al'ameen zaisamu ameer da ameera!
mai harararsa yadena!...takada kai tana dariya
Allah ya shiryeka!yace ameen.sannan yace na
fahimci kinfison waleeda akan waleed,lalle
zakuyi rigima dashi dan kishiyarsa ce.tace naga
alama komai saiya tambaya yaji ko anyi mata
shi ba a yimasaba? tace ba komai nasan yadda
zanbi dasu yace ko? kana shakk ne?uwace fa!
yayi murmushi yace uhm....naqosa inganki
mama.tace bari gatse dama sunan kenan! yace
godiya nake!dai dai lokacin daya dauki hanyar
minna.idanuwa waje tace yaya haka?yace haka
dinne.dan Allah ina zamu?yace yanda kika nuna
ni suprise haka zan nuna ki mamakiyos!ta
langume kai amma bakada kirki mesa zakamin
haka?yace mesa? tambaya kike?any
way....kinma riga kinba kanki amsa tunda kikace
banda kirki.rashin kirkin ne yasa zan nunawa
kowa cewa alqawarin Allah baya tashi.fuska
yamutse tace wayyo Allah na!yace ke yasu!?ta
numfasa bata bashi amsaba.yafara mata dariya
yana karawa don a gaskia tanajin kunyan su
mami balle kuma dady. Ganin abin yadameta
sosai yace to miye abun damuwar keda zaku
zauna nan bada dadewa ba.kinsan cewa ko
bajima ko ba dade zaku zauna tare.tace ai da sai
a bari na dolen yazo saboda Allah fa! Yace
gaskia bazan iyaba kiyi haquri kawai muje kisha
kunyar a yau.kinji ko bebina?tace naji sir! yayi
dan murmushi yace thank you mah!suka ci gaba
da hira kala kala.har suka isa minna.kai tsaye
yadauki hanyar anguwarsu.tace tsaya bansaya
wa mami komai ba.gayamin abinda tafi so?yace
idan kinaso ki burge mami kisaya mata
carrot.cucumba,da kankana.to muje insaya
mata.yace karki damu munayin kwanar can
akwai masu fruit.yana maganar suna shiga
kwanar sai gasu birjik!yayi parking duk suka fito
mama ta kwasa kamar banxa gaba daya akace
dubu daya.alameen yazaro zai miqa tace anyi ba
ayiba kenan.nice zansaya mata bakaiba kokai
kace?yakama kunnuwansa tuba nake wannan jan
idon?tayi murmushi harmai fruits na tayata.ta
zaro dari biyar biyar sabbi dal ta miqa masa
akasa a boot.suka wuce alameen na tsokanarta
hajiya mama kenan kinfara raina min wayau!tun
jiya kike kashe min kudi,karfa ki maidani mijin
hajia?tace sai me? yace sai ni baban ameer da
ameera.tayi dan tsaki ta kyaleshi yana mata
dariya.sunyi fakin harabar ajiye motoci,suka fito
shima ya ajeta waje kamar yadda
tamasa.yashiga ciki tare da sallama.maminsa na
dakin dady.daga can ta amsa sallamarsa.ya
qarasa ciki da fara'a maraba da bokan turai!.inji
mami yace mamina!ya tsugunna gabanta yadafa
guiwowinta.ta dafashi tace ya aiki?yace
mungode Allah mamina!141,ya juya kan dady
dadina!yace nidai ansaba min son kai.ai de ba
haka akeyi ba!yadawo gunsa yana dariya yace
dadina albishirinka?yace goro fari yace to duk ku
taso muje falo in nuna muku wani abu.meye shi?
mami ta tambaya.dady yace miye naki na
tambaya taso muje kawai.suka nufi falo.yauwa!
to ku rufe idanuwanku!kuma dai?inji mami.kedai
rufe dadi yafada suka rufe ido suna dariya.yace
minti daya yakoma waje da sauri ya kamo
hannunta tana fisgewa yashigo da ita.ya tsaidata
gabansu.kunya kamar ta nutse qasa yace kuna
iya budewa yanxu..alokaci guda suka bude duk
sukayi mutuwar tsaye.dadi yafara fadin sakeena!
taja mayafi ta rufe kai.mami kuwa da saurinta ta
rungumeta.Allah sarki sakeena! ashe Allah zai
hada fuskokinmu?kwalla suka cika idon
mami.mama kuwa ta goce da kuka.mami ta
dagota hannu biyu menene abin kuka sakeena?
don Allah ki dena.wannan ranar farinciki ce.dan
na tabbata dan tilon dana zaisamu farinciki data
dade dayin qaura daga jikinsa.karki damu da
komai kisaki jikinki kamar da kinji ko?ta
durqusa qasa baba ina yininku? haryanxu yana
mamaki lafiya qalau sakeena.haka shima
alameen idanu suka dauki kwalla.yace ashe har
umma ta rasu.mami ta kamota sukazauna a 2
sitter,tana rungume da kafadarta tace munji
rasuwar ummanki amma rashin jin dadin abinda
kikayiwa alameen shiya hanamu zuwa
gaisuwa.kuma bamu gaya masaba.karkiga
laifinmu sakeena.Allah kadi yasan wahalar da
mukasha kafin musamu mu ceto ransa. Allah
kadai yasan yan kudaden da muka batar dan
neman taimakon addu'ar Allah ya cire mishi
sonki.muka samu son yasuma.dan kuwa suma
yayi tunda gashi daga ganinki ya farfado.kiyi
haquri sakeena wannan al'amari duk cikin rashin
sani akayi.ta silale qasa tasake durqusawa wlh
babu komai mamii.idan kuwa dame laifi ni
yakamata nabada haquri dan angayamin dakanki
kikazo rokona.kina bani haquri amma naqi
sauraronki nima ku yafemin,,,,,ta jawota ta
rungumeta karki damu sakeena.wannan wani
qaddararren al'amarine daga Allah.babu mai iya
kauda shi.amma dayake bakida hakki gashi
ubangiji yabayyana komai....shikuma yaga
makomarsa.to Allah ya jiqan hajiya
halima.kidage dayi mata addu'a ita kadai ce
ribarki gareta.kinji?ta dago tana amsawa dakai
tana share kwalla!dady ya numfasa munyi farin
ciki da ganin wannan rana.muna masu tsananta
godiya ga Allah ta'ala mafificin dukkan
komai.saboda haka muke roqonsa ya karemu
daga dukkan sharri.yakuma jikan hajia halima
ya yafe mata dukkan kurakurenta.143Suka amsa
amin summa amin, bayan dadi ya gama
addu'oinsa alameen ya dubi mami yace ina
iyata?tace suna can bayan gida suna hira.ya
miqe yana fadin barin kirasu suga sakeena ta.ta
dawo mami tace yakamata.yashige kicin kofar
dazata sada shi da waje.mami ta dubi mama
tace inaa fata komai ya dai daita?biki kawai
zamu shako?ta sunkuyar dakai dadi yace kema
kinsan bazata iya fadaba.ki bari ya shigo muji
daga bakinsa,,,,sai ga hayaniyarsu dasu iya suka
shiga tafa hannu suna sallami lalle matar mutum
kabarinsa.suka zauna gefe suka gaisa.iya tace
ubangiji yanuna mana ranar auren nan.suka ce
amin.al'ameen yazarce da fadin musha rawa ko
iyata?baki har kunne tace sosai kuwa dan
iya.Allah dai yanuna mana lokacin lafiya.anata
raha suka bar falon.ladi ta tafi takawo musu
ruwa da abinci.mami ta gyara zama tace yadai?
ya ake ciki? nafa kosa..yayi yar dariya yace
komai dai dai mami.kinga tun jiya muka baro
zariya muka tsaya kaduna makarantar su
waleed.mukaje suleja gun waleeda yar
rigima.muka wuce abuja gidan abba.bakuga
yadda ya karbeni ba murna da farin ciki ba a
bayani.ya rungumeni yana kwalla.yanxu
maganarku muke jira yace ko yaushe nashirya
nazo adaura mana aure ai baza a bata lokaciba
ko dady? bakin mami har kunne tana fadin
masha Allah! dady yace me za a jira?Mu ai a
shirye muke in sha Allahu gobe zan tafi abujar
mu sasanta dole in durkusa in nemi afuwa zan
karbi lambarsa da adres kafin ku tafi Allah ya
shige mana gaba ya kore dukkan fitina suka
amsa amin al- ameen ya zarce da fadin amma
dadi karya wuce sati uku ayi komai a gama
kowa
BAKIN CIKI 3******11 kunga kuma zan sami wata
shida anan abin zai yi daidai suka yi dariya
mami tace gaskiya ne sati uku ai sun wa duk
shirin da za'ayi kai Allah ka nuna mana lfy,
murna cike da zukatansu bata misaltuwa mami
kamar ta hadiye mama ta tasa ta a daki suka ci
abanici tare bayan sallar azahar sukayi shirin
tafiya haka ta baza mata kaya kala kala tun
daga sutura zuwa kayan shafe shafe tace ta zafi
duk wadanda ta keso ta cire kunya ta zabi yan
tsiraru Al-ameen na taya ta shine ma ya jido
mata kayayyaki masu yawa dadi ya kwala wa
mami kira ta tashi ta fita mama ta dubi al-
ameen tace wai ka manta da tsarabata ne yace
ina sane kyale ki naiy in gani komawa zakiyi
dasu ta dan shagwabe fuska kai dokta saboda
Allaj baka san kunya ba maimakon ka taimake
ni, ya zuba mata ido maimakon ka taimakeni ya
maimaita a shagwabe tayi yar dariya tace don
Allah in ta shigo ka gaya mata gani ma na
shigon me za'agaya min mama ta sunkuyar da
kai ya fara dariya yana fadin wai tsaraba tayo
miki shine ta bari a mota tana jira ni in gaya
miki wanda ya siyo abu ba shi yake daukowa ya
bada ba? Mami ta dafa ta tace Allah sarki
sakeena kyale shi karya gadi din so yake ya
manna miki laifi dame dame kika kawo min cike
da kunya tace fruit ne kawai mami tace Allah
yasa da karot ciki suka kalli juna suna dariya
akwai mami ta ce to shine ki ka ki gaya min
abinda na ke ta marmari kwana biyu ban ciba ta
yunkura da sauri tacr bari a kwaso miki shi ma
ya mike yabi bayanta mami ta bisu da kallo tana
dan murmushin jin dadi jim kadan suka dawo
daddauke da ledojin guda uku manyan gaske
mami taji dadi sosai tana sa albarka sannan ta
mika wa mama rafar kudi dubu ashirin tace
wannan dadinku yace in baki tasa hannu ta
karba tana kada kai haka da yawa mami to
nagade Allah ya saka da alkairi tace amin
sakeena al-ameen yace mun gode mami bari inje
wajen dadin mu za mu wuce ya wuce suka zauna
jiran fitowarsa basu dade ba suka fito tare mama
ta zamo daga kujera ta tsunna tayi godiya yace
ba wani abu Allah ya sauke ku lafiya tace amin
suka rankayo waje al-ameen ya daga murya yace
iya ta na wuce suka fito tare da ladi sukayi masa
sallama sannan suka karasa wajen mota sai da
suka bar get suka koma cikin gida suna masu
addu'ar sauka lafiya ,, lafiyar kuwa suka sauka
cikin yarda ubangiji ya sauketa gida ya taimaka
kwaso mata kaya zainab ta fito ta tarbe su
bakinta har kunne tace ga amarya ga oga shirin
yayi yace kin ci ziro zainab kuma baki da sa'a
da kin fada daidai Allah kadai ya san yawan
ladarki tace sir zan gyara ga amarya ga
ango....yace kin makara". Zai wuce ta karbi
kayan hannunsa no sir ai ba wani sai ogan mu
yana yar dariya yace kinyi gaskiya zainab kina
damaki ashirin tace"thank yau sir mama tasa
musu baki har wata godiya ki ke yi ki na kware
baki kar kiyi karatu yarinya ki jira bonus" ta
bude kofa suna dariya dr al-ameen ya ce ina
ruwanta zainab ta amsa nima shi na gani ke ko
tukuicin baki bani ba amma kina sawa oga ido
suna tsaye tsakar daki ya laluba aljihunsa ya
zaro dubu biyar ya mika mata karbi wannan ki
kyaleta kawai sai mun hadu gobe -tana dan
murmushin jin dadi jim kadan suka dawo
daddauke da ledojin guda uku manyan gaske
mami taji dadi sosai tana sa albarka sannan ta
mika wa mama rafar kudi dubu ashirin tace
wannan dadinku yace in baki tasa hannu ta
karba tana kada kai haka da yawa mami to
nagade Allah ya saka da alkairi tace amin
sakeena al-ameen yace mun gode mami bari inje
wajen dadin mu za mu wuce ya wuce suka zauna
jiran fitowarsa basu dade ba suka fito tare mama
ta zamo daga kujera ta tsunna tayi godiya yace
ba wani abu Allah ya sauke ku lafiya tace amin
suka rankayo waje al-ameen ya daga murya yace
iya ta na wuce suka fito tare da ladi sukayi masa
sallama sannan suka karasa wajen mota sai da
suka bar get suka koma cikin gida suna masu
addu'ar sauka lafiya ,, lafiyar kuwa suka sauka
cikin yarda ubangiji ya sauketa gida ya taimaka
kwaso mata kaya zainab ta fito ta tarbe su
bakinta har kunne tace ga amarya ga oga shirin
yayi yace kin ci ziro zainab kuma baki da sa'a
da kin fada daidai Allah kadai ya san yawan
ladarki tace sir zan gyara ga amarya ga
ango....yace kin makara". Zai wuce ta karbi
kayan hannunsa no sir ai ba wani sai ogan mu
yana yar dariya yace kinyi gaskiya zainab kina
damaki ashirin tace"thank yau sir mama tasa
musu baki har wata godiya ki ke yi ki na kware
baki kar kiyi karatu yarinya ki jira bonus" ta
bude kofa suna dariya dr al-ameen ya ce ina
ruwanta zainab ta amsa nima shi na gani ke ko
tukuicin baki bani ba amma kina sawa oga ido
suna tsaye tsakar daki ya laluba aljihunsa ya
zaro dubu biyar ya mika mata karbi wannan ki
kyaleta kawai sai mun hadu gobe.............. -
Takarba mama na fadin ok mun gane dama da
mun ganki da manyan maki mun san na coge ne
yace eh ba komai zainab tayi dariya tace na gode
sir sai ka fito ta wuce tanayi wa mama dariya
yayi mika yana salati sannan ya zauna a kujera
ta ware ido tace zama naga kayi kar in zauna
tace gida ya kamata kaje yace korata ma kike yi
ta kada kai ba haka bane zai fi kyau kowanne
mu ya samu yay wanka ya huta kafin magariba
ta karasa ya munfasa yace haka ne yi hakuri don
Allah sai ina ganin kamar an daura ne unguwa
muka je muka dawo ta ware ido iye eh wallahi
kiris ya rage in fada katifar nan in kwanta fuska
yamutse tace wasa ka ke kin san Allah bada
wasa nakeyi ba a dai bar kaza cikin gashinta
miko min ruwa in sha in gudu,,Tace sai dai in
karbo maka wajen zainab ka sha na firij dina
babu sanyi yace to barshi kawai bari in tafi ya
zubo mata ido suka kalli juna yai dan murmushi
tace mene ne ya mike yana fadin nothing sai
munyi waya ko ta kada kai a ranta race dokta ke
nan ya wuce tanataka masa tana fadin ina
sauraronka tara kashi har mota suka y irin
sallamar sa suka saba yaja mota ya wuce ta
tako a hankali daki irin son da ala- ameen yake
mata shi yasa take jin kanta ita wata ce ta shige
wankanta ta fito ta sauya kaya ta kwaso
littatafanta ta baye a kasa ta fara karatu tana yi
tana zuba hamma barci ne sosai yake son
kamata gashi yamma tayi babu kyau yin barci a
wannan lokacin don haka ta aje littafinta
yunkura zata tashi da nufin fita wajen zainab
suyi hira ko barcin ya fita idonta, wani sauti mai
dadi ya fito wayarta alamun sakon ya shigo ta
dubi wayar kawai ranta ya kwao mata zakin
zuciyar tane tasa hannu ta dauko tana dan
murmushi ta bude sako amma sai taga sunan
yaya ali dake rubuce kamar haka, Assalamu
alaiki ya kanwata sai yau nayi saranda na sauke
hannayena daga rokon soyayyarki a yau na yarda
na amince kin sami gwarzo jarumin da nake da
yakinnin zai shaer miki hawaye tamkar yadda
nake zaton zan miki shine nake da tabbacin zai
rike ki babu gori balle mugun kallo ko zargin kin
taba yin wata mummunar rayuwa a. Baya amma
ina so ki aje a ranki wallahy wallahi!!! Wallahi!!!
Al-ameen bai fini sonkiba sai dai zanyi hakuri ne
saboda ke shi kika fi so a gunsa duk farin cikin
ki yake to nima ina son farin cikin ki mama shi
yasa na ke son abinda kike so ina muku fatan
alkari tare da tayaku murnar sake haduwa da
juna,,Yanyaki aliyu!! Hawaye kawai taji ya goce
mata saboda. Tausayin yaya ali to doka tagumi
tana kalubalantar kanta me yasa nake zama
butulu akan son da yaya ali ke nuna min laifi na
ne meyasa ban yarda. Na aure shi ba tun kafin
mu sake haduwa da dokta ta goge kwalla ta
kada kai abin ya dame ta kwari ta rasa inda
zata sa ranta taji sanyi sai kawai ta nemo
lambobin sa ta kira bugun farko taji muryarsa
yana mata sallama murya na rawa take fadin don
girman Allaj yaya ali kayi hakuri ka yafe min..
148-yace mama kuka ki keyi me yasa tace dole
inyi kuka yaya ali don ban taba sanin ni butulu
bace sai yau komai ya faru laifina ne kamar
yaya laifinki komai bana Allah bane tace laifina
ne me yasa ban aure ka ba tun kafin mu sake
haduwa da al-ameen kuma ni nasan kana sona
fiye da tuna ni na me yasa na zama butulu akan
soyayyar da kake nuna min ya numfasa ya dan
kada kai yace saura reni da kyau mama ai yanzu
mu ba yara bane dai dai gwargwado mun yi
hankali gane komai shirin Allah ne ni nayi imani
sabo dani ba mijin ki bane shi yasa aurenmu bai
yuwuba alkawari ne sai kin auri al-ameen shi
yasa Allah ya sake hada ku wallahi bana BAKIN
CIKIN auren ki da shi illa iyaka ina ciwon rasa
abinda ni nake so.. Abinda na rubuto miki a
sakona har cikin zuciyata haka yake Allah ne
shaida na saboda haka ki manta komai ke
yar'uwata ce ta jini abar alfaharina a ko'ina kar
ki sake zubda hawayenki idan har kin yarda kin
amince da abinda nake fadi kin yarda? Ta sauke
munfashi wasu kwallar suka sauko bisa kuncinta
tace na yarda da kai yaya ali ya ce to share
hawayenki tasa bayan hannu tana sharewa kafin
tace na share ya yi dan murmushi yace zamanin
kuka ya wuce har abada da yardar Allah farin
ciki muka fuskanta babu waiwaye yanzu gaya
min ranar da kuka fara ganin juna duk a sume
kuka fadi ko yasa dariya ta kubce mata ta cw
wane irin suma yaya ali ah ya baza ku suma ba
saboda murna ai so ba karya bane kanwata,,, ,
149-tace hakane amma ina mai tabbatar maka
shi din ma Allah ne yayi dole sai na aure shi
wallahi da da gaske nake bazanyi aure ba sati
uku muna dauki. Ba dadi har na bar makaranta
saboda shi daga baya muka sasanta saboda
abokinsa ya cika min ido yace baki kyauta ba
kuma da kin zalunci kanki akan aikin banza don
nayi rantsuwa kina son al-ameen to
alhamdulilahi tunda Allah ya gyara komai
sauranmu shan biki ko? Yayi dan murmushi ta
sunkuyar da kai kin yi shiru. Tace me kake so in
ce ki gaya min ranar shan shagali mu fara shirye
shirye tace kaji yaya ali baku. Ne masu sanyawa
ba yace eh gaskiya ne dama abba ya gayawa su
baba za'a zo asa rana da zarar sun turo ni zan
bada shawara kar asa da tsawo yaci gaba da
dariya yaya ali ke nan yace ba dai kunya ki ke ji
ba na sani to shi ke nan bari in kyaleki ki huta
sai mun hadu a gida ko to shi ke nan Allah ya
kai mu lafiya.. Yace amin suka danyi shiru jim
sannan tace yaya ali ya amsa ina jinki ta
sanyaya murya tace indan na gaya maka wata
magana zaka yarda yace me zai hana tace ina
sonka yaya ali ya yi jim shiru kana ya numfasa
yayi dan murmushi yace to na gode ki gaida min
angonki tace zai ji...bata karasa amsawa ba taji
ya kashe wayar ta runtse ido tana mai da
numfashi kwalla suka tsatso mata tayi sauri ta
goge su ta jawo filo ta jin gina shiru tsawon
lokaci sannan ta kada kai tace a fili Allah sarki
yaya ali Allah ya kara maka dan gana haka
zalika yaya alin jikinsa ya yi mugun mutuwa ya
dade yana sakar zuciya sai dai kalmar da mama
ta furta. Masa tayi masa dadi kuma ya tabbata
duk lokacin daya tuna zaiji sanyi a ransa, 150-
TABBATACCEN ALKAWARI duk inda ka duba
kofar gidan uban dawaki jama'a ne kwatsam
babu masa ka tsinke motoci kuwa sun tasar ma
bakin babban titi zan so mai karatu ya tsamo
mutum daya cikin wadannan daruruwan mutanen
ku kwatanta irin FARIN CIKIN da yake ciki a
halin yanzu kuma a wannan rana mai dimbin
tarihi cikin rayuwarsu sanye yake cikin wani
farin lallausan yadi yar ciki da wando hadi da
mulun malun hula fara da farin takalmi. Fari
hakan zai tabbatar da yanayin da yake ciki koba
ka kalli fuskarsa ba,idan ka kalleta kuwa kai
kace gonar auduga ne a haske da walwaki da
annuri wajen kwatance,Ayi kurum ke nan tabbas
shirun shine zaifi domin kwatancen bazai yuwu
ba tsaye yake jikin wata makekiyar jeep yayin da
wasu rukuni na manyan lokitici daga ko ina gida
da wajr suka zazzagaye shi domin dai akwai
wasu jajjayen kunnuwa su uku gab da za'a daura
auren dr lawal ya sake ketowa da wasu tawagar
bakin likitocin a matsayinsa na mai tarbar baki
al-ameen ya tarbesu kusan dama sune kawai dr
al-ameen yake zaton basu iso ba tawagar likitoci
ne da wasu ma'aikatan jinya daga sakkwato ana
ta musabaha baki yaki rufuwa kowa ka kalla ka
san yana cike da farin ciki daga ciki kuwa
waliyyai ne ke ta shirye shiryen gabatar da
daurin auran cikin dan kankanin lokaci alhaji
basiru ya mika amanar sakeena a hannun alhaji
nuhu waliyyin dr al-ameen akan sadaki dubu
hamsin... -nan da nan masu. Shela suka hau
aikin su wasu tsofafin mata suka fara rangada
guda makada da mabusan marafan lafai suka
dirfafi ango rerawa suke yi abin sai wanda ya
gani kwarai suka birge bakin turawan da ke tare
da ango shiyasa suka zaro wayoyinsu suka fara
dauka baya ga haka ga makadan nufawa nan
birjik kowa na gwada basirarsa da kwarewar sa
duk inda ango yake takawa kuwa kudi ne kawai
yake zubdawa marokan da mawakan na
kwashewa daga nan ma'aikatan hotel din da a
ka kwaso daga minna da kaduna suka fara raba
wasu manyan fararen ledoji guda biyu ake
mikawa kawanne mahaluki dake wajan koda
almajiri ne al-ameen ya bada umarnin a basji
kamar yadda akaba kowa leda daya kayan
kwalama ne dangin abubuwan da ake yi da
fulawa watau (snacks) nama kala kala akwai na
kaza rago da shanu jus iri iri da robar ruwa,
dayar ledar kuma abinda rabonka ya tsaga
domin dai babu abinda ba 'a raba ba,, Agogon
bango da na hannu da wayoyin hannu dardumar
sallah kai harda takalma da huluna turare masu
zafi banda kana nan abubuwa irin su tawul
hankici birorin rubutu da littafan addini da
sauran abubuwa zaiyi wuya ka bude jakar ka ka
sami kyauta kasa da iri bakwai can kuma sai ga
wasu kananan yara suna raba wata yar karamar
jaka mai ban sha'awa bakin jakar a tsuke take
in ka bude ka sha dariya domin babu komai
cikinta face SACET SACET NA PARACETAMOL
nan. da nan abokai suka kaiwa ango don ya
ganewa idanuwansa lallai yau shagalin na
likitoci ne yana karba ya kwashe da dariya
turawan wajrn na taya shi su kansu. Abin ya
basu al'ajabi har daya daga cikinsu yace lallai
wanda yayi kyautar nan yana da basira hakan
yasa al-ameen ya duba sunan take nan yaga
(CUT CEE BARAKA) ya kada kai yana yar dariya
yace best friend din ta ce aka ci gaba da dariya
tare da annashuwa mai yawa...... .idan muka
shiga daga cikin gida kuwa ita uwar gayyar
kusan can ake kankat.wajen ado tayi canji sama
da talatin tun kwanaki uku dafara shagalin
bikin.dole tasa domin angonta yasa mata kaya
akwati goma sha biyu.ita kanta dataga kayan
ciki saida suka girgizata.musamman kit din na
kayan karas.mai karatu nabarka da tunanin ya
suke?kusan yanxu abubuwa sun kawo
karshe.tunda anfara neman amarya ana zagawa
da ita gun manya dan su samata albarka.inna
saude ke riqe da mayafinta.sasan gidan aka
zaga da ita.iyaye suka tofa albarkacin
bakinsu.daga qarshe akajata falon abbanta.inda
gabadaya yayunta suke zaune shi.suna shigowa
ta wuce jikinsa,yawan shekarunta bai hanata
gaucewa da kukaba.shikuwa abban farin ciki!
yasanya shi zubda hawaye.yau autarsa zata tafi
gidan mijinta hartakai ga bai iya cewa
komaiba.sai yayunta ke mata fada tareda sawa
auren albarka.kamar wasa sai yazama dakyar
aka banbareta daga jikin abba.takoma dakin
ummanta takifa kai ciki.kukan rashin ummanta
takeyi.jitayi anzauna kusa da ita muryar yaya ali
taji yana fadin kiyi haquri kitaso mama!kowa
yashiga mota ke kadai angonki ke jira!nanda nan
tadago ta dubeshi duk idanuwa sun kode jajir!sun
qara fitowa waje. 153.yasake fadin pls.ki kwantar
da hankalinki ki taso a fita dake,,kin san hanya
ba kyau ko?batace komaiba.ta tashi zaune ya
miqa mata hankici yace share hawayenki!ta
karba ta share ya gyara zaman mayafinta ya rufe
mata fuska.sannan yakamo bakin mayafin
yajawo ta falo.inda su anty amina ke tsaye cirko
cirko.yace gatanan na fiddo da ita.ku muje nizan
sata a mota.ya wuce anata musu dariya.wasu na
guda.makekiyar jeep din sabuwa fil!itace angon
ya tanada don amaryarsa.yaya ali yasanya ta
aciki.inna saude da baraka tare da zainab da
anty amina suka take mata baya cikin
motar.gabadaya motoci suka tashi aka jera
kamar an rako shugaban qasa.sun iso minna
karfe biyar da rabi na yamma.akwai wasu
kosassun dawakai guda goma dake jiran
isowarsu.akan mahadar dazata shiga dasu
anguwarsu..amarya da zainab suka hau
biyu.sauran takwas din kuwa ango da abokansa
cikinsu harda turawan da sukazo daga
rasha.gaba daya sun daura alkyabba da rawani
na alfarma.musamman alkyabbar amarya tafi
kowacce ado.sai wanda ya gani suka tankaya
makada da mabusan sarakunan lafai na gaba da
bayansu suna qayata sha'anin.motoci na biye
dasu ga jama'a suna tafiyar qasaita anata dauka
da kamarori kala kala.tafiyar minti talatin
takaisu get din gidansu.mami ta fito ta tarbi
amarya da turarenta mai shegen qamshi.tana
fesa mata anata rangada guda.sannan takamo
hannunta suka wuce gida sauran ayari suka take
musu baya.sashi na musamman aka warewa
amarya da yan uwanta.babu abinda babu na
nau'in abinci dasu kala kalar kayan sha.sun cika
wani dan matsakai cin sito.sai abinda kake
sha'awa zaka debo kaci.
BAKIN CIKI 3***12 bayan anci abinci sallar
la'asar aka gabatar data riskesu a hanya.bayan
magrib da isha'i motoci suka sake kwashesu sai
gidan amarya.wanda layi biyu kacal ne a
tsakaninsu.dukiya taji jiki.irin dukiyar da aka
zubawa mama agidan sai ka rantse da Allah
baza a kwanta a kabariba.shikansa tsarin gidan
abin kallo ne.bayan yan rakiya sungama bawa
idonsu abinci.motoci suka sake dibansu suka
maida wajen mami.amarya kawai aka bari dan
bawa ango damar hutawa da amaryarsa.ganin
basuda isashen lokaci suma gobe lahadi zasu
koma zariya.karfe tara ya raka bakinsa hotel
dindaya kama musu.shikuma yadawo gida cike
da zumudi maras misaltawa..ita kuwa amarya
tuni tayi wanka saboda zafin datakeji.tasake
caba ado ta qame tana ta zuba qamshi.kawai
sallamarsa taji cikin dakin gabanta yayi mugun
faduwa.ta amsa masa tanajan mayafi.yatako a
hankali yazo gaban gadon ya zuba mata
ido.tsawon lokaci sannan ya sauqe
numfashi..yazauna gefenta ya duqa sosai.yaleqo
fuskarta suka hada ido.tayi murmushi tasadda
kanta qasa yayi dariya yace amarya
kenan.yadauke mayafin ya zura mata ido.yayin
da yake juyo fuskarta gareshi.ta dubeshi tana
murmushi kafin tace sannu da zuwa!yace
kezanyiwa sannu kin iso lafiya?tadan murmusa
lafiya lau.yace to alhamdulillahi.dukkan godiya
ta tabbata ga Allah.daya nuna mana wannan
rana dabamu taba mafarkin zatazoba.155.ya
lalubo yatsanta ya runtse cikin nasa ya nisa
sannan yaci gaba abinda nakeso dake shine ki
kwantar da hankalinki muyi zama na amana
wannan zama dazamuyi bana soyayya bane zalla
a'a harda ibada.mudauka hanyar aljanna muke
nema.ina fatan zaki zama mai bani hadin kai
har qarshen rayuwarmu.ta dubeshi ido taf
kwalla.tace insha Allahu zaka sameni mai
sadauqar da rayuwata a gareka.tareda bin
umarninka muddin bai sabawa shari'ah ba.kwalla
suka sauqa bisa kuncinta ya zura mata ido
sosai.yadan kada kai.meya kawo hawayen? yayi
sauri yajawota jikinsa.no pls bansan dalilin
wannan kukanba.murya shaqe tace farin ciki
dokta! bantaba tsammanin zansamu nutsuwa
kamar daba.azatona rayuwata tagama
rushewa.amma sai gashi kanata hidima dani
tamkar zaka auri.......yayi wuf ya rufe
bakinta.bana sonji.kawai kiyi shiru idan bazaki
fadi alheri ba.ta zuba mishi ido shima nasa sun
fara kadawa.ya share mata hawaye.kinga tashi
muje muyi alwala muyi sallah shine zaifi mana
kyau.yaja hannunta yakai bayi fara yi ki fito.tayi
ta fito.shida ya shiga sanda ya watsa ruwa tukun
yayi alwar ya fito.ya jagoranci sallar raka'a biyu
tareda miqa godiya ga Allah........ya juyo gareta
tana miqe kafafunta saboda gajiya.yace in
kwanta? tace kwanta mana waya hanaka?nazaci
za a min irin na rannan ne a koreni inaji ina
ganin abinda nakeso.tayi yar dariya.mesa baka
mantuwa?yayi lum da ido!yace sharp brain.!ya
qara bata dariya tace ai yanxu ban isaba,,,kayi
kwanciyarka mai gida... .kawai taga ya yada kai
bisa cinyoyinta kunya ta kamaata.ta kauda kai
daga kallonsa.yasa yatsansa yamaida
fuskarta.yace kalleni mana.mekike nufi da kauda
kai?ta yamutsa fuska tace ina na kai shi? yayi
dariya.wai naga har paracetamol kuka raba wai
ku doctors ko?tace babu ruwana aikin baraka
ne.tace alqawari ta dauka sama da shekaru biyar
dole ta cika.gashi nima tasaka min ajaka dazu
dazasu koma.yace kuma wlh ta birge har dr
begas yasarawa basirarta.sai dai kun mance
baku rubuta dose ba yakamata agayamana nawa
nawa zamu sha?tayi dariya ai yawuce
dokta.in,miqo maka kasha?.kawo min.tace to
dagani.ya manne ido daya yace nanfa daya.ta
watso masa harara.yayi murmushi.yace kinajin
yunwa ko?takada kai.yace aikuwa ko bakiji
yunwa dole kici tsarabata..tace dole?yace
yazama wajibi ne yau inshayar dake madara inji
manzon Allah.kinga kuwa dolene tayi shiru tana
kallonsa kamar yadda ya zubamata ido.karfe
biyar na asuba da kwata taji ana bubbugata a
hankali tabude ido taga fuskarsa dafda tata.yasa
mata ido za a iya tashi koda sauran gajiya?taja
mayafi ta rufe fuskarta yayi dariya.yasa hannu
ya yaye rufuwar.ta mulmula ta dirqa tadayan
side din tafada bayi.yanata dariya sannan yanufi
sallaya yatada kabbarar sallah.157.yayi nafila
kana yakawo farali.kafin ya kammala tafito ta
kintsa ta daura hijab.ta fara sallah.sai da ta
kammala tsaf harda azkar din safe.sannan ta
juyo ta dubi inda yake.yana kwance bisa
shimfida.yasa hannu yayi kiranta.ta miqe ta nufi
gunsa ta zauna gefe sannan tace ina kwana?
yatashi zaune yabita da kallo yace qalau na
kauna kefa?tace nima yace da kyau!kinsan wani
abu?ta girgiza kai.to rufe idonki.tayi murmushi
ta rufe.cike da annuri.ya tura hannu qasan filo
ya zaro dan mukulli.yakamo hannun damarta ya
damqa mata.bude ki gani.ta bude ta bishi da
kallo dan mukulli nagani.yace hausawa sunce
yaba kyauta tukuici.wannan shine tukwaicin
kyautar kanki daki ban jiya.wata yar mota ce
kiyi maneji.kanta yayi gingiri gin dokta
shine......ya nuna mata alamun tayi shiru banson
ji ok?ta wuce jikinsa ta qnqame.ban cancanci
wannan ba dokta!don Allah kadaina wahalar da
kanka akan......ya daka mata tsawa akanme?
nace akanme? ta gigice cikin kuka ta kasa
magana yace wallahi! wallahi!!wallahi!!!idan
kikasake aibanta kanki ayau zan barmiki
qasarnan.sai ranar da kikayi hankali
zandawo.kina jina?haba!jiya jiya fa kika min
alqawari? kina nufin abaki ne kawai?to wlh
bazan dauka ba.bazan jure jin lBAKIN CIKIN
Lafazinki susa min hawan jini ba.kin gane?
tafada jikinsa ta qanqamesa sautin kukanta na
ratsa kunnuwansa.shiyasa zuciyarsa taci gaba da
tafarfasa..don baison jin kukanta sam.haka
kuma bayaso taci gaba da aibata kanta.abinda
yafii tsana da kyama kenan.dan haka ya kyaleta
taci gaba da zubda hawayen.amma yadda ta qara
qanqamesa kamar zata shige jikinsa.shiya
tabbatar masa da lalle haquri take bashi dukda
bata furta da bakintaba. hakan yasa fushinsa
yadinga sauqa harya rabu da zuciyarsa.yabar
masa tausayin amaryarsa kawai..ya tallafo kanta
yasauqe numfashi ya sassauta murya.tun ranan
da Allah ya hada ni dake ya manna min
matsanancin sonki a zuciyata har rana mai
kamar yau. Banji sassauci ba.duk wani abu
dakikaga nayi a halin yanxu dama shiryayye
ne.tunda mafarki nane kawai yazama
gaskia.karkiyi mamakin irin tarairayar da
zanmiki cikin zaman da zamuyi.kiga kamar
shekaruna sun wuce hakan.ni a wajena dole
inyiKARA'IN Soyayyarki.duk abinda na shirya
mana a farko sai na nuna miki.tunda ubangiji ya
nufeni da mallakarki.idan kuwa shekaru basu
hanani dawowa yaroba.banga dalilin dazai
hanani aiwatar da abunda nayi niyyaba.don
faranta ran wacce ta faranta mini,,,,,ya dago
fuskarta idanuwa sunyo jajuz.yaci gaba pls
kidena kona zuciyata da zafin hawayenki.ta zura
masa ido na tuba dokta!yayo dan murmushi
amarya bata lefi. Kota kashe dan masu gida.tace
gara da kace wai.ya goge hawayenta baki yarda
ba? yanxu ki kamo waleed ki yanka ai babu
abinda zanyi.illa in miqo miki waleeda itama ki
yanka duk cikin nishadin amarci ne.159.tace
Allah ya tsareni nazaama mahaukaciya kenan!ba
amaryaba.karka sake min irin wannan misalin ya
lakucr hancinta nima karki sake min asaran
hawayenki.tace idan bakason hawayena kadaina
min hidima..ya dubeta yace uhmm....to shikenan
nadena.tamiqa masa yatsanta promise? yace
bawani promise.karkiyi mini wayau maman
waleen.ta watso masa harara.yafara dariya ai
gaskia kisan nanda watanni tara zuwa goma zaki
haifi ameer ko ameera.kinga kuwa hidima
takama babab waleed da waleeda uba awajen
ameer da ameera.ta shagwabe fuska takai masa
duka a kirji.ya kece da dariya yakwanta a filo
yana kallon shagwabar datake masa.zaka dace
da roqo tace masa wannan irin kirari?yace eh
bandeji haushiba..tayi dariya ta lallabo jikinsa
nagode dokta Allah qara budi na halas!ya
tallafota ameen bebina.abinda kawai nakeso ki
rinqa fadi kenan kinji?tayi far da ido insha
Allahu.good sai gari yawaye muje kiganta tana
motor park.ta dada shigewa jikinsa double thank
sir!sir sis!?babu sir a wannan gidan daga darling
sai cweethrt sai honey. Sai sugar da
mazarkwaila.ta fashe da dariya tana kada
kai.yaci gaba da nishadantar da ita tuntana ji
har bacci mai dadi ya saceta.shikuwa farin ciki
ya hanashi bacci gani yake tamkar a mafarki.wai
yau shine tare da sakeena?kana ya aje numfashi
yace Allah nagode maka. I60.qarfe takwas da
rabi wayarsa dake silent take hasko wa alamun
ana kiransa.yasa hannu yadauka mami ce take
kiransa..yayi sauri ya amsa sannan tagayamasa
direba nanan zuwa da abinci safe.yayi godiya
suka kashe wayar.ya dubi mama dake kokarin
tashi zaune na tasheki koh?tayi lum da ido
takada kai dama yakamata intashi.kiyi me?tace
inyi wanka inshirya.kafin baqi su fara zuwa.yace
gaskia ne mami ne takkira waya wai direba
nanan zuwa da abinci kafin ya iso jekiyi wankan
tace to.ta sauqa tashiga bayi ta tsalo wanka
tadawo baya dakin.taci gaba da shirinta.kafin
wani lokaci tahade kanar sarauniya.tafar a
gyaran gado kenan taji sallamarsa shima
yahade.da jar shadda mai duhu suka zubawa
juna ido sannan tayi murmushi tajuya taci gaba
da aikinta.ya matso yakama yana tayata.yana
fadin kinkalleni ki dauke kai.banyi kyau bane?
tace aidama kai mai kyau ne dokta!rudewa nayi
nakasa magana.ko?kamar yadda nima na gigice?
aida kika waigo kiris ya rage na zube qasa.sai
kuma kika dauke kanki.tace ashe na taima
keka?yayi yar dariya kintaimaki kanki dai.kamar
yaya?idan nazube.a sume zaki iya kwasata?
tafara dariya Allah yashiryeka dokta!wayarsa
taqara haskawa daga can inda take yashe .yasa
ta miqo masa tana fadin mami ne kuwa.yakarba
da sauri yadanna ok. Hello mami!tace wai ina
kake ne tun dazu?naketa kira?yace ayya yi
haquri mamina wanka nashiga.tace to direba na
waje fiyeda minti talatin wai baku fitoba.ai baiyi
maganaba mami mai makon yataba kararrawa?
sun ciki shirme mutanen nan wlh. yakashe wayar
yayo waje mama ta biyoshi harwaje.yana zaune
yatasa kuloli gaba sunata zuba hirada mai
gadi.ganin dokto yasa duk suka miqe sukanufosa
sukayi gaisuwa bai amsaba yafarafada.meyasa
kuke haka?donme aka manna waccarqararrawar?
kudaina maida kanku yan qauye gaku a
birni..suka ce tuba muke dokta!yayi guntun
tsakiyakama hannun mama suka wuce ma'ajiyar
motoci.Da ita direba ya lallaba ya kwashi kayan
abincin.maigadi yataimaka suka shigar falo suka
fito.mama tadubeshi bansan dokta na da fishiba!
shima ya dubetahaushi yabani wlh.ni banso
mutum yarinqa qasqantar da kansa saboda
wani.kawai yazo ya latsa kararrawako bacci
nake zan sauraresa.ko uzurin kansa balle
namami amma sun tasa kuloli gaba kuma hadda
magajiya biye masa..ta qara matse yatsunsa
Allah hucizuciyar wakilin marafan lafai.ya zura
mata ido yanasoyayi dariya.yaushe kuma kika
ban wannan rawanin.? tace dama can haka kake
bawani sai kai babanwaleed da waleed ameer da
ameera.ya bushe dadariya dai dai lokacin
dasuka tsaya gaban motaranrufeta da
tamfol,yace badan karki sake kukabadana qara
wata kyautar motar.!tayi dariya wannan mata
isa.tunda fushin dokta ya sauqa.buqata ta biya
danshine farin cikina.yabita da kallo yarasa me
zaicesaboda dadin kalamanta.yajawo ta jikinsa
Allahyayimiki albarka.tace amin.toga motarki.ta
ware idotace oh my god.!yasa hannu ya kwashe
tampoldin.idonta ya nuna wata tsaleliyar farar
mota.akallakudinta zai kai miliyon
biyar.162.hannayenta bibbiyu ta rufe bakinta da
wasa kakekoh?yace duk yadda kikace.tayi kwal
kwal daido.kwalla na neman zubowa.ya murtuke
fuska idankika bari hawayen nan ya zubo Allah
zanyitafiyata.kinji na rantse.batasan lokacin
datarungumeshi ba amma takasa magana tasan
tanayi zatayi kuka.sai shi ke fadin zanso kice
wani abubebina.don kalamanki nasanyani
nishadi.tadago tadubeshi bayan ta tabbatar ta
shanye hawayenta.banida kalaman godiya dokta!
wlh na rasa mezance.kagayamin me zance dan
Allah.?yakamohannunta yace zo muje kici abinci
wata qila inkin qoshi ki tina me zakice.ta kwace
hannunta tanazagaya motar kamar yar
qauye..tasa bakinta tasumbaci motar.yakawo
kuncinsa saura ni.shima tasakar masa babu
wani noke noke.tace ngd ngd.ngddokta. Iluv u
soo much iluv u yace nima haka murnarta isa
haka yar shagwaba nafara jin yunwafa.tayi
murmushi Allah ya temaki wakili muje kaci
abinci yagirgiza kai yace wannan nadi yamin
kina fasa min kaigaskia.tafigi hannunsa suka
wuce tana waiwayarmotarta.yace kina tafe kina
waige idan kikaci da bakiAllah bazan dagaki
ba.a shagwabe tabe Allah motarne tacika kyau.!
shima ya maimaita a shagwabe.ta fara dariya
jitayi ya ciccibota ya sure ya na bari kigani kada
kijamin ina tsakiyar angwanci.gabadayakunya ta
kamata. yakashe wayar yayo waje mama ta
biyoshi harwaje.yana zaune yatasa kuloli gaba
sunata zuba hirada mai gadi.ganin dokto yasa
duk suka miqe sukanufosa sukayi gaisuwa bai
amsaba yafarafada.meyasa kuke haka?donme
aka manna waccarqararrawar?kudaina maida
kanku yan qauye gaku a birni..suka ce tuba
muke dokta!yayi guntun tsakiyakama hannun
mama suka wuce ma'ajiyar motoci.Da ita direba
ya lallaba ya kwashi kayan abincin.maigadi
yataimaka suka shigar falo suka fito.mama
tadubeshi bansan dokta na da fishiba!shima ya
dubetahaushi yabani wlh.ni banso mutum yarinqa
qasqantar da kansa saboda wani.kawai yazo ya
latsa kararrawako bacci nake zan sauraresa.ko
uzurin kansa balle namami amma sun tasa kuloli
gaba kuma hadda magajiya biye masa..ta qara
matse yatsunsa Allah hucizuciyar wakilin
marafan lafai.ya zura mata ido yanasoyayi
dariya.yaushe kuma kika ban wannan rawanin.?
tace dama can haka kake bawani sai kai
babanwaleed da waleed ameer da ameera.ya
bushe dadariya dai dai lokacin dasuka tsaya
gaban motaranrufeta da tamfol,yace badan karki
sake kukabadana qara wata kyautar motar.!tayi
dariya wannan mata isa.tunda fushin dokta ya
sauqa.buqata ta biya danshine farin cikina.yabita
da kallo yarasa me zaicesaboda dadin
kalamanta.yajawo ta jikinsa Allahyayimiki
albarka.tace amin.toga motarki.ta ware idotace
oh my god.!yasa hannu ya kwashe
tampoldin.idonta ya nuna wata tsaleliyar farar
mota.akallakudinta zai kai miliyon
biyar.162.hannayenta bibbiyu ta rufe bakinta da
wasa kakekoh?yace duk yadda kikace.tayi kwal
kwal daido.kwalla na neman zubowa.ya murtuke
fuska idankika bari hawayen nan ya zubo Allah
zanyitafiyata.kinji na rantse.batasan lokacin
datarungumeshi ba amma takasa magana tasan
tanayi zatayi kuka.sai shi ke fadin zanso kice
wani abubebina.don kalamanki nasanyani
nishadi.tadago tadubeshi bayan ta tabbatar ta
shanye hawayenta.banida kalaman godiya dokta!
wlh na rasa mezance.kagayamin me zance dan
Allah.?yakamohannunta yace zo muje kici abinci
wata qila inkin qoshi ki tina me zakice.ta kwace
hannunta tanazagaya motar kamar yar
qauye..tasa bakinta tasumbaci motar.yakawo
kuncinsa saura ni.shima tasakar masa babu
wani noke noke.tace ngd ngd.ngddokta. Iluv u
soo much iluv u yace nima haka murnarta isa
haka yar shagwaba nafara jin yunwafa.tayi
murmushi Allah ya temaki wakili muje kaci
abinci yagirgiza kai yace wannan nadi yamin
kina fasa min kaigaskia.tafigi hannunsa suka
wuce tana waiwayarmotarta.yace kina tafe kina
waige idan kikaci da bakiAllah bazan dagaki
ba.a shagwabe tabe Allah motarne tacika kyau.!
shima ya maimaita a shagwabe.ta fara dariya
jitayi ya ciccibota ya sure ya na bari kigani kada
kijamin ina tsakiyar angwanci.gabadayakunya ta
kamata. ta rufe fuska da hannayenta tana
salati.ya diretaa falon.ko nauyi batadashi ashe
fafa lolo ce..ta watsomasa harara tace gemai
gemai dakai dokta?yace tome akayi?ai na
gayamiki sai anyi kara'i.ta girgiza kaihakane?to
saura kara'in cin abinci.bismillah zaunasuka
ciyar da juna cikin annashuwa.qarfe goma da
rabi suka koma daki ya tsinci missed cal goma
cikinwayarsa.yadanna yaga gabadaya dr lawal.ya
dafe kaina shiga uku! ta dafe kirji da akayi me?
yace missedcal goma sakeena yau na mutu
wajen drlawal..tawangame baki maza kira karya
sake kira.yakwashi sauri yana kiran layin yaqi
dauka shima saidaya kira sau uku yana tuqi
sannan ya dauka.danAllah malam karka dami
mutane!ya kashe wayarsayabar dr alameen da
salati.ya take mota dan kankaninlokaci yakaishi
hotel din.yana shiga dakin yakamakunnuwansa
yana i'am very sorry.! very sorry!!verysory!!!
Suka fara masa dariya.dr will dake malami ne
agaresa yataso ya riqesa manta dasu sun
mantaangwanci kakeyi.yace thank you sir!ya
bubbugakafadarsa bawani abu ya amarya?ya
amsa lafiya lautake.yace dakyau.zamuje mu
gaisheta daga can saimu wuce dan karmu rasa
jirgi.yace yes sir!ina fatankunci abinci?yace
munci yabi sauran duk suka gaisa.yana zuwa
wajen dr lawal ya ballo masaharara.sai ya
tsugunna yace ina kwana baba lawal?Dariya ta
kubce masa.sauran ma dabasu san meyaceba
suka kama dariyar ganin dr lawal yakai
masaduka.yace masa bafa kai kadai ne mai
mataba.mumamunaso muje mugansu.sannan
soyayyar nan ba afi mu iyawa ba. yayi dariya
yace nayarda na amsa laifinaamin haquri.yayi
shiru yana kallonsa murmushi yayiyana fadin
kun shirya mutafi? munshirya ango.ya juyaya
tambayi sauran da turanci duk sun shirya
sukafirfito da jakukunansu.suka rankaya wajen
amarya.tasawo hijabi ta fito suka gaisa.minti
goma kacal sukayi cikin gidan suka fito dr lawal
da dr alameen sukakaisu filin jirgi suka tashi
zuwa legos.inda zasu tashizuwa rasha.shikadai
yadawo gida domin dr lawalyadau hanyan
zariya.gidansu yaja birki ya tsayaharsuka gaisa
da baki haryana tsokanar baraka inafata kema
kin kora paracetamol din.?tace ai wannan dole
ne over dose ma nayi saboda inada
likitoci.yafitoyana dariya suna tayashi.ya wuce
shashin mami sukagaisa yazarce na dadi suka
gaisa daga nan yaketambayarsa yaushe zasu
wuce?yace bayan sallarla'asar.tare suka bar
gidan a motar dadin yamasarakiya wasu
harkokinsa.sukuwa yan rakiyar amarya mami
tasa aka maida su wajen mama don
kammalawasu al'adu.bayan sallar azahar dadi
yadawo da doktalokacin baki sungama shiryawa
komawagidajensu.godiya maiyawa da
kyaututtuka suka samugun mami da dadi.haka
dokta yanuna farin cikin saakan karamcinsu.bus
din kamfanin dady mai daukar mutum talatin ita
ta kwashesu suka bar mama nakwall.
BAKIN CIKI 3***13 Yasa mata ido ko yanzu din
ma idanuwan na ta tamsuke da kwalla ya girgiza
kai yace karki dami. Kankinasan kina da
masaniyar ajali sauka yake kodasababi ko babu
da zarar kwanakin suka kare shi kenan an gama
magana fatan mu kullum Allah yasatana cikin
hasken kabari tace amin yasa yatsansa ya goge
kwallar daya sauka kucinta please ya wuce
ina.Fatan kin shirya zuwan ameera kafin in koma
da saurita dube shi har da zame hannunsa a
kafadarta yakece da dariya harda tureni tace me
ka sani dole intoreka yace to ai ba ni na fara
fadiba mami ce ta kosaitama ta sami takwara ita
din ma bata sani ba kam!bai taba ganin irin
wannan hararar ba yasa yake ci gabada kwasar
dariya -mai da wukar mai jego duk ni kadai
wannankallon please rage in sami na gobe ta
make shi tanadariya ko tausayina ma babu abin
don bakaga yaddajini ke zuba a jiki na bane take
nan jikinsa kuma yayila'asar ya sake kamota
yace Allah sarki bebina toAllah ya kara miki
lafiya ina ganin ya kamata mu binciko dalilin
yawan zubar jinin idan akwai yuwuwarmagance
matsalar sai a tareta da gaggawa kogaskiya ne
kara a bincika yace sha kurumin kiwannan dole
ne tsakani da Allah ina son Ameera takada kai
tana kallon sa ai na san baza ka daina fadiba
yace "Thanks God da kika san haka yabi bebinsa
da kallo sannan ya sumbace shi yace ko dadina
Allahda ikonsa yayi yar hamma cike da fara'a
yace"yausee" shi ma ya amsa ya kara sumbatar
sa yace "whata sweet dady! Ta tabe baki tana
kallon sa sun shararihira har mami ta dawo ciki
tayi kwanciyar ta tabarsusuka kwana hira Washe
gari aka sallameta bayan ya gama tattaunawada
likitocin mata watau(gynea doctors) akan
matsalarta wanda suka tabbatar masa akwai
yuwuwartaimakon da za'a bata amma sai wani
cikin ya samusun koma gida baki suka ci gaba
da zuwa daga ko'inasuna ganin bebi yayin da
angon karni ke ta shirye shiryen walimar suna
adalilin bai fara aiba tukyna yasami damar zirga
zirgarsa yadda yake so har zuwagobe suna kafin
yamma gida yayi tankam da bakitundaga lagos
har arewacin mu nan tun daga lokacinhidima ta
kankam zuwa washe gari da ya kasancecikar
suna hajiyar ruqayya mata sami zuwa a ranar
dauke da alkairi mai yawa anci an sha a
sunansaifullah an bar arziki inda yake Rana ta
biyu sai da aka gyarewama jego ko ina sannan
baki sukafara tafiya rukuni rukuni anti rabice
kadai ta kwana hudu ta warwaregajiya sosai
kana ta koma innasaude ke kula da wankan
jegontahartayi arba'in tana je tana katatuta
kwashi alheri mai yawa sukakoma tare da mami
aka bar mamada dan bebinta maryam ta
samomata yarinya zata kai shekara shabiyar tare
suke zuwa makaranta tazauna mata da ameer a
motasaboda ya ruka samu yana shannono
isasshe to Allah ya raya shiya kwao Ameerar da
ke ta fatansamu nan gaba -BAYAN. SHEKARU
BIYAR. Satinda ya wuce ne akayi shagalin
bikinnadin wakilin marafan lafai wandaakayi a
fadar mai martaba sarkinlafai wannan yana daya
daga cikinabubuwan da suka kawo shi
wakilinmarafan kasar nan watau DR AL- AMEEN
dalili na biyu don tafiya daiyalansa sakamakon
makarantardaya samo wa mama taci gaba
dazurfafa iliminta shi yasa bayanbikin nadin
suke ziyarar bankwanatare da ban gajiya ga
wadan dasuka sami halartar bikin nadin tunsha
biyun rana suke garinfandogari da yaran su Allah
daikonsa mama ta iske yan uwantada yawa
suma sun zazzo ganin gidairinsu danlami dake
sakkwato gakuma yaya ali da iyalansa shi
yasafarin cikinta ya karu sukayi ta hirabar bayan
sallar la'asar abubuwadangin abinci da kudade
ta kawowa kawun nan ta da matansu Ta fito
suna tasa mata albarka yayaali na dauke da
karima(ameera)yar shekara daya da rabi dokta
yabude mota yaran suka zauna gidanbaya da
hafastu mai kula dasu yayaali ya mika mata
ameera ya rufekofar yayin da mama ke shiga
gabata zauna itama yaya ali ne ya rufemata
kofar ta dubi shi tanamurmushi na gode yace
Allah yatsare tace amin gaba daya
sukayisallama da al-ameen sannan yashiga
mazauninsa ya tada motasuka wuce ta dube shi
tun kafinsubar layin tace ranka ya dade
zakakaini wani gida nan bayan tashayace kina
so muyi dare dai yau Aawallahi bazama zanyiba
kawaigaisawa zamuyi in fito mantawanayi da
muka fito wajen inna damun wuce yace ok amma
donAllah sharp sharp kin san yanayinhanyar tace
Allah shi taimakimarafa ya dan dubeta
Dungurugunkuma? -tace me ya rage gaba
kadanmurabus zai yi ya bar maka gadonyace har
naji sanyi da kikacemurabus tsoran bakin ki
nakejikinsan wakilin ma ke ki ka faranada min
kawai naji dadi yace waiza'a min sarautar
wakilin marabatayi murmushi tace bakawai
baneakwai cancanta shima yaga dacewara
tattare da kai yace uhm..kinsabafasa min kai
wakiliyar marafanlafai ta dubi shi tana yar dariya
daidai yana tsayuwa kan mahada indashagon
danliti yake da Ameeara tafasa kara ta firgita
kowa duk sukajuya suna tambaya lafiya
hafsatutace ameer ne ya ja mata gashi Mama ta
nuna shi kafara ko waime ya hadaka da gashinta
nekullun sai kaja mata dadinsu yayidariya yace
baki ganin shi baya dashi al'ajabi abin ke bashi
ya ganshizalau zalau yana lilo ko dadina taceba
wani muguntace da wasuidanuwansa kamar na
agolannufawa, dokta ya saki baki suwaleeda
nata masa dariya jim yanakallonta kafin yace ke
maimaitaabinda ki kace kamar wa? Ta faradariya
ai kaji abinda nace tace okdama idan bana nan
zama ki kekina yankar min dadi akan wannanyar
rigimar yar taki ko to dadinabin idon nufawan
aka gani akarude ta tabe baki Allah shi
kyautameye a idon zai bata amsa ke nanwani.
Tsoho ya dauki hankalinsa dayake buga glass
din tagarsa kumada alamun taimako yake nema
nanda nan tausayi ya. Kamashi ya zuge glass
dinyace sannu baba kaitsaye yace ataimaka min
da kudi inci abincitake nan yasa hannu aljihu ya
zarodari biyar ya mika masa ya wuceda sauri ko
godiya babu tabbatuwarbabu hankali ke nan ya
kada kai yamaida glass sama yana fadinALLAHU
AKBAR ALLAH mungodemaka ki wannan
kyakkyawanmutumin da gani yana da zubi
dafulani ko ina yan'uwansa suke sukabarshi ya
lalace haka yanzu hakaidan kika bibiya matsalar
karamaceamma saboda rashin kulawa yasata
girma shiru bai. Ji tabashi amsaba fuskarta na
can tana kallon indatsohon yabi ya taba ta ta
waigo anatse ta dube si ta ina zamu bitace ka
hau titi kabi dama ya hautiti yana mamakin
yadda jikinta yamace haka shi yasa bai gama
hawatitinba ya tambaya yanaga kamarbaki tare
damu Tayi dan yake ta kada kai kaga tsohon
nan... Ya katseta bashi nake gaya miki ba abin
gwanin ban tausayi ko ina yanuwansa suka
barshi yana yawo tsirara? Gaba daya kayan
jikinsa ba su rufe al'aurarsa ba mtsw.. Ya ja
tsaki ta kara kada kai. Tace hummm..... A
zatonka tshone ko?da kyar in zai girme ka tsabar
rashin tsoran Allah ya maida shi haka banganeba
tace a takaice shine DANLITI... Yayi shiru yana
dawo da tsohon cikin kwakwalwarsa nan kwanar
zaka shiga yaji tana fadi yasaki siginal ya fada
har suka ja birki kofar gidan maman fati ba
wanda yace wani abu game da danliti ta kalli
gidan yana nan yadda yake sai dai akwai mutane
a. cikinsa ta dubeshi tace kaga wancan gidan
ciki ya ajeni ya rinka cin zarafina ya murtuke
fuska yace donme kikace in kawoki nan tace zan
gaida maman fati ne matar da ta rinka taimaka
min da abinci da sutura harma da kudi.yace ina
ne gdan -ta nuna na wanda zuke tsayegabansa
yace maza ki shiga nimakice ina gaisheta ta
wuce da sauricikin gidan ta bar dokta
zuciyarsana tafasa baya son ganin gidanamma
idonsa yaki daina nunamasa shi yan mintoti
kalilan mamata fito tare da maman fafi
cikinmurna har kunne tana fadin inayaran suke,
gasu nan a mota tadan duka suka gaisa da al-
ameensannan mama ta bude mota ta gayara duk
suka gaisheta ke mamahar kinyi uku tace ga
sunan kumakina gani lallai ba shakka Allah
yaamfana miki su tace amin nagodetace nike da
godiya wannan irinhidima Allah yasa bata gama
rufebaki ba al-ameen ya miko wasukudade yace
ki kara mata ta amsata mika mata zasu kai
dubu gomabaki sake ta karba tana godiyamama
ta shige mota tana fadin tosai wani lokaci Allah
ya sauke kulafiya na gode da zumunci
mamaAlhaji nagode yace ah muke dagodiya yaja
mota tana daga masuhannu Sun hau titi sosai
bakin al-ameen amace yake mama ta dube shi
tacekana mamaki ko ya numfasa yaceke dai bari
lallai Allah yayi gaskiyabaya zalunci baya son
mai zalunci"anyway"mu koma can inda kikaraina
min wayau ki kace ido kamaragolan nufawa ko?
Tace na shigauku yau yace sosai kuwa tunda
kintaba dadina tace ayi min afuwa abari idan na
samu abba na sai karama kace ido kamar agolan
fulaniyace ke ki kasan wannan idan ma Agolan
KATSINAWA ne "idon't care" tace wayyo Allah
tubanake yi Allah ya taimaki wakilinmarafa
Baban waleed da waleedauban Ameer da Ameera'
yayai yardariya yace ga tsoro ga neman fadaeh
ba komai muje a hakan yacekin san wani abu
gaskiya nextweek zamu tafi tace ayya na
zacizamu jira waleed kaga sati nasama za suyi
hutu kuma hutunkarshen shekara ne yana da
tsawozaiji dadi idan ya kasance taredamu ya
dubeta yana murmushinaji maman yara ina fatan
rokonaya karbu ya kamo yatsunta yamatse yace
babu wani rokon ki daba zai karbu ba a waje na
muddinnafi karfinsa karki manta kina gabada
dukkan abinda na mallaka hakakuma idan kin
dake iyayena dukduniya bani da abinda na fi
sokamarki raina yana kaunarkisakeena babu
abinda zaki nema awajena in hana ki insan
karshenmagana? Daya yau na zama Drsakeena
kawai ta tuntsire da dariyakai dokta na wannan
shinebanbarakwai yace namiji da sunansakeena
ai duk cikin so ne tace nayarda domin nima na
shagala dayawa kaga idan na dubi abba nayana
tafiya da kansa na tuna iringagarummar
gudummawar da kabayar Allah ya taimake mu
sai injikamar in mika wuyana ince kayanka
kullum gani nake ayyukanasunyi kadan ya
dubeta ya yimurmushi ya kara matse
yatsuntayace kiyi shiru kawai karki sanirusa
kuka tayi yar dariya yajahannun bakinsa ya
sumbata yace "ILOVE YOU" tace ME TOO ya
dubetaSO MUCH ta kai hannu zata turahular sa
ido waje tace kai na turerawanin wakilin yace
aikaji dadi yahadani da aiki dole sai na
nadafarin. Nan bisa kai idan zan shigajama'a -
tace kuma yayi gaskiya fa shirawani ai
musulunci ne kuma yanakara kima da kamala
dadin dadawayana yiwa dokta na kyau yace
banson zakin baki tura shi kawai kigaya min inji
dadi tasa hannu tatura hular goshi tace SO
MUCH shike nan? Yaran suka ji sun daukidariya
a bayan mota waleeda hardatafi ameer ya mike
ya ziro kansaya kama hular dadi gyara
hularkakaji suna ta dariya yace gyara mindadina
momin nan bata ji ko yagyara masa yana fadin
ido kamaragolan nufawa suka kece da dariyatace
oho dai dara taci gida yacedadina kayi shuka a
idonmakwarkwa bai dai gane karinmaganar ba
dariya kawai yake yi azatonsa dadinsa ya rama
ne shiyasa mama ke ci gaba dayi masudariya
motarsu na cilla gudu a titi.ALHAMDULILLAHI
sai muce Allahya sauke su lafiya a wannan
tafiyada wacce zasuyi zuwa rasha sati nasama
haka nima ina godiya gaAllah daya bani ikon
kammalawannan fararren labari zanyiamfani da
wannan dama in rokiaddu'a wajen bayin Allah
mutaimaka da addu'a ga yan'uwanmumusulmi
wadanda suka tsinci kansucikin irin wannan
musiba damakamatansu, TAKU HAR KULLUM
YAR MUTAN KAGARA KARSHE ALLAH HADAMU
A WANI LITTAFI.



COMPILED BY
ESHAAT SMILER HOM OF HAUSA
NOVELS DOCUMNTS
adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *