Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, September 4, 2019

DAMA TA COMPLETE HAUSA ROMANTIC NOVEL

adsense here
DAMA TA COMPLETE HAUSA ROMANTIC NOVEL
[3/12, 8:46 AM] Hauwa: Bismillahir Rahmanir Rahim


          *DAMA TA*

         
               *Na*
             
         *Batul Adam jattko*

1...
    KAINUWA WRITES ASSOCIATAN🤝 




  Tuki yake a hankali  cikin wata katuwar jeep kiran  vence, Yana karewa garin nasu kallo kamar ba anan aka  rage ran dunbin al umma ba  sosai yake kallon mutane  wanda yasan badan bakin glass  ne ba bai isa yayi wannan tafiyan ba, anguwan gargar anguwa ne na masu karamin karfi amma cikin garine sosai dan  makota suke da shewuri. 
     
Wayan sa ce tayi ringing  yajawo yadauka  yace " Allah yatemaki  ummi na  daga ummi tace "kamal be gaya maka inason ganin kaba 
Ya "gayamin ina gidan abba musa ne gani akan hanyan dawowa, 'tom kazo gidan yafatime  nasa hanif ya yauko Hadim dinma gata nan kazo muna jiranka.
Yace "ummi lfy kuwa
 tace "se kazo de
   "tom yace cikin jimami  dan dagajin yanayi muryan ummi yasan babu lfy,
 Sauke wayan yayi dai dai da  hango wata mata da take  taku dakyar  dalilin tsinkewan takalmin ta  ga shijab dinta a yage tabaya sosai   duk da bayan ta yake gani yasan tana bukatan temako  sosai dan shi baya ganin irin wannan yawuce
 Horn yayi tare da dan zuge glass din kadan yanda baza agane shiba  yaci gaba dayin horn din amma matar ko juyowa batayiba  yadan sake lekawa  yace "iya ba kyajin ranane g.......
 Magan nan ne yamakale masa   ganin yarinya.     wanda bazata wuce  15 ko  16  dasauri yakarasa  parking      dan zaton sa tsohuwa ce
 cikin harshen barbarci  yace" ke  ba kyajin rana ko bakiga shijab dinki ayage ba  har yazu bata juyo ba
   yayi wani tunani 'azuciyar sa  yace ko de mahaukaciya ce dan ya manta da halin yan Nigeria masu wasar da maskinan su a titi 
Danshi dafarko  yadauka  tsohuwa ce  yatemaka mata yakaita inda zai siya mata takalmi 
 
     Amma ganin yanda take taku anise yasa ya gane ba alamun hauka atare da ita    yasake cewa  ke bakiga hijab dinki ayage yake ba tabaya  kuma kina tafe cikin rana 
  Sai  asan nan  ta  juyo
 Cikin tsoron taja da baya
Ganin  bature yana kanuri sak   shiko yazuba mata ido  yana kallon ta  sai a sannan yagane  tana da zanen bare bari a fuskanta amma kanana sosai   kuma bibbiyu ce akowane kumatunta  kawai  ba irin taran nan nacika fuska aka mata ba  amma bakace sosai  duk da harda kazanta  karin bakin nata  hancinta baida tsawo  amma baza akirashi Tami lelle ba sai amfkin  ido wan kam tana da shi masha Allah

    Kallon ta yake yana tattare fuska dan wani irin yawu da yake taruwa a bakin sa dan shi yana da tsantsani sosai
 Daurewa Yagi yasake cewa "tom tunda bazakiyi magana ba ina fatan de ba kurma bace dan tambaya zanmiki
 Ahankali tsoron ya dan ragu   tunowa da tayi ana aikin titi a unguwan  turawa suna yawan wucewa ta dan matso tace mezaka tambaya?

 Yace "ina zaki? Ta  daga hijab dinta tayi ta nuna masa allon da yake rungume a kirjinta     tace "karatu

Yace "tom ya akayi kike yawo takalmi a tsinke?
Tace "bayan nafito ne ya tsinke.
Yace tom  "shi kuma hijab dinfa,?  tace" malam yace karna kara zuwa da wannan yayi datti.
'Azuciyan shi yace wannan dinfa
   Tom meyasa baki sa wani ba kallon sa tayi
"Tace banida wani
 
Yace "tom  ni idan kinaso zan temaka miki kisiya kinji  ko har da kayama kinga wannan duk yakode    kina Budurwan  idan kina wannan shigan waze soki   tace " ai damage bawanda ya taba cewa yana  sona  shima  shatiman  da baba yace yabashi ni ya karbane kawai dan dole  dan yafi kowa tsanata acikin almajiran baban   balle samarin anguwan mu ko kallo na basayi  mata sanne masuke cemin yanga acikin datti ko yanga acikin tsumma  yanzu haka da kawaye na muke  tafe suka wuce ni  wai  bana sauri ko menakewa yanga acikin sun har da yan gidan mu  ta kareshi maganan kamar zatashi kuka
Shiko zuba mata ido yayi yana  kallon ta kai daga karshe ma har wayan sa yaciro yana  mata video  zaikaiwa Hadim  dinsa tagani yasan  abin dariya baya mata kadan  dan yasan yana bata lbr zata ce ya mata bakin kici da bai dauko mata ba 
 Ya kawar da tunanin
Yace   zai soki kina wanka kina Gyaran jikinki kinji  ko amma ahaka ai ba zai soki ba   tace "tom ai ni mamarmu  makauniya ce bata aikin abinci sukuwa sauran matan kudin cefanen gidan suke dauka su sayawa yaransu kaya  muko sede mujira na babanmu sai sallah sallah yake mana  surutan ta  ya ishesa dan  haka yada katar da ita  m yace "tom  shikenan zan baki kudin da katina idan kudin yakare kimin mana zan sa akawo miki se kibawa mamankin tasiya miki duk abin d yan mata suke siya na gayu

Zaro ido tayi tace "kai maman ai fada Za tayi sai de na boye  nasiyi kayana da kaina  adena renamin   gabuwan har ta aiyana yanda idan tasamu sutuura zatayiwa yan gidan su,

Bandir din yan dubu dubu yadauko guda ukku yahada da katin sa yasa aleda yabata  takarba  tana godiya   sai a san nan ta kare masa kallo ta sake kallon sa  tace "ni kamar nasan ka  ina ganin fuska ka awani waje amma nakasa tunowa amma nake ga kamar a TV ne ko
dariya yayi cikin mamaki yanzu dama a Duniya akwai inda ba asan shiba  abin  mamaki ma akasansa akasan nashima acikin garinsu  amma wannan bakaraman  bakauyiya bace yana da tabbacin bayar gari bace kawai bayan gashinan yana zaune nan ma yana hango wani saurayi da riga me dake da photon sa ajikin sa yanzu wani ma yawuce da hulan me dauke da fuskan sa  murmushi yayi yace dan bani ledan nayi man tuwa  tana meka masa  ya bude yadauko  katin ya yaga wajen sunan shi ya bar wajen number kawai yameka mata  yace idan kina da matsalan kikira yaja glass yazuge ya tafi.
 Itakuma ko duba ledan bayayiba balle tasan meye aciki tafara sauri  dan tasan zata doku  awajen malam
Adai dai gate din kofar gidan yayar  ummin kuma uwar matar sa  yayi horn megadi ya bude masa  yana daga maga hannu dan yane  waye  yayi parking yafito  yana daga wa megadi hannu  kai tsaye  babba falon gidan yashiga  gaban sane ya fara faduwa idan kunnuwan wansa ba yaudaran sa sukayiba sautin kukan  matar sa abin kaunar  sa ya bashi,
ai dasauri yakara sa shiga  itama  tana hangoshi da gudu ta karasa jikinsa habibi yawwa  kazo kagaya musu wllh  ba kason kowa seni kaji abinda su  mama da ummi suke cewa kuwa  kafada musu wllh bamu sara rayuwarmu  akan zamu zauna da wata ba kace musu nima zan iya haihuwa kamar yanda likita yace  karsu mana haka kace musu bana son kishiya zaku rasani  wllh zan kashe kaina 
Shi abin ma dariya yabashi
 Dan bai fahimceta ba
Ahankali ummi ta taso takara sa gaban su  ta ja hannun su suka zauna tace  haba  Hadim dita  namiki bayani tunkafin yanzo naso ki fashinta ki nusu muyi shawara yanda zamu bullo wa al amarin  ni da uwarki ciki daya muka fito  yanda bazan so ace anyiwa jidda  da nabila da na haifa kishiya ba bazan so  amiki ba  se  dan dole  ki  daure ki fahimta kamar yanda mahaifiyar ki tafahimta 
Yayar mijin na bata son zaman lfy ita ta hada wannan abin tun farko bake taso  nabill ya aura ba  ZAINABU taso bashi acewarta mu shuwa muna mallake miji ni nagama da kanin ta dan ma bazan bar musu ba zan aura masa yar yar uwata mu mallake nabill din da shine karfin gidan  da ker alh yada ge akayi abin amma kinga wannan karon alhjn da muke samun  daurin gindinsa hardashi acikin bamu zabi  agabanki akayi komai
Sun bamu wata shida idan baki samu ciki ba ko  yayi aure ko yasakeki ko muga
hukuncin da zasu yanke  ni nasan dama suna cike dani hukuncin da zasu yanke bazai mana dadi ba gwara muyankewa  kanmu kafin  suyanke mana ki daure ya,ta kishiya bazata miki komai ba da gani har mahaifiyarki muna dasu me suka rage mana
Kan uba se yanzu  Nabill yagane me ake nufi  cak yameke yana  kada kai sam ummi wllh ba a haifi uwar matar da  zan yiwa matata kishiya ba  kai ko mutuwa ta yi  ina kishin yi bata kishiya  ummi kubar wannan mgn dan harkun sa na tsaneta tunkafin  ace na aurenta   dan duk matar da  za ta zo gidan mu a matsayan kishiya ga Hadim ummi abin tausayice  kuma ai.....
"Kai dakata inji ya fatime  uwar hadim din ta katsehi
                 *By*
          *Batul*
*Muje jezuwa*
DAnba da shawara ko ne man karin bayani 08062383027
[3/12, 8:47 AM] Hauwa: *DAMA TA*


                      *Na*

            *Batul Adam jattko*


2....


🌈KAINUWA WRITES ASSOCIATAN🤝

Kuma  sai  ta  kwan tar d  murya
  Nabil mu "cire son zuciya  mukawar' da zargin da dan gin mahaifinka" suke mana nace wa ganin yar" muce ah, gidan  shi yasa muka ki. Daukan mataki  aure shekara  shida ba haifuwa 
Yin auren me?  Zai rage, ku dashi  na gani dana haife ta ina tare da  kishiya haka uwar da ta haifeka kai tana tare da su  wata kila, ni ta gado dan se da nayi sheka ukku  a gidan nan ban samu  ciki ba se da"haka  kawo halima ta samu ciki ni ma Allah yaba ni   kuma muna zane lfy kai ma sheda ne  tuda ita kan  ta  Hadim  sunan  kishiya tace,

Wata kila rabon wata yana ga ba da"nata yaza muyi   kunu su kuyan kewa kan ku shawara ka fin lokacin da aka baku yacika   kuci gaba da addu a' mu ma zamu taya ku....
  Da kyar  suka shawo kansu  suka  hakura akan  za su nemi mafita ka fin lokacin yayi.

    Atare suka fita da, su ummi ummi ta shiga motan kamal  Hanif yaja na sa Hadim da Nabil suka shiga nasu..
 
Suna tafe ahanya
"Hadim tace yanzu my star da'gaske  auren zakayi.
'zuyowa yayi ya kalle ta bai ce komai ba ya zuya ya cigaba da tukin'sa
Cikin damuwa
 Bawanda yakara magana har suka ka raso gida 
Kai,yatsaye

Bedroom  suka wuccce shikam ma, wayoyin sa yazubar akan gado ya wuce bethroom ya sakarwa kansa ruwa  bai jima ba yafito  ya sameta  tana rike da waya tana kallon wani abu tana cin dariya
Matsowa yayi kusan da ita

"yace yade.
Me a ka, masa meka masa wayan tayi  shima dariyan yayi  ganin wannan yarinyar da, zun lokacin da take, ta zuba.

"tace wai ina kasa mota na tashi a lawan bor nefa nagan ta a hanya nayi nunanin matsohuwa ce ahe wai yan mata ce
"kasan meyabani dariya wai da tace  almajirin baban ta da za ahada su ma baya son'ta
"tom hauka, yake  mezai so anan kinga hakoran ta kuwa
 'hadim ajiyan zuciya tayi tameme ta  waze so ta da Nabil yafa da aranta  a ranta
 Anya wannan bawata    DAMAN Allah yajefo musu ba?  Ta ke tambayan kan ta
A fili kuma tace

"my star kasan  me na ai, yana.

"ah ah yace tare da meke'wa yayi ida'
Drssing mirror  yake tace   mezai ha na mucika wani burin mu akanta.
"yace kanwa

"tace wannan yarinyar mana wllh nayi wani nazari .
"bakiga na mata duk wani abunda zan mata ba har'fa  number dina nabata  idan kudin da na bata ya'k,are ta nemeni san sa hamza  yakai mata na tausaya mata.

"tace niba wannan tunanin nayi a kan taba. Ta sowa tayi taka raso inda yake ta lakuci man tana shafa masa.

"tace  mafitan da su mama suka ce musa mo ai inaga itace mafitan.

"yace kefa wani lokacin bakya, tunani a inda yadace ita kuma wannan meye ga minta da zancen da,zu.
Yatashi yabude wahdroof ya dauko jallabi yansa  yasa   ya tada sallah

Ba yada zatayi ita ma ta fada bathroom san da tafito yar ya idar ya haye gado  se da tayi sallah ta shafa mai  da duk abinda zatayi  tasa kayan bcc ta ta yaye bargon tayi

"tace katashi muyi maganan my star  kasan  bamuda i she'shen lokaci  gashi nanda sati samu bar, kasan nan  ga, kuma  DAMA tasamu  wannan yarinyar  itace  kadai 
DAMAR Mu.

"wai me'kikeson cewane ni fa kin,san idan ba fa,i yace zance kikayi ba,na ganewa

 "tace yawwa yan zu zaka, gane idan kabani hankalinka
 Kasan nayi 2  mu'bi daya da gacikin  shawarin doctor  muktar kaki...
"yace amma ina ce kafin yamani shawaran se da yaga yamana illolin yin hakan  tunda ance  ba haihuwa ne bazakiyi ba za ki haihu ma'haifan ki ne anesa muzubawa  sarautan  Allah idon mana har se mun dauki wani abinmu  mukai wa doctor yan hada sun bamu da' bayan sun tabbarar mana da balalene asamu halitta mekyu, ba.
Ba tun asan nan muka rufe maganan doctor na  mu dauki mani na da naki mukai ba.
Afusa ce ta fara  maganan dan tasan idan tayi san ya ba zai karbi uzurin ta ba.
 "itama afussa, ce tace  "yakake  son muyi ne nabil  tun nuni naba da shawaran muje gidan marayu mudauko  kace  baha ka'ba..

"yace nifa bawani gidan marayun da dan je dauko dan kowane shege  yazo yafi karfina ya,ran yanzun wanda aka haifa ma, yasu ka kare da'iyayen su balle mu dauko  wan da mamu san asalin saba 

 "tace ai shiyasa na ce maka gawata
DAMAN Allah yakawo  wllh idan baka, yarda ba se de ayita ta kare dan na, gaji nace wannan kace  ba hakaba....

"ooo my sweet kifadi  DAMAR muji. 
"tace ka'auri wannan yarinyar  me allo.
"wattt...
Yace yana durowa akan, gadon
Dariya hadim tayi dan tasan dole za ta fuskan, ci wannan kalubalin awajen nabil       hannun sa ta'kamo ta'zaunar dashi akan gadon

"tace please  shiyasa nace kanusu

Bawai aure nake son, kayi ta ita kamar kowa ba
Assalima za kayi auren ne batare da sanin kowa adan ginmu ko na baban ka ba  dan za, ka aure tane dan ta haifa mana yaro ka, sake ta batare da,  sanin kowa ba....
Katse ta, yayi da cewa "ta haihu dawa?
Dariya tayi tace  "damu mana  "yace ta ya zata samu cikin ko
"kezaki mata cikin kenan ko....

.dariya tayi
"tace kai zakayi 

"yace baki ji dai dai ba
"tace mucire maganan wasa fa, dan naga wasa ka dauki abin..
"to'ai wasa kike shiyasa.
Kuka'ta fashe masa dashi.
 Ya dago ta
"yace meye haka hadim
"tace wllh idan baka yarda da  wannan shawaran ba na,san ba nida kowane ma sayi awajenka  kanuna  min iyaka ta
Kuma daga wannan ni   da'kai kowa yaji  da kansa   dan wllh bazan zauna a namin gorin haifuwa ba  kuba bazan yarda   kamin kishiya ba....

"yace ba,yan  zu da bakin ki cike iran na miki kishiya ba  ni ina fada baki da kun,fa agaban su ummi aganki. Ashe ba, kya kishina
 ashe son naki abakine

Wllh duk tausayin da nake yiwa yarinyar da kika hada, ta dake kin ga harna fara tsanan ta   sabo bazan iya yi miki kishiya ba   ko ta mutanen kir,ki ce balle wannan..  Birki ceciyar...

"tom shikena zan samowa kai na, mafita hai ma' kasamo naka ciki harda shirin rabuwa dani  muddin ba zakabi wan nan DAMAN ta karshe ba'.....
-ta'meke zata fice yarukota ganin bai taba ganin irin wannan  bacin ran atare da, ita ba

" yace  tom  gayanin yan da abin zai kasance.
Murmushi tayi.
"tace  abin zai zo da  sauki dan  naga yarinyar ta na, da kwadayi  zakaje mata da suffan yau dara  kaci kana son ta amma a, gaggau ce kake son daura auren  se kace ciki sati  kai ba ba zauni bane tunda talakawa ne iyayen ka, ga bawani bin ciken da zasuyi  dan zaka tura kudi ba na wasa ba    idan suka amin ci se ka tura hamza ya yi maka hayan iyaye  kar ka bari su iyayin su kan ga ido da ido dan, nasan baza su ka, sa  gane kaba 
  Katura hamza a shine mijin  a yi auren ba wanda yasani mu tafi da ita   ta haifa mana yaro   idan burin mu yacika mu tarkato ta  kaga basu da  ikon jadamu ina ma zasu gan mu

Murmushi yayi
 "yace  Gaskiya nayar da da, akecewa kanlalin mcce baya gamuwa, har tagaba yayuwan ta
Iyayen nata wane irin iyayene za su yarda dani ciki sati  me ki ke nufi da ta haifa ta bamu
Kina gani duk daren dade, wa Gaskiya bazai yi halin  saba......

Ummmm ko  nabil ze yar,da, da aure yarinyar
Wacece yarinyar da nabil yakira me allo 
     *By*
*Batul Adam jattko    ✍🏼*
*08062383027*
[3/12, 8:48 AM] Hauwa: *DAMA  TA*


             *NA*
      *BATUL Adam jattko*

🌈KUINUWA WRITES ASSOCIATAN🤝

Cikin konciyan hankali take takun ta har ta iso makarantan allon na su ledan hannun ta ta  boye cikin shijab  din,ta  ta fito da daya hannun ta me kawa  malamin  malam tashir ya yamussa fuska yayi alamun baya so ganin ta
    Bulala 2 ka wai  yamata
Dan bayason ga ninta a gaban sa      memakon 5  dayake yiwa kowace maka, yarriya idan ta makara

*kusa da kawar ta ummahani  taje ta zauna ka mar yanda suka saba

..kowa karatun sa yakama dan  mlm akwai gyara ba yason  jin ko, mai se krt

A na tashi yan gidan su sukayi gaba dan  baza su iya da tafiyan taba

 hatta  kawar ta
 ummahani ba ko yau she tafiyan sun
Yake zama daya ba
Daf daza a kira magaruba ta shigo gidan ba tare da  sallama ba kamar yan da tasa ba

Gidan su babban gidane da  babu irin ta akaf anguwan   bawai kyau ba girma  ban garen baban su za ka fara cin garo dashi idan kashiga gidan  nashi ban garen kan  yahadu  iya haduwa 
Se ka, bi tawa ta, kofa ze sada ka da bangaren matan gidan wanda yake  ajere ka mar islamiya  babban  baran' dane  da kuna fudu ajere  kowane  daki falo ne da ciki    kai saye dakin su ta wuce ba ta yiwa ko  mamar ta da take ko fa magana ba duk da bagani take ba  bako bai a, falon nasu ko  tabur man kir ki babu   kicibis sukayi da  kanwata  bagana  wan da dama su 2 ne agun   uwar su.....

  "tace kai  ya fandau  yau kam ba  tafiyan yangan ba rarrafe kikayi ko..

_da harara tabita  ta wuce ta, 
Da, kin ciki tawuce da zauna abakin  gadon ta me runfa  ta bude ledan  ido ta zaru tare da sa, hannu ta rufe bakin ta,  dayake shirin fasa ihu yatona ma ta asiri  gani duk wannan nauyin da take ji a, ledan  ashe bakomai bane illah  ma kudan kudine    bata taba ganin kudi haka ba ya zatayi da wannan  kudin bata isa ta tunkari  maman ta da,  shi ba, to tashi tayi taboye acikin bakkon kayan ta  jikinta se rawa, yake   magaru ban ma ka sa fitowa tayi tayishi  se kusan ish'sha   tafito tayi alwalah  tana idar magaru ba aka kira ish'sha ta, ji anata  karatun dare  dayake   ana karatun dade  a gidan  su duk yaran anguwa haka za su cika, filin gidan da yake waje aka ware  a ha katangi  manyan almajirin ne suke koyarwa dasu.

 *WACCE  FANDAU*

 - ya' ce ga  zanna  moodu  babban malamine  me fada aji agarin  meduguri        yana da Gaskiya sosai  da amana  yana da  girma a idon mutanen gari  sosai   ba yadaga cikin malamai  masu subbace subbace duk da malamin  tsoro ne haka yana ka ramasa girma  amma ba shida ko mai talakane sai ilimin  da barin jini ganin,
 haka shehun barno ya bashi  muka min   *zanna* wato *hakimin* anguwan  da suke  yana  da, mata 4 da, yara  da, dama dan yayi aure aure da dama wasu sun fita wasu  sun rasu
 Matar sa ta tsakiya wato aisa   yaran ta 2 mata wato  fandau  da kuma     bagana    tanada  ra ruran idon dan bata gani  hakan  yasa kishiyoyin ta suka rena ta  dakuma  hade mata baki 
Dan ko awajen mijin bata da baki  dan cewa su ka'yi   tana zaune ba zasu dafa  su bata ta  je ta, kwan da miji ba to aikin gidan  ga me  ido ma yaya, 
Balle  makahuwa    duk da da baha take ba da ga  baya  tagamu da shi

 * fandau yarinya ce  me  jida kai duk da, bawani kyau ne da ita ba ga shegen kazan ta duk hakan yana da nasaba,  da, yan da yanayin gidan su yake  dan gidan zanna  matan sa ba abinda suke samu  balle      ita da uwar ta take makahuwa
Zanna moodu ya daukawa kansa nauyi da, yawa  dan albashin da ake bawa hakkimai  dashi ya dogara  yara da surukan san  na yaran sa maza  shine yake ciyar dasu  ga almajiran  sa ba sa bara yana siyan  kowai ya ajiye  baya bawa  macce  kudi shide idan  kana da   damuwa idan kagaya masa yagah   
Ya da ce  to yana ba yarwa  suma sauran matan   dan cuwa cuwan gida dashi suke fanta mawa.

*wannan yana bawa fandau takaici tunda  mamr su makahuwa ce ana kawo ko mai agaban idon su za a raba  sabulon wanka dana wanki da sauran  abubuwan  amfani  amma  baza a  basu ba shikuma  zanna moodu  ba me kula bane  ita kuma  mama wato  aisa abin duniya bai da meta ba se tayi  wata bata rike  ko biyar na kanta ba  se  idan  wasu daga  cikin  almajiran  gidan da suka manyan ta idan suka  kawo ziyara  su ma basu ahan ma ba kullum  ake bawa  Aisa  ba  wanda suka san yanayin gidan  ne ma suke bata nata  a hannun ta..

       tana kwance   tana  tunanin  yanda   zata   fara  sarrafa wannan kudin  dan ta sani ba  me tsareta  ina tasa mu da tambayan  tunda ba me bata lokacen da batada shi
Kuma ba matan gidan kan su suna shayin ta balle yaran su maman ta ce kawai ita ko ba gani take ba za ta gobi  bagana tace kar ta ga ya mata ta sinci kudi za ta siya musu kaya
 haka, ta kusan kwana  tayi  tana  juyi...
Har gari yawaye da yamma l
 _ lokacin  zuwa bakaranta yau balefi   tayi wanka  dan tazare  dubu a cikin kudin ta tsayo sabulu tayi wanki  ta siyi takalmin    fes  take  tana  takunta kamar yan da, ta, saba  allon ta cikin shijab 
 Ita daya kamar kullum

Jitayi  gaban ta  yafada dam  san da ta hango motan  jiya ta tabbatar shine dan  ita bata ta,ba ganin   irin saba       zubawa  motan  ido  tayi  karfa  ya,ce  zai karbi  kudin  sa  dan yayi  yawa ko de a rashin sani  yabata   wayyo ni Fandau yazan yi idan yace zai kwace
Har takaraso tana wannan tunanin  yita yi ka, mar zata. Zuce
Taji yace

" me allo ba gaisuwa 

Yau ma kamar jiya dan  fito da kan sa  yayi 
Juyowa  tayi
"tace......

                 *By*
      *Batul Adam* *jattko*
*08062383027*
[3/12, 8:48 AM] Hauwa: *DAMA TA*
       
                *NA*
     
          *Batul Adam jattko*

     *4*

 🌈 KAINUWA WRITES ASSOCIATION🤝

 "banza  takai  bane tadan ra,ge tsowon  ta, tace  ina  wuni..
            "yace lfy
shiru tayi   shima  haka   ita kam  jira take taji  yace ina kudin..
  Shima haka bai san ta ina zai fara ba  yadaure
"yace  se kika ganni yau mako
  "tace eh ai dama kudin da, ka, bani nasan  baka,  san  Yayi yawa hakaba  amma ban zata zan gan ka  ba ban fito  maka dashi..
"yace a a ba wannan  bane yakawo ni  a, kwai maganan  da na zo 
Miki dashi ne..
"tace ni
"yace eh
Amma  kaganan Gaskiya bata'nan   bane.
Dan  ni agarin nan ba kara  min mutum  bane  bazai yuwu  na tsaya da  macce  a cikin gari  ba
Idan bazaki damu ba ina neman wata alfarma  awajen ki..

 "tace ni kake ne man alfarma  awaje  na, bani da wata aba da  zaka nema  awajena 

Inma akwai zanyi ko menene..

 "yace na gode
Inason  nayi magana  dake  gobe  amma  ba anan ba da, fatan zaki min Wannan  alfarman?
"cikin tsoro tace  aina, zamuyi?

"yace a inda ba idon jama'a..

"tace inane?
Yadan  yi shiru  can

"yace kin, san  (nabil shid international  hotel  ).

"Cikin tsoro tace a a   
"to a nan zamuyi magana  saboda  mushin man cin sa kin san nace 
Inason na te maka miki..

"tace eh amma ai kudin da kabani  sun isa har sunyi  yawa ma nara sa yazan yi da su.....

Cikin kosawa da maganan da ita
 "yace  kinga ke ma karatu zakije  ni ma inada, abin yi  gawannam  kibawa  dan napep  din  da zai kai ki nasan  zai kai ki har wajen

Wannan kuma kibawa wayan da suke get din     ina son 10 na safe  yamiki  acan..

Gabuwan se kawai tasa hannu takar ba   shiko yaja glass  yazuge   yayi  gaba abinsa  yana takai cin wannan  wahalan.  Da,  Hadim  ta zanyo musu

*

Itama haka taja, kafa tayi  ga ba
da daddare bayan antashi akaratu suna, zaune su ukku     
Ada kin su Fandau..
"tace mama gobe inason zuwa gidan Zahra  da safe..

Mama tayi shuru yau kuma Fandau  da kanta, take cewa zata gidan kawa
  Itada  ko gida jen yan uwan ta, wanda suke  uba  daya  bata zuwa gida jen su  duk da da wanda suke, auren masu kudi  sauran yan mata gidan suyi ta zuwa suna samun alsheri  amma  ita ko  sun zo gidan se taga dama take musu  magana  shiya sa suke ce mata me girman kai  ka zama   me bakin  hali..

"mama ta nisa  tace mezaki jeyi.

       "Fandau  tace tun bikin ta banje  ba  kuma  ranan da  tazo  tace idan banje  ba ko tazo anguwan baza ta, zo gidan nan ba..

Zahra kawar Fandau ce duk kawayen su ba meyi da ita kamar  Zahra  da ummahani..
Mama tace  "tom se kuje  ke  da yar' uwar ki.
                Ta juya tayiwa  bagana  wani  irin kallo na baza ki bini ba

"bagana  tace mama inada  hadda'           gobe bazan iya fita ba

"mama tace  shikenan  taje ita daya, tunda  a gidan  ba  kula mutane  ta ke ba balle  ta samu  me rakata.
Fandau addua ta ga   Allah  yashiya ki  kiza ma mai daukan duniya saukake  inji mamn..
Fandau  batayi magana ba ta haye gadon ta ta juya baya  tayi  kwanciyar ta

Da safe balefi  tayi wanka  ta bude bakon ta, taciro dubu 2 Allah sarki  agaban mama tunda  bagani  take ba ta mata  sallama..
"mama tace  gashi bani da kudi da zan baki ki hau mota..

"tace bakomai mama  zan taka da kafana..
             " Mama tace
London ciki fa akwai nisa..
"mama se nazo kawai
"tom kigai sheta.
"zata ji
Tace
Tafice  ko kallon mutane  gidan batayi ba tafice
Ta taka har junction din lawan bor ta seda dan napep  tame ka'masa  takar dan da  yace ta bashi  yakar ba ya karanta  yace kai shid hotel   
"tace eh
"yace zaki bada  dari biyar
Shiga tayi "tace muje
            Tafiya sukayi menisa  har a wa guda har suka wuce ngmari airport 
"cikin tsoro tace aina  zaka kai ni  ne haryanzu  bamu zo, ba..

"juyowa yayi kalleta   yace" kin dauka tafiyan kadan ne  tuna nina mazan samu fasunja  ahanya nace  dari biyar  din kahi ban dau kowa ba Gaskiya dubu zaki bada..
 "tom tace  parking yayi dai dai  wani  mayen beni  wajen haduwan sa ba a magana  .

Yace "tom muzo ta cire  dubun  ta bashi
Tafito  Gaskiya  anya za ta iya shiga wannan waje  tun da take ko a film bata ta,ba ganin haduwan  wajen  haka ba  Sojoji dasuke gadin get  din suka zuba mata ido alamun  rashin  yarda  dan  batayi kama da wan da ta isa tazo wajen ba tsawa suka mata  tare  dacewa  ke me kike anan  dan atunanin su yar'aken muta nen  sune wato boko haram.
 itako cikin tsoro
Ta tattare zani zata gudu  aiko sukayi kan ta gaba daya   tafko ta sukayi  ai bata san san da ta saki  fisari  ba  na uran, su suka sa suka cajeta bako mai jikin ta
Tan bayan ta sukayi  me tazo  yi..
"cikin in ina tace wani ne yabani wannan yace nazo nan  ta meka mu su
Takardan  hannun ta na izini shi gane da ga oga    suna karan tawa sukace tabbas tubutun  oga ne  amma   duk da haka basu gaskan ta ba suka ce bari   a kira shi
Salees  kira shi  salees  yaciro  waya
Ya kira ya masa  bayani  yakashe  wayan  yanacewa  yace ashigar  da kita  itako

Ta kasa komai  dan  ita da zasu bar ta gida zata koma in ko tashi ga nan to  ta seda kanta da kata  dan ginin wajen a mar ba a meduduri  ba
Wani ne yawu ce gaba yace  muje ko
Ba  yan da zatayi  cikin fidda rai  ga  rayuwa  tabi bayan sa dan baza ta iya musu musu ba

     *by*
   *Batul Adam jattko*
*08062383027*
[3/12, 8:48 AM] Hauwa: *DAMA TA*
   
             *NA*


      *Batul Adam jattko*

   *5*
🌈Kainuwa writers
Association🤝
  Haka tabi bayan sa
Suka shiga wai ai waje bakomai ba'ne kallon naciki duk da,  tana cikin tsoro seda, ta dinga ware  ido tana bin  wannan  katon gida da kallo  wanda,  baza tace ga iyakan hawan ba  mutane suna shige tafice  duk yan'gayu   su ba babban  ginin suka dosa ba wani waje daga'bayan  sukayi  wannan  ginin sa kamar gida ne haka  madai dai ci   get din taga ya ja

Suka shiga shima wajene  na musam man  ya hadu  da gani wajene  na,shakatawa  bako,wa wajen  kusada swimming fool ya'ja mata  kujera  a cikin wani da, bukka
"yace kizauna nan  bawan da yake shiga  se ban yan bak'in oga ko shi  kansa.

Itade batayi magana ba,   dan tana, cikin tsoro 
 "yace me za a,  kawo miki na ci Ko sha.
Bata,  kalle shiba

"tace komai ma
Salees yaju ya, yana mamaki me ya hada  oga da wannan  kuma duk  da an, san  temako' halin sane  amma  mey zai wani ce akawota  wajen sana musam man  haka.
Bata taba komai  ba a, abubuwan  da aka'kawo mata.
  Bude get din akayi  motan yashigo
 Kusa da  inta take yayi parking  motan tabi, da kallo dan ba ta ta ba ganin irin taba bay fito ba yadan Zuje glass din
"yace rufe  bakin ko
Se a,san nan ta,gane shine.
Ka'fan sa yafara sauke' wa,  kafin yafito gaba daya
 * gabanta taji yaba, da, rasss ganin ahe mai  temako yawuce yanda ta,ke sammani duk ahe  kallon tsoro  take masa  kuma  azaune.a mota take kallon sa
Dogone irin zan, bat dinna  sayeyye,  baka k'en kot ne ajikina sa bakin glass din sa ya dace da mekekken  hancin sa, bari ko ba a, magana ahaka yadi, ga taku da takalmin minsa sawon ciki shima ba,kin
Itade zata iya rantsuwan  ba ta, tabaganin  ganin namiji  d yagaji d kyu haka  ba ahe da mada irin su a agarin nan itade  ayau  se  taji wanene
Ko shuwan  ne  amma  ai a, anguwan su ma, akwai shuwa

Ba irin suba, ne  kanshin turaren nan nasa tun ane sa yake bugan ta  har yaja kujera ya zauna  bata dena nbin sa da kallo ba
'Azuciyan sa yace  kode mayya ce ne irin wannan kallo
Amma  afili

"yace  baki hanci goshi duk nisu ke kallo  na idon ma bai isa ba yakare  maganan  cikin murmushi.
Ita ko kunyan kama tada yayi dumu dumu tana kallon sa taji ta sun kuyar d kan ta
Dan za muwa tayi tace
            "ina kwana
"yace kina lfy
"tace kalau
"tom alhamdulilah
Shiru yayi dan baisan ta inda zai soma ba,
Wayan sa yacire  kawai yaturawa Hadim  sako cewa  ta ina zai  fara
 Daga ban garen Hadim  dadin ta ji  ta yar da da mijin ta  ita ce ka dai a ransa
Nan da danan ta turo masa  yanda  zaiyi
"Gya,ran mur,ya  yayi  yace yawwa  dalilin  gai yato ki nan
Shine  ko kin san tun farkon gani na dake  shikaran jiya  na kasa sukuni 
  Ganin bazan iya jure waba yasa  na yanke shawaran ne man temakon ki  idan zan samu.
"cike da ladabi tace

"ai, nace kane mi kowane irin temako zan maka tun ajiya  kuma  zuwa na nan zai tabba tar maka da hakan..
"a hankali yafur'ta zaki  aureni.

Cak tameke  ta na zaro, idanu  ta na nunashi ahannu  tana, girgiza kai
Ta kasa magana
Jita yi harshen ta ya, mata nauyi
Da kyar ta lalumo wasu  kalmomi  ta,hada, tana, nunashi

"kai waye
Mekazo nema wajena
Kagayamin
Nufin ka, akai na
Dan nasan tabbas
Da wata manu fa  amma
Kabar ba ta bakin ka wajen cewa  kazo ne man aure na  ni wacece da  mutum kamar kai zai ce yana so
Ko,kasan dalilin zuwana nan ma ganin baza ka cutar
Da, ni bane fa idan kamin za kaci amanan yar dan da na maka ka gaya min me nufin ka akai na kai waye kai  dan mafiya ne dan idan bawan nan ba  ba abin da za kayi dani  kadu be ni ka dubi kan ka kace kana sona
Nabin 'azuciyar sa yace kin ji na furta ina son ki ne
Afili kuma yace "ke ma mutum bace se de idan zaki ce ba kyason aure na almajirin baban ki kike so.
Tace "wane ni inde har kai kanu na kana sona ni ban isa in ce bana son ka ba se dena san ma basa mun ka zan yiba baba na baya mgn ya canza ya riga yabawa Shatima  ni  ahan kali Nabil yafurta zai canza naki hadin kan kawai nake ne ma
Tace "bazai canza baka san baban muba  jin sa kawai  ko
Yace ina zan jishi  nida ban san shiba.
Tace "kai baka san babana ba amma kai bako ne ko
Yace "waye shi
Tace "zannah modu ai kowa yasan shi
Nabil cikin zare ido Nabil yace ki na nufin lawan din gar gar  Zanna Modu me wa'azin nan agidan Tv da redio
Tace "eh
Murmushi yayi dan yasan dole yan zu Hadim zata hakura ta canja  wata shawaran amma dan ya kara gaskan tawa yace "ke yarshi ce ta cikin sa shiya haife ki?
Tace *eh babana ne
Yace "agidan sa kike yanzu?
Tace "eh
'yace ba me kanin ki yace ke yar wani ne agarin nan inde zannan da na sani na gargar ne hakimi
Ne kuma babban malamine yanzu kina yar zan na kike ahaka?
Tace "ai baban mu ba ya damuwa da wani harkar  gida yaran sa manya su suke tafiyar  da komai na gidan niko mama ta bata gani ma.
Yace "aishike nan tunda bazai can za ba da ma tema kekkeni yace  yame ke tana ganin sa ya ja mota da gudu ya fice sai a san nan kuka yazo mata da kuma Babban a saran da ta yi na ga koshi ga rashi
Shiko tukin sa yake ankali kwace  cikin rashin da muwa har ya kara sa gida dan aganin sa ya rabu da kah ra tunda  dama ba iya rayuwan aure zai yi da ita ba yana horn megadi fakin bai yi ba Hadim ta fito da gudu ta bude masa tace "yade mai star anyi nasara ko?
Yace "ba nasa ra kinsan yar gidan waye kuwa tace "au har kasa mu iyayen ta kenan kunyi maganan ko yawwa  ita yar gidan wacece  yace bazai yuwuba yar gidan lawan Zannah Modu ce babban malamin nan  na gar gar  zaro ido hadin ta yi tace wllh karya take ita ta isa ma
[3/12, 8:48 AM] Hauwa: *DAMA TA*

            *NA*

       *Batul Adam jattko*



   *gdy ga, dukkan masoyan* *DAMA TA* *da kuma bada, hakuri yanda page 1 yazo error* *tun asannan anmin gyara kuma na fara kaman tawa  dai dai se Allah  Allah ya gyara mana kura kuren mu*

        *6*
🌈Kainuwa writers

   "yazaki ce karya ne ta tabbatar min da haka se de kawai kisamo wani  mafitan
"kama hannu sa tayi mushiga kamin bayani yanda kukayi da ita  suna shiga
Yaga yamata yanda sukayi  shiru tayi
"can ta murmusa tace my sweet baka saya kaji ra ayinta bane  gashi kanuna rashin damuwa agare ta kai da nace ka daure kanuna kulawan ka  gareta  kafin musa mu  tazo hannu

Yanzu ina wayan da naba'ka kaba ta,.
"yace na bata
"tace aikuma akashe yake balle mune meta  amma yan zu kira salees ko ma, bata tafi ba tunda kabar ta tana kuka ki,la tana wajen

"yace mezan ce  ma ta kuma.
"kai,de kirashi  yaciro wayan sa yaki, ra salees
yace kana jina salees "yace yes sir
"wanan yarinyar tana nan ko tafita.
"salees yace ah dama ba, tare kuka fita ba ai nadauka tare kuka fita ka, na fita na kulle get
"yace tare mukazo d zamu fita tare ko kaga, tayi kama da wanda zan dauka a, mota.

Salees yace "sorry sir  bari inbude ta,.
"Nabil yace a, a, ina zuwa.
Yakashe wayan  yana kallo Hadim
"yace kinji wai  shi bai ma zaci tana ciki ba,yarufe.
 "tace yayi  Daurewa  zakayi ka, koma. Anan ta, tagaya masa yanda zaiyi ya ja, ra ahinta.

"to yace yameke
Dan Nabil sam baya iyayiwa Hadim musu ko meyasa?
 Haka ta rakoshi har wajen mota  yashiga yana korafin.
"Gaskiya yanzu inaga son, da, yarufe miki ido baki damu da,  damuwa ta,ba my one."tace  shine kwan ciyar  hankalin mu' kadauren ta shafa kan'sa tare da rufe basa kofan motan

Yaja yafice.
 *
Tunda yabar waje  ko, mutsi takasayi kuman ba ga, gara'
Ta yayi  wai ita fandau da, aka' bawa shatima yana,  mata,  kallon  wulakan' ne Allah yabawa  miji  na,
K'e ce raini
Amma nayi wasa da 
*dama ta* waiyo  Muhammad  ina zan gan ka wallh ka, zona amince  aure ka, ko,ba sani baba ko zan kai ka,ransa kotu  kazo bazan bari  ka kuff cemin ba
       Baganan.    Sa,   ne yake mata  yawo cikin' kunnen
 _shi dama duk san da yazowa mutum yayi amfani dashi_
_idan kika, yarda kika, aure almajiran da ba,so, ki yake ba duk abin da_  _yafaru dake kiyi kuka da kanki_
Afirgice ta tashi ina zan ganka ne
  *dama ta dama ta*
   Da, bar ta,zube aka'sa tana cigaba da, kukan ta.

Ko, bude get da shigowa da mota bata jiba  balle  takun sa,
"kingan ni ko nasake zuwa  wllh naka' kasa hakura zuciyata ta kasa  yadda,  nabarwa  wan, nan almajirin  ke'
Shine na, dawo, gani
 Gareki ki yan kemin kowane irin hukunci  ban da, ra'buwa dake,
Arazane tame ke "tana cewa  daga'ke kaine  kadawo 
Wlh basan yazan yiba ni ma bazan iya ra'buwa dakai ba
Ban isa intun kari baban mu da zancen kaba
Wllh inason ka kai ma, kasone balle ne.....
"tom dakata  yanzu yaza, ayi
"tace Muhammad wlh ban sani ba ni yarinya ce  kai zaka samu ma,na mafita.

"wani irin murmushi yayi na yakusa cika burin Hadim  dinsa
Yace  idan da,  za ki  amin ce kinga ni ma, ba dan garin nan bane ni iyaye suna     neger  abin da, yakawo ni nan shine nayi dugun  auren wata yarinyar  da,  iyayena suke son subani  amma  ni kuma ba,naso, ta  dan bata da tarbiya  ganin ki da hankali da kama lah kuma  yanda kike yarinyan nansan ko' kema zaki bude ido  da ra, ayina  balle yaran mu
*
Da, zai yarda munda,  ce da juna yanda, kema  iyayen ki baza su yarda ba haka ni ma, nawa
Kawai muyi auren mu aboye idan  Allah  ya azur'ta mu  da haihuwa  muzo kusu da, abin da muka haifa  zasu  hakura musamman  ba  baban ki d, yake      "
"Tom yanzu bazan   fuskan matsala  awajen iyayen naka ba.
"yace baza ki fuskan ta ba dan ni  dama ba mazaune gida  bane  aiki na yana sudan  kuma can zamu
Ahaka, de yayi yaudaran ta,  abin ka,  da yarinta  ta, hau daram

 *
"Yanzu kinsan yanda yanayin auren zaika' san,ce?
Girgiza masa kai tayi 
"yace dawuri nake son ayi dan ajibi zan ko ma, sudan
Idan kin yarda  se ki bine za a daura mana aure akano  se muwuce ko?
"tom amma  fa ina tausayawa  mama ta makahuwa ce  kuma mu biyu  gare ta idan na mata,  haka anya  nama ta adalce
"
"yace Allah  sarki maman mu ashe  bata gani  karki damu  ki bamu shekara  ko baki  haihu ba,  zamu dawo  zan fita  da mama waje  a, duba idon zata  samu lfy   insha Allah.

"tace amma jibi baiyi kusa ba?

"yace bai yiba
"tace tom  yazan yi nafito.
 "cikin ko, sawa da maganan  yace  yanzu  ya akayi kika fito. Akwai  waya  acikin wannan  ledan  za'mukara sa sauran magana  a, waya.

"ido ta zaro tace  waya ai ni ban iya amfani dashi ba,
 Azuciyan sa yace
_nide bazan iya zuwa kusa dake yanda dan tsaya koya miki ba_
Afile "yace kisamu  wan dan zai koya miki ni  ina dawani  uzuri  ne. Zan  tafi  ya meke,  akan cuku cukun tafiyan mu  ya mey ke yafara tafiya
" tace ban san wan da daza koyamin ba?
"ada, kile ya bata amsa ki,zauna  anan zan turo akoya miki  ya shiga yaja

Kai badan yarin ta, ba da ta, gane
[3/12, 8:48 AM] Hauwa: *DAMA TA*


            *NA*


      *Batul Adam jattko*

*7*
🌈kainuwa wrirters
Association🤝

"tana kallon motan yafice ta sauke  ajiyan zuciya  tana hamdala, yanzu wannan shine mijina  duk dangin mu ba wacce tayi na saran aure irina
Tom su yafati masu ce'min mummuna
Suzo suga mijina
Bari muje muyi shekara dayan mu dawo
Duk se nanu na ban san suba uwata da yar, uwata kawai  nasani  ya, kaimin mama  abude  mata idon  ita ma, tayi rayuwa kamar kowa
Tana, cikin wannan  tunanin Sojan da'zu yakara so inda take
Mekewa tayi  cak ta,  zata zaice  ta tashi tafita   se taji yace
"zauna mana oga yace akaya miki waya?
Tace alle wayan ma soja ne ze koyamin
Umm zan sha gata
yasake cewa "ina wayan?
"tace bangani ba ko shine a  wancan ledan?
"tsaki yayi  yace tom kidubo
Azuciyan sa ko cewa yake oga  agarin wannan temakon nasa yariki to wannan komeye  abin se an koya mata waya wannan ba, kauyiyar  idan temakon ta, zaiyi  ya, bata mana abin da zai bata  harse  ankoya mata,
 Itako  bude ledan tayi  kudi tagani  wanda yafi nawan can karon amma ba ta, tsorata  ba,
  Wannan karan
Wayan ta dauko yar' karama ce  Nokia me tocila
Taciro ta, meka masa,  tace gashi
"yakarbi wayan  ya kunan  yace kin ga idan ankira ki nan zaki danna idan kuma kece kike son, kira gayan da  zakiyi   tanuna tasani  dan akwai  wata  makociyar su da take zuwa gidan ta tana bata wayan ta tayi ta danne-
 danne.
"yace yawwa tom aikin iya ma yame ka'mata  ita kuma ta meke ta dauki wayan tayi anyan fita.
Da tafito  se da tayi tafiya medan da ma nukun  ta samu  napep tace yakai  ta London ciki  gidan Zahra  tun kafin ta sauka a napep  taga gidan arufe, da' kwado  tace wa me napep
"kaga gidan arufe  jirani  nashi ga makotan ta, na tambaya  idan ba,ta nan mujuya ko

"yace wai nawa zaki'ba ni ne?
"tace konawa ne ni zan baka,
Tafita tashiga mako tan suka gaisa da matar "tace makociyar ki Zahra fa "matar  tace wai ta tafi duba  sirikin ta  bashi  lfy  "Yayya  tace idan tazo ace fandau  ce daga anguwan su.
"matar tace Ayyya anesa kike,  ai irin wannan zuwan yanzu ande da se kunyi waya ai  kishiga ki sha ruwa ki huta
"tace bakomai  na gode  idan tazo agaishe ta
"matar tace tom
Ta fice'bata  so ba taso, tayiwa kawan ta ta kallo  yaushe gamo.
Awalwalan ta ta shigo gidan  yau  fandau  harda sallama  da mamaki  mutane gidan suka amsa dan ba tafiye sallama almajirai ne suke ta layin karban abin ci  ba Fanta da Bagaji sune suke rabon  ta  raba gife tawuce
Atsakar gida ta tadda maman ta tana ta lalumen han yan banda ki  da sandan ta  da sauri ta kara sa inda take ta ka ma sandan ta kaita  tana  tsaye akan ta tagama suka fito ta kaita inda dake alwalan  dan azahar tayi  ta ita kuma ta shige daki  ta boye ledan cikin jakan ta ta fito da wayan shima tabo ye cikin rigan ta  tashi alwalan  tayi  sallah  tafita shara dan yau
*sharan tane  har ta fara shara taji  wannan  wayan yana k'ara Allah  ya temake ta bawan da yaji yayi saurin fita a gidan.

-hadim xaune kusa da mijin  ta sani ne a kujera da yake fuskan tan nasu 
Nabil  yayi gyaran murya
"sani  kasan dalilin  da yasa na kira ka
"sani yace a a yallabai
"na kira kane  acikin duk kan mutanen da  na ke tare dasu  nafi yar da da'amanan ka  bugu da kari baka da  yawan magana  baka shiga abin da ba ruwan ka  dan haka  nake' son saka cikin wani  sirrina  dan nasan kai  amincicce nane.
"sani yace haka ne yallabai  duk yanda kake son kasan cewa dani za ka sameni  fiye da yan da kak'e so
Babu ne kawai baka min  ba
"Nabil  yace tom masha Allah
Inason kamin alkawari  idan nayi sirri da kai  duk rinsi ba za kagayawa kowa ba  ba na fatan kowa yasani   da gani sai  kai sai mata ta.
"sani yace yallabai  na dauka wllh idan kayi sirri dani ko  wuka aka  daura min bazan bude wannan  sirrin ba.
"Nabil yace  sani  aure nake sonyi  na sirri  ba tare da sanin iyayena ba haka ita ma yarinyar basani  kowa nata shiya sa nake son kafita da ita daga garin munyi da ida akano  za adaura auren  amma kuma  gaskiyan  ba a kano  za a daura ba saboda  kada wata ran tane mi shedu a inda  aka daura  a kaduna ko zareya  nake son a daura.

"sani yace  tom yallabai  ita kan ta, kana,  boye mata wani  abu kenan.
"Nabil  yace  sosai
Nan Nabil ya kwashe komai  game da manu far su yagaya wa sani
"
"sani ya.ni   sa  yace    yawwa oga nagane nufin ka nace wa kaduna kano  ko da za tace bata yar da ba, tane miwajen ko  amma  yaza ayi  kana nufin ba tasan kano ba
"Nabil  yake  ai yanzu muka gama waya da ita tace ita ko damaturu bata,  taba zuwa ba.

"sani yace idan muka jen kano ta tambaye ni fa kasan   fa'kano  baya buya
Yace kai da zakayi  hanya  KADUNA meya hada ka da cikin  gari kayan ki baya kuma  gudu  zakayi sosai  yan da  baza ta tsaya kalle -kalle  ba.
Sani "yace tom yanzu  idan muje kadunan yaza ayi  da yanda auren zai  kasan ce  waye zai yarda  ya daura aure  batare  da shedu ba.

"Nabil yace  wannan  yarage kai da uwar  dakin ka dan ni ba nawa ciki  ita ta' tsara abin ta, yak'arasa  magana  yana  kallo Hadim.

"shima sanin  kallo ta yayi yace  uwar dakin na muna jiran ki.
"hadim  tace idan kukaje  ka samu irin anguwan  masu ka ramin karfin nan za kasa mu  masallacin  dai dai  rin ankusa shiga  sallah din na ka samu  limamin 
Kace masa  kanna son daurawa  kanwar ka aure  amma  da  ita zaka  je  idan  malamin yace ina manyan ku  ko yace  daga  ina kuke  kace  ku marayune  a Lagos  kuke da  zama  amma  asalin ku  yan  Niger ne
Kunzo  kaduna ne dalilin  fita da kanwar ka waje  za a mata  aikin idon  tom  bayan  kunzo  nan se  awajen  aikin ka akace  ba abaka izine ba
Shine wani  abokin  ka a India yace  katuro ta shizai mata kowai tunda  acan yake
Ganin ba muharra min ta bane yasa  kace  a a  shine  abokin naka yace  shi da ma yana son' ta idan kana tsoron wani abune  kadaura musu  aure kafin ka  turota  kai kuma  kafi amin cewa da hakan shine  kake son adaura  yanzu   dan yan zu za su tashi  yan ayi adaura auren  lokaci  zai kure
Nasan zasu  bukaci koda a waya ne ka hada, su da,  walilyan ku  se ka kirani zan sa  waya ta  a muryan maza  muyi mgn dashi  idan sun bukaci  na mijin  se ka kira Nabil
Wannan shine ka dai hanyar da zai bamu  *daman* auren boye asauka ke.

"sani ya tafa mata
Yana cewa  kai uwar daki na  baki da,  wasa
"shiko Nabil rungume ta yayi  yana cewa my one  ta ina kike fidda basira kine.

"tace Wllh dole ne my swt yan da wannan  baZAINABU  din taku tada ge  za ta  aura maka, mesu nan ta  wan da bazan  iya jurewa,  hakan ba.

"Sani yace yanzu goben da yau she za mufi ta
"Nabil yace da a suba.

"sani yace zaku sameni me rike muku sirrin ku ku ma zan yi duk yan da zanyi  na ga ma sa mu wa ni  matsala  ba awan nan aikin da ka bani.

"Nabil yace na gd.
"nine da gdy yallabai  kafi ko, mai awaje na,  fana mu Allah yara haihuwan da,  zatayi na narko  ta haifi yara 3 ko 4 kaga kwalleya yabiya kudin  sabulu.

    Fandau
Rasa, inda zatayi da wayan tayi  ta fadan kangon gidan  wanda ake karatu da daddare  nan suka gama magana amma yaja ta sun ba ta lokacin dayawa
Tana fitowa taga'har  anyi shara  matan gidan suna ta, faman yi mata habai ci da dan fadan su na bata musu shara kan lokaci ba dan  de suna shakkan  fandau  ne da bagana  ce  da, se inda mai yak'ere

Ko kallon inda suke ba tayi ba tawuce  dakin su.
Bagana ce tashiga
"tace haba ya fandau ina kika shiga ne ke kullum  se kinsa an mana gori  agidan  nan kin san sharan kine kika bare kika fita
 Suna cewa uwar mu azaune  su dafa su bata mu azaune
Sharan ma, de nayi  zakiyi  da naga abin yayi yawa na, tashi na, share.....
Ke ta dakatar da bagana  "anki amu su sharan banzaye kawai macuta   bin cin suden  banza na zalin cin  ko ba aga ban mu  suke dafa abin da,  ransu  yake,  so, ba bayan  sun gama jagolgolon  su sun ba mu mu na gani  baza abamu ba  in munci nama  a gidan nan se juma a shi ma, dan rago ake yankawa ne su bamu yan da ran su yake so su kwashi sauran su  shige  da,kin su   duk lemukan gwan gwani da naro ba da baba yake  sawa  ashigo dashi  sun taba bamu  da muda,  almajiran  gidan nan ki gaya mun  ban ban  cin mu  wllh  nede  naku
Sa   dena musu  bauta.
"Bagana tace  hakane kam nan da wata 2 ai shikenan  kina gidan shatiman ki  wllh yafandau  kinyi  dace  shatiman  yana da zuciyan  ne ma yabude shagon sa na kansa ke' kam kin dace  se de  fatana Allah  yasa  ya soki.
Tsaki fandau  tayi  tace  can ta, matse  ma sa kar ma yasoni  baya gabana Wllh.

"ya fandau  kin sanme kike cewa kuwa?

"Fandau  tace meko nace?
"naga da'kina  son  shatiman  shene de  baya sonki
"fandau tace tom nima yanzu nace banayi kuma Wllh  bashi zan  aura ba
"bagana tace  kin san me kike cewa  kuwa yafandau
Kin manta waye babane
Tom idan bakya son  sa  ina wani  ke da bawan da,  ya taba,  cewa yana son ki
"fandau  tace aganin ki ba  zan baki mamaki
          Jattko
08062383027
[3/12, 8:48 AM] Hauwa: *DAMA TA*




              *NA*
 
        *Batul Adam jattko*


*9*.....

🌈Kainuwa Writers

      Ahan kali talin ke,ninke   paper ta ajiye saman filon ta mama tagani ta, motsa daga ninda take ak'asa tana ta lalumen sandan, ta tasan ukku tayi lokacin tashin ta yayi dan mama macce ce meyawa,  ibada  Fandau ta sauko da sauri ta dauko mata sandan  tarike mata  suka fita ban daki ta kaita  ta gama  abin d zata  yi su ka fito  alwala ta, yi su ka,shige  daki
    Takai ta inda take sallah  ta dai dai ta,  mata,  sayuwan ta gabar kaman yan da  ta saba  ta koma,  bakin gadon ta ta'zauna  zaman jiran kisar sani  abokin  Muhammad  wan dan da, zasuyi  tafiyan tare  ka'mar   yan  da suka,  tsarashi idan anshiga  sallah  dan
Bada man fita idan ba, irin wannan lokacin ba har aka'kira'sallah  ta tashi ta, fita ita ma tayi  alwala  tun kafin a,  tada,  ikkama tayi nata sallahn tajuya  ta kalle mama tana faman lazimin ta har yan zu Bagana bata tashi ba  Muhammad  yace kar ta, dauki ko  mai  dan haka ita abin da,  tafi bukata  ma yanzu  taji muryar  mama  tana son taji muryan su  na karshe  dan shekara  ba, wata bane 

 'tace mama na tashe ta gyadda mata kai mama tayi alaman eh
 Tason ace magana  tayi  ta, tashi Bagana se  tako ma, dama tasan Bagana ba ta tashin wuri  dan haka  zata sake magana  taji  wayan ta da yake  kasan  maran ta  yafara gir giza.........
Dai dai  lokacin  da  taji  anta'da ikka'ma diri niya tafa ra tara same zata dauka  aha ka idon ta, yawulu mata wani tsohon  jakan ta dayake  rataye
Ajikin  kusa  tabude akwai hoton nan su ciki  har wanda mama tana da lfyn ido.
          Agur guje ta laluma   ta dauka tafi ta da  sanda, ta tayi han yan waje  kamar yan da,  taza ta duk ka,  kofofin abude yake  duk ka,  almajiran suna masallaci  kim2 ja,  shijab din ta,  tarufe  kanta tayi han yan babban titi idan sukayi zasu hadu   wayan ne yasa ke motsawa  Wannan  karon ta feto dashi  ta dauka  ta kara a kunnen ta taji yana cewa  "sani ne kifito  ta yamma  gani abakin layin dama ko nan tayi  tom tace   taka ra sauri  tana fitowa ko taga motan  ta, gane motan dan wan da, tafara ganin Nabil  dashi ne  ta karasa
Ta, saya  da sauri nacikin yasa,  hannun ya bude  yace  shigo karwa ni  yagan mu tayi saurin shigewa   wani  irin sanyi ta

Yara sata wanda  ba, ta tabaji ba  ga, kamshin Muhammad  wanda  baya ciki amma  Wannan  fitinenne kamshin yana nan  ajiyan zuciya tayi  kafin ta kara sa rufe murfin har yaja da gudu

-Waiyo  Fandau  kowa  yabar gida gida yabar shi..

  Tafiya suke yana  ta sula gudu harsu  ka bar cikin gari  a damaturu  ya tsaya  yasiya busu abin kari
 Message yahigo wayan sa  yana dubawa yaga

Hadim ce  yabude
_kasamu magani  Baccci  kasa mata a abin sha dan kuwuce kano ba ta reda, sanin taba,  nasan shigan yamma zakuyi ka'kama mata daki  a hotel  dan abar  daurin auren se gobe_
Yana gamawa  yagoge ya mayar mata,  da reply
_ok madam yanda kikace haka zayi_

 Aiko fitowa ya sake, yi  yasayo  tun agun yaballe murfin roban lemon  yasa magani Baccci  ya jijjigashi  yazo ya hada,  da abincin  ta yame ka mata

se  sannan  yakare mata  kallo   yaka'da kai Lalle  sai yau  ya tabbatar  da  hadim  taga'mada   Nabil  koshi da yake karkashin sa  basai iya dauka,  Wannan  ko a,  matsayin  yar aki ba balle  wai mata wan da zai iya mu amullan aure..

  -ayau Nabil  da  hadim  din suke,  sallama  da yan uwa dan agobe  zasu bar kasan  gaban hadim ne yak'e faduwa  dai dai lokacin da  drvr yaka' ya kwan gidan inna zainabu wato  yayar baban  Nabil  wanda ita ta kafa musu Wannan  dokan  sun sameta
Parlour  ta ahakim ce  bakace me kyu da tsafta ga kamala  zatayi kimani  shekara  68  tana ganin su  ta tamke  fuska

Sallama man  Nabil  yakara yi  yana zama ka'san tiles ita ma Hadim  sun kuyar da kan ta tayi  tazube  atare suka furta

'inna  nda dufto (  inna ina yini )

 Ita maciki harhen  kanurin ta, fara masifa
'tace na ce muku na wuni k'alau  nasan bakuso hakan ba ko  ai da kama hanyan ku zakuyi kuta fi se nasan  kuncika
So, nawa  ina kiran ka  modu  sai yau ka'ga daman zuwa  ko  baka zoba nasan uwar taka tafa da,  maka ko   dan  ina gidan ta dauki kururuwa  da kuka  tafita gidan uwar ta,ta,fatime  naji ance  duk  anan  kuka hadu  dan muna firci  da kuzo kuyi a gidan mana
Koma me kuka  kulla  ba, fasawa zanyi ba  na, baku  wata shida idan matar ka batayi  ciki ba, to ni zan samo wan da za ta, haihu
Haka ta karaci  matsifar ta da ker  ta saurara   da ta gaji  dan kanta.

Nabil ne ya sake matsawa gareta ya kamo hannun ta ya kwan tar da, murya yace,
'inna  duk munji  umar nin ki gare mu inna zan yi ko meki keso,   insha Allah  ki sa mana  albarka  dafa kan sa tayi kuma  cikin sanyi  tace
'modu na,sani kana son,  matar  ka nida nake ke zakewa amata kishiya ba ina kin halima bane
A,, a,  halima ta na da halayin da ta can can ci aso ta  amma  haka' bazai sa   muta ke  gsky ba adan ne maka hakkin ka, bayan taki  haihuwa wata kila rabon wata ne gaba da nata, kamar yanda uwar ta tayi se da aka auro halima ta haihu tukun ita ma, ta,samu  dan haka ita ma, tayi hakuri  amata modu ina son kasamu dan kan ka  kana, da yawan dukiya  yaran ka,  sune  Garkuwan ka idan basu yan uwan ka,  zasu  sa, ido akan dukiya  wanda,  wani nacikin su burin sa kamutu  ya gaji dukiya.
Wanda mu hakan kan bazai mana dadi ba modu  kana da' yawan alkairi  da zumunci
Amma  kasani yaran ka,  darajan ka haka tayi  ta tunatar dasu.
Har lokacin tafiyan su   yayi  har wajen mota ta rakasu
'' tace  yawwa halima kina da baki wanna hutun su    yasmin sunce keza sujewa

Rasss sukaji! gaban su  atura musu yan hutu suyi yaya da  shirin  na ajiyen  wan da za ta haifa musu yaran su  amma suka dake  suka  ce  'to inna  se sunzo
'inna tace wata kila madani za a'jeda,  na dade ban je England ba yasalam.!
'hadim tace azuciyar 
Nabil yace     "inna kin manta zaki je Jidda  ganin doctor watan gobe.
"inna tace  kai nifa  nawar ke
"Nabil yace duk da haka inna tun da yace  kikoma  abi dokan likita  yafe  da Girema zakuje ko  Kamal.
"tace shikenan Allah  ya tsare
Sukace,
"Ameen
driver ya ja suka fice 
,washegari  Nabil  yasamu rakiyan dinbin masoyan,  sa da abokai da yan uwa zuwa airport  motoci  kamar za ayi rakiyan.
Shigaba kasa  da kyar da temakon security  sa yasamu yaballe ya shiga cikin sekiya suke  old man  Allah yasa kafi haka  yan jaridu
Ko yagaji da fama dasu  suna shiga jirgi security suma suka shiga
Wasu daya wa seda suka ga tashin su suka
Bar airport din.
Itako Fandau daf da zasu fita a kano ta farka  tace  "lah nan inane
Sani bai zuyo ba yace  "naman ta sunan garin ko  hadeja  ne
"tace ummm  Baccci  ne yasake  kwasar ta   suna zariya tace

"inane nan
"yace zakirai mun kusa kano
Ko amsan shi bata jiba  Baccci  yasake  ibanta, har suka kasa kaduna
Har se da yaka  mamu su daki  tukun yazo  tashin ta  dakyar ta bude idon ta da ta kejin  yana,
Mata nauyi  ta daga kai ta kalle yana yin wajen mekyu  "tace  harmuzo kanon
"yace  eh
Tafito tana tafiya jikin ta duk asake  dan magani bai saki jikin ta ba,

Nuna mata dakin ta yayi  "yace  shiga
Ki rama sallolin da ake binki  za akawo miki  abin ci
Kici ki huta se  gobe zamuje  inda  za adaura auren ko.
Zan ce ni  yayan kine  kuma gobe da ganan zaki rube  idon ki  bazaki  bude  ba se  muje airport  dan amatsayin makahuwa  zan kai ki inda za daura  auren
Yagaya mata  yanda  suka  tsara
"tace tom tace  bamuyi waya da  Muhammad din bafa?
"Sani yace  yawuce England  wasu aiwuka ne da shi  zaki sameshi  can.
"
"zaro ido tayi  tace  England kuma?
"Sani yayi  saurin  toshe bakin sa  "yace auuw sudan.

Washe gari dami salin 12 na rana  ya  suka fito yace yame ka mata sandan  hannun sa  yace  to tun anan zaki rufe  idon ki  kada kibude  fa.
,yayi hakane  dan kar ta gane wajen
Allah sarki fandau  annade ki abai bai

Hakata rufe idon ta tarike san dan suka fito  yamata jagora  harwa jen mota
Yabude ta shiga  yarufe  ya zaga ya shiga ma zauni driver yaja  rigasa hai  ne  ya fado masa  arai  tunda  Hadim tace anguwan masu  karamin karfi  ta hayin makera yabi wani masallaci  yagani gefen sa wan babban  gidane   gefe yasa mu yayi parking  yace  bari  na gwada  nan naga    ya fita yanufi  wajen  wani baran dan da yake Wannan  katon  gidan  da gani babban  malamine.
Sallama  Sani  yayi  ya dukusa  "yace  gafur ta malam  wani abune  mai mushinman yake  tafe dani  malam "yace  tom Bismillah  ko  ciki  zamu shiga
"sani yace  nan ma ya isa   yakwashi  ko mai yanda  suka  sara  yagaya masa  harda kari.
Shiru  malam  yayi  yana girgiza  kai
"yace  hakan bazai yuwu ba har se........
               *by*
       *Jattko*
08062383027
[3/12, 8:48 AM] Hauwa: *DAMA TA*

           *NA*
         
       *Batul Adam jattko*
KANUWA  writers
     *8*
 "dariya bagana tayi  tace  ai mamaki  daya' zaki bani  naga  kin ja hankalin  shatiman  yafara sokin......

"dakata Fandau katse ta cikin tsawa    kar kika ra yimin maganan  Wannan  shatiman  yau she na fara wasa da ke
"bagana tace afuwa  yar uwa  na,bari
Dan bagana  tana mugun shayin yayar ta ta duk da ba,wani ratane  tsakanin su ba.

          *waye*
  *nabil shid*
 Nabil da'nega
*Alh abukar manga*
  Alh abukar  dan asalin maiduguri  ne  cikeken kanuri
 Su ukku iyayen su su ka  ahaifa  ZAINABU  itace babba  da tazara sosai tsakanin ta da abukar  wanda kafin ahaifi wanda ya biyo ba yan sa ita ZAINABU  har anyi auren ta wanda yabiyo bayan  abukar  shine inusa
Iyayen su sun da de da rasuwa  tunkafin  auren abukar  shiyasa suke daukan ZAINABU  tamkar  itace uwa da uban su  dan itace ko mai nasu,  abukar  yana da matan  aure biyu da yara da dama Maimutatu itace uwar gida suna ki ranta  da  bani  se  ummin  Nabil itace  amarriya
Sunan ta Hajara  duk yaran ita ma ummi suke  kiran ta  Maimutatu  yaran ta  9 amma mata ta fara haifa 6 mata 2 maza matan ta fara haifa
Ita kuma hajara  ummi   yaran ta 5  mata 2 maza  3 nabil shine babba      se kamal  se  Hanif   se Jidda  nabeela
Akwai hadin kai  da fashin tan juna agidan  yan da   baza ka gane dan, wannan d Wannan  ba ban banci kawai  yaran  ummi  fararene  irin sol din nan tunda,  ita ummi shuwa ce  Maimutatu  kuma kanuri...

Nabil tunyana yaro  yake mutukar  son ball kullum  yana gidan su abokin sa,      bilal  suna kallo  tashan ball  sosai shida bilAL ra, ayin su yazo daya ko da lokacin  sasu  a makaran ta yayi adare aka' sasu

Kan su baya ja sede afito,  dasu wasa ka,  wai  anan  za agane  su mazane  amma  aciki aji  kamar  sokayi   lokacin  jarrabawa  kusan  susu ke daukan  ajin  malam tunsu na complain har suka gaji wani malamine  yaga,  yanda suka mayar da han kalin su wajen wasan kolon ne  yasa  yace wata  kilah  anan abincin su  yake shene  yadage,  musu  irin idan za ayi gasa  na makaran tu  yake hadawa dasu  duk da basu kai ba amma abin  mamaki  sunfi manya  bada shimma  ba taba .kai su ga'sa  sun ba da kunya ba se de sulashe

Tun suna primary school  ake fita da su   jahuhi  ga san   bilAL  Nabil  yara  ne da suka sha  hara tun suna yara  karatu ko ba abin da suka sinta har suka gama primary  din su  ganin haka'

Baban bilal alh maina  khange  ya yanke shawarar  fita  da,  bilAL  England    dan sashi  amakaran koyar da ball din  gaba, daya wato  poot ball academy
Atake yana gaya wa bilal  yace ina shifa  ba inda zai je  inko  ba. Haka  ba se  de  idan  da,  abokin sa,  Nabil  za a fita  ta a kayi akayi  yaki  daga   karshe

Alh maina  ya nemi shawaran baban  Nabil  alh abukar  yace  shi  bashi  da kudin  da  zai  fida  dashi  waje  dan  yakoyi  wata  ball  acikin  yaran  sa maban da Nabil  ne  kada'i  meyin  private school  duk comvt suke yi shima  ga nin   Nabil  shini  babba  a maza  shiyasa.
'alh maina yayi Murmushin  yace  alh abukar  ni yar dan  ka nake buka' ta  bilal da Nabil  dayane  awaje  na
Alh abukar  yace
' yace  aini  idan za ka yanke  hukun ci akan  Nabil  base  kasa  nar dani  ba

Haka aka tarka tasu  aka kai  su  kasan na England
Aiko  a nan ne  suka san  an  sasu  makaran ta dan ko yaran  turawa  basu girma suke  ahaka suka,  gama
Secondary school  din su  koran  graduation din su
Yan gidan su bilal kam duk ka sukaje
Shiko Nabil inusa  ne yaje  kanin baban s
 Sunsamu karramawa  sosai  sun sha kyututuka  dan gasu sun murje sunyi kyu  dan duk kan su farare ne shikam  Nabil  yasa je da turawan sosai  se kyu ma daya fi dayawa acikin su
Atake malamn su suka bada shawaran  I'dan suka gama hutun su, suzo su  jona degreen.

a, nan dan shekara 2 ne bawani dade wa zasuyi ba

Dawowar su gida  yaga  hadim din sa  ta, girma  hadim  ka,  mar yan da nagaya  muku  yar gidan   yayar ummin sace  da  ummi da mama wato  fatime  uwa da uba daya  su 6 amma 2 sun rasu  yan zu saura  fatime 
Da,  ummi da abba  musa  da abba jabir
  A Wannan zuwan ne   suka nuna  bajin tan su wan da ba cikin maiduguri ka'dai  ba  Nigeria ma tasan  da zaman su wan da  awan lokaci  du du du bazasu  wace  shikara 17  dan  asan da,  sukayi degree din su ma a san  nan suka,  cika  19 yarane  ashe karu amma  bame  kallon su bai  ce mudu cikakkun samari  bane
Basu wani da de dazuwa ba bilal yayi  aure  amma  Nabil  yace shifa  yayi  yaro dayawa
Hadim  ba nacin  da batayi ba yace tabari  ta, gama sucondury  tukun
Wasa  wasa wadan  nan  yaran  sun  gan gar kananun  yan ball  na Nigeria  a na haka
Super eagles suka dauke su   mafarin  dau kakan su ken

 Ko daya basu sha wahala ba su ka sha hara duniyan  ta san su  baye Nabil  kafan sa, mey sa dane
Ahalin yan zu nabin yawuce tunanin me tunani  ganin  yan da kafan sa yake da  sa da ne yasa baya zaman kungiya  daya  in da aka fi siyan sa da  dara, ja
 Nan yake zuwa yana da mugun daukaka   yau na
Real Madrid Manchuria  da Munich  arsenal  dade  sauran  su

Ban ban cin sa, da bilal kenan  dan shi  bilal  kaifi daya ne  idan yamasa  korafin  meso  bazai zauna  waje daya ba  amma  bai yada  super eagles  ba  sabo da,  kishin  akasan sa
Dariya  yake  'yace  my friend kaifa  bason kudi kake ba  cikin sa kataso 
Sabanin nida  duk  dan ginmu  dani suke ta kama
Ka ga  dole nayi zafin nema  tun kafin sufa yazo mini
'Bllal yace  handama de irin naga koyan zu ka'ajiye  aiki  kana  da,  abin da har jiko kin ka baza susan  mey ba, buba  da ko yanzu  kafi  wani  governor  Nigeria  kudi  ga gauka ka
Dariya yakeyi   ya kyale bilal dan  shi yasan irin tarin alheran da,  yake  samu
Yayi  aure da  hadim   yanzu  shekara  6 kena  Allah  bai  basu  haifuwa ba
Wannan  kena  ta kai cecen tari shin
Nabil  kena
 Fandau  zaune
Akan gadon ta  Baccci  yaga gari idon ta  yanzu  shike nan  nan da  awane  ka'dan  zata  bar mama ta da bagana  tabi namiji
Anya batayi gan gan ci ba amma  idan tatuna kala mai da Muhammad  yake fada  akan ta  yana  kara kar fafa mata,  karfin guwwa  na zai
Ingan  ta mata rayuwa musamman  na cewa  da yayi  zai ne   mawa mama  lfy yan  idon da  take kanin  kamar  shine idan
a ka,  samu su  jin dadi kamar  kowa
Amma  ya,  mama da  bagana  zasu ji  idan  sun rasa,  ta  juyi  tayi  ta kalle  kowan ne su  tare  da,  goge  guntun  hawayen da yasur  to  mata
 Ahan kali ta sauko  tanufi   inda  take  tajiye  litafin ta
Taciri fefa  ta, koma   gado.
Ta'fara  rubutu  kamar haka  da  arabbiya  dan   bata iya boko sosai ba ta na  de karanta  hausa  shima  ta koyeshine  agidan  anty mairo  wata  makociyar  sun
_Asslamu alaikum ya,' uwata_ _nasan  asan, da_ _zaki ci karo da Wanne sa, ko,nawa_ _wanda sai zame muku bakin sa, ko_   _banyi haka'ba  mama_ _sedan  ina son cika wani buri na mama hukun cin da, nayan ke ni kai na_  _ina kuka balle keda,  nasan zan barki cikin gorin kishiyoyi ki_  _mama mama ki  gafurce ni  ki temaki  rayuwa ta_ _karki fadi mummuna kalma akai na asan da zakiga soko na zan yi tafiya amma_ _mama zan zomiki da abin mamaki duk  da nasan yanzu ma_ _naba ki makaki  nayi abin da nada sa tarishi adangi_  _amma mama ina baran addua ki  ke da yar uwar ta  na rayu cikin  rashin yanci mama_ _shi baba zai dauke ni yabawa  wanda zan ka'ra, rayuwa cikin kunci  dan mama shatima bazai taba so, naba_   _musam man da, nagano  yana son yar uwar ta bagana_ _mama kiji  tausayi na ina da, dalilin yin haka_
_amma dalilin mana kunta ta muku bane_
_yar' uwa ta roko, nah gareki  kar kibari mama ta, min baki  ki aure shatima_

*masoya masu bin Wannan lbrn  karku ga, bana sa, soyayya ko*
*ko kalamin soyayya  ina bada laabarin ne yan zun ata kai ce dan*
       Amama duk abinda kuke so akai
[3/12, 8:48 AM] Hauwa: *DAMA TA*

            *NA*
                   
           *Batul Adam jattko*


*10*
🌈Kainuwa writers Association🤝

  Hakikan ku
"Sani yace  kamar yanda nace gafarta malam  mubaki ne
dan de idan nadawo zan rasa aiki nane wllh da  da kai na zan kaita kamar  yanda na tsara.

Ahaka yayi ta kashe malam da kalamin gamar gaske.
 
Malam ya nisa yace
"badan wannan zamani  da tsarabe tsarabe  yayi,  yawa ba azamanin mu ni kaina hakan  yafaru akai na  auren bari  a meduguri nayi  ina   almajiri  aka bani  auren gaggawa,
Bani da kowa se malamina  kuma aminin babana,
Shiya karma min aure  alokacen ba hanyo yin sadar wa  harse na mata ta ta  haihu san nan muka  .
Zo nan kaduna  da mata ta bintu  da dan ta Muktar  bani nabar zaman meduguri ba har seda.
Mukayi yara 5 natare gida
yanzu  haka nikai na ina zirartar meduguri  dan kusan nafi wayo acan kusan dukan aminai na suna can musam man  babba  amini na  zanna modu.

Daba daya jijiyo yin jikin Sani  yaji yana harbawa  tunda yaji malam  ya ambaci meduguri  balle  da  yace zanna modu baban Fandau  kena ko da  wani  zanna modu
Tunanin  sa ya katse sanda  yaji  malam  yace  "to yanzu  aure  yazama na karshen  zamani se anyi wani 
Aune aunen likita
tom kaga duk da kace ita yarinyar  kuna tare kaga
Amma  tunda bashi,
Namijn   bazai yuwu ba.

Aiko Sani yamek'e  dan dama haka yake son jin tunda  yasan baban fandau
Yace "malam na gd  har yazuya yaji wani daga cikin su shima babban mutum ne  yace " malam  amma da kaduba Wannan al amarin
kaji fa yace nan,
Da 3 zata tashi kuma idan ba a,  yi auren  ba  aka turata malam  muma bamu kyu tawa Muslim ce ba sabo da annabin mu yace duk inda macce d namij suka keben ta shedan ne cikon na 3 su  malam  ko yaya ma,
Ka daura auren tunda aikin alkairi ne  muna shedu samu samu lada.
Malam yayi nazari yace "akira  shi
Sani yajuyo  yazo yakoma.
Malam "yace  zauna  Sani  ya zauna  gaban sane yake faduwa.
"Malam yace yasunan ka kace ma?
Sani yace " isa
Malam yace "isa kace ku mutane  Niger ne kasu wan ci yakawo mahaifinku legos  ko?
Sani yace "eh
To yanzu adan ginku za asamu wan da zaka hada mu ko a wayane dan neman izinen daurawa yarinya aure?
Sani yace "eh
Malam yace"masha Allah.
"       Tom shi  Muhammad dan inane?
Dam gaban Sani  yasake faduwa  dan baizaci zai tambayi dangin Muhammad ba amma yadaure  yace "dan Lagos  dinne shima iyayen sa suna can.
Malam yace
"Masha Allah kaki ra iyayen sa awaya  sune mawa dan su  auren  ko
Yasunan  yarinyar?
Sani yace "Fatima
malam yace
"ayya  kafito da ita  ga yusuf zai shiga da ita ciki  wajen mata kafin adaura ko.
Dakyar Sani yameke  dan farga ba mezai ce idan fandau ta fito suka gane ta  yaza yi.
Yusif yabi ba yansa suka kara sa inda mota take   Sani ne  yabude  kofan ya kama san dan.
Yace "kifoto za araka ki gidan Malam
Yadan sunkuyo dai dai kunnen ta yanda yusuf bazai jiba yace "idan kina son kada asirin mu yatonu karki kuskura kiyi magana me tsawo  kar kinu na kin kin taba zuwa meduguri  dan yanzu haka matar sa yar can ce  kuma ina sammanin ma yasan baban ki.....
Dasauri fandau ta bude idon ta.
Sani yace  "tun anan zaki tona mana asiri kenan  ta rufe  ta natunanin tabbas baban ta yana da mutane akano
"tace toyan zu yazanyi?
Sani yace  "kokar tawa zakiyi kiyi magana  da hausa san nan ki ja shijab din ki ki rufe rabin fukan ki dan zanen kiya buya.

Tace "tom
Yakama sandan  tafito yame kawa wanda aka kira da yusuf sandan shikuma yaka ma sukayi Wannan  katon gidan.

 A falon  mama ya ajiye ta bata nan dan sun fita gaisuwa  wani mutuwa  a dattawa
AISHA yakira kanwan sace "yace ga bakuwar malam  kiba ta ruwa
yafice
Samira tace "sannu da zuwa yasunan ki?
Fandau azuciyar ta tace 'ruwa akace  kibani
Ba gulma ba
Afile kuma tace "Fatima
Samira da taga ba fuska se ta dauko mata ruwan ta bata.
Malam ne yashi go harciki yazauna yace "sannu baiwar Allah  Fatima  ta gyada kai yace kin amice kina son Muhammad  da yayan ki yace  in a daura auren ki dashi?
Fandau taja shijab din ta tasa ke rufe fukan ta kamar irin me kunyan nan
"tasa ke gyada kai  tayi shiru
Malam "
"yace masha Allah  shima Muhammad  din yazu mukayi waya dashi ayan da  naji yana yin sa nayar da dashi yanzu lokaci sallah yayi.
Idan muka idan zan daura miki aure nayi magana  da kawun ki  Adam  shi yasake karfa fa min gwiwa  ma dan har number wayana  yakar ba yace zai  zo ya min godiya  shi ma nayar da da karam cisa Allah  yabaki sa a ayi  aikin idon naki cikin sa a.

Tace "amin malam  yameke  dan ankira  sallah
An daura  aure Muhammad abukar  da Fatima  Muhammad  a yau Monday  akan sadaki naira 5000 wanda Sani ko nace isa anan  yabada  Malam  yakar bawa Muhammad ahannun  isa yayan ta  wan da dumbin mutane suka zama shedu
Agaggauce Sani "yace  zamu makara  akwai  abubuwan  da ban ga maba na tafiyan ta.
Malam "yace yusuf  shiga kafito min da Fatima
Yusuf  yameka  yayi ciki  suna fitowa  haraban gidan se ga motan matan gidan yashigo  kafin su fito har yusuf  yaja fandau  sun fice
Har mota malam  yaraka ta yana mata nasiha duk yana tausayawa marai cin ta akwai  abubuwan da yaka mata ace uwace  takoya mata akan zaman aure  gashi nan kuma sunzo  akurerren lokaci  da yasa matan  sa sun mata duk a bin da akeyiwa  amarriya,
Bayan tashi  ga yusuf yaru fe  Malam ya meka mata sadakin ta yace "to Fatima  ga sadakin ki  Allah  yaba ku ladan  aure  da zuru'a nagari  addua yayi tayi bayan wanda  akayi a masallaci  Sani yayi godiya  yaja mota yana cewa malam  zan dawo  yanzu  idan naga tafiyan ta
Ita ma fandau  ajiyan zuciya ta sauke dan sarai ta gane waye shi  amuryasa ma  mlm  dauda ne  aminin  baban ta   dama  akano  yake tace  dan ita bata san inda yake ba dan  kunsan fandau  bame shiga shirgin da,  bai shafe  ta bace.

Wayan Sani ne yayi  kara ya dauka  yace  "eh yallabai  an daura
Wllh sunan sa Malam  dauda medara
Dakar fi Nabil  yace "yasalam! Sani  kasan waye medara  a waje na kuwa?
Ni dama naji muryar  kamar  nasan meshi  baban doctor  Muktar ne fa
Sani yace   "karka damu yallabai  tuda de  anri ga an daura  har nakusa fita anguwan ma,
Yanzu haka ina hanyan
Airport  ma.
"Nabil yace  ta kayi kamai  asirran ce sani yace
"Ok zanyi insha Allah  yakashe wayan
Sani duk dama yariga yagama  duk cuku  cukun duk ka
Se ga fandau  cikin jirgi tana wur wur ga ido  se yanzu take
Na daman anya tayiwa  mama adalci kuwa  koya take  yanzu  ita da Bagana  wani irin kuka  ne  ya kufce mata  Waiyo  mama
Kiyafe min  zan  dawo  gareki  da  alheri ban yi dan  na bata niki ba  se dan hakan shine  *dama ta* kuma damar mu  gaba daya  yun kurin tashin  jirgi ne ya katse mata tuna nin ta dan jitayi  kamar za ah juye mata kayan cikin ta   Sani ne  yakula da hakan  "yace  karkiji 
Komai idan yadai  dai  ta  sama bazaki ji kamai
Ita de tana cikin  tsoro  har ta dena jin girgizan  ta dawo 
Tunanin mama d Baganan ta
se washi gari d asuba suka sauka  abirnin  London   suna sauka
Yakira  Nabil  yace  gasu  yace  nan  yace natura driver  kufito zakaga  yakira ka ma   basu da wani kaya dan haka basu sha wani wahalan  bin cike ba   suna fitowa  driver  yakira  Sani  yadau ka yakayi  magana  cikin  harshe turan ci   taga yanu fi wani mota  ita ma tabi bayan sa wani matashin bature ne  yake ta yiwa sani murmushi  bude musu yayi ta shiga  baya  Sani  yashiga  gaba driver yaja su  ka dau  hanya ita de  fandau  jita ke  kamar  duniyan,
Aka canza mata se faman  baza  ido  take  ta na kallo  wasu  irin dogin gini wan da ko  a TV bata taba gani ba
Suke ta wuce wa tara sa,
Na kallo  hon driver Yayi  agaban wani  gidan mekyu  da girma wan da fadan  sa bata lokacine,
Wani na ura'taji  yana kara  can get  din da kan sa yayi  sama  driver yashiga  dasu  ita ko nunani take to nan din  inane  har sani  yafita tana nan  ta kasa mutsi  Sani  yabude  mata  sai  kuma  sani  yaji  mugun  tausayi  ta  da wautar ta na  amince wa namiji  yace mata
"nan shine  gidan  auren ki  Fatima  duk  kofan  da  zaki  shiga to  kishiga  da
Addua Allah  yakare ki  da ga sharrin abin sharri.
Gyada masa  kai  tayi  tafito.
Suka nufi  katon  ginen  wanda  seda  sani  yafito dawani  pepper  ya daddan  na wasu  number ajikin  kofar  san nan  tayi  wani  turan ci  da sauri Fandau taja  da baya dan jin kofa yana magana.
Shi ko Sani wasu number yasake sawa
Aka akara turancin,
Sannan kofar  ta bude wani katon  parlour ne marar misaltuwa  Sani yashiga itako ta kafe ta tsaya
"Sani yace shigo mana karyaru fe d bismillah ta shiga
 Bayan kayan alatun
Cikin akwai mata kalan beni guda ukku
Na ban garen  hagu Sani yanu fa da ida  shikan shi  upstais din ba irin na gidan Habib bane da ta
Taba hawa wannan
Awani irin murmurde yake  ga sansi tiles din bashida yan kan ga irin wanda tasaba gani gashi fari tas  se sheki yake
Suna gama  hawa
Wani katon parlour  ne ya baiyana  d kofofi ciki suka sake
Bita wani badai daicin falo yabude mata kofa yace
"to ga dakin kinan kai har babban falon .daki kaga mun hau naki ne shiga ki zauna kijira  angon naki  tashiga shiku ma ya juya  a hankali ta laluma bakin  gadon ta zau na irin
Gadon da  take
Gani  ajikin hoton zanin gado ashi akwai shi aduniya.
Ta zauna  wai ita yanzu  hakan amarrya ce ni ko ya aure kazo min da haka baraki yan yan   uwa se wani namiji
Ba kamshi bare gyaran jiki irin na amare  hannun yenta da kafan ta ta kallan ba irin na amaren barno bane
Yanzu ahaka wanna hadedden  gashen zai gan ta kafa duk kaushi ita kanta tana jin yanda jikin ta yake tashi dan ra bon ta da wanka yau  kwana 4 kenan tun agida dan data shiga bandakin  kaduna  ko nace  kano anata daukan
Kasa amfani  tayi da komai to balle wan da da take sammanin   yadoke  can ba za ta iya ba za ta bari muhammed yazo
 Ba kitso
Ba  lalle
Ba  kamshi
Ba  sutura mekyu irin na amare
Ba  gyaran jiki
Hannun ta tasa tacire  dan kwallin kanta wani irin turiri
Na warin gumin nan yaturni keta dan ta man ta rabon ta  da.
Tawanke shikan sa kitson yafi sati 3 akan ta
jita shi anbude kofa  zuyowa tayi  ta kalli wajen muhammed
Tagani shida wata me kamar sa sak  amma ita gajera ce hannun su sarke da na juna suna jifan  ta da murmushi

 *wah naso sako muku yan da zashi kwashe amma kubini akwai darisa*

           *by*
           *jattko*
08062383027
[3/12, 8:48 AM] Hauwa: *DAMA TA*


         
            *NA*

   
    *Batul   adam jattko*



*_🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION_*🤝


🌐HAJOW📝🌐
   


HAKURI DA  JURIYA ONLINE *inaya yaba kaunan ku gareni*  🤝🤝




    *11*




  Barno gidan
Zannah  Modu
"Bagana tace mama wai ina Ya Fandau take ne?
Mama tace "bata dakin aiko da asuba  ita tayi ta ta shin ki bakya son,
Tashin asuba
"Bagana "tace mama aine bana bccin safe itako  YaFandau kullum se,
Tayi bacci safe shiyasa aka cire ta a yan sharan  safe
yanzu ma nayi mamakin rashin ganin ta kwan ce  kuma bata,
Tsakar gida
ABu  kamar wasa
Bagana tana zuba ido shiru har 8  tayi
Takasa daurewa  tace "mama banfa ganta ba  mama tace
"tom ina tashi ga dan ita ba irin ki bace bata  shiga dakin kowa amma kin duba kango?
Bagana tace "mama ba inda ban duba ba,
Niban ganta ba
Mama tace "Fandau bata fita se tasanar dani balle ma da safen nan ina zata  kije de kiduba dakunan gidan,
Bagana tame ke tafita duk da tazan baza ta taba,
Samun Fandau dakin matan gidan
Ba amma hakan ta daure tafita duk dakin da tashi ga bata tambayan su sede tayi kamar taje gaida su
Tazo tace wa mama batanan.

Itako mama cikin rashin damuwa tace "shikenan dan bata  taba zatan wani abu  ba  Bagana ta tashi shara ta fara nade shimfedan mama zata daura bargon
Gado taga pepar da Fandau ta ajiye akan filo ta dauka
Tabude tayi  tozali da kyakkyawan rubutun yayar ta ta cikin harafi na larabci  zama tayi  tana karan tawa  amma se sake mai mai ta karatun,
Take   dakyar tasa mu ta har hada abin da ta fashin ta jiri taji yafara iban ta

Dakyar ta iya bude bakin ta ta fara hada kalmomi kamar haka "YaFandau   yazaki mana haka mutum cin gidan muda girman sa yawuce nan a idon mutane
YaFandau  bajiya muka yi magana da ke ba kiyin hakuri  ko mai mai wucewane  idan  shatima ne bakya so,
Da fito waki kayi kika fadawa baba  bakya son zabin sa yafi  ke kanki kinsa
Mama zata sha gorin kika jamata abin  gorin me mama ta miki kika  mata haka,
Koda ma wannan shine mamakin da jiya kimace zaki bane ta fashe da kuka ta fada jikin mama
Itako mama da bagani take ba bata  san me ake ciki ba atunanin ta ma Fandau din din tana dakin.
Saitaji  kukan  Bagana ya tsanan ta
Tace "meyake faruwa?
Dakyar Bagana ta karan ta mata wasika cak mama
Tameke  bakin ta yana furta
*wa'alahaulah wahlaku watah* *illah billah*
Kama hannun Bagana tashi tace "bani wasikar  muje  wajen baban naku
Karamin parlour
Sa takai ta baya ciki
Tasan yana babban
Falon yana koyawa manya mutane na anguwan da manyan almajiran sa karatu tace mama bari nakira shi
Ko sallama babu Bagana tashi ga cikin hawaye da in inah tafur ta "baba  mama tace kazo gata afalon ka.
Duk kansu shiru sukayi musamman
Malam da bai ta ba samun  irin wannan kiran daga gidan saba
Balle mawajen matar sa mehakuri da take kamar ba matar sa ba dan ba
Tada baki wato kwana.
Mekewa yayi yakama hannun  Bagana sukayi  ciki  kusa da maman  baba yazo yazauna
"yace Aisa lfy kuwa?
Mama batayi magana ba tame ka masa wasikan hannun ta  yakar ba yafara karantawa shima kan sa zuface ta karyo masa daya gama yayi shiru yana gyadda akai
Yasauke ajiyan zuciya yace "Aisa ni kam na godewa Allah dan yaba ni yara sama da 30 amma duk ban ta ba ganin sabanin tar
Biyana ba dan duk kan su masu bin umarni nane dan ya jarraben akan  fatima na dauki wannan jarrabawan    sai de ban so  wannan abu yahada dake ba naso ace awani dakin ne banaki ba saboda yanzu ma kinacikin  jaraftan ubangiji  ga jaraftan
Rashin ido ga na rashin baki da wani dangi akusa ga yaran ma basu da yawa acikin 2 da yabaki yaba'  tar miki dayan
Aisha kiyi hakuri  kici wannan jarrabawa zaki ga riban sa tun anan
Duniya Allah ya gani Aisa ina sonki dan kece naje na dauko awata uwa duniya amma gashi  yanzu yar'ki   tace kun rayu cikin kunci
Ina tuhuman kai na akwai wani kuncin  bayan wanda da da kan ki kikace  kin ajiye kwanan ki wannda ban so hakan ba najure.
Mama cikin kuka ta fara mgn  "malam Fandau tana da gsky mun rayu cikin kunci kuma haryan zu cikin ta muke
Mlm ba zan ce bakamen  adalci  ba dan nasan bakasan  abin da yake faruwa agidan nan ba  a nan mama ta kwashe duk yanda suke ciki
Narashin yanci tagaya masa banda  jinjina kai ba abin da yake shiba shiyake zuwa cefane ba  dansa  abdulkhadir  da dauda su suke gudanan da komai  shide idan sunce kudi yakare yaba su bai san yagidan yake ciki ba dan idan bawa ni abu me mushin manci bane saiyayi wata ma baishiga ba  yace
"tabbas ban yi mikin  adalci ba kimin afuwa zan gyara ko mai kuma da ga yau  na dawo miki da kwanan ki idan dan  dafa abin cine zansa ane mo mai dafawa     game da tafiyan fatima kuma ninasan yanda zan  yi ki kubuta ajin gorin abukan zaman
Ki, wayan sa yadauka yakira yaran sa manya magidan ta da kuma matan  gidan nan da nan suka hallara yayi.
" garan murya yafara magana kamar haka da farko de abin da yasa natara ku anan
Shine dan insanar muku da na aurar  da Fatima Fandau ga dan wani abokina
Da yazo ajiya da daddare kuma ajiya nabashi yata fi da ita, niger.
Sude manyan yaran cikin tuhuma suke kallon  sa su suna so suce yaushe aka daura aura basu sani ba amma kwarjinin mlm  yahana su mgn  matan ko murna sukayi andauke musu me rashin kunya.
Mlm yajuya yakalli
Shatima  "yace shatima kayi min afuwa akan karya alkawarin da na maka baka samu Fandau ba amma ga Bagana zata maye maka gurbin ta shiko shatima har da kukan murna
Addua sa da sadaka dayakeyi na Allah yakawar masa auren  Fandau ya amsa dama Bagana yake son

     London
 Cikin mamaki take binsu da kallo
Azuciyar ta tana cewa "to meya hada muhammed da wata mata shida yace ba da sanin dan ginsa ba yayi aure wannan daganin yanda suke kama yar'uwar sace
Katse tunanin tayi take binsu da kallo
Suna tafe cikin rigan baccin su iri daya ban ban cin nata na mata ne shi kuma na maza suna jifan tada murmushi kyan matar yaru data dankamar zata fi muhammed ma,
Har
suka  zo suka zauna akan  wani kujeran karfe suna manne da juna matar ce tafa ra magana
"inami ki barka dashigo wa sabon rayuwa yasunan naki ma?
Ita ko 'fandau kasa mgn tayi ganin yada Nabil yake manne jikin mata dagani irin shahararrun masoyan nane ko acikin yar uwar sa ce to yana jin da ita amma meyasa amasayin tana matar sa ita bazai
Zokusa da itaba  se ma wani irin kallo da yake mata me kama da na tsana.
Tuna nin tane ya katse san da taji matar  tana ce wa
My star ya sunan ta
Ma yamusa fuska  Nabil yayi yace "wlh naman  ta kinsan da za adaura auren ma Sani da ya tambayen  bantuna  ba kikirata  mai lallon tunda taki fada me naki nase kinsan sunan ta.
Murmushi Hadim tayi tace "hakane fa kamar yanda muma bai kamata taji namu sunan ba gwara mugaya mata abin ta yasa mukayi aurin sirri da ita kawai.
Mai allo bari naga ya miki tah kai tacen  tarishin mu da kuma abin da kuka dauko ki kimana.
Mijina kuma dan uwana  munyi aure da shi wajen shekara shida 6 Allah bai bamu haihuwa ba musha jigilan asbiti amma duk inda muka je se ace matsalan daga waje na ne  mahaifata tana nesa amma zan haihu to bai kama ta mu zauna na bamu san san  da Allah zai kawo mana ba shi nemu kayi tunani komuje gidan marayu mu dauka
Amma hakan  bai mana ba sabo da bamu san irin xuru arda zamu dauko ba dan
Haka ne  mukayi tunanin  wanan,
 han yan wan da itace ka' dai  damar mu waton mune min  da'  ta hanyan halak shine dalilin auro ki.
Zaki haifa mana yara 2 kacal ni inason da'namiji  shikuma mijin yana son macce  ni zan sawa dana Bilal shiku ma zai sawa ya'r hajara zamu kirata Fujjeera
Amma karki damu daga kin haihu zamu rabaki da shi  dan karki yi sammanin zaki shawa halal shayarwa  to kinji manu far mu da kuma dalili yin wannan auren
Na sirri dake ke zaki haihu amma a ido duniya da dan ginmu nice na haihu
Kina bamu zamu kadaki gidan iyayen

Kar ki neme mu dan me mota baya bin han yan me jirgi
Wato baza ki same
Muba se adarussalam  ta gama mgn tana kallon Nabil

My star kana da magana ne  tabe baki yayi yace "kin gama fadan komai
Ai yayi magana yana yamutsa  fuska dan yanda jikin ta yake tashin warin gumi har inda yake  yameke itama
Hadim tameke ta tana cewa baki da abin fada kenan ko.
Ita ko fandau mamaki da wani irin zuyawa kanta yake dan ta gane manufar su amma ita bata san mawane azalne yaja mata wannan
Ba anya  ba bacci nake  ba Allah kafar kar dani awannan dogon mafarkin  kasa ba gaske  bane
Inko da gaskene meya kai ni yin hakan bayan nasan
Hakkin mama ma bazai barni na zauna lfy ba 
Jinta kun fitan su yadawo da kita tace
"muhammed  muhammed yanzu haka zaka min ba haka mukayi dakai bafa
"yace na miki ko kikayiwa  kanki  tunda harki ka ai ka tawa iyayen ki irin wannan babban lefin abin da kikayi shizaki  gani nida kika ga dalilin auro kima umarni yayar  mahaifinane bama iyayene ba
Dan ina girmama darajan  su kina mcc kibar iyayen ki
Kibi namiji wata uwa dani ya ba da sanin suba duk abin  daki kagani sakai yansune ne  kuma ni,

 ba abokin yinki bane karki kara gigin yimin  mgn
Yanuna  Hadim yace gada wan da zakuyi mgn dan ita tasa aka auroki  mumunan  fuskarki  da kazan taccen  bakin ki ita zaki din  gabude wa bani ba.....

 *kah muje zuwa yazaman zai kasan ce* *labari yanzu aka fara*

   


         *jattko*
[3/12, 8:48 AM] Hauwa: *DAMA  TA*

       *NA*
  *Batul Adam Jattko*


 🌈KAINUWA WRITERS
 ASSOCIATION🤝

😭😭😭😭😭😭
   *Ta aziya  ta ga duk kan jattko* *nawan nan babban rashi da muka yi acikin family  Alh mustapha  yir jattko** *musam ma yayena Alh lawari  jattko da Alh Adam jattko* *da Alh goni sale jattko* Allah *yabamu jimirin daukan wannan babban rashi na uwar mu hajja zahra*  *Allah ya sa halin ki me kyu yabiki uwata*

 13
 Da karfin gwuwan ta taga ma safeta da mai d turaru ka
Tace "taso
Fandau bayan da ta iya haka  ta tako dan ta riga ta sallamar  da rayuwan ta daga ita sai towel  tace "zauna nan  ta zauna Hadim ta karasa inda Nabil yake yana karatun wani jarida  tasa hannu ta kwace  jaridan  tace
Tace "na gama nawa saura kai ahan kalin ya ajiye jaridan  hannun sa ya dago ya kalle ta yace "to sai yaya?
Tace sai muyi fatan a yau muda ce nasan ma zamu dace den dan nasan mijina jarumi ne  ko a felin  wasa
Yace "yanzu baza ki hakura ki kara min lokaci ko da gobe bane.
Tace "ina my star ai da zafi zafi ake dukan karfe amma alfar man da zan nema awajen ka ban yarda da taba ko ina ajikin ta ba kai de kawai kayi aikin da ya kama ta dan idan ba dole ba ba abin da zai sa nayar da da kasan cewar ka da wata.
Yace "tom ina jiran ki naji ta ina za afara dan ni ban san  yan da za ayi ba
Tace "kamar yaya baka sani ba inajin kai da bakin ka kasha  gayamin bani bace maccen  da kata ba kasan cewa kane mi mata kafin muyi aure ko?
Yace "yess
Tace "mekake son na gwada maka yace "kar ki hada sauran matan ta na kasan ce dasu da wannan mujiyar  balle kekan ki.
Dariya tayi tace "nasani shiya sa na hada ka da wanda nasan baza ka taba son ta ba ko da amafarki ne shi yasa kishin ta yakasa yawa akai na dan nasan ba ta isa ba amma duk da haka bazan ce,
Ba na kishin ta ba wllh daure wa kawai nake dan nasan wannan ne ka dai
*DAMA TA*
Yace *DAMAR* ki *DAMAR* ki shi ka dai kika sani ni ba kya ga  zan cutu
"tace bawani cutuwa biyan bukata ne fa ina wanda suke tarai ya da mahaukata  ma dan biyan  wani buka tan su ina wan da suke yi da gawa dan biyan  buka tan su kai har da masu yi da  dabba ma balle kai naka mutum ce wan da za ku hadu ta tsarkekkiyar  hanya wato ansha  fa muku fahtiya  haka tayi ta yaudaran sa har ta shawo kan sa aiko ya rungumeta  gam da kyar ta samu ta ban bare ta fita tana boye hawayen da yake shirin zubo mata dan tasan idan ta bari Nabil yaga hawayen bazai taba barin ta ba ita ko ta kwallafa  rai akan cikan  burin ta haka tana ji tana gani tabar mijin ta da tafi komai so da wata tafi to da gudu ta sauka ta haye nasu saman,
Ta fada gado ta saki  wani irin kuka anya kafin yarinyar nan ta samu ciki kishin. Bazai illata ta  ba.
Ita ko Fandau tana tsaye ta naga ikon Allah dan ita ta ma dena mamakin  duniya  wai muhammed ne yake  kiran tada  mujiya  da dukkan ba kaken magan ganun nan tace lalle sakai yan iyayen ba abinda yakai shi muni  mama ina zan gan ki
Shima Nabil anasa ban garen haka yadin ga tuka da warwara 'azuciyar sa yace ko nabari nadan jima se nafi ta nace mata nayi naga ma amma da yatuna da wacece  Hadim wajen sa ido da binci  ke  gashi tace idan bai bi shawaran ta ba za ta barshi wanda hakan dai dai yake da salwan tar da rashiwan sa dan Hadim itace rayuwan sa
Gadan gadan  yatun  kari Fandau ba tare da ya tsaya wani kallon ta ba yaja towel din da yake dauke akirjin  ta tarike  gem muryar ta narawa  tafara magana
"muhammed  katuna asan da kafurta za ka aure ni sai da nace maka ka fa damin menene  manu fan ka akaina  dan na san ni ban kai wanda za kaso ba duk da lokacin ma baka furta kana sona ba amma nara sa dalilin da yasa ban gane ba kaddara ya makantar  dani amma wllh ko alokacin  naso na gane ba sona kake ba amma na dauka yana yin kane haka,
Dan Allah ka mai dani gun mama.
Ko saura ron  tabai yiba dan shi  ko kallon ta baya son yi da karfi yafisge  towel din aiko
Sai gashi yaci garo da cikakkun nonuwan  ta sayayyu  gyam  kamar zasu sole masa ido bai san lokacin da ya sake daga dara daran idon sa a kansu ba atake yaji  sandan girman sa ya harba kamar ya fasa wandon  sa da sauri ya hadiye wani irin yawu yaji yawuce kut  ita ko bata san ma yanayi ba dan kokarin  ta kare jikin ta,
Shiko cire
Wandon  kawai yacire yabar  rikan sa dan  bawani son hada jiki  yake son yida ita ba don  kyaman ta yake
 ya dauke nunfa shin sa dan ba ya son jin wannan warin  najikin  ta da yajin dazu ya haye gadon  da karfi ya fusgo ta ya kwan ta yabi ta suka fada tare amma me yana hada fatan jikin ta da nashi yajin  wani irin mazari na iban  sa ba inda baya rawa ajikin sa bai san san da ya fara shafa ta da sauri ba   wani irin abu yake jin ajikin sa wan da ya ma man ta dawa yake tare sai sha sha fata yake ya ra sa ma me zai yin hannun sa da yake son shafa lallau san  fatan ta zai biyawa bukata ko sandan girman  sa da yake son isa fada zai  biyewa

*ummmm Nabil dama ai bar rena allura karfe ne*

Sosai ya fita hai yacin sa sai kiran Hadim My one
Kema ta bamin  nan shafa min can kina jin dadin  ni shiiiiiiiiiiiiiii

Itako Fandau dan karewa tayi addua amma ta kasa yan zu wannan zun gureren  abin jikin  ta zai huda  ita kam tasa ni yau ranan mutuwan  ta ne bata nemi yafiyan  mama ba tana cikin wannan tuna nin  taji yana shirin  kaiwa  ga fadan gashi ga ba daya ya mata rumfa  yasaki  duk kan nau yin sa aruwan cikin ta ba da man ture shin dan ita ko hannun ta ta kasa da gawa
Wani irin azabeben  zafi taji ya karbi duk kan jijiyo yin jikin ta da karfi ta sakin wani raza nen nen kara da ya amsa duka  gidan
Haka Hadim ma tasa ki nata na kishi yanzu shike nan ta faru  ta kare Nabil din ta yaji dimin wata

amma me tunta na irga  mintuna  har ta kai ga awa cif ba ta ga Nabil ba ga ban ta yafadi ita Nabil bai taba cika mintuna 40 a kan ta ba amma gashi ita  wannan ihun ma tafi mintuna  40 din tana yinshin  kafin tajin shiru kuma,
Aiko baza to ta ganta a kofan dakin  amma ta ji tsoron abin da idon ta zai gani ta kasa shiga

Nabil kam jin sa yayin cikin wata duniya ai ki kawai yake ana isarwa  gan gan jikin sa sakon sa ya man ta da wanda yake tare tuna nin sa ma Hadim din sa ce ta kara zam zam dan duk a matan  da ya nema kafin yayin aure ba wacce ta kama kafar  Hadim shiya sa yake ganin kamar duk duniya baye ita
Ita ko Fandau tun tana cewa kaji tausa yina  ni yarinya ce waccece  Hadim niba  ita bace ban san ta ba ba haka sunanan  ba ni sunana Fandau karamar yarinya ce kabar ni haka
Ina ai be tsaya ya saura  taba   ton wazai jin wani shi ma nasa samba tun yake yana kiran my one kin jikin uwa yau kuwa kin canza shiiiiiiiiiiiiiiiiii

 Ita ko tun tana ji sama sama har ta dena jin ji jikin ta yasa ke nufashin  ta tun ta na iya fusgo shin har ya ga gare ta ta bari ya dauke
shiko Nabil sai can han kalin sa ya zo jikin sa ya tuno da wanda yaje tare da sauri ya mirgina gefe yana sauke nufa shin jan idon sa yayin yarufe ruf  dan baya son yabu
De yaga wannan kucakan  yarinyar  baka a wai da ita yayi wanna aikin ai ita ta bashi wannan farin ciki mase idon yayi dan kar yaga wanan kucakar  kusa  da shin yaka sa gaskan ta ajikin yarinyan na yaji wannan ni imar  kuwa shiru yayi yana saura ron  dukka kofofin gashin  jikin sa yan da suke wani bashi ni im taccen  ni ima na gan suwan  wan da bai ta bajin irin sa ba dukka jijiyo yin jikin  sa jiyayi  kaman ana musu bayi ajiyan  zuciya kawai yake  saukewa ido arufe
Ko ban ko kofar da Hadim tayi bai ji ba sai salatin  ta yaji  tana cewa
"shike nan  Nabil ka kashe yar mutane da sauri ya bude idon sa ita ko Hadim gadon ta haye ta rumguma  Fandau ta na jijjiga ta  tana "baiwar Allah kitashi karki mutu mana anan
Shiko Nabil ko motsi  kasa yi yayi kawai  jikin Fandau yake bida da kallo yan da jini ya ke fitowa kamar an yanka  karamin  damba ita ko Hadim gani ba wani mata kinda ya dau ka ya sa tashi da saurin ta kwantar  da Fandau tayi hanyan inda fridge ta dauko goran ruwa  mey sanyi ta yayya fa mata amma shiru  ta saki roban tace "katashi mu  wan ke mata jiki musan nayin ko ka mar soko haka ya tashi yasa kayan sa suka ciccibi  Fandau su kayi  bathroom  da ita suka sakar mata
Showr   kusan mintuna amma shiru haka suka sake kin kiman  ta zuwa falo suna zuwa suka kwantar  da ita a kujeya threesi tar  Hadim ta haura sama da sauri ta kira doctor muktar tace yazo gidan su. Suna da
Pashent doc yace "au  yau she kuka zo kasan baku ne meni ba se da ta ku ta maso ku yan ke masa maganan tayi  cikin sauri  tace doc  kayi sauri fa serious  ta kashi  wayan tafito hannun ta dauke da kayan  da za tasa wa Fandau
Ayan da tabar Nabil  ahaka ta same sa tace "nasan  ba mutuwa  tayi ba suma ne na kira doc muktar zai zo duba ta
What Nabil yafa da da karfi kin san wayen  muktar ko a familyn  zanna Modu kuwa  ba na cemi mi malamin da ya daura auren baban muktar bane kuma  abokin zanna baban wannan  yayin yar
Hadim  tace to sai me ai da tajen  gidan ma ba su gane  ta ba balle doctor ba zai ma gane ta ba
"waya gaya miki ai sani yace taru fe fuskan tane da sun gane  ta  amma shi muktar zai gane ta dan yafi sauran yan uwan sa zuwa gidan  zannah  kuma ke kan ki kinsa wannan abin scret  ne meya kai ki yan zu idan yace wa ya mata mezaki ce  ko kin man ta dansan da da likita ba a sirri dasu

*Ummmm*
*Ni de nace muje zuwa*
*Dan nema shawara ko karin ba yani*
*08062383027*
[3/12, 8:48 AM] Hauwa: *DAMA TA*






             *NA*

        *Batul Adam Jattko*

🌈KAINUWA  WRITERS ASSOCIATION🤝

     
*12*


 Yaci gaba da gaya mata magan ganu,
Mayaudaruyar   banza ki rasa wan da zaki yaudara  sai kan ki dan idan ba yaudaran ba abin da.
Zai sa ki dubi kamar ni kice zakiyi zaman zaure dani dan jin Hadim nake amma bana jin zan iya wani abu atare da ke.
Yana gama fadan haka yajuya yafice.
Hadim ta matso inda  take tace "haka mijina yake akwai shi da  tsan tsanin  baya son ka zami yan zu kin bari yaji warin  jikin ki zaki bata mana plan kawai
Bari na samo miki abin da zaki ci kiyi shirin tarban aikin da kiko  zoyi ayau
Dan sai nazo na miki wanka sosai ko zai iya kusan tarki
Matsalan ki kinbari yaji warin jikin ki
Ke sai kace ba.
Kanuri ba....
My one taji nabil da yake parlour ya kira ta.
Dasau rin ta juya ta fece  tana sorry my star tana fita yaja hannun ta suka fece  se da suka sauka tazare hannun ta tayi hanyan kitchen  "yace acici me kuma zakiyi a kitchen.
 Tace "abinci zan. kai mata.
Zaro ido yayi yace "kina da damuwa abincin ma ke zaki bata.
Tace "ba kayan
Abinci a part din ne kafin gobe akai mata a koya mata yanda zatayi amfani da komai na kitchen  din ba dole na kai mata ba.
Dunda zata mana aiki kai ma yaka mata kaci wani abu bawai ruwan tea
Ba dan yaka mata ace kaci wani abu me nauyi da zai kara maka karfi kai da zaka karbi    budurci yau
Da gaske ya hade rai yayi upstirs yahaye  sama.
Ita ma dariya tayi tawu ce
Ita ko Fandau har yanzu bata jin tunanin ta ya dai dai tu dan dan ita bata ta,
Bajin irin wannan abun ba 'me yake faruwa  dani ne wani bangare  na zuciyar ta yace sakai  yar mama
'wayyo  mama sakai  yar ki zai iya zama illah  ga rayuwa ta  kar ki rike ne mama na miki nesa da ganin yan da muka  kwana ajirki  nasan  nayi nesa dake mama   da nazo ne man gafa ranki  tuna wa da wannan wayan da tayi ne yasa tayi saurin sa  hunnu  cikin rigar  ta    tafito dashi  ta daddan na ba numbar  kowa sena Nabil da Sani  ba ta karbi na kowa da takar bi na anty mairo tasan zata kai wa mama suyi mgn nashi ga ukku ni Fatima meke faruwa  dani ne.
Jin ana takun afiya
Ta dago kai Hadim  ta gani dauke da faranti  ajiyewa  tayi  agaban ta tana kallon fuskan ta tace "kici abinci naga alama ko sallah bakiyi ba.

Cikin kuka Fandau  tace Dan Allah baiwar kuji  tausayi na kar cima  mummunan  mamu  far ku akai na.....
Dakata ke  Hadim ta   katse ta kar kiga ina bin ki a sannu mana kine mirai namin hankali mu muke d mummunan  manu fa a kan ki ko keki ka biwa kan ki mumunan  hanya  aikin banza....
Fandau ta katse ta tace dan Allah ki temaka min wlh kaddara ce.
Murmushi Hadim tayi tace muma kaddaran  ne ya samu hakan idan ba kaddara ba mezai sa ina tare da mijina nayi hanyan da zai kasan ce da wata  se dole,
Dan haka kibar bata bakin ki wajen roko na tun da kin san inta ka kaddara
Ga abinci nan kici yanzu zanje na zo da kayan wanka zan miki tana gama fada ta juya

 Wai dan Allah my one yaki keson  nayi  ne kina fa amfa ni da damar  da naba ki kina cutar dani.
Ita ma Hadim  cikin salon ta na yan da take shayo kan
Abin ta kwan tar da kan ta aka fadan
Sa  taware igiyan gaban rigan sa tana wasa d yalwataccec gashin kirjin sa tare d dan shafa masa lips din ta akirjin daya ke iya tsawon ta daker d tattage  take kaiwa  kirjin  sa tace
"Haba mana my star nasan na isa da kai ne ai na gode da *DAMA TA*  daka mabi   wan nan daman fa ita ce karshe dan Allah ka daure pls abu fijjirat  .
Yace "pls my sweety   muyi bacci kinsan fa gobe ina da zuwa club.
Tace "amma fa da goyon bayan ka da yardan ka aka yi kazo yan zu kace baka yar da ba.
"yace hakane amma ayan da kake nan bazan iya ba kiji tausayi na mana ni ko iya zuwa kusa da ita bazan iyaba balle na dauki wannan jikin nawa na hada da nata kibari de nan  da 2 weeks
Kafin nan ta dan yi dama dama ko
"zaro ido tayi 2 weeks
Yayi  yawa mu da muke son ayi ta ta kare.
Ahaka har ta shawo
Kan sa ya 'amin ce dan ba yan da ya iya dan shi kam kafin yayi aure yasan yayi harka da
Mata.
Amma turawane yawan cin su  amma  tunda yayi aure bai kusan ci wata ba,
Amma yau gashi Hadim din da yake kishin ta yake ta yata kare mutum cin sa ita ce me cewa  yaku san ci wata anya ko son da ta ke masa na gaske ne  kuwa ya,
Jawo ta yayi jikin sa da karfin ya man nata jikin sa yace "Hadim kina sona kuwa?
Tace "sosai makuwa  I LOVE YOU my star
Ai son kane ma yake sani komai.
Murmushi yayi ya dai dai ta lips din ta dana shi yace "ina fatan haka  ta kasan ce har abadan.
Tace "toh muje ko
Bai so ba haka yabi ta. Suka sauka suka  hau ban garen da suka  ajiye  Fandau
Ita ko a zauke inda suka barta  dan ko meke wa kasawa tayi  balle tane mi inda ban daki  yake ita  sallah   nema yafi da munta dan bata san makan  lokaci ba ida de tasan da rana suka shigo garin  amma nan inda take baza ka gane rana ko dare ba   takun   tana kin haka taji  takun su ko daga  kai bata yi ba  shi Nabil za ma yayi saman kuje ra baya son ko da' ga ido ya kalli inda Fandau take  Hadim ce ta ka raso inda take abakin gado kamar  anda  sa ta  taja hannun Fandau d karfin ta tayi han yan toilet da ita se da suka shiga ta daka mata tsawa tace "duk abin da na saki kiyi shi idan  ba  haka ba taci jen baki.
Tace "ki cire wannan tsamen  men  hijab   din naki da kayan ki shiga nan tanu na mata  warmin wanka  ita ko 'Fandau  tasa mu kan ta da bin umar nin ta dan  tsawan  da ta mata bana wasa bane amma se me
Tana  kara sa cire  kayan Hadim tayi  wani irin zare  ido cikin mamaki  take bin ko ina na yarinyar da kallo baki bude ya haka dan kiran jikin  ta yaru da ta ta ko ina  ta cika abin da yafi bata mamaki hef  din ta d ki'ran   jikin ta acike yake gyam.
Dan ta san koda wasa baza ta hada kan ta da wannan yarinyar  ba duk  d ita kullum tana cikin  shafa magun gunan  da zai kara musu gir ma amma wan nan  nata  baiwane
Ahan kali ta furta Allah sarkin  halitta ba afus ka  kadai ka ajiye kyu ba wannan, ita ce masu halittan  boyen  anya  ban yi gan gan ci ba.

Ita ko Fandau  sun kuyar da kai tayin  dan gani take ruwan da ta nuna mata idan ta shiga  hadiye  ta zaiyi.
"nace ki shiga ko haka ta daure tana dafe dafe ta shiga dan tsansin  wajen  yayi yawa da ta shi ga taji a she ma ba me zurfe  bane da bas ta zauna aciki  wani gu ta  ga Hadim ta  dan na  kawai se ga wani abu zungu rere  ya na ta dir je mata jiki  sai da aka dade anayi ta sake  kun na wani wajen ga ba daya  ruwan cikin ya tafi se ta sake ta rawa  se da ta mata wajen so 3 tukun  ta mek'a  mata towel  tace "fito tafe to dak'ar  tasa ke me ka mata  wani towel din tace kina  goge  kan ki suka  fito  shiko yana zaune  ko kallon ida suke bayayi  Hadim  tace "biyo ni tayi  wajen
Drssing mirror
Fandau ta bita
Hadim kar ban towel din  kan na ta tayi tace zauna  tanu na mata abin zama mai ta dauko ta lakuta  ta murza  hannun ta   ta fara shafawa  kafa dun
Fandau ai   Hadim dan karewa tayi  dan ita mamaki ne da yado ke na bethroom  din yaka mata jin ta daura hannun ta awani irin
Fata me uban laushi   wanna dun da take ba ta taba shafa skin mai laushi  irin sa ba  ai ba tasan  san da ta juyo da  fuskan Fandau yana nan da munin sa kamar yanda ita da Nabil suke fa da kallon ta ta tsaya yi   dan ta kasa yar   da itace  gani de Fandau din ce yasa   gaban ta wani  irin faduwa yanzu wannan  za ta hada  da mijin ta far gaban ta yakaru  san ta ta tuna  ko shoping  su kaje  da Nabil  yadin  ga tambaya kenan  wane mai ne yake  sa laushin fata    kenan yarinyar nan ta hada abubuwa da Nabil yafi so a rayuwan sa har guda ukku  yana mutu kar son  (hop) da cikekken  kirji   uwa uba laushin  fata   idan ko tabari Nabil  yaji wannan abubuwan to ta tabe  ita taga ma dan  ita
Macce mata ji wani iri da ganin halittan  tan Fandau  balle namiji
Amma wani irin san yi taji da ta tuno  ai Nabil  baya son  bakar  macce sai dago ka murmushi ta juya taci gaba da mulke  ta da mai


*Maso yan damata  kumin  afuwa dan zakuji shiru kwana 2 dalilin  rasuwa  da  a kama na*
[3/12, 8:48 AM] Hauwa: *DAMA TA*

            *NA*
 
   *Batul.   Adam*

🌈KAINUWA Writers Assciation🤝

 *14...*

Hadim ita ma cikin zafin rai tace "yaza kayi wa yar muta ne wrippin  kuma
Kace meyasa na ki ra doc to kana son ta mutu hannun mu ne.
Shima cikin mamaki da bacin rai yace " wripping faki kace
tace "abin da ka ai kata akan yarinyar nan yafi karfin ma  ripping
Yace tom zaki iyayin duk yan da kike so asan da kike so kamar yanda kika saba ban isa hana ki ba amma ki sani baki isa kisa ni nayi karya ba dan ban saba  ba muddin muktar ya buka ci waya yiwa yarinyan nan haka zan ce nine kuma mata ta ce na san halin doc sai kowa yaji ya.

Yana gama fadan haka yayi hanyan
Waje
Hadim tace Nabil a gaba na ni  Hadim kake kiran wata da matar ka  matar ka yajuyo ya kalle ta ya bude kofa yafice
ita ko Hadim tambayan kan ta dinga yi meyake  faruwa ne dani
'tunowa da tayi da yace idan doc yazo gidan nan ya tambaya zai fadi gaskiya tabbas haka ne Nabil baya karya baya gudun gaskya duk dacin  sa
Da sauri tafito tayi han yan man falo na gidan ta can za security nako fan dan  gudun kar doc yajo
Dan Hadim ta tsora ta daka kalaman  Nabil bai ta ba mata mgn me safin  haka ba sun sa ba a kullum shawaran su yana zuwa daya wanda ko da daya daga cikin su mai masa ba suna yin  hakurin dan newa kamar de yanda Nabil ya yar da auren Fandau
Ko mawa tayi daki ta same shi ya na safara  marwa  a dakin hannun sa goye a baya ita ma tsayawa tayi  a gefe ta na karan tan yana yin mijin nata ba ta taba ganin sa haka ba sai taji wani tsoron sa amma ta daure  ta bude bakin ta tace
"my star yanzu yaza muyi da ita?
Afusa ce yaju yo yace
"ni kuma me nawa wan nan tsarin ki ne ke ya shafa ai wan da yaci buzu  shi zai yi  aman  gashi da kin ta ba ne man shawara ta ke ki ka zubar ke za ki kwashe  na rasa kaddaran  da ya jani  zalin tan yariya kara ma kamar wannan kin sani na sa yarinya taguji  iyayen ta kin sa zata kalle ni  amatsayin mayaudarin  wanda yanzu na san suna 2 zan amsa awa jen ta wato mugu  kuma ma karya ce Haba Hadim nayi nadama abin da nayi wa yarinyar nan bana sam mani  ko Karima kanwa ta akayi wa jan ji dadi wllh ba dan bana son yarinyar nan ba dase na enta ta ta........
"dakata Nabil Hadim tayi saurin katse shi ya kake shirin daura lefi akai na ni kadai bayan kafini  lefi harka na cewa ba kaci buzu  ba baza kayin aman   gashi ba  kai ko ai kai ko kai ne babban mai lefin ni nace ka yiwa yar muta ne fata fata haka  lefi na ne da na yar da kai nawa ne ni daya dole kanu na min kure na ta hanyan nuna min halin ku na maza wan da an dade a naga ya min ba na yar da dan na amin ta da nawa ahe ba haka  ba ne Nabil ni zaka tozar  ta sai kuma ta fashen  da wani irin kuka
Abin ka da zuciyar  masoyi  sai yaji wani tausayin ta ya kama shi a hankali ya ta ka inda take ya jawo ta jikin sa yace "pls mana my one ni nace miki ni ba naki bane ni nakine  har ga ban abadan kuma me ya  kawo na maganan halin maza  anan abin da kike sofa nayi  dan sonki da kwan ciyar hankalin ki  duk da nidin bana so amma da abin ya kwabe  kike kira zan kashe yar mutane na mata f'ede  shine ya bani  haushin  har yanzu Nabil naki ne ina fatan haka ta kasan ce har karshen rayuwar mu my  one kece araina.
Sake makalkale shi  tayi tace "bayan  yan zu a nan kace ba dan baka son ta ba da ka enta ta a ga bana kake kiran enta  wata macce  kenan can gaba zaka iya samun wan da kake so ko?
Dariya yayi yace "kar kisa wannan aran ki....
K'arar  wayan Hadim ne ya katse ta da gawa yi takara a kune daga can ban garen yace "to sara kan rashin yar da nazo amma kuwani canza security sai ku za kubu de min gani nazo
Hadim tace ayya doc sorry  dama kawai muna son ganin kane yasa nace haka dan nasan za kafi zuwa dawuri sai de sorry fita ya same mu na gaggawa yanzu haka ba ma gidan
amma idan muka dawo zamu  biya  ta washen  ku ka gaida  Habiba d dee
tsaki  doc muktar yayi yace ya muku kyu shegu biyu wake da shinkafa
Dariya Hadim tayi  tace "sorry yayana doc kashe wayan yayi
Hadim tace "tom yanzu  ya zamu yi da wannan  yarinyar ne?
Nisawa yayi yace "ba suma ta yiba  ki zuba mata ruwa acikin kunnen ta kina daddan na kirjin  ta zata far fado.
Tace "tom muje muyi mata
Yace "salllah  sanyi azahar  tayi
tace "tom idan kuma ba ta far fado bafa
Yace !yasalam dan
Allah jeki  tashi tashi ta na masa dariyan jin dadin rashin nuna kulawan sa ga Fandau
Shikam tana fita ya zame ya kwanta a hankali yana jin wani bakon al amari  ajikin sa idon sa ya rufe yana murmushin  da bai san dalili ba bai ta bajin gamsuwa  a jikin macce kamar haka ba wanna yarinyar  da ya gama  renawa hankali ce ta bashi wannan faren cikin,
Bude idon sa yayi da sauri tuno wa da yayi da maganan wasu abokan sa ranan da al ameen  yayi ya kawo amarriya sa bayan sati da suka kai masa ziyara a nan london sai da suka fito Nabil ya tabe  baki yace shi kuma
 Elman  duk fafan  sa anan yaga ma "kaman yaya? suka ka tambaye shi
Yace "bakuga  matar tasa ma wllh  bata dace  dashi ba  yanzu dama dan wannan mu kaje  har niger yanzu shi ko kunyan kawo ta Englang  bai yiba ai auren irin wadan nan a saran sadaki ne  Amjad yayi murmushi yace  a "wajen ka ba dan ba ka taba harka da bakar bace ba sai farare ai Elman  shege ne ya san kan mata usman "yace wlh kuwa ai Shid  bai san mata ba sai turawa da yasa mu Hadim sai ita ai idan kana son more sadaki ka auri  bakar mace ni ba gashi ina da farar ina da bakar ba amma wllh ko gaba zan kara da baka zan kara dan ni  baka ta min ko mai.
Amjad yace kaskiya kam baka ji kirarin  da ahamed yake yiwa mata ba farar  macce lantarkin gida
bakar macce  aljannan maza,
Usman ya dafa kafadan Nabil yace "yaro yi mata biyu yanda hadim take tas samu baka ka jefa acikin za kasa mu kon ciyar hankali kaga wannan ake kira da matar  dare da kuma matar rana da rana ka kalle fara ka more da daddare  ka sauke  gajiyan  kallon akan baka
Amjad "yace kai ma kasan  mayen  Hadim ba zai iya ba
Amma kabar
harka mu sammman ka samu yar hilah
Dan haushi awan nan lokacin ko kallon su bai yiba yashige mota
Sai yanzu magan ganun  su yake masa yawo
Musamman abin  da ya kasa fassarawa  wato
*Bakar macce aljannan maza farar  macce lantarkin gida*
*dakuma*
*Matar dare da matar rana*
 Sake kwanciya  yayi yana rufe idon sa sai suran Fandau yana masa zizau  musamman sayayyun  na shanun  ta wanda kamar zasu tsole  masa ido bawan nan yafi bashi mamaki  ba laushi irin na skin din ta shi a tunanin sa duk bakin mutum gausin fata ne dashi,
fari yafi laushi kamar yanda  yake gani a ido  haka yadin ga tuno a bubuwan  ta aran sa yana rufe ido ya gan ta murmushi yayi yana mekewa  zauke  yana tuhuman  gangan  jikin sa da yayi sauren  karban  abin da bai dace da shiba  amma me tunowa da yayi ranan da ya fara cin karo da ita da wannan shigan nata na hauka kafan ta duk kaushi  takalmin a tsinke shijb  a yage yaci uban daud'a  rugume da  allon  ta wannan yalon  hakoran nata  me fidda wani irin  hamanin  warin  ya tuno yasa ke tuna yanda ya kasan ce da ita a d'azu  ai bai  san sanda yayi  wani irin yunkurin  amai ba yayi han yan bathroom da sauri
Allah sarki Hadim mota me halin siya da na kirki  duk yanda Nabil ya gwa da mata shi tayi aiko se taga  nufashin  ta ya fara da wowa da gudu tayi hanyan fridge ta dauko ruwa me sanyi sosai  ta kwara mata ai sai gashi nan taja nufashi  da karfin a hanlali  ta fara tude
Idon ta amma dishi  dishi  take gani ta fara wurwur ga ido nan da nan ta tuno da meya faru da ita  wani irin kuka ta saka  ko saura ron Hadim din da take  ta jera mata sannu bata yi ba taci gaba da kuman  ta Hadim tace  ki tashi na kai ki ban dakin kishiga ruwan dimin  zaki ji dadin ta juyo ta kalle Hadim tace  "dan Allah kicewa  mijin ki ya kaini  wajen mama ta na san bazan de na cin karo da a zaban
Duniya ba se  mama ta taya femin   
Hadim se kuma ta jin tana  tausayin  yarinya tace za a kai  ki kuma kin de  na kuka a gidan na dan  bamu kawo ki dan mu din ga saki kuka  ba a zaba na yau  ne  yan idan kin warke shi kenan ko so goma za amiki baza kiji komai ba haka  ko wacce mace take ji a daren da ta kasan ce da namiji za ki ware kinji.
Fandau tace mijin  ki baya sona yace zai temaka min amma wannan shine te mako yanzu meye ma tsayi na a wajen sa mata ko karuwa idan na koma gidan me zan ce ina zance na je tuda ya yaudare ni da idan  mukayi shekara zai kai ni na nemi yafiyar  iyayena  ya kai mama ta kasar waje a bude mata  ido gashi kunce idan na haifa muku yara zan koma  kuji tausa yina ku kai ni idan na koma dakai na bansan yazan yiba zan  fukanci  gori da habaici  a wajen  mutane gidan mu wanda  nasan  yanzu ma na bar mama da Bagana  akai.
Hadim kallon ta tayin  ta fashe  da dariya tace "to ne  mezan ce miki ne  tambayan naki yayi  yawa
Nafar ko kin ce miji na baya sonki  da me matsayin ki agun sa matsayin ki kin zo yimana aiki ko ba  dazun  nan yace  kar ki kara magana dashi se  da ni idan kina da  matsayin ma se de a wajena amma ba wajen mijina ba ya taba cewa yana  sonki ne ?
Na biyu kince ya yaudare ki ba yauda ra bane kaddara ne  ya haumu  mgnn budewa  maman ki ido kuma
Koni  nasan  da baran  da zan yi ina  nan dinnan  nasa akai ta wajen a bude  ba ta ido amma na miki alkawarin sai san  da kika samu  ciki wannan  alkawarin  nane 
Maganan  gori kuma su  yan gidan naku basu  san  kaddara ba to kice saceki  a kayi
Kuka Fandau  ta fashe  da she.
Hadim tace " kinga  kuka ba shi zai miki magani ba ki tashi muje  na gasa  miki ciwon  ki  ko ki rube wllh Fandau tayun kura  ta tashin  da kyar  amma tsayu wan ma gagaran  ta yayi
*Ummmm  akai dabi  a page mezuwa*
*08062383027*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA     TA* 
     

             *NA*

   
  *Batul  Adam jattko*

*Zainab Ahamed*
*Aunty zee* 🤝
*DAMA TA grp*
*Muna tare*

*Grp namu  kainuwa *naga comment din *na kuma gode d sosar ku*

🌈Kainuwa writers
Association🤝

      *15*
 Itako Hadim ta tsaya kallon ta ga kishi wai mijin ta ne yayiwa wannan haka
Itako Fandau sai ciccije  baki take na azaba  tsayuwa ya gagare ta tafiyan ma ko yunkurin daga kafan,
Ya gagara zufa sai zubo ma  ta yake
Ga hawaye ba ta san adadin  da ta zubar ba cikin da shewar  murya tace "dan Allah aunty ki temaka min ban ban zan iya tafiya ba.
Hadim ta tsakalo  kafadun ta tace "tom kema ki daure kina takawa Fandau tarike Hadim sosai suka fara takawa ahankalin  Hadim take binda dan tasan a yanayin yanda  ta gaban yarinyar ai tayi ma kokari a haka har suka karasa bathroom a hankali ta zaunar  da ita akan wani dan dakali  ta hada mata ruwan zafi ta sa gishiri  kadan  ta temaka mata ta shiga wani a zaban zafi taji ya ratsata  tasaki wani k'ara ta sake ke kenkeme  Hadim za ta fito  Hadim ta danne ta dakarfi a haka ruwan yadin ga ra'sata  har ya huce  Hadim ta sake sakin  wani ruwan shima seda ya huce  tana ciki sai da tama ta wajen sau ukku  tukun ta mata wanka sosai ta temaka mata ta fito  tace "kawai kiyi niyar alwalan ma lokacin sallahn ahzzahar  yayi gyada mata kai Fandau tayi dan taji dadin a binda  ta mata gashi har radadin  ya ragu  ta kama ta suka fito whadrop   Hadim ta bude ta dauko mata wani dogon riga ta sa mata ta zaunar  da ita tace "
'zauna na dauko miki shijab a wancan dakin ta fita sai gata da shijab a hannun ta tace
"zaki iyayin sallahn a tsaye kuwa ta kyada mata kai za ta iya tace "tom yi zan samo miki a binda  zakin dan sa a cikin ki ko
ita ko Fandau da kyar tayi sallah
ta daga hannu tana rokon  Allah ya yafe mata ya kuma sawa maman ta hakuri da jiriyan  kuncin  rashin ta da gorin yan gidan su
har Hadim ta shigo da faranti  ta ajiye tace "kisamu kici a binci  ko kifara  shan ruwan Tea din dan cikin ki ya ware  " "tom tace dan ta fara ganin girman Hadim ta fiye mata mugu mahammed
Hadim ta juya  ta fita
Shigan ta dakin yayi dai dai da lokacin da
Nabil ya shiga tollet da gudu ita ma da gudun tabi bayan sa tana tambayan sa lafiya yunkurin  a mai yake amma yaki fitowa tarike shi tana cewa lfy my star
Harara ya galla mata yace "duk bake kika jaba
Zaro ido tayi tace taja me?
Yace "sai da nace miki kibar yarinyar nan tadan yi kwana 2  tana wanka da dan yi dama dama kika nace gashi kin jamin matsala ban da hamamin  ta ba abin da nake ji inaga nima sai doctor ya duba ni
Dariya tayi "tace haba my star kana tufin  baka ji wani abu ba?
Hararan  ta yasake yi yace "naji a bukamar  ya?
Tace "ina nufin dadi da ka sance da ita
Ya ya musa fuska kamar gaske yace "idan kina son naci abinci yan kide na min maganan nan
_Hadim baki harku ne ita a dole mijin ta ita kada yake jin dadin_
Amma a file tace
"kai my star kafa di gaskiya ka san fa hausa wa sunce  tuwon kwalama yafi dadi.
Tsaki yayi ya fara alwalan
"tace meka tsaya yine baka yi sallah ba haryan zu.
-'-azuciyar sa yace gan gan jiki nane ya tsaya yaudaran ban za-
Afili kuma
Yace "wllh tsantsa nin jiki nane ya hana ni shi gowa bathroom din ma
Tazaro ido tace "kenan wankan ma bakayi ba?
Cak ya tsaya dan sai asan nan maya tuno da wanka ya haukan sa sai da ya daga rigan sa zai cire yaci karo da jini ai da saurin ya saki riga  ya tsayan  kallon ta wai shi a dole yana tsantsa nin jinin
*Kuji dan renin H*
 Sai ita tazo ta cire masa zata jefa cikin  dusebeen  din da suke tara kayan dauda yace "karki hada min wannan da kayane dan na gama da shi ba zan kara sa shiba
Tace to abin har ya kai haka to jikin kafa ta fada tana masa dariya
Wani kwali  ya raruma  zai jefe ta dashi da gudu ta kauce ta fice a toilet din.
Fandau ruwan Tea din ta fara sha kamar yan da Hadim ta gaya mata amma haka take kurban  sa kamar magani ta bude filet fin fer fesun kifi ne da na kayan ciki da ker ta samu na kifin yashi ga ta ja gefe ta kwanta a nan katsa.
Su ko Nabil yayi 
Da dare yayi sun gama shirin kwan ciya Hadim tace "ya kama ta fa muje mudubo yarinyar nan na ga kai ko a
jikin ka wllh tana jin jiki amma da zu na bata magani sannan ta fara ta kawa.
Yace "au da bata takawa ne?
Haushi Hadim taji tace  ban sani ba.
Shiko ya juya ya kwanta yace karki sani kin ji.
Tace to taso
Yace "keda kika ga zaki iya kika daurawa kan ki ina ganin kokarin ki ni ba inda zani.
"Shikena  tace taju ya tafita
Bata jima ba ta dawo ta haye gado
Taja bedside lame ta kwanta a tunanin Nabil yayi bacci  amma shi ko likkimo yayi yana saura ron  mayaudarin  wato gangan  jikin sa da yake kaya ta masa wani a binda zuci yar ya bai yar da da shi ba  maganan Hadim na dazo ya tuno wato *tuwon kwalama yafi dadi*
Toko de hakan ne  amma shime Hadim  ai bashi da haushin maccen kirki balle wancen amma se gashi yana rufe idon sa zai ce karo da ma zaunan yarinyar  wato heeps din ta   jiya ke kamar yanzu   take gaban sa jiyayi sandan girman sa yayi wani irin mekewa  bai san san da yaja Hadim da sauri ya runguma ba ya manta jikin sa sosai kamar za akwaceta  wani masifefen kissng  ya ke aikawa  duk inda yasan zai samu sanyi a jikin ta  amma yara sa meyasa bai ji kamar wancen yarinyar ba
   yabari  ya isa  babban fada nan made bai kai yan da yaji ba a can  ba sai ya fara sunba tun  taba min na matsamin  nan jijjiga min nan.can
Ita ko Hadim abi na mijin na ta yaba ta tsoron ko de aljanu ne suka shiga jikin sa kai ashe ba ban za ba yayi wa yar muta ne fata fata dan gashi ida kan ta yau ta najin  canji  ga sandan girman  a fada amma yana kara meke wa ita kanta ya gama kureta har a bin ya fara da munta   kawai sai ta fara tofa masa addu a  shi ko yan zu ya ga ma yar  da  dacewa towon kwalama  yafi dadin dan ha da yadan ji gansuwa   kadan ya mirgina gefe ya kwan ta lamo ita ma Hadim a jiyan zuciya ta din ga saukewa  na gamsuwa  dan ita a bin ya mata dai dai yau shiko yara sa yan da zai yin yayi yaji shi a yana nin d'azu  ka wai sai ya sungumin Hadim
Yayi bathroom da ita nan ma se da ya bata lokacin a bathtub ya naja gwalgwalata  ya gaji suka yi wankan suka fito
Abu kamar wasa da ker  Nabil ya samu ya rinsa ga shi da safe  yana da zuwa campus suna da  wasa me zafi wanda  a goben zasun  fara gashi  shene numbar 12  amma bai samu hutu ba yanzu.
Kulle idon sa yayi  gem yaja Hadim jikin sa.

Ita ko Fandau da ta danji  dama dama tana  iya tafiya kawai se tashi take ne man han yan se rewa koda wajen ne ta samu ta fita goza ta samu ta gudu sai da ta wuce falo biyu  amma ba ta gan ta awajen ba babba kofan da take tsammanin  tanan suka shigo da sani taje bata ga mamurda  ajikin  kofan ba amma hakan ta dafa kofa  wai ko zai bude  wani abu tajin ya jata yayi sama da ita ya naka ta a kar  wayyo Fandau da ma bata warke ba gashi wani ciwon ya karu ta kasa daga ko da dan yatsan ta dan ta bugu jin hannun ta take kamar ba a jikin ta ba se num fashi take mayar wa taji kofan ya bude Hadim ce tashi go tana murmushi  tace "Alhamdulilah  sauki ya samu tunda har kika samu   daman zuwa nan ban sani ba ko yunkurin  guduwa kike amma me zai kawo ki har na,
To saya kiji idan  ma yunkurin guduwa kike kin  tafka kuskure  dan  bata yan da zakiyi ki fita a nan banga ren  ban garen kine anan zaki yi rayuwan kin har ki gama aikin da ya kawo ki  dan ya isheki falon ukku dakuna  shidda ga kitchen buyi  a gwai komai da zaki buka ta a kitchen dama wai so nake ki dan  warware  na nuna miko mai yanda zaki shi amfani  da shi dan bazan juri kawo miki  abinci ba  nima nawa da '''fawa ake a bani naci amma ke dolen ki kida fa wanda zakici  dan kaf ma aikatan gidan nan bawan da yasan dake dan iyakar kin nan idan ki kayi yunkurin  fita ke ko labulen  gidan ki kayi yunkurin tafawa dan ki leka waje to wllh shocking ne zai jakin  dan bama son koda leka,
Wajene kiyin  dan ma kar wani yagan ki  idan  baki jiba wan nan faduwan  daki kayi kadan ne dan  duk ban  garen nan mun masa  wireng na shcking   kuma ma kasan shi yana waje idan zamu shiga mu kashe idan zamu fita mukun   na idan kina son ki zauna lefiya ki kiyaye  kisan ce wa abin ba na wasa bane,
Kitash mujen na nuna miki yan da zakiyi  amfan da kayan  kitchen
Fandau  da a kwan ce har yanzu kanta  yana juyawa  dan ba kara min ja shocking din ya mata ba da  ker ta tashin  ta na dafa  kugun  ta inda ya bugu
Hadim tayin gaba ita kuma ta bita a baya suka  shiga kitchen takai ta  ta nuna  mata  komai  na amfani  tace
"amma sai gobe zakifara  amfani dan na ga kamar  bakin gama gane waba  da yamma  idan mun dako zan sake zuwa na koya mikin  bari na kawon mikin abincin da zai  kai  kin  yamman.
Tana kawo wanan  ta juya ta bar
Fandau a wanen baki  bude.
Aban  garen  Nabil kuwa ba saukin  ko a club bai  ware ba 
a cikin dressing room bayan  yaga ma shi gansu na yan boll gaban rigan d bayan sa  an tubuta  SHID  sai  nombar sa 12 ya gama  yana  jin  abokan  sa suna  fita  a cikin room nasu amma shi yaka ma waje ya zauna
Amjad ne yaga ne bai fito ba gaShi har  oga ya ison  ana  shirin jerasun  da saurin  yako ma  yanufin  room na  Nabil me numbar 12 yayi knorking  amma shirun  ya tura ya shiga  zaune ya gashi kai dafe
  ido Amjad ya zaro yace "kai kuma  me haka?
Sai a sannan  Nabil ya dago da idanuwan sa da  suka can zan kala ya kalli Amjad yace
"har kagama
Amjad karasowa yayi  ya dafa kafadan Nabil yace  "Shid lfy
Nabil bayi mgn  baya kama  hannu Amjad  suka fiton ko  a file ma sai da ya ga abin zai  gai su ga jin kunya ya ware ya man ta  da batun abubuwan  Fandau ya fuskan ci a bin gaban sa
Amma Alhamdulilah  antashi kuma  sunyin  nasara yanda  suke so samu.

*Bayan kwana  7*

Fandau ta warke ras har ta saki ranta  sai de zaman ka dai ci da  tunanin maman  ta d kanwar ta  Hadim tana  shigowa so daya a rana amma banda Nabil  dan tunda abinnan  yafaru bata sake  sashin  a idon ta ba duk da hakan  tafiso dan wani mugun tsoron  sa takeji  tana dafawa kanta duk  abin  da taga zata iya ci.
Aban garen Nabil ko ko mai  karuwa yayin   gaba daya  ya gama tsanan gangan jikin  sa dan a ganin  sa shin yake  kawata masa
Abin da baya son
koda  tunowa har Hadim  ta gane yana  cikin  damuwa  idan  ta tambaye shi yace  shi  ba komai  to yanzu ma mgnn  yau dole sai  yajewa Fandau take masa
Yace "Hadim yau she zakin bar ni  nahuta  ne akan magann  yarinyar nan
Dariya tayi tace daurewa zakayi  wai rannan  da kayin meya ragu  ajikin ka balle yanzu  wllh tana wanka  baka  gan ta ba duk  ta canza  ba  kamar  daba  muje kaga ni
Nabil  azuciyar  sar  yace
' kece baki ga meya  canzan  bani nasa ni
Hannun sa ta kamo tace dan Allah muje  my star karka ce aa
Shima bai  san  sanda yabi ta ba dan  umarnin  gangan  jikin sa yake son bi  kowai
Akwance  suka samu Fandau tun kafin ta juyo kamshin turaren sa yasa narda  ita  dashin yau Hadim ta shigo wani masa nancin  tsoro ne da faduwan  gaba  yaziyar ci zuciyar  ta  tama  kasa da gowa Hadim ce  ta matso kusa  da ita  yawwa my star kaga tayi wankan tama fes  baiwar Allah yau fakina da ai kin ki  bada  shimma  kisa mu cikin dawurin dan maman kin ta samu lfy kema  ki samu  ki tafi dawurin.
Tama tsa kusa da Nabil tayi  tattage tayi  kissing din lips din shi shikuma har da lumshe ido na wai bayason rabuwa da ita da gudu takwace jikin ta fice shikuma  ya tsaya kawar  gunkin dan bai san  ta inda zai fara ba ita ko fandau tashin  tayi da gudu zata shiga  toilet aiga nen yan da heeps dinta  yake rawa cikin rigan baccin  bai san  sanda zuciyar sa ta yiwani  irin kawa tuwa da ita  ba  wannan  da da ma a cikin sa yake ai baisan san da yayi  wuf cikin zafin sana yan ball ya caf kota ba ya man na ta yayi jikin sa yasa ki ajiyan  zuciya
Jinta a jikin sa ka dai  ba kara min  ni ima  yaji  ba a hankali yasa  hannun  sa ya cire mata  rigan  ta ai  yana cinka go da  abin da yafiso na shanun ta bai  san san da ya rasa waye  shiba ita ma kawai tsintar kanta  tayi
A gado bakin maga na ma gagaran ta yayi se tayi shiru ta na saura ron karshen  ta shi ko gogan ba a magana
 Shafata yake  ta ko ina  duk jikin sa rawa yake ai nan da nan sai ga Nabil a fada  wani  irin  kara  ta sa a dai  dai lokacin  da ya gallah mata cizo a kan  nonuwa ta da ya ke ta faman sosa kamar  yasamu na uwar shi bai san ma tayi ba  a bin  ga ban sa kawai  yake yi jini  ne ya kefitowa a nonon  amma har jinin  yake hadawa yana tsosewa

 *Wai nikam da gudu nafita  dan ina *gudun  kar Nabil ya dawo hankalin  sa ya hada da ni mutu min da ganin  jini *yake  sashi amai balle yanzu kayin  abakin  sa musau *rari shukun  cin sa*
*08062383027*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA TA*


       

           *NA*

     *Batul  Adam* *Jatto*





     *Aunty Fauzah*
*_Ina meka godiya ta a garekin akan san cigaban DAMA TA_*
*_dake da duk kan yan kainuwa muna tare sosai_*🤝

*Gudun muwan ki gare ni babba ne*
 *Aunty sis*

*DAMA TA yana samun cigaba ne tare* *da jago  rorin Alkairi *Lwaton*
*Nuncy*
*Da huguma safiya*

*Yan DAMA TA*
*_Ina ganin comment din kukuma ina jin dadin soyyyar ku_*
*_HDZ na isar da  sakon gai suwan kin ga Fandau_*


*_🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATIN_*🤝

*16*


 Ita ko Fandau kukan ma ga garan ta yayi sai yar fa hannu take tana jujuya kai gogan kam sai da ya gama samun gam,suwa fiyen da yan da ya zata tukun nusuwa ya zo masa   amma da ga kan sa da zai yi da zuman  sauka mirror dake jikin gadon ya nuna masa jinin da yake gefen bakin sa juyowa yayin cikin mamakin yake bin jikin Fandau da kallo yau ma ciwon yaji mata  ne amma me yahada ciwon ta da bakin sa  ita ko Fandau ta shi tayi zaune tana duba kan  nonon ta in da gashi har shatin  hakorin  sa ya bai'yana ga zugi   sai asan nan Nabil ya gane inda abin ya faru ai bai san san da ya koma ya  zube ba a hankali ya sa hannun sa dai dai wajen ya kamo wajen ciwon ya zuba ido tab,basa  shatin hakorin  ne nawaye?


Ya tambaye kansa  take yabawa kan sa amsan  nashine  da sauri yasa ki nonon nata yace idan kika kus"kura mata, ta!ta gani za ki dauwa macikin kuncin rayuwa cikin tsawa yace  kidau rigan kin ki sa sannan kiwuce ban daki ki wan ke wajen dan ya sani idan Hadim ta gani zata ce meya kai sa tsosan  har ya cijeta dan bai manta da gar' gadin ta na kar ya ta ba kobai nata ba cikin dauriya  yake wannan maganan  da tunanin  dan zuciyar sa wani irin tashi ya ke karnin jiin har yanzu yana jin sa a mako koran sa  cikin saurin Fandau ta sa kayan ta tayi bathroom dan yanzu a duniya ba abin da take tsoron da ya wuce Nabin da Hadim dan basa mata ta dadi
Shima Nabil cikin sauri ya fice amma ina dai dai babban folo aman  da yake dan newa ya kufce da saurin Hadim da ta ke safada marwan dadewan Nabil a dakin Fandau ta juyo jin kakarin aman  da saurin ta karaso inda yake tana tambayan sa "lfy
 Sha ko kwa kulo aman yake har da na gaiyya   rigan sa yaja yana goge bakin sa da fashi Hadim tayi ta na ta jera masa sannu
Barin ta yayin a gun ya tashin ya haura saman su da saurin saurin yake taka mata kalan
Ita ma bin ba yan sa tayi se da suka ka karasa batdroom  bai tsayako ina ba se a toilel tabishi  suna shiga tace se da yayi brush yafi sau  3 Allah ya temake shi bai bari Hadim taga jinin bakin sa ba da ya san ta da bin gwa,gwaf da sai ta san dalili
Duk nacin tambayan ta baice mata komai  ba se yaci re kayan sa yayi wanka nan ma se da yayi wankan sosai san nan yayi na tsarkin ya fito fuska daure ta mau  irin a dole da gaske yayi abin  da ba yason nan wani rigan baccin ya ciro ya sa ya hau gado Hadim tace dan Allah my star ka ga ya min me yake damun ka tashi yayin saune  yace wlh Hadim kin kusa rasanin mudin  zaki din ga torani gun wannan  kazaman  kekan ki kinsan kina cuta  ta ina ni ina wannan me fuskar kamar bakin shanu ke ko kishina ma ba kyayi  da kan ki zakin dauke ni ki kai ni gun wata da sunan na sadu da kita gaskiya ina shakkar sonda kike min.
Idon Hadim ya ciciko da kwallah  hakama hannun Nabil ta hada da nata tace wllh Nabil ina son ka son da ba na sammanin  akwai wata maccen da take yi wa mijin ta dalilin sonda nake maka shi ya hana na bari lokacin da aka bamu ya cika dan na san inna zainabu baza ta taba fadan mgn ta canza ba nasan zata ne  nema maka mata kamar yanda tace ni kuma nasan bazan iya jurewa ba inga a na kiran wata da sunan matar  ka wllh kunya zan ji  a waje kawayena a ce kamar ni ina da kishiya kuma kai kasani rabin kawayena turawane basu san mata biyu ba haka zasu ce kade na sona bayan haka ni a karan kai na bazan iya jure zama da wata na din din din ba shi ya sa nake ganin wannan hanyan yafi sauki tunda nasan baza ka taba son yarinyar nan ba wannan dalilin ne ma yasa bana jin  kishin ta sosai,
Amma duk da haka kaga da kajima ba ka fito ba wllh kabar  a na tafasa min zuciya ta nake ji to wannan make nan ina ga cikekkiyar  macce wanda za ka iya son ta wllh Nabil
duk san da ka so wata bayan ni za a  yi daya babu cikin mu 3 koni ko ita ko kai ido ya zaro yace" kashenin  zakiyi
tace "bana fatan haka kamar yanda bana batan kaso wata bayan ni ina misal ta maka rashin yuwuwan  amin ne kawai
Yace "tom Allah ya rufa asiri  ni ba wannan a ra, ayi na  wannan makeci sila
Tace" ni jimawan da kayi na me na san de ba ga mawa ne bakayi ba me ka tsaya yine  ni kuma ina tsoron na shiga naga a binda zai ta da min hankali yasa ban shiga ba.
Kamar gaske
Yace "ayya da kin shiga ai wllh ko za ki tema kamin dan ina zau ne ne kawai ina jin kunyan jiki na   sabo da  duk warin jikin ta yaga ma ta damin zuciya  ko tashin na kasa
Yin.
Tace "wllh tsoron nake na shiga na gan ka a kan ta.
Ya mutsa fuska yayin yace kema fada kike har tana da wani abin da zan dade da ita haka wata banza ta ita.
Dariya Hadim tayi irin ta gama yar da da mijin ta din nan
Tace "ni ko kaga ranan da zaku fara haduwa da naga suran ta kajin tsoron da najin sabo da ta hada a bubuwan da kake so wajen guda 3
Heeps
Laushin fata
Cikakkun nonu wa

Tabe bakin yayin
Yace "ke daki
 kadamu  da ita ke ki kasan wannan ni kam ban ma kula ba duk wani a bu na macce idan ba ajikin ki yake ba to ne de a guna bashida wani amfa ni balle  wannan yarinyar da ni ko da ga kai bana yi ina kallon ta da idan da zan mata kallo biyu bazan iya wani a buda ita ba shi yasa ma nake rufe idona dan nacika burin ki ne kawai.
Hadim fadawa jikin Nabil ashi.
Dan murna dan taga mayar da da maganan sa dan Nabil baya mata karya da bakin sa yake gaya mata kafin ya aure ta shi mane min mata ne har yana yin su bai boye mata ba
Ya kuma yi mata ransuwa na bazai kara kusan tar wata macce ba
Akwai yar da me
 karfi tsakanin  Nabil da Hadin dan  tamkar turawa suke kodan a cikin su su ke oho.

Ita ko Fandau a  bathroom tana wanka tana kuka tausayin kan ta ban da wayyo mama ba a bin da take ambata  tasan  hakkin mama ne kawai yake da wai ni ya da ita mama kar ki kullace ni kwadayin lfyn ki ne yaje fani wannan halin da kon a fim ba taba gani ba  wlllh mama da farin ban yar da ba sai da yace zai ne ma miki lfy na amin ce wllh mama nasan kina fushin danin  shiya sa ko a mafarkin ki ki kaki yar da na ga fukan ki dan Allah mama ko a mafarkin ki fito nane mi yafiyan kin mama duk ko ranan da muka gamu duk   hukun cin da zaki yanke a kai na dauka.

Haka tayi ta sunba tu har tafito da alwalan ta ta fara nafila da yaza mo mata jiki yanzu  ta dar sallah ta dauki Qur ani  tana karan tawa dan bata da wani a bin ebe kewa idan ba shi din ba ko dan  tv din nan babu se agogo wanda dashi take duba lokaci sai fridge dan tvn ma da gan  gan suka fitar na bangaren  gaba dayan dan suna tsoron ta kun na anuno  Nabil dan kunsan yan ball a turai da rajan su yafi na sarkin

*Bayan kwanaki*
"Haba my star kai kullum idan nace kaje sai mun ja da kai na rasa sa me yake ra guwa ajikin ka ida   idan kasadu  da yarnyar nan ni ma na dauri na tura ka balle kai
Yamusa fuska yayi yace ai ni duk ranan da naje kare ta wahale ta ke bani haba macce kamar  dusa ba gardin ba ni ima in fa ban gawani amfanin ta ba wata  biyu bacikin ba alamun zata se bakar  aza da take bani ka wai mu sallame ta mune mi wani mafitan.
Yakarashe maganan yana jan tsaki kamar da gaske  nanko cikin zuciyar sa fal murna dan ya san yau zai bawa gangan jikin sa hakkin sa.
Tace "kadaure dan Allah kaga idan muka dace a irin wannan kwanakin  macce zatafin  samun ccikin kamar yanda doc yafa da ka ga ina irgawa yau kwanakin  ta 10 da gama period   idan a kayin dace cikin yana shiga awannan ranan
Haka tayi ta lalamin sa.
Shiko sai wani jan a jiya ke a file azuci ko Allah yake ma su tafin ita ko haka ta din ga lallamin sa
Har ya yar da suka
Fito
Ita ko Fandau tana idar da issha ta sa kayan bacce  amma taji bacci har ya ishe ta ba tada abokon  fira idan ta rasa abin yi haka za ta sa mudubi a kaba ta yin ta kallo kan ta ko ta yin ta magana ita daya ta na bawa kan ta amma  dan haka ta keta yin idan na dariya ne ta yi  idan na kuka ne ta yi idan da Bagana ne kanwar ta harwanin shan kunu ta ke da fada fa kamar yan take afile da ita idan mama ne se tayin ta tausasa murya tayin muryin mama tayi na ta tayi na Baganan  yau  ma tana kallon mirron  se taga gashin ta yayin wani caburbur kaman na mahaukaciya  dan ta manta  rabon kan da gyara dan ko ma taji bata da shi tun kitson da ta zon da shi da  ta tsefe ba ta samu wani ba tun tana tumke shi har yazo baya kamuwa  ta kyale shi
  dan Hadim da akai mayuka Akan  mirron tazo ta kwale tace ba zan barki ki kishafa man da zai karamikin laushin kashin ba dan mijina yana da son gashin  da laushin fata dan haka man ma fazan barin kishafa ba a jikin ki da kanki
Tana gani ta kashe ta fice ita de sai afkin ce mata tayi wanka ta wanke kanta sosai wan da ta hakan  mata san dan biyan buka tan kan su ne amma ko turare wannan ba ta barin ta ta shafa sai de tana bata cima me kyu dan acewar ta tajin a na cewa macce idan tana samun cima me
kyu zata fi samun ciki da wuri dan haka fatan jikin ta kadai za ka kallon kasan tana cin me kyu dan tayi mugun canzawa
Tana cikin haka ta ji motsin kofa cak ta meKe tsaye dan tasan zuwan iyanzu bana  kirki  ba ne dan ta san da Nabil hadim za ta shigo mata ai ko tunkafin  sukara sa shigowa kamshin turaren sa ya mata sallama
Abin sun kamar kullum sakale  da hannun juna Hadim cike da murmushi shi kuma fukan nan kaman ce yau za kaga izzara ilu
Cikin shigan su iri daya kaman yan da ta saba ganin sun sai de ban ban cin na sa na maza nata na mata suna da kyu da bata san waya fi wani ba ga gashin nan na ko wannen su ya sha gyara ko gashin Nabil ba za ta hada da na ta ba balle Hadim da ta ke ganin ta kamar ba indiya pink din riga ne a jikin sun da bakaken  wando.
Hadim tace
"kallo haka me allo ko manta mu kikayin
Dan haka suke kiran ta tunda sun ce sun manta sunan ta ita ko takin  gaya musu
Nabil yace "banaga yami  kiba wata kilah mayya ce ya juya ya kalli Fandau  yace "to wllh ko ciwon kai mukayi keza muka ma.....
Hadim ceta katse sa cikin bacin  rai tace aa ba mayya ba ce waye bai san zannah  Modu ba idan mayene ai da ansani kuma ma wanda za ta haifamin yaran kake kira da mayya
Yace "sorry madam ton kice mata tade na yawan kallo na
Yafa di haka a k'agau ce
 dan shin ya k'agu

 Hadim tafice ya kwashi gara.
Hadim tace "toke ina gar gadin ki da kide na kallar min miji dan kar maki sashi a ran kin

Itakon  Fandau yau ranta ya gama baci da kiran ta mayya duk da bata taba mai da musu  murtani  ba yau tayi  tace."bazan sashi arai naba  bana son sa ku fitar dani a gidan ku  kinji.
Ta juya
Ta kalli Nabil tace kai idan a na maganan maita ma ai kaine baban sun ka ke cemin mayya kai da kullum sai kalash min jikina idan ba maye ba wayen zai din ga lashe jikin mutum ko ba kai kata ba cizar min lebe naba naga gatabon  cizon  da kamin akan nono na kai da idan kana lashe mutum har gurna ni gake kamar  zaki kai ai kafin kura ma maita to idan ba babban maye ba waye zai dinga lashe gaban  mutun na ga har gabana kake lash......... Ai
Wani irin k'ara Hadim tai  tai kukan kura yayi kan.....

*_Tofa ko kanwa Hadim zatayi Nabil ko Fandau ni de na fita da gudu kar ariske ni_*

*Masoyan DaMA TA*
*_Duk naji kwarafin ko na ina mukun typing kullum ban ki ba amma ga shawara idan zan muku kullm to baza kusa mu da yawa ba inada zamuyin tsalaken kwan 1 -1 naba ku yan da na saban wan ne ku ka zaba_*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA TA*

           *NA*

     *Batul Adam Jattko*



🌈 *Kainuwa* *writers*
*Associatin*🤝



17....

       Fandau tadan kota cikin wani mahaukacin kishin da bacin rai  da ita kanta batasan ta inda yake fitowa ba ta fara dukan Fandau iya karfin ta
Tana cewa "kehar kin isa maccen da zaki hadani da mijina kina karamar yarinyar kidake waya koya mikin irin wannan bade mijina ba nayarda dashin ni kadai ce a ran mijina kuma ni zanci gaba da zama
Ba wata maccen da ta isa ya sota  kema mun auro kine dan cika burin mu da  gujewa  wata tashiga rayuwan mu mun tsarashi iya mu da yaran mu Allah bai yini zan haifi yaran ba shiyasa muka dauko ki ki haifa mana koda 2 sun ishemu  wannan ma ne na tsara ba mijina ba dande ba makaucewa umar nin junan mune ya yarda amma bawai dan yana ra ayiba koda maccen kirki ce wanda ta isa balle ke da kullum idan zan kawo shin nan sai da magiya da tur sasawa kuma duk sanda ya shigo dakin nan yafita to da amai zai fito sai nayin zaman jiyar sa ke har kin isa mijina mai mugun tsada ne a duniya mezai ji ajikin ki  dube ki kanki kamar danbun k'aran giya   zaginta take tana cegaba da durman ta
Itako sai
Ihu take tana neman ceto amma ina bame jinta dan


 shi Nabil din da
 yaka mata ya kwaceta  komawa yayi kan kujera ya daura daya kan daya yana jifan su da murmushin  dan da farkon ya tsorata a zaton sa Hadim zata yarda da Maganan Fandau sai abin yazo masa da sauki Fandau ta gama tsorata shi shiyasa yabari  a koya mata hankali saboda gaba
Sai da yaga aibin  zai wuce k'a ida ya tashi  ya karasa inda suke  ya kamo hannun
  Hadim yace "hama  my one ya zaki damar mun kan ki akan wannan wanda bata ma kai ba kawai idan zata shiga rayuwar mu mukore ta tunwuri ni sai yanzu ma na kare mata kallo kidu beta fa yanzu wannan abunce zata haifa mana yara ki ganta fa idan ta haifo mai kamar ta muce wata biyo cikin mu ne sai yanzu mana tunada wannan my one anya bamuyi kuskure ba.

Hadim da har lokacin tana huci  da bacin rai tace "wllh baza tabar gidan nan ba har se ta haifa mana idan muka barta  kana nufin taci bulus kenan duk moron jikin ka datayi ya tashi a bati
  kacire wani zata haifi irin ta aranka  mai kaman mu zata haifa aiko data haifi mekamar ta tama bai baci ba ai sai ace ya daukon  dangin baban sane ga suna  duk bakake ne

Nabil yace "kema kinsan duk bakin dangin mu sunfin wannan yanuna  Fandau

Itako Fandau tunda tasamu akade na dukan ta lamo tayi akasa  tana mai da nunfashi cikin azaba
Hadim tace "shegiya gobe makikara  wai kema kinji dadin namiji zaki nunawa mutane karuwan ciko  marar kunya dan kinga girman mijina ko
ta juya ta kamo hannun Nabil tace "my star zomu tafi tunda na yau de bazai sa muba
Nabil daya gama  shiga wani hali dan dan mugun shaawa wan yarinyar
Baye ma sanda ake dukan ta rigan ta yazame duk ilashirin  jikin ta yabai yana wani matsanan cin shaawan  yana fuzgan sa jiyake  kamar ya rungumo ta a gaban Hadim dinma
Taya zata ce yanzu sufita  bayan idan bai biyawa gangan jikin sa hakkin saba bazai iya bacci ba
Ai baisan sanda yafurta
"meyaza  bazai samu ba
Hadim dahar ta fara
Tafiya hannun sacikin nata taji ba tafiyan yake ba ta tsaya kallon sa sai kuma taji yayi mata wannan tambayan
Tace "my star naga ta bata maka raine  nasan baza ka iyayin wani abuba shine nace bazai yuwuba mu hakura.
'azuciyar sa yace na hakura da umar nin gangan jikina  impossible
Afile kuma ya rausayar da kai fukar sa yanuna damuwa yabita har sunje kofa yaji bazai iya jurewa ba ya tsaya cak
Yasauke ajiyan zuciya yace
"amma keki kace awan nan ranan idan akayi dace cikin zai zauna ko?
Tace "hakane my star.
Yace "dan me zaki ce bazai yuwuba?
Tace ganin macin randa ta janyo makane  fa yasa kai   dama yaya balle yau da ta maka wannan iskancin
Yahade fuska kamar gaske yace "to yazan yin bacin rai ai bazan dena shi ba har sai naga bata cikin yayuwan mu dan haka inde ana zaton  zata samu cikin yazan yi zan hakura nayi dan nasa muna huta idan Allah yasa aka dace

'Zaka rantse harzuci zan cen haka yake
 Hadim tace "yawwa  nawan ina sonka kana son farin ciki na
Shima cikin farin cikin cin nasara  ya rungumota jikin sa  sosai yace"
 I love you    itama matseshi tayi sosai a jikin ta tace I love  you too  my star shiko idon sa cikin na Fandau wani kallon zakin gane kuren ki yamata
Ita ko takan tama take dan haka takawar  da kanta  'azuceyar ta tana juya magan ganun su yau zata samu cikin  nashiga ukku  Allah kar ka tabbatar da maganan su dan ba abin data tsana irin tasamu cikin dasu
Har suka gama rungume rungumen sun Hadim tafita bata sani ba sai ganin mutum tayin atsugun ne a daf da ita ya zuba bata ido
Cikin wani shu umin murmushi da tasan ta mugun tane duk da bata taba ganin murmushin saba tasan bana arzikin  bane.
Ahankalin  yace "inafa tan kin shirya  tarban  mayye  dan a yau tukun zaki san kaman zaki nake zaki san nafi kura maita dan yau ina ga ba inda bazan ci ajikin ki ba
Kishirya
Tunda tazo bata ta
 yin dogon magana dashi  haka ba idan yashigo abin gaban sa kawai yakeyi yafice.
Daga yana yin muryar sama tagane yau ba sauki dan haka cikin tsora  daga kwancen take ja da baya shikuma daga sugunne yake binta yana cigaba dawannan murmushin nasa
Cikin rawan murya  ta fara magana dan Allah kayin hakuri wllh bazan ara ba kaji tausayin na wllh  ni yarinya ce
yace "ai tunda kinsan kura kin san zaki kin zan mayye  kin girma.
Na tuba wlh kakira anty ma zance karya nake......
Ganin zata bata masa lokaci ne yasa yadaka mata wani
Tsawa da bata san san da tameke cak ba
Taca  "wayyo  Allah kulum ka shigo sai kamin mugunta wllh ni bazan haifu da kuba Allah kamayar ni gun mamata
Cikin wani irin tsawa
Yace "zaki cire kayan kiko  saina  sake nin ka abin da nayi niyar yi   miki abin da nayi niya waya gaya miki ni nadamu na haifu dake kigaya wa wanda  ta keson  hakan.
Tace "mekake sodani  ita haihuwa kai kace  ba haifuwa ba to me kake so kasheni ko.
Tsawa yadaka mata wanda bata san data  fada gadon ba 
dakan sa yacire mata kayan jikin ta cikin gaggawa yake sarrafa ta wanda
 yau tabbatar wa  Fandau basauki gashi ko
Komotsin bata iyayi balle daman
 manture shima balle halin kwace kanta
Shiko Nabil a yau yayi abubuwan da  yasake tabbatar wa kansa yeees  Fandau macce  dan haka yayi jimawan da bai tabayin  irin saba yarasa meyasa yarinyar bata gunduran  sa dan bai ki yaka sance da ita ko yaushe ba  har   ya juya zai fita sake dawo wa bakin gadon  ya daura kafan sa daya   saman gadon daya a kasa ita kuma tana zaune tasun kuyar da kai ahankali yasa hannun sa saman caburer  ren gashin kanta da Hadim ta kira kamar dan bun karan giya  yadam ko gashin  da karfi tasaki kara tana yar fa hannu idon ta kamar zai fado
Murmushi yayin yace kalle ni ta dako   cikin tsoro da
azaba
Idon ta yafir  fito dan azaba  tana kallon sa
Shima idon ya zaro mata yace "dazafi ko
Dasauri ta gyada kai hawaye sai surto mata yake jijiyoyi  kanta sun fito tsabar azaba

Shiko yace "good
Gaba maki sake tona min sirrina   kece a wahale  dan matata bayar da zatayi ba.
Cikin in ina tace  "bah ba' bazan fada ba Allah wayyo kaina
Shiko murmushi yasake yi yace
"good
   amma dan mugunta sai da yasake matse kan yasake ta dakar fe ta fada kan filo
Tasake sakin kukan da bata san ranan  gamashi  ba
Nabil sai daya fito yaji gaban sa yayi mugun faduwa Dan yau bai san karyar da zai  yin yakare kan sa awajen Hadim ba yarasa meyasa idan yana tare da wannan mayyar  yarinyar yake manta komai ba tsaki yaja   yaci gaba da sauka ransa wassai  dan har yashi ya karyan  da zai kullah
kamar yanda yaza ta a babban falon ko yasa meta tana jiran sa  a tsaye tana wani jijjiga  jiki shima daure fuska yayi sosai dan ta yar da da plan din sa yasake jan tsaki yace "my one anya ba gidan marayun zamuje mudau ko ba kuwa ni nagaji da wannan abun gaskiya  dasuri ta juyo tace" tamaka wani abuko   yace "kin san ba na iya kusan tarta idan bata yi wanka ba balle yau da kika mata wannan dukan duk yawu da majiya ya bata kazamin jikin ta nace tawuce taje tayi wanka kawai sai tashiga taki  fitowa ni kuma da kwanciya  dayake agajiye nake bacci  yakwashe ni.

Hadim ajiyan zuciya  tayi tace "Alhamdulilah
Wllh nadau kama wani abin ta maka kana kula da kan kafa kar kaje kasaki jikin ta illata min kai dan ma ban babu wani makamin  da zai illata mutu aban garen
Yace "danwan nan karki ji komai ko maza 10 baza su illata miki ni ba

 dariya dayi tace "na yarda da jaruntan ka shiyasa nake Al  faharin dakai ko afilin wasa shiyasa nake kiran ka my star
Murmushi yayi yace "wllh ina sonki my wife
Nima haka my husband  ina fatan de tafito din ko idan bata fiton ba
Sai  inje in fito da ita ni nasan ba iyasa scurity  tayi ba

Bayan ya tabe baki
 yace " ai sai da na tashi abaccin nagan ta ita ma har tayi bacci
Hadim tace "bakayi ba kenan?
Yadan kalli fuskan Hadim sai yaji kunyar
face to face yace mata yayin amma daya ke dan duniya ne yadan sosa  keya  cikin basarwa yace "nayi
Itama sai da taji wani iri aranta amma Afili tace "Allah de yasa anda ce
Yace Ameen dan shi ma harga Allah yana son yaga Fandau ta gama aikinta ta tafi  idan baya ganin ta wata kila gan gan jikin sa zai dena kawatar masa da wannan yriy  kuma ma yana san ganin kwansa a duniya

*wani sabo*
Wani matsalan da Hadim tafara fuskan ta  Kwata kwata tarasa kan Nabil  bai fiye damuwa da ita ba sai yayin kwana 2 bai ce zaiyi wani abu da ita ba duk da dama ba wani damuwa yayi da abin ba akallah so dayan de za ayi a kullun  sai kuma yawan wasanni  da jikin da wanda ya mafiso  feye da.....
Amma yanzu wasan nin ba yarage tun abin baya damun  ta har yafara damun ta

Bayan sun shiga badroom yace shi sai yasa ke wanka tunda ya hada jiki da wannan kazaman  bazai goga bata daudan ta ba.
Tace "dariya tayi tace ni inban da abinka banga wani datti a jikin yarinyar ba ai tawan ke
Yace "yawwa my one yaza ayin da wannan kan nata ne?
Hadim ta kalle shi tace wane kan kuma?
Yace baki ga gashin taba duk yayi wani irin ko taza babu ga gar zaza dashi.
Ido Hadim ta zuba masa can
tace "me naka da gashin  ta koya shafi aikin kane?

Daga ka fadun sa yayi yace "kumafa  hakane bai shafa ba yana dauke da nishadi  yashi ge bathroom dan yasa mugansuwa sosai jinsa yake saka yau.
Har ya shiga yasake lekowa cikin happy yace" yau baza amin ba wanka.
Tace "wankan Allah nama ka ai.
Yace"au wannan na shedan ne?
Tace "kai de yikafito  nagaji ne.
Yace "ok bari nafito namiki tausa.
Tana jiran sa har yafito tana kallon sa yagama komai nashi ya haye ka gado  yaja  blanket
Yayi kwanciyar sa tare da janta  jikin sa ai kafin kaceme har bacce  yayin gaba da shi
Hadim tameke zaune ta zubawa  faskan  Nabil ido baccin  sa yake cikin kwanciyar hankali har wani nanuri nada ban fuskan sa yake fitarwa  take wani  mugun shaawa  ya kamata wanda baza ta iya jurewa ba
Shiko yanda ya kwanta dinnan sai kuma asuba  hannnu  tasa tafara shafe fuskan kasa  cikin bacce yaji abin da take masa ya bude idon sa cike da      bacci  ganin ta zaune yasa yasake janyota  yace
"My one muyi bacce  ko yana gama fadan hakan yaja idon sa yarufe rif
Hadim tayi mika tasake shiga jikin sa  dan gaskiya baza ta iya hakura ba dan jiya masai  data massa masa yayi dan wasanni  ajikin ta sama sama  amma yau ko hakan ma bai samuba  kawai sai ita tafara sarrafashi shiko Nabil dama bai koma ba kuma tunbude idon sa da yayi yagane metake so amma shi bai jizai iya ba  lif yayi yana jinta ita zuwa yanzu ita kanta tasan ya tashi amma tarasa meya yasa yaki yinkuri  dan haka ta kai bakin ta dai dai kunnen sa tace" yade?
Yagane amma yace "bakomai
Tace "ah ah da komai.
Yace"tom  kibari saida safe muyin bacci yayi maganan cikin mayen  bcc dan kafin ta bashi amma har wani bcc yasake kwasar sa

Allah sarki Hadim ahaka ta hakura tayi bcc batare da ta zarji wani abuba  dan a yanda take jinta macce har macce baza ta taba sammanin   Nabil zai bar ta danwata  Fandau ba haka ta shi baccen  cike  da mafarke ma mafarke.
ahakade  sukeyin  rayuwa har kwana kin period  din Fandau ya cika dan Hadim yada tarike kwanakin  ko nata bata rike ba dan yanzu watanni 3 kenan cif  da zuwan Fandau suma wata 3 ya rage musu  sharadin su yacika  Hadim sai farga ba take
Tashi ga dakin Fandau dai dai lokacin sallan  magaruba  samun Fandau tayi tayi dai dai akan kujera threesiter  da sauri Fandau ta sauke kafafuwan  ta cikin ladabi da tsoro dan tana mugun tsoron su  tace "anty ina yine?
Hadim tace "kina lfy kinyi sallah?
Fandau tasun  kuyar da kanta tayi shiru cikin fargaba  Hadim tasake cewa nace kinyi sallah girgirza mata kai Fandau  tayi  alaman a a
Hadim tace meyasa?
Fandau  tasake sun kurayar  da kai ta bude baki ahan  kali tace "yau banayi
Da sauri  Hadim taja baya cikin firgici  tace what
Saida tafirgita  fandau duk a watan can mata data zo tama ta wannan tambayan  tace bata sallah sai da taga Hadim ta sorata  amma bakamar nawan nan da kamar an aika mata sakon mutuwar uwa da uba ba
Cikin karaji Hadim tace dan

 
 08062383027
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: DAMA  TA


              NA


        Batul  Adam Jatto



🌈 *Kainuwa writers* *Association* 🤝

18


Hadim cukumo Fandau tayi tace ke dan uwar ki gayamin me yahane kin daukan cikin?
Fandau
'zuciyarta tace
_indan fisari kayan ragone to_ _kaza matayi man_
Afili kuma cikin kalan tausayin ta tace anty nima ban sani ba.  Cikata  tayi cikin bacin rai tace yin cikin  shine   zai baki daman  fita acikin wanna gidan dakuma  lfy yar uwar ki  idan   baki  samu cikin nanda watan nin da muke   soba wlh  zaki dauwama cikin kuncin rayuwa idan kin kiyar da mijina yabakin ciki wlh wllh kinga abin da mijina yake shigowa  yayi dake to da kare zan hadaki yayi tayi dake harse yasa miki kanjamau ....

Fandau tace "nayiga ukku Anty dan Allah kiyi hakurin  ta zube gunwoyinta ta hada hannun ta tana ta rokon ta .
Dan ta taba ganin videos din kare yana saduwa da macce baturiya  a gidan uwar dakin ta anty mairo,
Kuma tabbas taji ana cewa ajikin kare  aka samu kanjamau  Tasan kuma Hadim zata iya yin hakan
Ai batasan san da tafurta afili Ya Allah kajikai na kabani cikin kar najawowa  mamata abin gori agari da yan gidan mu.
Hadim tace tode kinji   tayuya tabar Fandau awajen.

Nasu dakin ta haura  tasamu Nabil ya shirya cikin kayan  adidas akasan sunan sane da sunan asalin kayuyen su baban sa wato *damasak*    wan da dayawa mutane da damasak  ake kiran sa ful name
Muhammed Nabil Abubakar  damasak asalin inda yasamo
Sunan *shid* da kujaji abodan sasuna kiran sa kuma asali kakar sace uwar ummi sa take kiran sa *shitta* mezafi kenan dan Nabil tun yana yaron yake da zafin nama shine fa duk family suke ce masa shitta sai danwar sa zainab datake koyon baki take cemasa shid shine shid yabishi har Nabil yananeman yabata balle muhammd da dayawa nakusa dashi ma basu san shida shiba  shiya sa yake amma nida *shidmas* wato shid damasak  Nabil shid yana da mutu kar daukada a duniyar  wasan kollan kafa ball sana arsa yana mutukar kai masa dan shine na ukku ayan wasan da ake jidasu aduniya dan kafar sa yada da sada sosai  a yanzu haka yana zaune  da matar sa a gasan  England cikin london yana caccanza waje dan bashi da alkibula  a har kar  sanar sa inda akafi sayan sada sada nan yake amma yanzu yana tare da chelsea  dan sun iya ta fiya da shi  gidan sa yanan Bridge kusa da stadium din ma aka bashi gida kuma shine  12 dan haka suna jida shi sauran kungiya  kullum hari suke kawo masa amma chelsea suna fanshewa
Shiyasa yake tashen  kudi shida abokon  sa Bilal amma ra ayin su yanzu ya sha bamban shi Bilal kaifi dayane kungiya daya  garesa wato manchester united dan haka wajen zaman suma ya bamban  ta shi Bilal yana cikin England city 
Saide shida Bilal abotan yanzu yawuce  abota dan har  company  suka bude nasar rafa  kayan sawa har takalmi akayan sawa ajiki ba abin da company su basa yi.

Hadim gefen gado tazauna tasuba uban tagumi ta mirro ya hangota  yabar  tazan da yakeyiwa kansa ya dako  kusa da ita dur kusawa yayi bakin gadon yaka mo hannun ta yace " my one what is problem  idon ta taf da hawaye tace "my star kode wannan matsalan awajen kayake?
Yace "wane matsala kuma?
Tace"anya  ba dagare kabane kagafa  haryanzu yarinyar nan bata samu cikin ba.
Tsaki yaja yameke yana jan rigan as
Yace " kinada damuwa.
Tace "ya bazan damu ba gaskiya ina da damuwa inhar  watan nida aka iba suka cika bata re da wani mataki ba.
Nabil da shiba wannan ne a gaban saba damuwan sa yanda Fandau take sake kawatuwa a gangan jikin sa shiyasan irin dauri yar da yake yi idan abin ya matsoshi  amma afili yace "amma de kinsan ba  doc dinda yace inada matsala ko?
Tace "to idan baka da matsala ita wanna me yahana tasamu
 Cikin?
Gud  ga *DAMATA* yace  azuciyar sa
Dayake Nabil  namij ne kuma kunsa
Suba da ma akan abinda suke so duk  wayon da dabaran  Hadim  sai da Nabil ya ninkata abai bai,
Wajen cimma wani burin sa.
Yace "kinsan matsalan ne?
Tace "a a
Yace kintuno  da wani bayani da wani doc yata bayi mana nacewa yawan saduwa yana sawa a samu cikin dawuri sabo da yana sawa mahaifa tana bude wa muka bi shawaran sa mukayi da fama har kusan shekara muna fama damu kaga shiru muka wasar ko?
Gyada masa kai tayi alamun eh
Yace "tom mezai hana mu gwada akan wannan yarinyar ko za adace.
Yagama maganan yana kallon fuskan ta dan yagane yanda ta fassara zancen sa.
Allah sarkin Hadim da tagama yar da da mijin ta yana yayin komai dan farin cikin ta bata dauki zancen da wani manufa ba.

Murmushi tayi tace "ai nasa bayar da zakayi ba dan haka maban fara tunkaran kada wannan ba wanda duk bayan kwana 3 ma daya nake kai ka balle ace a rana zakayi so 2 kaban yanda doc yace.
_Shiru yayi dan a wancen lokacin mashi yakosa mayin yace wa _Hadim shiya gaji_
Yanzu kuma gashi _yasa mu wanda baya gajiya da ita saide da kunya yake ta idon Hadim yace zai iya dan kar tagano shi koda yake yasan idon ta  yagama rofewa  dane man d'ah kome yace zata yarda_
Yana cikin wannan tunanin yaji tace "to yanzu zaka iyayin haka?
ai tungafin yabata amsa yayi
_Hamdalah_
Azuciyar sa
Afili yace  yazan yi tunda burin my one ne
'dadi taji sokuwar
Saiga Nabil nan dumu dumu cikin irga  kwanakin da Fandau zata gama period danjiya ke kamar yaja kwanakin yakeji  duk da yana maleji  da Hadim yasan da banban ci yanzu ko yatabatar  dacewa akai matar rana akwai na dare kamar yanda su osyman  sukace

Aban garen Fandau ko bata da abinyi da yawuce yiwa Allah kirare ya kubutar da ita acikin wannan kangin ba abin da yake firgi  ta ta irin za a hada ta da kare
 Allah kamani cikin
Nan badan halina ba dan darajan fiyeyyen halittan ka
Aikin kena
har tadan rame dan fargaba
har tasamu tsarki
Nabil ranan kamar zai zubar da ruwa a kasa ya sha dan murna dan a irgen  sa yau tagama suna fitowa awanka suka gama duk shirin  da suka saba na kwanciya  har suka kanta baiji Hadim takawo masa maganan zuwa wajen Fandau ba mai makon hakama ita kanta take wa bukin  tsaf yagano ta dan haka yamata damara  ya tashi zaune ya jata jikin sa yana shafa cikinta zuwa maran ta yace "my one inason  samun da daka gareki  kena keso kibane da abin da mayafin  damuna idan natuna da wai nanda watan ni 3 inna zainabu zata  zata auro mana wata gawanan  sokuwar  takiyin  ciki ita ma.
Hadim tace "wlh nima abin da yafe damuna kenan  amma bari tagama period din shegiya  matsa mata zamuyin  mugani.
Nabil yasan  Hadim bata irga kwankin  ba gashi sai wani sakin  layi take  a wasan nin  da take dashin sama sama yake biye mata dan bayason  tazar  giwani abu dan haka ya hakura amma ina da bayan  sun gama har suje sunyi wanka suka sake kanciya  ita Hadim bata  dade ba bacce ya kwaheta amma banda Nabil da sai juyin  yake  yayi  tsaki afi cikin kwado ya kalli Hadim baccin ta kawai take tsaki yace duk keki kaja min wannan  matsalan  da bakin  hadani  da ita ba da hakan bai faruba  gashi kinja wowa rayuwata matsala matse idon sayayin  da karfe  ko bacce zai dauke shi amma ina kamar karawa kusan to da ita yake Fandau da suranta kawai yake gani  wani irin  abune yake  masa  yawo ajikin sa  wanda  jiyake  kamar  zai  ilatashi
Ahankali ya dauke hannun  Hadim a jikin sa  a hankali yake zame jikin  sa dana ta har Allah yabashi  ikon raba jikin nasu filo yajan yo ya maye mata  gurbin sa yalalla ba ya tashi yana taku ahankali har yasa mu yakara sa bakin kofan ahankali yabude  yafita yaja kofan  yarufe  cikin  sauri yake ta mata kalan  har yasauka  yahau  wanda zai   sada shi dana Fandau  yana shiga dakin  ma wani  sanyayyen  ajiya  zuciya yaja cikin zumudi  yake takawa har  yakara  sa gadon yaye bardon  data nade jikin  ta yayin rigan  dayake jikin  ta me nauyine dan yanayin garin  awai  sanyi ahankali ya zauna hannun sa yasa dai  dai fuskan ta yana shafa ta  ahan kali  gashi  de bawani  kyune  da itaba duk  da baza akirata maimuni  ba amma  fuskan yana sashin nishadi idan yana shafasu hannu  saya sauke  dai dai lips din ta masu  laushi da sansi shafasu yake  kamar  bazai  bari  ba lips dinsa  yakai  dai dai  idonta da suke  arufe yayi kissing din idon  nata  bai sammana ba yaji  bakin  sa  yafurta  yarinya kina da  kananan  kyu  masu  dauke  hankali
Ita ko kamar  a mafarkin  taji ana shafata tana  bude  idonta  tagan ta  a jikin  mutum ga wutan  dakin  mai duhune  na bacci
Dan haka  bata  san  sanda  tasakin  wani razanenen  kara ba  matse mata  bakin  yayin da hannun  sa yace "ke  karki  kawomin  hauka  anan  shirun  tayin  dan tasan  zai  iya mammarin  ta awannan daren  Nabil  yasamu  yanda yake  so har  da shiga bandakin  Fandau  yayin  wanka yafiton  dauke da towel amma sai  yaji   bazan iya  tafiya ba dan yana son kari anjima
 wani  zuciyar  yace  masa  kawai  kwanta anan  tunda  Hadim  batashi zatayin  ba sai  asuba  katafi  har  anjima  ka karan abin  ka kasamu Bonus marmushi yayin good
Tsawa ya dakawa Fandau  yace  "ki wuce kije kiyi  wanka  baza  kin kwanta min kina min  wari  ba danni  ba kwanciya da janaba  a tsarina  da saurin  ta tashin  tashi  hanyan  bathroom din  tana tunanin ta ta rayuwan kenan  a na amfanuwa  da  albarkatun  jikin ta  ana mata  wulakanci  hawayen  da suka surto mata tashare  ta  fara wankan  shiko  Nabil gadon yahaye  yayin  kwanciyar  sa jiyake duk gashin  jikin sa yana fiton  masa  dawani  ni im taccen  sanyin  ni ima  ai bai san sanda  yafara  burgima  akan  gagon  ba  yana  murmushin  da jin dadin  marar misal tuwa  bakin  sane  yaji yana furta  eyes eyes usman  matar daren  wllh  nayarda 
Da tafito  tagan  shin  cikin  wannan  halin turus  ta tsayan  kallon  san  amma  gudun  kar tayin  lefin  yasa  ta sunkuyar  da kanta  ta dena kallon  inda yake.

Shiko  yajima  cikin   wannan  halin  sannan  hankalin  sa yazo  jikinsa ya yatuna da inda yake  da saurin yaju yana cewa Allah de yasa bata fito ba
   atsugunne   yaganta   can  gefe   murtuke  fuska yayi  kamar bashi ba  cikin   tsawa yace  "ke kuma  mehaka dallah taso jiki na  rawa ta taso  amma  sai  ta tsayan  takasa  hawa  gadon  janyo ta  yayi cike da mugunta  ta  fado kansa  dai dai  lokacin  Hadim  ta fadon    dakin
Wani  ihu  tayin cikin  firgici   abin  tagane  idon  fazai   iya  gane mata  ba rufe  idon  tayin  tadafe kirjin  da daya hannun  daya  tana  nuna Nabil da Fandau Nabil da yaga ma dankarewa  awaje  ko ture  Fandau din  yakasa

Hadim nuna shi kawai take da yatssa  daker ta harshen ta ya iya burta  Nabil Nabil Nabil  tsugunnawa  tayin  dafe dakirjin  ta dan  kafafuwan  ta  kasa  daukan ta sukayi ita de  kawai Nabil Nabil kawai take  ambato sai tari kuma har  tarin  yahana  ta magana

08062383027
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA TA*



     
            *NA*


  *Batul  Adam Jattko*


*Ina kara godiya  ga masoyan DAMA TA*

*Yan duk kan group dinmu na kainuwa  ina meka godiya*🤝

*Dandalin  HAJIYA  Nafisa* *inajin dandin kasancewa  daku*

*Queen Teemah*
*Fandau ta amsa*





*19*



 🌈 *Kainuwa  writers*
*Association* 🤝

 Da karfi ya ture Fandau  a jjikin sa ya tashi da sauri yayi gun Hadim yana kiran sunan ta amma kafin ya sauka  a kan dan mata kalan  guda ukku  da gado yake kansa ya taka daya a na biyu yajisa tim ya bugu sosai dan sai da yadan kwanta a lamun yana jinjiki  sannan,
Ya tashin yana dafa kafan sa inda yabugu
Dakyar yake jan kafan sa ya karasa inda Hadim take kwance idon ta a rufe amma hawaye ne keta  faman surtowa a gaban ta ya tsugan ya tallahota  jikin sa yana jijjiga  ta  yace "my one kibude idon ki me  yasameki kike zubar da a bume medaraja  hawayen ki.
Nunfashi  taja bata bude idon ba tace "my star gaskiya idona yake nunamin  ka kashigo dakin yarinyar nan batare da izinena ba bansan zanyiwa  idona mugun gani bada ban zoba Nabil  macce   ce kwance a jikinka.

Nabil da yake tattaro  kalaman dazai  tsarata ya rasa ta inda zai bullowa al amarin duk girma da kiban Hadim cilak  ya dauke ta yayin hanyan waje da ita
nasu saman ya hauda ita a kan kujera ya zaunar da ita ya zauna a gefen ta yasa hannu ya jata
Jikin sa  kanta ya daura a cinyan sa yana shafa dogon gashin ta yana kallon yanda zuciyar  ta take bugawa amma har yanzu idon ta a rufen yake kuma bata dena zubarda  hawayen ba.
Pls my one bude min idonki ki gayamin me yafaru  dake bayan fetana  nasan kida saurin jin tsoro kamar ba shuwa ba kiduba yarinyar can duk girman bangaren can ita kadai take rayuwa amma ke dan fitan tan da nayi  shine kika kasa saida kika bine bayan nayi nayin dake bazan tafi ba kika nace saina tafi banso  ba natafi,
Kuma da kikaje me yasa bakiyin  knorking ba tunda kince ba kyason kiganta  kusa dani,
Hadim kam har yanzu idon ta a rufe yake dan batason  ta bude taga Fandau tafada kan mijin ta amma jin magan ganun Nabil da sauri ta bude idon ta tazuba masa ido,
Cikin sanyin murya
Tace "Nabil kana nufin ni da bakina nace kaje .  Shima cikin dagewa kamar da gaske yace dawa yake cewa naje  ai wllh my one ba kya tausayina  ni kadai kin mayar ni injin  ingama dake kikuma turani gunwata.
Da sauri ta tashin zaune " wai ban gane ba Nabil yaushe nace kajene  yasake bata fuska yace "tone yazanyin na gane tunda ke dakika bada da bakin ki baki ganeba.
Hadim  tace
"nede nasan munkwan ta kuma cikin farin cikin kawai juyi nayin naji ina shirin hawa tudun filo  natashi nayita neman ka bangan kaba ba inda ban duba ba shine na haura saman yarinyar  nan na ganka  Nabil ka gayamin gaskiya dannasan  baka min karya koka fara sonkasan  cewa tare da yarinyar nane wllh zuciyata zata buga  idan kace kanajin wata wllh wllh ko yau zata haihu idan kafara son katsancewa tare da ita se tabar gidan nan kafin ta tafi se na na kasata  yanda ko almajirin baban nata bazai sota ba gayamin gaskiya.
Ta garashen maganan tana dafe kirjin ta dayake bugawa kamar zai fito
Nabil yasake kamota  yace" gayamin gaskya kema kina nufin baki san sanda kikace naje ba?
Gyada masa kai tayi.
Yace "to wllh zansa malamai suyi miki rukiya kar ya zama sun fara shafa mike ne a kan son d'a   inde baki san sanda ki kaceba na kina kwance idonki ruke kikecewa  banje zaki iya mutuwa.


Wani a jiyan zuciya ta sauke tace "Alhadulilah  wllh nayi mugun tsorata a sheni nace kaje wllh bawani aljani kawai mugun sa abin  a raine yasa nayin  mafarkin  sa yafiton file kai kuma katashi katafi wllh se de mafarki   kasan da zamu kwanta munyin maganan.
Tasauke ajiyan zuciya tace my star kaci gaba da sona ni kadai Wlh kaso wata bazan iya jurewaba .
Murmushin yayin irin na ruwa tasha dinnan  yace"ke dayace my one amma dalilin son d'a yana ne man zautar minke.
Tace" ba dalilin son d'a bane dalilin kin kishiya ne wllh bana  son d'a yanda nake kin kishiya wllh ko yarinyar nan da nasan bata isa komai ba banason kasan cewar ka da ita dan de nasan idan bamuyin hakan bato za ayin mana megaba daya.
Yace" ga a lama shiyasa dakika cenaje  banyi musuba naje dan nasa a raina bazan kara miki musun  zuwa wajen yarinyar naba a sheke mafarkine.
Cikin yarda tace bansan manayi  ba
Amma nake ganin makamar  baka mata komai ba dan naga da kayan ka a jikin ka itama haka
Tabe baki yayi yace "ai kinsan ni idan naje sai naje taje tayi wanka  ita kuma idan ta shiga kinsan jimawa takeyi to tafito kena na fusgota ika shigo
Hadim tace "ai gashina jimawan nata ya mana rana badan haka ba da nasan turmi da tabarya zan tadda ku wanda nasan mutuwa ta kawai zan gani   tafadi haka cikin yarda da mijin nata dan tagama yarda dashi
Tace "af naman ta fa ai yau zata gama period dinma muje  inda zaka iyasai naraka ka koza a dace.
Shiko zuciyar sa fal murna zaiso hakan amma a fili yace "ke barshi sai gobe bacci nake ji ga gobe muna da meeting a club  tace shike nan dasafen zaka iyayi ai

baiji dadin hakan yaso a ce tanace sai yaje ya kwashi bonus.
Tace "mukwanta  kanada meeting nima gidan habiba zanje gobe dan bazan rakaka meeting ba zata min lale. "Tom yace a dakila dan baiso hakan ba yajata suka kwanta.

Aban garen Fandau  kuma suna fita taja bargo sede me wani a zabeben cikon mara naji hannun ta ta dura a maran take jujuya kai  saide a bin  baiwani jima ba ya dema mata ciwon nan  take wani  Baccci me dadi ya dauke ta.
 Su Nabil an sha adon cikin shigan  su kaman  kullum  iri daya  suka fito sakale da hannun juna Nabil ya juya yace "my one  bazamu  tafi da driver ba sabo yau nina keson samun ladan zumun ci  dariya  tayi tace"kai kam ai baka gajiya  da tuki yace "musamman  idan gani ga my one  ne ba tana mun wannan murmushin nata  metsada ai jina nake kamar nasaki  kan motan  dariya tayi ta daki bayan sa da daya hannunta  tace "kajika ko.  "yace da fadan gaskya ko suka shiga motan  suka dan na  security  get  din yabudu suka fita suna cikin tafiya wayan Nabil  yayi   kara yana dubawa yaka iya rigima  ce wato inna ZAINABU  danja kenan wutan ki a baya gefe  yasa muyayi parking   baiyi Picking ba har wayan  ya katse ya nayin yanda fukan sa yayi ne yasa Hadim  gane akwai damuwa  kiran ne ya sake shigowa  a karo na 2 Hadim  ce tasa hannunta  ta daukin  wayan dan gani waye  ganin  Inna zainab  yasa Hadim  saurin kallon Nabil  cikin faduwa  gaba dasuri ta meka masa wayan tace "kadaga idan baka dauka wani lefinle dafe kansa yayi  cikin darura Hadim  ganin kiran zai tsinke kuma wani  matsifan hakan zaija musu yasa  tayin  saurin  dagawa muryan inna taji tana cewa kaide modu baza  akira kaso daya ka dauka bako cikin ladabi Hadim  tace "Inna nice ina kwana cikin karaji  da fada inna tace Lalle  yariyar nan  ke meyasa wani  kolacin baki da tarbiya  ne wayan kina kira da saurin  Hadim  ta girgirza kai kamar tana gaban ta tace   a a
Inna tace "da dake na keson magana ina da nombar  naki kezan kira zaki wani dauka kice ina kwana da kina da tarbiyan gaisuwan meyahana ki kira ki gaisheni  wata nawa zakiyi baki kirani ba dan haka bani wanda nake don magana  dashi kawai a hankali tacira wayan a kunneta ta mekawa Nabil  da duk yana jin mesuke fada

Ya karba yace "Inna ina kwana  tace "kabari idan kaso jin na kwana  lfy  kakira ni amma ni yanzu nakira kane nagaya maka su yasmin zasuzo huto  kasa a basu  kudin jirgi dana sayayya su ko dan wajen su 6 har da meram ita ma tagama India  din tazo gida gaba daya  yace "eh wakil yagaya min  tace to zakaga meram tayi kyu idan kyu kake so inason kafin tazo ku daidaita kan ku kaji  kaji  yace "haba Inna  nayi yaya da dan uwana kuma  kanin abokina dayake son meram tun tana yarinya haba  Inna bagir mana  bane.

Inna ZAINABU  tace kaja  bakin ka  kaiwani gir magareka  gir manda ko kwai  baka a jiye
 shikena tsaya  wasa koba Meram ma zan samo maka mata inde lokaci Yayi tana gama fadan haka  ta kashe wayanta
Nabil  yajuya yakalli Hadim  ita mashi take Hadim  tace Allah  yanzu  matan nan baza ta bari na zauna lfy a gidan  aurena ba nida nake da ajiya a gida zata turomin wadan nan yaran nata masu shege sa ido ya zamuyi dawannan yarinyar  kenan?
Nabil yace "hanasu shiga  bangaren kawai zamuyi  tace "kaima kasan ba zasu hanuba tunba wannan Meramn  dinnan ba mezu ben kwailaye  ita a dole yar  boko dariya Nabil  yayi  yace "wannan  ai ko zubin kwailan bata samu ba shima wakil duk ga banyan babes agari me yagani jikin ta Hadim  tayi dariya  tace "aine inda ita din mata baka wllh bazan damuba yanda banda muda wancan  kucakar ba sai de kawai banason jin kunyane a wajen kawayena  dan nasan za a kirata kishiya ta hakan shine  babban  abin kunya  a wajen na
Nabil kallo  takawai yayi ya kunna mota yaja Azuciyan  sa yana ai yanawa anya soyyayan Hadim  Gaskiya ne yafara shakkun haka tun sanda tacusa masa auren Fandau

Akofan gidan doctor   Muktar  ya sauke yazuna har tafito  yace "ki gaida mamata  da didi tace"ah  bazaka shiga bane
Yace "zanyi let
Sai nazo ki kulamin da kanki  I love you  zaga yowa tayi  tayi kissing  dinsa dukka kumatusa tace "I love you too much  my star  murmushi yayi ya shafo kumatunta  yace "Allah yabar minke kina cikin aikina yaja  tana tsaye  tana daga masa  hannun  haryayi nisa sannan tanufi gidan
Shiko  Nabil  da ya kwana a ransa  da safe zata rakayi gun Fandau  amma  da safen batayi maganan ba kashi  yayi mugun sawa a ransa surorin ta kawai yake gani  a ransa bai san sanda  ya dauki wayan sa yayi  kiran ogan suba yace "ya masa alfarma bazai samu daman zaman  meeting ba  ai ko ogan baiji dadi ba dan Nabil  sheke komai a wajen amma  haka ogan ya hakura  dan ba a tursasa Nabil
Yana kashe wayan yayi Murmushin  a fili yace inada bonus  kena cikin farin ciki yake tukin harya karasa Bridge  inda gidan  sa yake

Itako Fandau  kayan ta tattaro set 3 zata wanke dan Hadim  tace  tadena  tara musu kayan wanki diriniya tayi  tayi dan injin din wankin tayi  tayin yaki aiki  daga ita sai wani dan towel  guntu korabin cinyar ta bai kai ba a fili tace kai mawan na injin din dan renin hankali  kar ka juya dinmana  bani da hannun  kawai sai da sunkuya tafara gurzan kayan
Tana rere wakan ta cikin harshe tana kanuri  tana cewa  _kanuri beri larrah sheu kanuri yani cab_
Nabil  da yashigo  baigan ta ba yana kasa kunne yajiyo wani zakekken murya a bathroom  din  bai sanya a kayi ba shide kawai ganil kansa yayi a toilet  din yajin ginar da gefen jikin sa a jikin bango ya daga kafan sa daya ya daura akan wani dan takali  ya harde  hanuwa  sa kawai  ya tsaya  kallo  ta sai faman  lunshe  ido yake yanayin  yada tayi tsugunnon wankin komai najijinta yana girgizawa  musamman  yanda heeds  dinta  yafi girgiza  kallon  mana dauriya kawai  yake mata  dan gangan jikin sa  sai ingizasa ya keyi zuwa gare ta.
Itako Fandau  da tafara jin kamshin sanyeyen  turaren sa bata dauka  shibane  a zatonta ko dunna jiyane dayayi wanka  bai gama fita ba tasara wane irin Turare  ne me azaban kanshi  duk kayan ta yanzu kanshin suke kota wanke sai taji.
Zuciya  daya  ta matse kaya zata  a jiye gunda a jiyewa taci  karo da mutum da sauri taja baya  tsabar   tsorata da tayi bata san sanda guntun  towel  dinda ta daura  ya tsilo kasa  ba gashi dama bakomai a jikin ta ihu tayi  tayi  saurin sugun tawa zata  dauki  towel  din sauri yayi  yariga  ta dauka ya cila a saman  shaya yace  "hauka  zaki min ihu kanwane  dalilin koda yake kinga maye ko wanda yafi  kura iya maita
da sauri  ta girgiza masa kai.
Yace barima  na tambaye ki  baki iya kuna injin din bane kike mana ja gwalgwalo a toilet  wato zaki  bata mana gida da kazanta  kafin  lokacin  tafiyan kiyayi ko?
Ta girgiza  kai a laman a a
Ma magana nake mikiba ya daka mata tsawa.
Murya na rawa tace a a nakunna kinyi yayi.
Yace "to hanaki shiga sauran  bandakan a kayi   duk  abin da yake ban garen nan zaki iya amfani dashi ko dakin idan kika ga dama zaki canza.

Tace "to kayi hakurin dan tagaji da sugunon gaba  tason ta tashi yaganta ahaka.

Yace "najin dan mekikayi ihu da kika ganni?
Shiru tayi
Yace "badake  nake ba?
Tace"kayi hakuri tsorata nayi.
Yace eh  ga zaki ga kura ga maye gawanda  yafi maye  iya maita har gurnani yake ko?
"tace dan Allah  kayi hakuri wllh bazan karaba
Yace "a wannan  karan bazan hakura  ba har se kinyi  tsallen  kwado
Da sauri  da dago kanta ta kalle  shi da dara daran idon ta
Yace "dena kallona da wadan nan shegun idon naki ko kin dauka zanji tsoron sune  tashi kiyi abinda na saki.
"ban iyaba fa
Taba shi amsa
Yace yau zaki iya  tashi muje daki duk giman dakin nan yau saikin zaga yashi sau Ukku wani irin  tsawa  ya daka mata wanda ya raza ta manta mada ba kaya ajikin ta  bata san sanda
Ta tashi   tsaye  ba hannunta biyu takare kirjinta dashi ganin  yafi kallon wajen 
Nuna mata kofa yayi yace "tom wuce  simi simi tawuce  shiko suman tsaye  yayi ganin yada  Heep's  dinta yake  kadawa ta iya juyasu  sosai yajiji nawa hannun sa da yayi  jarumta bai  janyota  kamar  yan da gangan jikin sa yake bashi umarni ba sai da ya sauke a jiyan zuciya     sanan yabita a baya  yana kallo  san tsar iya tafiya irin nata  wanda  ya sheda hakan  tunranan haduwan  suna fari   yace yariyar nan  kyune kawai  Allah  bai bata ba dasai  nace tafi  sauran mata komai.


A tsakiya  dakin ta tsaya  hannun  dafe da books  dinta sai har hada cinyoyi   take na kare gabanta  sai wani hula  da yake  kanta  kawai
Yace "to fara cikin tsawan nan  tasa yafa da aiko da sauri  ta fara  duk  da ba iyawa  tayi ba idan  tayi  daya biyu saita fadi ga tsansin  teiyel  shiko banda murmushi  ba abinda yakeyi  sosai  jikin  ta yake mutsawa  wanda  shima  kansa  nasa  sandan  girma yake harbawa
Da karfi tayi wani faduwa  se gashi  hulan  da yake kanta  yafadi  mezai  gani kanta yagani tallal kaman  glass  sai  sheki  yake  ba  alamun  gashi  yata ba zama a kan bai  san lokacin ya meke tsaye  ba sai gashi  a gabanta  yace  kedan  uwar meya samu  kanki  da sauri tafara magana  da yanda  yataso  a zuciyen nan  zai iya yimata  illa.
Cikin in in na  tace "wani  mai nagani  a bandaki me hoton  macce  da gashi  a kanta na dauka na gashine na shafa  sai da nazo wanka  naga gashin  duk  yafita.
Ta karasa maganan tana matse idon ta
Cikin  baciran  da mugun  haushi  yace  to jashila to man  askine  shine  kika  dan bara  a kanki  tozaki  zauna  harse sawon  watanni  3 sannan  gashi  zai fara  fito miki cikin mutukar  haushi  yake maganan  danya na mutukan son  gashi  ajikin macce  shida  yake shirin  siyo mata mai da mataji  a boye ya kawo  mata dan Yasan  Hadim baza  ta bataba tunda  tace  bai  shafi  ai kin suba yasan  kishine 
Itoko Hadim  tana  shiga  gidan  Habiba  tace Allah  yasa  kindauko  mana  lalen dan nawa ya k'are
Hadim  tace  "kuma  wane iskanci  ne ya hana kigaya mintun ina gida saiyan  zuda nazo
Habiba tace "maida  wukan indan  wannan  ne  bari  a dan jima kadan  a tashi yara  yau  doctor  baya gari gidan naki ma zamukai  kwana.
Hadim  cikin farin  ciki  tace kamar  ko kin san yau Chelsea  sun suro wai  meeting na safe  har dare  zasu rike mana  mazan  mari mudau ko yaran  sai muwuce  kawai  muyi  Lalle  mu ni  yau har wannan  gyaran jikin  zaki min wllh  kin iya my  star  yanason  wannan gyaran.
Habiba tace  ba damuwa akwai  kayan  gyaran
Hadim  ce take jansu yaran suna  baya Habiba  tana  gefi  get  din yana budewa  tunkafin Hadim  tayi  parking  idon  ta yagane  mata  motan  da Nabil  yafita dashi  tace "tooo  meya  kawoshi gida  kuma bayan sai  9 na dare  za sufito ba.

*Tonide nasan meya kawoshi* *kekuma kema idan kika shiga zaki*  *gani  toyanzu  de ba Baccci  kike ba idan ke me hankali*  *zakigane*
 Muje zuwa
*B *Jattko*
08062383027
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA  TA*



               *NA*

 *Batul Adam Jattko*

*Mum farhan*
*Hadim fa bata dauki* *Shawaran kiba*

*Masoyan damata ina kara godiya* 🤝

*Humairan Fandau ta gd*

 🌈 *Kainuwa Writers*
*Association*🤝

*20*

A general parlour  suka yada zango  yaran sunata  tsalle dan suna son gidan antymum haka suke  kiran Hadim   saida sukayi sallah zuhr   Hadim takira firseh me aikin ta a bangaren kitchen   tace  "ga yara kuje  su fade abinda suke son ki dafa musu muba yanzuba  firseh ta amsa da "ok taja yaran  suka  fice
Hadim  bata ajiye  wayan  ba tace bari nakira   my star  naji   meya kawo  motan  sa gida

Nabil  da har lokacin  yana  fadan  askin  kan Fandau  wayan  yayi  ringing  yana  zarowa  yaga sunan  my  one   yadaga  yace  "hutawan ki lfy  my  Queen
"tace  Allah yabarmin my prince  na  tace  fasa meeting  din  kukayine?
Yace "a a mundan  fito  hutune  na kunna  wayan  ya akayi  ne?
Tace to yanaga motan da katafi  dashi  a gida
Dasauri  yace  "gida kuma
tace "eh
Yace "ya akayi  kika  sani?
Zuciya  daya  tace  "ina  gidan fa
Hannun sane yafara  kar karwa  yabude  baki  amma  yaji  mgn ma yagagara
Dabara  ya fadu masa  yace"ok  munzo  da amjad  ne  shine  muka  fitada   tasa nabar  nawan.
Tace " ok ai muzone da habiba  da yaran kwana ma suka  kawomana
Yace  "ok sai  nazo
Tace  "ok my sweet
Yana kashe wayan  jiki na rawa yatashi  yafita  babban  parlour  part din  Fandau  ya canza security  din  kofan  duk  da yasan  balalle  bane  Hadim  tashiga  amma  yayi  hakane  saboda  tsaro.
Yakalli  yanda  Fandau  take. A sugunne  tana nishi nagajiya
 yace  "jekiyi  wanka   sanan ki samu  sabon  towel  ki daira  kisan  yanda  zakiyi  da Wannan  kannaki  dan bana san ganin sa me kamadana tsohon baya hude  karki kara bari naganshi kiwuce  kiyi  abinda nasaki  inajiranki.
Ya fadi haka  yana kwantawa  akan  gadon yana  tunanin    meyasa  Fandau  tafi sauran batan  da yasani  ne  ko wannan tsallen  kwadon  dan  yakarewa  jikinta  kallo  yasata  bawai mugunta ba shikan  sa yana mamaki  yanda  akayi  gangan  jikinsa yake yaudaransa akanta,
Allah Allah  yake  lokacin tafiyanta yayi  ko  idan  yaga bata kusa zai iya manta ta,
Dan  yanajin  kunyar  ranan da Hadim  zatagane  yanason wani abu ajikin  yarinyan amma  idan  yatuna da ita taja   sai yaji tausayin  nata yaragu.
Duk dahaka yana tsoron  ranan da zata  reskeshi,
Yasauke  a jiyan zuciya  afili yace Ya Allah  kacirewa  gangara  jikina  kwadaituwa  da wannan  yarinyar  kar  zuciyata  ta kasa  daurewa  itama takarba da ganan  na tozarta a idon  Duniya  dan babban  lefi nayi na  auri  yarinya  bada sanin  iyayen taba nima nawa basu  sani ba  nasan  ko shari a sai  tamin  hakuncin  hainci  da yaudara  danayi,

Dukan  filo yayi  yatashi zaune  dan  shi yafi ganin lefin  gangan jikin sa dan shiya kekai  tunanin ta cikin  kwakwaln wanshi.


Motsin fitowa tane  yadawo  dashi  daga  nunanin   ya daka  kai yakalli ta  daure take da towel  kamar yanda yace tayi  sai kanta  tadaure tamau da wani siriri gele na fakista  tsayawa Yayi  kallota ya nason yaganta  cikin kwalleya da Kananan  kaya English weres amma Bata dashi  dogayen riguna  kawai  da fakista  hadim  tabata  a cewar ta ba ado tazo ba karta  dauke  mata hankalin  miji  dan komai munin  macce idan tayi  ado tana kyu
Yana kallon ta ita kuma tasun kuyar  da kai  tana tsaye   a hannu  yadan bubuga gadon  a laman tazaune  ahankali ta zauna  ta sake sunkuyar da kai.
Nabil tashi yayi zaune  ya nade kafa yasata  agaba  yana kallon ta  hannun sa yasa yadago  habanta  yakai nasa fuskan dai dai  nata  a hankali yace "kinyi brush din bakin ki?
Gyada masa kai tayi alaman eh.
Hannansa yasa yaja lips dinta  na sama yabude  haske masa ido  fararen  hakoran ta jerarru  sukayi  bai san sanda yace wow
Dama datti ne  yadafar  dashi  kenan
zuba mata ido  yayi   yanason  yaga munin ta amma  sai  a sannan  yake ganin  wasu  sirrikan  boye  na  kyunta  da mutum  bazai  iya  ganewa ba  har sai yanusu   hancinta  bame tsawo bane  kuma  bana nen neba ne  daidai  misali  fukanta  yanada  dan fadi kadan  gawani  kwantaccen gashi  a gaban  goshin ta yazo mata har wajen kunnenta  sai  ka ratse  megashi ce dan  man  askin  iya kanta  ta shafawa idanuwan ta  suna da girma  da  haske  shide  Nabil  ko jurewa kallon su bayayi   Fandau  doguwace  bata da jiki  ban bancin suda Hadim kenan  ita farace tas  shuwaa  amma  gajerace ga jiki.

Ajiyan zuciya  yasauke  afili yafurta yarinya kinada  kananan  kyu wanda  yafina manya  daukan  hankali  ya sunanki?
Fandau  wani  haushi taji  ace mutu yana  amfanuwa  da jikin ta tsawon watani  bai san sunanta ba.
Ahankali yafurta kigaya   min mana
Fur taki  mgn  gashi  bayason  matsa mata dan yafi son tasaki  jikin dashi
Jikinsa ya
Jawota yace "niko fushiki dani ko nasaki tsallen  kwado  ko bari  namiki  tausa  ciwon  zai tafi. Ya nayin  yanda  yayi magana  cikin  sanyi  kaman  bashiba yasa  ta dago  kanta  ta kalle shi  ido  daya yakashe mata   shiru tayi  ajikinsa  yana  mammasa  mata  cinyoyi ta  tuntana  jin ciwon  har  tane meshi tarasa  daganan  salon  ya canza.
Haka ya wuni  yana cin bonus  injishi da fada🤣🤣
Wuni  guda  ajima  bini bini  abu daya  tana  manne  ajikin  sa,
Ba abinda yake  rabasu  sai  sallah 
Abinci ma kayan
Fruit kawai  suke sha  sai ruwan  tea


Nabil yayi  hakane  dan yaji  ko yarinyar   zata iya gunduran sa amma  ina  sai mawasu  surukan da dabai saniba  da suka sake nunkuwa
Akan nada.
Sai kusan 10 na dare  yakira  oucera wani  yaran  gidan sa yace  yazo  general parlour  yadu ba masa  Hadim  tana ciki.
Yazo yaduba  yace  "bata ciki
Harzai  fita  yajuya  yakalli  Fandau  yace "zan siyo miki  man da zaki  shafa  akan ki da kuma  wanna zaki shafa  ajikin kida sabulun wanka mai  kyu  kidena wanka da wancen  bashida  kyu  amma   zaki  samu inda  zaki  boye  idan kika kuskura  matar  gidan  ta gani  sai  nacikin  jahannama  yafiki jin dadi.
Yayi  shiru  can  yata ko  gaban ta yasa  hannu  yamekar  da ita  ta tsaya  yasa hanunu  ya tallaho  kumatunta  biyu  duk  da hannun  sa biyu idon sa cikin  nata yace "sai  me'kikeso  da bukata  na sayo miki  kwace fuskan ta tayi  tazame  jikin ta danasa  tace"  wajen mama ta  nake son naje
Wannan bazai  samuba  zakije idan  kingama mana  aikin  da muka daukoki.
Fandau  fashewa tayi  da kuka ta fada  gado.

Baki ya tabe tareda  daka  kafadun sa  yafice  da sauri   sai  da yaga  yafa da kan kujeran general parlour sannan  yaja  ajiyan  zuciya  yana  murmushi  wayan sa yazoro yakunna yakira Hadim  yace  "na dawo
Tace "kana  in  yace  ina babban  parlour  tunda  kince  gidan  da baki  tace  "ai  har sun kwanta  ni  ina daki  kashigo kawai  yace"ok my dear 
Hadim  da yau  ita  da habiba  sunsha jike jiken  suna na mata  Nabil  kawai  ta ke jira  yana  shigowa da godu  ta fada jikin  sa shima  rungumota yayi  sosai  yana  ajian zuciya  na karya  kamar  gaske  yayi  missing nata
Tace  "kasamu  meeting  ka manta  dani  nasha  iran  ka awaya  soba  adadi  barufe
Yace" meeting  ne yayi  zafi yaraba  jikinta  da nasa yawuce  toilet   tabi  bayan  sa  cikin  zumudi  dan magani na aiki  ajikin ta

Saida suka gama duk  shirin suna  kanciya  Nabil  yana sane  da ita   yaja  blanket  ya kwanta  yau  ko janyo tan  bai yiba  data dame shima  juya mata  maya  yayi.
Da sauri  Hadim  taja  wutan  ta kunna  my star  mekenan  hakan  nizaka  zuyawa  bayi  yajuyo  yace "wayyo my one  dan  Allah  kibarni  nayi  Baccci  wllh  agajiye   nake  kinsan fa wuni  nayi  a meeting.
Tace "Gaskiya  my star  ka binciki  lafiyan ka dan da bahaka kake ba  dada ko ball  kabuga  baya hanaka  yin kamai   balle  wani  meeting  nide  zamuje  wajen  doctor  baka da lfy  ina gama shiyasa  ka kasa bawa  yarnyar nan  ciki dukka canza  kamar  ba star  dina ba.
Shide  baiyi mgn ba  Baccci karya mayayi.
Da safe  duk  tare  sukayi breakfast dasu  habiba

 *Bayan wata 1*
Fandau  tana jin canjin  ajikin ta dayake  bawanda  zata gayawa  saita jure abinci ma bako wanne take ciba  ga saurin jin yunwa kocikin  dare saita tashi tane mawa cikinta  abinda zata ci
Gawannan   ciwon maran nan da tayi  tun ranan da  Nabil  ya fara satan zuwa  yananan  gaba daya maranta  jinsa  take  kamar  andaure mata  baye ma ranan  da Nabil bai samu shigowa  ba dan  yanzu  ba abin data keso irin  abinda Nabil  yake  mata,
Yanzu ma tsaye  take  a kitchen sai  cije hanunu  take  duk  abinda  ta dafa  takasa ci  dan jitayi
 Tana mugun son  shan kunun  tsamiya ga bagarin  balle  wani  tsamiya.

Nifa my star  inaga  kamar  yarinyar nan  tasamu  ciki  dan da bata kara ko kwana daya ba  amma  yanzu  gashi  har  two days   Gaskiya idan mu kayi  sa a burin muzai cika wannan  karon takara she zancen  cikin  farin ciki.
Nabil yace "inko  hakane my one zanmiki  kyutan da banta bamiki  irin saba zan jidake  sosai.
Tace "ai nice  yakamata nama kyuta amma  bari  da safe zamuje  wajen doctor  tukun
Zaro ido Nabil  yayi  yace  ta yaya zamu kai ta  wajen doctor?
Tace ba ita  zamu kai ba fisarinta  zamu  garba  sai naboye  idan na masa bayani  kaman  yanda musu ciki sukeyi  idan  yace na iyo  fisari sai nazuba natan.
"Yeeees yace tare  da tafa mata.

Fandau  tana  tsaye  haryanzu tana tunanin bayan kunnu tsamiya  ko mezata iyaci  taji  muryan shigowa su hamdala tayi  azuciyar ta  dan tana muradin Nabil din ma sosai da sauri tafito  dan kar tayi lefi zubewa  tayi kamar yanda tasaba gaishesu  Hadim ce kadai ta amsa  Nabil ko inda take bai  kalla ba yawani  sha mur kamar yanda  yakeyi  idan agaban Hadim ne.
Hadim tace  yawwa muje bandaki ko takamo hannun  Fandau suna shiga  bathroom din  dan roba tameka mata tace  gashi  kiyi fisari anan kibani  Fandau hannu narawa ta karba dan tana tsoron Hadim.

Doctor Muktar yazuba wa Hadim ido  yace" meda me kikace  yana damunki yamutsa fuska Hadim tayi  kamar marar lfy  tace  tashin  zuciya yawan ciwon kai  bakina yawu yana  taruwa
Cikin happy  doctor  yace "dan Allah  da'gaske  abin damu ka dade muna son jine  amma bari  nakira nurses kuje a gwada firarin ki  yabuga waya yakira nurse din tana zuwa ya hadata da Hadim din suka fita wani dan roba tamekawa Hadim tace kishiga toilet  kiyi fisari  ko Hadim ta karba tana shiga ta bude  roban  ta siyaya fisarin Fandau a ciki  tafito tamekawa  matar  saka makon  yana fitowa tamekawa Hadim tace ta kai wa doc
Hadim tana kawowa tamekawa doc
Hannu narawa  Muktar yakar bi pepper  suma Nabil da Hadim  gaban sune yake faduwa  doctor  yana budewa ko gama karanta wa baiyiba  yajefar  yayi kan Nabil  yafada jikin sa cikin happy  yana cewa "my friend congratulatins
Hakan yanuna musu akai ciki  kenan Nabil bai san sanda  yature  doctor ya rumgumo Hadima  suka fara kukan farin ciki  atare sunjima  a haka.
Kafin doc yakatse musu  nunani  dacewa ni fabaga ma yarda ba sai namiki scenning
Yafadi  hakan yana tunawa Hadim  dagon da yake scanning din
Atare cikin sauri  Nabil d Hadim  sukace scanning kuma

*To fa abin nema ya* *samu amma ya zan cen scanning* *zai kasan ce*
*Zaiyuwu kuwa*

*Karin gdy gamasoya*


           *B Jattko*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA TA*             



        *NA*

*BAtul Adam Jattko*

*Cikin ummata*
*Banida kamarki *Fatima goni saleh Jattko  ina miki fatan gamawa lfy*

*Maryam T Baliya*
*Na gode da soyayya daya bawan ki*
 
  *Asmau ta  mi u  meson DAMA TA*


*Fatan alkairi  gareki*
*AISHA SHEHU  mmn twine nafara novel dinki KURUMA MATAR MAKAHO Allah yasa kigama cikin sa a*

🌈 *Kainuwa writers Association* 🤝

*21*


 Doctor "  ya jijiga kai yace yes dan mu tabbatar ne ai kunsan  abin da muka dade  muna nema nefa doc muktar ya karashe maganan yana murmushi farin ciki.
Nabil  rasa mezai ce yayi yatsaya yana wara ido.
Sai Hadim ce tace "a a doc ban tabayin batan wata ba tunda nake sai  awannan dan haka bana tantama nasan cikine.
Danme za muce sai anyi wani scanning ai wannan ma yiwa Allah shi shigine
Kuma naji ma awani fadan ance yawan yin scanning yana juya idon yaro  balle idan karamin cikine yana sa illah  sosai
Sai a sannan Nabil  yasamu bakin magana yace  Gakiya ne baza a sawa yarona  kowane  irin na uraba haryazo Duniya.
Doctor yace "to Lalle za ayi dan gata ban tabajin ance scanning yana da illah ba sai awajen ku ni kam inason  ganin dannan tun aciki.dan haka yazama  dole nayi
Nabil yace "mayen banza  sai de  kaci  na wani ba nawa dan ba yafadi haka yana jan hannun  Hadim dan idon sa Fandau kawai yake son gani
Dariya doctor yayi  yameke dan yamusu rakiya
"ai ko yanzu baku yarda anyi ba idan  yagirma  lolene   saboda  duba lafiyan sa dakuma  sanin  E.DD dinta
Nabil yace "karyan banza  na likita Allah yake tsarawa  halitansa rayuwa baku ba d'ana lafiya lafiya zaizo  sanin wani  E. DD din banza kuma ai  Allah  shi yake  da lokaci  bawani ba ai kin banza muba
 Zama kukara ganin muba
Dacan damuke zaryan zuwa  bakuba muba sai  yanzu da muka dogara da Allah yabamu zaka kawo mana iyayin banza
Hadim kam da sauri take takawa dan gani take doc zai jata dakarfi maya mata.
Dariya  doc yake musu har sukazo wajen mota Nabil  sai da ya budewa Hadim ta shiga yarufe sannan  yajuyo  yace  "to mayun Duniya  Mungode.
"Doctor  yace  to yan gargajiya  Allah yaraba lfy  dan naga alama akan dan nan kunza yan gargajiya.

Nabil de bai kulashi ba yashige mota
Doctor yaleko yace " nasan yau habiba  zata sha albishi
Hadim tace "dan Allah abba didi karka ga yamata nafison  taji  abaki na gobe zanje gidan gaba daga ba nake son nagaya mata
Doc yace "to shikenan idan nakoma zan dauko ta kigaya matan amma wanna  babban albishir  din bazan bari sai gobe ba.
Dariya  sukayi  shima Muktar yajuya

Fandau  zaune  abakin gadon ta amma koni yau  shigan ta ya burgeni    wani shegen  English wears ne  ajikinta  wanda  Nabil ya sayo mata  a boye  yace idan  yana dakin zatana sawa  idan kuma akayi rashin  sa a Hadim ta gani  tace mata  a daya dakin nakusa  danata  ta dauka  to zatace na kannen sune  dasuke zuwa hutu.
Tace to amma bata  taba sawa bama sai yau  rigan yellow ne sai bakin  wando  wanda  iyakan sa cinyar ta fuskan nan nata shar da shi  yasha  mai mekyu  ga wani haske na jaririn ciki  gashin kanta  baka ramin bada mamaki yayi ba dan bame gabi yace  one month    da aski gawani baki na kyu da tsansi  da yakeyi  ta tajeshi  ya dan kwanta kamar irin na yan
Matan kabilan  Igbo dasuke dan tsetse kan sai hakan yazame mata kamar  ado
Tayi sosai  kamar ba Fandau me allo ma.
Kafanta daya akan daya  tana tunanin  raruwata da murkin mallaka irin  na Hadim hatta fisarinta bai huta ba   ga damu yau  kwana 2 ta dameta  da yawan zuwa kinyi sallah  baki ga al adan kiba  mekike ji ajikin ki tabbayan kenan   to metake nufi dani  tanason nayi wani jinyan kenan ko
Tunkafin ta hadani da kare
 Allah kabani cikin na nabar wannan gidan  gwara nayi  bara a titi da zama dawadan nan.
Tanacikin  wannan tunani taji security  yayi  kara kafin ta tashi  da shiga koda bandaki ne  ta canza kaya kar Hadim ta sameta dawannan.
Amma  kafin tameke
Har anshigo  tana  daga kanta taga  Hadim dince kuwa da gudu ta iyo kan
Fandau

 ita kuma
 Fandau  ta zata
 dukan ta zatayi akan kayan da tasa.
Kuka tafara tana ja da baya anty dan Allah kiyi hakuri Wllh bazan kara sawa ba Wllh tuda yakawo ma bansa ba saiyau  din kiyi hakuri ina Hadim ko fashimtar me fandau take nufi bata yiba itade sotake  ta rungumo Fandau a jikinta taji dimin danta

Fandau zubewa tayi  awajen dan tasan yau ta ta takare
Hadim rungumo ta tayi ta fara kukan farin ciki  yarinya kinbiyamu kema zansa a warkar da mamar ki tafadi hakan  tana shafe cekin Fandau.
Nabil baiso hakaba  bai ta bajin haushi Hadim kamar nayau ba ta masa shigan sauri yaso ace shine  rungume da Fandau yaji dimin  dansa abin da ya dade yana nema kai  da ita kanta Fandau  dan bata taba masa yau  kamar yau ba  sai benko ina  Najikita yake da kallo   baye kanta yabashi shaawa da mamaki dan tunran da  yafara gani ba gashi yace karta sake budewa  a gaban sa bayason gani  dama haka yayi  toho mekyu da santsi  yan da yayi kaman irin na mazan  India  dinnan sai  yaji  yafiye  masa me tsawon   dagani   zaiyi dadin shafawa 
Yana kai idon sa kan boobs  dinta da  suka dan fito dalilin danne wan da Hadim  tadan yi  take yaji wani yim  gashin jikin saya iba yana dan jan idon sa kasa kadan  ganin yanda  Heep'sdinta yazauna tab ajikin wandon  ganin cinyar ta yake sunbul awaje  ai bai san sanda yayi kan taba  da karfi shima ya rungumeta cikin da bara ya banbare  Hadim  ajikin Fandau  ya maye gurbin ta likata sosai yayi  ajikin sa yana sauke ajiyan zuciya hannun sa yasa cikin rigarta ta baya  yana Shafa bayan ta wani dimi yaji  na ni ima yana ratsa tafin hannun sa yana shiga har cikin bargonsa harwani fisgan nunfashi yake sai faman goga kirjin sa yake  a nata.
Fandau  shiru tayi  ajikin sa dan ita jitake kamar sudan gana  da gado  dan bata san jarabar  daya sameta ba na shaawa   hannun ta tadaga zata shafa  wuyan sa amma  takasa dan ita har yanzu tsoron mayar masa murtanin abin da yake mata ke,

Wawuyar  ko sai tsallen  murna take dan ita a tunanin ta Nabil  cikin murna yake kamar  yanda itama murnan  ya mantar da ita kishin,
Itama sake  rungumo Fandau din tayi  suka sata a tsakiya
Shiko Nabil  kakatun Hadim ne yasa yadanne  zuciyar sa yadan dawo haiyacin sa yajasu kan kujera there siter  suka zube  kwata kwata  yakasa control din kansa  jiyake  kamar yayi komai  a gaban Hadim din  cikin dashiwar murya yace "my one kije part dinmu  ki dauko min  kan wayana na family.
Tace "dama badashi  kafita ba?
Gyada mata kai yayi dan bayaji  zuwa yanzu zai iya daga harhen  sa yayi mgn
Dagudu  wawuyar tafice
shiko Nabil  yasan  kafin tazo zai rage zafi musamman daya san wayan yana jikin sa.
Juyo da Fandau yayi ya hade bakin su wasanni  yadinga jifan ta dashi masu zafi  da yaga mazai  iya jurewa ba yameke da kyar yana tafiya  yana tangade gamar  dan maye yana hada hanya yaje  ya janza   security  yanda Hadim bazata  iya budewa ba  cak ya dauke ta Yayi  kan gado ta ita yafara sarra fata son ransa   wanda ita mashi take jira  yana cikin harka yaji daya  wayan  yana ringing  a aljihun wandon sa da yacire akan  gadon
Ya dan rage zafide  amma  baiyi yanda yaso ba yatashi  harda gudun sa ya shiga bathroom  yawan ke  inda najasa yata ba dan ba daman wanka tunda yar yanzu  wayan bai dena ringing ba da ya katse  za asake kira yasan  Hadim ce da sauri  yafito  yasa kayan sa ya cewa  Fandau ki tashi  kije kiyi wanka yayi inda  kofan yake yana sa duk wayoyin a  silent  yama yarsu  aljihun  yayi inda kofan  yake  ya danna  security kofan yabode  Hadim  yagani  a tsaye yace"haba my one  daga ki dauko waya  mugayawa gida abin farin ciki sai  kije kikama zama
"tace wllh banga wayan ba nakira yana ringing amma ban ganshi
 ba  ai najima anan
Kasa bude security nayi  idan nasa nombar sai  yace min error ko dokin ne yasa na manta bana sawa dai dai ban sani ba
 nakira wayan ka kuma bakayi  picking ba
Laluman aljihun sa yayi  yaciro  wayoyin  yace "ah ai gata ma anan  na manta  nasa a silent  dazu  kafin mufita  tace "haba nema nema narasa
Tashigo dakin  tana
 ware ido ina takene? Ta  tambayi inda Fandau take
 dayake Nabil  dan Duniya ne kan kujeran da suka fara  zama ya kalla kar da gaske yadaga kafadun sa alaman bai sani ba
Hadim  tace "ko tana   toilet
Yace "inaga amma  kamar anan  nabarta amma  saime  yana jefa idon  sa tsakiyan  gadon gaban sa yafadi  dan bayan  yamitsewan da shinfidan gadon yayi ido ya sake  warewa da idonsa ya nuna masa tsakiyan gadon  inda yabaci  wanda bai kula dashi ba gadon  zaka kalla ko kai yarone kasan  anyi  wani  abu balle  Babbar macce kamar Hadim  tace" kaiiiiiiii


*Gaskiya yau kan saide nabaku hakuri dan naga baikai *nada ba sis  kuyi  HAKURI  DAMATA yanzu aka fara  ku gyara zama* 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻🌈🤝


              *B JATTKO*
       *08062383027*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA TA*


           *NA*


 *BATUL  ADAM JAJJKO*


  *Zainab*
*Zeee*
*Na gaisheki kyuta*




🌈Kainuwa writers Association 🤝

22

Kai kai meya  yamutsu gadon haka?
Ai Nabil cikin zafin sa irin nayin ball  yayi  sauri ya dure inda yabacin dan yaga idon ta bai jenan ba yafara yamutsa wajen cikin dabara yana cewa "ai nena yamutsa saboda murna dan burina yakusa cika na rabu da wannan  me idon cimolan 
Yana yi yana jan hankalin ta tsaf ya mutsuke wajen.
Ita kuma  kanta kaman ya fashe dan  murna mijin ta ita ya keso "tace muyi  addua  Allah yasa ta aiho yan 2 namiji da macce kaga atake  zamu  sallame ta ko  tunda kaga idan ta haife macce  ni bazan yarda ba dole sai tayi zaman haihuwan namiji  kaima idan ta haifi namiji  kace baka yar daba.
Yace "wannan haka yake Allah yasa  ta haiho 2 kawai

Fandau duk taji me suke cewa azuciyar ta tace niko  ai narabu da mutum nakama Allah dan shi yasan yadda zaiyi dani
Wani dogon rigan data hanya a bandakin shita sa tafito  da sauri  Hadim ta tashi ta kama hannun ta tazo  da ita bakin  gadon  tana cewa mekike jine ajikin ki ba inda yake miki ciwo
 Mekike sonci
Fandau da dama haka take so  dan jitake idan bata shan kunun tsamiyan nan ba baza man lfy  tace "kunun tsamiya
Dakuma kwakwa da dabino nakeso
Hadim tace "kai  zaki samu kwakwa da dabinon de  amma mu ina zamuga wani  garin balle wani tsamiya
Nabil ya katse ta dacewa  za asamu  awajin Zahran Usman  dan suna kawowa  sosai.
Hadim da sauri tadauki wayanta takira  Zahra  take cemata  tana son garin kunun tsamiya   "toke kuma yau
Acewa Zahra
Hadim tace "eh Wllh  akwai  albishr me girma amma  se kinzo da kanki dan  baza ki sameshi  a araha ba
Zahara tace "haba yar uwa dan Allah gayamin bama yar haka fa
"to tuda kince Allah  meyake sa mata jin yana yin su yacan za  kamar tashin zuciya amai  kwadayi da sauran su
Zahra "tace ciki mana
Hadim tace "tom shine  albishir din
Zahra tace  "dan ALLAH gayamin Gaskiya
Hadim tace "nataba shimiki  irin wannan wasan ne?
Zahra tace " a ah
Hadim tace to kiyar da wllh  inada ciki one month
Wani ihu Zahra tayi tare da kashe wayan Hadim  ta sauke wayan tana dariya  bayan ta daukowa  Fandau  kwakwa da dabino tace"kiyi  manager dawannan  kafin  akawo  meyawan  na aika  asiyo
Itade Fandau kwakwa da dabino ta karba  bakin har wani yawune  yake sinkewa  tafara ci
Nabil yace "yanzu waza afara gayawa  a gida?
 Hadim tace kai ma kasani  ai iya rigima mana inna amma  nafison nagaya mata da kaina ta fara danna wayan ta  yi calling  din  nombar inna Zainabu tana dagawa Hadim tace "inna ina kwana.
Inna tace "mun wuni lfy  dan munan  darene Hadim tace "lfy
Inna tace maganan zuwan yaran nan huto  modu da baso  yake ba saida yasan  yanda yayi basu  samu  viser bako dan nasan kede ba zaki  hana ba
Hadim da ita tayi kutun kutun yaran basu samu zuwa ba acewar ta idan sunzo  zasu iya sanin zaman Fandau  a gidan
Amma sabar iya issa
Tace "Ayyya inna  aishine nima naji shiru amma  suyi hakuri  ai mun kusa zuwa ma saura wata 3 sai muzo dasu tare
Inna tace "ai shikena sai kuyi zaman ku acikin wannan mahaukacin gidan naku
Danma kun kusa zama ku ukku  dan bazan fasa gaya muku idan kunzo sai Modu yayi  aure zaku koma ba.

Dariya Hadim tayi azuciyar ta ' tace bade niba inde kishiya ce akan yaran ki da jikokin  ki zaki yita gani.

Afili kuma tace "inna dama fa yatsmin?
Inna tace "gatanan
Dan Hadim ita kanta sai taji tana jin kunyan bude baki ta cewa Innan tana da ciki tayi  danhaka  take son tabata  yatsmin  din ta gaya mata.
Tana cikin wannan tunani taji muryan yatsmin  kamar zai fasa mata dodon kune tana cewan
ALLAH kabar mana matar  Big brother wllh anty Hadim  nayi messing  nake sosai.
Hadim tace "kwantar da hankalin ki yar uwa zan zomiki da alkairi
Yatsmin ce ta katse da cewa Hajiya anty sabon mota ne yafito kome idan mota kin san kalata ai  fari tas dan ni banason wani  kala idan kuma laptop
Nekin....
Hadim ta katse sa dacewa  dallah dakata duk bawan nan bane yafisu  wannan yafi komai na duniyan nan.
Yatsmin tace "meye anty
Hadim tace abinda kuka dade kuna jira ne nan watanni  8 zanba ku baby
Yatsmin tace "wai da gaske anty
Hadim tace "nata ba miki irin  wannan  wasan kuma kozan miki ai bazan kira a wayan inna ba itana  kira naga yawa na kasa dan Allah kigaya mata
Yatsmin tace Wllh tunda kikace  agayawa inna na yarda itama  yatsmin  ihun tasa ta fara
Tsalle tana cewa Wayyyo  anty Hadim sunan dan ki yaki yan uba wllh kamar  yanda muma bamaso  amiki kishiya haka dan ma bayaso tana ta ihun haka  Hadim ta kashe wayan
Haka suka dinka kiran mutane suna fada  shima Nabil  yana gayawa  abokan sa kusan wuni guda suna abu daya duk wani abin da sukeyi hankalin su yana kan Fandau ko motsi tayi se sunce yaya
Ahaka har doc yazo da iyalen sa kan dole suka sauka a part din Fandau

Fandau duk da basu gaya mata ba tagane cikine  da ita kwanciyar ta tayi dan ba taji dadin lbrn cikin ba  kuma baza tace taji ba dadi ba dan ita yan zuba tada wani zabin rayuwa dan ta siyar da shi  kyuta

A washer garin ranan ne gidan su yacika makil da mutane dan yan  kungiya su Chelsea  suka hada musu gagarumin dinner na happy  din kicin anyi taro sosai anci ansha hotona kam Hadim da Nabil sun sha yinsa wanda yawan ci yana shafa cikin ne  wani dafe  da cikin wani yana  kissing  din cikin fadin bidirin da akayi bazai  faduba  ai a take Duniya  ta san da Wannan ciki dan social media ba inda ba a watsa ba
Washe garin ranan baki yan taya  murna kasa sakat sukayi Hadim da Nabil muryar su har dashiwa yayi saboda yawan magana da gaishe gaishe da sukeyi  waya kan duk ko kunnawa basuyi ba dan sunsan nan ma wani damunne
Da kyar Hadim  ta samu daman lallabawa da yamma ta shiga wajen Fandau  tace" me kike sone
Fandau tace kunune na sha kuma
Hadim tace "kwakwan fa?
Tace "naci
Hadim tace "yawwa yar kanwata  kar ki zauna da yunwa kin ji ko tafice da sauren ta dan tabar mutane

Har kwana ukku sannan suka samu kansu
Aban garen Fandau ba abin da yake damun ta irin taga ta kasance da mijin ta idan  abin yaci wota  kamar ta daura hannun  aka tayi  ta ihu take ji wani irin tsananin shaawa ne yake da wai niya  da ita amma ba dama
Ga shi kullum tana sa Nabil  a idon amma kullum  suna manne da matar sa wanda ta kula yana mugun tsaronta  dan koci kekken kallo  baya tsayawa yayi mata
abin da yafi damunta ma idan sun shigo da safe  sundin da shafa cikin ta kenan  wai suna gaisawa da babyn su
To a wannan shafe shafen  Nabil yake sake tada mata da hankali danshi nasa da gayya ya keyi

 haka yanzu ma ana rige rigen gaisawan  atsakani su Hadim ce tafara shafawa tana  wani kissing
Din cikin
shiko Nabil a yau yakai  gejin da bazai iya control din kansa ba inde  ya taba jikin Fandau  dan haka yabasar bai  taba ba neman han  yandan zai yi mega ba daya  kawai yake da bara ya fado masa.
Yace "my one  yau fa zaki kaiwa sun Amjad ziyara dan suna kwarafi hakan
"tace zan so hakan amma bana son barin baby na nafita wllh
Nabil "yace shikenan dan baby saimu hanawa kamu sakan  kitashi muje kishirya dan ni a can zan wuce wajin wani meeting da zamuyi  a kan gai  yatar da Germany ta mana nake ganin bazan samu daman zuwa ba ina son naje na bada uzzuri na
tace "tom shikenan har a min Gyaran gashi ma dana finger
Cikin zumudi ya zoro wayan sa yakira  Amjad  Amjad yana picking  yace  a a Abu Bilal nan da watanni kadan dan tun ranan dinner da yan jarida da su yiwa Nabill tambaya wana  sunan da zai sawa abin da suka haifa yace burin sa idan macce ce yasa mata  hajara sunan ummi sa zasu kirata fujjirat idan kuma namiji ne Bilal  tun a wajen abokan sa suka fara kiran sa abu BilAL  abu BilAL
Dariya Nabil  yayi  yace  "ga ummu fujjirat zata kawo muku ziyara
"Amjad yace "taf gashi bama garin ma wllh sai  wajen  jibi ganin ba Abin da muke neyasa muka kai ziyarra torxar
tsaki Nabil yayi ya kashe wayan  yana kallon Hadim  yace "kinji ko da shegen gantalalun su shida matan nasa wai basanan sai na kaiki gidan doctor
Ya mutsa fuka Hadim tayi tace" ba inda zanje dama  gidan HADIZA ma ganin najima ban jebane Gaskiya bana jin fita kawai  mu zauna
Nabil yasan tunda Hadim tace baza ta ba bazatan ba

Ya rasa yazai yi dan inda dane hanyan kasan cewa da Fandau baya masa wuya Hadim tana cikin gidan zai ce zaije wani wajen  idan ta rako shi sunfito idan yafito  wajen ya kira wani daga cikin yaran sa yabasu motan yace su fita da shi karsu dawo har sai Yayi musu magana   a idan ya tabbatar  Hadima tashige  part din  sun shiku haka zai lallaba yashiga part din Fandau
Tunda yasan Hadim ba shigowa zatayi ba amma yanzu tana tan ta taro ban garen fandau dan idan ba baki tashi  ko dare yayi suka kwanta ba babu abin da yake rabasu da bangaren ko mai ita take yiwa Fandau
Afusa ce yace " shikena yameke  yafice yana fita wani tunani ya fado masa ai da sauri yayi inda motan sa yake yaja da gudu

Nabil  yace "Muktar kasan me yaka woni  doc yagir giza kai
Nabil yani sa yace wani  aiki  zaka min na temako  inaso a yan zunnan kaje gidana kamin wani temako
Doc yace" ina jinka
Nabil yace Hadim tuda tasamu ciki taki yarda dani  akan (sex) ni kuma bazan iya jurewa ba amma.
Akwai  abin da tafiso a fiyeda komai wato ta haifi me kama dani  sak
To ina son idan kaje gidan namaka tambaya agatan ta  meya kesa d'a yayi  kamar uban sa sai kace yawan yin (sex) yake kawowa  inde anayi  akai  akai toza afi haifan mekama da uba to idan kace haka zata yarda ka temaka min dan kasan bana cikin  masu ra ayin zina na dama ina rokon Allah yaya femin
Doc yayi shiru yana nazari can yace "shid abin da zangaya ma mata sun kasu  kashi kashe  alokacin da ciki yake jikin su a bangaren  saduwa wata zakaga ba abinda take so irin ayi ta mata har se kaza kana gajiya ma wata kuma idan tana da ciki ba abin data tsana irin namiji kai ko kusa da ita bata son ya raba harta hamshi turaren shi ma abin kine awaje ta
Idan kace zaka mata dole kaga zaka shiga haikin ta amma ko a likitance yana da kekyu idan macce tana da jaririn ciki yazama  ana yawan saduwa yana sa a haifi yaron me lafiya da kaifin kwakwalwa  amma tunda  bataso yanzu kayi hakuri kar atakura mata dazaran cikin  yakai watan ni kamar  4  zata dawo dai dai baza ta zauna har ta haihu ba zata denaji idan watanne 4 suncika  yace so hakurin yafi
Nabil yace "Gaskiya abin da bazan iyaba kenan inde baso kake na kusanci zina ba kayi  abin danace kawai
Doctor yayi shiru Gaskiya baya son abokina nasa yakoma wa zina dan yasan sa mayen matane  za ayi ta asa dayawa dan haka yace"ok
Idan na tashi zanbiya ta gidan ko
Wllh bazan iya jurewa har saika tashiba
Doc yace "to yanzu kana tufin idan ta ganmu tare ba zata gano ba?
Nabil yace  ah ah kai zaka fara zuwa idan kaje  tace bana GIda sai kace bari kakirani ni  kaga   sai naje baza ta gane komai ba
dukan kafadan sa doc yayi yace  "kaci sunan ka menasara  kana da naci akan abin da kakeso shiyasa duk abin da kake so kake cin nasara dariya Nabil yayi  dan sunan da ake kiran sa bazai iya irgasu ba doc yafita shikuma yadan kwanto da kujeran  yana lumshe ido dan shiyasan meyake ji ajikin sa cikin kwanakin nan game da wanan maiyar yarinyar da shigani yake lashe kuruwar sa tashi shiyasa ya nace wa nunanin ta dan da idan a nacewa mayu bai yar da basai yanzu da wuya idan wanna bashine kamu na maita ba

Kai my one kinada matsala wllh ke yanzu har kinyar da da karyan doc zaki fara takura min nifa ke kadai ce araina dama wahala nake  sha yanzu ina murnan nasamu hutu zaki ballo minda wani sabo
Hadim tace "wllh nikai na bana so dama can daurewa nake yi yanzu mun samu tasamu ciki muna murna to ga abin ga doc yazo da shi  kasan ina son yaro me wayo da hazaka a rayuwa ta kuma ga uwa uba mekamar ka  wanda she dane koda ko da watararan yarinya nan zata gano mutace tana neman danta idan yana kama dakai sak bata da hujja duk da yanzu ma bata dawani sheda ko akotu baza abata danmu   tunda tun farko mun toshe wanann hanyan  amma idan yayi kama da ita abin zaija hankalin mutane akan abin kuma
 mu  ma akarana kanmu ta haifa mana me kama damu wllh sai munfi son sa  dan haka zamu daure mubi abin dan doctor yace bawai dan ranmu yana soba.

Hakata yita lalashin sa dakyar ya yarda da sharadin so 2 arana bakamar yanda doctor yace so 3 ba
Shege Nabil shiyace wa Muktar yace amfison so 4 koso 3 dan yasa muyi so 2
Hadim  tace ajede kayi  kokari hakan ma

Baiwar Allah Fandau ko abin ba a mgn dan inban da Allah ya isa ba abin da take jawa Nabil da Hadima yasa bar mata abubuwa  gashi yanzu shi burin su yaceka ya barta da jaraba  da idan abin ya ciwota banda kuka ba abinda take se karatun Qur ani da yazame mata aboki koda su Hadim sunzu suna shirmen su a kan d'ansu itade karatun ta kawai take yi

data cewa Hadim tana son karin littafan andini  irin su umdatul  Ahkam
Hadim cewa tayi anki   akawo   mikin wato  keyar dangin  Malamai  zaki mana wani  addua da zakici  nasara akanmu  ko badan kar  Allah  yayi fushi dani ba Qur anin ma kwace wa zanyi kidena karan tawa

 da ta gama tunani  afili  ta tace idan in kwace ma ai bana cikin kaina zaki  kace ba dan ni duk inda nasani  a Qur anin  to inada haddan su aka  dan da kaina nake rubuta  allo ta

*Sister ku gwada kugani inde zaka *dauki abu karubuta da hannun ka tukun  ka karan ta haddan yafi zama  kowane irin karatu zakuyi ko da yarane ki gwada cewa su kwafe a pepper san nan sukaran ta zaki ga canji insha Allah*

 Tana cekin wannan tunanin  taji kofan Yayi kara a zuciyar ta tace yan  jaraban d'a
Nabil  akan sofar
Ya zauna ya daura daya kan daya yana wani ciccin magani shi adole anta kurashi Hadim  ce ta karasa inda Fandau take a zaune a kan sallalaya da  Qur anin a hannun ta tsugun nawa Hadim tayi  agaban ta tace yaya baby mu?
Fandau bata  yi magana ba
Tasake cewa "to ga abban sa yazo ba shi  taki ayanzu  *DAMAR* kine na kasancewa da mijina akan dole dan bayan da Zamuyi dan itace kadai  *DAMAR* mu  Hadim cikin bacin rai da kishiya   take wanan maganan dan yanzu tana dan jin kishin yariyar ta yiwani irin kyu jikinta yamirje sosai  laushin fatan nan ya sake karuwa ko ita kanta macce yana mata dadin shafawa  amma idan ta tuna da Nabil duk bai nuna ya damu dashima se taji sanyi  a ranta tunda tana yawan ce masa  my star kaji yanda jikin yarinyar nan yake da laushi  kuwa  tabe baki yake  yace  shi meye gamin sa da wani jikin ta baya tsayawa sauraron wani  abu  ajikin ta abin da yakai shi kawai yakeyi  shima akan  lole
amma   please ida muna tare karki kara kawomin zan centa wata banza yaci kunu kuma kamar da gaske ito ko  ta gama yar da da Nabil  ada baya boye bata ko mai  batasan  akan  Fandau  yazama  tan tirin munafiki  ba

Mekewa tayi takarasa wajen Nabil idon ta tabda hawaye dan da tasa aranta da ga yanzu ba Nabil  ba Fandau  har sai ta haihu  idan akayi dace ma ta    haifi 2 yanda suke so suka samu  ko  kwana daya baza ta musu a gidan ba
Rungumo ta Nabil yayi  cekin damuwa  na munafir ci  yace " shiyasa nace miki  karmu bi dokan doc  mubari kawai  dan  ni kaina ina cikin  takuran tursa sawa zuciyata abin da baya so
Cikin kuka Hadim  takamo habar sa dace yazamuyin  wllh dole ne nide  rokona agareka kar ka taba komai ajikin ta kayin aikin daya kawo ka kawai kuma dan Allah yau kar ka jima dan duk jimawan  da zakayi  yana gudu da zuciyata ne sai  har kafito nake samun  nusuwa dan Allah yau kar ka barta ta shiga wannan  toilet din na munafirci ta zauna har Baccci ya kwashe ka basai tayi wanka ba jikinta fes yake  ka tausamin kafito  dawuri shine samun  nusuwa ta
Tana gama fadan haka ta kwace jikinta tayi  waja da gudu
Ajiyan zuciya Nabil yasuke tare da
murmush yajuyo in da Fandau  take har yasha wanan  murdin din nashi  kuma sai  yatuno  da idan faskan sa asake  yake  Fandau  tafi  sakin jiki dashi shikuma yana son tasaki jiki dan yafi  armashi  a hankali yake yakawa har yakara sa gabanta ya sugunna dafda ita
Ita kuma tasa ke dukun kunewa cikin  shijab dinta take yi a hankali yasa hannun sa ya karbi  Qur anin hannun ta ya ajiye can gefe yasa hannun ya cire shijab din ma ya  ajiye ajefe !yasalam  yafur'ta ganin wani  arnen rigan bacci ne ajikin  ta wanda dashi da batu  duk  dayane  dan  net ne bai san san da yamekar  da itaba dan yakare mata kallo kirjin sane yaji  yabuga  bai samu sauki ba saida yajata ya mannata  kirjin nasa yace "me allo kin matani ko ni  ko ina can kewar  jikin ki yahanani  sakat.....
Fandau da bata gaskanta abinda  kunuwan ta suka jiye mata ba dago  kanta tayi  da sauri ta kalle shi
Sai a san  na yagano  tabar gazan da harshen sa ya masa  daure fuska yayi  yace  "dena kallo na
Fandau azuciyar ta tace  Ai dama nasami bane  kake so ba jikina ne kawai  shima dan amfa nin  kan kune kamar yanda matar ka tafada.


Yanayin yanda yake tafiyar ta ita da salon  sana mantar  da tunani ne  dan Nabil iya sarrafa macce halittar sace
kawai tsitar kansu  suka yi a gado
koda ya samu yanda yake so abin da bai taba yiba yau yayi  wato shiga Wankan  da Fandau  lif yayi  acikin  ruwan yana sauraron yanda wani  ni ima yake ratsa jikin  sa yana tuno  maganan ganun doc da yake  cewa ai banga lefin  kaba dan macce me jarirn cikin  ban yandan zan  kwatan ta maka ita ba koda yake kai ma shikaji  ka ki dime ai
Ajiyan zuciya Nabil sauke ya sake jan Fandau jikisa  rabin jikin su aruwan
wasanni  yafara yida jikinta yana tunanin ranan da yarinyar nan zata saki jiki dashi har tafara mayar masa da murtanin abin da yake mata Wayyyo Allah na yazanji ranan amma  wani zuciyar yace haba ai  raina ka zatayi  har tafara maka yanga da jan aji ya bata lokaci  anan toilet  din ma kafin  yana nado ta da towel shima daura towel din yayi  ya dauko ta bai direta ko ina ba sai gadon Shima ya hau yaja ta jikinsa yaja musu bedside lames Ahankali  yasake jan  barkon yarufe musu  rabin jikin su bai  san sanda wani Baccci me uban dadi  yazare shiba kojuyi bai  yiba kawai  bude idan  yayin yaci  karo  da agogan daya ke leke ajikin bango  ya nuna 7 na safe what yace tare da ture Fandau  ajikin yaduro



Aban garen  Hadim  kuwan abin tun ta na daukan sa wasa har yafara bata tsoro harta kasa jurewa taje  amma ta kasa bude security ta gwada sa nombar yafi a irge bai  bude mata ba parlour ta koma  tana dafe kirjinta  inda yake bugawa
Duk da tasan  Nabil  ya yabar wayan sa  a part amma  haka ta dinga kira tsabar kidima kiran wayan take taje ban garenta ta dawo na Fandau  ai security yaki buduwa kawai  sai  ta sa hannun ta dinka buga kofan da yaka nawani irin  karfene wanda ba abuka da hannu  kuma koda an buga nacikin ba zai jikaba yanda take buga kofan kamar  mahaukaciya tayi  duk ta baza gashin kan  hannun ta  ya kunbu ra suntum sabar buda kofa sai zugi yake mata amma sai  kara bugawa  take tana ihu muryar ta gaba daya ya dashe ita kanta bata jin me take cewa  ba
Saida tajji baza a jita ba daker ta iya jan  kafan ta ta koma general parlour  tana sauka idon yanuna mata  5 na safe ai bata san sanda tafara fatali  da kayan  parlour ba tana cewa lalale  yarinyar nan yau  taki  tazo  karshe  shekara  shida da auren bamu taba raba wajen  kawan da mijin ba sai yau  a dalilin ki bana son  cikin  saina zubar dashi  da duka ayu duk tayi watsi  da kayan  da yake parlour duk ta jiciwo  ta canza kama kamar  ba kita ba duk tajiwa kanta ciwo da gudu tayi..................

*Sorry masoyan - Hadim* 🙈

*B Jattko*
*DAMA TA yanzu yanzu  aka fara*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA TA*

        *NA*


      *BATUL ADAM JATTKO*

🌈  *Kainuwa* *writers Asso*🤝
*23*


Haka tayi ta facali
 da kayan parlour hatta Cup din da suke kan   dinning table tayi fa tali dasu farfasa pillow  kujeru da sauran su tun tana iya daga hanntun ta ahar ta kasa duk ta tattaka  glass duk inda ta daka sai tabbarin kafar ta yifito dan jinene yake fitowa sosai akafan  wani irin kara ta kwalla sanadin wani katon glass da ta taka yirif tayi kasa tasake fadawa kan wani. Flowers katon glass na wani   data fasa akife ta fada dan haka glass din yamata illa sosai  aciki jinine yake fitowa sosai  tun tana iya sanin inda take harta dena motsi

A gurguje Nabil yayi wanka tare da alwala yatada sallah har acikin sujjada saida ya roki ALLAH yasa ya shawo kan Hadim dawuri da ya iddar yashafa ya tashi yaje bakin gadon  yace ke dallah kitashi keje kiyi sallah kikuma zauna da shirin karban hukunci awajen matar da kika kwana mata da mijin inban da iskanci daki kaga zanyi Baccci meya hana ki tadani ya doka tsaki yafita

Fandau tabe baki tayi bayan yafita  can tamatse muku kaida matar ka me fuska kamar kosai da kumatun ta kar cin cin sakin fari  ta sake tabe baki tameke yayi hanyin bathroom tana gungune duk bakai kajawo ba gashi banyi sallahn asuba kazo kawani matseni ni niko baccecen ma baka barni nayi ba.

Ahankali kali yake takawa yana ayyana yana irin karyan da zai hadawa Hadim murmushi yayiwa kan sada yasa mowa kansa mafita harya sauka general parlour gaban sane yayi mummuna faduwa ganin yanda aka canzawa parlour kama tome yake faruwa ne ya tambayi kansa dan bawan da zaiga wanan parlour duniya guda yace mutum  dayane yayi wannan ai kin dan girman parlour yayi  full flogging guda ayan dan Nigeria afili yafurta ya ALLAH kasa bai karasa ba ya han gota yashe a kan dan matakalan da zai sadaka da dinning table da gudu ya karasa yana kiran sunan ta da karfi yajuyo da ita ganin  yanda katon glass  yake cake acikin ta jini ya gama rinar da rigan baccin jikinta bari  ba alaman nunfashi a tare da ita  jijjigata ta yadin gayi yana kiran sunan ta yau ba my  one din ma Halima Halima Halima Halima Halima Halima Halima  kawai yake kira
Karki mutu kitashe dan  ALLAH kinsan baza ki iya jure waba kika hada yayi yatashi amma yayi ya dauke ta kasawa yayi dan jikin ta yasake gaba  daya ga Hadim dama da kiba da gudu yayi ban garen masu aikin sa yazo d mata biyu  a bayan sa suka kinkime ta sukayi waje da ita abayan motan suka sata Nabil yashiga kanta ya daura akan jinyar sa yashiga hure mata ido wai ko idon zai bude driving  yafigi mota  sai  asbitin su doc Muktar  a Emergency aka wuce da ita  doctor Muktar bayanan amma akwai kwararren doc
Doctor jamx
Cikin kwarewan aikin saba afi minutes 20 yasamu nufashin ta ya dawo san nan yafito ya samu Nabil  da  yake tafaman safada marwa yana  Addua Allah yasa kar  yara sa Hadim  Halima kar kitafi kibar ne acikin wannan tarariyar rayuwa da kika jefani
Yana haka yaji doc ya dafashi yace matar ka tafar far fado amma jinenta yahau dayawa zuciyar ta tana cikin barazana amma  za ashawo kan abin sai de yanzu da gaggawa muke bukatan jini dan haka zamu duba naka ajikin ka idan yazo daidai
Nabil yace nawa zai mata amma nafi son fara ganin ta doctor yace a a nabari ana mata aikin ainda tashi raune dan nacikin har yakusa taba hanjin ta kuma jinin yajima yana zuba shine dalilin suman ta.


Bayan doctor Muktar yazu ya shima ya shiga yaduba ta yace "kakasa min bayanin waya mata haka dan  nasan bazai wuce masu son ganin bayan kaba  koci kin kungiyan ku kana da munafu kai balle wasu
Cikin biyu daya akazo nema   kokai  akazo mema ko dama ita din suka yi hari dan suzubar da cikin da sukaga duk Duniya kungiya sunnu na so ga cikin kodan Wannan alkawari da suka dauka za abawa danka na fari zasu nemi ganin bayan cikin  dan   bawan da aka tabayiwa Wannan happy a ciki ni naga bakin kinci ciki  kiri kiri a fuskan wasu kuma wllh sai munyi bicike tunba wanan ocash  dinba shege makiyin musulumci
Nabil yace "ya isa baruwan ka ame zaka zargi yan kungiyan mu duk halaccin da suka nunamin nide kawai naje sallah nadawo nagan ta cikin wanan hali.
Doctor yace kai aiba kasan meson kaba  nan da minutes 30 zata farka  zan duba  cikin idan babu  wllh  zan tsanan ta binciki kuma kasan halina se nagano  dan ta kan security dinku zamu fara
Nabil cikin fusata yace "ina ruwanka da wani bicike  ciki kuma da kake cewa sai kaduba naga de Hadim ba patient dinka bace ko zaka nunawa doctor aikin sane wanan ai shi shigine.
Muktar yace ai Hadim kowani  asbitin  akai ta nine doc ta balle namu
meyasa baka son naduba cikin matar ka kode da gaske  kana min zargin maitan ne
Nabil tsaki yayi yace wayasani wanan naci naka
Doctor fita yatashi yayi yana cewa zakaga maita wawa kawai
Nabil fuskar Hadim yazu bawa ido wanda yake nade da bandage  jikin shi yayi sanyi yanzu data  kashe kanta da duk Duniya ya iba
hannunta yaga yafara mutsawa yayi saurin rike hannun  yana kiran my one  kin tashi  juyowa tayi ta kalleshi tace bani ruwa da sauri yabude fridge ya dauko  roban ruwa da Cup ya siyaya dan tada kanta yabata cikin dashe shen muryanta  Nabil danme na rayu danme ban mutu ba tunda zan farka natuno da Wannan kayan bakin cikin  Nabil kaine ka iya Baccci da wata macce a daki daya  har waye wan gari kuma ka canza security bayan na gayan maka duk jimawan kada bugun nun fashina yake tafiya 
Nabil yace "kibari kisamu lfy ni yanzu  lafiyan naki shinafi bukata doc yace zuciyar kiyana cikin hatsari  duk keki kajawo muna zaman zanan mu gashi kin kawowa kanki ciwo

"zakace man nina kawo bayan kanane man fasanin zuciya.

Shama cikin bacin rai yace"nace kibar muganan nan sai muje gidan idan ba tozar tani kikeson yiba a Duniya
Kuma tunfar ko sai da nace miki bana son wanan abi amma kika nace akayi yanzu gashi yariyar ta samu ciki idan bakiye hakuri mun lallaba mun rabu lafiya ba zaki janyo min abin fada aduniya  kuma kema zakiji kunya a gun kawayen ki kuma abin da kike gudu dole ya faru wato kishiya
Hadim ta yarda da maganganun Nabil gaskiya ne in har Duniya tasan ta ajiye wata dan ta haihu taba ta  babban abin tuzar cine
yanda taga Duniya tayi murna da cikin tah
idan asirin su yatonu haka za ayi  Ala wadai dasu
da tatuno hukunci da gorin da inna ZAINABU zata zartar akan ta abin yasake bata tsoron dan wata kina tasa a saketa ma
Hannun Nabil ta jawo tarike  gem tace dan ALLAH  gayamin meya zaunar dakai adakin   ta

Shiru yayi can yace kin san agaban ki kafin na shiga nasha magani nako?
Hadim jijiga kai tayi  data tuno eye yasha maganin sa wanda yake sashi mugun baccci yana amfani ne dashi duk ranan da yabuga  wasa kuna yan ball da yan rack celing dole sai suna dan taba shaye shayen  duk da Nabil wada zai sashi Baccci kawai yake sha bawan da zai buguba da yasamu  yaware gajiya dama dazai shama kamar zata hana shi tunda ranan bawani wasa sukayi ba ahe rabon za ayi hakane
In hakane ko bacci yayi dan duk sanda yasa shi idan minutes 40 yacika zaiyi Baccci na awanni 9 cif
Wani dogon ajiyan zuciya ta sauke

 tace "wllh my star na shiga farga ba duk ranan da kaso wata aranan ajalina zai cika
Nabil da yayi murmushin cimma nasara dan dama bawani magani da yasha asalima kolban Empty ne yi hakane dan ya huta da Fandau  amma bai san Hadim zata jigata haka ba.
Yace Wllh my one nima ban san me dalilina nashan saba ahe wanan kaddara ne Allah yarufa asiri da baki tona mana asiri ba da nashiga wani hali ai  wanda zai sa makiyana sumin dariya masoyana suji haushina
Ni farga bana ma wllh wannan dan iskan yace wai dole sai ammiki scanning andu ba lafiyan abin da yake cikin ki
Dan ALLAH karki yarda
tace "bazan bariba

dakyar doc yarabu da maganan ganin cikin.
Nabil bai bar asbitin ba
Sai washe gari dan shiyake zaman jinyan  zaije gidan da zumar dauko musu wayan da dan  abin zasu bukata
Har ya gama abin da yakeyi zai fita yada ga kansa ya kalli part din Fandau   saida yajuya kamar  zai fita yaji bazai iya jurewa ba ya ajiye  througley hanun sa ya fara takawa ahan kali har yahaye da zai shiga saida yayi addua Allah yasa kar yaji sha awan ta yakuma janyowa kansa wani  abin bayan bai gama da Wannan bama
Fandau da taci gayen ta cikin kananan kayan da Nabil yasayo mata tana zaune a gaban mirror  tana tafaman jan kashin da wai ko zai kamu waje daya amma  ta kasa tsaki taja ta sa hannun ta biyu cikin tsakiyan gashin tafara bazashi  hashi cikin jin haushi  tana cewa kar ka kamu mana bataji bude kofa ba kawai tse ganin mutum tayi ya zuba mata ido tacikin mirror fuskan saba yabo ba fallasa
tayi saurin janye nata idon ta sun kuyar da kai
Ahankali ya tako ga banta yasa hannu yadauki  brush din da yake kan mirror ya sake zagawa bayan ta ya daga kanta  Ahankali yasa brush din yafara taje kan yanda ya daga kan nata yarike dole sai suna fukantan juna  dan seta ta yayi da fece din sa sai da ya gama kontar da gashin ya ajiye brush din yasa hannun sa yafara shafan gashin  da hannun sa  yasun kuya ya daura kansa dai dai kafadun ta ya kai bakin sa daidai kunne ta a hankali yace "yayi kyau
Sun kuyar da kan nata tayin
Ya sake cewa " kekam ba kya magana badan ranan da na fara ganin ki naji surutun kiba da sai nace kode kurma ce
Daga idon ta tayi ta kalle shi shima ita yake kallo ido ta lumshe kallon da ya mata ya gama kashe mata jiki dan dama tana cikin bukata
Shima yanda ta lumshe idon sai gashin jikin saya tashi bakin sa yakai kan idonta yayi kissing din dukka idon
Yasa ke cewa "ya bakisa turare ba ko yakare girgiza masa kai tayi  alaman a a
 yace " me yahana kisa shi  dauko kisa kinji
Mekewa tayi  taje wajen whadrop ta dauko turaren  a inda take boyewa dan kar Hadim ta gani kamshin ko taji baza tagane ba dan irin wanda ta ke amfane da shine kamshin sa yariga disha she a hancinta
Ta juyo da zuman ta shafa taga ahe nan dinma biyota yayi
Yasa hannu yakarbi turaren yashiga fesa mata yasa hannun sa cikin riganta dai dai kirjinta yadin ga fesawa duk inda turaren ya taba sai yasa hannun yahafa  da yagama fesawa ya cusa fuskan sa tsakiyar kirjin ta yana goga fuskan nasa
ya tsukun na dai dai cikin ta yanacewa  duk kinsani aiki daga zuwana nakasa gaisawa da baby na yayi maganan yana Shafa cikin nata cikin salon sa yazura harshen sa cikin cibiyar da yafara mata wanni irin tsusa da shar shen acikin cibiyan  ta
 duk dauriyan Fandau  danuna ita abin da yakeyi bai dameta ba yau kasawa tayi
bata san sanda tayi wani k'aran dadi ba tafa da jikinsa shiko kidimewa yayi yadauka kowani abinne zama yayi yajan yota jikinsa yana tambayan ta me yafaru ya akayi inane yake miki ciwo?
Kunyane ya hana ta bude idon ta
Yace "kiyi magana mana
Cikin kunya da tsoro

  tace " bakai bane kamin  cakulkuli da harshen ka acibiyata
Ba sarwa yayi yace "ooo baby na gaida  daukan ta yayi  cak yayi kan gado da ita abakin gadon ya zauna yakamo hannun yana shafawa  sai dayayi wasanni sosai da ita da yaga zai gala baita yameke yace "kiyi Baccci  ana son macce me ciki ta yita yawan Baccci
Fandau sai lumshe ido take danya kwadai tar da ita sosai amma gashi yana shirin tafiya yabar ta da gwanjabo har juya bata san lokacin da ta meka hannun ta takamo nasa ba cak ya tsaya cikin mamaki ya juyo yana kallon ta tana wani lumshe ido da matse kafafuwa
Yagane yanayin ta tsaf
tsugunnawa yayi yana kallon cikin idon ta har yanzu bata saki hannun nasa  ba daya hannun yasa yana Shafan gashin kanta da yadan baje
Shikan sa yana mararin hakan amma yasan idan yabiye wa hakan  akwai matsala Hadim tana  asbiti
Afili
yace  "dama kina son abinda ake miki dan munafirci baki taba nunawa ba
da sauri tasaki hannunsa ta juya tayi ruf da ciki ta boye fuskan ta tana dan cuccusa kanta  tana dan girgiza  alaman  a a
ganin yanda Heep's dinta yake girgirza dan jujuya kai da take wai alamun ita taji kunya ai bai san sanda yabi lafiyan gadon ba Shima........


*Masoyan  Falmata Fandau wannan page nakune*
*Kusha shagalin ku kafin Hadim  tawar ke tazo*

      B Jattko
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA TA*


 
               *NA*


 *BATUL ADAM JATTKO*

*Maryam Ahmed*
*Rayuwan Yusura*
Kinason Hadim

_Inakike_
Sawwwama
_Keda duk masoyan ina gdy ALLAH_

_Zauren Beibei  Isa_
_Wanan page_  _nakune_

🌈Kainuwa writers  Asso🤝



*24*


 Yace "tom tunda kema inaso yanzu komai yazo da sauki nima na huta  daga yau ke zaki dinka yin komai  dan nima da nakeyi da wahala nakeyi  maza tunda de kina so sai kiyi da kanki  Fandau jitake kamar  katifan ta tsage ta shiga
Yace  oo ya  fara dan inada abinyi inkuma ba kyaso ni inada abinyi 
Ahankali tace "nide a a bance ina soba
Yace "nikuma nace  Eh kina so
Tace  "toni yau she nace inaso?
Yace "ai dama bada baki kika fada ba
Tace to ame na fada mekewa yayi zaune
 "  yasa bakin sa yahura mata ido yace "ga inda ya fadamin nan ya zuba lumsassun idon sa cikin nata Ahankali yasa hannun sa yana mata tafiyan tsutsa a saman idon nata yace" gashinan haryanzu yana  gayamin
Dan haka fara kawai
Tace "toni yazan yi
Yace "ni yana keyi
tace"nede bazan iyaba
Yace  "tosai kinyi  tace a a
Yayi yayi  tace  a a
Da yaga bazata yin ba bata masa lokaci zatayi.
Yabata  rai yakoma Nabil dinshi sak.
Yadaga mata uban tsawa yace  wllh idan na irga 5 bakiyi yanda nace ba na lashira sai yafiki jin dadi uban wa yace kikamo hannun na dazan fita
Cikin tsoro da dabar barcewa tace  "zanyi
Murmushi yayi  yakoma yakwanta rigingine yace fara da ciren kayan ki sai  kicire min nawa
Hannun ta na karkarwa ta fara cire rigan ta ai ya nacin karu da abin da yafi son dan dama Fandau ba bra take sawa ba
Lumshe ido sa yayi yasake  budewa yaga ta sunkuyar da kai
Yace "sikek din fa
Shima tacire sai  pants kawai  tabari nuna mata nasa rigan yayi da  ido  alaman tacire
Idon ta tab da hawaye ta fara balle bottle din rigan nasa shiko sai faman ajiyan zuciyar yake  sauke wa yanayin yanda take gudanar da abin cikin sanyi yafita komai dauke masa hankali
Data gama cire masa rigan saita sake sunku yarda kan
 yanu namata wandon sa da yatsan sa yana daga mata gira
Da sauri  ta daga kaita kalle shi
 tace "shima ni zan cire.
Yace  anawa kika siyoni da kike jiran nayi miki.
Cikin kuka tace "nide bazan iya cire maka wando ba
Zoro ido yayi yatashi zaune yace "mekikace ni kikecewa baza kiyi abin dana saki ba
Ba tayi magana ba ta juya masa baya
Haushi ya kamasa yaju da ita da karfi  afusace yace  "harkin isa kijuya min baya dubeki kidubeni ko kina tunanin kina da wani  matsayine awajena yasa zaki wani faramin jan  aji to tsaya kiji matsayin ki dayane  mun dauko kine kawai ki mana kina gamawa zaki kama gaban ki
Dan makin samu naji tausayin ki zanbaki jikina me tsada zakiyi  yanda nace ko sai nayi miki abinda zan baki mamaki  yayi kwafa
Tace "zan cire
Komawa yayi yasake kwanci Bottle din ta fara ballewa sannan ta zuge zip din Ajiyan zuciya ta sauke da taga da gajeren wando na adidas aciki  ahankali tadin ga jan wandon tana bin silbeben ciwoyen sa da kallo wanda ita kanta ta gaskan ta shidin me tsada ne ba karya yayi ba hata cire  tadaga kai tana  kallon sa yace "saura gajeren
Yanzu kam tagama kulewa dan haka tarufe idon gem taja da karfi.
Dan kara yasake yace "Wayyyo yi Ahankali kar kijimin ciwo nace na fasa itako Fandau  Azuciyar tace fasa mana da yafi ai
Yace "kinja ido kin rufe nizan fara kena  dan Allah kayi min rai wllh bansan yanda zanyi ba
Yace bude idon ki na gwada miki

Azuciyar taf nabude nagan ka ahaka
Yasake cewa nace  bude idon ki na gwada miki ko
Koda yake
 kema kin iya bakina gani ina yiba tace "aini bazan iyaba
Yace "
Ahe da wuya idan nagama ko godiya bakya min
Tomaza yi abinki banan tayaki ba dan nima
Baki taba tayani ba dan haka nima bazan ta yaki ba

 tayi shiru wani uban sawa ya doka mata wanda bata san san ta fada jikin nasa ba dagota yayi keni dokine da zakimin irin wannan hawan ko haka kikaga ina miki  itade duk a tsora ce take dan haka awai sai  tafara  yi masa yanda yake mata amma cikin zubar da hawaye  ba abin da bata masa ba awasanni shikan sa yajijina mata dan yafita hai yacin sa sosai  sai sun batu yakeyi
 Cikin da shewar muryar yabude idon sa da kyar ita ma nata idon arufe yake yace "ashe da libar ba jaka bace me daukan darasice daganan yajuyo da ita ya mata rufa..

*Nima kam da godu na fita dan nima yar uwar Hadim ce idona bazai iya gani ba*

  Da sallama ya shigo  dakin yasa meta akwance  bata amsa ba sai juya idon ta da tayi ta kalle agogon dake jikin bango  ta sake kallon  sa
har ya karaso yace "sannu my one  yajiki naki
Bata amsa ba tace meka zauna yine haka  kajima tun 7 nasafe amma yanzu  gashi sai 2 kazo  har lokacin sallah yawuce banyi ba nayi yunkurin nata ka kafan bazan iya takawa ba.
Yace" Ayyya  please  my one  wllh miss call  na tadda awayo yina ba adadi shine dana zauna benayi wannan  zaman  tace kaima da gangan ne taya zaka biyewa wani miss call  basai  ka yine ka kwana baka karasa ba

Yace" ai bana  permanent nabi ba kawai na family and friends  nabi kinsan wannan ya zama dole
tace"nide ka kaini  toilet kar lokaci ya kure banyi ba
Da sauri  ya ajiye kayan hannun sa ya dauko keken ya temaka mata ta hau  ya turata 

Washe gari Nabil yace zaije gida Hadim tace kayi me idan wani  abun kake son dauka kasa su jooppy sukawo maka mana yaran sa kenan
Yace "ba abu za adauko min ba training zanje
Tasan ni dama Nabil da safe idan baiyi training ba toba zaman lfy duk  jikin sa sai ya dinga masa ciwon yadinga mika kenan harsai yayi yake jin dadi dan
tace tom amma kar ka  jima irin na jiya  bazan jima ba ga wayo yina ma anan.
Bayan fita dasu ba
Da yafita
 Hadim wayan ta ta dauka ta dinga kiran yan uwa da abokan ta Awwwa kanwar Nabil wanda suke uba daya ta kira a karshe
Awwwa tace "se ANTY  ni Wllh two months  din nan ma kamar ba zai zo dawuri  ba naga dana ba nakeji  bani kadai bama  duk family  ban taba ganin abin da abba yake so kamar cikin jijikin ki ba har lisafin watanni yakeyi  iya tace ko sune suke da ciki bai taba rike date haka ba yanzu har  tsokanan sa su ummi sukeyi  wai abin cikin kwan yafi  kwan dadi
Hadim bata san san da hawaye ya sarto mata ba inama wanan dan jinin tane ita zata haifa yanda kowa yake nuna soyayya  gareshi  Awwwa da taji shiru tace Aunty"  kina jina
Hadim da kuka yake  shirin kwace mata tayi saurin kashe wayan.
Atake Awwwa tasake kira Amma  bata dauka sai  akiran na 4 ta dauka dan tasan Awwwa da shigen naci
Tace"anty  lfy
Hadim tace  amai ne yazomin dan ina fama dashi
Kai sorry anty kice dan nawa yana baki wahala
Hadim tace ki gaida iya ita ce kawai ban kira ba se anjima zan kirata idan naji sauki

Nabil  a gurguje yayi training din ya shiga  ciki direct part  din Fandau yawuce

sati guda kullum haka kuma kullum  sai yajima amma sai yalalo karyar da zai kulla Hadim ta yarda  har aka sallame su suka dawo

*Bayan watanni* *biyu*
Lokacin hutun su yayi amma  sunyi iya yin su sunra sa mafita ya zasu suyi ne da Fandau  idan zasu tafi
Hadim tace "kawai mubar mata komai na abin ci wanda zata bukata sai  musiya mata sim a Wannan karamin wayan nata  idan mun samu lokaci muna kiranta munajin lfy yar danmu ko

Nabil yace " gaskiya wanan ba shawara bane idan  kuma tana da number wani  akan ta takira fa?
Hadim tayi shiru can tace "kaman ta  ita ana ta daukan nan sudanne ko ta kira sake batar dasu zatayi

Tana zaune da hotonan  mama ta da bagana da ya zame mata kamar akin yi tana musu magana 
Idan inda zasu bada amsa ne sai tayi irin muryar su
Tace bagana Allah dai yasa baki  auri shateema ba dan banji  ina son saba sai yanzu  ina nan zuwa dan nayi  rayuwan da shi zan koya masa sona kuma ma yanzu nayi kyu zai sone  shine dai dai dani

Jitashi cikin karaji  Nabil yace "aida mashine dai dai take  shine kalanki  amma zan miki last worning karki karamin maganan almajiri  agida na dan da cikin mu ajikinki kibari  zai kin sauke kar kidan gan tamana shi da wani wawa
itama
Fandau ranta ya baci dan ta tsani taji yace cikin su dan me zai dan ganta da Hadim bayan ita bata iya samun cikin ba.
Afili ko tace "ALLAH Shateema  ba almajiri bane yanzu shima me kudi ne dan yana da shago akasuwa  kuma ba wawa bane duk  yafi almajiran  baban mukyu da gayu ko kai baza ka gaya masa gayu ba.

Ai Nabil  wani irin bacin rai  yaji  bai san sanda yadaga hannu yazuba mata ba har yasake daga wa Hadim tayi  saurin shiga tsakanin
Haba meye haka kana son yimana asara ne zaka mata irin wannan marin idan ta kife fa
Nabil yakoma gefe yana wani irin huci sai iska yake ja abaki yana fesalwa dan jiyayi wani irin sanan shateema  da baima san saba yaka mashi afili kuma

Yace "ke bakyajin yanda take amba ta mana sunan wani da jikin mu ajikin ta
Hadim tace "me naka ba saurayin ta bane ina ruwan ka idan tagama mana  aikin taje a auresa kum.....
Ai bata karasa ba ita ya daga hannun sa zai wanka ma marin amma kome ya tuna sai ya dunkole hannun  ya taushi daya hannun sa
Ita  ko Wawuyar bata gane wani kishi bane yakama mijin nata
Sai matsawa da tayi kusa dashi hannun ta tallafe da kumatun ta
Tana cewa "my tsar yau ni zaka mara akan na dangan ta danka da almajiri  lalah nayar da maganan Àmeena da tace idan na haifu sonda kake min zai ragu zaka bawa danka rabi tun kafin yazo Duniya gashi ka tabbatar min da haka  inama ni zan haifi dannan da cikina
Nabil juyawa yayi  yafice adakin dan ransa amugun bace yake
Hadim ta juya ta kalli Fandau  ina wayan nan da Muhammad ya baki tun a meduguri?
Tace "gashi can acikin loka
Hadim
Tace" dauko
Fandau taje ta dauko wayan ta mekawa Hadim
Takar ba tace  jonata a change bari nasa miki  sim dan mu yau zamuyi tafiya zamuyi wata daya kafin muzo shiyasa kikaga munci kamiki kicin da kayan abinci  ki kula da kan ki sosai da abin da yake cikin ki ta bude wayan ta sa sim din ta mekawa Fandau
A daki ta samu Nabil haryanzu cika yake yana batsewa
ta matso kusa dashi tace kaki tsayawa kayi sallama da babyn muko to muyi wankan sai muje muyi sallaman  ko

Dasu ka shigo  sallama har lokacin  Fandau bata dena kuka ba Hadim  tace "Kaga ko har yanzu baby bai shuce bako
Hadim ta karasa inda  fandau take tace "munzo yin sallama d babyn mu tabude cikin Fandau ta fara shafawa cikin da ya ke a shamile baza ka  taba cewa a kwai jaririn dan wata 3 acikin ba dan Hadim dayake tana da teba zugudan ta yafi  na fandau me cikin ma sosai har
Tace "kai baza kazo kayi  sallama d baby namu ba
Nabil ya tabe baki yace "ki gai sheda shi kawai dan har yanzu kunnuwan sa basu dena bashi sautin  abin Fandau take cewa ba
Da zasu fita Hadim ce a daba Nabil  yana baya saida yajuyo yayiwa Fandau wani kallon  zaki sani  yafita
Itako fandau kuka ne ya kufce mata a zuciyar tace yanzu mutanen nan da gaske bulaguron zasuyi harna wata guda subar ni nikadai bawan nake gani bansan dare ba bansan rana ba sai na kalli agogo

*Barno birnin SHEHU*
*Yarwa yarturam ajaye bula maiya maluma*

Bakaramin murnan ganin su akayi ba fadin yanda sukayi murna bata lokacine
Harwani kwarya kwaryar walima aka hada  wan yakasu kashi kashi  na abokan sa daban na family daban 
Amma duk wannan ba damuwan Nabil bane shide damuwan sa yaga Fandau wanda bai taba sammanin bazai iya jurewa ba sai da yayi nesa da ita din
Jiyake kaman bazai  iya rayuwan dan bacci wannan yakagare shi yakira number da suka sa mata a wayan yafiso airga a kashe
Wani da bara ne ya fado masa yayiwa kansa murmushi   yasan inna ZAINABU ce kawai zata iyayin wannan ai kin nan dan haka ya juya yacewa Hadim  zanje gidan abba isa dan yasan nanne kadai zaice  zaije  bata ce zata bishiba ta tabe baki tace adawo lfy

Inna dama nazone nagaya miki anne meni meeting kasan waje  amma nasan idan nace zanje Hadim zata ce saita bine nikuma bana son wanan yawan tafiye  tafiyen har sai ta haifu shiyasa nake son idan muka zo yimiki salama sai kice sam ita bazata ba dan kar ta wahala
Inna ZAINABU tace yo aikin bansa dama ba kai ka sangar tar tada hakan ba macce kamar jela ko ina da kai  ai ko ba kace ba bazan bari ba kubari idan ta haifanin jikan tabani kuwuce  birnin sin ma
Nabil yace "to amma karki nunan ni nagaya mikin dan  ban ma gaya mata  tabiyan ba
tace to sarkin  yan tsoron Hadim ya tashi yafita
Yana murmushi

Nabil ne suke tafiya da sani wato wada yakai  Fandau kona ce wanda yasan sirin su  suna tafe akan hanyan suta zuwa sheuri Nabil ya juya yace "sani kode mutumin nan yagane ni na dauke masa yarinya ne amma me dan na aika masa da abin alkairi zaice sai nazo yaganni
Sani yace "haba yallabai taya zai gane bayan bawan da yasan wanan sirrin sai ni sai ku kawai  alheri ne yaga yayi yawa  kafasa masa gida za amasa ginen zamani  ka dauki nauyin matar sa za amata aikin ido  a kasan waje  kaga ai dole yanemi waye ya masa wanan abin alkairin ai
Nabil yace" to yanzu wannan har yakai  yace muhadu agaban sarki SHEHU  nema nafa yayi afada ina tsoron ace yasani fa kasan Malaman nan fa anya ba istahara yayi yagani ina tare da yarsa ba
 shikan isan da yatuno da haka sai gaban sa yayi wani irin faduwa har sai da yaji hanjjin cikin sa ya muda.....

*Muje zuwa*
*Me zannah  zai* *cewa Nabil*
*Nabil zai samu* *daman lalabawa yaje Landon kamar yanda yatsara*

*B JATTKO*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA TA*

         

           *NA*



 *BATUL ADAM JATTKO*




 *Mmn Waleeda*
*Ina miki fatan* *alkairi da fara wanan kaya taccen* *novels naki*
*YAROMA NAMIJINE*
*ALLAH yasa agama cekin sa a*


_Godiya nake_
_Marya_
_Ummiee_
_H Bilkisu dan mlm_
_Amal biebie_ 🤝❤



🌈Kainuwa writers Asso🤝
*25*

Sani mai da hankalin sa yayi kan titin yana cewa "insha Allah ma yallabai ba hakan bane ma  haka suka karasa cikin sheuri daga shi sai sani amma da motocin security  dinsa  suke binsa abaya  dan idan zaije irin wanan wajen da security din sa yake fita  suna kara sawa fada dogarai da mutane cikin fada harma da yan   sarautan ma kowa iban gaisuwa yake a wajen *Shidmas*
Dogare sai washe baki suke dan wanan ganin suke cewa farin gani  dan ganin Nabil  fari ganine cikin kasaitar sada iya rike girma   yafito yana daga musu hannun biyu biyu sai kirari dogarai suke masa yaro da kudi abokin manya mekyu d kyun hali makiyan fadawan ka aljanin kudin dan Habubakar jikan DAMASAK har suka shiga ciki direct cikin fadan suka
Nufa sai da suka kai inda yaka mata su tsaya suka ja burki security din har zasu bishi ya daga musu hannun cak suka tsaya daga shi sai sani suka shiga  wanda yafara cingaro da shisai da gaban shi yayi mugun faduwa  wato Malam Zannah Modu sai yau yagan shi ido da ido dan dama wani lokaci yana ganin sa a TV  suna mugun kama da Fandau
Zubewa yayi  agaban su yana kwasan gaisuwa dan da hakimai da sauran yan kusa da fada suna nan  lawuwan girgiri  ne yafara magana yace  a a manyan gyaran wasa Muhammad Nabil  hasken Barnawu
SHEHU  murmushi yayi yace  dana yaushe kazo garinne sai jiya Malam yake cewa wai wani ya tura  turawa gidan sa sunyi aune aune sannan yaturo wani har sun fara gini anfasalta tsarin part na mata acikin gidan inda ake karatu dare wai matan sa ake  ginawa idan aka gama sai sukoma ciki  da kuma wasu manyan kudi shine yake sanar dani da ga gomnati ne ko  meye muka binci ka ba daga gomnati bane
Shine ya da katar da   aikin dan Malam yace bayaso sai yasan wannda yayi masa tukun shine da wannan yaron naka yaje duba ma aikata nace akawo min shi  yana zuwa naga yaron kane dan nagane shi nace yace maka kazo kugana da Malam din mana  shima kansa Malam  kaine baka sani ba kodan bakayi rayuwan nanba ai mutumin baban kane sosai 
Gashinan matsa kusa dashi kugai sa Nabil tashi yayi
 cikin baduwar gaba ya karasa inda Zannah  yake ya zube guiwowun sa yace Baba barka da warhaka

Dafa kansa Zannah yayi yace "modu kaine haka kai kazama haka  Nabil ya daga kai ya kalle Malam ya sake sunkuyar wa
Zannah cigaba da cewa ni ban sankai ne meyin wanan  a bubuwan ba duk sunbi suncan zamin sunan ka wani shidmdas  wanan sunan kawain nake ji  ana cewa me kyauta to dana jin ace dan kwallone ban damu na bin cika nasan waye ba ana fadan alkai randa kakeyi abin da yafi burgeni shine daukan dauyin yan shijira da kuma bada tallafi magani ga mata masu ciki da kananan yara da ka dauki nauyin
bazan manta ba lokacin da aka fara daukan ka kwallo saida na kira Habubakar nace bakyu wasan kwallo ya hana dansa amma da yake anan  abin cinka yake dana kuma na al umman da ka dauki nauyi kaga bai hanaka ba yanzu nima nabin cika naji boll ba haramun bane inde zaka tsare mutumci adi ni Alhamdulilah naji ance kana da kishin addinin ka
Kuma nima na sheda
Allah yamaka Albarka duk wajen suka amsa Ameen Ameen Ameen

Nabil sake dunkufar da kansa yayi
Azuciyar sa yana cewa
_Da gasan mena maka da bakamin wannan sa albarkan ba_
Bayan  anga ma  wasu tattaunawan
Malam yace" kiramin Habubakar din   Nabil ya dauko wayan sa yakira abban sa yame kawa Malam
abba yace "Nabil fasa tafiyan yau din kayine
Zannah yayi murmushi yace "wannan baban Nabil ne  abba ko daga Baccci  aka tashe shi zaigane muryan malamin sa   kuma uban gidan sa zannah modu
Kamar yana gaban sa sai na yadan rissina yace"gafanta ina wuni ya fama da jama a
Malam yace "Alhamdulilah  yau  gani ga dana ko jika zancene kuma me sunana

Cikin zunudi da murna abba yace duka duka zaka kirashin gafarta dan yaji dadin kiran Nabil  da yayi da me sunan sa dan Nabil tabbas me sunan zannah ne
Zannah yayi murmushi  yace"idan ka samu lokaci kazo inada magana da kai
Abba yace  malam daga yanzu zuwa lokacin da kake son gani na duk lokacin kane yanzu kake son kaganni
Malam yace "Eh to kazo yanzun

Nabil _azuciyar sa yace meyake faruwa yau dan ma abba yasan mutu minnan haka anya ban shiga ukku ba_

Malam yaka shi wayan yame kawa Nabil
Malam
 ya juya yana kallon SHEHU yace to *alguro*  nizan wuce gida da dan nawa zan tafi dan zamu hadu da Habubakar a can malam yata shi  SHEHU ma mekewa yayi shida sauran hakimai da sauran su dan girmama Zannah modu  dan yana da girma sosai   awajen ko wada yake cikin meduguri
Ai Nabil kasa tashi yayi dan shi har yanzi bai yarda Malam bai san komai ba da idan baya sani ba na meye zaice wani sai yaje gidan sa kuma ma yakira abban sa

 Zannah ne yaka ma hannun sa yace "taso ko ka tsaki jikin ka zaka yi mamaki idan kasan nidin waye a wajen ka yaro

 ai Nabil jiyayi ya koma yazauna jabar atake wani irin gumi yafara sassafo masa
zannah yasa ke sa hannun ya da gosa yace muje shiko  Sani dan karewa yayi awajen aiko suna fita Sani yayi hanyansa ya lalaba yafice zannah yana rike da hannun Nabil din harsu ka karasa inda moton zannah yake driving sa ya bude musu suka shiga dogarai da sauran mutane sai cije hannun suke dan sunyi mugun sa raida abin da Nabil zai basu har suka fice basu dina hangen moton ba ga ba daman tambaya ko yimasa kirrari ga SHEHU nan  ko idan SHEHU yana waje ba ayiwa kowa kirari SHEHU yarako Malam ne
Nabil tsumu yayi a moton zannah kaman anka kamo barawo

_Koda yake nide a gani na kamun barawon yaka mata a masa ranan da a sirin ya saya tonu_

Har suka karasa kofan gidan zannah zannah ne yafara fitowa Nabil yana ciki driving yazo yabude masa amma yakasa fitowa Malam ya leka yace "fito mana modu
Nabil yace "ina tsoron nafito ne saboda yanzu mutane idan sunga ni zasu cika gidan  baza su bari muyi abinda yakawo nin ba Malam ya huya yabawa driving umarnin abude get  dan  a shiga da Nabil ciki ai hakan akayi
bangaren Malam sukayi shikam ba ataba shiba dan ginin zamani ne ba abin da babu dan governor ne da kan sa yasa aka rushi aka masa gini part din sa shikaru 2 da suka wuce   malam yazauna a kasa akan wani kaya taccen Capet dinsa da Nabil  har yanzu bai saki hannun nasa ba
Suna zama ABBA yana shigowa  abba zubewa  yayi yana kwasan gaisuwa cikin girmamawa

 Malam yake
 amsawa cike da fara a irin nasa
Malam yayi gyaran murya yace abin mamaki kazo kasame nida
Me sunana ko abba ya gyada kai to yanzu na dawowa da shi yakoma me sunana kamar yanda yake da Habubakar kaya femin magan ganun da nayi akan ka mesunana a yanzu nabin cika na kuma gane ball sana ane ide zaka kare addini ka ayanzu nake son ka gayan wa Nabil waye ni da dangan takarmu.

 abba sai da yabari  Malam ya gama maganan sa,
Shima cikin adabi ya fara magana

 yace "haba Malam yaza kace min na yafiya maka bayan nine me lefin da shekara da shekaru  kunya ya hana ni neman yafiya kabari bana ni nane ma kai din tam kar ubane awajena dan ni uban ma ban shaku dashi kamar kai ba ni zanne mi yafiyar rashin  min umarnin ka danayi na bijirewa umarnin ka

abba yakalli Nabil da sai faman zare ido yake yace "Nabil wanan shine malamina awajen sa nayi duk maratu na shine yane mamin auren fari da nabiyu  kuma shine me sunana ka amma tunka na dan shikara 4 yace na basa kai za afara koya maka  karatun allo to ni kuma ganin kaine Babba na kwallafa rai azakayi bokon ban bashi ba saima na dena kawo ka dan hutun da nake dan kawo ka  dan yadena min zancen aiko  yadena din yaga bana son zancen sai yabari,

Karin riki cewan abin de lokacin da yaji kana ball ne yakirani yace na hana ka nace masa to amma ban hana ba kwatsam yaji zancen andau keka an kaika England makarantan koyan  ball
Aranan naga bacin ran malam dan  kasan yanda Malamai  suke kyaman ball  aranan yace idan nasa ke dan ganta ka da sunan sa bai yafe min ba kuma kar na nuna maka hanyan gidan sa,
Kai kadai ne baka san Malam ba amma su kamal yan gidan nanne sosai  haka su ummin ka
Kaima rashin zamane dana san  koda baka zodin kamar yanda Malam ya hana nasan zaka san dangan ta garmu amma ina maka murnan sa santawa da me sunanan  dan kasamu jagora  mana garci idan ka  sabawa umarnin sa bazan yafe maka ba dan nima shiya zaman ubana

Ya huya ya kalle Malam yace "Malam kayi hakurin na rasa wani dalilin ne yasa na kasa bin umarnin ka akan hana Nabil ball

Murmushi Malam yayi  yana dafa kan Nabil da yara sa duniyan da yake ma Malam  yace "dalilin  da rabon Albarka  acikin sana ar mana  gashi yadauki  daushin al umma da dama dana hana ai hakan bata faruba  Allah yakara daukaka Muhammad Nabil
ABBA yace Ameen

_Nabil yayi shiru azuciyar sa yana cewa da kasan mena maka da baka zauna zaman samin albarka ba_

Daganan suka shiga fira da Abba shide Nabil yana zaune ne kawai
abba yace "bari nashiga mugai sa da su Bagaji  Malam anan yake gayawa Abba  abinda Nabil yayi na gyaran gidan da kuma sawa dayayi za akai Aisa wato  maman Fandau  India dan amata aikin ido Abba rungume Nabil yayi yana masa godiya dan atunanin Nabil danshi yayiwa mal wanan abin
Shikon Nabil dadi yaji dan bai taba gani farin cikin awajen Abba haka ba dan yayi abin alkairi
 Nabil yayi mamakin girman gidan dan part 4  aka fitan na mata wana  buyu suna  kallon juna buyu ma haka tsarin ginin da girman kowane ban gare ya burgeshi   dan turawane  suka fasalta bangaren matan sa nada yananan ko taba wajen ba ayin ba Nabil sai mamakin girman gidan  yake dama acikin garin ana samun irin wanan girman gidan   har suka karasa ban garen matan wanda suke cikin  ginin ajere reras kamar islamiya dakunan 4 da duguwar baranda  kowa yana saf gan gaban sa su bagaji da bafanta suna ganin abba suka fara washe baki dan sunsan yau zasu sha raban naira
Duk a tsakar gidan suka gaisa da sauran matan mama ce kawai basu gani suna ta tambaya sa ya Hajja bintu da Hajja Hajara yace lfy  Bafalta ce tace Alhajji kowannan shine mesunan Malam yace "shine aiko  sai sabon gaisuwa yaran da sauran mutanen gidan wanda suke daki m a sai suka fito dan kallon Nabil
Abba bai ga mama ba ya tambaya sukace tana daki kai tsaye Abba yatufi dakin dan yana ji da Aisa duk da sai da yayi aure mada dadewa aka auro ta
Tana zaune kamar kullum  ita daya dan  Bagana da take e be mata kewa anyi auren ta wata daya da yawuce da shateema
tana jin sallaman sa  ta juyo kamar me gani tana murmushi  tace a a Alh Habubakar ne yau agidan namu  yace nime harda megidan ki Nabil
Mama ta meka hannun tana laluman ida suke tana cewa  megida matso nagan ka rabuna da kai tun ina daukan ka akan cinyana daya ke lokacin da ake kawo Nabil mama amarya ce  tana da son yara dan ta dade bata samu haifuwa ba idan aka kawo Nabil jitake kamar kar  azo daukan sa ita ta matsawa Malam ma akan yace sai anbashi Nabil din
Abba yace "jeka wajen ta wannan mamar kace ita take renon ka kana yaro ba irin ta adin da baka mata ba
Cikin sanyin jikin Nabil ya karasa inda mama take  ya durkusa ta kamo hannun tana cewa  Nabil sarkin kirini ina ball  tana maganan tana laluman kansa tana shafa

Nabil mgn ma gagaran sa yayin sai bin matar yake da ido yanzu Wannan ita na cuta ita na daukewa y'a anya Allah zai ya femin mutanen da suka soni tun ina yaron na cuta
ya daga ya sake kallon ta cikin tusayin parlour taba kujeru sai leda amma kakal ashare ba kace na makawuwa ba dan yanzu shateema yana kula da ita sosai shiya tsiye ledan ma ya shin fida mata
Nabil dakyar ya iya bude bakin yace "Eh nine mama nadawo gareki kuma zan cigama da zumuci insha Allah amma kiyin hakuri bazan samu daman rakaki India ba ina da wani uzuri mai karfi gobe zanyin tafiya ku kuma jibe ne tafiyan ku amma idan nasa mu yanda nake so zan taddaku acan naga yanayin
Anan mama tasan Nabil ne yadauki nauyin a fita da ita
Mama tafara kuka tace nagode nagode nagode  bana shikarana 13 da dena ganin amma yanzu antabbatar min idan akamin wanan aikin san samu lfy
Nabil bai san sanda ya fada jikin matar ba yana bata  hakuri  tadena kukan ba wani irin tautsayin tada kaunar ta yake ji yana ratsashi
Har suka  fito mama tanayi wa Nabil  fatan alkairi
 Abba ne yace re kudi yabayar araba dan Nabil  bakudi ajikin sa yana mota
A motan abba suka tafi abba yana sake gaya masa yanda zannah yake awajen


  _Nabil Azuciyar sa yace dame yahana ka gaya min sai da me afkuwa ta afku_

Afili  yace "ai abba da kagaya min koda ba zanje ba akalla nasan da shi ai
Driving  din ABBA ya sauke gida sannan ya  kawo Nabil gidan  sa

Hadim ce  zaune  cikin kanen ta dana  Nabil sai  lisafin shidi manda zasuyi asuna suke suna ta iface ifacen yasmin tace nin anty cikin ma yaki fitowa mugan shin dan na fison naga yafito  yayi tibibi dariya suna dukan  susa ce Eh wlh   zainab kusan dama ace me zuguda ba agane cikin ta dawuri  yakura tace " kuma ma ance cikin  fari baya fitowa dawurin jidda tace mude katon da muke so

Ko sallama bai yiba yawuce su  suna cewa yashid sannu da zuwa bai ko kalli idan suke ba yawuce part din su
Hadim ta tashi tabisa zaune ta samesa kan kujera yazuba uban ta gumi
dafashi tayi ta zauna kusa da shin tasa hannun ta cire masa ta gumin   amma ta ga bai dago kai ba  dago kansa tayin taci karo da idon sa daya kada yayi jajir wanda ita de zata iya ratsewa bata  taba ganin sacikin wanan hali ba
Cikin firgice tace  Subahanallashi my star meyake faruwa wllh kasa min faduwan gaba  mahassa dako  ture hannun ta yayin cikin bacin rai yafara magana
dagaskiyan da suke cewa kwakwalwar  macce karami ne ban taba gaskan tawa ba basai yau na biye wa karamin tunani irin na macce na janyowa kaina  abin kunya da k'askan ci da tozar ce a idon Duniya nayi zalinci  naci amanan wanda bai kamata naci musu amana ba nayi karya nayi yaudara  awajen wanan yarinyar data yar da ni nayi lefin da nasan abba bazai yafenin ba asanadin macce nayi  abin da ko a tatsuniya ban taba jin irin saba.........

Hadim daka tar shi tayi ka bar jan zancen kagayamin abin yake faruwa bani da hakurin saura ron kaga min abin da yake  faruwa kawai

Yace"ai  Fada mikin yazama dole dan ke    direction tun a farkon aikin
Daganan ya she komai ya gaya mata
Itama Hadim gaba tane yafadin amma dayake idon ta arufe  yake  da kudirin ta.
Sai cewa  tayi to  yanzu yaka kewa son muyi meye mafita  ga cikin mu ajikin ta

cikin.
 tsawan da Hadim bata taba jin yana yiba  yace kekan wuwuyace ina mikin naganan yarinyar tamkar kanwata  take gareni ina magana cikin ki
yanzu bana bukatan naji  shawaran kin dan nacire ki cikin masu lissafi
nawa za abin kuma yaza ma dole cikin buyun  kizabi daya

Tace "fadi najin
Nabil yace "na farkon mu dauko yarinyar nan tunka fin abuyayin nisa muje gaban
Mahaifinta nagaya masa gaskiya na ne mi yafiyar sa sai naro keshi yabari murenin cikin mu  ko........ 
Ai kafin ya karasa  Hadim tace Nabil kanka daya kuwa kasan mekace mudauko ta muce me
Mununawa Duniya muce kayin tarai ya dawata kuma cikin da nake tutiya dashi ba nawa bane ni nato zarta a idon Duniya yin hakan zai ba damar mayar da ita matar  permanent dan nasan baban ta kai  din zai lanja nawa yin hakan yana nuna kenan  kishiyar da nake gudu nayiwa kaina da hannuna kanan kawaye na da sauran mutane surai nani kamata da kishiya cikin da nake fariya yaza ma banawa ba Lalle idan hakan yafaru nagama tozar ta tozarcin da zai za memin gwara mutuwan daya daga cikin mu Wllh wllh  Nabil  dahakan tafar....
Shima kaseta  yayin cikin huci da bacin rai
Yace "to sai ki tsaya kijin dayan idan kuma bawanda yamikin ni nazabin wanda yamin a ciki
Na biyu
za muje na musa azubar da cikin sai na kawota wajen iyayenta nace tsintar ta nayin  a wani garin nasam........
What  Hadim tace da karfin tare da cikumo wuyan Nabin ihun da tayin da karatun data fara shi yajan yon hankalin su jindda da gudu  suka iyo wajen.....



*Sorry masoyan*
*DAMA TA*
*Zakijin shirun har zuwan Monday dan muna da bikin*


         B JATTKO
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA TA*


         *NA*

*BATUL ADAM JATTKO*


Mufeeda
Hafbee
Munan tare🤝


🌈Kainuwa writers Asso🤝

*26*

*GiDAN ZANNAH*
Bayan sun fito daga tara sun da Mlm yayi na gaya musu yayiwa Fandau aure ne da bako sun tafi

 matan gidan guna guni suka fara  har ayi aure afita da yarinya muna gidan bamu sani ba
 bagaji tace "yo ai gwara da akayi hakan idan ance auren za ayi  me uwar ta ta ajiye a wannan zamanin da kayan turaren tuta kawai ya isa uwa tanadi.

Bagana ta kama hannun mama suka shige cikin kuryar dakin su
Suna shiga Bagana ta fada jikin mama cikin kuka sosai ta fara mgn tace "mama yanzu kin yarda Baba baya son mu ko ai dama Ya Fandau kullum tana gaya miki kina kin yar da gashi Ya Fandau ta gudu dalilin zaman kunci  irin na gidan nan  na shiga ukku ne Bagana wazai mayemin ke yayata bani da kamar ki meyasa kika mana haka kin tafi kinbar ne cikin yan uba masu nuna yan ubanci kuka take sosai

Mama ta shafa fuskan ta tace"karna kara jin kince baban ku baya sonku...
Bagana katse ta tayin tace "da yana son mu me yasa  bai yi yunkuri ne man taba tunda bashida ni yar ne man ta tunda gashi nan  ya rufe bakin mutane dace wa ya mata aure daker mama ta lallamin bagana

Auren su Bagana ya gabato mama kullum cikin tunanin Fandau  da kuma abin da zata hadawa Bagana take  kishiyoyen ta kullum suna cikin siyayya  na nasu yaran da za ahada da Bagana
Akwai ranan da duk tawakali irin na mama sai da kishiyoyi suka sata kuka
Irin kwalaben bama nan da robobi na chug gum fararen nan suka tar kato mata sukace  gashi idan kika samu ikon siyan turaren wuta kya zuba a cikin tunda yanzu duk karyan yakoma kan jeren turare wuta mukam mun kokar ta mun siyawa namu yaran kwalabe na yayi da kayan kitchen dan
, mun san mlm shine kawai baya siya ke kuma gashi dan ginkin sun sallama ki balle kisa ran zasu sayawa yarki tukunya ke kuma baki ajiye ba baki bawa wani ajiya ba
Kirike wannan kafin musa mu mu kokar ta musa yaran mu su tsaya  mata tukunya dan baza mu bari ayiwa Bagana aure ba tukunya ba tunda tana mana biyyya amma  da wancan fisararriyar ce yaran mu ko cokali ba zasu siya ba.

Suka fita Bagana da ta ke kwaleman daki ko ajikin ta sai da taga mama tafara kuka tazo ta rungume ta tace mama karki damu  ALLAH yaga maraicin mu tunda ya hadani da Shateema wanda ya san komai namu yace ma badan abubuwan sun masa yawa ba da duk abin da uwa takeyin zai min kuma yanzu ma yace yayi bakin kokarin sa zai kawo mana mufitar ki rabu dasu duk bakin cikine na yaran su basu samu kaman shateema ba

 yanzu damu wata ta inda zan samu Ya Fandau  kawai
Mama dan ALLAH nasan kina mata  addua amma kikara dan ALLAH
Mama tace "naji je kiyi aikin ki
Bagana tana cikin aiki taci karo da jakan kayan Fandau  tace Allah sarki Ya fandau tabude ta fara zazzago da kayan wasu leda ta ga  sun zubo guda 2 dauka tayi tana bude wa na farkon ta koma baya cikin tsoro  amma ta sake bude dayan shima kudinne  amma wannan din da letter aciki hannun ta yana rawa ta bude  taci karo da tubutun
Fandau gaban tana
 faduwa ta fara karan tawa

_Yagana wanan kudin nakune keda mama kar kuyi zargin na sameshi ta hanyan haram a a bani shi akayi kyuta dan nasan inda zanje za samu finwanan nabar muku ne bani da buka tan sa_

Kuka ta kara fashewa dashi ta jeta nunawa mama
Mama tayi shiru tana dafa kudin
Ta sauke Ajiyan zuciya tace  "
"Ni kam bana so bazan iya amfani da  kudin da bansan tawane hanya aka same shiba
Amma ke nasan kina da buka ta wanda ALLAH yana kani nauyi nane amma Allah bai bani ba yar uwar ki ta baki ba zan hana ki ba kidauka kije ki siyi turaren wutan da kwalaban   da kayan kitchen din kibar mata sauran ta ALLAH yakare min ita a duk inda take
Aiko Bagana murna awajen ta dama ba abin da ta ke tunani irin wanan kayan

Take tafa da siyayya a rana Sawu 2 takeyin kasuwa
Komai nata me tsada take siya har ta gama siyyar ta
aranan da za aje jerin Hafsa da yamma kuma ayi na    Bagana acewar su  ai ita b
Bagana bawani abu za ajera ba tuda gado ne anriga an  daddara

Sai de wani abin mamaki da yamma  uwar dakin bagane wato anty mero tadin ga sa  almajirai suna jido wa kaya suna shigawa da  suna a jiye wa a kofan dakin mama dan Bagana gidan anty mero ta kai ajiya
Dama

Bagaji akayi silli silli da ido tace "mero wannan kayan fa daga ina mero tace" na Bagana ne ai maman tace ta tara mata agida na

Abin yayi matukar basu mamaki amma mlm yaga ma dasu dan idan bashi zai bata ba
Aisa ko ita da dangin ta aka siyar ba zai basu wannan  uban kayan ba
Mlm karara yanuna ita da yaran ta su ya fiso  kenan bayan yaza ba bata mijin kamar Shateema wanda ya nin ka mazajin nasu yaran yanzu ya bata kudin aboye tayi wa yarta siyayya baza su taba yar da ba

*Niko nace yaza kuyi da mama Aisa kainuwa ta shin ALLAH ga ba de gaba de* *se surukar Shid mas*

Ai karin haushin suma da damu wan su sai da aka kawo lefin  Bagana
Sai da suka zubar da kwallah dan haushi amma  suna jiran agama bikin su daukin mataki akan mama

*Wannan kenan*

Wlh baka isa ba nace kayin ka dan cikin da muka same shi a wahala da sa daukar wa kasan yanayin fama da kishi da juriya dana sha  har sai da kwan ta a asbiti dubi ta bon da yake fuska  ta da duk wahalan amma yata shi aban za Wllh bazai yuwuba ka kaskan ta ni ba
Tanayin tana sake yin tsallen cukumon wuyan sa gata gajera da kadan ta wuce cikin sama

Ko shigowan su  Jidda bata kula dasu ba shiyaji shigowa su dan haka Ahankali yaka hannun sa ya kwace rigan sa ya shege betdroom

yan matan suka kara so inda take Aunty yaya ne me yake faruwa sai yanzu ta dawo haiyacin ta  tace "me me me kukaji me ya shigo daku nan
Ashwa ce kanwar ta tace "Aunty kiji wani uban kuka da karan da kika yine munzo kuma  munsa meku kuna cikin wani halin da bamu sanku da shiba keda ya shid
Cikin tsoro tace me kukaji nace tukun?

Jidda tace "cewa kike cikin da kuka samu da wahala za a zubar dama yaya baya son cikin ne?
Ajiyan zuciya  ta sauke na hamdalan basu ji ba

Hadim tace "yana so har ya fine so
Yasmin tace "
 amma meya kawo zancen zubar dashi kuma cikin wata 4 har ya shiga na 5 za a zubar
Hadim cikin hassala tace "waya gaya muku haka wanan wani sirrinmu ne Wllh kuma ya tsaya iya nan kar naga kungai gaba
Shike nan suka ce tare da ficewa
Ita kuma tafara safada marwan

 azuciyar ta tana cewa  meyake shirin faruwa dani ni ni Halima Nabil zai kalla yace zai yiwa walakanci mutumin  da baya mun musu yau shine ahar da daga min mur yana  min ihu Lalle zan sake shiri kenan tun kafin ina ji ina gani
*DAMA TA* ta kubce min

Nabil yana shiga daki ya dafa kansa yana tunnanin yazai yi ne yasamu mafita

  har  Hadim  tazo tasa meshi yana zaune  ya dafe kansa
Zama tashi a bakin gadon ta kamo hannun sa cikin

 tattausan mur tace "my star na kaine kuwa yaushe ka chan zamin ne har ra a yin mu ya fara ban banta ko ka dena sona ne amma kafin kayan ke,

 hukuncin kai yi tunani akan abin da zai faru na farko
 idan kace *zubar* da cikin za ayin ka kawon ta kamar yanda ka fadan ka sani yaran nan sunjika kuma anacewa ba cikin zasu gayawa su ummi dama sunji kana cewa zaka zubar
Ga ita kan ta yarinyar ba lalle ne ta iya  shiru ba,

Na biyu idan kace zaka kawota ka fadi gaskiya zaka tozar ta kanka a Duniya kana da mutumci  agarin nan  bayan haka,

ABBA bazai ya fema kama lefin yin aure baka gaya masa ba

Auren ma irin wanan na ma nufa kuma da sata kuma ma  yar malamin sa
Wanda yake  ganin sa tamkar uba
 Kana ga da wane idon zai kalle Malam idan bakayi wasa ba sai yatsine maka

ga Malam zai sake kya matan halin ka dama yau she yayar da dakai
me zakace wa SHEHU duk mutane da suke ganin darajan ka zasu dena gani
Za ayada ka Duniya wanda nasan zaka rasa masoya da dama


Cikin  bacin rai yace" duk ba ke kika jowo ba

Tace "na yarda nina jawo ka yar da hakan wani *rubutaccen al amarine* ALLAH ya kaddara ita zata fara haifa mana yara
Nabil yayi shiru  yana tunanin  magan ganun Hadim ba karya duk gaskiya ne idan ya dauko tan ya kawo bai sira ba idan ya zubar da cikin ma bai sira ba
kuma shikan sa fada yake ko da andura masa wuka baya jin zai iya zubar da wanan cikin da ba abin da zai iya kwatan ta irin son da yake masa

Ya nunfa sa yace tom amma de  kin san babu da mafita ko kinsan kinje famu a bala iko.

Tace "akwai mafita
mutar ta tagama mana iya yaran da muke son ta haifa mana idan ta gama  musa mu wani doctor musa yeshi da kudi me yawa a London yasa mata alluran da zata manta komai acikin kwakwal war ta ajuya mata kwakwalwar ta man ta komai mu dawo daita

musa mu Sani tunda shine yasan sirrinmu muce ya kaita gidan TV a ma tsayin yatsin ceta ne daga idan iyayen ta su kaji cikiya za suje su kar bota kaga wanan shine babban mafita wanda zai baka daman mu amallah da gidan Zannah hankalin kawnce

Kuma ita kanta nasan iyayen ta idan suka ga haka za su dauka ba cikin hanka linta ta shiga Duniya ba zasu fi yafe mata


mu kuma za mu daukin dawai niyar ta har a sake koya mata sabon,
Raruwa
Koya kaga?

 Nabil yayi shiru yana tunani aiko  ya kar bi wanan Shawaran dan ya san shine kadai han yar da zai rufa masa  asiri
Amma  yaji tausayin yariyar  har cikin ran sa
Afile kuma
Yace "hakan yayi sai de akwai karin zunubi akan mu

Hadim tace "bawani zunubi ai za a koya mata komai  a sabon brain nata  please  please  bamu da hanyin da yawu ce wanan

Nabil yace"gaskiya  babu kam
Allah ya sauke ta lfy yanzu goben ni kadai din zan tafi
Hadim "tace to yaza muyin wannan danja ta hana wai za a bawa jikan ta wahala
bata san jika ya na London ba dariya suka yin su kaci gaba da firan su kamar basu ba


Bayan sun kwata Nabil ban da juyi ba abin da yake yin shawaran Hadim shene ka dai rufin asirin su amma ya rasa meya sa abin bai mar dadi  a ransa ba
ga wani mugun son ganin ta da yakeyi dan jiya ke ma kamar garin bazai  wayen ba

Rakiya zuwa airport cewa yayi ta zauna da kyar suka rabu harda kukan ta driving yaja
bayan sun shiga cikin
Ashwa  ta fashe da dariya tace "kai Aunty ALLAH yabani miji irin nakin sauran suka ce Ameen  yasmin tace "kidu ba kamar bajiya su kayin fada ba yau har sun shir ya
Hadim dan taci re musu shakku  acikin zuciyar su tace kunsan dalilin fadan na mune suka ce "a a
Tace "dan mijina bayan son abin da zai rabani da shi kona kwana daya ne amma yanzu gashin dalilin cikin nan zamu rabu har na sati shine yace idan hakane ma acire cikin ma kunsan da ciwon shekara 6  da auren mu bamu  taba ra buwa ba sai yau.

Jidda tace hakane kam ai ya Shid yana son ki amma  akan ra'buwa da ba zai wuce na sati ba zai ce  arabu da abin da aka da de ana nema


London Bridge
Fandau tunda suka tafin bata da abin yi sai karatun Qur anin ta  sai Azumi data keyin dan taji ance yana ragen sha awa amma  ita kamar ma karuwa yake takeji

haka idan abin ya matsota tayin ta matse cinya tana kuka tana ja wa Nabil da Hadim  ALLAH ya isa da sani wada ya kaita akayin auren
Tunowa da wanin magana da Nabil  ya gaya mata ne yasa ta gane cewa cikin ne yasa mata wannan sha awan

*Bana ce gaba ke zakiyi komai ba dan yanzu kin fini son abin ni kuma bazan din ga miki wahala ba*
*Dan likita yace wani cikin yana sa aso  abin wani kuma yana sawa atsanin abin ke nakin baiwar me kyu ne injin doctor*

Cikin kuka tace bana son wannan bai war ya ALLAH ka bani na tsanan abin

Ba Ameen ba taji yafur  daga idon ta da zata yi ta cikin mirror face to face sukayi da shin kamar a markin

Ya tako yazo har gaban ta
  Ya hau kan abin mirror ya zauna "
Yana bin ta da kallo
Yace
"ban ji dadin yanda  naji kina cewa ba zaki ya fe mana ba me yasa kin man ta ALLAH yana son bawan sa me yafiya dan me baza ki yafe mana ba bayan lefin namu me girma ne
Ki dauke ni tam kar dan uwa kuma dama dan uwan naki ne
Sai de zan mikin wani nefi bayan wannan wan da
Na mikin na baya

 wanda nake tsammanin girman lefin,
Yawuce wancan  dan haka zan ne mi yafiyan ki tun kafin na mikin dan bayan nayin ba am fanin ne man yafiya  nasan kafin lokacin  zaki yafe mana

Fandau ta daga kanta ta kalle shi taga ba alaman wasa afuskan sa kamar  yanda taji a muryar sa
Cikin fadu wan gaba tace "gaya min wane abun zaku muin wanda ya wuce wanda nake ciki?

Yace bayan kin gama mana waifuwa zamu sami ki alluran da zaki manta duk kan tunanin ki
Ya zama sabo fil yan da ko kin gan mu gaban ki baza ki gane muba
Haka idan kika ga mama da baban ki ba zakin gane su ba kinga muma awannan lokacin ba daman mune mi yafiya tunda  baki san ma me muka miki ba

Ture hannun sa tayi
Ta meke tsaye ta da fe kirjin ta cikin kuka tace dan dan ALLAH duk  abin da za kumin kumin amma dan ALLAH kar kusa na manta mama da bagana  ku bari na nemi yafiyan mama ta
Idan kuka min  haka zaku zama masu son kanku daya wa

Kuma ida hakan ta faru bazan iya yafe mu kuma
Yace "shiya sa na nemi yafiyan tunda wuri ai  kafin lokacin zan san yan da nayi kika yafe mana

Tsugun nawa tayin ta zube guiwowun ta a kasa ta dafa kafan sa
tace "dan ALLAH Muhammad  kar kamin haka wllh da gani sai Bagana  mama ta ta haifa kuma mudin abin tausayi ne a cikin gidan mu dalilin da yasa naje fa kaina a cikin wanan halin ma  dan na temaka mana ne

Shima idon sa taf da hawaye ya dago ta
yace "yar Mama ki karbi wanan a masanyin kaddaran mu  da kuma beyewa shawaran macce dana yi tun farko na tafka kusku ren da wanan ne kawai mafita

Dake da mama da Bagana kuma ni nayin wanan alkawarin daga yanzun za kude na kiran kan ku abin tausayi

Zaku zaman yan gatan
Da za ayin  kwatan cen ku acikin  meduguri

kuma
 mama zata yafe mikin
amma
Ni Duniya ba zata  ya femin ba ni ya ka mata kiji tausayi
Sabo da ke yanzu wata kila iya yan anguwan kune kawai  suka san me  ya faru akan kin
NiKo  idan muka bari kika tona min asiri  duk  Duniya ne zasu sani dan ha ita ce kawai *DAMA TA*

Fusgewa tayi zata kwace hannun ta
Yayin saurin mannan ta da kirjin
Sa  yace"kehar kin isa kice.........


B Jattko ce
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA TA*


     
           *NA*





*BATUL ADAM JATTKO*

Aysha kazafi
Muna tare🤝

```Masoya karku ```karyanin guiwa ```mana yau shema aka fara
 DAMATA
Zaku fara kwarafi ```ban ```muku dai dai ba tun ban idar da sakon``` da nake son isarwa``` ba zaku``` ```karaya ai wani lbrn ma saimun yi gama  da fatan zakuyin hakurin jure bina har mukai kar shen lbr```

*Nagode da soyayyan kuga*
*DAMA TA*

_Dan wllh bansan DAMA TA_
_Yana tafe da dubin_ _masoya ba sai da_ wannan abin _yafaru_

_Masoya DAMA TA yanzu  aka fara_ 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻




*27*




Ke har kin isa ki fisge ajiki na ban gaisa da baby naba.
Yayi maganan yana juyo da ita tare da shafa cikin nata wanda yanzu yadan fara tasowa,

Cikin dakiya ta sake kokarin kwace jikin ta
"ni karabu dani dan kai den gubane agareni  kai da matar ka
Na yar de maka ka yaudareni na baka amana kacimin amana bayan da kace zaka aure ni saida nace meye nufin ka akai na amma ka yaudaran,

Duk dani ma nasan da hakkin mama da Bagana a kaina nasan mashi yake  yawo  a kaina  shiya jefani  wannan bala in
Da duk da karamin tunani na ban tabajin sa ba
Matar ka tace idan ban samu ciki cikin wata dayan da  ta yanke min ba zata hadani da kare yabani ciwon kanjamau
Nashiga damuwa nadin ga rokon ALLAH yabani cikin ina jin dadin na tsallake wannan kai ka sake zuwa min da  zancen ko na haihu na baku zaku samin alluran mantau
Na manta
Mama ta
Na man ta karatun Qur anin da nake ta k'ama dashi wanda tunda nasan kaina  nake neman sa katuna na kwana azaune dan nayin hadda
Ruwa da iska ya bugeni ahan yan neman sa rana kuwa ko ranan da ka fara gani na kaga yanda nake tafe cikin sa ko takalmin kirki bani da shi

Wllh ku gubane agare ni
Inde zaku samin wannan alluran dazan manta komai nawa to zaku iya rabani  da rayuwa ta.

Marmushi Nabil yayi yace "idan da rashin  ima nin mu yakai haka har mu kashe rai da haka bata faru ba

Zata sake magana ya rufe mata bakin ta da tafin hannun sa

Yace "nasan daga wanka kika fito amma ko mai baki shafa ba kika zauna kina kukan neman wani abu kinga  me baki maganin a bin murna yaka mata kiyi
Yana maganan yana janta wajen mirror ya zaunar da ita ya lakuto man yashiga shafa mata  amma ita kam  wani  irin  tsanan Nabil da tsoron  sane  yake mata  yawo wanda ya ma man tar ta da tana bukatan wani  abu
Jin ya kunce igiyoyun rigan wankan jikin tane
Ya dawo da ita daga firgi ceccen tunanin ta dan tasan yana zame  rigan ba komai  ajikin ta
Tarike rigan gam tace "ka bari ni zan shafawa nan da kaina.

Yace "baki  isa ba na shafawa wani gunma balle inda baby na take
Ya fusgo rigan ya jefar  kusan dan karewa yayi awajen ganin  komai  daya sani  ajikin ta ya karu musamman boobs wanda suka sake cukowa
A hankali yaja idon sa zuwa kan Heep's din ta ai bai san san daya zube ba akan guiwowun sa aga ban ta ba wani irin yawu yaji yana taruwa  abakin sa yana wucewa kut kut
daya daga hannun sa rawa hannun ya fara
  dan yara sama ina yaka mata ya sauke su
Kawai sai ya rungumo ta gaba daya  laushin fanan nan ya sake nunkuwa
Bai san,
sanda ya furta yar baiwa zaki kasheni  da tsadaddun bai war ki  shiya sa gangan jikina ya kasa jure  rashin ki har ya wahalal da ni cikin kwana kin nan

Dago kanta tayi ta ta kalle shi suka ha da ido sai a san nan ya gane  tabar gazan da bakin sa ya masa
Ya wayan ce da cewa nayin missing babyna ne daga nan ya fara ai ka mata  wasan ni masu zafi da baza ta iya jirewa ba

A wannan daren
Nabil ya samu  ni shadi  a gangan jikin sa kome yasa duk sanda ya kasan ceda wannan yarinyar jinsa yake kamar sabon ango 

Ita Fandau haushin kanta ta dinga ji na biyewa Nabil da tayi  suka bawa kansu farin ciki da zata iya baza ta bari ya kusan ceta ba

Zama yayi kusa da ita ya kamo hannun ta
Yace "naga hankalin ki yatsashi da yawa karki damu har da muwan ya shafi yaron cikin ki  ya jawo masa illah tunda kinga ke bawani  asbiti za a kai kiba
haushi ya sake ka mata
tace  "idan kuma na mutu  a haifuwa  sai kusan ya zakuyin da gawata
Dariya yayi yace "bar maganan mutuwa lokacin sa yake jira
Haka yadinga lallamin ta harya samu ya shawo kanta da kalami

Cikin satin guda baya fita ko ina ko part din su bai leka ba tunzuwan sa

Suna manne da juna sallah tare wanka tare
Karatun Qur anin idan yaga dama ya biye ta suyin tare idan kuma bai da ra aye ya koma gefe yafara danne dannen wayan sa
ko abinci ita take musu simple abinci   
Nabil ya,sake mugun shakuwa da Fandau  awannan dan zaman da su kayi  sosai  ya fukanci  halayen ta masu sauki da kyu   yana jinjinawa hakurin ta da rashin sa abu a ranta yana burge shi

A yau zai  tawo amma ba dan son ransa ba sai dan yakure iya karyar da yake shir yawa Hadim
Cikin damuwa ya kalle ta yace "zan tafi amma nan da satine zuwan mu gaba daya  kiboye duk kayan da na siya mikin  idan satin yayi na gaya miki duk sanda kika bari ta gane ina tsiya mikin abu bata re da sanin ta ba zaki  karawa kan ki azaba
Kuma Kar ki kashe mana waya
ki kuma kula da kanki da baby
Yana maganan yana shafa tafin hannun ta masu laushi  da gogin yatsun ta wan da yasan lale za suyin kyu  dashi yace "kin iya  Lalle
Kallon up and down  ta masa ta gir giza kai  alamun a a

yace "aiko dole ki koya dan ba nason ganin kafa da hannun mcc fari  kinsan jinin shuwa
Dan haka idan Auntyn ki tazo kice mata ke kina son lalle kafan ki da hannun ki kai kayin yake yi  zata baki kinji
Itade bata yi magana ba

Ya sake cewa"  mezaki bada akwai wa mama

ta bude ido ta kalle shi tace "wacece mama kuma
Murmushi yayi yace " mama Aisa mana ko.....
Ai kafin ya kara sa tameke zaune
Cikin in ina tace "mama ta ina kasan ta?
Yace"aine nariga ki sanin ta.
Dama kasan mama ta ka cuce ni dan ALLAH ka kaini nagan ta

Shiru yashi yana bin ta da kallo  cikin tausayi da jin haushin Hadim da ta janyo
Tace"zaka  kaini wajen ta
Ganin hawayen da yake fitowa  a idon ta yasa nasa idon cikowa
Ya kauda kansa dan
 kar ta gani

yace "kiyi adua ki haifi yan 2 aranan zaki  ga mama

Cikin kuka tace "ganin da ba zai min amfani ba ko  ganin da baza tayi farin cikin dashi bako
Ganin da bazan gane ita din Wacece bako?

Mekewa yayi yana duba agogon hannun sa yace  "kar ki kashe wayan
Yayi kissing din dukkan kuma tunta ya fice yana  waigen
Ta

Akan kujera
threesiter
Nabil yana zaune  Hadim yayi mata shi da cinyar sa daga ita sai dan wani karamin rigan da ko cibiyan ta bai  rufe ba cikin damuwa tace "yanzu my  star ba zaka dauki wani mataki ba dole sai da yasmin  din zamu tafi ?
Yace " wane mata ki zan dauka shiyasa muka jinkir ta tafiyan nan dan musamu mutafi iya mu amma kinga inna tace dole sai anje da ita kuma kinga nina isa nace baza aje da autan inna ba

Hadim tace  wllh yariyar muguwar yar sa ido ce  jiya nafito  daga wanka kafin na samu nasa kaya in cusa tsuman da nake cusawa aciki sai gata ta shigo min ba ko knorking tana shigowa idon ta akan cikin  nayi wuf na shege  bathroom kamar mai jin amai  ahe ina tagani
Sai bayan na tafito muna zaune
Tace ai ita cikina gizo yake mata wani lokaci  ya girma  wani lokaci ya zama karami   dazu kam ma babu tagani dariya na mata na bayar da abin wasa

To nake ga idan muka je da ita akwai matsala

yace  "Gaskiya baki iya sa cikin ba wani lokaci kisa kato wani lokaci baya kai yanda  kike sawa

Tace "tom amma idan  iya mune  a gidan ai bawani  ta kuran sa ciki  ai

Yace "sai mukula kawai da takun mu dan zuwa da yasmin  ya zama dole ba muda han yan da za muce  baza ta muba

Alhamdulilah  mama anje andawo cikin  sa a darai take gani sai glass da suka bata na rage haske amma  gidan Nabil  na cikin  danbuwa road a Ka wuce da ita dan doctor yace tana yawan kallon  korayen ganye

 shiyasa Nabil  yace awuce da ita can dan da flower  karawa idon karfin gani a gidan  yagina wa  hanif ne kanin sa amma bai gaya wa kowa na hanif bane
Yace akai ta can kafin  agama ginin  gidan malam din yasa anyi order flower  masu tsada awaje wanda za a sawa gidan mu samman ban garen mama wada daga baya yaje ansake kaya ta part  din yafi na sauran matan saruwa


ranan da yaje yiwa mama sallama har da Hadim su kaje sun sha shira da mama
 mama sai jan Hadim take a jikin ta  yan nan Allah de ya sauke ki lfy amma de  ba a can kasan turawan  za ki haihu bako?

Hadim tace  "da a canne amma naji su ummi suna cewa idan na shiga watan haifuwa za muzo
mama tace yawwa yafi de sai yanzu Hadim ta karewa mama kallon macce  ce kyakyawan gaske fara tas ba ta inda suke kama da Fandau
Suna cikin fira sai ga Bagana  da Shateema Bagana ciki ne a jikin ta har ya fito sosai  gaisawa  su kayin da mama
mama ta tuna musu  Nabil tace wannan shine dan nawa Nabil  shatiman da dama yasan sa amma sai kallon sa yake yi wai yau ga shi  ga  shiddams ido da ido  ba TV  yake kallo ba

Shima Nabil bin wanda mama ta kira da Shattema  yake da kallo  ba zan taba man tawa ba yaji sunan sa a bakin Fandau  ke nan da Bagana  aka masa madadi  Lalle  kam dole
Fandau tace  Shateema yana da kyu

Dan shatiman  buzune tunyana dan shekara  5 iyayen sa suka kawosa karatu wajen mlm har yanzu  basu zoba mlm  yasa anyin  ne man Duniya  a Niger  din ba a samu inda suke ba
mlm yana son Shateema har ya bashi jari kamar yanda  yake bawa  yaran sa da almajiran  maras sa gata irsu Shateema  man  sai  ALLAH  ya sa nasibi a harkan na sa dan yanzu haka a de mata san gidan mlm bawani  a gaban sa

kyu kam sai de ace yafi Nabil ma

Mama ta sake cewa Hadim "Halima  ga kanwar  ta kufa bayan  sun gama gaisawa

Hadim  da tun tuni take son  bugan cikin mama a kan maganan Fandau dan taji me mama zata ce
tace "mama ina sauran yaran ki?

Shiru mama  tayi  zuciyar ta yana kunan tuno mata Fandau  dinta
Cikin danne zuciya  tace "ai su biyu  ne dama dayan tana aure ne a Niger

Hadim  tasa ke cewa mama amma da anga ya mata kin samu lfy da zata zo duba ki ai
Mama cikin kosawa da zan cen
 tace  Eh an gaya mata

Haka suka ciga ba da fira Hadim uwar yan sabo da wurin har ta saba da Bagana.  Har da musa yar number waya

Har gidan mlm  sai da suka je amma Hadim  ko sauka bata yi ba Nabil  shika dai ya je suka sha firan su da mlm ya masa  sallama  ya fito suka tafi

A ban garen Fandau  ko tunda Nabil
Ya tafi  ta ke tunanin hanyan tsira take tana zaune  tana tuno yanayin gidan su kawai sai tajin number baban ta. yazo kanta kamar yanzu  take  ke ganin  sa ajikin fango  inda  almajiran  gidan su suke kurtawa taja idon ta tarufe  rau rau ta ke ga no din da sauri da dauki wayan  har wani haki ta ke ka mar irin ance mata ta tsiran nan hannun  ta narawa ta zuma  number tana dan nawa taji ringing  ai cak ta meke  tsaye
Jin muryar da ya doko sallama cikin dodon kunnen tane yasa jikin ta ya daukin rawa
In ina ta fara tana cewa " ni ni


*Masoya  kuyin hakuri wllh banjin dadine sister idan naware zan muku dayawa kamar yan dana saba*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA TA*



       *NA*



*BATUL ADAM JATTKO*

🌈Kainuwa Asso🤝


28


 Hello ya naji  kinyin shiru  kodan kinji  muryar wada ba she kike tsammanin kin kira ba ko  dariya yayi yace to sorry

Cikin in ina
Fandau  Wllh ni number baba na kira

 Nabil Yace," na sani me kike son ki gaya masa ki fadamin na gaya masa dan yanzu haka ina hanyan  zuwa gidan  ya fadi haka cikin dariya k'eta
Dan idan ke kika kira shi ba zai shiga wayan sa ba sai de nawa,
Ke bama shi kadai  ba duk wanda zaki kira wayoyin mu zai  shiga  yanzu ha ka idan kin sake kira to wayan matata zai shiga
Kin san dalilin  tun kafin mubaki layin da wayan munriga mun setting  din shi ba zai kira kowane layin ba sai  namu
Dan damu yaka mata kiyin mgn dan zaman mu kikeyi
Idan  baki yar da ba sake kiran wani layin kiga
Idan ina tsammanin  kawai mun dauki waya ne mun baki  bata reda lissa fiba
hauka muke ko kin manta zaman sirri kike ne
Yaci ace kin sallamar kin hakura dan tun daga ranan kika shigo gidan mu kinsan ba kida mafita

Hadim da take jinsu tana ta faman murmushi  tasa hannun ta kwace wayan a hannun  Nabil taci
Hi me allo ya baby na dan ALLAH ki kai wayan dai dai cikin ki zan yi kissing din dana dan wllh neyi missing nasa sosai ki gaya masa  jibe iyanzu yana tare da mom dinsa ta Gaskiya

Wani irin k'ara  Fandau tayi ta doka wayan a tileils atake wayan yayi filla fillah

Hadim  ta kalli Nabil  tace"ai kaji  ta doka wayan fa kar tayiwa dana illah irin wannan ihu haka bakin zuciya irin na kanuri ya motsa

Hararan ta Nabil yayi ya bata rai
Tace sorry kanuri

yace "har kun kuru zai yiwa bushiya  kafa
Idan bakin zuciya ne waya fi shuwa

Tace "wai kai meyasa kafison yaren mahaifin ka akan na mahaifiyar kane
Sai da yayi paking  yajuya ya kalle ta yace nida uba nake ado

Tanayin jifa da wayan ta fada gadon kuka sosai  tafara dan tariga tagama sa ran zata bar gidan da taji number bban ta yana ringing
sosai take kuka tana jujuya kai tamkar yau abin ya fara faruwa akanta take ji
cikin da shewan murya ta fara mgn _Yarabbil alamina yazanyi  yazanyi _ALLAH bani da gata sai kai ya_ ALLAH
_ne melefice nayiwa uwata da tasha wahalan cikina da nakuda ta da renona  da tarbiya na lefi ya ALLAH  gashina tun ba ayi nisa baka fara saka mata dan_ ni nawa dan idan na haifa maba zai san _ni na haifeshi ba wannan shine sakai yar mama_
_Allah ina neman afuwan ka cikin alfarman ka kar ka bari su cutar da kwakwalwa ta_

Nabil acikin jirgi  jiya kema jirgin ba tafiya yake ba kaman ya karba ya tuka yake ji Itako Hadim ta kwanta cinyar sa sai baccecen ta ta ke shararawa
Tsaki Nabil yayi  ya kalli  agogon har  yanzu da saura

yasmin tana  daga waje dan shi Nabil  awajen su daban ne kowane jirgi ya hau  ana ware masa waje na musamman wajen da suke harda gado dade ababen mure rayuwa kamar daki yake
Suna sauka Nabil  bawani  bincike  da ake masa sai dae ma girmamawa

club din su suka turo  motoci na ta ransa
Yan jarida sai  faman cunkusun shege masa suke  bai tsaya ba sai  daga hannun da yake har ya shiga mota Hadim cema ta tsaya basu  amsa
Manyan abokan sane suka raka su har general  parlour  masu aikin sa sunga ma shira dining kamar yanda suka saba akowane zuwan sa shide saman su ya wuce
Agurguje ya saki shower yana  ga mawa yafito  komai  bai  shafaba  sai brush din kansa da ya dan yi sama sama ya dauko wani rigan  adidas jaa da bakin wando  yasa yafita ko turare  bai saya shafawa  ba
Tun kafin ya gama saukowa  su jopihiy  suka fara masa kirari   shiddams shide  kujera yaja ya zauna setting  saman Fandau  ko abin cin cacca kala yake ko  firan da abokai  sukeyin bakowa yake bawa amsa bama wani fashimtar su yake ba   shide  duk hankalin sa yana saman Fandau  daya ke turawa akwai fashim dasu kaga haka sunzata gajiya ne Duk  suka memeke suna meka masa hannun
Zasu tafi
Kora kasu sai da Hadim taga bashida niyar tashi takamo hannun sa yame ke tace muje ko

Suna dawowa  daga rakiyan sukaga yasmin  tana jan jakar kayanta zata  tayi saman Fandau

Hadim tace"ke yasmin idan kina son kanki da lfy kar ki kara yin hanyan Wanan part din din gawan can koki zo muje anamu part  kizabi  dakin da kike so koki dauki wancan tanuna mata wani  saman dayake dama hawa  ukku ne
Yasmin da dama tana tsoron saman karshe koda su Jidda suka zo  basa hawa saman karshe dan duk glass ne  gashi da girma  sosai
Shiya sa suke sauka a na tsakiya  wanda fandau take ciki
Tace " a a aunty bazan iya zama a sama tsololon can ba wllh kamar  awaje mutum yake

Hadim tace aiko gwara miki shi da inda kika tufa din dan muma yanzu tsoron nan muke dan aljanu ne suke tsorata baki kwana naki da mukayi baki har  sumar da wata budurwa suka yi
Ai yasmin uwar yan tsoro kafin Hadim  ta karasa tasaki jakan ta iyo gunsu da gudu tana haki

Tace "Aunty da aljanu agidan na
Hadim tace "a a babu asauran ban gare Shima  can din muna shiga kullum  akwai addua da aka bamu muna yi  idan mun shiga  amma banda bako dan sunce basa son bako
"a a anty bazan shiga ba naku zan je
Dariya Hadim tayi taje ta dauko mata jakan
Shiko Nabil yayi gaba
Da suka hau Wani daki dayake parlour barko Hadim ta nunawa yasmin tace nan zaki shiga kinga kina jin mosinmu ai

Hadim wanka tashiga Shiko yariga yayi nasa
Bayan Hadim tafito
tana ta faman shirin  ta ta shafa wannan ta goga wancan
Nabil dan haushi ma kwanciyar sa Yayi dan gani yake kamar son jamasa rai take ba abin yake so irin yaga Fandau
Saida ta gama komai nata tasa rigan bacinta
ta same shi  akwance tace "gaskiya nide inason zuwa duba babe na dan naga kai da almun gajiya  ka huta kawai
Da sauri yabude idon  sa yana kallon ta har ta kusa bakin kofa yace "yau kuma ruwan baby akemin ne baza a nemi rakiya naba

Tace "ai nasan halinka na gwasa lewane Tunda kana cikin gajiya
Musamman da naga kana wani  jan kanshi shiya sa ban ne meka ba

Yace "bawani kina son farayi min rowane kinga yakusa zuwa ko yafadi haka yana mekewa

`` *Fandau*
 Doguwar rigane ajikinta marar  hannu iya kansa guiwa yabi jikinta sosai ga cikin nan yafito yayi das ta taje kanta ya kwanko mata duk da ba dogo bane amma gyaran yayi sai sheki yake da kane kasan an kashe masa kudi  Ahankali ta kekurban tea din  tana lashe leben ta jajaye kamar tasa janbaki sai sheki yake
Dan wani oil lips  Nabil yasayo mata me sada yana rage girman lebe yasa su suzama jajaye sai tsada yanda take kurban tea din da yanayin  zaman ta da shigan ta zaka iya ran tsewa me degree ceko wanda tawaye
 Ahaka taji shigowan su kai tsaye dakin ta suka mufa basu kan ta ba dan dining din baban falon nata yashiga dan lunlu

"Kin duba sauran  dakunan ne

 Hadim tace "bata nan fa
yace "kitchen fa ?
Tace"bafa inda ban duba ba, naga kadauki abin da wasa Wllh bata
 shiko cikin
Cikin kwanciyar hankali  yace"to ina zata je kema kinsa ko aljane bai isa ya fita awannan part  dinba sai da sanin mu so tananan kide duba duk ka bedroom da bathroom na part din ai Hadim  ahar wardrop  saida ta duba  cikin ki dima tazo tace wlh batanan mun shiga ukku

Nabil ma awannan karan yadan tsorata  tare suka sake dubawa aiko
Suna fita babba falon suka kanta ta daura daya kan daya tana faman jijika kafa akan wani kujera na karfe  tana  cin kwakwan ta
Hadim gaban tane yayi mugun faduwa  ganin yanda Fandau  tayi wani kyu fatan ta tasake gogewa duk inda yar gayu ta kai to wanan ta kai
Amma da tatuno ance macce me cikin ta na kara kyu   sai bata sa wani Nabil  yana kowa mata abubuwa  aboye ba
 Shiko Nabil cinyo yinta darigan yazame kawai yake bida kallo  itako sodaya tamusu wani kallon  kasan ido tajuya taci gaba da harkan gaban ta amfa cikin farga ban yau dame suka zo mata take

Hadim takula da kallon da Fandau ta musu azuciyar ta tace yau she wannan ta fara rena mu dole ma
 Ya zama tana tsoron mu inba haka ba aikin bazai tafi yanda suke soba
Cikin wani irin tsawa tace "keeee  dan uwar ki bakya ganin mutane ne ko de ganin kina cin mekyu kina kwanciyar  awajen da ba ajin kiba shiya janyo ko dan  dama ance talaka baisan  kan saba sai yajishi cikin dola ya gane
Fandau da aduniya ba abin da ta tsana irin a zagar mata  uwa
Mekewa tayi  tsaye  agaban su tace ,"duk abin da zakumin kumin amma wllh daga yau andena taba min mutumci  uwata ne me lefice awajen ta wanda nasan  yanzu haka ina ja mata zagi agari
Na gaban idona bazan kara dauka ba Wllh kar ki kara zagar mun uwa zan iya yin komai aka.....
Ai bata kara saba Hadim ta kwashe ta da wawan marin  zata sake karawa Nabil yayi saurin reke hannun ta
Yace"mekenan hakan  ba kya duba halin da take ciki

Hadim tace "bakajin zagin na takeson yine badan darajan baby naba wlh  sai na mata abinda zata rena kanta

Wai tsaya ma ina kika samu wannan rigan me tsada kika  sa

Fandau batayi magana ba da sauri tayi hanyan bedroom
 Hadim tace "my star  akwai ayan tan baya akan yarinyar nan fa  kaman ta
Wannan giran shine  fa wan da nagani  a fashion bane nai tane maban samu ba ina ta samu
Nabil da duk yawani  da burce  gashin sanin  amsan da zai bata yace" kema waya san iya yawan kayan ki komai kikaga kina so duk kincika mana  gurin da kaya wannan da hannun na na tsayo miki amma banga kinsa ba sai de naga sanda  kika hado kayanda  zaki bawa wanan yarinyar  dawannan aciki
Hadim tace "Wllh to ni ban makula ba
Dana sa dan yamin  dube yanda take juya mazaunan a ciki wannan data samu  waje irin  fallin da zatayi
Rigan yayi
Yace "bawani  nawa kike tarawa kiba da batare da kinsa suba
Tace aiko zan bada bazan bawa wannan mekyu Wllh  ban san na bata ba
Hadim tace "ni duk bawan nan ba kaga wani sabon reni da wani falli attare ta ita

Nabil yace "dama fa ance idan macce cikin ta ya girma zata fara janza hali
Hadim tace haka ake cewa amma ita wanan kaga idan muka bari tarena mu aikin bazai  tafi dai dai ba
yace haka ne mushiga mugaisa da baby ina jin Baccci
Tace aine bazan shiga ba dan kasan bana son reni shiga kafito

ai jiyayi kamar  sallah  cikin sauri  yayi  hanyan bedroom din
Hadim tace "doki kenan to ka gaida min da baby
Shiko juyowa bai shiba ya shiga

Yabar Hadim da nunanin ya akayi Fandau ta goge haka  fatan tashi luwai
Yarinyar da take turkusawa ta gaidani  jikinta na rawa ce yau take mayar min mgn Lalle sai na dauki  mugun mataki  anan ta zauna  tana jiran fitowan Nabil

Yana shiga yaganta  kwance idon  ta a sama gefen idonta ta guntatta kin hawaye
Bed din ya haye ya kwanta  agefen ta
Bakin sa yakai dai dai kunnen ta yace "yawwa nagode kogaba karki yarda ta kara zagar mana mama
Karamin bakin ta tamotsa zatayin magana  taji ya cafke lips din nata
Cikin nasa
Romance  masu zafi yashiga  saka mata itama dama iris take jira  ai  nan da nan tawani irin  bankarewa dan aduniya ba amin da tafiso  irin taga  yana mata wasa da boobs  Nabil yana koyar da ita wasu darusa masu  wahalan fashim ta
Cikin wani irin muryar yace "kema kina so ko gashi harwani gunani  kike kamar wata zakanya
 dama haka ke sokanan ta wani lokaci
Idon ta arufen ta ja hannun sa ta daura  akaran maran ta cusa hannun  yayi cikin  pants  dinta jin tayi wani  irin jikewa fiye da sammanin sa ai wani irin harbawa sandan girman sa yayi duk jikin sa rawa yafara ga farga ban Hadim  tana nan a parlour
 Yashiga daka mai wuya wanda idan yace zai fita a haka Hadim zata gane shaawan sa yamotsa zata kuma gane dalilin Fandau ne dan idan da ida bai taba kaiwa wannan  matakin ba meyasa idan  yana tare da yarinyar nan shikan sa tsoron kansa yake
Kuma ma tana da juriya fa da take iya daukan sa
Jin hannun ta ahan sandan bai san sanda yameke  ma yana tafiya  kaman na yan kacira se hada hanya yake yaje bakin kofan ya janzo security
Ya dawo
Sai  da yadan samu nusuwa yafara jin yan da ake  sa security kofan yana cewa bai yarda ba sai  ansake  da sauri ya sauka ko goge jikin sa bai tsaya ba yazura wando yace "kiyi saurin ki shiga  kiwanke jikin ta meke dan ta gane  a kidime yake  tana ta shi yaga inda yabaci yace goge nan kuma idan  kin shiga banda kin  karki fito har sai munzo zan sude ki da kai na
Sai
Yayi hanyan  kofan  yana zuwa yadin gasa number is rong security  da gan gan dan yasan Hadim  tana ji
Haka yadinga yi
can ya zaro wayan ya yita kiran no din Hadim duk da ya tabbatar wayan ba a hannun ta yake 
Can de yasa yabude  yana cewa canza  security din kikayi  nayi nayi  yaki  buduwa wllh kin ban wahala
tace "Wllh ni ban taba security ba dana ji shirune ma nazo nata ba kofan  sai naji da security  bayan da ba asawa abedroom ina ga adan ne dan ta taje tasa amma   acire gaba daya sabo da kar aje wata rana tarufe  kan akasa gano kan  kofan tana ina ne tayi maganan tana shigewa cikin dakin
Muna fikin tabe baki  yayi yace "ni ban ganta ba inaga ta dauka wani abun nazo  shiyi taki fitowa a bathroom din mana
Anan Hadim ta sake tabbatar wa  eh Fandau a toilet din take zama  tace "rabu da ita zan koya mata hankali  ai 
Sunjira sosai  bata fito ba Hadim taje ta taba kofan  tace "wlh nan din ma da security  tasa da kyar Nabil yabude
Hadim tayi ta yin mata mase fa kamar tacin yeta
Dajan kunne kar ta kara shanya mata miji

ita ko Fandau atsaye take  tasun kuyar da kai tayi wankan ta maida kayan jikin ta kar ba ayin komai ba
Hadim tace " dallah fito mu mugaisa da baby mu mutafi agajiye muke  kuma idan kika sake  daba kofan  banda ki kona daki to shocking zai jaki
A haka tafito  sukayin tamata shirmen su a ciki  suka
Fita

Cikin Fandau yacika  wata  tara har lokacin Nabil yana satan shigowa wajen Fandau wada karya da da barun sa sun sake karuwa
Saide yanzu  yana tausayin fandau din sakoda girman cikin
Kuma har wanan kolacin doctor Muktar yana bin bayan subari aduba lfyn cikin  fur suka nuna basu yar da ba har yayi fushin yarabu  dasu
Tun cikin yana wata 7 Hadima ta fara dirkawa Fandau maganin zaki  irin na gar gajiyan nan wanda tasa mama ta hada mata amma  tun asannan mama tace mata Hadim kuda na Asibiti kuka fiyar da dashi danme zaki shada dana gar gajiya  tace nede mama nafison gar gajiyan
Maman  ta hada  mata
Shita keta fa man dirkawa fandau

Suna zaune a lanbu  suna shan isha Hadim taci re cikin kona ce sunman da tasa ba cusawa ta ajiye  ajefe  sai firan su sukeyi cikin nishadi  sai kawai  sukaji maryar yasmin  akansu tana cewa Aunty anyi baki Nabil yakalli cikin Hadim  yada ga yakalli yasmin yaga sai  zare ido takeyin tana kallon cikin Hadim cikin tsoro
Ai wani irin tsawa yada ka mata ke yar iska bance karna sake ganin kin shigo min ba sallama ba jikin yasmin  narawa ta juya azuciyar tana ciwa anya anty hadim mutum zata haifa  cikin wataran akwai  wataran baku inko mutum ne to da wani abu akatsa
Ina da ja da wannan cikin ban yarda da shiba gaskiya ma ba banza ba ai naji yanda suke  fada da doctor akan bata zuwa awu cikin  amma zanbar abin arai idan naje gida naga yawa inna

Yau Fandau tun safe take zubar da wani irin ruwa wanda dama tana zubarwa amma na yau yafi na kullum  Ahankali  take jin ciwo amaranta ga cinyoyin tasun kara mata tauyin  da kyar ta ke jan su kafin  azahar  har ciwo yakaru dan kozama ya gaga reta sai faman yarfa hannun take tana tsaye takasa zama idan tace tafiyan ba iyawan zata yin ba kawai  sai  ta daure ta sugun na tana yarfa hannun ta rike  katakon gado gem  tana ta adua
 sai dare su Hadim suka shigo dan basu wuni  agidan bane amma tunda ta shiga watan haifuwa basa ne sa da kita
Fandau ta gama jigata dan kukan da take ma gagaran ta yayi duk idon ta yafirfito kaman ninta ya canza 
Tana jin motsun shigowan ta dago da kanta dukan su da gudu suka karaso inda take cikin kidima suke  tambayan ta lfy baye Nabil  dayayi saurin rungumo ta jikin sa tabar yazauna cikin jinin  kamar ba nabil me tsantsanin jine ba
Hadim gani jine dayawa kamar ba ajikin mutum yafito ba kawai  saita kama kuka Fandau tadaga kai ta kali Nabil  takamo hannun  tadan kamishi wani pepper a hannun sa cikin da shehiyar murya ta fara magana
"wanan mama ta zaka kaiwa  idan kaje anguwan gargar kace gidan zannah modu  za anu na maka mama ta sunan ta Aisa  abata da hannun ta ko kanwata bagana idan Mama tace ta yafemin tonima nayafe muku duk abin da kuka min amma  idan bata yafeba nima ban yafeba
Cikin kidima Nabil  yafara cewa "bazaki mutu ba kanwata wllh baza ki mutun ba nida hannu na zan dauke kina kaiki wajen mama da ranki  da lafiyan  ki
Hadim  da gata mukai ta asbiti
Ita ma cikin kuka tace "taya zamu kai ta asbiti  ka manta haifuwan  sirri   zatayi ai bawani asbitin ta za akai ta asirin  mu yatonu  Nabil  yace "Hadim kina da hankali  kuwa ana maganan rai kina wani maganan tonan asirin  yana cikin haka yaga fandau tayi wani  irin mika tana  salati
Dasauri Nabil ya sake runguman ta cikin kuka yake cewa Wllh baza ki mutu ba Wllh  sai kin



*To masoya Fandau yau ne fa* *amma  yaza ayin  da maganan kaiwa *asbiti ga yasmin  yar sa ido dama ta fara gano su*





          ```B JATTKO```
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMA TA*



               *NA*





   *BATUL ADAM JATTKO*

29


Bazaki mutu ba
Duk jikin ta rawa yake  gem ta kenkeme shi  cikin wani karfin da Nabil  baisan macce tana da shiba dan idan ance ya kwace bazai iya ba
Gumi ne yake keto mata  salati kawai take yi
wani irin ne shine taji  yazo mata sake kenkeme Nabil  tayi gem
Hadim sai yanzu  ta tsorata  dan bata taba ganin haifuwa ba azaton ta fitan raine ganin yanda Fandau take yun kuri cikin karfi
Abin ya bata tsoro tace  "Nabil idan ta mutu yaza muyi
Tafa de haka tana cikin riki cewa

Shiko Nabil yanda Fandau da danke shi ko halin magana ba shida shi  balle yayi yunkurin ta shi
Shikan sa gumi ne yake keto masa duk  addua da yazo bakin  shi yake tofa mata

 Cikin sa a Wani yunkurin tayi  da karfi sai gawata  sun guceci y'a  ta fado  dama yau riga da zani  tasa zanin  dama ya dade da kuncewa sai ciket din ta na ciki
ajiyan zuciya ta sauke ta saki Nabil
Shima jahota yayi jikin sa ganin yanda take sauke ajiyan zuciya  ya rungume ta gyam yana sakin ajiyan zuciya  bai masan me aka haifa ba
Sai jiyayi  Hadim tana tace"kutuma  macce  macen ma  baka me kamar ki kika haifa mana
Nabil
Yace "alhamdulilah alhamdulilah
 sai faman shafa kan Fandau yake

  yace "yanzu ina ne yake miki ciwo sai a sannan Fandau  ta bude ido tace ruwa zan sha da sauri Nabil ya saketa yayi hanyan kitchen yana zuwa ya bude fridge ya dauko roban ruwa  ya daga kanta yaba ta kurba daya tayi  ta tuno da mejego bata shan ruwan sanyi  asanin ta ta zare bakin ta tace na zafi nake so
Ya juya zai hanyan  kitchen  Hadim  da take ta faman  fadan anhafi macce  kuma baka amma kuma ta daga yar ta daura ta a cinyar ta na goge bata furka

Tace "Nabil kaga macce ta haifa fa 
Yace "good mekyun kenan
Tasake cewa "amma fa tafita kyu zo kagan ta
Yace ina zuwa

Hadim
Zanin Fandau da yake cikin jine Hadim ta jawo  ta kwan tar da yar ta nufi  lokan gadon fandau inda dama ta tana di almaka shin ta zare  duk takawo part din ta ajiye  ta dauko  ta seta yatsanta kamar yanda aka mata bayan yankan cibiya ta yanke ta daure  ta dauko wani zanin a  whardrob din Fandau  ta nade yar  dai dai lokacin Nabil  yafito da cup ahannun ya tashi Fandau  ya bata
Hadim ta kalle shi ta bata rai tace wai Nabil mehaka ruwan ma sai kai zaka bata
Cikin tsawa tace keee kalle ni idan zaki ware maki ware  ki temaki kanki dan mu muna fita adakin nan ba kara shigo miki zamu yiba sai munje mun dawo kafin nan  kin gama jegon dan muna zuwa zamu  daura daga inda muka tsaya kin haihowa mijina abin da yake so macce ni namiji nake so dan haka baki kubuta ba da namijin kika haifane ma wata kila shi ya hakura mu sallame ki inkinga mun barki to kin haifi namjiji
Amma  abin da zan gaya miki ki temaki kanki kicire ragonci  ki kasa jikin ki da ruwan dimi dan inda wanan sun kucece yar ta fito ba karamin budewa yayi ba
Inba haka ba kirube Wllh
tana gama fadan haka ta dauki zanin Fandau da yake cikin jini ta daura ajikin ta cire  siket din ta  ta zauna dabar acikin jinen da kazan tar haifuwan ta na Goggo ga cinyar ta take tayi jagab kamar ita ta haihu ta meke

ta kalle Nabil tace "zomu tafi Mu nunawa  yasmin  ko
Nabil ya kalle Fandau da kanta yake sunkuye tana zaune cikin jinin har yanzu
yakalli Hadim data rungumi jaririiya tana jiran sufita

Yace"haba yaza mufita mutar ta cikin wannan hali  mu temaka mata da koda gyaran wajen ne mana

 yamutsa fuska Hadim tayi tace wllh bazan iya ba zuciya ta bakaga yanda yake tashi ba ko wannan tsayuwan karfin hali nake
Gazanin ta dana daura dan yazama sheda awajen yasmin da ma aikatan gidan nan ya dameni da wani irin garni sona ke muje na kunce zuciya ta sai haurowa yake

Nabil yace " toki tsaya ni zan gyara
daukan Fandau yayi yayi hanyan  bathroom da ita wani kishine ya kama Hadim cikin tsawa tace "my star  a gabana kake daukan wata 

Yajuyo ya mata wani irin kallo
yace "meyasa wani lokaci imanin ki bashida yawane idan ban dauke taba kina ga zata iya tafiya ne aga ban idon ki taci wannan a zaban
Itama cikin bacin rai da kishin yanda Fandau tayi wani lif ajikin Mijin ta

Tace"to meye wani  a zaba a haihuwar macce  macce fa ta haifa
Nabil wani kallo ya mata yace "in fisari kayan ragone kaza ma tayi mana yana fadan haka ya shige da Fandau  bathroom  ya sauketa abakin  bathtub ya hada mata ruwan wanka me dimin ya sata yace "zaki iya yin wankan ko gyada masa kai tayi
Yace yawwa kidin ga kula da kanki  dan mu ayau zamu tafi dan su ummi dama basu so Hadim ta haihu a nan ba sai cewa mukayi doctor yace ba ason tayi zaman jirgi  cikin zai iya samun matsala dan haka muka musu alkawarin aranan da ta haihu aranan zamu taho dan haka  ki kula da kanki kinji  abin da tace  ai zaki iya rubewa  dan ki kula nima ina kaisu zan dawo cikin kwana ukku nan zaki ganni
Bata ce komai ba shikuma har yaje bakin kofa ya sake dawowa  yarugume  Fandau yace "wllh ko ban zauna da keba kina da mushin manci  arayuwa ta daga nan har karshen ta
Kin bani abu biyu  arawuwa wanda bazan taba mantawa da shiba
*Budurcinki*
Dakuma
*Y'ata ta fari*
Kissing  din lips  dinta yayi yace "ke ta musamman ce

Ita ko Hadim Nabil yana gaya mata wannan maganan tayi tsororo a tsaya ta bisa da kallo  tana mai maita
_idan fisari kayan ragone kaza ma tayi mana_
Idan ta fashince shi gatse ya mata ne ko gori yanzu ni Hadim har nayi saken da Nabil zai gaya min wannan  maganan kuma yasa hannun sa agaba na yadauki macce wanda ni bai taba dauka naba koda bani da lafiya sai yace nayi girma
Me hakan ke nufi
Kwaban zuciyar ta tayin da cewa tausayin ta yaji ganin ta wahala ita ma kan ta lokacin da Fandau take cikin nakudan ta tausa ya mata  balle Nabil sarkin tausayi
Kukan baby ne yadawo da ita haiyacin ta tayi saurin kijjigata
Alokacin Nabil yafito ko kallon inda jaririiya da Hadim bai yiba  yafara gyara wajen
Hadim cikin mamaki take binsa da kallo yau *shidmas*  guda da sa hannu cikin jine  yana aiki tukuru  tas ya goge wajen  yashiga yafita  yana cikin wanke kayan jinen ne yaju ya yakalli Fandau da take ta faman gasa jikin ta da towel  sai da ya gama wanke komai  na kayan da ta haifu mabiya kuwa dakyar yasa mu yayi  fishing din sa

Ya karasa inda take
 yace "wankan ya isa haka  kodan kin wahalu fa ba keba ai koni sai nayi wankan sati ina ga wannan matsa da akamin  Duk jikina ciwo yakeyi a tare suka fito

yasa mu Hadim tacika fam
Sai faman jijiga jaririiya take
abakin gado fandau da zauna shikuma yayi hanyan kitchen
Tace ina kuma zaka sake Komawa

Bai kalle  taba yace" zan hada mata tea me kaurine
Aiko Hadim tasake cika cikin fusata tace wai me kake nufine

Ko juyowa bai yiba  ya wuce  kitchen
Bayan yaka wowa Fandau tea din yabata karba tayi ta fara sha

Yaka rasa wajen Hadim da bakomai cikin idon ta sai tsabar bala i
Yasan idan bai yin lallami ba sauki dafa ta yayi yace maman baby girl  ya akayi ne muga yartaki kinwani kan kame ta dan rowa

Bata rai Hadim tayi
Tace"Nabil kasan me kayi kuwa
Cikin salon sa na yaudara yace "menayi?
Tace"baka ma san me kayi ba a gabana fa kake tattalin wata macce
Yace ba tattalin ta nayi ba kinsan ance dan tuwon gobe ake wanne tukunya

Duk magan ganun su cikin kunne Fandau dan bawani  nesa suke ba

hima kansa yana fadan haka yaji wani iri azuciyar sa yace Allah yasa bata ji ba amma  yana juyawa ya ga idon ta da hankalin ta duk akan su da gani yanayin  kallon da
Take musu taji komai

Hadim tace "aisai kai karbi yar karike  yasa hannun yakarbi  yar ita kuma Hadim jagaf jagaf da jine ajiki ta fara ta fiya wanda baisa nima zaice haifuwan gaske yi
Dariya yakama Nabil daya tuno lokacin da hadim ta zage ta na ta shafa kazan tan haiwuwa ajikin ta
Ga zanin Fandau
Daga nan suka fito
Hadim tana takawa Ahankali  sai wani cicci je baki take
Aiko kamar yanda suka zata a man falon ko suka samu
Yasmin tana kallo 
Ai tana hango su  dagudu tayi inda suke aunty karde haifuwa kikayi ne ina tan take tayi  kan ai tama manta dawani tsoron Nabil da suke yi wanda ko waje yaje tofa basa zama awajen dan shi ko kamal wanda yabiyo bayan sa soron sa yake
Kai har yayinsa mata su zainab wada suke uba daya  suna tsoron sa dan Iya uwar gida maman su zainab cewa take kar karaga musu ai kaine babba tunda kaine namiji amma sai ga yasmin taca muko ya baby ha hannun sa tana tace  "memuka samu mugani meka mata yayi
Yajuyo yana yiwa hadim sannu harda  riketa kamar wanda ita tayi nakudan

Yasmin tace lahhhhh anty  kin haifi me kama da Kala wllh suna kama da kala
 Hadim sake kallon jaririya ta tana murmushi dan mata so yariyar tayi baki ma amma taji dadi da aka dan ganta tada Kala Kala kanwar Nabil ce uba daya  ita ma yar gakin iYa ce
Wow  amma fa hancin ta irin na yashid dakum.. ...

Hararan ta Nabil yayi tayi gum da bakin ta

Tabi bayan su suka haye  sama
Toilet hadim ta wuce ta tayi saurin yin jifa da zanin duk jikin ta karni yake  wani irin amai ne taji yana taso mata wanka tayi yafi so 5 turare kam bawan da ba ta fesa ba tafito  daure da towel bata ga Nabil ba dan tasan yaje  daya dakin wanka ne yanda jikin sa ya baci
Yasmin ce da waya ahannu sai kolotun ihu ta ke takira wannan idan tafa da ko amsa bata sayawa ji zata kashe takira wani
Hadim ce tazo ta zauna abakin gadon yasimin tace"aunty  kin ganki uwa ras kaman bake kika haifu ba
Amma ANTY tare kuka haifu da yashid ko yanda naga duk jikin sa jine har yafiki baci

Gaban hadim ne yafadi ras tace ban gane kamar bani na haifuba
Yasmin tace "wllh anty fuskan ki tayau kamar baki sha wahalan nakuda ba sai tafiyan ki da ya canza kawai anty

Hadim tace"yasmin  kinada yawan shirme a maganan ki mekomin wayata naki ra Habiba da su faridan Amjad
Suzo suga baby dan yanzu zamu wuce
Kita shi ki hada mana kayan mu

Yasmin tace "yawwa anty ina siyayyan kayan baby da mukayi kinga kamar nida yashid munsan macce zaki haifa muka dinga iban kayan baby girl  keko kikayi ta jidan na baby boy
 Wai ina suke ma wllh akwai wani mekyu dama na nace idan macce ce shi za afara sa mata
Hadim tace "inaga fa anwuce da shi 9ja dan kayan da muka bari anan ba yawa duk mun aika  anty yanzu wazai mata wanka Hadim tace "bana jin za ayima ta wanka anan sai munje gida dan awai wasu abubuwan da  ake yiwa diya macce a wankan fari a al adan muna shuwa
Yasmin tace "shuwa iyayen....
Keee bani man zaitun  da auduga na goge mata jiki dashi tana maganan tana kiran wayan Habiba babbar amini yar ta
Aiko habiba cikin ihu itama da murna ta kaye waya  kawayenta zallah nanan London take kira  dan su zo suka baby kafin suta fi tana ganin kitan yangida amma bata dau ka
Tafijin kawayen  baye idan ta tuna kyutan da kungiya su tayi akan abin  da a ka Haifa baki yaki rufuwa
Nabil kwance cikin
  Bathtub  yayi  shiru  nunani yakeyi  wai dama haka nakuda da haihu yake da azaba Lalle annabi  yayi gaskiya da yace  abi uwa uwa uwa ummattii
 Akwai wani hassari da akayin agaban sa ankayi ta mutuwa da raunuka manya harda wanda kafansa ya fille yabar gan gan jikin sa amma  mai ga yashiga halin da Fandau tashiga ba
Anya yayiwa uwar Fandau a dalci da yara bata da yarta  gashi ita ma Fandau din zai rabata da yar ta
Yar fa nima tawa yar ta girma a mata haka
Tsaki yayi  afili yace  aine y'ata tafi karfin haka yata
Wllh ina ma wani zai ganta tana yawo  a kafa balle ya yaudareta kofilin wasa zan shiga aisai na hada ta da body gard sannan baza tayi Rayuwar  Nigeria ba
Da wannan karfin guiwan yafara gasa jikin sa da yake masa ciwo baye kafadun sa inda nan Fandau tafi matsewa

 Sun samu rakiyan dinben mutane  wada yafi na da zuwa airport  doctor Muktar ko kin zuwa yayi dan yaji mugun haushi da wai  Hadim haifuwan gida tayi kuma bayan hakama yayi yayi  subari aduba lafiyan ta amma sunki shiya fijiye mata ma karuwa dan yar da girman ta
Haka agidan ma Hadim kin yarda tayi  kowa ya bata wanka sai fada suke  da mamar ta sai tace ita zata iya ai ita ba yarinyar bace  ummin Nabil ma tasa baki  tace Hadim kibari a koya miki abubuwan  kinga haifuwan farine
Ai ita kanta ummi ce mata tayi ita fa bame kanin siraicin ta dan bakyu wani yaga siraicin wani

_Niko nace keko kika gama ganin na Fandau_ _a he kinsan da haka_

Haka suka rabu da ita ga hade haden na shuwa ba kadan ba amma haka suka bata ta shiga dashi idan na tsugun none   zata zuba tana gani zai gama hayakin sa yagama  idan na wanka ne ko wanke wajen tayi floshing  dinsu
da wayan ta ma take shiga  tayi zaman ta tana chatting dinta da kawayen ta akan  baby

Nabil ya sake sunkurar da kai a gaban Maman Fandau  yace"yauwa mama idan  macce ta haifu  me dame ya ka mata abata
Mama tace  kowani irin abinci ne inde megina jikine da kuma wanda zai sa ruwan nono ya gudano zata iya ci

Shiru Nabil yayi dan yagane mama bata gane meya ke nufiba yanda yaga anayiwa Hadim shidema ya tabbatar  idan macce ta haifu ba abarinta haka dan yaji su ummi sunayiwa Hadim fada ta dage da abinda zai gyarata

Dan haka ya yir  yawa kansa tafiya  London a gobe in yaso ya dawo kafin suna
Sunkurar da kai yayi cikin kunya yace "ina nufun wada zai  gyara mata jiki
Mama murmushi tayi tace "inban da abin ka Malam k'arami ai shuwa sun san irin wanan abubuwan  ai
Sake sunkuyar da kai Nabil yayi
Yace"basu bata ba ita kuma tace naki  take so
Murmushi mama tasake yi tace Allah sarki Halima y'ata wllh nima ina sonta tana da kirki da iya gimama mutum insha ALLAH gobe idan zanje duba yar jikalle zankai mata
Nabil yace "Mama ai kunyan ki take ji ni zaki bawa na kai mata ko kinje kar kimata zance ta ce kunya ta keji
Mama tace"shikenan idan naba da antsayo abubuwan sai nakira ka awayan ko
 yace to" mungode  mama tace rufe min baki har kai zaka bude baki kace zaka min godeya akan wani kan kanin abu
Nabil dubi yanda ka mayar ni kamar nina yi cikin ka da haifuwan ka bangare na ya ban ban da dana kishiyoyi na dubi yanda ka ajiyenin komai na rayuwa kullum sai kakira ne mun gaisa ga yaron dakin ka kullum sai kace yazo yaduba abinda nake bukata
amma abin da nake soda kai sauran matan ma kana musu baka gafa yanda  ban isa fitowa tsakar gida ba za afara min gorin na shanye zubiyar ka har  taka nas suka je gidan ku suka gayawa Hjjy hajara dan ma ita bane daukan irinwanan bane  sai tace musu haka halin danta yake da kyuta  suyi hakuri ran da yajiyo kuma zai muku  kaga duk suma kana musun amma Gaskiya bai kai nawa ba,
ni kaina ina mamakin yanda kake nuna ban ban ci a tsaka nen mu  kaga dole su zargi wani abu,

Shidi man nawan ne yafina su dan haka nake neman alfar ma wajen ka kana mana komai dai dai


Nabil ransa ne yabaci yadade dagano matan nan basa son mama shiya sa ma yake jin haushin su yake kuma nuna ban dancin amma idan ba haka ba shi kishiyar uwar sa ma amatsayin Uwa yadauke  ta bai taba ban ban ta iya  da ummi  ba
Yayi kwafa badan mama tace alfarma tane maba da abin da ya saba musun ma de nawa zai yi  dan shi a rayuwan sa ya tsani mutum me hassada

Yameke yana cewa to shikenan mama
Hada komai kafin na dawo agidan ABBA musa sai nabiyo ba karba dan ni gobe fitan  asuba zanyi
Har kofan babban falon ta tara kosa  tayi saurin komawa kafin afara yada mata mgn dan tana jin muryoyin mutan gidan

Yanzu dan Allah baza suma ka alfarman wasan nan daya ba abari idan anyi suna katafi
zaka tafi ka barmu duk yanda kake son babyn ka

Nabil da yake wasa da baby  yace"baby  wai kinji Momin ki tana hanawa naje nema muku kudi bayan da mun nemi   na banza ma balle yanzu gaku masu bukata kun fara zuwa
Dariya tayi tace" wai kai yanzu meyasa baka fiye son mgn dani ba komai sai kagayawa baby
shima dariya yayi yace ai ke komai na fada sai kinmin musu ita ko bata yimin komai nayi  tana so
Dariya ta sake yi tace "amma Wllh ABBAn fujjirat  zaka haukace
Yaci ro wayan sa yana daukan baby da su kansa ma
Hadim tace "yanzu idan katafi saifa  ran gobe suna yace "eh Kamal da Girema zasu yikomai da kuke buka ta
Nima da baki zanzo  Hadim cikin zunudi tace  har da su Sir  ko dan da alkawarin mu zai zo nabil yace "eh mana  ni abubuwan su ma mamaki yake bani baki ga yanda suke  zumudi babyn nan ba,
Yanzu haka Duk sunce sai sunjo da yawan suma basu taba sanin ida Nigeria yake ba

Fandau  suna fita ta sauke cup din abakin ta kala man Nabil yana mata daci wai
_dan tuwon gobe ake wanke tukunya_

Kuka ne ya kwace mata wane irin Duniya take cikine meyake faruwa da ita kamar a farki  amma yaki karewa
Afili tace  sakai yar mama banga komai  ba ma  inde wanan azaban nakudan mama ta sha nazo Duniya na gujeta to banga komai ba
Gashi nan tun ba ayi nisa ba Allah ya fara saka mata  naguje ta nema gashi nan  an raba ni da abin da na haifa wanda ko ganinta banyi ba baza ta masan ne na haifeta ba
amma  ALLAH kai kasan manufa ta akan haka banyi dan na kuntata mama  ba nayine dan zuwa gaba musa mu yanci na mema mata jin dadi na har abada ahe ni kuskure nayi bansa niba,
dan yanzu nasan dacin rabuwa da d'a nima da ba shakuwa nayi da ita ba ba wahalan renon ta nayiba naji  d'acin rabuwa da ita balle mama yata ji da ta rasani
ALLAH kayafeni

Haka Fandau tayi  tashiga ruwan zafi  tayi kokarin da cikin kwana ukku ba kace ita ta haifi wannan yar ba ga abinci wanda taga dama zata tafa taci tacika cikin ta daruwan tea mezafi sosai wani lokacin yana kona ta har  kuka take amma sabar wayo irin na Fandau tasan shine kadai magani  awajen ta dan haka bata wasa dan yaran kanuri bade sani ciwon kai 
Yarinya karama amma za kaga tasan komai

Yasmin kwance acinya uwar ta inna ZAINABU uwar danja  kenan inji Hadim
Tace"inna nifa naga abubuwan mamaki  a haifuwan nan  na Aunty  ciki kamar na aljanu wataran ya girma wataran yazama kara mi kai wata ran ma babu zan gani dan nasha kamata ba cikin  abin da yafi ban mamaki saman sakiya tun rar da muka je suka hanani shiga wai da aljanu  basa son bako amma su kullum sai sunyi ta shiga  tunba ma yashid ko anty tayi Baccci haka sai yashiga ko idan anty ta tafi anguwa  sai ya shika kuma ya dade idan su biyu ne kuma ba sosai suke jimawa ba

Amma abinda yafibani mamaki  asaman anty ta haifu
Kuma ai idan macce ta haifu bata sallah meyasa ita anty naka tayi sallah ranan da ta haifu
Inna da abin dubawa fa awannan haifuwan nasu da kinga shikara da shekaru suna neman haifuwan ba ayita ba sai da kikace tunda baza ta haifu ba zaki sashi yayi aure sannan aka samu ciki nede jikina yana bani akwai wani abu tabbasas kuma hak....

 ... Wani irin tsawa inna ZAINABU ta.......


*Tofa nima nayar da*
*Da maganan Hadim *yasmin dinnan muguwar yar sa ido ce*


_B JATTKO_
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: DAMA TA


            NA













BATUL  ADAM JATTKO


GODIYA  TA MUSAMMAN  GA WADANDA SUKA KIRANI DA WANDA SUKAYIMIN TA'AZIYYA THOUGH ONLINE NAGODE NAGODE ALLAH YABARMU DA SOYYAYAR JUNA, ANA TARE🤝

   30







Tace ashe yasmin bakida hankali, wanne irin maganane wannan din? Daza kice kinada shakku akan haihuwarta kodazu danaje gidan tana bawa 'yarta nono,

 yasmin tace "Allah inna kiyarda maganata kinsan yanda akayi aka samu ruwan nonon ne shinema yakara sakamin shakku don likita dinda take cikin jirgin  takira tace yau kwananta 3 da haihuwa amma haryanzu ruwan nono bai sauko mata ba matar sai tace mata meye dalili sai takalleni tacemin inkoma gurin zamana toh day anan bansan  ya akayi ba sai naga tana bawa 'yar nono sai inna zainab tayi shuru cande sai tace wasu daman ruwan nono baya sauko musu dawuri balle ita da kikace randa tahaihu nema,

Tasake sai tace "toh inna meyasa tace kwananta 3 da haihuwa
Inna ZAINABU cikin fada  takoreta agurin tacemata kedan Allah kitashi kibani guri banason surkullen zance ni bana daukan  magananda bashida ma'ana kinsan halina sarai yasmin de tatashi tana zumbure zumburen baki




Nabil tsugunne gaban mama tana fada masa yanda za'ayi amfani da magungunan
 shiko dayaga bazai iyaba kawai sai yaciro pen yake rubutawa tana masa bayani a tsinake idan yarubuta sai yajefa acikin ledan ahaka tagamama sa bayayin
 yatashi ya bata salama

Hadim ko ajikin ta da Nabil zaitafi dan tasan Fandau  tana jego
Kuma ma ita haryanzu bata wani dauki fandau din da mushin manci sosai ba

Fandau ta shafa nonowan ta da sukayin hulu hulu dan cikan ruwa acikin yau kwannan ta 4 da haifuwa amma  ciwon ta keji agaban ta yanzu ta dena
Yanzu cikan nonon ne kawai yake damuwan ta dan jitake
 Kamar zasu fashe
Dan matsawa  tashi saiga ruwan nono  ya tsarto mata  abincin y'ar ta dayanzu tananan  dashine abin cikta yanzu ko mezasubata inama  ko sodaya kun barmin ita nabata amma kuka fikarfina
Cikin kuka tace kiyafemin
  y'ata  Wllh ninayiwa uwata lefi har kema abinya shafeki inama zan ganki koda sodaya ne wllh da ko karfina zai kare sai kin dan dani abincin ki
Jin kofa yayi  magana ta san shikowa za ayi tasan bame shigowa tunda tasan basa nan akasan

towaye
amma da tatuno Nabil yace zaizo
Kafin tayi yunkurin tashi tasa riganta har yashigo
Cikin shigan sa kamar kullum  black cout ne ajikin sa amma rigan cikin blue ne kamar yanda   yasaba rigan cikin kawai yake sa irin daban
Idan ba da Hadim zaifita ba inda ita kuwa irin daya duke sawa sai ranan da tace ina yau liffaya zatayi shima yakeyin shigan cout din
Bata tashiba harya karaso inda take
Tsugunawa yayi  agaban ta dukda idon sa boye cikin bakin glas
Daganin yanayin sa tasan ba karamin kallo ya ke jefa mata ba
Towel  dinda tayi kasa dashi taja zata rufe jikinta
Yarike  towel din gem yana kallon ta fuskan sa dauke da murmushi  me narkarda  zukatan  mata
Bata rai tayi  ta juyar da kanta daya gefen yasa hannusa yajuyoda ita yace tunanin mekike?
Ko tunani na?
Ko dayake
Nasani kina tunanin inda yarki take ne datana nanda yanzu  zata rage miki cikan suko yayi maganan yana shafa mata boobs dinta
To kar kiji komai yariya tana wajen Momin ta tana kuma shan nono yanda ya kamata  kulawan da take samu bazai misaltu ba.

Idanuwan ta masu haske ta daga ta kalle shi ta tabe baki

Hada yatsun sa yayi tak yadaki leben ta
 daya
Taji zafi tayin saurin kai hannun ta kan leben tana murzawa
yace"barshi yayi jizafinsa kidena  murzashi hukuntashi nayi  yacika lefi
 bai iya sannu da zuwa basai rashin kunya ko
Koda yake mijin gaske akewa sannu dazuwa ba Mijin wucen gadi bako.
Dan nasan da Wannan mekama da barorojin kika aura da kinmasa sannu ko?

Fusge towel dintayi a
Hannun sata ta daura  zata meke

 yada kafa fuwan sa ya danne guiwowun ta daya sa a tsakiya  tasaki dan k'ara  tasake zama
Yadago haban ta yace "badan halinki baya yajikin ki?

Cikin dakiya tace"
    kazo daura tukunyan ko har goben tayi

Cikin basarwa
 yace" mama ta bada sako akawo miki shine dalilin zuwana
Kuma ina miki albishi Bagana ta haifu danta namiji  shekaran kija.

Cikin sauri
Tace" dan ALLAH ina kasan yangidan mu.
Yace"bakiji nace miki nariga ki sanin yangidan ba
Ina kasan su me mamata ta maka idan kasanta meyasa baka cuci sauran matan masu yara dayawa ba sai ita me biyu kuma makahuwa.

Yace" rashisani ne yajanyo amma  banso kaddara ta hauta kanta ba
Kuma karki kara cewa mama makahuwa dan yanzu tafiki lfy da jindadi

Cikin sauri tace da gaske tasamu lfy
Kuma bagana wata aura.
Shima cikin jinda din sakin fuskan ta yace "wannan sada ka yallan da aka so hada ku mana

Tace"Shattima
Yace "Yees   dan haka kicire shi aranki kar kikara tunanin sa kinji
Keba mashiba kowane namiji ne

Itako bata maganan sama take ba  taluma cikin murnan warkewan maman ta saide dan tasake tabbatarwa tace"dagaske tawake tana gani ras harta bada sako akawo miki
Nabil ganin firan mama da bagana yana sa Fandau cikin farin ciki yasa yakudiri niyan wannan mawani daman ne
Da zaisa ta cikin farin ciki  kozai ragewa kansa alhaki
Hannuta yakamo yace da gaskene mana bari nayi wanka nafito  zakiji sauran bayanan muje kimin wankan danni mata ta ita take min wanka mikewa wayi yace  "shikenan bakya son jin komai na mama haka yaja hankalin ta tabishi suka  shiga wankan  ko acikin bathtub dinma  bawani wanka take iya masa bashide ya janyota jikinsa yana faman jagolgola ta
Danwani kyau ta kara masa kamar ba ita ta haifu ba
Saida yagama jagolgola ta  yace tafita  zaiyi wanka
A kunyace tafita a bathtub din ta dauki wani towel din ta daura tafito
Shikuma duk yana binta da kallo komai nata sha'awa yake bashi yasauke ajiyan zuciya yasaki ruwa yasake tara wani ruwan yayi wankansa yafito yasameta har tagama gayunta cikin wasu English wears masu dan karen kyu
Sunfuto mata da Heep's dinta sosai ga boobs dinta da suka yi tsage tsage acikin rigan wow yafurta yana binta da kallo takawa yayi har inda take ya jata jikin sa yasauke ajiyan zuciya  cikin kunne ta yarada mata
"kirage wannan gayun ba yanzu ba karki sana kauce hanya.
Dago kanta tayi ta kalle shi tace" ina   labarin mama ta

Yace"na aika ayimin ordern abinci  ina jin ya iso ma bari nasa kaya na karbo abinci saimu yi firan  mama ko
Daga shi sai towel din yawuce  part dinsu

saida yagama mata bayanin komai tace "da'gaske wanan daga hannun mama yafito
 Bai mata magana ba yadauko wayan sa yashiga gallery ya shiga nuna bata hotona mama da kuma wanda suyi selfie  da maman

Ai Fandau bata sanyanda tawarce wayan ba
Wllh mama ce itace
Wllh
Tana maganan idon ta yana zubar da hawaye kamar ansaki kan fanfo
Mama wannan da kikayi hoto dashi mama ba masoyinki bane harkina dariya  akusa dashi mama kin manta niko harkina dariyan ki bayan kin rasani aduk kan alamu kinfini jin dadi kamar yanda  yafada kin canza
Fusge wayansa yayi  a hannun ta
Tace"dan Allah kamani bangama magana da ita.
Yace" kingama tunda kika cemin ba masoyin mama ba bayan baki fine sonta ba kingujeta akan wanda bai taba furta miki kalman soba Allah ma yatemakeki kin fada hannun nagari da kuma idon sani da wlh kin gama bata.

Tace" Naji nayi kuskure kaban hoton nagani

Yace"naki nabaki kinamin kuka.

Tasabayan hannun ta tagoge hawaye
Tace to kabani
Wani mugun tausayinta yaji yanda tayi maganan    janta yayi jikin saya rungume ta yana shafa kanta

Cikin sarkewar murya
tace" kace Bagana ta haifu ko meta shifa
Yace namiji ne
tace kaganyi ne?
Girgiza mata kai yayi
 baka gayamin inda kasan mama ba?
yace "zaki kisani da sauran lokaci
Tace "idan lokacin yayi zaka samin alluran mantau din?
Shiru yayi yace "bar wannan mujira lokaci banace kiciga bada addua ba
Tace inayi ai yace yawwa kida ge

Tace ina yariyar ya akayi take shan nonon wanda bata haifuba
Har yabude baki zai gaya mata kuma yatuno  kar hakan yazame mata sheda ko hujja wataran.
Yafada
Afili yace"wannan  bai shafeki ba
Kidauki kayan da mama ta aiko miki  da mushin manci ki fara amfani da shi

Sai asannan ta juya tana kallon kayan ita har taman ta dashi ganin hoton mama
Dasauri ta kwace ahannu sa tafara bude laidojin tana ruguman su wai yanzu wanan daga hannun mama yafito to dasunan  waza akawowa tasande bada sunan  taba 

Cikin kuka
tace"ni tace akawowa tasan inda nake ne?

Murmushi yayi yace "taya zata san inda kike
Anan yagaya maya yanda yayi yakarbo amma bai gaya mata dangan takar suba.
Kuka fandau tasake fashiwa dashi

Yace"idan kina kuka banace bazan karamiki baganan mama ba
Cikin sauri tace "nadena
Ahaka yayi ta mata firan mama ganin tafi sakewa idan yana mata firan mama da Bagana
Wani wajen tayi kuka wani tayin mamaki labarin dayafi dadi nasamun idon mama ne
Ahaka suka kwana tana like ajikin sa duk da bai nemeta ba dan ba hanya amma yayi wasanni masu gamsarwa da ita
A washe garin suka bar kasan shida dimbin abokan sa
Sun iso ran gobe suna
Fadin shidiman da ahashi da shagani bata lokacine anko na mata da maza iri daya  Hadim taci makeup kamar wata amarriya kyukam harsun kaji
Kyuta sunsha shi ba adadi Hadim kam har gajiya tayi da karban
 kungiyar  sun bawa hajara  kyutan kofi irin na yan ball dinnan  karshe a sada  na farin golne wanda sadan sa yakai rayuwa wani  babban mekudin ma     (BBC) (CNN) (ALJAZEERA)   (France 24 )da sauran kafafun yada dalaru sun yada aduniya
Balle kasan mu  duk ida kaji zancen sunan ake
A *shid* *hotel*  akayi taron amma duk girman shid dayawa basu samu shiga ba
Su yasmin sune manya awajen Inna ZAINABU sai washe baki take idan taduba wanan dinbin mutanen nan suntarune dan  saboda  Nabil sai taji  dadi da son Nabil kamar acikin ta yafito  takeji

Kwanan bakin Nabil ukku a garin meduguri suka tafi
Nabil yashigo yasamu Hadim tana bawa fujjirat nono yazauna abakin gadon
Yana cewa"maman  mama  yane
 tace "akwai damuwa fa  wllh wannan shidima sunan yayi yawa ko ina kashiga social media da kafafun yada labaru banda labarin mu bawani yarmu ta shiga Duniya ina tsoran bakin yayiwa babyn illah fa

Nabil yasa hannun yadan daya nonuwan Hadim da sunyiwa bakin baby wani ragajaf jaf  yace kinga kidena shan maganin sauko daruwan nonon nan ya isa harya mata yawa kuma jiya banaji ummi tana cewa kidinga rikewa idan zaki bata ya mata nauyi ba idan ba haka ba tazama me katon baki.

Hadim tace "Wllh nadena sha
Yace "maganan bakin  mutane kuma ba abin da baki zaiyiwa jinin Muhammad Habubakar damasak
Dan ni jinina da baki yataso yazama jinina ba abinda zai sameta.

 Fujjirat tanada kwana 20 wani tafiya yasamu Nabil zuwa Bangladesh sunada wasa acan  fur Inna ZAINABU tace idan yarinya bata yi watanni 3 ba bakasan daza sake maida ta sai idan shika daizai tafi
Dan haka Nabil bai so rabuwa da yar babyn saba haka yatafi kuma dasunan idan  suntashi shida yan kungiya London zasu wuce wannan ne damuwan Hadim dan tasan da Fandau agidan wanda wata kila ta gama biqin
dan ita matun gwanaki maman ta takamaya tana sallah dan aboye takeyin sallah
Sai jitayi tace "Hadim irin bik'ina kikeye danni ma bana jimawa inada kwana 15 ko14 nake fara sallah
To tunda garanan tafara sallahn ta afili

Tana suron idan yaje ya jone da Fandau
Koza ayin tafison da saninta

Tace "wllh bana son zuwan ka London dinnan dan  ina gudun kar kaje agarin rashina kayi  sha a'wan Waccen yarinyar

Yamusa furka yayi yace"wacce yarinyar kenan
tace" wacce muka ajiye mana
yace "wllh zakisa ma inazuwa na sallah meta
Tace" haba  impossible dan kasan naka bukatan yabiya ko
Agogon hannun sa yaduba yace"ana jirana makarasa ta waya
tace"aide baza ahanani rakiya airport bako
Waneni inhana baby da Mom dinta rakiya airport

Nabill kwance amakeken gadon hotel din a kasan ta Bangladesh sai juyi yake shide yasan bawai gajiyan wasan bane yahanashi Baccci dan yasha maganin da yakamata yasha yasamu Baccci  amma ya kasa daukan sa
Yana rufe idon sa suffan ta kadai yake hangowa yayi saurin dude idon dan bazai iya jure rufe sunba dan yarasa yazaiyi  dan zandan girma ma cewa yayi bazai kwanta ba jiya ma haka yakwana
Wani bangaren yace anya bazan fita innemi wanda sata yimin magani ba
Da sauri yagirgiza kai dayatuno da dazu yagama ganinsu daga su sai pant da bra amma baiji sha awan kowane daga cikin suba sai ma kyamar su kuma koyanzu daya tuno su haushi yaji jiyake kamar yacire gangan jikinsa yajefar yadena kawata masa wanda yasan mazai samuba
Amma ina Nabil nusuwa ya dauke masa
Tunowa da wani dabara yasa yayi saurin rarumo wayan sa
Sani yakira  yadaga yana
cewa allah yajan jamanin  Abu fujjirat wasa yanzu nayi niyan kiranka amma dana duba sai naga ku acan dare yayi sosai nabari sai dasafe congratulations ALLAH yakara dauka ka  amma sir nagajikin ka asanyaye afilin lfy kuwa

Ajiyan zuciya Nabil yasauke yace "gaskiya sani ba lfy ba
"Subahanallashi meyake faruwa
Sani ina son ayau zanshirya maka tafiya zuwa London kadauko min wannan yariyar kakawomin nan dan wllh jinake idan ban kasan ceda itaba Bazan iya.
 samun nusuwa ba

Angama sir amma ai nakega jegotake ko?
Yafadi haka yana dariya dan Sani aboko ne awajen Nabil kafin yazama yaron sa

Nabill yace"kaide kayin yanda nace kawai dan ina cikin wani hali

Cikin mamaki Sani yace wai duk akanwan nan yariyar
Nabill yace"wai fa abin kunya  shiyasa banason kowa yasani koda Hadim ce
 Sani yace "ai bawani abin kunya ai kabar rena allura dan karfene
Amma kabari adan kwana biyu dan naji anacewa idan macce ta haifu batayi  arbain ba aka koma mata to mashaifan bai gama komawa yanda yake baza iya samun ciki  wanda hakan zai iya janjo konika

Nabil yace "ai idan zatayi  konika zamufi kowa murna dan tayi saurin fita acikin yaruwan mu nima nayin saurin mekata iyayen ta dan idan nasan bazan sameta ba dole zan hakura

Sani yace "amma ni sir wllh bangama gamsuwa da amata alluran dazatayi losing memory  taba aganina kaman ba amata adalci ba.

Numfasawa Nabil yayi"yace  rashin adalci kam anriga anyin tunfarko
Iya adalcin kuma da zanyi in mantar da itan shine mafita dan kare mutumci  na
Amma yanzu duk bamuzo nanba
Abinda nace maka shine damuwata

To sir yanzu tunda har kake jinta haka zaka iya rabuwa da ita ne
Cikin fusata Nabil yace "Sani kayi abinda nace kawai

 Sani yace sorry sir amma  fa ina tsoron yanda zan tauko ta idan  ta ganta awaje ta nemin ta zille minfa ko tanemi taramin jama a
Ayanda tasha wahalan wajen shekara adaki akulle nake ganin idan taganta  a wajen dawuya idan zata kara yarda da bina musamman idan kaduba nina kaita 


*Tofa kode DAMAN KUBUTA NE YAZOWA FANDAU*



*To masoya zakumin hakuri dawanan dan hakan  ma agurguje nayinsa* *dan kuna rainane*
*dan munacikin makoki ne*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMATA*

       *NA*

*BATUL ADAM* *JATTKO*

*HJJA ZAHRA*
*ANTY KIKKIU*
 *GAISUWA DA JINJINAN BANGIRMA AGAREKI AUNTY NA MAGANIN KUKANA*
*GATAN  MARAYU  NDOROR AMBAKI* *KIN BAWA YARAN BAYA KIRKI INKIYAR KINE  MUTUMCI GEGANKINE MULKI AJININ KIYAKE ADALCI DABIYAN KINE TAUSAYI* *HALINKINE*
*AMARRIYA AGIDAN SECRETARY* *COVERNOR BAMALUM WALI* (SSG)
*ALLAH DE YABAMU *SA AN SHEGA GOVERNMENT  HOUSE  2019*
*FIRST LEADY SAI KIN  AMSA DA IZININ ALLAH*

31

"Kaga ai  banajin zata sake yarda dani
Nabil yace "kai nakeson kadauko min ita dan
Bayan kai bawanda yasami sai kasan dabarar da zakayi danne ina son kasancewa da ita.
Sani yayi dariya yace sir kasancewa kuma ina jego take ko wana 20 bata cika da haifuwa ba
Kona daukota ba abinda zata maka
Idan bata gama jinin bik'iba

Nabil yace " ni basai nayin megaba daya da itaba nasan hanyan dazanyin insamu nusuwa wllh banida nusuwa"
Sani yayi dariya yace " oga kode kakamune
Nabil yace "meba?
"sonta mana
Nabil yace "ALLAH yasauwake tabewan  baikai nanba
Banason yawan mgn kadau ki passport  dinka kaje airport  nikuma kafin ma akarasa zangama maka komai

Sani Yace" wanan girman kane yallabai
Nabil ya kashe wayan yadau ko loptop  dinshi yakunna  ba adau lakaciba yakira Sani tunkafin  ma yakarasa airport yace "masa Cumoci  yana jiran ka kana karasawa  zai dauke ka a jet  zuwa KANO  kaje office din NDARORO zaiba ka duk kan vezer harna yarinyar  zaka samu jirginda zai kai porthacourt ayau akai jirgin England idan kasauka akwai wada zai karasa dakai zuwa London atake kayin saurin karasawa gida kadauko ta dan saukan kuda mintuna 40 jirgin  Japan zai tashi shizaku bi idan kunzo Japan atake akwai jirin India idan kuzo India jet zai dauko kuzuwa Bangladesh shima kaga cikin kwana 3 tukun zaku iso

Tafiya awajen manya bawani abubane asanda sukaga dama asannan suke samun vezer wada idan kai gijari jijari ne saikayin wata kana nema  koza afita kasuwanci sai ajama ka aji kai idan marar lfy nema dakai hakanne
Kafin kasamu sai ranka yabaci


Aiko hakan akayin Sani yasamu sauka a London
Fandau tana kitchen taji motsin anfude kofa gaban tane yafadi amma ta daure ta kashe gas din tafito atunanin ta Nabil ne dan ita idan basu biyun ba bata saran ganin kowa ba
Sai gashi taci karon da Sani
Dasaurin takarasa inda yake tana nunashi kaine mugu na ukku yau kuma dame kazomin
Ashe kai kasan auren manufa za ayin dani ka kaini aka dauramin
Nace yau kuma dame kazomin  dan ku ganin kuba al sherin bane

Sani lumshe idon sayayin yana tunanin inama zai iya kubutar da ita dayayi shikan sa yasan anhada bakin dashi anyi zalumci
Wanda
Ankalin shi bai gama tashiba saida yaji zasu mata alluran nan
Tundaga ranan yafara rokon ALLAH yakubutar da ita har sadaka yakeyi da niyar haka yasha bawa malamai sadaka da niyar ALLAH yakubutar ta.

 amma yanzu bashida zabinda yawuce yabi umarnin megidan sa.

Danhaka yace "nasani nime lefine awajen ki
Amma ayanzu nazone nawan ke lefina nazone namayar ki gidan ku amma bamuda isheshen lokaci dan haka kizo mutafi

"Kaini zakayin
Yace"koba kyaso
Shiru fandau tayi tana tunanin yanzu idan takoma gida mezata cewa mama inazata ce taje taya zata wanke kanta da zarginda za amata na tatafi yawon banza tasan ko mama baza tayarda da ita ba
Wata kilama agane ta haihu agarin gyar gira kashi tarasa ido itada tafito ta nema musu yanci sai gashi yanzu tazo tana sha'awan rayuwan su nada tunda acikin sa batayi abin kunya ba
Amma yanzune zata fara fuskan tan kuncin rayuwa wanda idan takoma zaman gidan gagaranta zaiyin
Inama zata iya mai da hannun agogo baya da sai tace da aljanna suke akan rayuwan dazasu fuska yanzu
Metayin kenan tayar tazo atsiya yanzu zata koma batsiyan ma,

Yanzu duk dokin da take na zuwa gidan tamanta da wannan kalubalin da yake gabanta,
ashe komawan ma makaramin aiki bace da karfi tace " Wayyyo ALLAH tasaki kuka mai rikitar wa

Sani cikin tsoro yace"bakya son zuwa gidan ne?

Cikin kuka tace ina gudun abinda zan tarar ne nasan kishiyoyi mama zasuce karuwanci naje kuma banida bakin musawa ina zance naje dan haka dole na amsa sunan karuwa mama kuma nasan aranan bazata kwana a Duniya ba bakin ciki ne zai kasheta dan tun ina karama take cemin ta tsani zina  ta haramta mana idan mukayin zina daga ranan sunan mu tsinanu inde da sanin muda yardan mu mukayin,
Tona sani mama tana sona zata iya rasa ranta idan ankira nida haka agaban ta
Kuma nasan za a akira din
Za abazani a gari  dan gidan mu babban gidane kowaya san babana
Koda babana ya kwale ni zanrayu cikin bakin cikin agidan mu"
Kuka me tsanani tasa harda durkuso

Sani ma cikin tausayin yarasa mamezai ce
Tabbas yarinyar tana cikin wani hali fita kusan a shekare  idan ta koma tana macce bawan da zai yarda da ita
Musamman yanda yaga yarinyar  takara wani kyu wanda shi badan ita tafara masa mgn bama da bazai ce ita bace dan haka kowa yagan ta dole yace tajen yawon Duniya ne kawai

Yace" kiyin hakurin idan inkoma kawai kiyin shiru duk juyin Duniya karkiyi  magana dan idan kika fadi kaskiya bame yarda dan Nabil bakaramin mutum bane karo dashi bazai zamemikin alkawari ba
Amma anzu gawata Shawara Nabil yafara sonki da gaske kibi duk yanda zakiyi kisake susa soyayyan ki yanda bazai iya rabuwa dake ba kinga idan lokaci yayin tare zakukoma gida kuma Nabil yana dakima malam zai yafemuku suna ma matan gidan  kashinki zasu dawo inde Nabil mijin ki ba wanda ya isa yamiki kallon banza balle  yagaya mikin maganan da zai bata miki rai dan koyanzu kinfisu komai
Fandau ta daga takalli Sani tace "ina zan sake ganin sa bakace fitarni zakayi ba ina zanganshi incusa sonnawa azuciyar tasa
 Sai anan Sani yatuno ashe yakusa sakin layi yayi saurin gyarawa dacewa "ina nufun  idan baki yarda kin binen ba to ki gwada wanan shwaran kiga

Tace"binkan yafi alkairi  dan idan nazauna suka min alluran ta yazan nemi yafiyan mama gazan manta karatu na suna son mayar dani mahaukaciya

Yace "shikena  dama ina gaya mikin ne koda zaki samu  *DAMAN* kasancewa dashi tom kirike *DAMANKIN* kar kibari ya kufce miki"

Tace"nikam  ai *DAMATA* ta dade da kufcemin ai

Yace" bakomai akwai ALLAH
Ki kashe duk wani abuna wuta agidan kizo muwuce dan yanzu jirgin muzai tashi
Amma karki tsaya daukan komai
Zan tsiya miki komai
dama da shijab dinta ajikin ta dan haka tace"mujeni mana barin kayan wuta akunene

Fandau saida tashiga jirgi tatuno da bata daukin hotona su dasu mama jitayin kamar takoma  ta dauko
Tayi shiru tana tunanin makomar ta
 Saiga Fandau a Bangladesh  tana zarrare ido dan garin yayin bakarya daga airport  wani
Awani dankareren mota ne yaza daukan su zuwa hotel dinda zasu sauka
Acewan Sani anan zasu kana gobe suwace Nigeria
Yana tafe tana bansa abaya harzuwa wani daki wanda kana gani kasan na musamman ne
Yanuna maya yace "ga dakinki nan sai da safe  karki manta da shawara ta kiyi amfani da *DAMANKI* itace kadai mafita

Cikin rashin fashita tace "wane damar?

Murmushi yayi yace "saida safe zan sake tunamiki
Yana fadan haka yajuya yana murmushi
Ita kuma tamurda tashiga wani dankareren parlour tagani amma  kamshin turaren da ya amsa sallaman yasa gabanta faduwa ajikin mutum daya tasaba jin wanan kamshen  tana karasa shiga tana sake daga hanci dan tunanin ta hancinta ne yake shako mata gizo
Kofofe ukku tagani tarasa wanda zata nufa dan fisari ya matseta sosai kamar yazubo
Dasaurin ta nufina sakiyar  tana budewa nanma kamshin turaren taji fiye da na parlour gawani gado na alfarma amma duk kallon ta bata saya kallon saba tajefa jakan hannun ta kan gadon azuciyar ta 'tace kallo sai nafito
Dan fisarin kamar ma yafara zubowa wani kofan tasake tufa wanda take tunanin shine bathroom din
Tana tudewa ko toilet dinne sai taci karo da dankareren TVn dayake jikin bango akunne  tana karasawa tsakiyan bathroom dasaurin ta tadaga siket dinta ta tsugunna ta saki fisarin duk daba nan ne wajen yinsa ba tadaga kai tana kallon TVn dan tajima bataga tv akune ba nuntana gidan su ko ajirgi ta gani amma kowane kujera danasa ita ko bata iya kunnawa ba dan haka bata taba ba duk da inda tabarin ma akwan ako ina na gidan dan na bandakin ta har yafiwannan girma tana son kallo shiyasa kullum saita goge na gidan  abin yana bata mamakin wai bandaki mada tv
Tsaki tayin tace danma ball ne niko na tsani ball ina mazan iya canzawa   tameke  takarasa inda taga kan fanfo  ta dauki wani kofin tafara tsarki atsayen dan fitsarin yataba mata cinyoyin ta
wani ihutaji anyin acikin tvn tajuyo ta kalle tvn dama tasan bai wuce acesun ci ball dinba tace "mahaukata kawai
Sai kumata ga gaman Nabil aka hasko baki bude takura idon ta aiko sai gashi ansake haskoshin yadaga hannu yana ihu ta cire tan tama shine    andagashi sama shikuma sai daga hannun yake
Ai batasan sanda tasaki kofin ba tana nuna tvn tana cewa wllh shine mugun ne wllh

Nabil da yake kance cikin bathtub yana kallon ta tun shigo wanta azuciyar sa yace 'dole nema na yiwa yarinyar nan alluran da  zatayi losing  momory ta dan bazai yuwu nabar ta haka duk inda ta ganni tayi tanunani shine shine kamar wanin barawo ba

Itako Fandau sai nuni take tana shine dama dan ball ne wllh shine

Cikin tattausan muyarsa mai sanyaya zukatan yan mata
Yace"shine wa?
Dasaurin tajuyo tagansa kance cikin kunfa  iya kirjin sane kawai a waje  da remote a hannun sa yana jifanta da murmushi
tafara jada baya tana tunashi da yatsa tace "dama wajenka yakawone karya yamin yace zai kaini gida

Mekewa yayin ayanda yake bakomai ajikin sa danma kunfa ya lilibe wasu guraren   yanufota dasauri tajuya daya gefen duk da inda sabo tasaba da ganinsa haka amma duk sanda taganshin abin sabo yake zuwa mata babba baya shayin nuna tsiraici haka

Yana karasawa yarungumo ta tabaya baya ya zaga hannun sata kirjin ta yakaki ajiyan zuciya
Cikin kunnenta ya rada mata "kinga lefin sani ne dan yakawo mata gun mijinta

Tace"wacece mata kuma waye mijin
Yace"ai mata kece mata
Tace"matar wa?
Yace"mata Muhammad?
Tace" harka manta nifa matar wucen gadi ce kai kafadi haka
Dan haka nita merabo"ce
Juyo da ita yayin
Yahade rai yace "gwara da kikace me rabo ai merabo yariga yagama diban rabon sa duk wani rabo yana cikin budurci kuma nine
Harda riban rabon y'a
Duk wanda zai sameki  wllh haka zai jiki kabar kuntun tuwu dumame.

Tace "bakaji ba ance dumaso kafi zabo dadin
Zan samu wanda zaisone dan ayanda nakega kaina    zansamu masoyi
 Kaide kamin fatan ALLAH yabani mijin zanjiyar dashi dadin da wanda yake takaman yasamu budurcin bai samuba
Zan masa abubuwan da zaiman tadameye budurci zanmayar dash.....
"keee bakida hankalin da auren nawa kikemin mgnn wani katon  anki amiki fatan samun mijin
Zumura baki taye tamasa kunkune
Cak yadaka tacikin bathtub din yajefata shika yashiya shijab dinta yacira dasauran kayan ta yacire duk wani kayan da yake jikin ta runfa yamata yasakar mata dukkan nauyin sa cikin mugunta yakamo lips dita ya shiga tsosa da zafi zafi  yakeja yanda zataji zafi
take tafara yarfa hannu  dan lips dinta yafara mata zugi  saida yagaji dan kansa hakan ma bai saketa ba saida ya garzamata cizo yacire bakin sa
hannu tasa tana murza wajen
 ya janye hannunta datake murza wajen

 yace"kirabu dashin kar kibawa hannun ki wahala nayin maganin rashin kunyan sane
Wannan kadan ne yasake min mgnn wani katon yagani idan ban raba shida jikin MATA ba

Tace "ciyeni zakayin
Yace mata kenan tan ta damakike kin manta nafi maye iya maita har gurnani nake

itako wannan sabon sunan ne yake bata mamaki wai Mata

Wanka yafara yimata cikin sabon sana sonmore albarkatun jikinta dan tana jin yanda yake sarra fata
jin zai kauce hanya yasa
tace "ni kamar ni zanje nayin sallah

Wani dadi yaji yakamasa kenan tasamu cikekken tsaki
Ajiyan zuciya yasauke
Afili kuma yace" a a kibarin mana na nuna miki merabo ayanzu  yafi merabo wata ran

Daure fuska tayin tace " aidana ga tukunyan tawanku goben tayin said.....
Katse tayayin dacewa "yawwa ahe kinsani shiyasa zan daura ki akan sanwar da zai baki mamaki
Shiru tashi dan ta fashinci shi irin masu dukan mutum su hana kukane

Saida yagama jagolgolata sanan ya dauraye jikin sa  ya tashin yaja towel din yadaura daya kuma ya fara goge jikinsa dashin yajiyo yakalle ta yace"kigama ki fito kiyin sallah
yajuya yafita
Ita kuma tafada kogin tunani wato dama Sani dabara ya yakoya mata kenan tayace tayin amma nida *DAMARTA*
Wajen tsiyen zuciyar Nabil anya yanda ta kejin haushin sa zata iya sakin jiki dashi kuwa

Amma wani ban gare na zuciyar ta yace mata wanan ma dabarane  kiyi amfani da DAMARKI wajen janje hankalin sa kanki  tawannan hanyan ne kadai zaki samu  daman kunta tawa matar sada ta fuskanci tanada mugun kishi takoya mata hankali sannan shikansa Nabil saita jigaratar shi a soyayyar ta yanda bazai iya rabuwa da ita ba zata dauki fansa akan sa
sani tabbas wanan shawarar taka tayin
Zanyi amsani da *DAMATA* nima  incire tsoron su in kwatowa kaina yanci dan babu maraya sai rargo
ALLAH katemakeni ka aramin DAMA koda na lokaci dayane naga Hadim tayin kuka agabana adalilin wani abu danayin yabata haushi zanji sauki azuciyata idan naga kukan ta
ALLAH kacusa sona  meyawa azuciyar Nabil yaji duk Duniya bazai iya rabuwa dani ba
Alokacin nikuma zan rama duk abinda yamin nakunta ta masa
ALLAH kabani karfin guiwan yaudaran sa fiyeda yanda shiya yaudareni.

 Haka har tagama wankan tafito
Tayin alwala saita tsaya  tana waige2 dan neman abinda zata daura tafito
Ba towel shine yafita da dukka 2 gashi  yajika mata kayanta da kunfa ta dauko shijab din tawanke kunfan ahaka ta daura yalike mata ajikin duk yafito mata da duk suran jikinta
Shima Nabil dama jiran fitowan nata yake danyasan ahaka zata fiko
Daure da towel din ta samesa abakin bed azauke shijab a hannun sa
Yana ganinta yabita da kallo kamar wani tsohon maye yakasa kodan kibta idan sa bako maibane sai wani salo natafiya dayaka ta canja
Ga Fandau dama da iya tafiya balle yazu da zatafara dagaiya saiwani girgiza boobs dinta take bai gama rikicewa ba saida tajuya bayan ta yanda take sarrafa Heep's dinta  aibai san sanda yameke ba amma taku 2 yayin yagane idan yakara sa zai war ware mata alwala shikuma yafison tayin sallahn taci abinci ayi megaba daya
Dan haka cillah mata shijab din hannun sa yayin
Yace kisa kiyi sallahn
Tacafe cikin wani salon murya tace" ngd
Yaji muryan harcikin ransa dasauri ya daga kai dan ya tabbatar itadin ce
Bata gama bashin mamaki ba saida tasakin jikekken shijab din kasa ta tsaya ahaka tana kiciniyar sa wanda yajefa mata
Da saure yajuyar da kansa daga  ganin ta azuciyar sa yana yaushe yarnyar nan ta fissare haka
Yana cikin wannan tunanin yajin tasake cewa "lah ahen shijab din kamar riga yake yayi kyu kaga yamin kyu
Tunka fin yajuyo yace" !yasalam
Wai wanan wane irin murya ta ara wanda ban santa dashi ba kodan banajin yawan maganan ta amma idan ban manta ba koranan damu kafara haduwa muyar ya bugeni kusan shiyasa na dauketa camara ai

"Bakaga ba
Tasake mgn
"yin sallahn tukun
Baijuyo ba yabata amsa amma saime bazato kawai sai jinta yayin ta fadan jikinsa
Cikin wani salon tace" ALLAH sai kace yamin kyu
Ai Nabil jiyayin kamar bashiba dan mamaki cikin wani dasheshiyar murya yace"a a mata  kiyin sallahn karki karya alwalan kin
tace haba mijin kaman ta Annabi idan yayin alwala zai fita sai yayiwa matar sa haka tajefa masa kissing  awuyan sa
A take jikinsa yafara rawa gaba daya gashin jikin sa yameke towel dinda yake daure ajikin sa dakan sa yakunce dan yanda sandan girman yahar ba
Fandau ta gefen ido ta kalli abin tadago da fuskan sa takalli yanda yarikice idon sa yazama ja yakasan bude bakin sama yayi magana  'murmushi tayin azuciyar ta tace baza kayin wahalan kamuwa ba ashe''
 Afili kuma Tace"umm barin na tashin nayin sallah akwai abinci kuwa?

Cikin in ina yace"  eh eh yana parlour  barin na dauko mikin
Wani fari tayin da manyan idanuwan ta tajuya tayi inda abin sallah yake
Tana idar da sallah taga yasa tulin abin ci agaban sa tasowa tayin cikin ran gwada daf dashi tazauna suka faraci canta ajiye fork  nakoshin
Cikin  salaon magana ta fadi hakan
Danhaka sai da yajuyo yakalle ta
Yace"ok yana cin nashi abinci
Can tawani gan sare kirji tayi mika tace "washhh
Yace"yayane
Tace"gajiya
Yace"jeki kwanta
Kawai saita kwata a acinyar sa kuma ba wanciyan kadai  tayin ba saida takai hannun ta inda take gani yana harbi hamar kumana
 Ai abincin bakin nasa atake yafurzar dalilin wani kwaruwa da yayin  yana buga kigirjin sa
Yace"meye haka kashenin zakiyin
Tace "Haba dan na kwanta acinyar ka shine zan kashika kaifa da kake hawa kaina,,
Abin nata yanzu yadena bashi mamakin sai
Ka wai yada gata sama yace" to bari naje nasosa miki inda yake miki kai kayi tunkafin ki illata ne kijan wowa matata  asara

Awanan daren Nabil yatabba tar Fandau mace ce
ba itaba ma hatta mama acikin sururun Nabil ya kwararamata albarka  bai taba jinta kar na yau ba kodan bata ta ba biye mishi kamar haka ba dan tama sa abubuwan  ya gaskan ta mgnn mutane da suke cewa kowace macce da wayon ta ake haifanta
Nabil kenkeme ta yayin ya yakwata har baci ya daukeshin
amma
Ita batayin bacci ba
Abu daya taketa tunowa  acikin sunbatun nasa wanda kusan duk sauran bata rikeba sai shi
MATA KETA DAMAN CE BANTA BAJIN IRINKI ACIKIN MATA BA NANEMI MATA DAYAWA AMMA BA KAMARKI

Kenan ma zinacine haryabin matan da maisan adadin suba   bata san sanda tafashe da kuka ba
Afirgice ya tashin  yana sake kenkeme ta yana tambayan mata meye?
Fisgewa tayin yasake rukota dakyar ta masa bayanin tunanin data
Takara dacewa dama bayan mugutan da kamin da lefin zina ma  akan ka
Dariya yayi yace "kina kishi nane
Kallon sa tayin bata ce komain ba
Yace"tokwan tar da hankalin ki
Ya mata bayanin komain
Kuma yanzu yadena
*BAYAN WATA DAYA*
 Badin irin zaman soyayya da Fandau da Nabil sukayin awannan kasa bata lokacine
Har abokan tafiyan sa suka taho suka barsa shi sai yau ya tashi yau din ma sai da aka nace masa akwai wasa a London din yayi gagawan zuwa sannan ya fiton

Amma ne suna shiga jirgin  Fandau takama amai da zazzabi abin ya bashi tsoro sosai  yakira doc ya masa bayani doc ya daga idon Fandau yagani yace cikine da ita barin na auna ta sai na bata mgni da ya dace da ita ko
Cikin tsoro Nabil yace cikin kuma
Doc yace yes doc yayi 2 Nabil yace shifa ba cikin bane kuma baza a auna ba
Doc yace medin kace ai nasan matar ka wanan din bansan taba Nabil ya daure fuka yace sister ditace
Dc yace, "yawwa kamarin na mata tambaya wllh cikin ne da ita cikin kosawa Nabil  yace" bata jin English
Kuma ba cikin bane dama idan ha shiga jirgin haka yake mata
Shiru dc yayin danshi yaga cikin amma Nabil  yana son musa masa akan aikin sa
Shima nabin wani irin faduwan gaba yake ji yaza ayin ace tayin ciki kode  mgnn Sani ne ya tabbata nacewa idan batayi arba in ba zatayin konika ne ya tabbata inko hakane  yazaiyi
Mezai cewa
Hadim dan yafara hango gaskiyan abin dan wata kuda da kwana dayayin da ida baga tayin  period ba
Bama Hadim ko amutanen wajen idan akace ciki  yasamu yanzu  to
akwai matsala


Ammm nima de haka nace fandau tayin  handa ma

*Ya Hadim zatayin idan taji lbrn cikin dan kutuna zuwanta  saura wata 3 fa*

```Ina bawa masoya kakurin rashin jina saboda wasu dalilai dan fadan zakumin afuwa```

*Sain najin*
*Commet*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: DAMATA





              NA



BATUL ADAM JATTKO

*Gaisuwa gariki*
*Aisha Bukar gana*
*Aunty Atta*

WANAN PAGE NAKUNE
🌈KAINUWA WRITERS
Aunty Fauzah
Maryam Ahamed
Aysah sada
Farida Talba
....

33



Danme zaka katseta  fade muji
Wani irin tsare Fandau Nabil yayin da ido

'Itama Fandau wani tunani ne yazomata na bai kamata tatonawa Nabil  asiri yanzu ba da sauran lokaci dan yanzu neman kai take dashi idan ya abinta da ita tukun taci masa amana kamar yan daya mata zai fijin haushi amma yanzu idan ta tona masa asiri yanzu bazata ci galaba ba
Tunda yanzu tana samun sanyi a wajensa idan ta tona asirin sa shima zai iya kunta ta mata dan haka kwai sauran lokaci tace azuciyar ta'

Hadim tasake cewa" baza kifada ba shiwanda yakawoki shine yazo da bamanan?

A a anty kintuna ranan da nazo kidan nan to tunranan rabona da nasa wani d'a namijin a idona kai har maccan ma ban gani ba sai keda mijin ki shinake son cemiki aunty wllh cikin kune."

Ajiyan zuciya Nabil yasauke
Yasan wawancin Hadim zata yar da kuma yajijina wa Fandau da dabaranta'

Tace "tomeya yasaki kace shiyazo."

Fandau tace"inason nace tunzuwan mune fa."

Nabil yace" kinsan ta da gi gicewa ai."

Hadim tace "nede bana ganin alamu wani gigita ajikin yarinyar nan saima wani raine bakaji yanda takewani gadara dawani jinkai da isa ba."

Nabil yace"kinsan fa jinin sarauta take ko ina sai sunnu na kansu."

Hadim tabata rai tace"sarautan tadin banza wayasan ta wata sani kadena mafadan haka ai wanan ma salon ka sata din gajin ita watace."

Fandau saida tayi wani murmushin kasai ta tace "Ayyya aunty kiyi hakuri."

Hadim tace "nibawan nan ba yanzu my star yanda zamuyi da wannan cikin shine damuwa ta."

Nabil yace "kinsan bai kamata muyin anan bako muje part dinmu ko

Suka dauki y'arsu suka fice

Fandau tabe baki tayi tace  ai kinbanza zanen baya

Nabil yace "my one shawaran da nayanke kawai idan ta haifu mubar mata   ta rike kayanta inyaso nex sai ta haifa mana dan.....

What! Hadim ta katse shi haba haba kenan kai baka gaji da zaman ta ba nida nake jin dadin munkusa rabuwa da ita zaka kawo min wannan  surkullen shawaran
Wani lokaci wllh kanka baya ja taya zaka yarda ka bar mata jinin ka ko hale halin wata ran asiri yatonu idan yaro yamemi waye uban sa."

Yace"taya yaro zai nemi uban sa bayan uwar data haife sama ta manta waye uban dan
Ina son mubar mata wannan ne kodan murage hakkin ta akan mu bai kamata ace mun kwace mata dukkan yara ba."

Hadim tace "danme muka dauko ta dama wannanne yasa,
Muka dauko ta
ALLAH ya temake mu yakawo mana  hanyan rabuwa da ita cikin kankanin lokaci amma kana neman sakar mana *DAMARMU*."

Yace"to idan bamuyin hakan ba kina ganin akwai wata hanyan daza muyi wa mutane dabara ayar da da cikin nan ne bayan fujjirat ta nada  kwana 15 nabar meduguri."

Dariya hadim tayi tace "mungode wa Allah katuna ranan da ina sallah  mama ta kamane ranan da zaka tafi."

Yace " eh
Tace"to ai ranan Inna danja tana wajen mama tace ida na gado itama batawu ce 15 ko 16 take samun tsarki kaga idan mukace daciki zasuce tunna ranan ne aiko.''

Nabil yace " to yanzu yaza ace."

Hadim tace "ka kira Inna danja kace mata dana zobani da lfy shine da aka aunani akace inada ciki wata 4 shine
Na tada hankali na sai anzubar da cikin   zakaji me zatace
Kaga ankara wata daya kenan dan da arage kwara akara dan dama yawanci wani cikin yana fita ana 10

Jijina kai Nabil yayi *azuciyar sa yace ai  four month den ne ma* *bak'ar ya*

Inna ZAINABU  tana daukan waya tace "modu lfy kira a sakar daren nan bance indan zaka kirani kana duba lokacin muna nanba danaji kira sai da gabana yafade."

"Inna kiyi hakuri nasane darene wllh wani rigimane ya taso mana atsakanin mu neda Hadim."
"inna tace yau kuma auren shekara wajen 7 ba ajikan kuba sai yau meya faru?
"Nabil saida yayi jim yace"wllh inna Hadim tunda tazo bata jin dadi dana kaita wajen likita yace tanada juna biyu shine fata  tadamin hankali,
Yanzu haka tace sai anje ancire cikin."

Inna tace" zuwan na ta kwana 4 tasamu cikin konace kawana 3 nema tunda dayan ajirgi akayi shi cikin kwanaki 3 har aka gani lalle turawa sufi mayu ina maita."
Nabil yace "Inna watan cikin 4 fa."
Cikin mamaki tace dama ranan da zaka tafi da akace ta samu tsarki awanan shigewa dakin naku kukayi abin ku muna gidan ma ko dan nima naje duba Hajara ranan ai ina gidan."
Nabil yayi shiru alamun irin yanajin kunyan nan."

Sai dayaji tace" dama ita Halima har zata iya kisan kai bansani ba
Bani ita."
Nabil yamekawa Hadim data fara kukan karya harda sheshaka wayan
Cikin dashewar murya irin wanda tajima tanayi dinan
 Hadim tace "Inna
"wane Inna asheke shasha ce bansani ba asaran dan wata 4 zaki mana saboda kedin ishe shiyace  to karfin Modu kikafi mani ba kuma duk abinda yasamu cikin nan bake ba uwar da ta haife kima sai tayi nadaman haifuwan ki
Saboda mu zurua mukeso dayawa ba kadan ba
Dan mu 3 kacal iyayenmu suka haifa
Neda Habubakar da inusa amma ALLAH ya albar kacemu jiyan na muka irga yaran muda jikoki mutum  89 muka samu  sai gacikon na 90 din allah zai kawo zaki ce zaki zubar,
To ki haifa mana wanan din idan bazaki cigaba da haifuwa ba idan Modu yana son yara dayawa dole yayi auri wacce zata haifa masa yara mu kullum burinmu mu hayayyafa dan annabi yayi alfahari damu shiwanda kikeson zubar war kika san baiwar da  ALLAH ya masa."

Cikin kuka hadim tace"inna mutane zasuyi magana nayi konika fa yazan da surutun tutane."
Inna cikin lallahi tace"haba Halima kirabu da mutum kikama allah kinji akan surutun mutane zaki aikata kissan kai idan kin zubar da cikin 4 tamkar kin hashi danshika ra ahirin ne dan anbusa masa rai balle ma wannan da ya shiga watana 5 ma,
Kar kidamu da maganan mutane bake kadai kika fara irin wanan konika ba Maryam dita ta haifi zuhuran da wata 10 ta haifi me sunan baban ta meya sameta,
Dama irinku wanda kuka dade baku samu haifuwa ba idan kuka tashi sai kunwu ce wanna suka samu dawurin  ba abin da zai sameki kullum da safe itan kin tashi ki tofeku da adua keda yarinyar kida cikin ma shafeshi da,
Lahaula kinjiko
Hadim tace" To Inna

 cikin nokewar muryar irin tajima tana kukan nan

Inna tace"kidena kuka kikula da yarinyar ki da cikin ki kawai."

Hadim tace "Inna to na yaye fujjirat."

Inna tace Danme zaki yayeta kibarta tasha ba abin dazai mata idan kin haifu ni zan kar bi ita Hajjaran
Gaban Hadim ya fadi za arabata dayar ta farin cikin ta yanda ta kwallafa akan yar nan baza ta iya rashin ta kona lokaci kadan ba,
Sai jitayin Inna tanacewa bawa modun wayan
Dasauri ta basa
Nagaya mata ta hakura kai ma kazama meyawan kula da su kajiko ALLAH ya sauketa lfy
Nabil yace " Ameen inna
sukayi sallama yakashi wayan yana dariya
Yace gaskiya my one kin iya kuka haka ashe."
"Kai  my star waye bazai iya kuka ba akan d'a ai kaga anwuce wajen tunda yar kormoton nan taji nasan yanzu kowa sai yaji dan de darene acan da yanzu zakaga ruwan kira
Gari yana wayewa zata yada."
Nabil yace "banason rashin mutum ce yayar uban nawa kike cewa yar kormato ko
Tace " sorry amma
Kaji wani batu wai idan na haifu zata karbi fujjirat dariya suka sakeyi
Hadim tace "niko wuni ne bazan bada yata ba

Washe gari Hadim yaka kama ranan suka tsara zasuje England
Nabil yakira p A din ogan su yace yana son yadauki wayan oga yarutu test  na suna da meeting gobe amma yana turawa yayi delete din sa dan kar ogan yakani
p a yace" yes sir
Bayan kaman mintuna  30 wayan Nabil yayi kara alamun message yahego
Wayan yana kusa da ita Hadim din ita ta dauka zata meka basa shikima yana shirya baby yace"
 kibude mana tana."

 budewa tace "Innalillashi !."
Ido Nabil yazaro yace "lfy?

Tace" wai gobe dasafe kunada meeting."
Nabil hade fuska yayi yakarbi waya yakaran ta yaja tsaki yayi jifa da wayan kan gado
Yasa hannu cikin suman kansa ya zauna yace" dasun san uzurin da yake gabana a England da basu fara sawani meeting na shirme ba amma bari nakira naji in bame mushin manci bane bazan jeba."

Hadim tace"kaima kasani basa zama meeting bakai kawai mutafi mu idan goben kagama sai kabimu ko mujira ka gobe muwuce tare."

Da sauri yace"a a kutafi kawai
Na same ku acan yafadi haka yana karasawa fujjirat shiri
Ko rakiya airport kinyi musu yayi acewar sa yana jin haushin katse masa tafiya

Yana daga musu hannu har driver yaja

Fandau tana kwance dan wannan cikin yana sata yawan Baccci  yanzu ma haka kwakwa take ci  amma tayi bcc hannun ta danke da kwakwa gana bakin ta ma bata gama taunan saba tayi bccn
Nabil yana shigowa yaga halin da take ciki dariya yayi yahashe gadon ya daura bakin sa kan nata yazaro kwakwan da bata gama cusashi cikin bakin taba yana zarowa bakin yabudu sai yaga nacikin da ta tona mabata hadiye ba harshen sa yacusa cikin bakin yadinga hakowa na cikin bakin yana tauna cikin bacc taji abin da yake mata
Tayi saurin bude idon ta
Tana ganin sa cikin murna da zumudi ta kyankemeshi tace " mijin kaine ba, mafarki nakeba Wllh tunjiya da abin nan yafaru
Nake neman son ganin ka dan nabaka hakuri."

Nabil ya shakunu ya janye jikin sa yace" ai kintuno min ma ahe fushi nake dake kuma nazo ne naga lil baby  badan keba."
Yana maganan yana cin kwakwan da yahako abakin Fandau

Dan ALLAH kayin hakuri wllh baz......
Kee yimin shiru kinriga kingama renani ai bawai jiya kika saba tona asirin auren kiba dan haka kici gaba  ni nawa mesauki ne dan zaman na
Zucen gadine mijin kina har abada shine dajin haushi."
Dan ko addinace an haramta tona wanan  sirrin ."

"ALLAH yaya ka yarda dani bazan sake ba jiyan ma banyi dan na bata maka ba dan naga tana shirin daurani lefin zina ne wanda anriga an haranta min shine  yasa na keson nayi shirin gaya mata amma na maka alkawarin hakan bazai kuma faruwa ba inde dagani nice."

Hararan ta yayin tareda sake hade gira

Juyoda fukansa tayi faces dinta
Buge hannun ta yayi tare da kwace fuskan sa
Tace haba habibi please mana mezan maka ka shuce ko sai nace mata  my dear  ko my sweetthr

Yace" adana kayanki duk ban nema ba yafadi haka yana shirin Mekewa
Janyo hannun sa tayi
"Allah yaya sai ka huce konabika nafita nima."
"Sai kin zage dukka kayan jikin kinmin irin wannan tsallen kwadon nan daki ka tabayi zan huce."
"idon tabda hawaye take kallon sa tace" yanzu dawannan cikin zanyi sallen?
"sosai makuwa baneman sulhu kikeba."
Hawayen da yake tare a idon tane yazubo  ta ja zet din rigan dama mai zet gaba da bayane tacire ba bra ajikin ta dama basashi take ba dan boobs nata ba alamu dan kwafa atare dasu sai cika war wani sheki yake
Nabil ba abin da yakasa sabo da ganin sa irin suran Fandau kullum sake kawatuwa yake hannu yameka yajawo ta yaman nata da jikin sa yace"na yafewa lil amma banda ke ko kin haifu sai kin yi bashi kika dauka."
Dago kanta tayi tace " aina yarda dakai mejin wajen tausayi na
 sai yawwa awannan haifuwan mekake son na haifa manane?  kwantar da ita yayi agefe suna fuskan tan juna yace"kefa mekike son haifa?
Tace macce?
Danme kike son kihaifi macce bayan dama maccan kika haifa?

Tace"dannaga  yanda muguwar zatayi idan na haifi maccan

Dariya yayi har fararen hakoyan sa suka baiyana kamar kinsan murina keman wllh nafison kiyi ta haifuwan mata dan bana son ranan rabuwa dake  dan nasan kina shifan namiji zaman ki yakare,
Idan ko macce kika haifa namiki alkararin idan nakai su gida bayan suna zan dawo na daukeki muje  saudia muyi irin wanan zaman da mukayi a Bangladesh."
Fadawa tayi jikin sa ALLAH mijin wayagan ni adakin ALLAH dana roki Allah kada Allah yabada sa a amin
Wanan alluran."
Kede kindamu da wannan allura kamar wanda za amiki namutuwa.''
"Yo ai gwara mutuwa ga badaya wanda nasan zanmutu akan akasheni da raina  asamin hauka."
Yace" ba hauka bane su turawa idan mutum yafiye ga gara ko yatsufa yadena gane abubuwa sai suma sa alluran susake koya masa sabon rayuwa yanda suke so".

Toni de banaso kuma ina rokon ALLAH karya bada sa a asamin."

Yace"kinga kibar wanan  yahade bakin su yace " ina kwakwan
Tadaga hannun ta tanuna masa na hannun yanoke kafada yace "nina bakin ki yafi dadi."

Kafin tabashi amsa yafara jujjuya harshen sa acikin bakin ta
Daga nan suka lula  bayan sungama nusuwa tare suka shiga cikin bathtub din nan masai da suka bata lokaci da taga abin nasa bana kare bane kawai sai ta masa wayo tafito gefe tayi wankan tsarki ta tafito yana cewa "au fita zakiyi  saida tajen daidai bakin kofa tajuyo ta masa wani irin fari da idon wanda ta san tana riki tashi idan tayi  sannan tayi kissing din hannun ta jefa masa tafita da gudu shikan sa gudun ma na gaiya tayi duk da rigan wankane menauyi ajikin ta hakan bai hana juya komai ba ajikin ta dan yanda take kadasu

 bai san sanda yadinga kwalla mata kira ba "mata "mata zokiji."

Itako tana zuwa daki taga wayan sa yana rinning da sauri ta karasa inda wayan yake MAMATA  baro baro arubuce ajiki amma tarasa yanda zatayi ta dauki wayan  anan tafara nadaman dama tace yakoya mata irin wanan waya wata kilama mamar tace da yanzu taji muryar ta dan kullum sai yagama wayan sada maman zai zoyana bata labari wanda har yau bata gama yarda da gaske mamar tabane kafi
Dagudu tayi hanyan bathroom din amma kafin ta karasa sai wayan ta katse  har zata komo taji kiran yasake shigowa da sauri tashige  karo sukayi yana shirin fitowa tame kamasa wayan yana karba yazaro ido yarasa yanda zaiyi yana soron ya dauka Fandau tayi wani abuda mama zata gane kawai sai ya kashe wayan gaba daya

"Mamata ce ko shiyasa baza kadauka agabana bako?

"mata nasan zaki tonamin asiri ne ai."

Tace"allah muryar ta kawai nakeson ji ni bazan yima magana ba."

 yace" tokije idan nafito zan baki kusai sa."

Salle tayi tarungome shi tana murna tace"da gaske yace"  serious
Ta tsakeshi tafita."
Tana fita ya can wayan sa muryar maza wada idan da me magana da mebada amsa duk maza zakaji tukun yakira mama sai da suka fara gaisawa yace" mama gawani yaron nazaku gaisa yanason kugai sa dashi

Yafita da sauri yakaiwa Fandau wayan yace"gashinan kugaisa da uban gidana tukun

Fandau ta karba hannun tanarawa tace inawuni?
Mama tace lfy yakuke ya fama da jama a
Fandau tace lfy
Daganan sukayi shiru
Sai can tace" to kabawa Nabil dinko
Fandau tame kamasa wayan
Yakar ba yana dariya sunyi fira sosai kafin yace "to mama sai kinjine
Kai mama ba komai fa."
Fandau tace " mama kuma yace" yes
Tace "kabani ita mugai
Yace bayan wanda kumayi ai kun gaisa canza murya nayi dan nasan idan mama taji muryar ki zata gane haka kema idan kikaji nata zakiyi kuka ki fallashe mu
Aiko bai karasa ba tasa wani uban kukan da ya rikita Nabil
Yanzu dama da mama muka gaisa ban sani ba naki maganan kirki dan sake bani ita wllh banan yiba yace "a a
Sai watarana kuma
Haka tasha kukanta shikuma sai aikin lallahinta yake

Washe gari suna zaune a parlour  akasa tana wance a cinyar sa yafara wayan nasa najaraba da hadim wanda sai suceye awa guda sai kace abin ibada yawan rabin firan akan fujjirat ne wai sai yaji muryar ta sai kashe ita kuma anyi anyi taki dariya
Ita kuma Fandau yakamo mata gallery a daya wayan tana aikin kallon pic din baby da mama idan tazo nashida Hadim ta tabe baki duk da suna mugun kyau da dacewa zugo iya Nabil take ta kallo
Yana sani da abin da take yakashe wayan
Yace"yanaji kiba tsaki ko kina jin haushin inayiwa matata kalaman soyayya."

"Ni ba haka ba waya nakeson ka koyamin."

Yace"kamar yaya inkoya miki waya wani irin koyawa?

Inkoyi shiga ko ina kozan kamo hoto basai ka kamomin ba amma kai naga alaman idan zakayi amfa dashi agabana sai kayi yanda bazan koyaba."
Yace"kikoyi imin bincike ko."

Tace "nibawani bincike dazanyi
Bazakice zaki kira mama ba
Tace"wllh kokai kace yanzu inbai yana kaina ga mama wllh ALLAH bazan baiyana ba komai yana da lokaci inaso nafito da shirina yanda zan bawa kowa mamaki,
 .shiru yayi yana tattara kalaman ta yaji taci kakiramin Sani mugaisa
"Naki wai mekuke shiryawa da Sanin ne kwana kadan sai kice nakirashi kuma baza kuyi, maganan agabana ba sai kinfita gefe."
Tace"yanzu ko agaban kaza ayi."
Yace "bayau ba

Zreky yau zaije siyaya meda me kike son kari asiyo miki."
tace "ummm abubuwan dayawa kuma sai yazo natuna kaga dana iya rubutun da sai narubuta ai dama nace kakoyamin kak'i."

Yace"nima awajen rubutu katon jakine ko a class har karatun ma ne abinda nabudi idon dashi tsalle tsalle koba haka kike cewa ba".
Taso ace yakoya mata rubutu
Amma tunda dana hada bak'in
Me zai hana tana jagolgola rubutun dakan tama tana rubutun koda hausa ma to mema zan rubuta  aiko tarishin ratuwan ta idan tace zata rubuta kafin ta gama ta gama kwarewa darubutu

Tace" to inason cemasa ya tsiyo min biro da takar da ma tafadi duk abubuwan da take bukata

Haka sukayi wanan zaman cikin soyayya sowajen 3 hadim tana saranan zuwa yana cemata tabari sai gobe sai data gaji tace"ita sai tazo ya kyaleta

"Yanzu da gaske yau zata zo dan ALLAH kasan yada zakayi kahana zuwan
yace "wllh bahali nayi nayi nakasa
Amma ai zandinga fakewa da baby ina shigowa ai."

*Bayan wata* 4

Fandau tashiga watan haifuwa  yau ko gobe amma ko min rashin ima in mutum idan yaga Fandau awanan lokacin zai tausaya mata ita kanta hadim mugun tausayin ta take   dan gaba daya kaman nin ta ya janja fuskan tada kafafuwan sun kumbura sosai gawani irin girma da cikin yayi nunfashin ta kansa awani sama sama takeyin sa magana idan tafara da kyar take karasawa kwanciyar ma gagaran ta yake  ko tsakar dare ne saide ta tashi tayi ta yasho kullum bakin ta yaya aunty kuji tausayin kukai ne aciremin cikin nan wllh ayanda nakeji cikin nan kaine zai
Nabil yace "my one mukai ta acire banason ta mutu."
Bazata mutuba
Wani lokacin haka Nabil zai rungume ta yayi ta lallashita
Jiyake inama ajikin sa cikin yake da da  sauki ina ma shi doctor ne da yatemaka mata
Ana haka yau ta tashi dawani matsanan cin ciwon mara wanda sunsan na nakuda ne ita da Nabil amma banda Hadim da taketa faman cewa juyine dan ita adaukan ta cikin wata 8 ne

Gayakama yau ne zuwan inna ZAINABU wanda tace zata zo idan hadim tasauka sai su hada sukoma tare suna cuku cukun zunan inda wana sai dare zata sauka  itada Kamal da Grema
kawai sai Fandau tashi da Wannan hali
Tajiga ta sosai
A zuciyar sa yace '
 amma hadim sai tayi duk abinda zatayi awanan karan sai yakaita hospital

Dagota yayi cak zaiyin hanyan waje da ita Hadim tarike shi" ina zaka kaita?

"Hospital  yabata dan bazan barta agida tawahala irin wacen ba dan wan da alama yafi wancen ko agoyon cikin wannan yafi wahala

"kana nufin haifuwa zatayin nagayan ma juyine kata ba ganin an yin haifuwa wata 8
Yace "saketa mutafi nace miki haifuwa ne
Cikin karaji tace "inko haihuwa ne cikin nan banaka bane

*Nace ummm Hadim zauna nan*

 *fans ankusa fa Inna takusa sauka ga fandau ba lfy*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: DAMATA



            NA



BATUL ADAM JATTKO


34

Ai Hadim tana ganin dagaske Nabil kaitan,zaiyi sai tayi sauri tarigashi fita parlour karshe wanda zai fitarka a part din Fandau  taje da saurin kafin Nabil yakaraso tacanja securityn kofan saida yazo yanasa  no akofa yace ba daidai bane yajuyo yakalle ta yace  "come an open
Tace "my star kashiga hankali ka mana yazaka rushe mana shirinmu da muka sha wahala, akai
Yanzu kana fita da ita asirin mu yatonu ko awajen ma aikatan gidan nane,
Nikuma nayin yaya da wanan tarin summan danatara aciki

Ahankali yasauke Fandau dayaga tanawani irin mika
Zaije wajen Hadim dan bai tabajin arayuwa ya tsani ganinta irin yauba dan jiyake idan yayi nasaran dankan ta sai yaga tadena nunfashi
Amma yana sauke ta fandau din tayi saurin rikeshi
tace" Muhammad inawannan wasikan da nabaka a haifuwan Fujjirat to dan Allah  shinakeson kakaiwa mama idan ALLAH yasa na mutum kayafemin abin da namaka badaidai ba."
"mata mazaki mutuba jikina yana bani tare zamu rayu zaki haifamin yara dayawa...
Hadim "tace dame kakirata mata fakace?
Nabil baisan metake cewa ba danshi burinsa yakwace daga hannun Fandau  ita kuma ta kenkemeshi da dukkan karfinta shikuma yakasa fizgewa dan lallaba ta yake dan gani yake kokamata yayi zataji zafi shine yaki kwace jikinsa da karfi

Take kenkeme shi Fandau tayi tana cije baki saiwani gumine yake keton mata
Tana salati cikin wani irin sauti take salati
Nabil yajuya yakalli Hadim yace" Halima idan baki zokin budemin kofannan ba wllh zammiki abunda baki taba sammanin wani mazai miki ba balle ne idan matata tamutu wllh kema saide ajera kabarin ku ai Hadim cikin wani irin kishi da hargagi takaraso inda yake tana nunashi Nabil nizaka kashi akan wata dani nayin silal haduwan ku zaka kira wata macce da matar ka ayu.......
Aibata karasa ba jin kukan jariri cikin sauri takara sa ta sugunnan tazaro jaririn da Fandau take shirin dannewa dan sabar wani sabon ciwon dataji wanda yafi nada yarfa hannuwa ta fara tanacewa yaya yazanyi da ciwon nanne
Nabil gaba daya yagama gigita  yarasa yazaiyin
Hadim ko tana zaro dan tazare ido kai my star wllh Namiji ne ALLAH Namiji ne fari mekamar mu har yafimu kyu wllh ban daba ganin jariri me hancin saba
Ina shi Nabil ta Fandau yake
Wani irin nishi Fandau tasakeyi saiga wani katon jaririn yafado ai Hadim dasaurin taje tasake daga wancen ma tace kai yan biyu duka maza ALLAH mungode maka
Fandau tasauke wani nan nauyen ajiyan zuciya
Tayi lamo ajikin Nabil da yakasa kowane irin yunkuri tsaba gen murna da farin ciki bai san yana mutuwan son yara maza ba sai yanzu da yasamu shiko mezai yiwa Fandau arayuwa yabiyata yazai da wannan farin cikin da tasashi kawai sai yakwantar da Fandau ya matsa jefe yayi sujjada yana meka godiyar saga ALLAH  nawan nan baiwa da yamasa cikin  watanni 10 yamasa kyutan yara 3 idan ba shiba wazai masa wanan kyuta sai rafkawa ALLAH kirari yake yama banta  yanda jikinsa yake abace sai da yadago yaji Fandau tanacewa dan ALLAH yaya ka daukesu sudena kuka
Sai asannan yajuya yaga ba Hadim a wajen da sauri yakarasa inda yaran suke amma sai yarasa yanda saiyin dasu dan cibiyan su ba ayanke take ba baisan yazaiyi yadauke suba sai wusilni ya suke a kan tyles yace" mata yazan musu sai ita Fandau dince tayinkura ta tashi zaune ta matsa kusa dasu tayi Bismillah ta daga dayan ta dorawa cinyan Nabil dayan ma tasake daurashi daya gefen jinyan nasa taso ta dauki dayan amma take ganin idan tayin nesa dasu zasu iya jin ciwo dan duk ajikin mabiyi daya cibiryar su yake
 Ta kalli Nabil tace "kamusu adua mana."
Yace"bari namusu kiran sallah ko."
Fandau sai kallon yaran da suke cikin jinin take yaran  shuwa sak ashuwan ma dama su Nabil nasu kyun daban ne'

Dagudu Hadim ta shigo hannun ta dauke da almakashi da zare dama iyasu ne agidan dan ma aikatan gidan suna ban garen su wana tsakanin suma da katanga zasu shigode da zasafe suyin shara sukoma  sai kuma masu abin idan suna son abu sumusu waya dan Hadim cikin ma, basosai ta kesa tsunman basai taji za ashigo,

Jikin ta harrawa yake ita tamanta da batun wani watan cikin bai cika ba murna kawai take tanason  ya kawayenta da family s
Zasuji aceta haifi twins kuma duk maza  farare
takara sa inda suke ta tazauna dabas ta kama dayan ta yanke masa cibiyan ta kulle tayankewa dayan ma
Tana daura almakashi daga Fandau har Nabil rintse idon su sukayi dan jisu ke kamar yaran zasuji ciwo
Awanan karon ma Nabil neyayiwa Fandau komai  suna futowa sukaga ba Hadim ba jaririn
Itako Hadim awannan bata goga jini ajikin ta ba dan tasan ba megani
Amma tana kaiwa yaran part dinsu takira wata acikin ma aikatan tace" tazota haifu matar da godu tazo dayake bature ba hankali bata gawani alamun rashin haifuwa ba atattare da Hadim saima santin yaran da taketayin
Hadim tace tanazuwa tajire mata yaran part din Fandau tanufa yayin daidai dafitowan su
Tace" my star ALLAH de yasa baka wanke kayan ba?
 Nabil baiko kalli inda takeba yaje yace"Fandau  yayane mezaki ci
 tace "kafara bani tea sai kafani abinci   to yace" yayi hanyan kitchen ita kuma tadan jingina da fukar godon yanzu kam ba abinda takeji jinta take sakayau ta kalle Hadim da tayi hanyan bathroom  tace "aunty."
Hadim tajuyo takalleta tace"yayane? Fandau tace "dama danaga yaran biyune shine nanemi alfarman ko zaku bar bin daya nima narike."
Kallon ta Hadim tayi ashake tace "ina miki wasane ko kindauka zan lalabaki irin yanda Nabil yakeyi har zaki dubi sabar idona kice mubaki danmu daya ko goma kika haifa alokaci daya bazamu iya baki koda hoton daya ba balle d'a
Naga kinaji dawani fallin rashin kunya sa anki daya yanzu zaki bar gidan nan dan yanzu zankira doc yamiki allura  Sani zai zo jibi kuwuce

Zama yayi dashir yana bata tea din abaki kuma yasa ayin mada pepper chicken nama kala  kala hadim tazo da kayan da fandau ta haifu  acikin wani baho
Yadaga yakalle ta yace"ina zaki dawanan kayan kuma?
Murmushi tayi tace "part dinmu mana ai karin sheda ne awajen inna ZAINABU dan bar mata zanyi tawake da kan ta idan tazo."
Tabe baki Nabil yayi yajuya yaciga ba da abin da yakeyin
Ita kuma tafice sabar murna yau kishin ma tamanta dashi

Sai aka hada komai yaje yakarbo yabaje mata a gaban ta dahuwan  saide kowanne idan ta taba saitaji lami hakan tasamu naman dawusu taci sosai sai da Hadim ta dameshi da kira akan yazo gashinan doctor Muktar da habiba dasu Amjad  Da usman duk har sunkara so
Koda ya tashi zai fita Fandau rike masa hannu tayi tafara kuka sosai
Zama yayi "yace mata ya akayi ne?
Cikin kuka tace"shikenan idan kafita wata kila bazan sake ganin ka inacikin hankali naba ko?

Yace"saboda me?
Tace "yanzu tace min yanzu zata turo amin alluran jibi muwuce da Sani idan yazo gobe."

Wannan fadan tane  kinga yau yayar babana zatazo yanzu haka saura awani kadan su sauka kuma idan tazo tare zamu wuce da ida  ko wajen jibe amma sai tazo dinde kinga ba muda wani lokacin cewa za akira doctor ko
Ki kwantar da hankalin ki idan na kaisu zan dawo ko suna bazan tsaya ayin dani ba zan daukeki muwuce Saudia ai namiki alkawari dama idan mudawo tukun sai musan yanda za ayi   shiru tayi
Shikuma yafita

Tun kafin yakarasa shiga yakejin shewan mutane maza da mata turawan da fakaken fata yana shigowa abokan sa duk sukayi kansa ban da doc Muktar da kollon inda yake baiyi ba gaisawa sukayi duk suka tayashi murna yana  a gurguje ya tsaya suka gaisa yawuce bedroom kai tsaye toilet yawuce ya sakarwa kansa shower yana wankan yana tunanin mezai yiwa fandau arayuwa kai kome nabata banbiya taba'
 Daya fito haka yasamu Zahran Amjad da habiba suna goge jikin yaran da man zainu  Hadim an hakimce akan godo sai amsan waya take ba kakkautawa
Da dare tunkafin zaukan Inna Nabil da abokan sa da securities dinshi sukaje taran ta Nabil yana hangota da gudu yaje ya fada mata sai kuma yafashe da kuka abin yabawa kannen sa Kamal da Grema mamaki yau Nabil da kuka meya sameshi Inna tadan zamoshi tasake kallon fukansa

 tace" Modu lfy usman ne yayi saurin cewa Inna lfy lau sai alkairi akwai albishir sai Munje gida tukun
Haka suka karasa gidan
Inna direct inda su Hadim suke akayin da ita tana shiga habiba tameka mata jariri Inna tace"meye dan waye
habiba tace"inna kibude kigani mana Inna tabude tace"aiwanan Modu ne jaririn sa karde kucemin Halima ta haifu dasauri zahra ta meka mata dayan ma idon Inna kamar yafado take kallon yara takasa cewa komai kawai sai Halima Halima take kira Hadim ta sunkurar da kai wai ita irin kunyan nan
Inna ta Kalli Nabil tace" modu dole kayi kuka sai itama kawai ta fashe da kukan ta zauna kujera tahada yaran  tana daga hannun tana godewa Allah tace" kubani abukar a waya nagaya masa."

 Dariya sukayi sukace ai kowa yaji dama kune dakuke hanya bakuji ba sai  dare sosai kowa yawatse ina tana shiga toilet tace karo da kayan jini a baho tace"aikin banza duk wanan taron kawayen naki ko kayan jinin ba asamu mai wankewa ba yau naji rashin hankalin irinna afuno yo ko hannu zaka sa awanke ai kawanke balle dagawa ka jefawa injin yawanke haka tazuba kayan a engine tas tagama tukun ta fito tana fadan da Hadim tace" basu shiga nan din bane basu gani ba nikuma dazun idan natashi sai indin gajin jiri shine nabari namanta."
Inna tace"dama yaushe zaki iya shiyasa fa dawatan haifuwan yakama nace bazan zauna ba zanzo kuke cewa wani karna zo
Shiko Nabil daga rakiyan abokai dakin Fandau yafada amma Baccci take yasameta dakani nagaji yane dakuma ramukon Baccci dan shi bcc inkaci bashin sa sai kabiya tsayawa yayin yazuba mata ido kunburin na fuskan ta yananan ajiyan zuciya ya sauke afili yace"yar albarka kenan yafito
Yayi saman karshi inda su Kamal suke suma suna shirin kwanciya yasamesu   dan haka suna kara gaisawa yafita
Daya dakin na gefen su har ya kwanta kuma ya tashin ya canja security yayi part din Fandau  har yanzu Baccci take dan haka yakwata agefenta yarungumo ta
Da asuba yatashi yayi alwala yafita masallacin gefen gidan sa wanda su basufi 4 suke sallahn asuba saboda karancin musulmai a wajen hakan ma 2 sai sunyin tafiya sosai  amma idan na ranane akwai wanda suke zuwa awani anguwan suyin jam i yau de yasan su Kamal sunzu
Tare ko suka fita

Da daren yayi Hadim saida tarena kanta dan Fujjirat kuka saita sha nono idan aka bada madara bata so gaba ruwan nonon twins  sunzuge idan Inna tace''hakan ma bata hadim harda kukan ta dan wani irin ja fujjirat take wai zata zuko ruwa ana cikin haka sai dayan yatashi shima kukan neman abincin yake ga doc Muktar agaban Inna yace kada a kuskura abawa jaririn nan madara kowane irine idan ba nono ba har zuwa wata 6 sannan adaura su kan madaran da yadace  tasan idan tace zata basu madara Inna  bazata bari ba daya nonon Inna tafita tasa jaririn aiko da karfi yaja saida tasaki kara  inna tace" ai dama yanzu sai kin daure dama tsosan namiji yafi zafi kekuma naga alama kinada tsoron tsosa Hadim cikin yarfa hannu tace"inna to ayaye fujjirat mana."
Inna tace" a a bayan zuba sai tacika shekara tukun kafin nan adage da koya mata cin abinci amma yanzu lokaci daya idan akacire ta zata sha wahala ana haka dayan ma yatashi shima da kuka Hadim tace"wayyyo nashiga ukku
Inna tace" karki damu nazo da garin kunun kanwa zan miki kisha yana gudano daruwan nono haka Hadim suka kwana ana kwantar da daya daya zai tashi bakin nonon ta yayi jajajir kamar ataba jini yafita sai faman gyangyadi take azaune ai koya nonon yazame abakin su zasu sawani uban kuka  har asuba Inna ta tashi tayin sallah ita kuma Hadim Allah yasota awanan karon tana rashin sallah  sai abin yazo mata adaidai  har pants  dinta tacire ta jefar a toilet dan Inna tasake gaskanta ta haka inna da ta shiga alwala tagani tadauka tawanke tana cewa Allah sarki ai wanan jaraban tsosan yaran ma zaisa ta taman ta garashin bacci
Hadim tana zaune ido yamata hulu hulu kowa yaganta sai yatausaya mata ba medauka ba ita ta haifu ba dan yanda tayin kaya kayan Nabil ma daya shigo saida yayi mugun tausaya mata daya tambayeta meyasame ta tafashe da kuka tace "kai bakaje kana Baccin kaba nina kasa yara sai kuka suke min sorry dama reno akwai wahala Allah zai baki lada

Fandau tana kulada jikinta yanda yakamata dan tanada wayo sosai ruwan zafi sosai take shiga kamar nawancen karan amma awancen nafari tafi jin zafi kodan wannan din bawani  girmane dayaran ba
Washe garima haka Hadim tasha azaba har yafi najiya itan kaganta har tafara rama sosai
Aranan sukayin shirin tafiya dan yan gida sun matsu suga wanan twins dan wasu ma harcewa suke zasuzo shine Inna tace to atafi dama ita tace ta gaji saita huta


 Nabil da zasu tafi yana ta kallon saman fandau amma bai shiga ba yasan idan yashiga zata masa kuka jiya de yabata waya yace "zaina kiranta dashi  amma kafin yabata saidaya settings din wayan number sane kadaya zai shiga


A meduguri fadin murnan da family din nan sukayin bata lokacine misaltashi kowa yagani yace kamar kara katsaga da ubansu Iya ko kishiyar ummi haka tace har zafin irin na Nabil ne dan yanda suke wusulniya shima haka yayi yasha faduwa amannun mutane idan yabank'are shiyasa kakar sa tasamasa shitta
Kwana 3 Nabil yace zainafi Hadim tace "haba katsaya mana suna jibi ne yace "tafiyan nefa yakama dole sai naje" wane abune da bazai yuwu kayishi online  ba kace dole sai kaje ko uzurin can din yafi kanunawa Duniya murnar kyutan da ALLAH yamaka."

Ai kyutan da ALLAH yamin basai nanunawa Duniya ba wanan tsakanina dashine dan bawani ne yasa yabani ba nema bani nasa yabani ba,
Ana miki maganan meeting ne gameda companyn mu kina wani zance
"Amma ai general manager yana nan basufiye neman kaba."
"Waine meyasa kikafiye son jan zancene bayan hakan bazai sana fasa ba."
" zuba masa idon Hadim tayi meyake damun Nabil ne yanzu badama tayi masa kyara ko shawara bazai dauka ba wanda da kome tace daidaine awajen sa nunfasawa tayi tace tom "amma da Sani zakutafi ko?

"yayi me?
"yatawo dawanan yarinyar munyin da doctor agadys ta samo alluran sai kusame ta kawai  amata yazo da ita ."
"A a Sani nabashi aikin company nan yakusa kammaluwa amma naga anfara mun wasa da al amuran shine nacirin ahannun Sandan da Bunu nabawa  Grema da Sani jiya naje har an sa suna sunan yayi   fujjirat Muhammad akasa baro baro
"amma kai kace susa natan ko?
"Yees ninace."
Hadim batasan dalili ba kawai sai taji ba dadi ai kwara yabari asunan sa nada dayake sawa *shidmas*
Kasa hakuri tayin tace kawai sai kasa sunanta bayan da sunan ka kake amfa ni dashi kumama ga maza nan sai asa na macce bayan na gaba ma bakasan abinda zamu samu ba ni kacireni sawun mata masu haifuwa ne."

Saida yakare mata kallo yace "baki ji ance ko dukane karbi nafari ba ai duk wani da dazan samu bayan uwata yake dan hakama jiya nasiyi file zan gina mata company nata na kanta akudinta da kungiya ta bata dan jiya ankawo min korafin duk girman meduguri bamuda company man abinci atake na bada umarnin memo inda yadace yayi kuma muje dan har ansiyi filin yanzu za afara aikin( *Fujjirat groundnut oil* )
Ai Hadim ido ta zaro dole ta batar da Fandau karma watarana tane mi tada mata hankalidole tayin abinda yaran nan zasu zama permanent
Awajen ta
Tanacikin  wannan  tunanin sanda tajin  fujjirat tana tamata kwaranci wai tana mata bye kafin tabude baki har Nabil yafita parlor gagida acike ba daman magana ga tanason taji towane shawara yayanke akan yariyar nan ita kam ayanzu tanaganin alluran mantau yayiwa Fandau kadan ga ita bata san bin malamai ba yazatayi  tana jitana gani Nabil yayi sallama dasu ummi  yafita,

Yara sunci sunan bilal da kuma Habubakar  baban nabil dan haka suna kiran su bilal da maaruf suma ansha shagalin suna

 *YAU FANDAU  A KASAN SAUDIA*

Amma ita kira take ita bata gane ba saita ganta ak'aba
Nabil yace"a a sai kin samu tsarki dan kiji dadin ibadan ki muzauna a Riyadh kawai kafin kisamu tsarki
Ai ko ko awanan zaman Nabil yana rage zafi da Fandau ga yana kula da magugun ta yakar bomata awajen mama Kafin yabar garin
Ba inda yake fita kullum suna makale da juna koda zaije gaida sarkin Saudiya zuwan bazata yayi musu saboda yan jarida shikuma yanason zuwa da Fandau tare sukaje Fandau de jinta take kamar aduniyar mafarki bai san dalili ba idan abokan sa na larabawa suka zo aidashi faya shayin nuna fandau amasayin matar sa sukuma basa ganewa tunda tana cikin shijab d nikaf wani wani company yakaita na gyaran jikin ta mata  sun yiwa Fandau aiki sosai fadin yanza Fandau takoma bata lokacine sosai sunfito mata da  colour chocolate dinta sunada kwana 10 a Riyadh Fandau ta samu tsarki lokacin tanada kwana 18 da haifuwa ai ranan Nabil bai hakura ba dayake dama amatse yake saida yahana ta saket
Washe gari dasafe bayan sungama break yaja kujeran sa gaban ta yace"Fatima
Saida Fandau taji wani yar ajikinta" dama kasan sunana?
Murmushi yayi yace"bansan sunanki ba zanmiki passport din fitawani kasan."
Ai sunan ki narike shitun sanda kika furta minshi Fatima amma anakiran ki Fandau kokin manta ranan acikin shid hotel lokacin kina me allon ki
Dariya tayi tace  "yanzu ma aini me allo ce wazai ki karatun allo yafi zama akwakwalwa."
Yace "Fatima shigowan ki rayuwata kin shigomin da abubuwa dayawa cikin na alkairi kinbani farin ciki maran misaltuwa arayuwa wanda bawani nunfashina dazai wuce batare da yawuce da tunanin kiba kowane irin bacin rai yasamemi ke nake sawa arai naji kin yayemin
saide wani babban matsala idan natuna rabuwa zamuyin dan koyau Hadim tasa kafar ta cikin London zaman ki yakare agidana wanda nikuma shine babban tashin hankalina."

Fandau tace" kana sona ne?
 Zuba mata ido yayi  yace "ai wani son baki bazai iya furtashi ba idanu da ganganjiki kawai kenunawa."
Tace" kenan baka sona ko?
Batarai yayi yace" karki kara tambaya na batun so
Yanzu abinda yake gaban muyafishi mushin manci
Kuka tasa tace ai dama nasani bazaka taba sonaba shine Sani yace" wai zakasoni
"audama munafircin da kuke kulawa kenan keda Sanin ko
Tace" shikenan za amin alluran ko?
Yace"bar wannan nifa mafita nake nema kin kasa nusuwa kigani nufina
Yanzu me mafita bazan iya rabuwa dake ba sannan bazan iya kai kaina gaban malam amatsayin wada ya dauke masa yar ba dama badan malam bane baban ki dasai nace zain iya yin hakan amma yanzu  kinsan bazai yiwuba in keta idon mama innuna nine nayi mata wanan aikin ba
kinga kebazaki iya zuwa gida dasunan kin batane kika fito ba dasai nace" kije daga baya sai nakoma na aureki yara kuma kibarwa Hadim kawai allah yabaki wani
Fandau tanisa tace" hakan bazai yuwuba dan agidan ansan guguwa nayi har nabar musu wasika kaga banida bakin cewa ansaceni ko mama baza ta yarda ba."
Yace "Shine aina cemiki alluran shine mafita."
Tace "danme baza ka kai kanka wajen baban ba ba ALLAH mamuna masa lefiba kuma munemi yafiyar sa yakuma yafemana ni ina macce banji tsoron zuwa dakai amatsayin  nayi aure bada sanin iyayena ba sai kai namiji da yakamata kakaramin karfin guiwa zaka ce bazakayi rai abace take maganan."
Shiko bayason bacin ranta dan haka jawota yayi ya rungume yace "za ayin abudaya yanzu kitashi ki shiya kar murasa jirin yanzu zamu shiga cikin makka jin haka tasakin ranta

Fandau da taganta adakin ALLAH tameka kukanta sosai wajen kwanan ta ukku can tatare Nabil yayi yayin taki binsa gidan sa wanda shine masaukin su idan sunzo sarkin Saudiya ne yabashi 
Yau sunsha pic da Fandau acikin k'aba  tayi mugun kyu Nabil ko dama mekyu ne sukan su larabawan sai kallon su suke dan sun burgesu  sai daukan su hoto ake tako ina dan kowa yana soyaga yadauki picture  din ficece Nabil

Suna kwance cikin  bathtub rabin jikin su ajicin kunfa amma Nabil duka hankalin sa yana wajen kallon labarun da akeyi  Fandau tafaki idon sa tadauki su pic ahakan  ta tashi cikin dabara tafito
Azuciyar ta tana cewa wannan shine  *DAMATA* nafara sa muguwar kuka
Da sauri ta bude whassapp dinshi dan whsp shiya fiye mata saukin taturawa Hadim pic dinsun wada sukayin ak'aba dawan da sukayi acikin wani kayataccen waje sunyi kissing din juna da nayanzu nacikin bathtub sai da ta tabbarar yashiga sanyan tayin  delete dinsu ta ajiyen wayan ta zauna akan mirror ta fara makeup

Hadim da jaraban chatting tana kan online yashigo tasauri tayi murmushi tace my star ansamu wani abun cin dariya kenan wanan pic rututu haka  tana shiga ko hotona suna budewa idonta  yaci karo da wannan bakin ganin wada inda gayi mata akayin ko mutum zai hadiyi Qur ani bazata yar daba  mijin yadauki wanan yariyar yajen saudia kuma yashiga cikin cikin bathtub daya shida ita kwance ai dawanan mugun ganin kwara mutuwanta wani irin razanenen kara tasa tare da jifa da wayan tana cewa Nabil  Nabil  tana nuna wayan ai da gudu yan matan tasuke parlor suka shigo lfy suka ce ganin tana nuna wayan yasa amma bata cikin haiyacin ta yasa sunzata nabil mutum yayi duk suka gigice Jidda koji take nunfa shin ta kamar zai dauke  da saurin Ashuwa ta  dauko wayan tana dubawa tagani tasauke ajiyan zuciya tamekawa sauran suka gani  sai asannan ahankali su yakwanta dan tunanin mutuwa ne kawai zai cefa mutum cikin wananan hali amma sunyi mugun tausayawa hadim dan taciwo ace anturo maka hoto miji da karuwa sunbatu Hadim tafara tana jifa da duk abin da tasamu  wllh kasheki zanyi idan na kasheki na kashe banza wato kun hadani da renon yaran ku kukuna cin dunya fujjirat tana haka ta fara kuka ta zowajen ta ai wani irin cille Hadim tayin ta ita wan ko shakka babu yarinyar ko bata suma ba zata samu karaya gadon ta hau ta dauki maaruf da yake bacci shima zatayin cinlin dashi da sauri suka kar bi yaron dama BilAL yana parlour
Da yasmin da fanta gana suka rike ta su Jidda suka fita da yaran da gudu amma ganin yanda take fusgewa ta na dukan su sunsan yasmin sun san bazasu iya rike taba da tafara dukan su kawai sai suka saketa suka fita da gudu kafin ta karasa suka rufe kofan suna jinta tana cewa kukawo yaran nan Wllh ta kansu zanfara afin uwar su da uban

*Tofa masoya kuyin hakurin yanda kuke *samun posting bayan da kuke soba Ahankali komai zai daidaita*

*B JATTKO*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMATA*




               *NA*


*BATUL ADAM JATTKO*

*Wanan page nakine*
*AUNTY SIS*
*Allah yaraya mana*
*IBRAHIM KHALEEL*

*MRS OMAR*
*AUNTY MEJIDDA MUSA*
*MMN FARIDA*
*MIE MIE MIE MIE*
*Ina mugun tare daku tare kuma da soyayar ku kuda duk kan masoya mabiyan DAMATA*

*35*


dagowan da zatayi ido 4sukayin da Nabil da yajima yana kallon ta cike da zargi damashin kullum acikin dar dar yake idan Fandau da daukin wayan sa to yanzu mayana saneda yanda tafita da wayan cikin tsand'a shine yayi yabiyeto amma shi tunanin dama idan tadaukin wayan karta kira malam ko Mama yana fitowa yaga tana tura abu jikin ta harrawa yake karasowa wajen yayin
Yasa hannu ya dauki wayan yabude  dama wayan a setting yake inde bashi bane yayi amfani dashi to sai yanuna masa abunda akayin da kuma fuskan wanda yayi amfani yana shiga yanuna masa komai ido yazaro cikin tsoro yake bin bayanan wayan tabbas Hadim ta turawa
Meyasa yariyar takasance hakane danme tafito cikin mata masu miyagun hali masu tona tsirrin aure
Dagowa yayi yakalle ta dum gaban ta yafadi dan bata daba ganin sa cikin wanin yanayin ba idon yayi ja kaman nisa sun janza kamar wani zaki take ganin kallon da yake binta dashi kadai idan kaduba kasan ransa amugun bace yake
Cikin mugun tsoro ta jada baya
Tace" abban Fuj lfy?
Kasayi mata magana yayi yana sauke wani nunfashi dan idan yace zai furta wani abu tabbas yasan zai fadi kalman da yasan daga baya bazai  mar dadi ba idan ransa ya bace haka yake tunyana yaro dan ko agida ansani idan kuma yace duka zaiyi yasan bazai kyalita ba saiyaga tadena nunfashin akwai ranan da ogan sune ya bata masa rai daya dankeshi sai dakyar aka samu nunfashin sa yadawo daidai
Dan haka wajen  whadrrop yayi yabufa ya bude yasa kayan sa yafice
Tana binsa da kallo yana fita ta sauke ajiyan zuciya tome aka masa nide nasan nagoge lefin danayi wata kila shida matar sane taga sako daga kafada tayi taci gaba da makeup dinta

Sunyin jugum jigum a parlorn ga Fujjirat da take ta kwala musu kuka tana ta shafa goshinta inda ya fashe yana fitar da jini
Suna cikin haka Allah yakawo hanef     yace"ku kuma lfy kunsa yarinya gaba tana kuka haka ina uwar ta sai asanan yaga suma ahe hawaye suke yace "ba tambayar kuna keba dan uban ku".

Gana ce tamasa bayani yace"bani wayan nagani." yasmin tameka masa

Dayagani ransa yayi mugun bace
Yaza ace  Nabil yayi haka atake ya kira Nabil

Lokacin Nabil yafito kenan ransa abace bai sanma ta ina zaifara ba yanaganin kiran Hanif ya daga
Haba Yashid meyasa zakamana haka acikin yara yanzu dawani ido zaka kallemu kai da yaka mata kamana fada....

"dakata yimin bayani meyafaru?
Hanif yamasa bayanin komai
Nabil ransane yasake bace Hadim  zata kahemasa yara akan abinda bai kai yakawo ba ina duk sonda take musu

"yanzu kai aina kake?
"Ina gidan."
"ina nufin kana gaban yaran da abin yafaru akaban sune?
"Hanif yace"eh
"sunta ramin wadanan mahaukan kawayen nasune ko iyasu na gidane?
Hanif yace " duk yan gida ne
"wayan Hadim din yana hannun wa?
Hanif  yace"gashinan ahannu na."
"to samin wayan  naka a handsfree
Yasa
"Nabil yayi gyaran murya yace" kuna jina sukace eh"
"kunawane awajen?
Sukace
Yasmin Gana jidda Ashwa Zahra mu 5 ne."
"ok Hanif ne cikon 6 ko?
"eh
"to idan naji wanan maganan yafito a family zanyi muku abin da baku taba tsammani ba kuma bani baku ko abin da nayiwa mutum na baya sai yabiyani balle nasake muku wani abu idan inada matsayi ko kima awajen ku ingani akan wanan."
Dasauri harsuna hada baki sukace "Allan Yashid bameji
Dan idan Nabil yace yadena musu abubuwa sunbanu dan shine ta kamarsu idan sabon motane acikin garin meduguri awajen su ake fara gani duk bawace bai budewa account ba duk wata yana dura musu kudi
Sa ansu ma yau yasu yasu dan suna da tara kawaye sosai

Nabil yace"good kurike min sirrina."
"insha ALLAH Yasihd

"Hanif inason kayin delete din pic din gaba daya katab batar baka bariba sannan yaran tunda bata so zata iya hukunta su da lefin uban kadauki twins ka kaiwa ummi ko Inna,
Kai Inna mayadace ka kaiwa dan nanne inda baza taje tace zata karba ba,
Sai Fujjirat ka kaita Gargar  gidan Zannah wajen, Mama Aisa kace injine anyayeta tarike ka tsiya madara da duk abin yaro zai nemaka kahada kafin ka kai ma zanmata waya."

Hanif yace" to amma yaya kaima fa kasan baka kyuta ba yaza kamar waya inda wata karuwa zata.....
"kaiiii plustop.
 Hanif duk da ba agaban sa yakeba saida jikinsa yafara rawa
"sorry Sir
 Nabil saida yasauke wayan akunne yanafitar da nunfashi ahankali yana karajin haushin Fandau ita tajawo aka kirata karuwa,
Inama agaban tane daya bari Hanif yakasa fada yaga yanda zatayi
Saida yadan daidai ta nufashin sa
Sannan yasake kara wayan ajunnen sa
"yace zakayi yanda nace ko nanemi wani yamin  "anyi angama har nayi delete din pic din saura kaiyaran kawai."
Tsaki Nabil yayi tare da kashe wayan

Hadim bayan takama buge bugen ta tagaji ta zube awajen tafara kuka shima saida taji ba dadi tayi shiru
 Me Nabil yake nufi da turo mata wanan abin yanason fasa mata zuciyane yazauna da wanan y'ar da yake ikirarin  ko ganinta bayaso yafara sonta ne dasauri ta girgiza kanta no nop Nabil dina ne nidaya bazai min hakaba bincike ya kamata nayi

Dasauri daduba saitaga  daya wayan yana nan da sauri ta karasa
Dialing Nabil bai sammaci kiran Hadim ba dan bai gama tattara karyar sa ba danyana zaune nazarin yanda zai bullo mata kawai yake
Sai kawai yadauki wayan da burin kunya
"mezaki cemin kinsamu nasaran kashe sunne kika biyo uban ki kashe ia dan kince zaki kashe yaran wllh bazan ga lefin kiba ai ketaka hayece ba sanin ciwonsu kikayin ba da ace koda bari kin tabayin da baki, fara hakan ba
Amma gwara da hakan tafaru nasan yanzu baki cancanki kizama uwa ba agare su....
"dakata Nabil  ba yara da kai kanka ba nikai na inhar ya tabbata son yarinyan kake,
Wllh wllh bazan yafewa kainaba nawa jinin ma ya halata awajena na zubar balle naka kona yara,

Abinda nake gudu kenan ni zan siyowa kaina kishiya ace yaran da nagama nunawa Duniya suzama banawa ba ka k'askan tani,
Wajen kawayena kai kanka kasan rayuwa ta batada wani amfani,
Sai kuma tafashe dawani irin kuka mai ciwo tace "Nabil gayamin, Gaskiya kar kaboye min nasan ada kai mesonane naci darajan soyayyan  da ina sonna sanwani addua, tamaka nasu na yaran malamai tayi wani kulinne kawai gayamin yakake ji wllh asiri ne?
 "ai yanzu baki bukaci kijiba kibari sai kinshirya jisai kimin mgn."
Yana shirin kashe wayan
Tayin saurin tace"karka kashe kabari gayamin Gaskiya wllh banzan rayuba ."

"my one tunda kince gsky zangaya miki iya gsky amma kiyiwa uzuri na kyakyawan fashita,
Kema kinsan yariyar nan tamana abin Alkairin da duk abinda mukayi mata bamu biyata bako,
Shine nace mata mezamu mata wanda zataji dadin sa kafin mumata injection shine,
Tace ita tanaso akai ta makka tanemi yafiyar Allah to kinga idan nabarta ita kadai ta tafi idan ta gudu yazamuyi,
Shine kan dole na kawota,
Sai yanda akayin kika ganmu cikin bathtub awasan ku na karshe an bigemin hannu har kema kin nacewa naji ciwo ne nace miki a a to naji na boye mikin ne kawai, dana, shiga wanka ne na kasa wanke bayana, sai dana kirata nace tawanke min,
Sai maganan pic din mu aharami kuma  bani na dauka ba wasu ne nima ayanda kika gansu haka na gansu amma kema kinsan yanda duk inda nashiga sai nasamu masu daukana pic to ita kuma muna tare kinsan den bazan yarda tamin nesa ba,
 inaga sundanka matata ce   wani ne yaturo minshi aganin sa yaburge nine wai hakan tonasan wata kila wani ya daura a media kigani shine nayin saurin turo mikin dakaina dan kar asamu kuskure sai gashi ansamun wai harda neman tona mana asiri haba my one da munafurci naso ko cin amana ko son yariyar ai bazan turomiki dakai ba."
Ajiyan zuciya Hadim ta sauke
"tace yanzu duk wanan ruguman da kissing din hadawa akayin?

"yazaki min wanan tambaya sai kace baki sani ba namuma sonawa ake hada wanda yafi wanan ma."

"Gaskiya kam amma wllh sunkusa susa zuciya ta yabuga wllh."

"kai my Love you baki fine jin haushi ba shiyasa naturo miki dan muraba haushin tare ai."

"kai koda kakusa rasani kasan ko dama tunkafin nabude nace amsamu labari kenan dan nasan bakabarin labari yawuce ne."

Dariya Nabil yayi yace"ai ina sonkine ummu Fuj."
Sai asannan Hadim ta tuno da y'ar ta tace "kai najiwa my dear Fuj ciwo fa inaga ga yaran nan sunrufeni yazanyi."

Bata rai Nabil yayi kamar yana gaban ta
Yace "kekika sani
 de."
"dan Allah my star kace subude ni naga yarana."
Kashe waya yayi
Yana kashewa yakira Inna bayan sun aisa yace"Inna Hanif yakawo su Maaruf?
"Eh."
"yawwa Inna suzauna awajen ki kafin nadawo."
"bangane kafin kadawo ba kana katsan ne anjima zaka zo kadauke su".
"a a ina saudia yanzu haka
Mundan samu sabani neda Hadim shine tace bazata rekesu ba."
"dan Allah jimin wani surkullen akan fada da miji zakice bazaki cigaba da rike yaran ki ba yaran da ko kwana arba in basuyin ba ni daya kawosu ma fada nayin meyasa yafito dasu idan inason ganin ba inazuwa na gansu ba,
To akan me kukayin fadanne?
"yace Wllh Inna kawai acikin  haramine wata yar Nigeria tagan ni shine tace tana son muyin hoto da ita mukayi dan kar ta gani awani wajen ma sai naturo mata da kaina ta gani shine ta tada hankalin ta."
Ai kin banza tunda ta aiuri dan ball badole tadan ne zuciyar taba dan daukan hoto kawai zata tada hankalin bayan tasan kai din sha hararren ne to matan yan wasan kwaikwayo fa suyin yaya,
Bari naje nasame ta namayar mata yaranta."

"Inna dakin barsu."
"inbar su nayin yaya dasu ai reno sai uwa musamman yanzu su suna bukatan dumin uwar su
"ke Yana tashi ki kaine gidan...
Nabil yakashe wayan yana juya maganan Inna *ai reno sai uwa musamman suyan zu suna bukatan sujin dumin uwar su*
Anya nayiwa yaran nan adalci idan aduniya asiri bai tonu ba alashira nace musu me?

Mama Aisa tunkafin Hanif yakarasa Nabil yagaya mata gashi za akawo mata yar yaye murna awajen Mama ashe da guntun kimanta a Duniya zata reni yarda ba Bagana ce ko Fandu ta haifa ba ashe da inda ake ganin ta damutum ci haryanzu ita ko arayuwan nan tarasa ina Nabil yakeson kaita yasiya mata mutumci ya mayar da ita mutum dan yanzu kishiyo yinta masun subar da makaman yakin su bin bayan ta suke dan suna kawo mata bukatun su ta gayawa Sani yamusu bama sai Nabil ba duk da agefe suna mugun jin haushin ta amma bayan da zasuyin da ita dan sunbi malama duk idan sukaje cemusu ake akwai alkairi meyawa atare da ita idan sunaso subita kawai dan me ibada ce basu isa dosan taba

Tasake kenkeme yarda taka jinta tamkar Tajudin dan gidan Bagana afili tace "dole naji son ki Hajara mahaifin ki mesonane

Hadim bayan Inna tazo tagama mata tatas ta tafi tabar yaran kenkeme yaran tayi tana kuka  tana musu magan kamar manya
"kuyafe min wllh wasu ne suke son cutar damu ina sonku yarana.''
Su Ashwa sai dariya suke mata dayake Hadim ta gayamusu  hada hoto akayin kawai dan sunga suyin hoto da Nabil sunzata matar sace

Ranan wuni sukayi suna kwaikwayo abinda Hadim tayi  amma ban da Hadim da tunani ya addabi
Kwakwalwar ta yanzu Nabil yana nufin tare suke da yarinyar rannan adaki daya kome?
Ke idan ba tare suke ba ina zai ganta har tawanke masa baya karde daki daya suke kwana meysa yarinyar nan ta canza tazama wata kamar black  American daganin fantan ta irin wanda aka kashe masa manyan kudin nanne yanzu haka shima Nabil yake kanin ta inawanan laushin na fatar ta yananan ne dawanan hannun nata me laushi takama wanke masa baya aide idan sauran pic din editing ne ai banda wanan nacikin bathtub din kuma idan tagani adaidai arungume tagan sun nanma wani kara tasa da yafir gita su jidda tace inawayana?
Nace ina wayana?

Fandau tagama shirin ta tana jiran Nabil zai kaita sauran wuraren ziyara dan gobe zasu zuce Madina amma tunda yafita rai abace bai kara shigowa ba gashi har azahar ta kusa ta dauki wayan dazumar zata kirashin sai gashin yashigo still ranasa abace ko inda take bai kalla ba zaiwuce bedroom
Tace "haba mijin tunyaushe nake jiran zuwan ka kasan zamufita.....
Wani kallo yajefa mata da saida hanjin ta yakada
Yace"kuskure mafi girma da zakiyin na kisake kirana da mijin danni bana mata da macce me bude asirin aure mekuma son tadawa mijin ta hankali dan nagodewa allah dayasa na gano halinki muna fuka ke anufin ki kita  damin hankali kitadawa matata ko to kisani ko pic din muna six kika dauka kika turawa matata nasan hanyan da zanbi nawanke kaina kece akwana ke inbanda butuluce ma kyayiwa Hadim haka idan badan ita Hadim dinba wllh ko ayar aikin gidana baki isa kizoba balle har aure yashiga tsakanin mu."
Maganan fita dake kuma angama sai de ki hada kayan ki gobe zaki koma kasan da kika zokiyin zaman dakin dayan da kika sabo kafin my one tazo ta san yanda zatayi dake dan dan ita kikayiwa lefi ita zata hukunta ki tace zata miki abin da baki tabajin anyiwa wani ba ciki harda batun hadaki dakare yabaki  HIV ni ne ne mehanawa nikuma yanzu nadena yayinki sai kin kamu da shi musamiki allura muyasar dake kinga kowa zai gane yawon banza kikaze." yana  gama fadan haka ya shige daki tare da banko kofan
Sugunnawa tayi awajen tarasa koda bakin kuka yanzu bazan cinasa ra bakenan su sune da nasara kullum meyake faruwa akaina hakane meyake faruwa dani alhakin Mama ko tabbas kowa yabar gida gida yabarsa

 ina kunyin karya Nabil kaida muguwar taka  dama da nikaf dinta da shijab agefe kawai sai tazara dasaurin tanufi kofan fita Allah yabata sa a kofan abude taketa dake dama ba megadi a gidan tafiya take cikin saurin duk da tana ganin Text amma ita rabon ta da tarike kudi a hannun ta tun a Nigeria wanda Nabil yabata tabari dinnan dan haka tafiya kawai take

Nabil dayaji kiran sallah azahar yayi alwala yafito baiga Fandau ba a parlour   a zatan sa tashiga toilet din falon ne yawuce daya dawo sallah bai ganta ba tunanin sa  tana bedroom yashiga dakin bai ganta ba wasa wasa ba inda bai duba ba bata kidan dasaurin yazaro wayan sa yakirata yana ringing amma  bata dauka ba bata gidan kenan tagudu  na shiga ukku wannan sausayin ne yasa nafar kofan abude kenan asirin mu yagama tonuwa   bata fita da dakardar izinin shiga kasa ma yanzu za akamata a aunata Nigeria tatona asiri mezan cewa  Mama d Malam  anyi Baba bazai tsinemin ba lalle babban matsala yana shirin faruwa dani
Wanda kwara na kaiki da hannu na Fatima kar kimin haka wllh maganan da nagaya miki a iya fatan bakiya yake ba harzuci ba bazan iya rabuwa dake ba dan kiyin hankali nagaya miki haka kuka yasa ganin hakan bazai karbe shiba kawai saiya dau waya ya kira abokin sa Abdallah dan sarkin saudia ne yamasa bayani yace susamu matsala da matar sa tafita yasa jamia tsaro su nemeta Abdallah yamasa jajen yakumace yakwan tar da hankalin sa za a sameta
Abdallah yasan Fandau kuma yana da pic dinsu na haramin dan Fandau da tace tana son abude bata kaba Nabil shiya kiran yazo aka bude musu suka shiga dan haka yace zai baza hoton ta
Dasaurin Nabil yace "a a kar abaza dan yasan idan anbaza anan ma atsirin zai sake tonuwa
Abdallah yace "to tunda tafita bawani takadda ba visa ba paspot yanzu za akamata zaisa afita kame gadan gadan a layin yanzu  za ama kamata kar kaji komai."

Nabil yayi shiru
Yanzu idan ta tafi yazan yin  idan ba asame taba

*Niko nace ga rigiman Hadim ma agaban ka idan taga wayan*

*Tofa masoyan Fandau kuta ya Nabil adua*

*Yaude nasan namuku typing*

*B JATTKO*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMATA*



                *NA*


*BATUL ADAM JATTKO*



 *Wanan page gaba dayan sa nakine*
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
*nagode danuna kaunan ki gareni*
 *B JATTKO takice* 🤝

*36*


*G*aniyayi zama bazai karbe shiba kawai saiya meke yazari key dinsa dama motan yana kofan get sai yanzu yake nadaman hana Security's dishi binsa da suna nan basu bari Fatiman sa ta fitaba toma tunyaushe tafice ne?
Dasauri yayiwa motan key yaja dagudu hanyan harami yayin yana zuwa inda suke  zama da Fandau baneman da bai bata ba acikin har dare yana zakawa wata yakani kamar irin tsawon ta daya da Fandau dayake kowa cikin nikaf ne yazaci itace da sauri yaje ya saida yaje kusa da ita ya kusa daga nikaf din ma amma sai yaga hannun balaraiya fala sol yamatsa haka yake tabin mata masu kai daya da Fandau ga masu binsa suna *shiddams* larabawa da bakaken fata ko ta kansu bai biba abin da yake tsayar dashi  lokacin sallah Abdallah yakirashin yace "yana ina ba afasamu Fandau dinba dan gashinan shine da kansa acikin sujin din duk Waccece aka kawo sai yasa ambude fuskanta amma ba ita gashi ka hana abaza photon dinta da ansame ta yanzu koda gida gida za ashiga

Shiru Nabil yayi yama kasa magana  sai wajen 2 nadare ya koma gida yan dashi baiyi bacce ba haka bai bar Abdallah yayi ba dan cawa yayi wllh  duk yanda zasuyi sune momasa matar sa ranan gsky anyi kame wanda a suban fari Nabil bai hakura ba saida yaje sujin din yaga matan da aka kama abin tausayin sai kuka suke atake yamemi alfarman  asakesu umarni Abdallah yabada sai gashi har tsofin kamu sun samu fita  basu bar sujin din ba sai wajen  karfe  10 nasafe Nabil sai dayaga angama kashe mutane kakaf  yayiwa Abdallah gdy kowa yayi nashi gu

Fandau bakara min tafiya tayi ba kafin tasamu ta isa haramin tana shiga ko alwala batayi ba ta fadi awajen tana kai kukanta wajen ALLAH saida tayi tagajin ta tashi tayi alwala tayi sallahn laasar dan tana hanya akayi dan bakaramin tafiya bane tsakanin k'aba da gidan Nabil dan haka acikin k'aban ta kwana tana kai kukanta wajen ALLAH sai da gari yawaye wata da itama dagani bauta tazo takalli Fandau tace " zanso naji meye damuwan ki haka kina yarinyar ki kina kuka kina magana kedaya kuma nasan da Barbarci kike magana dukda baji nake ba ni yar Nigeria ce shiyasa nagane yaranda kike sai da nakura mikin ido da mukaje alwala naka ashe harda zanen kanuri a fuskan ki amma kananane  medamuwanki?

Fandau cikin hausan ta irin na barnawa
Tace "gidan mudani sa kuma najefar kudin motana."
Matar tace "ayya agarin gudu ko wllh jiya kame  ayi sosai nema shine nakasa feta."
Shiru Fandau tayin matar tace "inane anguwan nakune?
Fandau tace "bansan sunan saba."
Yanzu idan nabaki kudin mota natare miki zaki iya gane anguwan akaiki?
Dasauri tace"eh tare suka fita da matar ta tare mata texi tanatuna masa har  sukaje kusa da layin yayin parking daidai layin da larabci yace "tafita ba ashiga da text  anguwana nan dakyar Fandau ta dan hada kalaman sa kasancewar malam yasa anakoya musu larabci kuma haduwar su dasu Hadim yasa ta koyin larabci dan dashi suke magana yawanci sauka tayi  take takawa Ahankali tana bin anguwan da kallo da gani irin anguwanin manyannan ne har ta karasa gidan bataga mutum daya ba kodan safiya ne gidajen anguwan duk irin dayane ban abin da yasa tagane na Nabil saboda tambarin ball dayake jikin gidan har ta karasa gidan  tana tura kofan a bude dan Nabil bai saya korufewa ba
Bedroom ta wuce ko wankan da take sonyi batayi ba dan idonta fal bacci

Tsabar fargaba ko gajiyan bayaji ahaka ya kara so gidan kansa yana juyawa amma mamakin sa yana shiga bedroom yaganta kwance tana zugar bacci tunanin idon sa gizo yake masa da saurin yakarasa indan take Ahankali ya tabata saida yatabata yajita ahannun sa tukun ya gaskanta ba gizo bane Fatima yafurta cikin wata iriyar marya dayake batayin nisa abaccin ba sai ta bude idonta idon cikin nasa take masa murmushi kamar bawani abinda yafaru

"ina kikaje?
"najen dakin k'abane. "
Ajiyan zuciya yasauke tare da matse hannun ta yace"karki kara irin wanan fitan kinta tamin hankali tunjiya nazata kin gudune."

Murmushi tayin tace" nagugu sai kace Fatiman mahaukata duk wanan abinda kuka min kuci bulus,
Bakudurin gudu a raina najene nakai kukana wajen wanda rayuwa ta yake hannun sa dan haka kaga gudu banawa nane dan na ALLAH shine Gaskiya kuma mafi alkairi haba nagudu aiko ku kuka koreni yanzu bana fada dan kamar yanda kuka cika burin ku akaina nima kina jiran *DAMATA* incika nawa burin inaganin yakusa zuwa kuma ai nabar *DAMATA*."
"meye burinki akanmu?
Murmushi tayi tace "ai meyin baya fadi."

Kallon ta yayi wani lokacin ganin takun ta yake kamar babba
*Meyi baya fadi*
Mezata mana kenan
"kina nufin zaki iya cutar damu kenan?
"kai Yaya yakake neman yimin wayo ne na fada maka abin da banyin niya ba kuma sirina wannan ma ai tambayan kurene wllh."
"Saboda ke munafuka ce bazaki fadamana ba mukuma da mukeda zuciya daya komai sai mun fada miki."

Zame hannun ta tayin ta mekin sai da tayin taku kamar  4 tace tabbas da kaida matar ka kunada dabara idan anyin duba ga yanda kukaci nasaran aurena har kuka samu yanda kuke so kunyin damara amma bakuda wayo bakwa aiki da basira bayanzu naso nagaya muku ba kuda wayo ba sai sanda rashin wayon ku ya baiyana kansa san nafada muku kuskuren ku,

amma yanzu takama kasani ne yasa zangaya ma   tunda har kake tunanin nima kamar zan iya guduwa a mata kinda nasan bani dawani hujja da zanja daku kamin wayuwar fashin ta sai kace ku
Rashin wayon ku tunranan da nashiga gidan kuda kuka zauna kuka dinga baiyana min manufan ku akai na nagane da kunason kuci riban aikin ku yatafi daidai cikin nasara da,
bazaku fadi manufar kuba barina zakuyi nayar da daku na haifa muku yaran ba tare da kunnuna min nufinku ba wllh da nasan zuwa yanzu kunci nasa ra akaina kuskuren gayamin nikuma na dage da addua gashi na haihu har ukku amma kunkasa komai saboda ni nariga nasani kuma ina gayawa ALLAH  baza kuta ba cinnasa akai naba na bayama ba tabbacecciya bace,
Saboda nariga nasani kuyin Gaskiya kunyi rashen basira
Dan haka ne bazan gaya muku ba gudun kar dukkan mu murasa nasara dan idan ni nafada bansan kuma ta nadin da zakumin ba saboda sai kasan cita zaka nemi maganin sa
Shiyasa nace maka meyin baya fadi."
Tajuyo tana masa murmushi
Tace"dafatan kalamai na bai girgiza mijin Hadim ba?

Shima mekewa yayi ya dafa kafatan ta yace"sosai karki damu bai girgiza ne ba dan nasan ke dinnan bakida abin da kika isa kimana amma Gaskiya ne batun ki na cewa  munyin gangancin gaya miki amma kema kinyi rashin basiran nunda kinnuna kina da wayo a inda akafiki karfi ba kya tsoron mu sakewani shiri akanki?
 Shafo fuskan sa tayin tace" Ayyya ai kunriga kunsaki wannan DAMAR bakaji ba nace tunran da nazo kuka saketa kabari kuga *DAMATA* bari nadanyin wanka ko." ta sakeshin tayin hanyan toilet
Zama yayi yana juya kalaman ta daya ga zai bawa kansa wahala akan yarinya karama wanda ba abin data isa tamusu kawai sai yazoro wayoyin sa yakunna dan lokacin da kansa yadan zafi hadim tanata kiran sa shine yakashe wayan saida yafara kiran Abdallah yagaya masa Fatima  tazo gida
 ba ajima ba tafito a bathroom din da rigan waka iya guduwa
Kanta nade da towel  kusa dashi tazo tana murmushi tace "bazakayin wankan mane ina tajiran shigowan naji shiru har nagama."

Wani harara ya kalla mata yace kinsaki wanan DAMAR  taki na wanka da *Shiddams* yanzu yafikar finkin marar rike sirri ."
Murmushi tayi tace" amma ai haryanzu sunan matar *Shiddams* nake amsawa ko mukamin kawai aka rage min ko to nagode hakan ma,
ai anayi dakai yafi ba ashi dakai kana sarkin amai dakai mai anguwa kum........
"keeee waine abokin wasankine kike yagamin mgn."
"aukayi hakuri ashe fa miji fa abokin wasa bane."
Har yabude bakin zaiyin magana wayansa ya fara ringing hadim ce dama yakira bata dauka ba
Ajiyan zuciya tasauke
"haba my star meyake faruwa ne da kai nakira waya yana ringing amma ka kashe wllh hankali na bai kwanta ba da tafiyan ka da yariyar nan zuciya ta tamin wani irin tsake tsake wai daki daya kuke kwanne?

"Nabil yace "haba yake zuciya tsarkakakkiya mecike da yada da Nabil yaza kabani kunyar wajen jefa kwakwalwar mana garciya a cikin mata ba abociyar kyu me biyayya da iyarike tsirin aure   awani halin salon ka  saka bacin rai a kyakyawan fukanta kadauke min murmushi ta meyayewa Nabil damuwa mes....
Katseshi tayi dacewa "Dan Allah ni bawannan ba ina amsata." yace"amsar ki kisa aranki kece daya bawata da ta isa ta wuce gabanki Halimatus Sadiya matar kwai. "

"kana tufin dakin ta daban da naka ko yace "sosai ni kisa min video call zan gaisa da su my  twins  haka suka fara shirmen video call din da suka saba Fandau tana jinsu idan kaganta zaka ratse abin baya da munta amma nan jitake  kamar zuciyar ta zai fashe dan kishi  dan zantukan nasu har da batsa aciki  bama inda suka bata haushi sai idan yake cewa" *ai my one kehar yanzu sabowa ce kuma haka kike daidai da kofa ta danba d'a ne yafito ba  a kofan ba balle ya karamin k'ofa* taji ciwon wanan kenan ita yanzu fankoce

Da dare yayi haka ba kunya Nabil yariba ci jikinta

*washe garin haka suka daga garin madina*

Sunsha ziyara kafin su koma  dan wata guda tukun suka koma

              *Landon*
*Bayan wata ukku*
Awanan kara shakuwa yayin yawa tsakanin su wanda har baya barin ta a iya part taba yanzu  Fandau  ba inda bata sani ba agidan

Hadim dakyar tabari  Fujjirat tayin sati daya a gidan Mama ta karbo abinta
Tasha saranan zuwa tunda sukayi wata 4 amma Nabil sai yace bayan zuba Hadim ta tada hankalin burin ta kawai ta dawo ta sallami yariyar nan dan idan tacewa Nabil ya sallameta sai yace da shawara sai tazo yaude sai gata zuwan bazata

 Texi yasauke ta ita da yaran ta  anci sa a bata tadda Nabil a gida ba da tayin mugun gani yanda suka jone da Fandau yanzu yafita sayo mata magani dan bata da lfy  komai tace sai ta amarar ita tasan ciki neda ita wanda tasan Nabil bai sani ba dan tunzuwan su a Saudia so dayan tayi period wata 2 kenan

Hadim ta tana jan hanun Fujjirat takira wata a ma aikatan gidan tace ta daumata sun Maaruf  suka shiga

Bayan Nabil yazo  dukda bai jidadin yanda zai rabuda kwana da Fandau ba amma yaji dadin ganin yaransa dan a babban parlour ya same su amma yanayin yana ganin saman Fandau
 Dan sarai yagane cikene da ita yakin nuwa matane saboda gani yake kamar zata damu dan yanda yaji tana addua ita kar ALLAH yasa sake bata ciki sabo da haka yaki nuna mata yasani gani yake idan tasani zata iya zubarwa duk da ba wani hanyan fitane da itaba amma  yanzu
Babban da muwar sa yanda zaiyin ya tari Hadim da zancen cikin ne

Suna kwance fayan komai yalafa yace "Halima dasaurin ta kalle shi dan idan nabil yakira sunanta to awai wani mushim min magana juyowa tayi tana kallon sa yasake kiran ta
"naam. "

"Shawaran da nace mikin idan kinzo zamuyi

Shawarane gameda neman alfarma kamar yada aurena da yarinyar nan alfarma namiki dan sonda nake miki shine nima ayanzu nake neman alfarman awajen ki ina fatan zaki iyayimin?

"My star kome kake so zammaka banda zama da kishiya kamar yanda kasane tunfar ko."

"Ba zama da kishiya bane  wllh tunsan da aka haifi  su Bilal naga su biyu ne nafara tausayin Fujjirat dan ita shikenan ita daya jal macce batada wani abokiyar shawara yakamata  ace tanada yar uwa itama
Koba haka bama inada wani hujjata guda biyun Wanda nake son ace su biyu ne
Na farko idan akace ita daya ce macce zamu nuna mata sowanda zai iya sangar tata ko bata sangar ceba idan yan uwan ta sukaga munfi sonta zasu sawani abu aransu na munfi sonta,

Saina biyu abinda bama tafa yanzu idan akace Fujjirat ta mutu shikenan ni bani da yamacce,
Dalilin yin wanan tunanin ne yakaini ga aikata wani aikin da idan kikayimin kurman Fashinta za ki iyace wa ban miki adalce ba."
"Wane aiki ka aikata?
Kagayamin."
Yasauke numfashi "Nasake bawa yariyar na ciki dan ta haifa mana macce
"What! Ai dakyar da yaudara irin nashin yasa Hadim tadan nusu

"haba Shid yanzu kanu nufin zamu sake zama ta ita har sawon watanni 8 tana da cikin wata 2 yanzu mezamu cewa yangida kumama ni wllh wani irin kishinta ne yanzu yake damuna  bana jin zain iya zama da ita tsawan watanni 8
"haba my One  kikayin zaman shikara dawani abu mada ita balle watani idan maganan kishine ni nayarda bazan kara yarda taga idona ba kotazo haifuwa bazan shiga ba ko sunan tama nayar da karki kara tunomin na dan ka komai a hannun ki amma yanzu inajin bata da lfy kikai mata magani,

Maganan mutane na irga watannin haifuwa kuma muyin shirun idan kamar watanni 4 yayi kawai sai kifara sa summan ki kamar da idan akayin haifuwan naga uban daya isa yace bana mubane."

  da kalami dakomai Hadim tayar da

*Washe garin*

Hadim dasafe kafin yan sannu dazuwa suzo mata tafara shiga path din Fandau ita da Fujjirat
tana shiga da taga yanda Fandau tako ma saida tajiwani faduwan gaba ya akayin yariyar nan tayin wanan kyan haka ai a photo ma ashe fata bata mata wanin kallon nusuwa ba
Tomeya yakai Nabil siya mata suturu masu tsada ne
Tabe baki tayi
Afili tace "sannu agogo sarkin aiki kinsamu daman wani kara haifuwan ko Gaskiya kin biyamu kodan muma idan kikaje gida zakiga munbiya jatumi da jatuma,

Ga magungunan ki."
Har tajuya Fandau tace "Aunty ashe kun dawo yahanya?
Hadim juyowa tayi ta kalle ta ta doka tsaki tayin gama dan ita yanzu aduniya ta tsani Fandau

Itako Fandau saiyanzu ta gane dalilin rashin zuwan Nabil ashe dama sune suka zo shine ya lallabani da nazauna zaije ya suyomin magani
Shikenan yanzu zande na ganin sa agai akai wani kuka tasa


Nabil yayi duk wani hanyan da zaiyi yasamu shiga wajen ta har tsawon kwana ki 3 dayajin yafi shekaru 3 rashin  tafiya ko bakin ya bude zai kira Hadim saide yace *MATA* yanda yake kiran Fandau ita ko Hadim
Tazata da ita yake  saida akayi 3 yaga bazai iya dauka ba yayin dabaran bawa  Hadim maganin bacci cikin wani just dinta daka ida ne saita sha daddare  dan yara sa yanda zaiyi awanan karon duk wayon sa sai yarasa dan Hadim tayin mugun sa ido bayan sun kwanta ya lallaba yadauki su Maaruf dan yasan sune zasuyi kuka sutashi Hadim amma Fujjirat bata tashin yana fita ya janza security yayi bangare Fandau

Bacci take yasameta wani ajiyan zuciya yadauke ya kwan tarda yaran  gefen yarebe ya kwata dan baya son ya tasheta
Cikin bacci takejin hancinta yana shakomata kamshin turaten wanda ta kwanta da tunanin sa idon ta rufe take laluman sada da hannu ai tanajin sa tayin saurin bude idon ta murmushi same tsada ya mata zaune ta tashin tana binsa da kallo can ta tabe baki ta juya masa baya yana ganin haka yasan fushi take dashi dan haka rungumo ta yayi

 "haba Mata dakin san yanda kika azabtar da zuciya ta da gangan jikina da bakiyi saurin juya min baya ba."
"tace "nide abinda nasani dayane kasamu wada d'a bai fito ta hanyan da kayin ba yananan daidai shine yasa kamanta wanda yara 3 suka fito."

Tono musa dawanan yasashin murmushi yana son ganin kishin sa awajen ta sosai

Har zatayin magana yahade bakin su dan amugun matse yake

Itama tuntana nokewa har ta fara  ramawa a wanan daren Nabil haukane kawai baiyi ba sai asuba yayi wanka yayi sallah
Yaje zai tafi amma tana baccin ta bayason ya tasheta ahankali yasa hannun zai daukin yaran ta kama hannun tace "yanzu kuma sai yaushe nufasawa yayin yace "banki na kasance dake ba har abada ina cikin wani mawu yacen hali wanda bana raba dayan biyu sakaiyar kine jinake kamar incire raina."

"kafara sonane? Tajefo masa wanan tambayan

"bansani ba nide nasan kin gimama agareni,

"Mekike kike so arayuwa zan baki
Kinga wanan gidan da muka zauna a Riyadh da Makka gidanan ne nacikin Makkah sarkin saudia ne yabani awani fira  da akayin dani a CNN aka tambaye ni wane gari nafiso a Duniya nace Makkah shine yamin  kyutar sa kinaso nabaki shi tunda naga kina son garin?

Murmushi tayi tace"tabbas ina son abu awajen ka mai sauki amma ba asamun sa akasuwa kuma bana tsiya bane?
Yace "fadi."

Tace " kasoni soyayyar ka ita nake so. "

Ajiyar zuciya yasauke
Yace"kefa kina sona?

"aini batun so awajena ka dade  da samunshi.."
Wani dadi yajin da baisan dalili ba yayi kissing nata yace"kije kiyi alwala."
Tana shigewa toilet yana daukan yaran da jakan da yazuba abincin sucikin yayi waje

*Kwana 5*
Jere yana haka sai ana 5 Hadim ta tashin da asuba bata gansu ba amma kafintayi wani yunkuri sai gashi yashigo dayaran tace"ina kuka jene?
Yace"haba ai kwana biyun nan kin baromin aiki wai wane irin bacci kikeyi haka yara suyin ta kuka kinajin su dama haka kukeyi a gidan ma."
 yasuna fuska tayin tace "wllh kwan nanan ne bansan meyasa idan na kwanta banajin komai ba."

"Haba saikace me cutar bacci tunmunayi anan dasu har saida nafita falon dasu."

 *Bayan wata 2*

Cikin Fandau yanada wata 4 Hadim takamu dawani masanancin rashin lfy farkon abinda tafi tsana ma arayuwan ta saduwa shiko bai damu ba dan yana da wajen zuwa sai turaren Nabil kaishi kansa Nabil dinma ko baisa turare ba batason yazo kusa da ita gata muguwar raguwace dama gaba daya tasaki jikinta Nabil abin ya cabe masa ga yara yasa dan hadim bata kulasu ta kanta take dukda baya son harka dayan aki dole yakira yabasu yaran shikuma yafara jigila tsakanin hadim da Fandau

Hadim da Nabil zaune gaban doctor Muktar tana fara fabayani ma yagane yafara dariya yace"kai wadannan mutane sannun ku kunda ge sai kun taddamu ko to kuna sauke wanan kun taddamu nanda shekaru 2 harkun zar tamu."
duk basu gane ba
Hadim tace Abban habibi neyake damuna?

Doc yace "sai nafada  ai kobaki taba jin labarin masu cikiba  zaki gane kina dashi  daga Nabil har hadim mekewa tsaye sukayin "ciki!?
Suka hada baki
Dariya doctor yayi  yace" meye abin damuwa naga wannan karon kunyin kokarin ja ma har yara sunkai watanne 6 naga awacan  acikin watan haifuwan kukayin abin ku."

"tace Gaskiya nide banyar da ba sai an aunani."
 Murmushi doctor yayi yace "kuyi planning ne bai yuwuba?
Nabil kasa bashin amsa ayin dan idan ana cewa Daurewa kai toshi yau a tukunya yakejin kansa

Doctor yaki ra Nurse ya numa Hadim yace taje amata awun  fitsari
Dukda Result yanuna awai ciki amma Hadim sai cewa tayi ita bata yarda ba sai amma mata scanning
Doctor zaro ido yayi yace "yau kuma me dokan bacci  kode kunfara gajiya da yaran ne kun manta jaririn cikin  idan akayi scanning za a iya juyen masa ido kuna yiwa Allah shishigi zaku fara."

Hadim tace"doc kawai kamin kafin ya bata amma har Hadim tayi wajen godon da doc yake  scanning
shiko Nabil jiyake ina ma mafarkin yake yafarka Hadim  daciki yazaiyi da cikin Fandau

Yana cikin haka yaji Hadim tafada masa wllh Nabil da Gaskiya inada cikin wata 2 wai wayooo ALLAH nagode maka ashe da rabon zaga....
Dasuri Nabil yace "toya isa karki sa kanki ciwo yayi hakane dan yaga ta fara sakin layi
Mekewa yayi yakama hannun ta suka fita doctor yana musu dariya yana tsokanan su sarakan aiki

 Nabil yace "yanzu to yakike son ayin?

"Kaime kagani ai muzubar da nata mu sallelameta kawai."

"yace bazai yuwu azubar da cikin wata 4 harda kwanaki badan yariga yazama mutum sai de azubar da naki wanda yake gudan jini naki za azubar

"What!



*Tofa masoyan Hadim badan nariga naba da wanan Page dinga ga Garkuwa ba dasai nace nabaku DAMAR kuce*

```Basoya ina sake tuna tar daku banida lokacin typing kullum abari kwana 2```


*B JATTKO*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMATA*




                    *NA*



*BATUL ADAM JATTKO*

Kainuwa writers
Aunty Fauzah
Maryam Ahamed
Jamila Samaila
AISHA Sada
Sa adatu Alkali
Aysha Hamza
Sameena Aliyu
Muneera
Mum Hanan
Mmn Yusura
Farida Talba
Jidda Saudia
Jidda cool
Mmn twins
ummy Ontop 
Miss Marriyaam
Aisha s bayaro
Nafeesat
Halima M K
Fauxia M B
Maryam mn Imrane
Firdausi M Auwal
Zainab Aminu
Hajjajo
Maryam muhphar
Beebaloh
Maryam shitu
Aysha Ehman
Mom Ayman
mmn Shaheed
Amira Aliyu
Farida Sarki
Khdijah Kt
Ummia Fauzah

Da dud kan wannan basu sunan suma anatare



(Editing mzz daddy)


*37*



       *H*aba mekakeson cemin ne? mu zubar da cikin da muka shekara 7 muna nema mun shiga garari dayawa akansa harmuka nemi wanda zamuyi *manage* dasu sai yanzu da muka samu na gaskiya amma kace mu zubar kaji yanda naji da akace inada cikin ne wanda ban taba tsammani ba dan da banga period dinna bama ko aka ban kawo wani cikin basai da akayi test."

"to yanzu yakike son ayi?
Tace" azubar da na wancen mu sallame ta."

"to bakijin daidai ba impossible daza kice wani manage, su Fuj zaki kira da manage,
Idan kina tunanin za akaramin wani haifuwan da zanyin farin ciki dashi kamar su kin yaudarin kanki."
A firjice Hadim ta sake tashi "tace Shid kana nufin bakason wanan cikin?
Girgiza kai yayi yace "yazan ce banaso saide dukka daya ne awajena tunda suma yarana ne ke idan kin nuna banbanci ba lefi bane dan banaki bane da naki ne da baki kirasu da manage ba."
Shiru Hadim tayin tana tunanin idan bata nuna so ma yaran nan ba zai zamo mata  problem a wajen Nabil, ko agun mutane dole ta danne tanuna musu so duk dama yanzu ma tana son su amma tafi son natan. Ajiyan zuciya tayin ta zauna
tace "haba Nabil kalman da kafada na azubar da cikin ne baimin dadi ba amma nima inason yaran ai ko ban haife suba ina son su kuma suma suna sona ban haife suba amma sunsha nonona wanda zaiyi ta gudana ajikin su har karshen rayuwan su ina son su, amma wanan cikin nata yazama dole azubar a sallame ta."

Yace "bazan iya zubar waba."

Ido hadim ta zuba masa ta san halin Nabil baya taba cewa no yace yes, bazai yiba tunda yaki.

"To yanzu me mafita nima baza azubar da nawaba."

Yace"na sani Halima idan na nace azubar ban miki adalci ba, amma wllh bazan iya yarda a zubar da na Fatima ba."

"Aishine nace maka me mafita?

"yace kibari mudawo daga tafiyan nan kafin nan nasan zamu sanu mafita. "

Numfasawa tayi tace
"Tomorrow ne ko?
Yace" yes

Gyada kai Hadim tayi dan ta riga ta aiyana kudurin ta aran ta wanda kafin yadawo two weeks  tagama abinta dan shi taga bazai iya ba kuma ta san ba komai bane illa tsabar tausayi irin nasa dan haka batasa wani Nabil zai sowani Fandau aransa ba tasan de yana da tausayi.


"haba Fatima  sati 2  kawai zanyi nema inajin yanda zanyi missing naki datun da muka hadu bamu taba rabuwa na sati ba sai awanan karon dan haka kikula da cikin ki da kanki kuma ai ga waya zamu dinga fira idan na samu lokaci kinji my Fajjjiiii ta.'' Share hawayen ta tayi tace" ALLAH yakai ka lfy yadawo da kai lafiya cikin nasara da ribar tafiya yakara maka daukaka da karfin mulkin sa."
bai san sanda yasake rungumo taba yana cewa "Ameen nagode   my Mata."
 Yakalli agogon dayake daure ahannu sa ya mike dasauri yana rike da hannun ta har falon karshe
Har yabude bakin sa zayin magana waya yafara ringing yana daga mata hannu ya fice ita kuma ta juya cikin tana juya kalaman sa kobai ce yana sonta ba amma ai ya gaya mata kalamai masu dadi wani kalma da yake yawan gaya mata ne ya fadomata *so abaki ba sobane son gaskiya a aikace ake ganeshi* murmushi tayi ta fada gado.


Hadim kam duk ta zube sabo da bakaramin azaba cikin yake bata  ba da yace zai tafi ko kanta bata daga ba balle rakiya ya dauki Ma'aruf da Bilal yakama hannun Fujjirat suka fito driver yaja suka tafi har club dinsu haka akayin ta rubibin daukan yaran nan ana cilli dasu bare Fuj har oga ita ya d'auka, aida zasu tafi yameka wa Security's dinshi su dakyar Fuj tayar da sai kira take "my ci" wai zata ce my Star yanda Hadim take  kiran sa yana gani aka dannata a mota yajuya kansa bayajin akwai wani abinda yakeso fiye da son yarinyar nan yanzu idan yatafi yabar ta haka zatayin ta bulayin awajen yan aiki bawani kula Hadim yanzu take dasuba dan ta kanta take,  tuno da kukan ta har cikin dodon kunnen sa yasa yayin saurin zaro wayan sa yakira su yace sudawo masa da Fujjirat haka yatafi da ita abinsa abokan sa suna masa dariya na cewa sun samu karin yar autan club
Nabil yace" ba kuyi karya ba, yanda idan kunci wasa ake dauka kofi abaku, ita ma an bata" dariya suka sakeyi.

Sun tafi da kwana 2 tukun ya kira Fandan da safe, tana dauka yace"Mata kinga ban kiraki bako wllh  ban samu nusuwa ba gashi da Fujjirat nazo kan kara akeyi sosai  akasan sanyin ya zuba mata zazzabi amma yanzu da sauki,
Yakike ya MAMA Aisa kina kulamin da ita ko?
Murmushi tayi tace" Mama kuma?
"Eh mana bakisan da me sunan ta kike tare ba."
"ALLAH da naji dadi amma yajikin Fuj din? dama da  ita katafi?
"dasauki eh muna tare."
"Kuma idan zaka shiga wasa ya kakeyi da ita?

"akwai abokai nada sukazo ta matan su awajen su nake barinta."
 "To wane kasane har ake yayyafin kan kara haka?
"yace Rasha ne."
Sunyi fira sosai kafin yace" bari nakira Aunty ki zumudin jin muryar ki ya hana nafara kiranta."
Kafin tayi magana harya kashe wayan.

 Ba ajima ba Hadim da wata suka shigo matar farace Hadim tanuna ta tace "gatanan matar tabi Fandau da kallo ita cikin gurbattacen hausanta tace"sannu ko za a miki allura ne".
Dasauri Fandau ta mike tana karanto Innalillahi afili cikin tsoro tace "wane irin allura?
Hadim tace "kinason sani kenan ai da kinbari an miki dan na taimakon kine kar kije gida ace kinje yawon karuwan ci shiya sa nasa amiki allura da zaisa ki manta komai akuma miki wada cikin zai zube dan wataran kar dan yace kinemo masa uban sa kinga kekuma bakya cikin haiyacin ki yazakiyi dashi ai gwara azubar."
Ido wajen Fandau take kallo su, ganin mata ta bude jaka tazaro allura da gudu Fandau tayi hanyan kitchen wuka ta dauko tace"wllh sai de ayita koni koku tana kuka tana zaginsu a haka aka kira wayan Hadim tana dubawa Nabil ne tayin saurin fita dan karyaji abinda ake tana fita doctor adegas ta karaso wajen Fandau tace ina hada ido dake naji tausayin ki meya kai ki beyewa mazan turawa daga kawo ki aiki suka baki ciki gashi yanzu kinsa uwar dakin ki tarasa  yanda zatayi saide aminki allura."

Fandau tace" haka tace miki ni yar aiki ce?
Doctor tace "eh mana."
Fandau tace "bata gaya miki gaskiya ba."
Matar tace "daga yanayin kalaman ta tunfar ko nagane ba gaskiya bane dan Hadim kawata ce nasan halinta sarai gayamin gaskiya zan temaka miki."
Aguguje Fandau tabawa matar labarin ta.

Doctor tace "na gaskata ki kuma ciki tunna fari nagane cikin kawata ba na gaskiya bane amma kisani mijin ta yanada mugun kudi har ita kanta baza ki iya ja dasu ba temakon da zan miki dayane alluran batar da memory kine bazan miki ba amma na zubar da ciki yazama dole tunda zata gani idan bai zube ba dan tafiyanki sai gobe, inason kinuna na miki alluran kinuna kin manta komai idan kika je gida kikaga za'a iya dau miki mataki shikenan kinji kuma abin d...
Hadim ce tashigo "tana cewa tayar ko sai taji ciwo kafinnan
Doctor tace "ai har angama dayan saura na aborton din ai."
Hadim murmushi tayi tace"yanzu  shikenan ta manta komai ko?
Doc tace" sosai."
Fandau tana gani matar ta dan na mata allura da zai zubar mata ciki takama ta ta zaunar ta ita abakin gagon tace "nan da anjima zakiga tafara zubarwa."
Hadim tace "nagode   Hadim tana ganin wayan Fandau ta dauki wayan suka fita.

Suna fita Fandau ta fashe da wani irin kuka yanzu burina da kudiri na bazai cika ba kenan yanzu naje gida nace me, anya bazan kira matar nan nace tamin alluran nan ba kuwa? tana ciki haka taji cikin ta yayi wani irin murdawa juyi ta dingayi akan gadon tana ihu dan yafi nakuda ciwo tana jin abu yafara bin jikin ta har yasauko cinyar ta tasa hannun ta shafo tana ganin jinine tasake sakin wani kukan saide bawani jimawa taga jinin ya tsaya haka cikin ma ya dena ciwo.

sai yamma Hadim ta shigo, tasamu Fandau akwance jinin har yafara bushiwa anan Hadim ta sake tabbatar wa da lalle bata cikin hayyacen ta dan da tana cikin hayyacen ta zata tashi.


Tace" kinga anyi maganin ki yara sun zama nawa na har abada kije can uwar ki taci gaba da renon ki".

Dole ita ta gyara ta, Ita kuma Fandau sai juya ido take alamun bata san ma me akeba, da Hadim ta doka mata tsawa tace  "kina jina kitashi." Bata ko motsaba tana kallon Hadim a shagwabe kamar yarinya janta Hadim tayi tafiyan ma dakyar takeyi haka ta kaita bathroom ta kitsata suka fito tana rike da hannun ta ta zaunar da ita akan kujera ta janza  zanin gadon
Har zata fita ta tuno da ai yaka mata ace ta bata abinci waya tayi wa ma aikatan gidan suka kawo abinci ba ajimaba taje ta karbo tazo ta ajiye abincin ko kallon abincin batayi ba, irin bata sani ba saida Hadim ta zauna ta samata abaki nan ma kin taunawa tayi saida Hadim tasa abakin ta tafara taunawa sannan itama ta fara ahaka ta gama bata.
ALLAH sarki Hadim duk abin da takeyi cikin karfin hali takeyi dan tana jin jikinta sosai.

Washe garin Hadim da dama tagama duk wani ciku cikun tafiyan Fandau haka ta dauke ta da kanta dan bata son driver yasani wani tasamu a maikatan airport tace ya hadata dawani fasinja zata bashi amana haka akayin kuwa aka hadata dawani yaro bawani babba bane tace "bawan ALLAH yasunan ka  yace" musa." tace"  idan badamuwa zan baka amana." yace"Allah yabani ikon karba da kuma rikewa" tanuna Fandau tace "kaga wancen yarinya bata da lfy  kuma ni nasame ta tunda guntun lafiyan ta tace min ita yar maiduguri ce amma yanzu idan an tambaye ta ma bata bada amsa, nayi mana shirin tafiya tare maigida na yakamu darashin lfy  shine nawa tafiyan bai yuwuba,  nace sune mamin wanda zaije Nigeria musulmi shene
Aka hadani dakai, kai dan inane?

yace " ni dan kano ne karatune yakawo ni yanzu ma hutu zan tafi."

"Yawwa kanina inaso ka kai min ita maiduguri nauyin da zan daura maka kenan zan baka kudin jirgin da zai kai ka can dakuma wanda zaka dawo harma da kari."
Yaron yace"amma wllh badan kin riga kin hadani da ALLAH ba da bazan karbi wannan  aikin ba tunda kema kince baki san gidan su ba to yanzu ina zan kaita?
Hadim tace " wanan badamuwa bane ka kaita B R TV ko N T A maiduguri kace katsince tane amma kace a garin ka tsinceta." Dayake yarone bai wani san haka zai zame  masa illah ba yayi saurin karba , Hadim ta bashi kudi meyawa tayi saurin barin airport din.

Yaron bai wani kai saurayi bama shiya kama hannun Fandau har cikin jirgin
Itako Fandau tana shiga tana zama tafara kuka, ba wajen zaman su daya bane da wanda aka hadasu tunda ta zauna kuka take yanzu haka zan koma gida nazo a siya zan koma awulakan ce to ina shi Nabil din kikasani ko bakin su daya da matarsa yasan metayi koma dama bawani tafiya dayayi tunda ta zauna wata mata yar gayu take binta da kallo itako Fandau ba alamun zatayin shiru, matar tasowa tayi tazo wajen ta, kanwata meyake damun ki haka tunda aka fara tafiyan nan sai kuka kike ko da akazo tambayan mezaki ce bakice komai ba kuma naga da yayanki ma kuka shigo ko kanin kine ."
Fandau batasan dalili ba kawai sai jitayi tace"ba yaya na bane banma sanshi ba kawai gani nayi yakama hannun mun shigo ."

"to meya saki  kukan nan meke damunki ki gayamin?
Tace" gaya miki ba wani amfani dan idan kikaji tarihin rayuwa ta bazaki yarda ba, a bune da banta bajin sa aduniya ba."


"Kigaya min ko dawani taimakon da zanmiki", saida Fandau taci kukanta ta more tukun ta kwashi komai na rayuwan ta tagayawa matar, a firjice matar take jinta itako Fandau tunda tafara bata tsaya ba sai da taje karshin labarin ta.
Itama matar kuka take sosai, ko magana kasayi tayi tashi tayi tajen wajen ta, ganin kukan Habiba yayi yawa doctor Muktar yace" waike meya faru meke damun yariyar naga kin dade awajen ta Habiba  ta kwasa shi komai ta fadawa doctor shikan sa abin ya firgita shi haka Habiba ta koma wajen Fandau ta yita lallashin ta har tadan saki jikin ta.

Hadim fal murna takoma gida.  Dan ita abinda yake bata mamaki ba Nabil ba hatta yan gidan su da kawayen ta ba suwani nuna mata dokin cikin nan ba, ummin Nabil har yanzu bata kirata ba haka Inna ma mamar ta cema takira ta hatta kanwar ta Ashuwa bata kirata ba.

Ga babbar aminiyar ta ma Habiba  data kirata cewa tayi baza ta samu daman zuwaba dan tana cikin shirin tafiya gida.

Kowa bayawani dokin cikin nan.

Jirgi su yana sauka atare suka fito da Fandau sun riga saurayin fitowa  koya tsaya neman Fandau ne wayasan masa itade dama tun kafin susauka Habiba tace mata gidan mu zaki bimu dan mutantan ce gaskiya acikin maganan ki,  sude har driver dinsu yaja basu ga idon Musa ba.

Sun sauka ne  a ABUJA  dan haka gidan doc na nan ABUJA suka yada zango suna shiga babban parlour gidan idon Fandau yasoma cin karo da tabkeken photon Nabil da yake jikin bango yana sanye da kayan ball yarike ball din ahannu sa turus ta tsaya tana nunu photon bakin ta yana rawa tafara magana "wllh gashinan shine shine   shine".

"shine wa suka hada baki Muktar da Habiba."

"Shine wanda nake gaya muku sunan sa Muhammad ana kiransa Nabil ko Shiddams wllh shine."
Sai tasake yi musu bayani sosai suka yarda, abin yayi mugun bawa Habiba mamaki dan bata zaci kawar ta da wanan halin ba
"Abban Nofal me mafita."
"Mafita  daya kawai mukaita gaban iyayen ta dan nasan bazasu iya jada suba, amma nima sheda ne alokacin cikin farko a toilet din office dina nace ta shiga tayi fitsari, saide mamaki na dana shiga sai naci karo da wani kwalba shima dana sa aka auna sai yanuna iran fisarin Hadim ne kinga yanuna da abinta tazo ko kuma ba abinda banyi dasu ba suzo awu suka ki, ga haifuwan gida suke dama abin yana bani mamaki  amma awanan cikin sai suka yarda aka auna kuma bugu da kari ma ita Hadim awajen haka tace ashe itama darabon zata ga......
 bai bari ta karasa ba."

Amma wanan bai isa sheda ba dan haka hakuri shiya dace dake mude zamu danka ki ga iyayen ki danni maiduguri ba bakona bane kusan ma garin mune anan aka haife ni kuma garin mama ta.
Inane anguwan ku?
Fandau tace " gargar doctor yace"ok anguwan Zannah Modu kenan Babana."
Da sauri Fandau ta kalle shi tace " nima shine Babana ai."
Da suari doc da Habiba suka kalle ta "Baban ki?
Habiba tace "haba sai yanzu na tuno inda nasan ta wllh itace wanan yariyar da nake gaya maka agidan Malam me girman kai kazama dinnan wllh tun agirgi nake mata kallo kamar na taba ganin me kaman ta Wllh itace."
Fandau daga idon tayi sosai ta zuba musu ido  tabbas shine dan gidan Malam Dauda abokin Baban ta wanda idan yaje yan gidan su aketa turoruwan shiga bangaren bak'i gaishe shi shine take kiran matar sa me girman kai ashe ita ma kallon me girman kan suke mata.

Muktar yace "ke yar gidan Wacece acikin matan gidan." "Aisa
Rai abace doc yasake kallon ta yace "amma ba kanki kadai ba hatta Malam baki masa adalci ba shi me fada aji agari kuma duk abinda yasameki kije alhakin Baba Aisa ne dan ubanki kinsan Malam Dauda?
Tsawan yadaka mata yasa ta ja da baya tana gyada kai alaman eh
"kinsan ke me sunan wacece acikin matan sa?
 tace " Inna Falta?
Yace"to ni Inna Falta ita ta haife ni, yanzu in ban da lalacewa irin na duniyar yanzu kamar ke da darajan ki da kimanki kibi na miji, gwara da suka miki haka kuma bawani gida da zan maidaki na kaiwa ubana wanan kayan bakin cikin, duk da Shiddams nada daman sani bazan kai ki ba sai kin koyi hankali da zaman duniya, wawuya sakarya ni ahannun na zaki dandani azaban da yawuce na gidan Shid ai."
"Haba dear kamata ahankali man da wanne zataji."

Doctor yace"Wanan yar iskan za'abi a sannu, ko ke bance kibita a sannu ba", yana gama fadan haka ya haura sama
Habiba tace "ishiru Mamana, dama Abban Nofol haka yake yanada zafi akan kannen sa, kiyi hakuri nasan kema kina da lefin yarda da namiji, shiddams abokin sane sosai nasan za'a shawo kan abin kafin akai ga manya, saide ina tsoron kishin Hadim nayi mamakin jin da kanta take kai miki Shddams na yarda lalle akan buri ba abinda bawa bazai yiba,
 ga daki nan kushiga keda su Ummulkkairi ina zuwa."
 itama ta haye saman


Nabil yayi yayi yarasa Fandau a waya yagaji  ranan da gobe zasu dawo yakasa hakuri ya tambayi Hadim saicewa tayi tana nan nima ta kaina nake.

A ranan da Nabil ya sauka ita kuma Hadim har ranan akwance take jiki sai abinda ya karuma ciwo, sai dare Nabil ya lalla ba yayi bangaren Fandau ba inda bai duba ba bai ganta ba cikin faduwan gaba yafita
"Halima ina wannan yarinyar?

Cikin rashin damuwa Hadim tace "wace yarinya kuma?

"Fandau mana."
"au dana sunan ta kenan kai da karike sunan ma bakada aikin shine, to ma meya kaika part din nata ma, ya mukayi dakai."
"Halima amsa zaki ban tana ina?

Tana maiduguri, na kasa hakuri na turata dan idan na biyewa tausayi irin naka wankin hula zai iya kaimu dare na tura ta anan ta masa bayanin komai.
 "Dan me zaki yanke hukunci bada sani naba."
Tace "dan baka da iko akai ne, ni na aurota kuma dan na sallame ta ban......
Ai Nabil yama manta dawani ciki ajikin ta wani irin shaka yamata wanda saida yaga alamun zata rasa numfashin ta yanda idannu ta suka fito.
Sakinta yayi  ahankali yace" Halima dan ALLAH karki dauki al'amura na da wasa, wllh zuciya ta zata fashe da gaske kin zubar da cikin Fatima da gaske kinsa amma ta alluran idan ta ganni baza ta gane nima gayamin gsky kin illata min Fati na."

Hadim hannun ta awuyan ta tace "eh eh na aika ta."

"Hadim meyasa kika min haka inda kinsan halin da gangan jikina da zuciya ta suka shiga akan yarinyan nan da koda kudi aka hadaki bazaki min hakaba meyasa meyasa?

"Shid saboda nina  samu  na aura maka ita saboda wani bukata tamu kuma mun samu biyan mukatan zaman me zatayi mana a gida, yanzu wannan har yakai kayi yun kurin kasheni."

Nabil cikin wani irin karajin da ya firgita ba Hadim ba har su Fujjirat
Yace "ai yun kurin kashe ki kadan ne har uwar ki da kuman ki sai sunyi nadaman haifuwan ki idan baki ne momin mata ta cikin kwanaki ukku ba kuma da lafiya ta  dan duk inda lfy yake sai kin nemo, zakuyi nadama."

"Nabil ne kake gayawa haka, uwata bata ci darajan ita Yaya ce awajen ta ka uwar taci darajan daukana da tayi tabaka aure bana."

"Aure fa kikace a tsakani na dake yanzu bawani aure naba ki kwanan 3 kine momin mata ta bawani aure a tsakanin mu balle naga darajan sa".
Hadim dafe kirjin ta tayin tana jawo numfashita amma ita yaga gare ta kasa fusgo numfashi tayi jikake yif ta zube kasa ba wani alamum numfashi.

*to dama de na gayamu ku Nabil bai iya bacin rai ba me nufin san nacewa ba maganan aure Hadim ta saku ne?*

*to masoya ina Hadim zata fara neman Fandau me zai faru*

*B JATTKO*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMATA*




               *NA*




*BATUL ADAM JATTKO*


Khadija salisu
Mmn Nabil
Muna tari



(Editing mzz daddy)







*38*



      *Y*ana gani har takai kasa baiyi yunkurin tareta ba dan shima ta kansa yake, ji yake kamar yafadi yanda zuciyar sa take wani irin tafasa yanzu shikenan Fatima bazata gane niba acikin sabon kwakwalwar tata? ko zata soni kaman da? ranan da zan tafi ma fa sai da ta furtamin kalmar so.
Meyasa ni ban bata amsa mata ba?
Hadim kin cuceni, shi yanzu bama ta tonan asiri yake ba yagan ta kadai ne burin sa.

Hadim meyasa kikamin haka, mena miki?
Dakyar ya taka kafafun sa ya karasa inda fridge yaka  ya dauko roban ruwa ya fincike murfin yana daga tsaye yasaki ruwan me uban sanyi akanta ai a firgice ta saki ajiyan zuciya
"ai baki isa ki mutu baki nemomin mata ta ba."

Hadim dafe kirjin ta tayi setting  inda yake mata zafi.

"haba Shid kaji tausayi na mana kanason rasani ne idan wasa kakemin kadena, banason kana ambaton wanan yariyar da matar ka ko kanason kasheni ne? ni kake cewa karna mutu sai nemo maka matar kar cikin kwanaki ukku, idan ban sameta ba ba aure atsakanin mu, bani ba iyayena ma zasuyi danasanin haifuwata da'gaske ne? Wllh wannan sautin kunnena ya bani muryar tane ya fara tsarkewa .

Shikuma yanda yaran suke kukane yasa ya dauki su Ma'aruf  ya kama hannun Fujjirat zai fita.

Hadim tace" Shid kar kafita kabar ni cikin wanan  halin  kaji tausayina".

Ko juyowa bai yiba
"Habibi kar kafita Habibi  inacikin wani hali".
Saida taji k'aran buga kofa sanan ta,
kwantar da kanta da take jin yana mata wanin irin ciwo, ko makiyin ta yaga halin da take ciki zai ji tausayin ta.

Da kansa yakai yaran bangaren ma aikata yazo ya fada mota baima jira security dinshi ba yaja mota direct airport ya wuce office Oeid  yana shiga Oeid ya mike yana cewa "welcome  Shid" mika masa hannu Nabil yayi sannan suka zauna, ba yani ya masa nayana son a tabbatar masa da tafiyan  Fandau, ya fadi sunan  ta na jikin passport aiko atake aka bincika aka tabbatar masa da tafiyan ta yace aduba masa mu amullan ta acikin jirgin  tunda gashi Security's ya mai daukan wajen, ya nuna inda Musa yakama hanun ta suka shiga cikin jirgin amma saime da aka kira security na cikin jirgin ya turo da audio recording na ranan sai cewa yayi yayi delete din su, hannu Nabil ya dunkule jikinsa sai rawa yake Oeid yace "aiko da Dr MD  akayi tafiyan aranan amma bazai wani santa ba saide  dauki numbern shi Musan da sauri suka yarda da wanan, bugu daya Musa ya dauka suna masa bayani yace"wllh da yazo sauka ba neman da baiyiwa yarinyar nan ba amma bai ganta ba saide tun acikin jirgi yaga wata taje wajen ta yaga suna fira alhalin shi Hadim tace masa bata magana kuma har matar yanema bai ganta ba".
Nabil dura masa ashar yayi yace "to ka nemota duk inda tayi inba hakaba zaka gane kuren ka".
Yaro ko dama dan maikudi ne, suko yaran masu kudi ko na kwarai suka kashe sunsan bawani abunda zai samesu dan haka cikin isa  yace "nide amana akace an bani kuma saboda ALLAH aka hadani na karba dan bangan ta ba za ace wani idan ban nemota ba zan gane kurena, kai waye da zaka gayamin wanan kasanne waye kuwa?

Nabil da kalaman yaron ya sake bugansa ko magana bai tsaya ya masa ba ya kashe wayan atake ya kira office yan sanda na kano yadauki address din yaron ya tura musu yace sukamo shi harsai yazo.
A take suka amsa komawa yayi mota harzai tada yaga zuwan sa gida ba shida wani amfani dan idan yaci gaba da kallon Hadim zai iya hallaka ta kuma ma me zai zaunayi a garin bayan an tabbatar masa da FATIN sa tana can, amma yakira sani yace ya bincika yace ba wani labari gwara yaje daga gidan ayi komai agaban sa yafi, ya ciro wayan sa yacewa wani daga cikin yaran sa yace ya kawo masa su Fuj yana airport dan bayajin zai iya barwa Hadim yaran sa.
Shikuma ya fita yayi ciku cikun tafiya  nan danan aka maida jirgin da zai je sudan akace sai yafar sauka a 9ja dole maiduguri yafara yada zango saboda ya ajiye yaran kafin yashiga neman Fandau.


Dr MD tunda ya shiga d'aki ya fara safa da marwa wanan wane irin zalunci ne abokin sa yayi? wato shine dalilin da yasa yayiwa Malam wanan hidima, shine yasa yafifi ta mama Aisa acikin matan Malam ko, har shigowan Habiba yana tunani tace "haba Abban Nofal wllh banji dadin yanda kayiwa yarinyar nan ba, yaci ace kamata yaki taji sauki tasha wahala."
"My Habtee naji tausayen ta kawai inason nuna mata kuren tane, tana mace tabi saurayi yanzu da wanda zai lalata rayuwanta ne fa?
"hakane tayi lefi amma me mafita?

Yace "A yanayin bayanan ta nagane Shid yakamu da sonta kuma nasan zai nemeta yanzu idan na dauke ta na kaita gidan Malam  shid yana zuwa zai dauketa ya bada ita dan yanason Shid kuma bai kamata Shid yasake samun ta a araha ba inason sai yayi kuka yayi nadama sosai kafinnan zamu koma da ita London zansa ta makaran tawaye tasan al alamarin rayuwa,
Inason sai shida kansa yakai kansa gaban malam ya tunawakansa asiri ya wahala wajen nemanta kafin nan ta zama cikakkiyar mace wanda zata iya kwatarwa kanta yanci."

Tafa hannu Habiba tayi tace"yawwa my sweetheart wllh Hadim zata gane kuren ta dan sunban mamaki daga ita har shi."

Ummi da abokiyar zamanta Hjy bintu wanda suke kira da *Iya* sunyi mamakin ganin Nabil a rikice wanda ko gaisuwan wani irin yake amsawa.
 Iya tace"Shid lafiya yau sai kukazo ina Haliman?" Grema yace "kaida yara ne kawai ina take?

Ajiyan zuciya yayi yace "yayesu tayi ni kuma kawai na daukosu su zauna ahannu ku ita Fujjirat zan kaita gargar gidan Malam."

Ummi tace "amma ko yayesu akayi bai kamata arabasu da mahaifiyar su ba kuma ni bakomai nake jiba irin yaya ZAINABU, yanzu koni bazan tsira ba zata ce dasanina akayi, dan haka nide bazan karbi yaran tazo ta gama tozartani gaban yara ba, yaya saide ke idan zaki karba."
*Iya* tace" a a wace ne."

Ummi tace " to dauki su duk ka kaimata su karma kanuna kafara zuwa ta nan kuma kar kace Hadim ce tasaka kawo su gwara kace ra'ayin kane."

Nabil yace "Girema dauki yaran nan kakaiwa Inna nema gani nan zuwa yaja hannun Fujjirat suka fita. Direct gidan *Zannah* yasa driver yakai shi  yana zuwa ya tarar tarar da shi yayi manyan bak'i.

Almajiran da yaran gidan suka ta kwasan gaisuwa kota kansu baya bi shide baiki yana shiga yayi tozale da Fatin sa ba dan yanzu ba wani fargaba ko tsoro na ganin ya gurfanar da kansa agaban malam ba, inde zai sameta. A tsakar gida ya gaida matan gidan ya wuce part din mama bai ganta ba ta na area din kitchen dan duba yanda ma'aikatan suke sarrafa abincin dan malam yana da bak'i. Zama yayi akan kujera ya daura Fujjirat saman cinyar sa amma me yana dagowa yaci karo da wani tafkeken photo Fandau alike a bango tayi irin tsayowan rike kugunta nan tasha hoda da janbaki kan ta kile dinnan duk da bawani kyau tayi ba Bagana tasa anyi editing dinshi ba laifi,  ya kasa dauke idon sa akan pics din.

"kai lale da bak'in ba zata, ko dama daga Rasha din nan kuka yo ne?

Ahankali ya janye idon sa akan pics din ya zamo kasa yana gaida mama, itako mama daukan Fuj tayi tana amsawa. Mama ta daga ta kalli Nabil da take ta masa magana baya bata amsa sai taga photon Fandau yake kallon."

"kaide baka gajiya da tafiye ta fiye gashi kana shirin koyawa Hajara ni da kun bani ita ai gara ma Shateema yaki barmin Tajjudin yana manta nono suka karbi kayansu."

"au shima anyaye shi kenan?
"Eh ai uwar da juna."
*Azuciyar sa yace"zuri ar ki akwai albarka gashi daike kin tsaya a 2*

A fili kuma yace" ai dama yanzu Fuj zata zauna awajen ki har sai na dawo."

Mama tace"aiko na nagode".

Sake kallon pic din yayi yace "mama wanan yariyar fa?

Mama takalli photo cikin sosuwan rai tace" kanwar kace."

"Mama ya banta bajin kin kira sunan taba tana ina yanzu haka?

Hawayen da mama take boyewa ya biyo kumatun ta. Ta tashi ta koma daf dashi yanda bawan da zaiji zancen.

Tace"Muhammad ban taba gayawa wane wanan maganan ba dagani sai malam sai Bagana muka san zancen nan amma bansan meyasa naji inason gaya maba sai dan nasan kai mai kaunata ne nasan kuma zaka rike sirrina daganan ta gaya masa yan da akayi suka rasa Fandau har yanda malam ya rufe bakin mutane da cewa ya mata aurene da bako, ta karashe zancen cikin kuka."

Nabil shima hannun mama yakamo ya hada dana Fujjirat ya dam ke yasa kuka, dakyar mama ta lalashe shi ganin Fujjirat ta fara kuka.

"ni yanzu cikin kwana kin nan ma mafarkin tane yake damu na kullum cikin kuka nake ganin ta."

Nabil tsoro ne ya sake kamashi  karfa tana cikin mumunan hannun gashi atunanin sa zaizo ya sameta amma shiru.

"to mama tunda ta tafi bawani mataki da aka dauka na neman ta."

"malam cewa yake yana addua akanta kar naji komai."

*yanzu kenan idan nasa mu Fatima nakawota wajen Malam zaice dama ni ya aurawa awuce wajen yazanyi na samota?*

A fili kuma yace "mama zan samota zan kawo miki ita da hannuna." bai jira amsan taba yamike da sauri yace "mama sai na dawo zan sa Grema ya kawo mata kayanta."
"Ai idan kayane karma kadamu tana da kaya agidan nan sif dina cike da kayanta Hajara akwai sutura ai".



Har yanzu wajen Malam da bak'i dan haka kawai wucewa yayi.

Jidda ce take jan motan  Yasmin tana gefe sai Gana da Zahra suna baya zasu wuce daidai Gargar anguwan Zannah Yasmin tace" yawwa Jidda dan ALLAH ranan da muka raka  Aunty Hadim daukan Fuj gidan Malam a parlour matar ina pic dinda na nuna miki da muka fito nake cewa na taba sanin me kama da ita amma na manta to wllh da yariyar nan wanda  Yashid ya turowa Aunty Hadim pic din su suke kama."
Jidda ta kalle ta girgiza kai ta ckgaba da tukinta
Gana"tace wllh Yasmin kin shiga ukku wai ke nan ana wani zugaki anacewa lauya kikewa ko mai sai ido akai wllh inde wanan zance yafito awani waje to kece dan bazaki jamana awajen *Yashid* ba."
Jidda tace "ke kika kulata mutum sai sanin kwakwaf ki dubi wanan  kucakan  local ki hadata da wanan tsadaddiyar baby's da sukayi pic da Yaya"
Zarha ko dariya tayi tace "se barrister yasmin computer." dama tun suna secondary haka ake kiran Yasmin AISHA Lauya.  "Nifa ta idon mutum nake gane kaman mutum shiyasa idan mutum yasa nikaf mani nafi ganeshi."

Duk sunsan da haka dan haka dariya sukayi Jidda tace "kingamu da aiki ko ai".

*GIDAN. DR M D*

Habiba tace "kin san ALLAH ba wanda zaice wai wadan nan yara ba yaran ta bane lalle, Hadim sun bagalar da mutane, wllh ko zamu rantse da Qur ani ba wanda zai yarda damu kamar yadda Abban Nolfal ya fada ba muda sheda ko akotu mafita, kawai a bari har sanda Shid zai tonawa kansa asiri yafi dan ayan da yake bani labari Shid yana da wayo da dabara gashi da DAMA ahannun sa wato naira zai iya karawa koda da shugaban kasane dan saboda shifa ake tsorin karawa da kungiyar Chelsea a duniyar wasan ball shine na 3 amanyan yan wasan da aka tantance kinga ko wazai iya karawa dashi mutumin ba inda ba a sanshiba."

Fandau ta gyada kai tace"Aunty  naga alama koda yanda ake karra mashi a Saudia."
"na Saudia kikaga dan baki ganshi cikin turawa a acikin gari haka ba ne."

Kharat da Nofal ne suka shigo da gudu Kharat tace"Momy kinga Nol yana cewa wai Aunty kirki tafi sonsa ko", Fandau ta kamo hannun Kharat tace duk inason ku."
Nol yace"aunty kirki  ai kinfi sona?

Murmushi Fandau tayi tace" ba kuga cinyana 2 bane na dauraka kan daya itama na daurata to ai duk so daya nake muku."
Aunty kirki ni wananne ciyana inji Nol.

Haris da yake shine babba yace wllh Anty kirki kidena daukan su zasu gajiyar dake fa".

Habiba tace "nima Gaskiya bana son ki dinga daukan su dan cikin ki zai sha wahala."

Fandau tazaro ido tace" Anty dama bai zube ba."

"Au ashe bai gaya miki ba."

Fandau ta sunkuyar da kanta Habiba tace "yayi waya da doctor dinda ta miki alluran, ashe dama ba dayawa ta miki ba bai kai wanda zai zubar da cikin 4 months ba dan haka  jiyan ya aunaki yace akwai."

"Anty dama yasan Dr din ne"? Ai kina cewa kawarta ce kuma fara nagane dr adegas ce dan kawar muce ni na koya mata hausa ma har Kaduna tazo adalilina taje majduguri dalilin Hadim ko sunan Fuj taje."

Nabil zaune a office din Ndororo a airport din ABUJA suna jiran isowar Musa yaron da Hadim ta danka Fandau a hannu sa dan duk kwanakin nan atsare yake, Nabil dafe kansa yayi shi kadai yasan abunda yake ji ana haka wayan sa yafara ringing yana dubawa Ummin sace dagawa yayi yace"Ummi ina wani aiki idan nagama zan kira ki."

Dan inba dan itaba kira nawa baya dauka.

"Saurara  Nabil kar ka kashemin waya kana ina?
"Abuja." yabata amsa a takaice
"Nabil."
 ta kirashi
"Na'am."
Ya amsa
Kagayamin meyake faruwa da kai tunda nake ban taba ganin ka cikin wanan halin ba kuma inason kagayanin Gaskiya."
"Ummi zan gaya miki gaskiya kodan kitayani addua amma bazai yuwu awaya ba har sai nazo."
"to yaushe zakazo din?
"Ummi bansani ba sai nagama abinda nakeyi."

"ALLAH ya baka sa'a dan nasan koma meye yana damunka."
"Ameen Ummina
"dama maganan Hadim zan maka dan ance bata da lafiya har tana kwance a hospital amma banji abakin kaba sai Ya Fatime aka kira aka gayawa shima wata kawar tace ta kira."

"wai Ummi ba nace ta dawo gidan Ubanta ba ni mezan mata naji da balain da ta jefani ciki mana sai.....
Katseshi Ummi tayi tana
"Innalillahi yau mezanji ni Hajara ALLAH kajishe mu alkairi Nabil ni kake gayawa Hadim tazo gidan Ubanta meyake faruwa gaya min inda kake a ABUJA yanzu zansa akawoni,
Me hadim tama haka?
"Ummi zakiji sai nazo. "
Yakashi wayan ya dafe kai har aka shigo da yaron, yaron yana ganin Nabil yayi saurin zuwa ya fada masa yace "Shiddams nawa banji haushin daurin ba wllh tunda daurin kane dan ban taba tsammani zan saka a idona ba idan Ya Bello yace kai abokin sane bama yarda dan baita ba hadamu ba."

Dagoshi Nabil yayi yace "nima banso nasa aka maka haka ba sai dan rashi girmamawa da ka gwada min, ashe ma kai kanin abokona ne Bello ne", shima Bello waje ya samu ya zauna suna gaisawa Bello yace "Wllh kaga yanda hankalin Hajiyar mu yatashi dan autan ta kwana 5 ahannu haba Shiddams."
 Nabil yace "badan itaba da wllh bazan bar yaron har sai ya fitomin da kanwata".

"Bello yace "aikuwa ta gode shi Dad baya kasan ma."

Nabil yace "Yanzu  duk ba wannan ba kai Musa ba kace kasan matar da taje wajen Fatima acikin jirgin ba?" Musa yace "yes", "toh zaka iya nunata?" ya gwado masa fukan laptop din gaban Ndaroro video din mutanen da suka shiga jirin ne a London dan namu na Nigeria yaso ya samu inda suke fita aga inda tayi wai na'uran ya lalace nan ma ashar kam sun sha awajen Nabil dan da sun dauka wata kila da aga inda tayi tunda tana cikin rashen lafiya.

Musa ya zuba ido yayi saurin tsayar da loptop din yayi alokacin da yaga Habiba tana rike da hannun danta gefen ta Dr Muktar Dauda ne yace "gatanan nagane ta wanan ce so wajen 4 ina zuwa duk ina ganin ta awajen."

Nabil da Ndaroro tare suka hada baki wajen cewa Habiban Dr M D
Nabil yace "yes dama ranan yazo amma da yake dan rainin wayo ne shi da nake kwatanta masa ita sai cewa yayi ai ba shida mata ya fito ba gashi matar sa ya gani ai."
Ndro yace"suna kd ai jiya munyi waya yace zai shigo ajiyan."
Nabil yace "sun shigoma suna nan Abuja dan dama yazo duba jikin wani  bari naje gidan kawai."
Sukayi sallama da  su Bello ya mike da sauri ya fita jikinsa na rawa.

Bello ya kalli Ndaroro yace" lafiya kuwa"
Ndro yace" Wllh ya damu da neman yarinyar nan, Shiddams guda ya shiga wanan halin har yabar komai nasa yazo yan club din Chelsea tinda dazu ma bakaga yanda suke damun sa a waya ba."
Dariya Bello yayi yace"ba dole ba ai sunsan shegen  bashi da alkibila zasu zata zai canza ne." Ndaroro yace" *Shiddams* shegene."
 Musa yace ."amma shid bai taba jimawa a kungiya irin yanda jima a Chelsea ba."

Fandau da yarane kawai a gidan dan Habiba sun fita da Abban Nol.
Fandau tace "kar kuyi fada Khairiya ta zanje na gyarawa momy bedroom  kunji" hankalin su yana kan kallan da sukeyi basu mata magana ba har ta haye sama bata karasa shiga bedroom din ba taji wani irin faduwan gaba sanadiyan jin ihun yaran suna my pappa Oyoyo tasan Nabil suke kira da wanan sunan da sauri ta karasa shiga kafanta yana tsakewa dan Muktar yace karta kuskura duk randa Nabil yazo tayi garajen ganin ta.

Shima cewa yayi Oyoyo Nol Nol and Kharat ina my son Haris yaje wasan ball da gudu shima Haris ya shigo yana my pappa shima, rungumo shiyayi yace"ina su ABBA?", "sun fita sai anty kirki kawai yace " ok yana zama ya zaro wayansa ya kira dr Muktar yana tuki da yaga kiran Shiddams yayi parking agefe ya dauki wayan yana cewa "manyan gatan wasa Abu Bilal da Fuj.....
Katseshi Nabil yayi dacewa
"ina Habiba ne?
Yace"gata ya mikawa Habiba wayan.

"Yaya na."
"Mamana  yakike?
Tace "lafiya yayana."

"na sake kirane akan wanan yariyar", da sauri Habiba ta kalli Dr shima dama yanajin su dan saida yasa wayan a Handsfree yamika mata da kai ya mata magana tace "eh"
 yace "yawwa ashe har kin mata ma magana."

Cikin faduwar gaba Habiba tace "Nikuma?" yace "eh" Dr ne ya karbi wayan yace"wai wace yariyar ce ne ni kadamu kanka da mutane akanta haba shiddams kuma bincikin harya biyo ta kan Habitees kai..... Nabil yace bazaka gane ba ne Dr M amma kuzo idan ku na asokoro gani nan agidan tabbas Habiba tayi magana da yarinyar."

Cikin sauri Dr yace"kana gidana suwa katarar agidan?

yace" yarane sai sunce da anty wama da sauri Kharat tace "anty kirki"

Kashe wayan Dr yayi yace "shikenan ya ganta."

"Y asalam yanzu shikenan zai sameta a arha kenan burinmu namu wa yar da ita bazai cika ba, Wllh my sweetheart ko ya mayar ta cikakkiyar matarsa wllh wanan yarinyar bata isa karawa da Hadim ba wahalan da yake gaban ta yafiwan da tasha a baya yawa indai Hadim ce akan mijin ta."

"Habites yaci nasara dama bana gaya miki Shiddams shegene bane, baya samun rashin nasara a aikin sa ba ko kinsan bincike yayi a office Security's na cikin jirgi ya nuna kece kikayi fira da ita wata kilama har inda muka fito ya nuna naso ya gane kuren sa, naso ya gane aure ba abin wasa bane naso ta samu *DAMARTA* ta rama abinda suka mata.

Habiba tace
"yanzu shikenan Abban Nol?

"ba shikenan ba nima zan gwada sa'a ta nagani zanyi amfani da *DAMATA* naga komai ya tafi daidai zan baki mamaki."

Habiba tace"me damar taka?

Yace "cikin da yake jikin ta shine babban *DAMATA* dashi zanyi  *AMFANI*".

Ta rasa yanda zatayi Haris sai knocking kofan yakeyi da karfinsa
" Anty kirki ki bude ga pappan mu yazo kizo kigan shi shine yakeyin Ball Anty kirki  bude anty.......


*Masoya wai ya labarin Hadim ne meyake damunta? naji Ummi tace tana hospital*

*Nabil zaici nasara a fafatawar da zasuyin da Dr Muktar Dauda.*


*Team yasmin yar Inna 🤣🤣🤣  lauya* 🤝🏻

*B JATTK*
[3/12, 8:49 AM] Hauwa: *DAMATA*





                  *Na*



*BATUL ADAM JATTKO*


*Gaisuwa da jinjina* *gareki*
*Biebie Isa*
*DAMATA*
*yana tafiya tareda* *ingan taccen shawaran kune keda Aunty Sis*
*Kaunan kuda karam cinku gareni babba ne*
*Adade anayi sai Gaskiya*

*Mn amir muna tare*


(Editing Mzz daddy)


*39*

*A*unty kirki kina bathroom ne shikenan idan baki fito dawuri ba wllh baya jimawa."

Da gudu yasake saukowa "pappa bari kaga Aunty."
Shiko Nabil bata suyake ba hankalin sa yana kan wayan sa inda suke cht da Sani akan binciken yakeyi shima

Gudu dr yake sosai har yakara so dan yasan halin surutun su Kharat

Suna zuwa ko gaisawa bai bari sunyi baya nunawa Habiban pic din Fantau yace"tabbas kinyi magana da ita acikin jirgi dan haka nake son kigaya min,
Abinda kuka tattaun da kuma inda tayi bayan fitan ta agunki kawai nake da daman wanan bayanan please."

Wanan tambayan nasa shiyabawa Habiba daman gane Nabil baisan mesuka firata da itaba kuma baisan inda tayi ba besan suna tare ba cikin dakiya

 tace "awo wannan kake magana kwarai kuwa nayi mata magana ganin tunda suka shigo da yayanta ya ajiyeta yaje side dinshi  sai kuka take ko da akazo tambayan meza akawo bata ko daga kai batayi ba shine naje wajen ta nake mata tambaya meyake faruwa amma ko kuffan bata cemin ba kuma mun rigasu sauka dan haka bansan inda sukayi ba."

Nabil wani k'ara yayi da yazame kasa ya dafe kansa idon sa yayi wani irin kadawa kamar ansa masa barkono matse idon yayi yana son hawaye su fito kozai samu saukin radadinda idon da zuciyar sa yake masa amma idon a soye yake daya daga ido ya kalli dr saida dr yaji gaban sa yafadi
Cikin wani irin muryar wanda basu sansa da shiba yace "MD da kunsan wacece wanan yariyar awajena daba kubari ta yi wani wajen ba, da baku bari ta bata ba."

    Dr yace"matsayin ta kuma kace kanwar kace, ni narasa ina k'a samo ta bayan ni bansan ta cikin family kuba." Habiba tace niko abban Nol kallon sani nake mata, tamin kamada wata a maiduguri fa na manta inda nasan tane."

   Dr yace"niko ganin ta banyiba." Ajiyar zuciya Nabil ya sauke yace." amma kikace tana kuka ko?

  Habiba tace "eh kuma sosai."

   To me yasata kuka anya an mata alluran nan kuwa duk da Hadim tace anyi amma meyasa banje na binciki Dr  Adegas ba? yace kai gwara da banje ba idan naje nasan sai naga gawar ta dan bazan kyaleta ba idan da anyi allura ina zata san ida take balle tayi kuka da sauri yada go yakalli Habiba yace" kiramin Adegas din."

   Murmushi Muktar yayi yasan za aje kan haka dan haka sai yakira Adegas tun zuwan su lokacin ma Nabil yana Rasha yace idan Nabil yazo duk juyin da zai miki kar kice bakiyi alluran ba kice kinyi.

    Jin haka ma yasa Adegas tabar gari tace sai ya huce ta dawo.

     Habiba ta dauki wayanta ta dannan dialing ta sai suka gaisa tace" mata Shiddams yana son magana dake ta mekawa Nabil cikin kakkaurar murya ya tambaye ta tabashi amsa cikin tsoro kamar tana gaban sa tace tayi mata, wani irin cilli Nabil yayi da wayan atake yayi filli filla.

"kai kai kai saboda kai me kudin banzane zakamin asarar wayan matata."

    Habiba tace "ran sane ya baci amma waya isa yacewa d'ana me kudin banza ne bayan da gumin sa yake aiki."

   Nabil ganin baza su taba gane wacece Fandau awajen sa ba shiyasa suke masa wanan abin dan haka ya mike ko yara da suke faman yi masa surutu bai kula su ba ya fice yana hada hanya kamar me jin bacci, ganin Nabil bazai iya tukin ba yasa ya fito da wayan sa ss dinshi ya kira yace yazo yana gidan Dr na Asokoro, Dr ya fito yace bari nayi driver din ka ko, bude mota yayi yashiga baiyi  magana ba bayan sun fita a gate Dr ya kalle shi
 yace" ina muka dosane dan gidajen Nabil a ABUJA suna da yawa nan ma kinyi masa magana yayi shide wuse yayi da shidan yaga yafi sauka acan.

    Sunayin parking me gadi ya washe baki yallabai saukan yaushe yau banga labari. ba bansan da zuwan kaba."

 Nabil bai masan yanayi ba sai Dr "yace" baba zuwanne na bazata." Ya bude musu suka shiga da gudu yazo zai budewa Nabil mota kafin ya karaso ma ya fito, yace yallabai barka da zuwa, kansa adafe Nabil ya shiga cikin gidan main parlour ya zube dukda da dan kuransa amma akasa ya zube wanda da dane akwai ma aikatan da ake turowa a cikin gidan gomnati villa sukula da gidan kafin ma ya shigo gidan zai taddasu Dr yace" ni zan koma dan naga kaima ko alluran kin maganan aka maka."  Kirane ya shigo wayan sa ya dauka daker dan ya kashe sauran layuka a wayan sai na wanda  suke masa bincike akan Fandau kawai yabar inde yaji kira to sune.

   Ya daga wayan "sir mezai hana a yada photon ta asa wasu kudade wllh  ayau za aiya samun ta." Da kyar Nabil ya bude baki  yace" ka fini sanin hakane, to tafi karfin a bugata ya zama wanda bai isa bama ya kalle ta."
"Sorry sir Dr saida yatsaya yaji kwakwaf yasa kai ya fice  yana dariya wai Shid ya zama haka kuma akan mace lallai ya yarda duk ajin maza su ba komai bane agun mata, Shiddams da manyan babes ke tsoron tun kara yake garari akan wanan yariyar tabbas alhakin tane da na cin zalin aure da sukayi yake dawainiya dasu."

     Fandau sai da Habiba tace "Anty kirki bude tukun ta bude.

"Aunty ya tafi?
"ya tafi saide fa ya zama kalan tausayi."
Da sauri Fandau tace "meyasame shi?
_Sai asannan habiba ta tuno ashe Dr ya hanata tacewa Fandau Nabil yana neman ta dan kar ta tausaya masa._

  Da sauri ta gyara zancen da cewa
"wai Hadim ce bata da lfy." A nan Fandau ta sake tabbatar wa kanta dasanin Nabil komai ya faru ALLAH ka ciremin son wanda besan da daraja taba na dena wahala akan  son maso wani dama bai taba furta yana sona ba ya lallaba ni ne kawai ya mori albarkatun jikina bata san afili take maganan ba saida taji Habiba tana bata baki sai cewa tayi  "Fandau kin samu dama da shaidu masu karfi amma kika bari damar ta kufce miki meyasa da yace zai iya baki komai har gidan sa na saudia meyasa baki karba ba da yazama shaida awajen ki." Dr yace" kota karbi gidan bai zame mata shaida ba dan kowa yasan Shiddams da kyauta, ai shaidan ta daya shaidun aurenta magabatan ta tunda ta saki wanan damar ko ai dole, tunda bata samu wanan gatan ba bata  da wani dama yanzu ai da agidan su gaban iyayen ya aureta ba zai mata hakaba marar tunani me kwakwalwan kifi, kuka yanzu kika soma ai
sai asannan Fandau tasan da zuban hawayen da yake bulbula a idonta da ya jika mata gaban riganta. Da gudu ta sauka tayi dakinsu.

*BAYAN KWANA 2*
Nabil  duk wani hanya da zaibi yaga ya sameta cikin *kwanakin nan 2*, amma shiru ba labari idan yace zai yada pic dinta shine zai fi saurin samun ta amma hakan bazai yiwu ba yin hakan tamkar ya dauki wuka ne ya dabawa cikin sa dan asirin sa ne zai tonu, shiyafi son ya same ta yakai wa mama amasayin ya tsinceta ne daga baya sai yace yana sonta tunda dama yayi wa mama alkawarin zai kai mata ita da hannun sa
gashi Ummi ta matsa masa akan maganan Hadim gashi shima jikin sa ba yajin dadi. Wayan sane yayi ringing yana dubawa Ummi ce ya daga "gamunan muna ABUJA awane gida kake? " wuse" ya bata amsa atakaice
ba jimawa suka shigo Mala kaninsa wanda suke uba daya ne sai Hanif dan Ummi da ita Ummin.

Mai makon amsa sallaman nasu daga kai yayi kawai ya kalle su ya mike zaune yana matse fuska yanda kirjinsa yake masa ciwo da sauri Ummi ta karasa tana "subahanalla Nabil meya mayar dakai haka? kana ganin kanka kuwa yanda karame idanuwan ka sun sake fitowa meyake faruwa?
Nabil fad'awa jikinta yayi ya saki kuka Mala da Hanif sun tsorata basu taba ganin kukan Nabil ba sai yau kome yake damun sa abin babbane suma durkusawa sukayi agaban su cikin tashin hankali Ummi take tambayan sa.

  "Ummi kuskure nayi wanda bansan hanyan gyaran saba, Ummi zan gaya miki kadan daga ciki ke kadai nakeson gayawa, ke yakama ta kisani kirike min sirrina ki kuma yimin addua."

Kallon su Hanif yayi alaman su fice aiko suka fita.

"Ummi na tsinci  wata yariyar a saudia watanni 7 da suka wuce sai dana a cikin harami, tana gani na ta kira sunana tace min ita yar gidan Zannah Modu ce dan ALLAH na taimaka mata wata mata ce ta yaudare ta da sunan zata kaita tayi aikatau acan tasamu kudin da zata budewa Mamar ta ido shine ta bita saida ta gama tara kudin tukun sai matar ta gudu da kudin yanzu ta rasa yanda zatayi tazo gida, acikin harami take kwana abinci kuma tanayin bara taci shine da ta ganni ta ganeni.
Nima tana fadan haka na gaskanta ta dan kaman ta da Malam, nace zan dawo da ita shine tace idan tazo gida kishiyoyi mamar ta zasuce taje yawon karuwanci ne  ta nemi alfarman na aureta inyaso nace nine nace ina sonta alhalin ansamu su rana da Shattema munsan bazamu samu juna ba shine muka gudu mukayi aure da ita, ganin bazan iya barin jinin Malam ya tozarta ba yasa nayar da dawanan Shawaran aka daura mana aure".

   Na yarda an daura mana aure da itane kawai dan darajan iyayen ta shine na ta fida ita London da zuman idan tasamu ciki idan munzo za afi barinmu mu zauna tare shine ni kuma gaskiya na kamu da son yariyar dan burin ko wace, amma kishin Hadim yasa dana bar yariyar na tafi Rasha shine ta kira wata kawar ta likita ta yiwa yariyar alluran zubar da ciki dana wanda zata manta komai nata ta aunota nan Ummi bansan inda zan samota ba Ummi inason yariyar idan bangan taba wllh akwai barazana cikin rayuwa ta." Ya sake fashewa dawani irin kuka.

   Itako Ummi  kasa bakin magana tayi sai tafa hannu take da kyar ta samu bakin salati ni Hajara wannan zamani ita Hadim wacce iriyar macece da zata ce baza amata kishiya ba har ta illata yar mutane haka inda ba'a kishiya aduniya da uban ta bai auri uwar ta ba dan wata tatarar karewa ma ita me sunan kishiyar uwar tace, inda ba'a kishiya da ni kaina ba'a aureni na haifeka ta sameka ba nima wata na tarar duk da kai ma kanada naka lefin na boye mata musamman mu da ka gayamana ko da ka tashi daga saudia da kaitsaye gida ka iyoda ita da hakan bai faruba dan meza ka boyeta kace wani saita haifu gashi abinda ya janyo da wane ido zamu kalli Malam da Aisai mutumiyar arziki."
Nade Ummi tayi tayiwa Nabil fada

_Shiko hamdala yayi ganin koyau Fandau tafito zai mallake ta basai_ _asiri ya tonu_ _ba, yaran su zauna a yaran Hadim din kawai shide_ _yakasan ce da Fatin sa sai yaji wani karfin guiwar nemanta dan yasan Ummi zatayiwa Abban sa bayani yanda zai_ _gane._

Ummi ta sake cewa
"yanzu kenan tayiwa mutane asaran cikin wata 4."
"Ummi barni da ita na daga mata kafane dalilin cikin da yake jikinta ."

"amma inason ka janye kalman saki da kamata."

" shikenan yanda kikace haka za'ayi Ummina na maida da."

Ummi tace " yawwa sai kuma abuna 2 dole Malam da Aisa susani dan su tayamu adduan nemanta, sai kuma inason kai ma Baban ku yasani daga iya mu kar kowa yasani har sai an sameta kasan halin wanan Innar taku yanzu zata jakula komai." "to Ummi amma Ummi kimin alfarman koyawa Hadim hankali dan kiyaye gaba."

"Wane koyamata hankali zakayi bayan halin da take ciki ma ya isheta jiya wata kawar ta takawota ai bakaga yanda takoma ba ninan da niyar naci maka mutumci nazo sai na tadda lefinta yafi naka, saide ya fatime dole inaga itama tasani dan tananan tana fada baki da kunfa."

Mamar hadim kenan

"shikenan Ummi amma itama kartasan na maryar da Hadim din."

Ummi tace
"Bazata sani ba."


A ranan Ummi ta tasa Nabil a gaba suka koma. Alh Abubakar baban Nabil har marin sa yayi dan lefin shiya daurawa idan bashi yasakewa mace ba har ta isa tayi.

Shiko Malam lefin Fandau yagani dan a ganin sa Nabil taimakon ta yayi ma ai godiya dasa albarka ba irin wanda mama da Malam basuyiwa Nabil ba dan susan saboda su yayi.

Ko wacece wannan matar ta cucesu ta yaudari yarsu ta kaita har saudia.

Malam ya dukufa addua sosai duk dama yanayi dan yana mutukar son Fandau.

Itako maman Hadim cewa tayi kawai taji tayi lefi amma bai kamata ya dauki Fujjirat ya kaiwa uwar kishiya ba a karbo mata jikar ta, tayi akira mata Nabil kinzuwa yayi sai ita ta taka taje gidan Nabil din amma security suka hanata shiga dan waya suka yiwa Nabil yace kar abarta.

Aiko baki da kunfa tasa Sudais ya juya da ita gidan su Nabil ta samu Ummi ta mata tatas tace takira Nabil din
Nabil yana shiga ya gaida su "yace Mama ya mai jikin?

"lalle Nabil karena min hankali sai anan kake tabbayana ya mai jiki, aiko mutuwa tayi kaine sila tunda kai kamata duka ba kaga halin da take ciki ba yanzu tun yaushe tazo amma ko ajikin ka bakaje dubata ba."

"Mama inajin baki gama sanin abinda ita Hadim din tayi bane, ai gwara nida na daketa gashinan na bar miki ita kina kallon ta,
Itada ta tashi ba la'anta yar mutane tayi ba? ta kuma batar da ita, amma ina son idan kin koma ki gaya mata Wllh wllh darajan cikin da yake jikinta na kyaleta yanzu amma zata haifu zata ga yanda zanyi da ita, zuwa duba ta kuma karkiyi fatan wannan dan inhar zansa Hadim a idona to zan hallaka ta dan haka rashin zuwana rahama ne."
Kuka mama tasa tana nuna Ummi Hajara kina gani a gabanki dan da kika haifa a cikin ki yake gayamin wanan maganan?

Ummi itama bata ji dadin abinda yayi ba amma tasan halin Nabil idan ransa ya baci zai iyayin fin hakama dan haka tace "tashi katafi kafin ka rufe muda duka."

Cikin kuka Maman Hadim tace ni yaje ya karbo min jikata ya karbota kawai."

Har zai fita Ummi tace "kaje ka karbo Fujjirat."

Juyowa yayi ya kalli mama yace jikar ki ya wuce na jikin yarki  idan ta sauka idan macce ta haifa inason asa mata Fatima idan kuma Namiji ne Abba inusa amma fa Fatiman da na fada kar ki dauka sunan kine tunda kema Fatime sunaki."

Girgiza kai Ummi tayi tace "bance kafita ba."

Yafice yana cewa danme baza ta barni da masifar da yarta ta jamin ba sai tazo tana min masifa
Wllh in Hadim batayi furcin ba to wllh Fatima ta baiyana kafin haifuwar ta kai ko ta baiyana inde bata cikin haiyacen ta sai tayi zaman gidan yari baki koyawa yarki yand.......  Ummi ce ta katse mishi maganan da jifansa dawani cup na glass sannan ya karasa ficewa  "Yaya dan ALLAH kiyi hakuri ke kanki sheda ce akan yanda halin Nabil yake tun yana yaro idan ransa yana bace ba a masa magana bake ba koni idan na matsa wllh abin ba zaiyi kyauba."
"hajara ke sai ya miki ki kyale shi amma banda ni.  A zaburi Hjy Fatime ta mike har da gudun ta tafita wajen a daidai inda zai shiga parlour Iya ta same shi ta baya ta fincikoshi "kazo ka gaya min matsayin y'ata awajen ka kuma ko a kotu sai na karbi dukka jikokina."

   A hankali Nabil yasa hannu ya kwace a hannu ta idon sa fes cikin nata sai kace a gaban abokin sa yake yace "matsayin yarki bata dawani matsayi a wajena sai dai idan ragowan sakinta kikeso zan iya bin umarnin ki a masayin ki na uwa a gareni in baki sakinta.

"Sai kuma batun yara kema kince jikoki, jika ko ba d'a  bane ki bari me yaran tace a bata da bakin ta" Iya ce ta fito tana "Subahanalla Nabil ya haka" Ummi mari tafara zu bawa Nabil shiko Nabil nade hannunsa yayi a kirjin sa yana jin yanda Ummi take zuba masa marin, kanne sa dukka suka fito sai kuka suke dakyar Iya ta ja Ummi itako Mama zubewa tayi tana rinjin kuka
Nabil ficewa yayi ya fada mota driver yaja motocin security dinshi suka rufa masa baya suka fita cewa yayi airport zasuje dan shi gani yake kamar ABUJA ne zai bashi Fatin sa.

*GIDAN DR MUKTAR*
"Aunty yanzu jibin zamu tafi kenan?
"habiba tace insha ALLAH kirki ta Ghana zamu tashi saboda ke Dr ya sara tafiyan ta can dan a wanan kasan bazai ykwu mu tashi dake ba yanzu haka Ghanan ma a mota zamu tafi saboda Shiddams ya tsanata bincike."

"Aunty yanzu haka zankoma banje naga su mama ba."
"Toni Fandau ya zanyi ne nayi nayi dashi yaki, nace idan munje dake kisa nikaf har mufito a kallah de kinga mama zakiji dadi, amma sai cewa yayi ai baki damu da ita ba da baki barta ba, saide idan kezaki gaya masa kiji."

Fandau tace"ni kema kinsan ban isa ba jiya haka yace wa maimu me aiki kar ta karayin komai a gidan nan nice sabowar me aiki ni zanyi."

Dariya Habiba tayi tace"wai dan kikoyi hankali ne yace ko amma da nake tambayar sa yace yana sone kina dan mosa jikin ki kinga cikin ki ya shiga wata 6 dan kisamu sauki wajen nakuda."

Ko da zasu tafi kaduna barin Fandau sukayi da meimu suka tafi.

Shiko Nabil abubuwa ya kacabe masa ga yan kungiya sun matsa masa wata 2 bashi har sauran kun giyoyin sun fara kawo farmaki ana ta yadawa wai Shiddams yabar Chelsea fans dinsa da sauran mutane sun damesa a media ga zaryar hospital yake ma dan ba shida cikakkiyar lafiya kullum ciwon kai dana kirji yake fama dashi, kowane dr idan ya duba shi sai yace yasa wani abu ne a ransa wanda yafi karfin zuciyar sa idan bai cireba to yana barazana ga rayuwar sa aiko yan club din su sunajin haka suka zo tafiya dashi ayi jinyar sa acan yace a'a abu har ya kaishi ga kwanciya sosai.

*HADIM*

Ko makiyinta ya ganta cikin wannan hali zai tausaya mata "Mama yanzu Nabil din bazai zoba bayan ance yana garinnan Ummi yasani a blacklist  bana samun sa mama kibari naje London din mana na same sa tunda kince yakoma."
Mama cewa Hadim tayi Nabil ya koma dan ta kwantar mata da hankali amma kullum zancen ta Nabil da kuma a karbo mata Fuj yanzu dai Ummi ta sa ankawo Fuj sai Nabil da take ta ambata wanda acikin asbitin daya ma suke akwance bata sani ba dan ita ma sosai take akwance kullum Dr  suna cikin yimata nasiyar ta kwantar da hankalin ta saboda kwata kwata BP dinta baya sauka zai iya janyo matsala idan watannin haifuwan ta yayi idan zamu mata aiki dan.......
"aiki kuma?
 inji Ummi da mama
Dr Hafeez yace ba na rubuta muku bayanan acikin katin da na baku ba amma kubini office na karamu ku bayani."

Ummi da Maman Hadim zaune gaban Dr Hafeez
 Yace " yaka mata ku kula da halin da yariyar nan take ciki, yanayin cikin ya kamata a kula da ita sosai tunda ba haifuwa zata iyayi da kanta ba aiki za amata dan mun duba mugani kugunta bazata iya haifuwa ba sai de aciro to alluran da zamu mata idan lokacin yayi ba ayiwa me hawan jini dan zai iya barazana ga rayuwar ta ita kuma BP mai makon ya sauka kullum kara hawa yake....

 Mama kaseshi tayi da cewa aikin banza rashin sanin aikin kune na kasannan yaza ace bazata iya haifuwa ba itada ta haifi yan biyu ma lafiya haifuwa na 3 ace kugunta bazai iya haifuwa ba."
Dr yace" hjy a kugun akwai wani kashi a kugun kowani mutum mace ko namiji to dana maza ta na bata akwai ban banci na maza babu tsagu na mata da tsagu yanda idan mace tazo haifuwa wannan kashin shi zai bude shine zakiji nishi yazowa mace a daidai budewan tsagun na kashin bazai koma yarufe ba harsai d'a ya fado zai rufe, to ita Halima wanan kashin ba tsagu anata dan haka zan iya ja da kowane likita akan bazata iya haifuwa fa."
Mama tsabar haushima kin magana tayi  Ummi "tace Dr dena fada duk haifuwan ta da kanta take haifan su Dr Hafeez yace"hjy kina nufin wannan ta taba haifuwa?

Ummi tace "Wanne irin tambaya ne wanan Dr muna cemaka haihuwa na uku zatayi na 2 ma yan 2 ta haifa yariyar da ka gani a gefin ta tana bacce itace yarta ta fari"

Dr Hafeez yace "Hjy ni a bincike na wanan mahaifan bai taba daukan ciki ba sai wannan asali ma shikan sa mahaifan cike yake da matsaloli dayawa da farko yana iy.......
"dakata inji Ummi dan itama yafara bata haushi itako Mama fuuu ta fice Ummi ma mara mata baya tayi.

Dr yace "niko idan matar na ta haifu da kanta daga ranan zan bar ai kina dan bai min amfani ba."

Sude basu saya bashi amsa ba suka fice.

Suna fita wajen dakin da aka kwantar da Nabil sukace karo da su Jidda sai runjin kuka suke suna ambaton  Ya Shid kar kamana haka wllh kaine gatanmu shi kawai suke mai maitawa Ummi ji tayi bata iya daga kafanta  dan dama tabar Nabil cikin wani hali yana aman jini dasauri wani Dr yafito yace"wacece Ummi? Da sauri Kamal ya kamo hannun ta yace" gatanan ya farfado ne? ni nasan dama suma yayi ai
Nabil yana gani Ummi yayi wa Dr  alaman ya cire masa roban jawo nufashin da yake hancin sa dan baya iya daga hannun sa Ummi tana karanta duk addu'an da yazo bakin ta takara sa inda take kamo hannun sa tayi dakyar ya bude bakin yace "ba'a ganta ba Ummi an nemeta an rasata bansan hanyan da zanbi na samota ba Hadim ta hallakamin ita naso ALLAH ya barni naga haifuwan Hadim na daukarwa Fatima fansa bakin cikina Ummi tasha cewa nace ina son ta amma ban taba furta mata ba ina ma zan ganta ko a mafarki da nace inason ta inason ta ba a dadi, Ummi zan barmiki wasiya idan ta baiyana kice ina sonta har na rasa raina akanta karki damu da yanda take na rashin hankalin ta kigaya mata nina sani ni da ita zuciyar mu ahade yake Ummi  me na yiwa Hadim ta lalata rayuwa ta bayan ni namata duk yanda take so ita fatasa na auri yariyar dan................. 



*Tofa Nabil Allah ya baka lfy amma kar ka tona asiri*😭😭😭

*Ya Hadim zasu kare da Dr Hafeez me tonan silili mai gani har hanji da gaske ne kashin kugunta irin na maza ne wato ba zai iya budewa ba idan tazo haifuwa wane irin matsaloline a mahaifarta*

*Ya Aisa maman Fandau taji da taji yanda rayuwa ya juya da yarta*


*B JATTKO*
[3/12, 8:50 AM] Hauwa: *DAMATA*





                   *NA*





*BATUL ADAM JATTKO*

*Phareedah umar sokon ki ya iso gareni kuma na gdy da kauna ki zanduba bukatun ku na insamu ina muku typing koda (2days ) ne*

*Haeeza Murtal*
Banman tadake ba
Dakeda duk kan masoyan damata

 *ME ZOGALE*
*kema muna mugun tare*


*Gaskiya kina mutukar godiya agareku masoya ina mamakin yanda kuke nuna soyyyyan ga* ```DAMATA```
*Ina baku hakuri wanda suka min magana ban samu na amsa musu ba wllh abubuwa ne suka min yawa amma ina dare da masoyana aduk inda kuke karfin guiwan ku da addua anku yake kara karfafanin guiwa musamman JATTKO GROUP kuna sani nishadi wllh 🤣🤣🤣🤣ina tare daku*


( editing mzz daddy)


*40*


*K*asa k'arasawa yayi dan yanda dan tumfashin da yake ja yagagare shi yaja idonuwan sa suka kakkafe atake da sauri Dr yabayar masa oxygen ahankali nunfashin yafara sauka

Ummi kuka take sosai Kamal ya kamata yafita da ita yana kwantar mata da hankali

Wani sadeden gaye nagani shida familyn disa badan karnayi karyaba zan iya cewa wane  Nabil akomai da sauri saurin yake takawa haryabar ss dinshi da family shi su Jidda suka meke kai Ya BilAL  BilAL Maina kangeya kenan d'aga Ahj Maina kange millions wanda ya dauki dauyin karatun Nabil shine yake takawa har gaban su Ummi ya durkusa ya gaida su Kamal cikin girmamawa yamasa jagora har gaban gadonda Nabil yake kwance Bilal yasa abokin nasa agaba yana mamakin wai Nabil da mata suke tsoron tunkara yakoma haka akan macce

Yakalli Kamal yace kamal "kiramin Dr din ."
kamal yafita suka shigo da Dr tare
Bilal yace"Dr  kuhada mana kwararun doctor wanda zasu ina control din matsalan sa acikin jiri har kukara sa England."

Dr yace ok sir yaushene tafiyan? yace "yanzu."

Kamal dadi yaji dan bayanda ba ayi da Nabil afita da shi amma yace shibawan da ya isa yasa shibarin Nigeria dan Fatin sa tanaciki sunrasa wacece Wata Fatin dansu har yanzu ba agaya musuba yanzu koyasan bai isa hana BilAL fita dashi ba

dasauri doc yafita

daidai da shigowan malam da Baban Nabil da Bunu dan gidan Malam
Addua malam yamasa yace Bunu da Baba su daga shi abashi rubutun Baba
 Yace
 "akkaramakalha da anbar rubutun nan tunda kace na dan ganane kar kuma wata rana matar sa ta baiyana yakita azo ana nadama."

Murmushi Malam yayi yace" Abukar abashi."

Bunu da kamal suka daga shi kuka Nabil yasa daker yabude bakin sa yace"Malam kar abani abinda zan manta Matata."

Matsawa Malam yayi inda yake yakama hannun sa yace"baza ka manta ta ba wannan na samun saukine acikin cunci ko bakaso Fatin naka ta sameka da lafiya ne?
" ina somana Malam
Yaushe zanganta?
"kakusa ganinta kasha rubutun komai zai zomaka da sauki."
ai dasauri
Yace"idan nasha za aganta?
Malam yace "insha ALLAH."

Ai da sauri ya daga kansa duk da bazai iya tashiba alaman abashi Bunu ne yakara masa roban abaki yadan sha sosai sai da yaji cikin sa yana murdawa yabari shiko kashi zai iya ci inde za asamu Fatin sa
Kamal ya kwantar masa kan a filo
 Bilal ya durkusa ya gaida su   Baba yace "Malam waifa BilAL soyake ya fitar da abokin nashi."
"ai ba lefi saide aikin da zan masa na kwana 3 addua idan angama sai su tafi."

Cikin kwantar da murya BilAL yace"gafurta sai atafi da kai ai inde badamuwa."

Malam yace "badamuwa zanso hakan saide gobe akwai meeting namu na hakimai  wanda yazama dole na halarci taron da safene da yanma sai muwuce."
Baba yace "da yau da goben duk dayane ai."

Haka washe gari aka tarkata Nabil da har yafara samun sauki dallin aduar da ake masa aka fita da shi  yan club din Chelsea su sunji dadin hakan su suka dauki nauyin komai

Maman Fandau danne watayi agaban su Malam amma hankalin ta bakaramin tashi yayi ba harya fi na sanda Fandau ta tafi tashi yanzu shikenan anmata alluran da ta banta da komai arayuwan ta bazan iya yafewa matar da ta dauketa ta kaita saudia dan ta nema mata kudiba ALLAH sarki Fatima na da taji labarin zan warke shine aka yaudare ta da dashi dama nasan yanda kike sona da kishina komai zaki iyayi akaina saide yarinta  daya hana baki gane illar kina macce me karancin shikaru barin ki gida da hatsarine ba bakiyin tunani ba gashi har kin fada halinda kwara makantata so dubu amma nasan Halima bata san ke y'ata bane da bata gwada wanan zalincin akanki ba dan kina kishiyar ta
Koda ta gayawa Bagana haka bagana taci kukanta tace "mama wllh dawannan labari kwara ace ta mutu."

Mama tace "ina zaki hada dama ai mutuwa kowa zaman jiranta yake."

"mama ALLAH ya isa tsakanin muda Hadim."

Mama tace "kai dena fadan haka kiyafe mata dan nasan ba lefinta bane lefin mesunan Malam ne daya gaya mata  yarmu ci danasan halin kirkin Halima da bazata mata ba."

"mama wllh da lefinta ai kishi ba hauka bane koma yar wacece yaka mata tayi hakane  jiyan nan fa naje naduba ta baga yada taba ni tausayin ba bata da lafiya abin dausayi tunda nazo nakecewa abban Tajjudeen anty Hadim ta zama abin tausayi ashe ita ta jefa min yar uwa cikin wani hali ban sani ba sake fashiwa tayi da kuka tana cewa YaFandau ina zanganki."

Dakyar mama ta lallasheta
 tace" keda kike hakin haifuwa yau ko gobe bai kamata kijefa kanki cikin damuwa ba shima Nabil din yana iya kokarin sa wajen nemanta
Mama ta dauki Tajuddin tace "dashi zan tafi dama an dauke Hajara."

Bagana tace "wllh Mama tunda muguwace kar ki kara rike mata yarinya."
Mama de har suka fito harabar gidan bata yiwa Bagana magana ba dan ita son Fujjirat ajinin ta yake har driver yaja suka fita suka bar Bagana da tisisin ciki

Nabil yasuki yafara samuwa yanzu har takawa yake da kafafuwan sa memakon da da kowanka yimasa ake yadena jin ciwon kirjin aman jini duk yadena sai kuma  tunanin Fandau yananan dan duk baya ji kamar da
Malam da Baba har sun tafi sun barsu amma tunanin Fandau kam haryanzu yana fama dashi kullum yana makale da wayan sa yana ganin photon ta a status dinshi kam kullum kalaman soyayya yake daurawa instagram, tweeter dasaura media amma baya daura photon dan yasan yana kishin ta a status dinshi na whassapp kawai yake daurawa dan yasan bawan da zai gani dai wanda yayi saving dinshi shima da wata ta dauka da shijab a saudia yafi daurawa
Akullum Billah yana kwantar masa da hankali daza  a sameta Dr MD da Habiba sunzo sunduba shi agidan bayan an sallame shi ko da suka zo saida Nabil yace "wai Habiba wanan yariyar haryanzu baki kara ganin mai kamarta ba wllh wanda nake sawa bincike duk basu san akin suba."

Habiba tace "kai YaShid kadamu da yariyar nan dayawa fa wai meye masayin ta awajen kane?

Nufasawa yayi
Yace to yau zakuji basayinta awajen na yagaya musu kamar yanda yakayawa su Ummi   amma yace "saide fa sunce nabar zance sai sanda tafito kawai sai ace dama ni aka daurawa  kunga lifin ita yariyar na bin matar saudia ya bata sannan lefin Hadim yabata  abin da yasana fada maka innaso tunkafin ta fito anemo mata maganin da zata koma kamar da shiya sa nake ta meman wanan yar iskan Dr Adegas din bana samunta
Inason tambayar ta wane irin allura ta mata
Dr yace "Ai yanda kafada bawani magani da za asamu alikitance wanda zai dawota tunani kunriga kuncici yariyar kawai."

*Yafadi haka fal da haushi Shid wani irin makar yacine akan abinda yanacewa yanzu kenan zai rushe masa komai tunda gashi har ya ganar da iyayen sa cewa Fandau matar sace*

Nabil kamar yaro haka yace "wllh ban cuceta ba nide Hadim ce kuma wllh jiran ta haifu nake ta gane kureanta."

Dr da Habiba dan haushi kasa magan sukayi yanzu shikenan Nabil yaci
Bulus kenan ko sallama Dr bai saya yiwa Nabil ya fece


*Gidan Dr*

"yanzu yaci nasara  yara kuma dunzama na Hadim kenan waishi Shiddams dinnan wane irin mutum ne komai nasa cikin ruwan sanyi yake zuwa dubi yanda yake tsara mana zance kamar gaske da irin wanan kalaman ya yaudari yariyarn fa kuma haryanzu ta na mugun sonsa ayanda da karance ta." cewar Habiba

Dr yace "ai dama nace miki shiddams shegene zai iya rusa kowane irin shiri akan abinda yake so,
Yayi kokarin ya fashim tar dasu yanda nasa lefin basai fito ba ko toni kuma na yi  alkawarin insha ALLAH  yarushe min *DAMATA* *DAYA* acikin ukkun amma biyun nima sai na cinasara sai ya karyata kansa da kansa ."

"haba Abban Nol yazaka rike matar aure ka fito da ita kawai ayita da kare wllh iyaye zasu yarda da ita abata yaran da aware karyar da yayi musamman idan bayanan da Dr Hafeez ya maka in Gaskiya ne kaga kowa zai yarda da da yaran tane su zauna suyin zaman auren su me amfani cigaba da rike matar wani kai kasan bazaka iya karawa da Shddams ba wllh."

"Bayanan Dr Gaskiya ne naduba sosa,
amma ai su Ummi basu yarda ba Dr yabari ne sai tazo haifuwa su gani maganan garawa da Shid kuma kowa yana da dama fa sai de inbai iya amfani dashiba zan baki mamakin cikin *DAMATA*."

Fandau kam ba asata makaranta ba amma ta gama wayewa duk inda za akira wayeyiya za asoko da ita yanzu kam ta iya turanci sosai ba abinda Habiba bata koya mata ba dan yanzu haka zaki iya sata sawun matakin yan secondary  dan duk abinda habiba takoya mata dauka take idon ta yabude sosai

Cikin ta yacika wata 9 cif Aunty Habiba ta tafi dauko yara a makaran ta wayan habiban ne ahannun tana dan danne danen ta de sai ta shiga whassapp dinta pc din Hadim ta shiga amma tajima bata hauba pic din Fujjirat ne a dp tarike ball tana dariya tayi kyu

Ta tuce na Nabil  shima Fuj ne saide nashi tana cikin taron jamaa duk yan mata ne kyuwawa wasu farare wasu bakake Fuj tana tsakinyan su sai da ta jawo taga ashe abinda suka sa agaba cake ne ansa happy Birthday to Hajara
2years
Amma me tana shiga  status dinshi ta cikaro da nata pic din wanda tayi a harani akasan photon anrubuda
_yaushe zan ganki matata ido da gangan jikin suna bukatan ki baki yana son turta miki kalman da kika dade kina son ji_

Kifa kanta tayi a hannun kujera kenan Nabil bai manta da ita ba yana son ganinta fa yace da sauri da daga idon ta ta Kalli tafkeken photon dayake manne jikin bango tace nima ina sonka bansan yanda zanyi bane to idan kaganni me zaka gayanin min akwai wani kallma ta yarage baka gayamin ba kokana nufin zaka furtanin karman```SO```ne dan shi nadade ina nema awajen ka

 goge hawayen nata tayi ta shiga  ta  rubutu masa _SLM_ amma sai da yajima yaturo amsan

 _Waalaikumus salam Mamana ys Nol Nol,_

 dama Nol sunan Nabil ne dashi shiyasa Nabil yake cewa Habiban mamana

Rasame zatace tayi dan hannuta sai rawa yaje cande ta daure ta mayar masa da reply

_lfy abu Fuj yasu Fuj ya kawata?_

_yace Fuj de lafiya amma jiya ta cika shekara 2 su Jidda sun mata happy shine suka turomin pic dinta kawar ki kam ban sani ba kunfi kusa_
_yazakace munfi kusa kai da matar_
Cewa yayi
_uummmmm_
Daganan bai sake cewa komai ba

Itama shiru tayi tana so tace yayi mata voice taji muryasa ta tuno ashe wayar matan mutane ne

Jira take yace wani abu amma taji shiru har shigowan yaran da hayani yanzu tayi saurin tayi delete din chet din

Hadim iya wahala tana sha har yanzu a asbitin renon cikin take  tayi kaya kaya dama gatada uban tinbi ya hadu da cikin wata 7 wani irin ciwo mararta yake mata wanda duk doctor da ya auna sai yace matsala ta na cikin ma haifa
Mamar tace ni Hadim nagaji da yanda kowane likita sai yace da matsala acikin mahaifar ki bayan da kalau kike haifuwar ki kode wajen zamu fita."

Hadim dama dukda ciwon da yake damunta tana son ganin Nabil tace "eh mama muje kawai nake ga kamar sun fisu sanin aikinsu yanzu haka bawani matsala sai nasu na rashin kwarewa."

Nabil yayi shiru yana tunanin chat dinsu da Habiba yaji dadin sunan da takirashi dashi wato *Abu Fuj* dan shi Fandau dinsa cekawai take kiransa dawanan sunan ****

Yau Fandau ta tashe da nakuda Habiba takira Dr yana hospital din ta gaya asa nurse kawai yaturo da kayan kinsu yace sugaya masa duk abinda yabiyo baya Fandau taji dadin wanan haifuwar dan sun temaka mata sosai sanda kan d'a yafaso
Awanan karan ma namiji ta haifa mekama dasu maaruf sak yana  duk wani kulawa itada jaririn ta sun samu kunsan de gidan doctor
 Fandau tayi kyu tayi shar da ita dan tasan idan tana bawa Akkaram nono jitake kamar ta kaida shi cikin ta dan so sunan Malam Dauda Dr ya sawa yaron dan  isa shine yace kar akira masa uba dawani suna sai Akkaram ko dawud to de Fandau tace gwara Akkaram din

Fandau tana son yaran har ta kasa ban bance wanda tafiso shida Fujjirat dan ita tana ganin twins kamar ba yaran taba takeji   amma  Fujjirat  bata san iya sonda takewa yarinyar ba kullum pic dinta ne a fukan wayanta
***
Ranan da yakama suna duk da bakowa aka gayawa  ba Fandau tayi makeup tayi kyu
Habiba tana shigo ta fara mata kirari
 "kai kai cankaji wanan hawan  girman fa yayi gimbiya y'aga Zannan barno hakimin Gargar mulki da sarauta bayeku a barno  koda karfin rawani zamu karbo yaran mu kinyi kyu wanan idan Nabil yakanki ko zai ganeki?
Gaki dama da iya kasai ta wllh tun lokacin da nake zuwa gidan ku duk baki ta bamin magan ba nasan ke jinin sarautane ne kinfi sauran yan uwanki iya tsate gida

Murmushi tayi tace "Aunty foundation din kara hanci tasamin wllh duk na canza kama gawani gira data samin a ido Aunty ba kyu fa canza halita  wanan abinda ta samin acikin ido ba abin da zaiyiwa idona ina tsoro."
"eh bawani abu kwaliya nefa kuma ba sallah zakiyi ba Abban Nol yace amiki zai turaro wani wanda ya kware a daukon photo da editing yamiki pic dan yayi amfani dawani *DAMAR* kinga ma kayan ma caccanzawa zakiyi."

Itade dan Dr ne bayanda zatayi amma da wannan kayan canza halittan bada itaba








Wani bature ne yamata photo  wajen kala 10 harda wanda aka mata da English wears fadin kyun da tayi ta adin lokaci ne

Wahegari Habiba tace zata jen duba Hadim dan sun sauka ita da Ummi da Mamar ta asbitin dr suka sauka dan sun dauko Hadim agalabaice

"aunty da Fujjirat akazo?
" eh da ita man kinsan Hadim baza ta iya zama ba Fuj ba shiyasa nake tausayawa Hadim duk ranan da asirin zai tonu dan wllh abin tausayi ce inde za akwace Fuj da bata da lfyn nan fa a asbitin a bed daya suke kwanan ga shima uban ya kwallafa dukkan buri akanta nede Allah yasa Hadim macce zata haifa dan abin yazo muku da sauki amma idan ta haifi Namiji akwai rikici dan naga kema kinfi jida Fuj."

"Aunty ai itace macce nisu zo su hada har Akkaram surike subani Fuj."

Habiba tace" yanzu kenan bazaki iya bar mata ita ba jenan?

Fandau tace" Allah Aunty koda kotu sai na karbi y'ata

Habiba tace "to  mude munanan muna zuba  ido muga wanan rikicin ta inda za aballo
Sai nadawo."
"Aunty kizo da Fujjirat di."

"Anya na isa kuwa zan duba baga."

"Yawwa Aunty dan ALLAH kiyin da baran daukota."

"Bakida kunya Aunty kirki agabana kike nuna so ga yarki ta fari sai kace ba kanuri ba."
Da sauri ta rufe fuskan ta da hannunta



*Gidan Dr*

"yanzu yaci nasara  yara kuma dunzama na Hadim kenan waishi Shiddams dinnan wane irin mutum ne komai nasa cikin ruwan sanyi yake zuwa dubi yanda yake tsara mana zance kamar gaske da irin wanan kalaman ya yaudari yariyarn fa kuma haryanzu ta na mugun sonsa ayanda da karance ta." cewar Habiba

Dr yace "ai dama nace miki shiddams shegene zai iya rusa kowane irin shiri akan abinda yake so,
Yayi kokarin ya fashim tar dasu yanda nasa lefin basai fito ba ko toni kuma na yi  alkawarin insha ALLAH  yarushe min *DAMATA* *DAYA* acikin ukkun amma biyun nima sai na cinasara sai ya karyata kansa da kansa ."

"haba Abban Nol yazaka rike matar aure ka fito da ita kawai ayita da kare wllh iyaye zasu yarda da ita abata yaran da aware karyar da yayi musamman idan bayanan da Dr Hafeez ya maka in Gaskiya ne kaga kowa zai yarda da da yaran tane su zauna suyin zaman auren su me amfani cigaba da rike matar wani kai kasan bazaka iya karawa da Shddams ba wllh."

"Bayanan Dr Gaskiya ne naduba sosa,
amma ai su Ummi basu yarda ba Dr yabari ne sai tazo haifuwa su gani maganan garawa da Shid kuma kowa yana da dama fa sai de inbai iya amfani dashiba zan baki mamakin cikin *DAMATA*."

Fandau kam ba asata makaranta ba amma ta gama wayewa duk inda za akira wayeyiya za asoko da ita yanzu kam ta iya turanci sosai ba abinda Habiba bata koya mata ba dan yanzu haka zaki iya sata sawun matakin yan secondary  dan duk abinda habiba takoya mata dauka take idon ta yabude sosai

Cikin ta yacika wata 9 cif Aunty Habiba ta tafi dauko yara a makaran ta wayan habiban ne ahannun tana dan danne danen ta de sai ta shiga whassapp dinta pc din Hadim ta shiga amma tajima bata hauba pic din Fujjirat ne a dp tarike ball tana dariya tayi kyu

Ta tuce na Nabil  shima Fuj ne saide nashi tana cikin taron jamaa duk yan mata ne kyuwawa wasu farare wasu bakake Fuj tana tsakinyan su sai da ta jawo taga ashe abinda suka sa agaba cake ne ansa happy Birthday to Hajara
2years
Amma me tana shiga  status dinshi ta cikaro da nata pic din wanda tayi a harani akasan photon anrubuda
_yaushe zan ganki matata ido da gangan jikin suna bukatan ki baki yana son turta miki kalman da kika dade kina son ji_

Kifa kanta tayi a hannun kujera kenan Nabil bai manta da ita ba yana son ganinta fa yace da sauri da daga idon ta ta Kalli tafkeken photon dayake manne jikin bango tace nima ina sonka bansan yanda zanyi bane to idan kaganni me zaka gayanin min akwai wani kallma ta yarage baka gayamin ba kokana nufin zaka furtanin karman```SO```ne dan shi nadade ina nema awajen ka

 goge hawayen nata tayi ta shiga  ta  rubutu masa _SLM_ amma sai da yajima yaturo amsan

 _Waalaikumus salam Mamana ys Nol Nol,_

 dama Nol sunan Nabil ne dashi shiyasa Nabil yake cewa Habiban mamana

Rasame zatace tayi dan hannuta sai rawa yaje cande ta daure ta mayar masa da reply

_lfy abu Fuj yasu Fuj ya kawata?_

_yace Fuj de lafiya amma jiya ta cika shekara 2 su Jidda sun mata happy shine suka turomin pic dinta kawar ki kam ban sani ba kunfi kusa_
_yazakace munfi kusa kai da matar_
Cewa yayi
_uummmmm_
Daganan bai sake cewa komai ba

Itama shiru tayi tana so tace yayi mata voice taji muryasa ta tuno ashe wayar matan mutane ne

Jira take yace wani abu amma taji shiru har shigowan yaran da hayani yanzu tayi saurin tayi delete din chet din

Hadim iya wahala tana sha har yanzu a asbitin renon cikin take  tayi kaya kaya dama gatada uban tinbi ya hadu da cikin wata 7 wani irin ciwo mararta yake mata wanda duk doctor da ya auna sai yace matsala ta na cikin ma haifa
Mamar tace ni Hadim nagaji da yanda kowane likita sai yace da matsala acikin mahaifar ki bayan da kalau kike haifuwar ki kode wajen zamu fita."

Hadim dama dukda ciwon da yake damunta tana son ganin Nabil tace "eh mama muje kawai nake ga kamar sun fisu sanin aikinsu yanzu haka bawani matsala sai nasu na rashin kwarewa."

Nabil yayi shiru yana tunanin chat dinsu da Habiba yaji dadin sunan da takirashi dashi wato *Abu Fuj* dan shi Fandau dinsa cekawai take kiransa dawanan sunan ****

Yau Fandau ta tashe da nakuda Habiba takira Dr yana hospital din ta gaya asa nurse kawai yaturo da kayan kinsu yace sugaya masa duk abinda yabiyo baya Fandau taji dadin wanan haifuwar dan sun temaka mata sosai sanda kan d'a yafaso
Awanan karan ma namiji ta haifa mekama dasu maaruf sak yana  duk wani kulawa itada jaririn ta sun samu kunsan de gidan doctor
 Fandau tayi kyu tayi shar da ita dan tasan idan tana bawa Akkaram nono jitake kamar ta kaida shi cikin ta dan so sunan Malam Dauda Dr ya sawa yaron dan  isa shine yace kar akira masa uba dawani suna sai Akkaram ko dawud to de Fandau tace gwara Akkaram din

Fandau tana son yaran har ta kasa ban bance wanda tafiso shida Fujjirat dan ita tana ganin twins kamar ba yaran taba takeji   amma  Fujjirat  bata san iya sonda takewa yarinyar ba kullum pic dinta ne a fukan wayanta
***
Ranan da yakama suna duk da bakowa aka gayawa  ba Fandau tayi makeup tayi kyu
Habiba tana shigo ta fara mata kirari
 "kai kai cankaji wanan hawan  girman fa yayi gimbiya y'aga Zannan barno hakimin Gargar mulki da sarauta bayeku a barno  koda karfin rawani zamu karbo yaran mu kinyi kyu wanan idan Nabil yakanki ko zai ganeki?
Gaki dama da iya kasai ta wllh tun lokacin da nake zuwa gidan ku duk baki ta bamin magan ba nasan ke jinin sarautane ne kinfi sauran yan uwanki iya tsate gida

Murmushi tayi tace "Aunty foundation din kara hanci tasamin wllh duk na canza kama gawani gira data samin a ido Aunty ba kyu fa canza halita  wanan abinda ta samin acikin ido ba abin da zaiyiwa idona ina tsoro."
"eh bawani abu kwaliya nefa kuma ba sallah zakiyi ba Abban Nol yace amiki zai turaro wani wanda ya kware a daukon photo da editing yamiki pic dan yayi amfani dawani *DAMAR* kinga ma kayan ma caccanzawa zakiyi."

Itade dan Dr ne bayanda zatayi amma da wannan kayan canza halittan bada itaba

Wani bature ne yamata photo  wajen kala 10 harda wanda aka mata da English wears fadin kyun da tayi ta adin lokaci ne

Wahegari Habiba tace zata jen duba Hadim dan sun sauka ita da Ummi da Mamar ta asbitin dr suka sauka dan sun dauko Hadim agalabaice

"aunty da Fujjirat akazo?
" eh da ita man kinsan Hadim baza ta iya zama ba Fuj ba shiyasa nake tausayawa Hadim duk ranan da asirin zai tonu dan wllh abin tausayi ce inde za akwace Fuj da bata da lfyn nan fa a asbitin a bed daya suke kwanan ga shima uban ya kwallafa dukkan buri akanta nede Allah yasa Hadim macce zata haifa dan abin yazo muku da sauki amma idan ta haifi Namiji akwai rikici dan naga kema kinfi jida Fuj."

"Aunty ai itace macce nisu zo su hada har Akkaram surike subani Fuj."

Habiba tace" yanzu kenan bazaki iya bar mata ita ba jenan?

Fandau tace" Allah Aunty koda kotu sai na karbi y'ata

Habiba tace "to  mude munanan muna zuba  ido muga wanan rikicin ta inda za aballo
Sai nadawo."
"Aunty kizo da Fujjirat di."

"Anya na isa kuwa zan duba baga."

"Yawwa Aunty dan ALLAH kiyin da baran daukota."

"Bakida kunya Aunty kirki agabana kike nuna so ga yarki ta fari sai kace ba kanuri ba."
Da sauri ta rufe fuskan ta da hannunta


Nabil yana zaune yana dan danne danne sa a waya yashiga status kawai sai yaga dr MD yana wasa dawayin jariri yayi saurin budewa aiko yanayin searching yaga maaruf ne dariya yayi yace kenan ranan da aka haifesu yayi dan yasan rabon doctor dayaran tunranan haifuwan su
amma kuma mamakin sa saiyaga a parlour Dr ne da sauri yarubuta _*pls Dr send it 4*_

Dariya Dr yayi a zuciyar yace cewa anzo wajen Dan yajima yana daura video amma dayake Nabil bai damu dawani hawa media ba bai gani ba musam man yanzu da ya fara fita wasa dariya Dr yayi yace *DAMATA DAYA*
amma sai ya masa reply da
_Yatura masa anki din nasamu d'a kowa yana min barka kai saiyawu_."

_Sorry my friend wlh banida video yaran suna jarirai Maaruf ne ko dan suna jarirai Billah bai kai haka girmaba_."

_Dr "yace bangane ba kaima kana son kacemin Akkaram yana kama dasu twins dinka ne_?

"Muktar bangane ba _kana son cemin ba Maaruf bane wanan_?

_Sosai mako wanan d'anane  ashede da gaskene suna kama _da su Maaruf dan ni kasan rabona dasu tun suna jarirai sai dai pic din birthdays _dinsu dan haka bazan gane wani kaman su ba sai dai mutane suke ta fadan kaman ashe kai ma kagani to namusu friend sunan sa dauda dawud muna nace masa Akkaram_

Aiko sai gashi Nabil yakira
"dan ALLAH mehaka nufi please  ba Maaruf bane?

Dr yace"Nace bashi bane amma kaduba da kyu kuwa?

"Dr bana son irin wanan zolayan?

"Wllh Shiddams ka yarda wanan ba Maaruf bane amma nayi murna da d'a yayi kama dasu kasan nayi  sammanin nin zaka sa sunana tunda 2 nida Bilal sai ALLAH baiyin ba inason yaran inajin shiyasa na haifi mai kamada su...

"Dakata Dr  Nabil ya katsesa
"yana ina yanzu yaron?

"yana gidana mana nace maka d'a ne ai ko."
"yazu haka idan nazo zan ganshi? "sosai ma yanzu haka gashinan Acinya na."
Nabil kashe wayan yayi yatashi da sauri yafita ko drive bai saurara ba balle security haka ya fada mota yaja

Nabil daukan dan yayi yana bin ko ina na raron da kallon bashi da ban banci da jinin sa hatta daidai ta faracen yaron nasu Maaruf ne
yadaga kai ya Kalli Dr
yace " ina iyayen sa?
"ni nine uban sa nace maka."
Nabil yace
"iyayen sa na asali nake nufi bawai kai ba."

"ai sai kayi agunwa kaga yaro d'a nane nacikina."

"yaushe Habiban tayi koyon ciki har ta haifu ban sani ba?

"Dr yace kana mamaki ne?
Nabil yace "kai yafi karfin mamaki ba."

Dr yace "amma kam bai kamata kayi mamaki ba dan kuma hakan yafaru akanku saide muganku da d'a koda goyon ciki kobabu."

Nabil yace "amma ai mukuna ganin muda ciki ko?

"kai Shid *walla tazzazasu* amma kai aboki nane da bazan iya boye maka komai ba zan gaya maka Gaskiya nasan kai mai rufanin asirine kasan Habitee ta ce maza ta kara haifuwa ba nikuma naga yara ukku sun min kadan dan haka mukayi yar jejeniya da ita nayi auren boye da wata yariyar ta haifa mana koda yara ukku ne mukara akan su Haris kaga idan ta gama sai musa mata alluran mantau yanda goda ta ganmu awani wajen bazata gane muba
bawan da yadani saikai dan bazan iya boye maba yasa nagaya maka
gashi yariya ta iya haifuwa dan ta haifa min mekama da abokina."

Nabil har yawu sai da yazubo abakin sa tsabar sakewan da jikin sa yayi jin jikin sa yayi kamar ba nasa ba dan mutuwan zaune dayayi
dan da yake hannun sa bai sanda da yasubuce ba.........



*Sorry masoya dan bashida yawa sonku da kaunan ku yasa na kawo muku wanan dinma wllh bana dindadi*


*Amma yakukaga page na gaba sai kasance dr yafara amsani da DAMARSA zaici nasa ra koyayi*

*Kuyi kuna tunawa da HAJIYA HADIM de*


*Nagode masoya muna tare da jikar ALHAJI MUSTAPAH YIR JATTKO*
[3/12, 8:50 AM] Hauwa: [2/8, 6:22 PM] BATUL ADAM JATTKO: *DAMATA*



               *Na*




*BATUL ADAM JATTKO*



(editing mzz daddy )



*41*


*d*asauri Dr ya tare Akkaram
Yace"Shid lafiya zaka jefarmin yaro mekake kallo haka?

Nabil jamowa yayi katsa bakin sa narawa shikan baisan irin kalman da yake fitowa a bakin sa ba yace"dr mekake nufi dama anayin irin wanan auren ne aduniya?

Dr yace "Sosai makuwa kai ma ai kusan irin sa kayi dande Hadim ta ma katsalandan ne."

 Nabil yace "Bangane ba Dr ni aiban aure ta danufin ta haifamin yara nasaketa ba na aureta ne da niyar temakon ta kawai. "

Dr yace "naka nufin kenan ni nasan halin matata tanada kishi bazata iya zama da kishiya ba musamman idan friends din suka san tana da kishiya aisai su renata  shiyasa idan ta gama  mana aikin zamu sallameta musamman yanda naga kawar ta nakasa yar mutane kaga idan gemun dan uwanka yakama da wuta ance kayayya fawa naka ruwa."

Cikin tashin hankali Nabil yace "doctor bawannan ba komai naka yayi kama da nawa aharkan auran boyen da mukayi inaga hakan a musulumci babban zunubine shiyasa ALLAH ya jarrabemu."

Dr yace" sosai babban zunubi neman musamman ma idan Budurwace dan da farko maba ita yaka mata kafara yiwa magana ba magaban ta yaka mataka tunkara dan su akabawa zabin mijin fari kaga mun tsallace wanan dokan kaga gakuma na alhakin mun jefa iyayin ta cikin damuwa wanda bamuyin aikin da hadisin da akace kasowa dan uwan ka abinda kasowa kanka dan na san  bazakaso ayima ka haka ba akan Fujjirat ko?

Rudewa Nabil yasakeyi sosai cikin in ina yace "Muktar dena fada zannemi yafiyar Allah bazan iya jurewa ba idan hakan ta faru zan iya fadawa halinda yafi na yanzu bazai faru akan Fuj ba."

Dr yace ."wane yafiyar Allah ai anan Allah baka masa lefiba tunda ba zina kayi da ita ba aurene amma ba bisa tsari ba
Lefi kuma iyayenta kayiwa musamman ma idan na amanane."

Ai Nabil kara gigicewa yayi yace "na amanane mana nawakam nashiga ukku meyasa nabi shawara Hadim da ban fada cikin wanan hali ba."

Dr yace shawara Hadim kuma?

"Eh wllh bakin su daya da Habiba dan komai naka irin nawane."

Dr yace.
"Nide nafi shawaran Habittes amma aikai kace a saudia kuka haduda Fandau  aikai ba amana kaciba illah temoko kaman yanda kafada  tome yasa kace kaci amana idan na tattara bayanan ka yana bani kamar akwai  wani abu da kaboye idan baka fito da shiba baza musamo kan abinba."

"Sosai dr akai abinda na boye mana fadan saba abin fahari bane,
 amma ni duk bawanan damuwan bane damuwa ta jaraban da ALLAH yanuna mata akan auren boyen yazamuyin da wanan babban jaraban?

 "bangane jarafta ba"
 inji dr
Nabil yace "yanzu kana ganin danka dayayi kamadani sak gamu abokai zargi ba zai shiga zukatan mutane ba?
Dr yace wane irin zargi kuma?

"Meyasa dan ka yayi kama dani bayan kai da matar ka duk bakake ne kuma kuka samu farin d'a?
Dr yace" ana haka ai bakin tukunya mai fidda farin tuwo."

Cikin karaji Nabil yace "Dr ka dauki abin dawasa ko to ba abin wasa bane dan ko makaho yashafa yaron nan zaice da nane
Dan haka duniya zata zargeni da inacin amanan ka bawanda zai yarda."

Dariya Dr yayi sosai acikin ransa yace anzo wajen amma danya ruda Nabil afili kuma idon yazaro

" yace hakane fa yanzu yazamuyi wllh bansan hakan babban matsala bane saiyanzu shiru sukayin Nabil wani gumine ya yanko masa kamar ba sanyi ake a London ba
Shima Dr nuna jimanin sa yayi afili

Nabil yace "ina uwar yaron?
Dr yadan daga murya yace Habitee...

Nabil yace "ba itaba uwar gasken nake nufi."

Dr yace okky ai tana wancen dakin mun jonamata shocking mun sa security mun setting yanda bawanda zai shiga sai nida Habite."

Nabil abin yadena bashi mamaki dan yanzu ya tabbarawa kansa shida Dr suyin kuskuren bin shawaran mata ne Allah yamusu wanan jarabawan dan yasan bakin su daya da Hadim kawai amma bata gaya masa sun hada baki da Habiba ba ita ma Habiban da alamum bata gayawa Dr ba

Nabil yace "kacire shocking da security din inason nagan ta."

Dr yace no problem amma ba yau ba dan tana bacci bata jin dadi namata alluran bacci."

Kafin Nabil yace wani abu wayansa yasoma ringing Ummi ce yadauka yana seta muryar shi yan da zai mata magana yaji tace

 "Nabil kai wane irin mutum ne bance lalle lalle kazo  asbitin nanba idan yariyar nan ta mutu a dalilin bacin ranka wllh bazan yafe makaba kome tayi katuna cikin ka ajikin ta cikin nan yana bata mutukar wahala amma ka kasa zuwa dubata sai fanan aiken abaka Fujjirat  to yanzu gashi jikin ya matsa harda suma nabaka minti 10 naganka dan haka kashe wayan yayi yameke  yace"wai Dr meyake damun Hadim ne?

Shiru Dr yayi can yanunfasa yace "ayanda Dr tan ta yake gayanin akwai matsala sosai saide muyi fatan Allah ya sauwake mata."

"Yanzu ummi tace wai har suma tayi bari namekawa habibi yaron mutafi ya haura sama Nabil sai binyaron da kallo yake

Nabil zaune abakin gadon da Hadim take kwance ya hade rai ganin yanda maman Hadim take son yimasa kwarafi amma ganin ba fuska yasayi shiru
Itako Hadim jawo hannun sa tasake yi ta kenkeme
" habibi ina kashiga kabair ne cikin nan Wllh yana bani wahala wani irin ciwo marata takeyi amma kullum bana ganin ka ina neman ka su Ummi sai suce kakoma idan nace subani kai awaya sai suce wayan arufe dan ALLAH kasa acire cikin nan Wllh zai kaini lahira ."

Nabil yace "duk abinda yake damun ki kisani alhakin
*FANDAU*
[2/8, 7:21 PM] BATUL ADAM JATTKO: NE

" HADIM."  "tace *FANDAU*  Nabil? kana nufin har yanzu baka cire wanan yariyar acekin babin rayuwan muba ba kaman ta daba mukayi dakai ba,
Munyi da kai daga ranan da muka rabu da ita mundena tuno ta acikin babin rayuwan mu,
har kana tunoda ita a rayuwan ka bayan ba haka mukayi da kai ba tun farko dole kacireta aranka domin yan......
"keeeeee dakata kiji idan ina mafatki kifarka naga alama ke wawuyace dakikiya da kika kasa gane meye so acikin ido da gan ganjiki  to bari infito miki dashi afili inayi wa Fateema sonda ban ta bazaton wani dan ADAM zaiyiwa dan uwansa ba da kike cewa nacireta araina saide idan Zaiyuwu acire  zuciyata adasa wani saide idan gan gan jikina za araba a min filla filla dan ni alluran mantau yayi kanda yasa na manta da Fatee na inko  hakan fa zai samu ba to cire ta araina abune da bazai ta ba yuwuwa ba Hadim kinyin kuskuren hada zaciyata da wanda tadace da shi dan ban gane munyi mutukar dacewa da Fandau  ba saida narasa ta,
 kinyi kokarin hadamu kuma nagode amma hakan bazai sa na kasa daukan fansan salwan tarmin da mata ba zan bar...... 
Ganin yanda Hadim take fitar da wani irin nunfashi ne yasa Dr  yayi saurin toshewa Nabil baki

Maman Hadim tace "Mutari barshi ya karasa ta ya futa barshi nace."

Fusge bakin sa Nabil yayi yana son cewa Maman Hadim wani abun

 Ummi tace "Muktar fitar dashi kazo kaduba Hadim din."
Torashe waje dr yayi da sauri yazo ya sawa Hadim roban nunfashi yace "Ummi Nabil bashida hankali nace kudena kira mana shi wajen aikin mu tunda bashi zai bata lafiya ba yana bata mana aikin mu."

Daga Ummi har Mama Fatime kuka suke dan bawanda zai ga Hadim bai mata kuka ba


Dr Muktar ne zaune a England acikin  parlour BilAL babban abokin Nabil  ya kashe komai na rayuwan Fandau ya gaya masa
Ya daura da cewa "
B G abinda yasa na gaya maka komai dan inason mu hada karfi da karfi da kai wajen cikan *DAMATA* nabiyu dole sai kaine zaka iya kai ne daidai karawan Nabil wanda bai isa yanuna maka komai ba ni yafi karfina bazan taba cin nasaran sa ba."

"mene ne bukatan naka duk temakon da kake nema awajenan zanyi inde   za afidda yariyar nan acikin kunci dan an zalinceta,
 kuma Shiddams yayi mugun bani mamaki ko zai boyewa kowa Gaskiya bai kamata ya boyemin ba bamusaba boyewa junan mu komai ba tunmuna yara atuna nina ko kisa zamuyi mu binne dashi."

Dr yace "inason kanuna masa pic din yariyar da sunan zaka aureta,
Kaga daganan zai gigice  yace itace wacce yake nema matar sace kaga zakace ita wanan tayi haifuwa Har 3 yaranta 4 kai ko matar ka ko haifuwa batayiba kaga dole yafadi Gaskiya dan kasan sa shegene yadasa sonsa sosai azuciyar yariyar yanzu ana fitowa da ita inde bai tona asirin da kansa ba to zai yaudari yariyar bazata fada ba dan nafuskan ci hakan yake sonyin dan yanajin kunyar tonon asiri kaga nafiso rigima yashiga tsakanin ku sosai yanda zai tona asirin sa agaban manya dakansa."

"ok na fashimceka ina photon yariyar?

"natura mata inbox."
BilAL yace "amma ina tausayin iyayen yariyar musamman uwar ta yaka mata tasani dan tasamu nusuwa."

Dr yace" yes zanje Nigeria  jibin nan dan banason Nabil yadame ni dan jiyama kiran Ummi ne ya hana nacemin sai yaga uwar yaron nafison idan natafi tukun kufara karawa dashi gashi kuma Hadim cikin satinnan zata haifu bana son ta haifu ahannu na dan idan Maganan Fandau ya baiyana zasu iyace wada gaiya nayi dan haka gwara ayi bani ciki kasan mata dan inaganin take taken uwar ta."

BilAL yace "aiki za amata meyasa?

"wllh matsala ne babban a mahaifiyar ta damani Habiba tana yawan gayamin Hadim tanada yawan cushe cushen maganin mata batare da ka ida bato wanan ne yassada mata cancer a bakin mahaifiyar ta duk da bai shiga ciki ba yanzu haka yaron cikin ba shida koshin lafiya tuda a mani da zai shiga ya shafi cutan shiyasa ta ke yawan ciwon mara wanda wata kila idan ancira dan saide ayanke makaifar  dan zai iya bin cikin ya kasheta
Kuma bayan haka bata da kugunda za ta iya haifuwa da kanta saide acira nande yamasa bayanin da yagani da kuma wanda Dr Hafeez yamasa."

Jinjina kai BilAL yayi yace "lalle sakaiya yanzu baya zuwa lahira."

"Yawwa kaga idan naje Nigeria zan bari sai bayan Hadim ta haifu na gayawa ita Mama Aisa kokai dan ta kwantar da hankalin ta kaima kabar aikin ka sai Hadim ta haifu ka fara  dan abin ya tafi daidai."

BilAL yace "ok amma kafinnan gawata shawara mezai hana kafinnan kabawa ita Fandau din private no na shi Nabil din tafara chatting dashi tace tana son sa nasan bazai yarda ba daga baya   idan yaki amin cewa kuma ta  cemasa ita dama shaharan sa awasan kwallo take so tunda yakita ita yanzu tasamu wanda takeso kuma dan kwallo kamar sa sai ta tura masa pic dina tace gashinan kaga zai zo yasame ni idan yazo kuma nima sai na gaskanta masa nace ga pic dinta gaka hakan zanfi hawa da plans dinmu ko bawai ni na baiyana masa itaba."

Tafa masa Dr yayi yace "well-done shiyasa akace sarkin yawa yafi sarkin karfi."

Fandau zaune agaban Dr yace"kinji de abinda nagaya miki idan soyayar ta rufe miki ido kika nuna kekece kin rusa jindadin ki yancin da muke son samo miki bazai taba samuwa ba kiyin komai yanda nagaya miki."

Tace" ALLAH yaya zanyi yanda kace."

Yace "Gud jeki fara tundaga yanzu."

Bayan ta gama komai na kwanciyar ta har Akkaram yayi bacci ta hawo wayanta
Whassapp ta shiga taci sa ako yana online

Shiko Nabil alokacin tunanin Fandau dinshine ya dameshi yanzu ma chat yake da Sani akanta yana masa bayanin yanda  binciken yake bawani cigaba
yaga message ji yashiko da bakon number  daya ke wayan private ne yasan na jikin sane amma duk da haka yaki budewa dan yasa bazai wuce kannen sa ba dan ba no din kowa yayi saving ba
Ita ko Fandau ganin shiru yasa ta dinga damunsa da call

Gani yanda aka damoshi da call dinne yayi tsaki yabude message din dan inda a general wayan sane baya kula bakon number

_*amincin ALLAH ya tabbata agakeka ka shugaman yan wasan Duniya haske kashe fitula abu FUJ*_

Yana gama karantawa cikin mamaki yace towaye ai kannen sa basa masa irin wanan sallama abokan sa kuma zai iya irga iya wanda yabawa wanan numbar amma sai yasamu kansa da mayar da *Ripley*
[2/9, 9:37 AM] BATUL ADAM JATTKO: _*wake makana dan bani da contact din*_

Dadi Fandau taji dan doctor yace sai sa a ya amma

_*dama nasan baka da contact dani amma ne ina da kai kuma ni me bibiyar rayuwan kace Shddams nasha yimaka magana a kowacece kafa ta media amma ba Ripley sai da nasha wahala kafun nasamu nasaran samun wanan private din naka dan ance kafi yin Ripley idan akama magana dashi*_

Tsaki yayi kamar bazaiyi Ripley ba kumade yayi

_*ba abane amsa bafa waje magana*_

_*sorry abu FUJJI sunana Fateema maiyarka me bibiyar rayuwan ka dan ALLAH kadauki al amarina da girma dan saboda kai nabar katsata da iyayena nazonan london*_

Sai asannan Nabil yaduba number yaka ni na England ne

Amma jin sunan Fatima yaji bazai iya sharewa ba

_*me kikeso awajena  harki ke bibiyar rayuwata*_

_*yawwa Abu Fujjirat tun ina yar yariyar nakamu da sonka yan gidan mu sunamin dariya wai ina zangan ka balle kasone naki kowa akan ka bana sauraron kowa akan ka na bijirewa iyayena akanka nakasa karatu akanka kaga yanzu haka da sunan karatu nasa aka kawoni kasan amma ni nasan bakaratu nazoyin ba naso neman sonkane dan ALLAH kayiwa Fateen adalce ta samu wajen koda kadanne amatsayi zuciyar ka in kuma hakan bazai samuba to koda amatsayin yar aikin gidan kane nide indinga ganinka in bazan samu so na aureba kamar yanda akecewa kafi karfina*_

Dan kari wani asher ya maka yace yaushe mata suka fara renani har zasu kawonin wani kalman banza amma da yatuna mesunan Fateema ce  mace mafi girma agareshi bayan Ummi sa ba abinda yake so arayuwan sa sama da Fatin sa da Fujjirat dinsa dan haka yamarar mata Ripley

_*nagode da SOYYAYAR ki bazan miki rashin mutumci ba saboda darajan sunanki aguna saide nabaki hakuri kiyi kokarin cire sona azuciyar ki dan zociyar Nabil a rufe yake*_

Itama ta mai damasa da
_*kaji tausayina kaduba raunina kaduba  al amarina da girma kodan alfarman sunan nawa ko wataran zansamu kasone duk da ban san wane irin daraja Kabawa me sunan ba nagode da yaza medaraja awajen ka*_

_*Fateema kenan zaki batawa kan ki lokacine nagayaki ~zuciyata~ arube yake*_

_*nede hakan ma nagode kayarda muna gaisawa*_

Yace
_*no problem*_

Ita ma tatura masa _*gud bye*_

Saida yagama yafara tunanin meyayi kenan harshine yau ya saurari wata macce har tajashida fira haka yayi mamakin kansa daganan yakoma kan aikin gabansa da Sani

Itako tana gamawa ta fada tunani to Wacece Fateeman tasa tasan de ba ita bace to wacece ko kanwar rasa ce tunda matar sa ai sunanta Halima

Nabil yakira doc yace "doctor gani gidan ka amma ance bakanan kayi tafiya."

"eh gani a kasata...

"what!! Nigeria
"doctor yace kayi kakuri ban sanar da kai ba anne meni ne da gaggawa shiyasa."

"Amma doctor kana sane da muna cikin wanan matsalan zaka tsalake kayin tafiya."

"Sorry Shid nifa bansan yanda sanyi da wanan matsala bane abin yana bani mamaki yaza ayi d'ana yayi kama dakai sak ni kaina badan nasan yariyar arufe take adaki kuma da security ba da bazan yarda da kai ba."

"to ai kaji matsala bai kamata katafi muna cikin wanan matsala ba."

Dr yace "tome mafita anaka bangaren."

Nabil yace "inaso naga yariyar kaga idan tayi yanayi damu farace kaga yaro uwar sa yabiyo kaga yazama dole ka baiyanata kowa yasani dan adena zargina."

"yazauke ajiyan zuciya alamun da damuwa amma  aransa dariya yake sosai yace "Wllh baka kirin take kuma mummuna ai Habiba ba hauka take ba zata hadani da mekyu ta kwaceni  bakace."

"Innalillashi wainnah illaishirajununa ALLAH humma gafuni!
Yace "sai kazo mayi abu daya ya kashe wayan
Cikin jibami indan Kinga Nabil sai kin tausaya basa ga neman Fatima gakuma wanan matsala da yatunkarosa

                    *Yau*
Hadim ta tashe da labour sai ihu take mamar tana toshe mata baki dan acewar ta bawani Dr da zasu kira da kanta zata haifu dan ita tunda suka fara maganan aiki tace inta fara nakuda bazata jeta kaya musu ba suna yawan zagayota dan haka ma ta sakace kofan ta ajiye Ummi akofan idan sunzo tace bacci take  tunda sun tanka sai sun tsagamin y'a ba zasu san ma tana nakuda ba sai ta haifu shegu mayu."

 aiko Ummi ta  zauna duk da ba son ranta ba taso Hadim ta samu kulawan likita tunda de a asbitin take dande tana tsoron yayarta ta ne

Tun Hadim tana iya jure ciwon ta ta galabaita cin dan take yazo mata cinyar ta ta dafe jiyar tace mama dan yazomin ciyata kamar ta cinya zai fito nakeji Mama kiji tausayina kikira min doctor zan mutu aiko Ummi tana ganin cinyar ta ganshi akun bure sunttom nashiga ukku  mezangani ni Fatime dan yadawo cinya na shiga ukku  Hajara kizo kiga ikon Allah."
 da gudu Ummi ta shigo aiko ita ma dora hannu tayi aka tafara iho da gudu nurse suka shigo Hadim kam ba fakin magana juya kai kawai ta ke danjin kamar ana sa wuka ana yanke mata naman cinyarta take ji bakinta abode koda man rufeshi bata samu ba nurse duna ganin abinda yake faruwa ko daman fita basu samu ba da sauri dayan ta danna kararawan doctor nan da dan doctor yazo yana zuwa a tsorace yace  " oh my God!!" da kansa yada ga Hadim nurse suka temaka masa suka daura Hadim da tariga ta sume suka fita da kita
da kyar akasamu nasaran daidai ta dan akacireshi  amma baizo da rai ba

Nabil zaune gaban likitan doc ya fara masa bayani kamar haka

"Sir matsala matar ka babban ne shine yasa muka riketa a hannun mu dan idan  ta fara nakuda tana farawa mu cere mata kuma kullum ina jadda da musu idan tace tana jiwon labour kar abari ta kara ko sakan daya dan idan ba ayi gaggawan cirewa ba daga ita har baby cikin suna cikin matsala gashi ansamu akacin haka ta samu matsala fiye da ma tunanin mu,
Saboda idan akabari yaron yabar mahaifiyar to zai gamu da cita to yabar mahaifiyar yafito file dagin mahaifar anisa yake da yafito kuma bashida kofan fitowa dan kugun ta bazai bude ba shine dalilin da yasa yaron yabi hanyan cinyar ta dan yana neman hanyan fitane  ga shigan sa mahaifiyar  idan ba ayanke ma zai iya baza mata cutar cancer acikin ta dole muka yanke shi amma fa dauk wanan ba shine damuwar ba

*BABBAN DAMUWAN* shine cinyar ta dayaron yabi dole sai anyi aiki ahan sa inba baka ba zai kamu da cutar gaba daya har yakai ga yankewa dan haka zamu mata aiki mucire iya naman da kwayar cutar  ta taba."

Bayan anyi akida kwana 3 tukun Hadim ta farfado Mamar Hadim tayi nada banda kuka ba abinda take yanzu shikenan ancire mahaifiyar kuma kafan Hadim yana cikin hatsari da ta sani da tabari an cire tunda cikin yashiga watan haifuwa sukace za acire amma tasamu Dr Muktar tace bata yarda ba abari kwana kinsa yacika haka Dr yada katar da aikin akan abari sai taji nakuda yanzu gashi yanda ta kasance

Nabil azaune abakin gadon Hadim bayan ta farfado kafanta nade da bandage
Cikin kuka tace, "Nabil da gaskene dan da na haifa ya mutu?
 duk yanda Nabil yake jin haushinta da kuma alwashin da yadanka na idan ta haifu aranan a. Furzin zata kwana yarushe dan wani mugun tausayin ta dayakeji
Yace "yamutu Hadim danki mekama dasu  Maaf sak ya mutu dalilin sakaiya Hadim mun tafka kuskure  kituna rananda yariyar nan zata haifu kika rufe kofa kikace bazan kai ta hospital ba ko?
Togashi da Allah yaso saka mata ke akan godon asbitin kike amma uwar ta haife ita ta hana akira miki doctor har kika gamu da matsalan da bakaramin sa a kikaci bada ba ayanke miki kafa ba dan koyanzu doctor yace ba zaki iya dakawa yanda kike daba dan har kashin ki ankankare ancire mahaifiyar ki saide kiyi fadan ALLAH yabaki lafiya kinemi duk inda yariyar  nan take kinemi yafiyar ta."

"Nabil yanzu ka nanufin anciremin *mahaifa*
[2/9, 10:11 AM] BATUL ADAM JATTKO: Kuma *kafata*bazan iya taka shi kamar da ba?

Yace" Hadim naki da sauki ma nima bansan ta ina zai zomin bansan tawane hanya Allah zai cire hakin yariyar nan ajikina ba tsorona kar ALLAH ya jarrabeni ta hanyan Fujjirat ni idan ni abin zai samu komai ma yasamen amma bazan iya jure na Fujjirat ba Hadim
Yanzu haka ina cikin tashin hanka da ALLAH ne kadai sheda na dan gidan abokina yayi mutukar kama dani ban san yazanyi da wannan kaddaran ba Hadim kincuceni
 kin cuceni kema kincu ci kanki duk su kuka suka fara kamar za su shide
Hadim tace yanzu shikenan anmatar ni tsohuwar dole mazanyi period adan banida mahaifa ba inda jinin zai taru ajikin ba haifa Awai wani jijiya da yake mada ni ima ka mata narasa Nabil nawa nake zan rasa wadan nan abubuwan da kake cewa naje nanemi yafiyar yariyar na yanzu naji na tsane ta ma yanzu naji inason kara batar da itama dan yara su tabbata nawa dan nasan yanzu dasu kadai na tsira."

 tafara wani irin kuka na taba zuciya
Ido yazuba mata yarasa abin cewa ma
Can yace "abinyi....


*To masoyan Hadim sorry fa sakaiya yanzu baya zuwa lahira banyi dan bana donta ba saide ina son nuna nuku illar cutarwa musamman awanan zamanin ya Hadim zatayi da kafan zata taka kamar da ko zata zama gurguwa tayi nadama? kamar yanda Nabil yayine?*

*Karku manta akwai karon Nabil da BilAL fa*
*Ga Fandau da Nabil kuma*

*Ga matsalan kama da dan gidan Dr abinfa yayiwa Nabil yawa wayyo team Shiddams kusa bo mafita cikin comment dinku*


*Zakujine insha  Allah* *muna tare*
*B JATTKO*
[3/12, 8:50 AM] Hauwa: *DAMATA*



 
                 *NA*



*BATUL ADAM JATTKO*


*Gargadi*
*Banyarda  ajuyamin lbr ta kowane irin sigaba saida izini dan lbr DAMATA ba kirkirarriyar lbr bane lbr ne dayafaru da gaske sai abinda aka dan kara dan kawatar da lbr banso fadamuku lbrn Gaskiya neba sai danaga wani matsala yana neman kunnuwa dan haka akiyaye tabashi danni banyi shima saida izinin maishi kuma yanzu fara DAMATA zuwa yanzu inajin (4months)*
*Bisssalam*

*42*


*A*binyi shine kiyar da muyin adua Allah ya bai yanata dan munemi yafiyar ta."

"Shid kadena min maganan yariyar nan dan ni bana son kodajin sunanta,
Kuma da kake cewa zasu nemi yafiyar ta kamanta batada tunani bata masan memuka mata ba....
"kedakata inde wannan abinda  yafaru dake bai zame miki izina ba baza kitabayin nadama ba,
To albishirin ki ni yanzu kowa yasan ni mijin Fatima ne bai yananta kawai nake jira na zauna da kayana duk da bata da tunanin inason ta kuma zan gyara kuskurena yarane de kamar yanda kika fada kin tsira dasu dan bana son asirina yatonu akaran kaina ma,
Kuma kina da hakki na shayarwa da reno da kikayiwa yaran dan anbar miki bawani abubane Allah zai bata wani tunda ita tana da lfy keko baza ki taba iya haifuwa ba."

Har yagama tana jinsa kalaman suna kona mata rai amma bata da karfi da lafiyan da zatayi wani yunkurin dan haka tarabu dashi dan tasan abune da bazai taba yuwuwaba ta zauna da kishiya

Dr Muktar zaune gaman Maman Fandau yagama mata bayani koma tunda ga kan yanda Nabil ya yaudari Fandau da yanda duk abubuwan suka kasance bai boye mata komai ba
Mama wani irin gumine yake raso jikinta na murnan yarta tana cikin koshin lfy da kuma mamakin abinda Nabil yayi yanzu dama maganan da yafada karyane yanzu yan biyun
Nan jikokin tane Fujjirat jikartace
" Mutari hadani da Fandau din a waya mugaisa."

"Dr yace Mama kiyin Hakuri komai yakusa zuwa karshe badan  yanayin jikin Hadim bada yanzu angama da komai,
Nide fatana kar kowa yasani har sai yafada da bakin sa dan nasan halinsa."

"bawanda zaiji Insha ALLAH  Muktar Allah yamaka albarka ban tabajin labarin da yafaranta min kamar wanan ba ko budewan idona banji haka ba ni Aisa ina da jikoki 4 daga Nabil haryanzu banji son ya saragu araina ba saide makaruwa dan tun farko baisan yata bace da yasani kuma sunriga sunzama taya,
Bazai iya rabuwa da itaba shine yakulla wanan karyar dan yasamu daman zamada ita."

Dr yace"gaskiya kam kodaga yanda yayi jinya adalilinta dakuma yanda yake nemanta yayi nisa sosai akanta."

Hakade suka gama tattaunawa har yafi
Mama cikin al ajabin duniya da mamakin yanda wai suka yaudari Malam Dauda har yadaura musu aure

Bayan sati 4 Hadim tawarke sosai dan harta danfara takawa da sanda take takawa dan de tagamu da kwararen asbiti ne da sosai anyarda da ingancin aikinsu har an sallameta sunzo gida

*Nabil da Fandau* sunyi nisa sosai a chat dinda sukeyi wani lokacima shiyake tabota dan yana jin dadin yanda take tsaramasa kalamai daku ma kwantar masa da hankali akan Fatiman sa dan yazu tagane itace Fatima dan tamasa tambaya cikin dabara kuma yagama ta tayi mugun jin tausayi sa dan ba abinda yaboye mata na karyan da yayi wa Iyayen duk ba gaskiya yafada ba taji dadi
Yanzu ma da kansa ya tabota ganin tana online

 _slm bakiye bacci bane dawa kike fira haka kode nasamu kanine_

Tana cikin bawa Akkaram nono taji message ya shigo tasan Nabil ne dan wayan nasane nashi  kadai jawoshi tayi ta bude tana murmushi har ta gama karantawa ta maida masa da Ripley
_Ameen kaima ina nema maka yardan Allah yakake ya Fuj da kuma me jiki?_

_Ameen Fuj gata tayi bacci mejiki tana dakin ta ba kinki zuwa dubata ba."_

_Ayyya Abu Fuj naji tsorone kaga matar ka tanada kishi kartamin abinda tayiwa Fatin ka_

_Hhhhhhh baza tamiki ba aike bance ina sonki ba Fatina kodan nace inason tane taji kishinta_

_hakane fa aheni akatsa nake to Allah yabarka da Fatin ka_

_Ameen nagode sister kin iya adua da gaske kinkusa aure_

_nade kusa samun mijin amma bance nasamuba_


Yace _ok_

Tace _dadi na dakai kajerce magana bakason magana me tsawo nikuma gashi yau voice naka nake sonji duk da bayau nafara jiba ba_

Bayi mamaki ba datace ba yau tafara jin muryar saba dan yasan ana fira dashi akafafen labaru dariya yayi afili yace  maki gama koshin wahala ba

Audio  Yayi cikin zakeken muryarshi yace "muryata kawai kike bukata kenan to gashinan ai muryata tanada araha wanda bai kaiki bama yaji akyuta balle keda kike farantamin kike tayani aduan samun *Fatina*."
Yana dariya yake maganan cikin kayatarwa

Ai Fandau jitayi kamar ta shide dan jindadi tana sauraron muryar sa tana wani lumshe ido saida ta saurara yafi so 10
 Sannan tarubta masa Ripley

_kasan wani abu?_
_"a a_
_Allah yayiwa muryar ka wani baiwa ko kasan dahaka?_

Yamayar mata kamar haka

_nasani dan naji abakin mafi zakin murya acikin duk kan muryoyin duniya dan Fatima ta dabance muryar ta daban ne kullum sai muryar yamin gizo_

_bayan ita bawan taba gaya baka kenan sa ita_

_nasha ji bazan iya lissa famiki wanda suka ce ba kamar yanda bazan iya irga gashin kainaba amma inason nuna miki nata yafi kwanta min_

_Gaskiya kana fifita wanan Fatin fa zaka sa nadawo yar aunty Hadim fa_

_dako zaki rage girman ki a idona_

_Ummm saina kega kamar kafison Fatin ne wai wakafi so cikin su?_
 Yace _Uumm kinsha min wanan tambayar ina baki amsa to dukka inason su dan dukkan su matanane kuma yan uwanane amma ya isa dan bacci nakeji_
 Tayi saurin mayar masa

_please amma meyasa nekake nuna rashin damuwa agareni kamata yayi kaji muryana nima kamar yanda naji naka_

Sarai yaga message dinta amma yasauka bai bata amsaba

Dariya tayi tace bawan Allah kenan

Hakan ma saida tayi recording dinta tura masa

 "shikenan dama inason nace maka nayi mafarkin kaga *Fannndo*
[3/12, 8:50 AM] Hauwa: *DAMATA*

                      *NA*

   *BATUL ADAM JOTTAKO*


               *43*

*Editing AYSHA ALIYU GARKUWA*




       



*Hadim*  duk suna zaune a  genaral parlour su Nabil Ummi Maman Hadim,
 saiga driver yashigo da Fujjirat dan gidan Dr ta wuni sauk'eta da drv yayi ta arce dagudu tayi wajen Nabil tana cewa.
" Abuu." cikin gwarancita ware hannun sa yayi yace "Oyoyo Mamana."
sannan ya d'an kalli drive yace.
 "Kako kyauta dan yanzu nake shirin  zuwa d'auko ta."
 baturen murmushi yayi yafice

Cikin kulawa da k'auna Nabil ya shafa kan Fuj tare da cewa.
"Wow waya miki wanan gyaran? yayi kyu sosai."
Cikin gwaran cinta tace.
 " *Aunty  kirki* ."

Maman Hadim tace.
 "Kaji harda wani cewa yayi kyu,
 wannan bak'ar wani kyu gareta bak'a sai sadaka."
 Hadim tace.
"Mama ai Fuj ba bak'a bace."

"Eh mejin tsoronta zaice ba bak'a bace,
 wankan tarwad'a ce,
 niko bana tsoron ta kinga dole bak'a zance mata."
Hadim tace.
 "Kalan chocolate cefa Mama tafi fari kyu yanzu su ake yayi."
Aiko Nabil dad'i har ransa dan Fandau dinsa yatuno kai ya jinjina
Yace.
 "sosai Maa sunfi shiga rai da ratsa zuciya."

Hadim sai asannan tagane ta kwafsa daure fuska tayi tace.
"Fuj zonan wai ni Nabil wacece Aunty kirki nanne a gidan Dr?
Kullum taje ta dawo sai tayi tamin zancenta."

ido ya lumshe tare da cewa.
 "Bansan taba sunanta kawai nakeji awajen yaran gidan da Fuj."

Amma wani abune yafado masa Aunty kirki ko itace matar Dr kai ba ita bace ita da take kulle adaki tunuwa da wanan yatuno masa Akkaram d'an gidan Dr tunda yaga d'an so d'aya bai k'ara kanin saba,
 Dan yaje gidan Habiban tace,
 anfita da yaron gayana son doctor yazo su d'auki mataki d'aya amma  Dr ya makale a 9ja.!

Ummi ma dariya tayi tace.
 "kai Ya Fatime kina kushe min cuwuna fa to ki dubi mace har mace kice sai sadaka,
 to kwantar da hankalin ki batayi ta tsohon naku."

Duk aka sa dariya banda Nabil da yake duniyar tunani.

Fuj tasa hannun a aljuhunta tafito dawani paper ta mik'awa Hadim
Tace.
"Aunty kirki sweet."
Karb'a Hadim tayi ta bud'e sweet d'inne ko a ciki  an nad'e,
amma takar dar da rubutun cikin yafi daukan hankalin ta dan kullum idan tadawo da sweet d'in aciki amma da acikin pepper kuma duk rubutun irin daya ne tana karantawa amma bata daukan abin da muhin mance sai yau da taga ansa sunanta wai  *mum Fujjirat*

Ga aminda aka rubuto kuma ba banbanci da na kullum

```Rance ba kyuta bane..! sadaka yana da ranar fansa..!
 Dutse ba abincin gara bane..!
 wani baya amsa sunan wani..!
 ajiya maganin wataran..! ~Aunty kirki~``` ..!

Hada hausar tayi amma bata fashici komai ba dama kullum hakane zata karanta amma bata fahimta,
 amma yau da tasa mum Fuj tasan ita akayiwa massage din kenan gabanta ne taji yafad'i to wacece Aunty kirki?.
  Ita dai Fuj karban sweet dinta tayi tana sha.

 Itako Hadim sai ta sauk'ata ta dauki sandar ta tana dingisawa ta haura saman,
Wayan Habiban ta kira tana dauka tace.

"Wacece Aunty kirki?."

Habiba tace.

"Ranar ma kinmin wanan tabbayar nace miki bakuwace yar uwar Abban Nol ce.!"

"Kibani ita."

"Ok tana sama bari in kirata,
 ai tana da kirki tana son FUJJN ki."

"Ok kiratan."

Habiba ta kashe wayan tukun ta kira Fandau  ta mata bayane yadda sukayi sanna takira Hadim tace.
 "To gata."
Fandau ta karbi wayan bayan tayi salama tace.
"Mum Fuj ya Fuj ta sauka lafiya?."
Wani irin faduwan gaba Hadim taji danjin muryan wada bata kaunan ji arayuwar ta amma tasan ba ita bace muryane kawai yazo d'aya
da haka tace.
 "Eh tazo muna godiya fa da kulawan ki akan 'yarmu,
 amma wani abu da kike rubutawa bana ganewa,
 shine yau nace baride na tambayeki me fassaran sa??."

"Au wai
RANCE BA KAUTA BA NE..!
 SADAKA AKWAI RANAN FANSA..!
 DUTSE BA RABON GARA BANE..!."
WANI BAYA AMSA SUNAN WANI..!."
Hadim tace.
 "eh."
"Ok kinsan yaran Aro ALLAH  yabamu ba dukuba ko,
 abin da ba duka aka baka ba kinga rancene ba naka bane  nasiha namiki dakuma tunatarwa yara rancene."
 "tace hakane fa to nagode dawanan tunatarwar ina fatan wataran zaki kawo mana ziyara ko?."

Wani irin bahagon murmushi mai d'an sauti Fandau tare da cewa.
"ai Aunty zuwa gidan yafi K'arfin ziyara karki damu wataran ana mugun tare."

Hadim tace.
 "gaskiya kinci sunanki Aunty kirki kinada kirki,
 to bawa Auntyn naki ko."

Fandau tana dariya  ta mik'awa Habiba wayan
Habiba tace.

"to ya k'afar?

"Alhamdulilah da sauk'i."

daga nan suka dan taba hira dan ita Hadim bata kawo akanta wani Fandau tana kusa ba kawai tana son jinne me Aunty kirki take nufine kawai.

Nabil ne zaune a d'an wani runfa na shan iska acikin gidanshi kiran Maman Fandau yashigo woyar sacikin murmushi ya d'auka Yace.
"Allah ya taimaki HAJIYA Mama."
 Tace.
"Ameen tareda d'ana ba."

"Mama ya gida?

"kowa lafiya amma sai rashin Fandau bawani labari ne?."

Abin yabawa Nabil mamaki dan shi bata tab'a tuntub'ar sa akan Fatima ba koda shine yamata zancen haka take cewa yayi hakuri insha ALLAH za aganta yadena damun kansa,
 sai gashi yau da kanta take tambaya,
 karfa taga gazawarsa shiko ba irin neman da bai yiwa yariyar nanba cikin rawan murya da kamar zai yi kuka yace.
 "Wllh Mama ana cikin bincike fa,
 amma har yanzu bawani labari,
 mama idan bansamu Fandau ba rayuwa bazata zo dai-dai ba yanzu nakoma bakin aikin na amma nakasa shiga filli ko sau d'aya Mama,
 amma nasa ayi istahara man agani nide na sha sawa anamin anacewa tana  hannun mekyu da kaina ma nayi amma danagan ta a mafarki sai tajuyamin baya."

Cikin kuka yakarasa maganan

Mama taji tausayinsa duk da tasan karyar da yayi.
 "Haba mesunan malam kazama namiji mana ka kuma sake kokarin nemanta dan tunkafin kagaya mana matar kace kamin alkawarin kawota da hannun ka."

Yace.
"nayi Mama amma gashinan nakasa cikawa Mama duk tunanina yakare akanta narasa yazanyi har wajen 'yan duba saida na Ayyana zuwa sai kuma naji tsoron,
 *Hukuncin Allah."*
book din Aysha Ali Garkuwa kenan mai fitowa

Mama tace. "Subahanallahi kul kai da kasa addu'a  kana da Allah meyakai ka sakin reshe ka kama ganye."

 haka takoma lallashinsa saida yadan sauk'o
Tace.
"ina Fuj?."
Yace.
"Sunfita dasu jidda da su Gana."
"kasuwa sukaje?."

"eh harda Iya da Inna ZAINABU suna da yawa sunzo
Duba Hadim ne."

"kai dana sani da nabisu nazo ai dubata nima."

"Ba damuwa Mama akwai yan zuwan jibi zansa Grema yakarbo passport dinki ayi visa dake."
"nagode d'ana."
A haka
Sukayi sallama

Yau har su Maman Fandau sun sauka Hadim ta tarbi Maman cikin fara adan ita arayuwan bata da matsala dakowa sai kishiya bata sonjin wanan kalman ko ga watane ba itaba.

Shiko Nabil sai yau yabud'e sakon Fatima menaci kamar yanda yasaka mata
Yana dariya ya bude a
Audo saida ya gama karan ta sakonnin ta duk na korafine akan kwana 2 yashare ta sai ida tace.
_amma banso mukayi irin wanan rabuwan ba dan na d'aukeda amatsayin d'an uwa dalilin haka na nemi muga juna kafin nabar kasan amma kayi burus dani inason inmaka albishi da maganan da nagaya maka na nakusa samun masoyi ya tabbata dan nasamu *mijin raina* shaharare kamarka wanda da maka dama ni burina na auri wanda ya shahara a ball dan tun ina yariyar inke da wanan raayin burina yaci ka nasamu mijin raina kaima ina maka fadan samun Fandau dinka_

_nasan kasan mesonnawa dan makusan cinka ne_
_*BILAL MAINA KANGE BG* nayi murna da zama matar abokin kaga muna tare *FATIMA MUHAMMAD GARGAR*_
*Bissalam*.

Sai pic din Bilal da yagama budewa ya baiyana afili yafurto nima ban soki ba me BilAL zaiyin dake ta haka kika bullo  kuma yariya dariya yayi sosai yace amma da nake pic din kika turo da yafi dan naga yanda kike amma fa sunan Gargar yabugeshi dama yar meduguri ce kuma gargar anguwan Zannah ne.

 kunan audio nata yayi saime jin muryar da arayuwansa bazai taba banta meshiba ya fara dukan dodon kunnen  sa
 kamar agabansa take maganan.
*SHIKENAN DAMA INASON NACE MAKA NAYI MAFARKIN KAGA _FANNNDO CE_*.

Meyasa tun ranan bansaya naji ba nace ina bacci ashe me irin muryan Fateena ce dan tundaga ranan bai wani sake bude message nata ba
 saiya sake dubawa *FATIMA MUHAMMAD GARGAR*
full name nata ya akayi sunan ma yazo dayan da Fatima sa gaban sane yaji yasake faduwa yace to wacece yasan de ba Fandau bace dan Fandau batada lafiya kuma me zai kawota London! amma daya duba Last seen
Wajen 1week kenan  rabonta da online yariyar da kullum sai yaganta on ya kunna
Voice yaji so ba adadi muyar natane  de ba wai gizon ne ba kawai sai ya yanke hukuncin yayi call nata har yayi dialing amma aka ce masa anrufe layin gaba daya cikin haushi yasake shiga cikin sakon nin nata yaci karo ko da sokon da take cewa.
 _To YASHIDDAS yaune tashinmu fa dan ma nasan zakaje bikin mudan yazame maka dole_
Afili yace.
" Towai ko da gaskene?." da sauri yagirgiza kai yace.
" Sam bade BilAL dinaba bayanda za'ayi ya shirya aure batareda ya gayamin ba."
 amma shi yanzu duk bawanan ba yafison yaji muryar wanan wanda take masa gizo da Fandau

Yana cikin haka wayansa ya fara ringing yana dubawa BilAL ne ya dauka yana cewa.          "Kamar ko kasan kaine araina dan yanzu nake shirin
 kiranka."
BilAL yace.
"Sai kuma gani ba toya akayi?."
Dariya Nabil yayi yace.
"kimanin  3 months kenan muna chat da wata yarinya har tace galabata mukayi dan sabo da ita to dan tamin tayin kanta nace a a, yanzu kuma naci karo da sakonta wai dama shaharata a wasan ball take so yanzu tasamu wani shima shaharare ne burin ta yacika kawai saigashi ta toromin pic dinka dan ita wawuyace."

Dariya BilAL yayi yace. "Me abin wawanta kan aciki ai wanda Fatima tayiwa tayin kanta yaki amsa shine wawa domin *DAMACE* babba sosai tazo masa yasake yarinya yar sarauta yar babban gida bata inda bata kai macce ba,
 burin kowane namiji na karbeta nikam dan gudun kar *DAMATA* ta kubcemin,
 yanzu haka ma ina airport din London zan tafi neman auren ta ahe dasai dai kaji na angwace."

"Wai dama da gaskene ?to wacece ita tacemin sunanta Fatima Muhammad garga,
 kai kuma gashi kacemin Yar sarauta ce yar wane gidane kaina yadaure? ."

BilAL yace,
"yes da gaskene naji tausayin tane dan tafadan min tarihinta kakaf kusan irin abin da Hadim tayiwa matarka,
 aka mata saide ita ba aci nasaran sa mata alluran ba,
 kuma ita nata zalincin ma yayi yawa wai fa auren sukayi dan ta haifu su dauka sumata sakin wulakanci  kuma har ta haifun yanzu haka yaranta ukku suna wajen su amma tafita da cikin nabiyu amma acewar ta wai nima nasan mijin nata masai dai dan tanason cusa masa haushi bazata gayamin ba sai bayan munyi aure,
Da  auren gaggawa naso muyi da ita saboda nina daukawa kaina lefin nina yaudareta  na aureta gudun kar abata wani wada Iyayen suka zaba mata nikuma inason ta shine muka gugu na aureta,
dan tacemin
kishiyoyin Mamar ta zasu mata gorin taje karuwanci amma dayake ta na tsorace da abin da wancen mugun ya mata shine tace ita sai anje gaban iyayen tukun ."


Cikin firgice Nabil da yaji kamar ya dankare awajen kode Fateen sace
Dasauri da rawan baki yace.
 "tagaya ma ya zaman ta kewansu ta kasance? tagayama ya yanayin yaran nata yake mata ko maza?

"Eh tagayamin da farko macce ta haifa na 2 kuma twins duk maza
Yana yin zaman su kuma labarin da tsawo idan kanason ji ka sameni a airport din dan bayanzu zamu tashiba."
 ai Nabil baima gama sauraron BilAL ba yakashe wayan jikin sa yagama bashi Fateema sace kawai da sauri yashiga gidan.

 amma me yatarar ana wani danjan da Inna ZAINABU  idan maku manta ba a koi photon Fandau adakinta na itada Bagana da Mama kuma na taba cemuku Fandau da takeson koyan rubutu tarishin rayuwan ta take rubutawa to pic din yana cikin wannan life story nata ta turashi kasan bed sai yau yasmin ta fito dashi  tana gama karantawa ta cikin kuka tace.
" Wllh awannan karon idan ba ayarda dani ba zanfasa kowa yaji." kunsan Yasmin lawyer ce mekare hakkin dan ADAM dan haka tana da mugum tausayi gakuma ta jima tana tara bayanan dan bata yarda da yanayin Hadim ba su Jidda ko dasu aka karanta Inna ZAINABU da Maman Fandau duk suna dakin sai da akayiwa Inna filla filla ta tusiye maman Fandau akan ta fada mata gaskiya aiko Mama ta fadi iya abinda Nabil ya fada musu dai ita bata so hakan ba ta fison taga Nabil yacire taurin kai yafadi komai da kansa kuma ko min daren dadewa tasan gaskiya zaiyi halinsa.


Dasauri Inna ZAINABU ta sauko har tana hardewa ta haye saman Hadim da dama Mamar ta da Ummi sun sata a sakiya ta fadi gaskiya dan dama agaban Ashuwa kanwar Hadim abin yafaru dan haka ita tazo da gudu da gaya musu shine fa gidan yasake cakud'ewa Inna tana ganin Nabil tace.
" Zonan babban munafiki itan idan shegiyar muguwa bata fad'i gaskiya ba ai kai baka isa kak'i amsamin ba."
 daganan tabasa bayani komai yace.
 "Hakane amma batun yara natane ba gaskiya bane,
"K'arya take yaran Hadim ne."

"Kunci uwar da kaida uwar Hadim din munafuki matar taka mai kugun mazanne zata ta hafi yara har ukku,
  Dama Dr Hafeez yace min bata taba haifuwa ba kuma tana da matsala,
 bazagin da banyiwa yaron nan ba har maita na daura musu har uwar Hajja meram saida naje nayiwa cin mutumci kuma nace idan Halima bata haifu lafiya ba to dasa hannun dan ta sai nayi shari a dasu yanzu haka ina cuku cukun makashi kotu,
 wannan abin ya bullu gaskiya tayi halinta ashe kune abin jefawa kotun wannan wane irin masifa ne ALLAH kakawo mu karshe zamani da mutum zai iya jin abinda yafi karfin jinsa wanan wane irin masifane?."

Shiko Nabil bama fahim tar ta yake ba hankalin sa yana wajen BilAL ga ihun da ake masa yarasa ma meyazo d'auka cikin dan haka kawai yace "kuhada kayanku kusameni a airport."

"au ni ban isa kagayamin ba sai munje gaban uban ka za kama fadi gaskiya ai dama yasmin tace min a haifu wan fari ranan da Hadim tace ta haifu tagan ta tana sallah da sauran bayanai dan de nak'i yarda ne ashe kune mak'aryatan  ko duk jikina kunne ne bazan yarda dakuba."

Shide ficewa yayi bai tsaya ba."

Zaune suke wani kebeben daki na musamman acikin airport din
"Yanzu kana nufin har ka yanke shawaran aure batare da sani naba kenan?."

"Shiddams kenan ai ance *ASIRIN CIKI SAI HANJI* kuma kai ba auren ma kayi har kazauna da matar tayi ciki batare daka gayamin ba,
 nima kuma surprise din ka nasoyin dande kazomin da batunne da bakaji ba amma yanzu ai andena yarda da kowa yaro kayarda da kanka kawai."

Nabil yace.
 "Kai kasani niyanzu bani tarihin nata tukun."

Dariya BilAL yayi  yakwashe komai yagaya masa...
Ai tun kafin yakarasa jin lbrin ya  zube k'asa yanayiwa ALLAH sujjadar godiya yad'ago yana cewa Alhamdulilah Rambana."

Bilal yayi murmushi irin na nuna ana tayasa murnan nan
 Yace.
 "ai nasan dole duk wani masoyina ya tayani murna sai ma kaganta wllh nasan har kyutan kujerun Makkah sai kayi thanks kum....!"
Nabil yace.
 "Wane kai wllh itace Fandau d'ina ita nake nema."
BilAL kamar da gaske Afirgice yace. "what!?"

"Wllh itace nima bansan yanda akayi ta samu lafiya da kuma zuwa London ba."

BilAL yace.
 "To kadawo hankalin ka dan ita taka bata tab'a haifuwa ba niko wanan ta haifu yanzu ma cikin da tafita dashi yananan tana goyon d'an,
 in maso kake na barmaka ita dan kai tafara cewa tana so to wllh baka isaba,
 nariga nakamu da sonta kariga kasaki daman ka niko bazan yarda nasaki *DAMATA* ba dan sau d'aya take zuwa arayuwa kuma inajin son....!"
Ai kafin yakarasa fada Nabil ya wankeshi da wani irin marin da yajawo hankalin Security's d'in BilAL dana Nabil suka shigo da gudu amma ganin abokai mafi kusa wanda basu isa su shiga tsakani suba yasa sukayi curku-curku shiko Nabil duk yagigice mari kawai yake zubawa Bilal ya cukumo wuyan rigansa shiko BilAL tsayawa kawai yayi yana kallon ikon Allah wai yau shi ake mari bai taba sanin mezafin mari ba sai yau sai da yagama iya marin sa yagaji har fuskan BilAL ta kumbura yayi jajir abin kida fari ga hutu sakin sa yayi kuma yadurkusa agaban BilAL din yana rokon sa yagaya masa inda matarsa take da gaske cikinta bai zube ba.
shima BilAL dur kusawa yayi yace.
 "Haba Babana me yayi zafi ka hukunta danka haka kaga yanda kamin akan mace,
 lallai na yarda mata masifane kalli yadda kamin."
yaja hannun Nabil ya d'aura kan fuskansa shiko Nabil hanunsa yajanye yace.
"Ba maganan wasa bane seriously ina matata?
Kai kanka sheda ne yanda nasha wahala akanta gayamin inda matata take?."
Bilal yazaro wayansa yace.
 "Ni kaga tawa banajin tana kama dataka."

Dasauri Nabil ya d'ago jajayen idon sa ya zubasu kan pic din Fandau da tayi wani mugun kyu wanda bayan kyanda tayi saida akayi editing duk yanda aka canzata idan yaganta bazai kasa gane taba yafara magana
"kagani ko Wllh itace ina take?."
Ya Allah yasake daga hannu yana godiya ga Allah

Daure fuka BilAL yayi.
 "To idan itace me hujjan ka kokana da huja bazan barmaka ita ba ai koda itace wllh baka isa na hakura da itaba azabure Nabil ya tashi yana tunkaran BilAL yana cewa.
"Matata cefa da aurena akanta ko atarihin kaji kalman saki a ciki da kake abbaton kana sonta zakayi mugun nadama idan bakinka yakara furta wani kalma akan matata."
a hatsale
Bilal yace.
 "Kai kaine zakayi nadama idan kak'ara cewa kasan Fateema dan tawace ka.....!

ai BilAL bai karasa ba sabo da wani irin shaka da Nabil yayiwa makoko ransa........!


*To mabiya DAMATA yakukaga page gaba zai kasance dan kunsan dole agurfana gaban ZANNAH MODU abinda kuka dad'e kuna nema anza wajen fa ga Inna danja natafe ya Hadim zata dauki bai yanan FANDAU*
*dan Fandau tace mata rance ba kyuta bane* ...!

*karku manta fa tsakanin abokan biyu akwai rigima NABIL yayiwa BILAL rashin kirki  bayan uban BilAL shine yayiwa Nabil gata ko ya manta ne

*

*B JATTKO*
[3/12, 8:50 AM] Hauwa: *DAMATA*



                *NA*

 *BATUL ADAM JATTOKO*

*44*




*j*uyowa BilaL yayi yakalli securities dinsa dana Shiddams alama yamusu da sufita,
 sumi sumi suka fito amma na BilAL ba ason ransu ba sunso su dauki mataki amma ba yanda zasuyi shiko Nabil sai sake shakansa yake yana cewa
"nace kafitomin da mata maci amana agabana kake cewa matata zaka aura....
"to sakeni na gaya maka."
Da sauri Nabil yasakeshi
Yace" gayamin."

"haba my Abu zauna mana yanuna masa kujera sai da yabari Nabil ya zauna ya fara magana amma yana maganan yana tafiya hanyan fita adakin cikin dabara yana cewa "Gaskiya nayar da matar kace don da bakin ta tacemin mijinta makusan cinane dan haka ma tace ayi auren  gaggawa dan idan nasan waye mijinta bazan Aureta ba amma saide gashinan da nasanen ma bazan  iya bar maka ba dan nikuma Dagaske na kamu da sonta dan haka mufafata agaban Zannah ko."

Yana gama cewa haka cikin zafin suna yan'wasan ball ya fada waje yaja kofan da sauri ya rufe Nabil aciki har da key yazare key din yayi office din Gdororo yabashi yace "ga key amma kar abude shi har sai muntashi."
Gdororo ya girgiza kai
 Bilal ya wuce jirgi shida security shi wanda ya shirya tafiya dasu dama ankusa tashi

Hadim kam sabar bacin rai yau saida tarufe ido tayiwa Inna ZAINABU rashin kunya
Inna taja hannun Fuj tace "zonan Hadim tareke hannu Fuj itama tace "agaban ki yanzu Nabil yace "yara nawane danme zaki karyata shi bashine uban su."

"ai duk kan shedu sun tabatar min da yara banaki bane gashi arubuce nima nagani yarinya tabar komai arubuce."

"to Inna tunda baki yarda anyi hakan nedan abata mana sunane ba kiyi yada zakiyi naga uban wada ya isa ya juya yananan su zama ba nawa ba aikin banza ina jiran naji an makani akotun."

Inna ta kame baki "Hadim ni kike zagi yau.
Kafin Inna ta karasa maganan har Khadija yar gidan Inna ta wanke Hadim da mari kokuwa suka fara Hadim ta doku dan bata da lafiya Ummi da Maman Hadim kuka suka fara da kyar da temakon Maman Fandau aka rabasu fadan Mama  Aisa bataso abin ya kasance da haka ba aiko koba komai Hadim tanada nata hakkin na shayarwa akan yaran
Inna sai cewa take ai ayau kinkawo karshen Aurenki da Modu.
Hadim batayi  magana ba dan ta kanta take ciwonta ya famu sosai
Maman tace"
 de sukayi ta da Inna haka suka tarkata sukayi airport din rankowa ba dadi saide fa Inna ta hana yaran dukka ta goyi BilAL ta bawa Mama Aisa maaf Fuji tana wajen Zahra dasuka zo airport

Shiko Nabil yana ganin BilAL yarufe shi ya fara safada marwa komai nasa ya kunce dama da Fandau dinsa yake chat ya akayayi hakan ta faru ina alluran da aka mata ta samu hankalin chatting  meyake faruwa  maganganun BilAL da wanda Fatiman Chat idan suna chat take gaya masane kawai yake masa yawo a cikin kwakwalwa

*ummm Abu Fuj kenan baka ta bacewa kana sha awan ganina ba fa   ina jiyema ka nadama ranan da kasan koni wayen*

A'lokacin ina shiko kulata bayayi dan yasan bawata a gabansa illah Fateen sa
Gashi yanzu abinda ta ke gaya masa ya tabbata
Wlh itace ina BG yaganta ina yasanta  meyasa bai gayamin ba ina take yanzu har dororo yazo ya budeshi yace "yatafi ko? suntashi ko?
Dororo yace "Shiddams suntashi. dukan hannun sa yayi yace "AD shir yamin tafiya yanzu Dororo yace "a yanzu haka gaskiya bawani bucking na zuwa 9ja gaskiya  idan ka matsane  ma zuwa gobe akwai mezuwa  Gabon kaga sai nasan yanda zanyi yafara sauka a Nigeria ko.
"a yanzu na keson tafiya ko akwai wada ya isa hanani tafiya asan da naga dama inada jirgi har 2 acikin airport dinnan.
"Dororo yace "oga gori najiran ranan fad'a  amma ai duk da kana dashi bashine zaisa kasame shi sanda kaga dama ba dan haya kabada ba kyuta ba amma girmanka da kimar ka yaci a shirya madin saide ayanzu ba jiri akasa wanda ya fuce duk da safen yau suka sauka saide akwai wani Zg   to gaskiya yayi girma idan akace kabiya Drop  dinsa akwai kudi fa."
Tsaki Nabil yayi yace "akwai din kenan.

Nabil kam yamanta mada batun su Ummi saida yaga kiran Khadeeja ya dauka yace "dije yanzu zamu tashi fa ss dinsa yayiwa magana yaje ya nuna musu jirgin da zasubi
Nabil acikin jirgima jiyake kamar ba za ajeba duk wani fargaba ya gushe masa murin sa yasauka yanemi BilAL kawai
kulle kansa yayi awajen na musamman acikin jirin ya kasa sha bare ci
Inna kuwa sai sake jajjaba abin take maman Fandau bata hakuri har Allah yakawosu meduguri Nabil motan sa shikadai yahau sai drive da yake tuka shi bai san ina zaisamu BilAL ba dan haka yazaro waya ya kira babban yaron BilAL yace kuna ina yaron yakalli ogan girgiza masa kai bilal yayi  alaban yace bai sani ba
"Sir kanason ganin ogane koni?
Uban me zanma ogan naka nake nema.

"Sorry sir mun rabu da oga a airport ne yace yanada wajen suwa mu muzo gida kakira shi kaji.
''da suwa kukarshi?
Alama bilAL yamasa da hannu akan yace shi dayane  ai yana gayawa Nabil yace karya ne BilAL baya zama shidaya dan haka duk inda yake kai nasan kana wajen idan baka gayamin inda yake ba na bincika nagano wllh zakayi nadama BilAL yasan halin abokin nasa dan haka yasa hannu yakarbi wayan  yana dariya yace "anki afa d'ama inda nake din mugun uba Babana kanason karasani ko inde maganan matar da zan aurane kaje gaban Zannan kanemeni mana dan ni agidan na sauka na gama masa bayanin komai,
Kai mukejira muji ta inda me haifuwa 3 tazama matar ka.

Nabil yace "Please Bg  ganinka kawai nakesonyi akwai wani tambayar dazan ma  ne.

"Haba Baba inafa son raina dan nasan muka sake haduwa ba manya akusa rabani dashi zakayi.
 yana gama fadan haka yakashi wayan gaba daya yamekawa yaron nasa dan shinashi nun ajirgi yakashe
Shikuma Nabil hanyan gidansu BilAL da yake porlor yayi

Su Fandau dama tun last week suka zo
Suna kaduna agidan  Dr na *kinkinau* yau suka shirya zasuje gidan Malam Dauda da ita dan dama Dr yagaya musu komai  amma yahana Malam kar yagayawa zannah dan yafi son Nabil ya fada da bakin sa
Fandau tafito cikin wani lafiyayen lace maran nauyi light blue takallmin ta flat shoe ne maki sai mayafinta baki da jaka mahadin takallmin kana ganin kasan ba kananan kudi ake kashe mata ba dan Dr dayasa muguta aransa sakin bakin aljuhu yayi yana ta barin kudi akanta ga BilAL yana bada nasa gudun muwar sosai suka fito da ita kalan fatanta kawai ya isa sheda  cikin wani irin taku take saukowa tana lase lasen wayanta dan Habiba tasata grp na manyan mata harda Hadim aceki dan tsabar  tsokana ma Fandau Mrs Shiddams tasa a sunanta sukuma yan group tunanin su Hadim ceta canza  layi saiyi suke yajiki ashe kindawo na can London kuma suna cewa yaushe kika tafi
Dande Hadim yanzu ta kanta tace bata gani ba sukuma kawayen idan suka kira Fandau cewa take ba Hadim bace ita kuma Hadim bata masamu daman wani amfani da waya ba
Har takarasa saukowa Habiba baki bude take kallon ta
"Wow Aunty kinyi kyu inama yaya yagan ki haka.

Habiba tace"bana son gatse fa kinaganin kanki kuwa Fandau tafiyanki kadai abin  kallone nede kar kidinga wanan tafiyan agaman mijina yagani yare namin dan ma nafara koya nima awajenki.

Dariya Fandau tayi"tace haba  Aunty har wane tafiya na iya karki zama Abu Fuj mana wai atafiya ta kadai yafara jin sha awar  yagani wacece wai atafiya na kadai yagane ni ba tsohuwa bace ranan da yafara ganina haka kowa yakecewa ni meyangace wllh Aunty bansan yanda zan canza ba.
Habiba tace"Fandau
Kin iya tafiya tun kina yar gargar dinki ma balle yanzu da kike jinkanki kema watace bame kalloki yace baki gama ganin karshen biro ba duk inda macce me aji takai awanan duniyar kinkai zanso Shiddams yaganki ahaka bame ganin ki yace kintaba sanin me aure.

"to ai Aunty dama girman ne na dole dakuma yanayin gidan muna  rashin sa macce aboko amma har yanzu fa shekaruna 19 kinga ko acikin manyan yanmata ma baza asani ba har yanzu banfara  nawa yan matanci.

"shegeya kinason kicemin sai agidan Shiddams azama nabiyu ko?

Rufe idinta tayi tana dariya tace "Allah Aunty duk abinda bakumin ba zai kunbiyani a shiga na 2.
"kamar su medame kenan?
"sakin lalle cuda da kuma dukkan events dakomai na al adan mu.

Habiba tace"haba yarinya kinriga kinsaki wanan *DAMAR TAKI* ai.

Cikin shagoba tace "Aunty kenan nazama local nide sai anmin abunda za anunawa Hadim ni cikekiyar yar sarautan meduguri ce kullum idan ta tashi sai tace min wani sarauta ta ta banza a wulakance suka tsinceni.

Habiba tace "gaskiya tariga taga yanda kike da so yanzu duk abinda akayi zata ce tsilar Shid ne towai ke danme duk yan gidan ku suna gayu sosai ke kina cikin kazanta ne?

 Wllh Aunty ba kazanta bane kamar yanda nagaya miki su sauran yayun mune suke musu da iyayen su mata kinga YaManu da YaBunu inde zamuje gidajen matan su mumusu bauta tofa matan zasu z
Gaya wa mazajen su yiwa mutu komai har suma sudauki kuncen su su baka haka yayun mu mata masuke cewa inada giman kai haka fa sukece min ni ba komin komai ba ya dillalin kashi bai fadin rai niko ko sunbawa Bagana bana karba idan tabani dan ma karsu gani ajikina suce nadamu da kayansu dinkin kuma sai sallah shima YaKadir ake bawa kudin komai kinsan komai nagidan ahannun shida YaBashir yake to sukuma sai subawa iyayen su mata suce asiye abinda yakamata wllh kala 2 suke abani amma yaran su zaki gansu da kalala da biyun ma ba mekyu ba duk inda nawuce sai naji ancemin yanga acijin Summa akwai inda aka daba cemin ma yargidan me aikin gidan Malam ce kuma aishi Baban yana ga.

Habiba tace "karkiga lefin Baba shifa Akullum me jama ane balalle yakulaba.
Tabe baki Fandau tayi dan ita bawanda take daurawa lefin komai irin Baban ta
Dan haka ta katse zancen dacewa
"inasu Nol ne?
"Kishiga suna wajen Furera ko ta kama shir yasu ki karbo Akkam ma.
Habiba ce take dauke da Akkaram suka fito sauran yara suna finsu abaya
Suna fitowa Fandau tace aunty kibari ni zan tuka.
"kerufamin asirin dan kin koyin tuk'i a London wllh baki koyin na Nigeria ba sucan komai nasu atsare yake hanyan mutane daman hanya abin hawa daban to nan kina cikin tuk'i dan mutum zai tsallako miki balle *Rigasa* fa zamuje

 *ALLAH* zan iya.
Habiba ta meka mata key Fandau ta shiga su Nol suka shiga baya Habiba ta shiga gaba dauke da Akkam
Fandau tayi Bisbillah tayiwa motan key tayi horn megadi yabude tafita

sai gidan Malam Dauda

Rungumeta Inna Fajii uwar Dr tayi tace wllh tunranan da Yusif yake gaya maba yanayin yanda daurin auren yakasance muketa jimamin abin har yayan yazo yake gaya mana ashe kece dama AISHA da Yusif sunce kamar su daya da ta kwaranki ta gargar asheko ke dince haka akayi ta jajjabin abin"

Koda Malam Dauda yashigo shima ya jajjaba abin yakuma yimata nasiha yace su shirya gobe za ajen meduguri ayita takare

Dr a jet ya shira musu tafiya meduguri suna sauka dama Bilal yatoro drive yakwashe su yawuce da su malam Dauda gidan dama da gidan sa a meduguri shima Dr da iyalen sa suka wuce gida su suma da zuman saida safe za ahadu agidan Zannah

Inna Zainab cikin kuka take tsarawa Baban Nabil Alhajji Habubakar  shima Baban Nabil harda kukansa ina ma zancennan bazaije gaban Zannah ba yanzu dawane idon zai kalleshi Inna Zainab tace "shegiyar yariyar na duk ita ta sa sa ai
nadade ina gaya muku kujuji shrrin muna mata shi gansa shidan ya jinjina mana kanjin macce kar kaga lefin danka yahau dokin macce'ne amma inason Nabil yanuna mata matsayina awajenta yanda tagayamin magana a gaban sa uwar ta daure mata gindi kai badan nima bawasa ba dabazan karbi yaran bama amma ga Fujjirat taki zama agida na abarta anan.
Baba yace "itama Hadim din tana nan ai.
Inna tace "bazan kore taba dan tana gidan kanwar uwar ta amma nace banda gidan d'ana

 shiko Nabil har  yanzu ahanyan neman Bilal yake  gashi idan yakirashi sai yace muhadu agidan Zannah kawai

*Washe gari agidan Zannah*

Nabil wurjajan yafado gidan Zannah ALLAH ya temaka ba shida bak'i sai wasu almajirai sai malam Dauda da bai gayawa Malam komai ba tun,zuwan sa gaban Malam yaje yazube dan yaje wajen Mama tace bataga Fandau ba tunda tazo    kuma tun ajirgi ya gaya mata Fandau tana wajen Bilal
"Malam ansamu Fandau ta fito wllh tana wajen Bilal amma yace sai agaban ka zai bani matata.
"Waye?
Bilal kuma?
 inji Malam
"Dan gidan Ahj Maina kange ne.
"abokinka kenan?
"eh Malam gashi kuma nazo da ta shiga ciki Mama tace batanan wllh idan ahannun sa yarikemin ita hartsawon wannan lokaci wllh zamuyi shari a dashi.

"Subhanallah!
meyayi wanan zafin kuma?
Shiko Malam Dauda dayake yasan komai nunawa yayi kamar baya jinsu

"toyanzu ina yake shi Bilal din?
"yace wai idan nawo a kirashi kiran Bilal yayi yace gani agidan Malam din

Shiko Bilal sungama duk wani shiri da zasushi kuma sun samu Baban Nabil sungaya masa komai
yace "suyin daidai yanzu ina Fandau din.
Dr yace suna gidan nan tare muka zo sunshiga ciki,
 zamu tafi  Gargar tun tuni Nabil yana can.
Yace "au haba.
Ai dasauri Alhajji abukar yayi ciki dan yanason ganin Fandau

Fandau da Habiba sanda suka shiga gidansu Nabil a falon Iya suka tarar da Ummi alokacin suma jajabin abin suke amma dasu kaga su Habiban sai sukayi shiru  suka gaisaUmmi tace "ina su Haris Habiba tace "suna Gargar da Inna.
Ummi tace "ah da  Hajja Fajji kukazo kenan?
"eh
Iya ce ta zubawa Akkaram ido tace "Hajara ganomin wani d'a ahannun wanan yarinyar kamar d'ana yana karami gayanda yake zillo kamar Shid.
Ummi sai alokacin ta kalli yaron tace eh kuwa amma Habiba dan ta basar da zancen tace "Ummi ina yaran gidanne?
"suna dakin su har kawar kima gaban Fandau yafadi duk da tasan dama yau dole taga Hadim amma taji wani irin dan haka tafara karanto addua
Itama Habiba saida taji wani irin wata kila yau kawancen su da Hadim yazo karshe
Tana cikin wanan tunanan taji Ummi tana cewa Tasleem "rakasu dakin Gana
har zasu fita Ummi tace yarinya kawo dan gidan waye ne?  Itade Habiba fita tayi da sauri dan baza aji abakin taba
Fandau ce tajuya ta bawa Ummi Akkam Ummi da Iya suna cewa ikon Allah ga yaro hamar su Maaf suna jarirai Fandau sun kuyar da kai tayi ta fita
Hadim jabe akan katifa tayi wurjanan da sauri Habiba ta karasa inda take
"Mum Fuj kina hutawa fa
Ta karasa ta rungumi Hadim
"lfy naga kinrame ko jikinne? Kafin Hadim ta bata amsa saiga Fandau ta shigo cikin takunta na isa idonta fes abude sallaman da tayi muryarta yadoki kunnen Hadim da sauri ta daga kai aiko sai gashi idon ta cikin na Fandau da sauri ta meke wacece?
wanan mekikazo yimana gidannan yawushe kika warke?
Suma su yasmin sai kallon Fandau suke dan yasmin kam tagane wacece

Hadim a tsorace take nuna Fandau "kece kece?
Habiba tameke tace Ayyya kin santane?
Itade Hadim kallon Fandau take jikinta yana rawa ga dama kafa ba lafiya
 Hadim tace wa Habiba "ke kinsanta ne?
 Habiba tace "sosai yar gidan zannah cefa Zannah namu na Gargar.

Kafin Hadim tace wani abu sai ga Fuj tazo awaje tana ganin Fandau tayi kanta tana cewa "Aunty kirki.
Itama Fandau daga ta saba tayi kamar yanda ta saba tace "iyye wannadin Fujn wacece?
Fuj tace "yar gidan Aunty kirki dama sunsa ba haka idan taje tadin ga tambayar ta kenan yar gidan wacece tace yar gidan Aunty kirki
Fandau" tace eh mana rance ma kyuta ba ajiya maganin watarana Fujn Aunty kirki.....
Ai Hadim sandan ma bata tsaya dauka ba taja kafa ta karasa inda suke da jarfi ta fusge Fujjirat ahanun Fandau tana huci tafara magana dama kece Aunty kirki kina nufin kinban race ne kindawo rayuwa ta dan ki tarwa tsamin ne wllh saide ki      tarwatse aniyar ki tabiki yar gidan matsafi har alluran bantau ya kasa aiki akanki  to wllh aniyar ta biki bade....
"Ameen Ameen Fandau ta katseta haba Aunty yazaki min addua bazaki ban *DAMATA*nace Amin ba ai duk wada aka cewa aniyar ka ta bika baice amin ba tofa aniyar ce batayi kyu ba Ameen.

Shiru Hadim tayi tana huce
Fandau
Tace "Haba aunty kici gaba mana kokin gamane?

Hadim tajuyo kan Habiba tace"Habiba meya hadaki da wannan yarinyar?
Ina kika santa?
da kinsan ko wacece ita acikin rayuwata kuwa nasan da kinsani da zaki gayamin mu hallakata nayarda dake bazaki zauna da itaba to wannan da kike gani annobace da gaiya take rubutu min latter nasan da kinsan ita wacece da maki bari ta kai iyanzu ba danasan bazaki bari ta  baiyana ba baiyanar ta kamar tar watsewar rayuwa tane ina....  Maganan ne ya makale mata sanda Tasleem ta shigo da Akkam tana cewa "wai gashi yana kuka.
Fandau tameka hannnu takarbe shi tasashi a nono   su Jidda da sun gane wacece Fandau bin yaron sukabi da kallo Gana tace "cikin bai zubeba kenan Yasmin tayi saurin karbar sa tana cewa" haba ai dagani ba tambaya wanan jinin YaShid dukka suka fara murna banda kanwar Hadim Ashuwa
Hadim tace" Innalillashi waninna ilaishirajuna cikin da da idona naga jini ace bai zubeba...
Fandau tace"kina mamaki ne Aunty ai ba abin mamaki a kikon ALLAH kowa yayi iko ba zaiyi irin nasa ba kinyi mamakin ganin abinda kikaso yabaru akaina yafaru akanki ko  kin sa azubar min ciki Allah bai yarda ba ke kin haifu yakarba ko gani bakiyi ba sanan anyanke miki maifan balle ki saran samu nan gaba gashi yaran da kike dasu kuma na arone shikuma kayan aro baya rufe katara  kinsa asamin alluran bantau gashi ke Allah ya nakasa kafanki.
"Nizaki cewa naka shesheya zata iyo kan Fandau daidai da shigowan Baba da su Ummi Iya tana cewa "haba  nifa inaganin yaron nasan namune itako Ummi tarasa mame zatace
Baba yace "kai kai Hadim ta dakata tana huci
"kinyi na farko ba adauki wani mataki ba shine kike yunkuri kai mata duka acikin gidana daga ke har mijin naki ayau zakusan wacece Fandau duk kuzo mutafi dan nasa adauko uwar taki me cewa bata yarda ba anmiki sharri ana shirin kwace mata jikoki tar ta maka mutane akotu to Allah yakaimu Monday ayi akotun ma yafi Duniya ta gama sanin me kuka aikata keda azzalumin mijin naki  yanzu haka kafin kotun ma Zannah yana son ganin mu kuma harke duk kutashi mutafi.

Hadim tace" nide ba inda zance
Baba yace "shikenan yizaman ki karki min rashin albarkan da kikayiwa Yayata.
Kusauran kufito mutafi haka zuka tafi akabar Hadim dasu Yasmin


*GIDAN ZANNAH*
Fandau da motan su yayi parking kasa sauka tayi duk sauran mutane sun  sauka tadaga kai taga yanda kofan gidan suya ya canza duk da dama zanen sarauta ne amma baikai wanan kyu ba wasu daga cikin almajiran gidan ta gani kamar suna kallon ta sun kunyar da kai tayi kasa Habiba ce takula da Fandau bata fitoba ta zagayo ta bude ta jawo hannun ta
Tace "Aunty ina tsoro.
"tun agida nagaya miki karkiji tsoro tsoro me?
"Aunty haduwar muda Mama Aunty inajin kunyar ta kuma ina tsoron Baba Aunty kisa amedani gida bazan iya shiga ba.
Fisgota habiba tayi ta fito da kita "kinga   aiko ke zajija hankalin jama a kanki wanda idan wucewa zakiyi dom dom bazasu ganeki ba kiyi adua kawai haka suka fara takawa har get na biyu wada anan baban parlour Zannah yake nan mutanen suke ta duruwa akofan ma saida ta tsaya tare da kyankyame hannun Habiba  janta Habiba tayi ta shiga da ita

*wai wai koni*
*B Jattko saida nayi kamar zan  sanbada da gudu ganin taron maza da mata awannan makeken d'akin taron*

Habiba ta ja hannun ta Fandau kanta ararufe har suka samu waje suka zauna wayanda suka zo tare ne kawai suka gane itace amma duk basu ga fuskanta ba
Bayan Malam Dauda ya bude taro da adua
Zannah yayi kyaran muryar yace "to Nabil gaka ga BilAL Maina da kakawomin karan matar ka tana wajen sa.
"eh Malam tana wajen sa
Malam ya Kalli BilAL yace" Bilali  ya akayi haka ina kataba jin ana aure kan aure kuzaku fara kaida abokinka?
BilAL cikin nusuwar yafara magana "Gafarta agabana Nabil ya tsara muku yanda ya auri Fandau ba akasannan ba kuma tana da ciki aka zubar da cikin to meye hadita danawa wanda gayanda akayi auren ya bawa Malam labarin auren Fandau na gaskiya wanda Malam Dauda ma yakara da cewa shine maya daura auren.
Zannah yace "to wandan abu da rikitarwa to  inaga ba yarinya daya bace wacece tawa Fandau din aciki? Dasauri BilAL yace"  tawa itace Fandau dinka dan yanzu haka neman aurenta nazo.
 Malam yace "Masha ALLAH to kai Nabil kayi adua ALLAH ya baiya na maka taka Fandau din kaji ba ita bace
Nabil yace "itace Wllh  itace.....
Baban sa yadaka masa tsawa yace "kama yarda mutane sha shawu ne irinka bayani da kamana da wanda BilAL yayi ba daya bane zaka kafe akan matar kace.
"Baba itace yazama dole nafadi gaskiya koda duk duniya za su tsinemin ne akan inaji ina gani arabani da matata
Ni newan da BilAL ya bada labari yanzu duk abinda na gaya muku wancen lokacin ba gaskiya bane shiryawa nayi dan na rufe nawa lefin ga Sani shine sheda na kuma shiya karbomin auren awajen Malam Dauda amma kuya femin.
Yana gama fadan haka ya fashi da kuka
 Zannah kansa Afirgice yake kallon Nabil dan abin yabashi mamaki yajuya ya kalli Malam Dauda yace"Malam  kasheda wanan Sani shiyaje da Fandau aka daura auren?
Malam Dauda yace "shine kuma ni dama Mutari yaga yamin nasani  saide munbari ne kawai ya fadi kayansa kuma gashi ya fada.
Zannah yace "yanzu ina ita Fatiman Dr yanuna masa Fandau
Malam yace "ta matso kusa kanta asunkuye tafara ja dabaya dan tsoro Nabil ana nuna ta yameke a razane zaiyi inda take Baban sa yace "koma ka zauna.
Yakoma yana binta dawani irin kalllo yana so yaga fuskanta amma  arufe  Yana son ya gaskanta Fateeman sace meyasa wanan ranan tazomin da haka naci burin ahuwar mu dake zannuna miki matsayin ki agaban kowa amma Baba yahana.
Malam yace "Habiba matso da ita.
Haka Habiba tameke ta daga Fandau har gaban zannah hanunta yakama yace "tabbas wanan itace tawa Fatiman Fatima Muhammad Nabil shine mijinki?
Gyad'a kai Fandau tayi
shiru Malam yayi duk wanda yasan shi yasan ransa amutu kar mace yake da kuma mamaki da kunyar kunsan shikansa  yayi karya wanda zai iya cewa shine karyar sa ta fari aduniya dawane ido zai kalli matansa da yaran sa dayamu su karya yayiwa Fandau Aure da bako yana daga kansa yaci karo da matan sa sunzuba masa ido har yaran sa maza manya rasa mezai ce yayi ya sunkuyar dakai cikin damuwa Baban Nabil ya fukanci haka yameke ya karasa wajen Zannah yazube guiwowunsa  cikin tsananin bacin rai yafara magana
"kaicona kaicona Malam karene ni kamaye min gorbin uba asanda narasa nawa uban amma gashi yau nina haifi dan da yasaka b'acin rai wanda banta ba ganin sa acikin fuskanka ba atsawon rayuwata daka ina nema almarman ka zan yankewa Nabil hukunci agaban ka dan Allah kabani DAMATA na hukunta shi kar kace komai lefin sa babbane
Kai Nabil wandan auren naka na zanba cikin aminci kai tsaye bazance haramcecen aure bane amma ba abi yanda shari atace ba baka nemi kauren ta hanun waliyen ta ba bayan tana dashi koni waliyin auren Fandau ne amma ban sheda ba dan haka ba ka can canci zama da itaba tunda bakasan yanda ake neman aure ba shikan sa auren ka nafari kana England na dauki matar na gaimaka shiyasa baka san yanda ake neman aure ba ayanzu nake son karubutawa Fatima ta kardan sakin ta kai ba mijinta bane yarinya me daraja kamar ta ba matar ma karyaci maha inci irinka bane
Wanda hattta iyayen sa basu fi karfin ya musu karya ba  yameke yaje ya ciro fefa acikin littafin Malam ya karasa inda Nabil yake ya meka masa tareda biro yace ina son karubutawa Fatima saki.

Girgiza kai Nabil ya shiga shi
"yace wllh da wanan hannun nawa bazan iya rubutu saki ga Fati ba.
"idan baka saketa amasayi na nawaliyin ta ba zaka saketa matsayayina nani ne uban ka bisa umarni idan baka sake taba kadena amsa sunan d'ana kuma ta take anan zan tsine maka.
"Baba kaji tausayina wllh mutuwa zanyi idan nasake rasata.
"ai idan da zaka mutun da yafi komai sauki da anrage iri dan gaba bansan irin yaudaran da za kuyiwa a wani wajen ba kuje kusake wannan zanban nakuba musamman yanzu ta matar taka take juya.
Nabil zaka saketa ko kazabi tsinuwa
Ni *Habubakar Ibrahim damasak* nat.......
"zan saketa kar ka tsine min Baba.
"to zaketa
Yakarba yabara rubutu duk awani karkace saboda hannun sada dayake mugun rawa

 Afirgice Fandau ta bude fuskan ta ta fara magana cikin kuka da firgice

 "Baba kar kasa yasakeni kar kamayarni karamar bazawara wllh inason mijina
Nabil da dakawa yayi yatsaya kalonta cikin kuka
Tsawa Baba yadaka masa yace kazabi...

Rubutun yafara amma fa wahaye duk yajika fefan sai yankewa yake yaru buta
_ni Muhammad Nabil nasaki matata Fatima Muhammad bisa umarni mahaifina amma batanin komai ba ALLAH kayafemin_

Yajefar da biron yakifa kansa a kujera
Baba ya dauka ya karanta afili
 kowa tsaida yaji ba dadi
*dama haka saki yake yana da korjine wanda ko makiyin ka akayiwa sai kaji badadi*

 itako Fandau jirine yafara ibanta Habiba tayi saurin zaunar da ita

Baban Nabil yace "kwantar da hankalin ki Fatima ki godewa ALLAH agobe ba yau ba zan daura miki aure tunda ba wani idda akanki dan da ciki kika fita tunda kika haifu baku haduba bakida wani iddan sa
Kai BilAL kanason Fatima?
BilAL yace "Eh Baba badan kar ayi aure marar tushe ba da anan zan aura maka ita amma kaje gobe kaso da waliyan ka.
"nagode Baba.

Afirgice Nabil yajiyo atsawace yace "
Wllh wllh duk wanda ya aurin matata yafara irga kansa cikin wanda zasu yi gado da makara aranan ga Fatima naga uban daya isa ya daura auren ta ina raye. Yasake kifa kansa yafara rusa kuka kamar yaru ba necewa shine Shiddams  mutumin yafi SHEHU da gomna acikin garin meduguri adon mutane
Baban bai ceko maiba azagin da Nabil yayi dan yasan halin d'an nasa idan ransa yabaki zai iya bude baki yazageshi ma

Malam yayi Gyaran murya zai cewani abu Baba ya tashi yakara sa inda yake cikin kunne sa yarada masa wani abuda duk bacin randa Malam yake ciki saida yamurmusa
Daganan Malam yarufe da adua ya sallama kowa  Akkam yanawajen Ummi har zasu fita

 Malam Dauda yace" ina mesunsn nawa ita ko Fandau kuka take sosai Habiba tayi bangaren Mama da ita su BaGaji ansamu abin fada sai kira suke duniya abin tsoro abin magana irin wanan agidan Malam mama de shigewa tayi bata kulasu ba Hadim kam dama batazo ba
Baban Nabil shima bangaren Mama yashiga Fandau yaja gefe sunjima sannan yafito yatafi Fandau ta rungume Mama sai kuka suke har dare matan gidan suna shiga suna fita har zance yafara yaduwa gari itako Fandau burinta taga Bagana dayaran ta kawai

Shiko Nabil kinfita yayi agidan yasa Zannah agaba yana kuka har 10 dare shima Malam dannewa kawai yake amma jiyake kamar yayi kukan dan bai san hanyar da zaiyin ya gyara kuskure karyar da yayi ba dan bai zaci abin zai zoda hakaba amma ya danne nasa yake lellashin Nabil amma ina kamar kara masa suke sai zaje zaje yake ganin idan ya matsa shidin ma Nabil gaya masa magana zayi yasa Malam yafita wajen Abokin sa akaramin parlour sunfita sun barshi
Sai wajen 11 Malam yashigo ganin baiga tafiyan Nabil ba yace "Nabil yau kenan agidannan za ka kwanan?

"Eh wllh namai da matata sakin umarni nayi kuma na mayar zanga wanda ya isa yazo yafitamin da mata tunda na mayar ta Malam ka tekamin kar na rasata.

" a a Nabil wanan rigimane tsakanin kada mahaifin ka kana gani yahanani magana yace nabashi DAMAR sa amatsayin sana ma mahaifinka kaga dolo nabashi damar ko yanzu haka ma maganan daurin aure yake agobe karfe 8 nasafe Nabil tayi yayi yafada jikin Malam yanawani irin fitar da nunfashi saida Malam ya tsorata yace kaga tashi tashi kashiga ciki kasame ta idan tace kai tafiso akan BilAL sai insan yanda zanyi injuya abin bana son  kasake danuwa irinna wancen lokacin kasha wahala kaji.
 Nabil yace" tana ina?

"Tana wajen uwarta.
 Nabil yameke da sauri zaifita.

Malam yace "ina zuwa  kuma?
 "Malam wajenta.
Dariya yabawa Malam yace"amma saida safe ko?
Aiko waigen Malam baiyi ba yafice

Mama kam yau ba bacci ita da Fandau  fira kawai ake ayi kuka ayi dariya tayi mutukar mamakin yanda Nabil yake kula da Mama suna cikin haka sukaji anata dukan  kofan falo da karfi kamar za aballe duk suka sorata itada Fandau saida ta zo kofan Mama tace "waye?
Yace "Mama kibude nine.
 Mama tace "lafiya Nabil yace" kibude.
Mama takalli Fandau alaman ta shiga ciki tunkafin ta karasa fudewa ya fado ciki yayi falon yazube agaman mama yana kuka yana mata magiya yagaya mata yanda sukayi da malam
Mama tace"tunda yabaka dama ka shiga tana ciki.
Da sauri yayi hanyar dakin da akace Fandau take
Amma me yana shiga yatsaya jin wani irin dariya Fandau takeyi awaya

Haba my BilAL kasan fa aurenmu na gaggawa ne
Amma nide nafison koda  bayan daurin aurene ayi dan events wanda zai nuna munyi auren SO dakuma yanci
Nima na dandani irin abin da yan gatan amare sukeji
dariya ta sake fashewa dashi
tace kamar ya gobe iyanzu muna manne kana nufin daga an daura aure zaka rabani da
Mamata kenan  nima zanso ace gobe iyanzu muna manne.........
 Wani irin mari taji yasauka afuskan ta wanda saida ganin ta yadauke na wucen gadi duk da tasan yana wajen bata zata zai tabata ba aiko bol yadingayi da kita mama da take falo taji marin da gudu ta shigo taga Nabil yana ball da Fandau wanda gaba daya hankalin sa baya jikin sa tako ina dukan ta yake  Mama kasa kwatar ta tayi gashi da zafi safi yake dukanta aiko da gudu Mama tayi wajen ganin yana neman hallaka mata yar  tafita tana kururuwa neman

 akawo agaji
Shiko Nabil  tunkarfin sa yake makarta yana surutai
"aiko gawar ki bai isa yagani ba zan kashiki in yaso nima akashine kin huta.....

*Tofa shikenan kurunkus Nabil kafutar dani*

*B JATTKO*
[3/12, 8:50 AM] Hauwa: DAMATA

NA

BATUL ADAM JATTKO

🌈Kainuwa writers Asso🤝🏻

45
*M*atan gidan kowa da yaran su sunfito jin yan da Mama take niman temako ta san su mata ba abinda suka isa dan haka bata tsaya cemusu komai ba ta wuce part din Malam  tana shiga yana sama dan haka tadinga zan bada masa kira
"Sayinnan kafito zai kasheta."
yana karatu a parlourn sama yaji kiran Mama da abinda take cewa ai da sauri ya fito yana tambayan ta
Tana gaya masa ya fara taka stareas da sauri
Yayi ban garen Mama har yanzu Nabil dukan yakeyi duk ta gala baita

"kaiiiii wani tsawo Malam ya doka masa

Yana ganin Malam yabar dukan yayi wajen Malam din dafe da kirji yana wani layi kamar dan ganye amma sai ya kasa karasa wa inda Malam yake dan jiri yana iban sa kuma duhu yake kani
Lun ya zube awajen
Dasauri Malam ya karasa inda yake yana kiran sunan sa  ya dagashi ya daura kansa acinyar sa

Nabil ya kama hannun Malam ya fara magana cikin tsarkewar murya yace "Malam  Fandau ta yarda da auren BilAL taci amana na bata sona na rasata na....
Bai karasa ba yanemi nunfashin sa ya rasa jijiga shi Malam yafara
Bagaji tace "lah meta masa Malam  yasuma fa ko?

Jin wannan yasa mama ta saki Fandau tayi inda Nabil yake
Ita ma Fandau afir gice ta juyo aiko da gasken taga Nabil ba alaman numfashi Mama ce tayi yunkurin tauko ruwa a fridge ita ko Fandau tana ganin haka ta meke duk da kafanta yana mata wani irin zugi amma sai da ta meke da gudu ta karasa inda Nabil yake acinyan Malam hannun sa ta daga sai taga ya koma kamar ba rai wani kara ta kwalla daidai ta zuba masa ruwanda Mama tayi  hakan yayi daidai da farfa dowan sa amma bai bude idon  jin yanda Fandau take kuka
Dan ALLAH ka tashi Abu Fuji wasa nake maka wllh ne ban taba waya da BilAL ba bansan shiba sai dazunnan
Baban kane yace....

 Dasauri Malam ya doka mata tsawa Kiyiwa mutane shiru yadubi Ba Alta yace daukomin wayata
Fandau ta koma gefe itama goshita akumbure gashi ko ina ciwo yake mata  musamman hannun ta da take jin kamar ya targa d'ata
Mama tace" kai Sayinna dama mesunan ka yananan da wanan bakar zuciyar tasa wai meyasa duk masu sunanka suke hakane nekam Shateema da yaban shawara ban bari yasa maka mesuna ba dan shima Tajudin da gani irin halin masu sunanka yayi.
Shiko Malam yana kallon Nabil yasan ya farfado
Itako  Fandau sai kuka take amma bana ciwon da take jiba
Ahaka
Ba Alta ta kawo wayan ta durkusa  tameka masa
Kiran sojojin da suke tsaron kofan sa yayi dan lokacin doka yayi dole sai su zasu kai shi hospital
Su hudu ne suka shigo suka dauki Nabil zasu fita dashi itama Fandau ta meke zata bisu cikin tsawa Malam yace "ina zaki kuma tace" zan bisu yace"zauba." bude ido Nabil yayi cikin da shewar murya yace "kusaukeni  a hankali suka sauke shi amma yana dubawa yaga duk matan Malam suna d'kin shiko arayuwan sa basu masa ba sam kuma bazai iyace komai agaban suba yadaga ya Kalli Malam yace "Malam inason ganinku kaida Mama
Malam ya Kalli matan da sojojin tunkafin yayi magana sojojin suka fice suma matan suna zunbure zun buren baki suka fita dan de basu isa su furta wani abu agaban Malam bane
Nabil ya Kalli Mama yace "Mama dan ALLAH kiyi Hakuri nasan ban kyuta ba na shigo har d'akin ki na dakar miki yarinya bayan banwake lefina nada ba na daura wani nikai na tsani hallina dan nasan zai iya sawa ha hanani
( *Hasken rayuwa ta Aisha sada* ,)
Amma Mama nasan Fandau bata san irin sonda nake mata bane bata san yanda na mutu akanta bane da ko na mutu ba zatayi sha awan cewa za ta auri wani ba  yanzu lefin da nayi wa Fandau har yakai ta shukun tani da haka ina raye agabana take waya dawani kigaya mata inhar nine mijinta to ta kiyaye abin da zai tuzurani haka wllh wataran saide akwashi gawata
Tashi yayi ahankali yakara sa inda take ya zube guwoyinsa yakamo hannun ta yace "Fatina meyasa kika gujeni  meyasa tun a chatting da mukeyi baki baiya namin ganki ba shiya sa kike cewa kina gujemin nadama duk sanda nagane kewacece baki san rashinki barazana ne na rasa rayuwa ta agareni ba
Kiyi magana mana ya matsa hannunta wada yake mata ciwonne kuwa wani kara ta kwallah  cikin
Dama Malam da Mama sun fice tunda dama bakinta ne  duk basu ga fitan suba

"me yasa kika boyemin kanki Fatina?
Zubura baki tayi ta janye hannun ta cikin tasa nata ta daura hannnun cikin tafin hannun ta dayan tafara juya kai
"Ayyya mata nine ko ya sake jawo hannun ta fizge har hannun ya kumbura yazubawa hannun ido yana gani yasan tar gadene kunsan dan ball baiwani dauki targade abakin komai ba dan she tunyana yaro ya iya gyaran targade idan yayi da kansa yake gyara kayansa ko idan acinkin abokan sa wani yayi yana gyarawa
Fakon idon ta yayi yaja hannun nata k'ara tasa jawota yayi jikinsa cikin dabara ya hadeta sosai da jikin sa yanda zata saki jikinta yana mata wani wasanni har ya fara gyara mata hannun  ita ko Fandau jinta aduniyar da tajima tana nema yasa tayi lamo saida taji zafinyayi zafi ta fara jan hannunta tana kuka da yaga kukan nata zaiyi karfi kawai saiya hade bakinsu waje daya  amma yana jan hannun wani kara tasa alokacin da yatsan ya fada ya gyaru kenan sake hade bakinsu yayi yanawani irin fitar da nunfashi itama haka sai da yayi facale da kayan jikinta da dafi zafi yake aika mata sakonne yazame mata tamkar wani mayunwacin zaki saida taga yakusa isa babban fada duk da itama ba abinda take so irin abin amma ta daure tameke da karfi ta fusge ta tunkuda shi tameke
Daga kansa yayi yana kallon ta idonsa yayi jajir cikin wani irin muryan da yake janyoshi cancikin makogoro yace "me haka Fatina?
 itako sai kare jikinta take tana jada baya da rarafe ya karasa inda take zai kamota ta matsa
"yace mehaka?
"kai kai zan tambaya mehaka zakazo har cikin dakin uwata kanemi kayi lalata  dani  bayan kasakeni kaban dinbin jama a
 "Mata na mayar da kefa wllh karkimin haka kar.

" karka renamin hankali mana kana nufin Fandau din  dane daka yaudara ka aura
a gaban din bin mutane ubanda ya haifeka yace bani da iddan ka tun dana haifu bamu haduba dan haka bawani maidani da kayi.

"kiyarda indaura miki iddan yanzu wllh dole su hakura subarmu."

"Lalle Nabil  duk dama nagane jikina kake so fiye da komai wllh banzaci abin har yakai haka ba karasa inda zaka nemi jikina sai dakin uwata."

"wllh bakiyi karya ba inason jikinki kuma ko aina zan iya neman sa tunda ina son komai naki inaso.
Cikin karaji tace "dama nasan jikina kakeso ai duk sanda jikina yadena baka sha awa zaka dena yayina ne kawai nikuma yanzu kadena moran jikina dan......
Cikin muryar tausayi yace" karki min haka wllh bazan iya daukan wannan horan ba idan baki amince dani ba wllh nakai gejin komai zai iya faruwa dani yana maganan yana dafa maransa
Tana ganin gasansa jitashi gaban ta yayi mugun faduwa  da sauri ta dauki riganta ta sa shiko yanda ta sunkuya ta dauki rigan ne idon sa akan dukkan halitun jikinta da yafi so maranshi  yasake dafewa maransa da yakeji kamar zai kashi shi ya kwata yana birgima dafe da maran "yanzu mata bazaki ji tausayi naba itako tama gasa juyowa dan ita tsoron sama takeji
Ayanda yake
Karasa wa tayi gaban gadon ta dauki Akkaram da yake bacci ta tayi hanyan waje saida take bakin k'ofan fita tajuyo ta kalle shi yana nan inda yake yana ta juyi

Tace "shikenan tunda bazaka fita mana ad'aki ba nina bar maka.
"dan Allah karki fita wllh zan iya shiga kowane irin hali idan na rasaki.
Kiduba halinda nake ciki."

"Wllh  bazanji tausayinka ba nagaya maka kadena samuna da araha."

"wllh ke bame arahabace idan kinason duk abinda na balla ka aduniya zanbaki kibiyamin bukata yafi."

Abinda nake so dayane awajen kuma ka tabbarar minda bazan samu ba shine kace kana sona."

"idan ana magana kidena kawo banun so Fandau sonki yayiwa bakina girma da na furtashi idan kuma kinaso nafurta ne _INASONKI INA SONKI_ ."
"Taya zanyar da kai bayan kai din makarya cine mayaudari kayaudare ni kamin karya har gaban iyayena kace nabi wata saudia bana sonjin son naka dan bansa meshi asanda nake soba taya zanyar da da kai bayan nasan kai waye ne afannin yausara.

"Wallashi  yanda nake sonki ban tabajin ina yiwa wani abuso kamarki ba kiyar da dani ki bani DAMA ki karbi sona zaki sameni mai amana akaru na 2."

"a a Rike abinka dan banyar da dashi ba."

dukan kirjinsa yayi da karfi Wayyo zuciya bazakayi magana ba kafito kanuna mata son nata da yake dankare atare dakai baka da amfani inde bazaka yi magana ba kafito zuciya Fatina shiyasa nace miki sonki abaki bazai faduba.
Zatafita mamakinta kawai sai taji fashiwan kukan Nabil tana juyowa taga kuka yake wuiwui yana dukan kansa da kirjin sa rasa ma yazata yi tayi dan bazata iya fita ta barshi acikin wannan haliba dan tayi mugun tausayin sa gashi idan ta tuna gargadin Dr da Baban Nabil sai taji idan ta amince dashi yanzu ba ta kyuta ba amma sai wani zukiya yace idan yamutu wa akayiwa asara dama ba anacewa tsakanin macce da miji sai ALLAH ba kawai saita fara takawa ahankali har kinda yake shiko kukan yake cigaba da rusawa
Karasawa tayi ta zauna ta daura Akkam aciyar  ta sannan ta dago habar Nabil  idon sa yayi ja da fuskan sa
tace "ka dena dukan kirjin ka haka mekake sone.
"kenake so much.
"To aigani gaban ga"
Kawai sai ya jawota zan hade bakinsu tayi saurin girgiza kanta
Tace "tokaga abinda yake tabarar min da jikina kawai kake sha awa kenan
 yace "komai naki inaso nide nasan inason komai naki."
Ganin bazai yuwuba saida lallami yasa tayi da baran gwara ta lallaba shin
"to kaga yanzu bai kamata muyi wani abu adakin Mama ba kabari da safen asan yanda za ayi."

Dasauri yace "to mufita agidan.

"a a Abu Fuj baka tsoron yanda mutanen gidan zasu fassara ni yanzu ma  tun dazu nakasa fita a part din Mama amma haka ma ban tsira ba har na ake biyoni da bakaken  magan ganu sai ma gobe idan yaransu da suke aure sunzo  zanji sauran."

"kigayanin suwaye suka gayamiki magana?
Wllh bazan bar duk me kunta ta mikiba. "
Tace"a a kar kaga lefisu ni cime babban lefi ai abinma yazomin cikin sauki banzata zaizo da haka ba."

"to yanzu yakike sonnayi."

"Kajen dasafen kadawo."

Kamar wani yaro haka ta dinga lallamin sa dakyar ta tasamu ya yarda zai tafi amma saida yadan rage zafi

Yana rugume da Akkam suka fito falo yace "wllh duk  harda lefin Dr wanan yaron cemin yayi wai dansa ne shiyasa nake son ki gayamin gaskiya ya akayi kika gamu da su dashi shegen BG din."
" duk gobe zakaji.
A parlour ma daker suka rabu dazuman shikam anan sai kwana dan yajima  da sallama escort dinsa ba inda zaijen sai anyita ta kare
Ita ko Fandau tana samu yana fita tarufo kofan tana cewa zaka gane kurinka tunda nasanu *DAMATA Bazan bari DAMAR* ta kufce min ba saina rama duk abin da kayimin  amma har ta kwanta kalmo minsa na soyyyya daya furta mata ne yake mata yawo akunne gakuma kamshin turaren sa da tajima tana mafarkin sa ajikinta wani k'aran dadi tayi da tatuna wataran ko tace nanda dan kankani lokaci zata amarce juyi tadingayi tana murmushi

shima anasa

ban garin hakane kwana yayi yana juyin dan ALLAH ALLAH yake gari yawaye abashi matar sa banda suranta ba abinda yake bijiro masa
Sai asuba yasa mu bacci bayan yadado daga sallah falon da ya kwanan yakoma yakwata akan kujera saiko yasamu bacin ya kwashishi cikin mafarkin me dadi

Washe gari Fandau bayan anyi sallan asuba ta durkusa ta gaida Mama tace "Mama inason naje gidan Bagana Mama ta kalleta taganta da shijab har katsa  kibari ita ma zata zo anjima kad'an zaki ganta idan kikaje sauran yan uwanki idan suka zo bazasu ji dadi ba.
"Mama idan na zauna ma awajen su ba fita zanyi ba  ba komai zai kawosu basai sai yada magana.

Mama tace "to kema kinsani dole ki zauna ki karbi lefinki  kafin komai ya wuce ai kinyi abinda ba atabayin ba azurir ku dole ayi maganan kuma dole ki karba kina ji jiya ma da nafita wajen girki su Ya Karu ba maganan da basu gayamin ba ashe su amin bai musu dadi ba wai nayi muku rokon Allah duk kunsamu masu kudi  suke bakin ciki da Bagana ma balle ke  wai zaki wari BilAL dan gidan Alhajji Maina Gange masu kudin garinan ga na hada jini da Nabil wanda zamu lashe dukan dukiyar sa nayiwa matar asirin ancire mata mahaifa Lalle nayi aiki,
kede kinsan ba rabuwa zakiyi da magana ba yanzu idan ki kaje gidan Bagana haka zaduce kinnuna ban banci kizauna sai andan kwan biyu.

Fandau tace " Mama idan nazauna agigannan to plan dinmu da baban YaShid bazai yuwuba ba YaShid yana da shigen naci akan abinda yake so kinga jiya ma wai saiya tafi dani dakyar nalallaba yafice yace agidan nan zai kwana idan ina gidan Bagana kinga bazai gane ina canba."

"shiru Mama tayi can tace"gaskiya bai kamata kije gidan BAgana ba idan dole sai kinfitan gwara kije gidan Dr Mutarin yafi sauki idan Tazo taje ta sameki ajan da sauran yan uwanki yafi kiware kidan Bagana kije ko.

"to.
Fandau tace dande baza ta iya musu da Mama bane amma ita gani take gidan Dr Nabil zai iya zuwa kuma ta b'aran da zaiyi agidan yafi nanan dan ba shayin kowa yake ba shi yasa ma Dr din yace ta zauna anan.

"to Mama ki kira drive kigaya masa zan fita ta kofan baya.

"a a wai yanzu da asuban nan zaki tafin.

"Mama idan gari yawaje ya tashi ya ganni ai zai san inda zanje."

Mama tace "to ta kira drive yace ta fito dan dama amakotan yake gidan Malam na saukan bak'i

"amma zaki bar Dauda ko? Dan ban gaji da ganin saba."
"Mama ni kingaji da gani na?
 ta fadi haka cikin shagwaba

 Mama "a a dan kin ce zaki tafine."

"wllh Mama nima ban gama abubuwan da zan gayamiki ba balle na gaji da ganinki dan de idan na zauna da matsala ne  kawai.

"to ALLAH yatemaka Malam yace cikin satinnan za agama komai amma fa yace yaran zai raba muku keda Hadim kowa yadauki 2 - 2.
"What! Mama yaran za araba?
"Eh adalcin dazaiyi kenan a tsakanin ku nima nayarda da hakan dan Hadim abin tausayi ce bazata kara haifuwa ba kuma idan akadu ba itama tana da hakkin na shayarwa.
Fandau bataji dadin abin ba taso abata yaran ta tanunawa Hadim bata isa ba amma bata da iko akan abinda Malam ya yanke
Cikin muryar tausayi tace "to Mama amma Fujjirat za abani na hada da Akkam ita tarike su Maaf ko?

"Eh nima zanso haka itace macce ita yaka mata abaki dan nima haka kurun nake son yarinyar.
Fandau tace "yawwa Mama shikenan zan tafi."
"To kigaida Habiban au
Yawwa anjima zan bada wani abu akai miki zan rubuta miki yanda zakiyin amfani dashi.
Fandau tace "to ta meke
Mama tace "kishiga kigaida matan gidan  ki musu sallama.

Ranta ab'ace tafita dan ita inba dan Mama ba da baza taje wani gaida su ba dama  bata zuwa gaida su bare yanzu da tayi abin fad'a

 part din Bagaji ta fara shiga amma sai da taci kunu takoma Fandau dinta nada da suke shayi tukun ta shiga  sallaman ta maciki ciki tayi tasa meta akan salllaya tana jan carbi yaran kuma duk suna karatun Qur anin ta zauna a kujera Meram ce tafito a d'aki tace "Ya Fandau sannu da suwa.
Murmushi "Fandau tayi tace  "iyeee Merama anzama yan mata."

"YaFandau kekuma kin zama yar gayu."

BaGaji ta sallame lazimin
Tace"Merama ta zama yan mata amma ina roka mata Allah  kar tayi yanma tanci irin naki nashiga duniya a auri dan Duniya daga baya azo abayar ta bazawara naki ma kadai ya isa dama ance duk gidan babban malami ko babban dan siyasa sai ansamu abin fada yanzu gashi mukece ki ka janyo mana abin fad'an....

Fandau azuciyar tace wanan kam *HUKUNCIN ALLAH* ~ne inji Garkuwa muna jira~

 afili kuma katse BaGaji tayi da cewa
"ina kwana dama Mama tace na shiko mu gaisa.

"yo ai dama ko baki fada ba nasan ke akaran kanki bazaki zo gaishimu ma da dakike cikin Summa da kwarkatar kima bakizo ba balle yanzu da kikaga ma kwancin manya ai ita ma uwar taki bakomai ne yasa ta turoki ba dan muga yanda kika komane,
 koda tana turoki gaida mune to agaban mu akayi komai ke sakkeyace bazawara saide aci wanda aka tara ke har kin isa ki auri mijin Hadim baturiya maganan auren jikan Kange kuma fitar sunfi karfin ku saide kiyi zawarcin cikin almajiran kidan wada yaga zai iya ya dauka...
Itade Mekewa tayi tafice  part din Bakaru shima hakan ne yafaru tanayin sallama
 Bakaru tae"lalle yau wanake kani ya shigomin kamar Fandau lalle Duniya yafi gaba ba ruwa iya jima tunda yakoyawa Fandau shigowa inda mutane suke  Duniya makaranta to zauna mana manyan zawarawa agidan Zannah.

Fandau tace "a a basai na zauna ba Mamata tace na zo na gaidaki ina kwana.
"ba shakka dole ki gaidani atsaye dan kinkai ai kin aurin Shiddams kina shirin auran jikan Kange kinga ai dole ki gaidani atsaye.
 dasauri Fandau ta fita dan ita bata daukan raini tana iya biye mata
Sai part ita amarriya gidan  wada yanzu idan mutum yagani zaice  tariya mama shigowa gidan dan ita take bin bayan Mama kuma ita tanada yara manya mama bata samu haifuwa dawuriba
Ita ma sallama tayi mata tace BaAlta  inakwana.
 cikin fara ata amsa dan kita bata da halin wadancan kawai tana tsoron sune ita ma Fandau har tadauki jikanta wada aka kawo mata yaye dan gidan Amsatu wanda take sa ar Fandau ce kuma dama suna dan shiri kadan da Fandau tace "Bani yasunan sa Sultan sunan Baban kune tamasa wasa tace Bani zandan fita idan Amsatu tazo ta sameni gidan Dr na polo.
Ba Alta tace "to zangaya mata Munyi waya kuwa tace zata zo zan gaya mata gwara kije can nima banso zamanki agidan nan ba kwara candin yafiye miki kafi amaida auren ku dan wllh abun yana damuna saida nasamu Malam jiyana ce amma a addini yasan kinada idda yabari ake zancen auren wani shine yake cimin dama shirine da aurenku nayi murna ALLAH yatsareki da sharrin wannan matar tasa.
"Ameen Fandau tace tareda cewa "Baani ina  Nana?
"ai am mata aure itada inana da Ramatu har sun kusa shikara.
Abin yabawa Fandau mamaki aurin gidan suna yara yanzu yaran da kannen Bagana ne har anmusu aure

Afili tace" shiyasa naga kowa su bangan su ba.

"eh ai duk zasuzo yau inaga dan Nana muyi waya tace zatazo itama suma sauran nasan iyayen su sungaya musu.
"to Bani natafi.
"ina Dauda?
"yana wajen Mama
Tana fitowan takofan baya tafita dan yansa idon Almajiran tasamu driver yana jiranta ta shiga baya yaja tace "dan gwaza ashe har yanzu kaine kake jan matan gida.
 yace "Eh Wllh ansha canzani gidan wasu  Hakiman amma sai nasa Malam yane mamin alfarma inajin dadin aiki da gidan Malam.

Bayan yasauketa da zauri shige gidan jin kukan Ummulkkairi  tanayin sallama dukka suka juyo har Dr suna folon "Alhamdulilah  amma ya haka da safen nan ko kema kasa baccin kikayi kamar na ummuna kingan ta tun dare muke fama wai sai an kaita wajen Aunty Kirki.
Fandau tana dariya tace
"Ayya kharina iyeee yar gidan wacece taware hannunta Khairi tazo ta gudu ta dakata sama
Tace"yar gidan Aunty kirki ce  tama haka suke ko amakaranta tazo shiyasa takewa Fujj ma

"ina Nol Nol dinna.
 Haris yace "na bacci
Fandau ta durkusa ta gaida Dr da Anuty Habiba
Habiba tace ina Akkam din kuma.
"Yana wajen Mama.

Habiba tace "to ya akayi kika fito da wanan kuban safen haka.
Fandau ta gaya mata abinda yafaru

Habiba tace "Ayya kinshiga hannun maza.

Dr dariya yayi yace "dama ai nace ta kiyaye Shiddams idan ransa ya baci hauka yakeyi  shiya sa a makaran ta har malamai suna tsoron sa dan idan ransa ya baci baya musu ta dadi yanzu ya hannun?.

"Da sauki ai  tace
Fandau tayiwa su Nol  da kharat wanka Haris da kansa yakeyi bayan sunyi  break fast Fandau ta kunna wayan ta hau YouTube  tasauke film suna kallo taka message yayi yawa a whassapp dinta ta cewa su Kharat     kuje kuduba kar su Momy subarku da gudu yaran suka fita ita kuma ta bude whassapp taga ashe cakwakiya ake sosai acikin group nasu Habiba ta gabatar da ita a matar shiddams ta biyu kowa yana fadan albar kacin bakin sa sosai suke fada aiko sai ga Hadim dinma ta fara ruwan asher tana cewa ita tafi kalfin ta zauna da kishiya dama ita tasa ya aureta dan ta haifa musu yara amma yanzu yasaketa da ganan tabada labarin Fandau ashe har da wanan video da Nabil yayiwa Fandau a haduwa suna farkon ta tura musu
Wasu dayawa gan gancin Hadim suka gani wasu tausayin Fandau  dan dayawa sun bita private suna gaskanta abin wasu kuma suna bayan Hadim ana ta zagin Habiba Farida amarriyan Amjad wanda basa shiri da Hadim saboda kishiyar ta Zahra kawar tace itace tayi ta tura rawa tana cewa woohohho yau ranan farin ciki da murna
Itama Habiba tace "dakenan take Fandau yazu ko Fantastic take nan danan ta fara tura pic din Fandau  nan danan aka fara wow beautiful lady Amina matar BilAL dayake tasan komai ita ma tace "woow kaji yar kanurin asali ai amma kawas kin iya zabe fa nima kine mowa my sweet dina iran wanan  ta haifa mana yariya kamar Fujji Biebiee  ai nan danan akafara turo pic din Fujjirat ana cewa Wllh suna kama sosai
Hadim tace "nace muku kudena zancen ta wlllh jiyannan yasaketa dan kunsan nafi karfin zama da kishiya ita ma muna fukar Habiban da taturo maganar nan kuma har agidan ta zauna ita ta mayar ta mutum  ita taci amanata zan sameta har gidanta ashi ita tana bakin cikin duk mijina yafi nakowa kudi duk abin da nake mata bata gani tacimin amana ni Hadim sai gani da ido wllh.

Ita ma Habiba zata maida mata da ganan de matar Usman da taga abin zai b'aci ta *Removed* din kowa Tarufe *group* din
Daga nan Fandau tayi dariya afili daba a rufeba da sunji murtani dagan nan takoma  bude yan private
 _slm sunana Farida matar Amjad Abokin Shiddams na san kinga yanda muka yi a grp amma naso ace kin fito kin nuna musu  ba kya tsoron  su kishiyata kawar Hadim ce kinga muna zaman lafiya amma Hadim gaba take dani har tafi kishiyar tawa kishina kullum burina naga yanda zatayi idan akace an mata shishiya cikin ikon Allah wai yau sai ga Hadim da kishiya kishiyar mana  BANGIRMA wacce ta game gida da yara ashi duk soyyyyar Hadim da Shiddams zai iyayi mata shishiya wai yayi aure dukda ita ta hada kuma tace ta raba wllh nayi murna ALLAH yasa maganan mmn Nol kaskiya ne da tace anmaida auren kuna da gaske ke kanwar Dr MD?_
Murmushi tayi ta maida mata Ripley
_Ameen Waalaikumus salam Ayya duk naji labarin ku abakin Aunty Habiba bacce bansani ba hatta pic dinku kai kunsha zuwa gidan ma kina ganin ku amma bana fitowa Eh Dr yayana ne kuma auren muda shiddams banajin akwai ranan rabuwa sunana Fatima Muhammad Zannah Gargar nima inason mukasan cetare FARIDA Amjad_

_Masha ALLAH dafatan zansamu karbuwa awajenki muyi zumunci maganan Grp kuma awai wani Grp shima yawanci mumatan abokanne aciki kinga yanzu haka zancen yayadu duk Grp na mu zancen ake kuma kinada masoya duk da itama Hadim tanada nata masoyan zan sa kiciki amma inason idan kinshiga karki kiyi  sanya kinuna kema kinkaisu kibude idon ki sosai kishiga awayen idan kika nuna sanya suka renaki wllh abin bazai miki dadi ba ga amarriya usman ma tanason kuyin zumunci dan itama kishiyar ta kawar Hadim ce kewani bayanin masai kinzo London._
Fandau tama yar mata
_Eh sis dama Aunty Habiba ta gayanin halin kowa nagode_

Haka Tayita budewa sakonni wasu su zageta wasun su kuma irin FARIDA ne

Ummi dakira Nabil yace yana Gargar

 tace ,"to kazo gidan gashinan antaru za ayi meeting kai kawai ake jira.yace "to
Amma saida yashiga bangaren Mama yagaisheta yanata raba ido yaga inda Fandau zata fito sai yaga shiru yadauki Akkam yana masa wasa yace "Mama amma Akkam yafi su Maaf kama dani ko?
Dariya Mama tayi tace "gasunan de duk kodaddun rana.
Dariya yayi yace
"Mama ina take ne?
Mama tace wah?
Yace "Mama mata mana.

"Wacece kuma mata?
"cikin shagwaba yace "matata mana uwar yarana.

Dariya mama tayi tace "yanzu agabana kake kiran matarka mata baka kunyata.
"Haba Mama wllh ni nafijin kunyar Ummi ma akanki dan me d'a zaiji kunyar uwar sa bayan itace maganin kukansa Mama kisa baki abani matata a yau wllh agidan nan na kwanan falon bak'i kiga jikina duk sauro sun cijeni ga rashin matata duk banyi bacci ma.

"Ayya Nabil dina zan maka iya kokari naka ka koma da matar ka amma kaima ya haka daka cewa kazo kanemin biko sai kazo ka hauta da duka.

"Mama rainane ya baci amma nabata  hakuri tana ina?
Mama tace
"Ayya inaga tashiga gaida matan gidan.
Shiruru yana zaune har Ummi ta sake kira tukun yace Mama akirata mugaisa zanje nadado?

Mama tace "jeka kadawo din kaga inaga kiran Ummi kane ko?
kafin ya bata amsa akasake kira mekewa yayi yace
"Mama inazuwa  amma da Akkam zanta fi FUJJI ta nason sa.
*Gidan su Nabil*
Iyayen Hadim har kishirar uwar ta da Abba Musa yayan su Ummi da Baba Inusa kanin Baban Nabil da Inna zainabu da sauran yan uwa najiki bayan Nabil yashigo aka gama tsara komai ayanzu kam mamar Hadim tayarda kuma ta bada hakuri zata janje karan da tayi dan ita ma tana ganin Fandau tayarda lallle ita ta haifi Fujjirat babanta ko rasa bakin magana yayi dan Malam yana da kiba sosai kuma dan shima yayi karatu awajen Malam saide yagayawa wani Malam ciki bacin rai yace "amma kai ma Alhajji ba ka kyuta ba yazaka sa shi yasaki matar sa kenan kayiwa wanan yar banzan abinda take so dan uwar ba akara aure  nakara da uwar ki sha sha sha
Ai kodan darajan ubanta ba zakasa ya saki matar sa ba kowa agarin nan yana son had'a zurua da Zannah ni kaina saida na nemi wata yariyar Zara ban samu ba kuma har yanzu ina son koda yarana ne su samu saboda ai a aure addini da nasaba akesu sukuma sun tara shi
Inna zainabu haka tayi ta b'a batun fadanta tace kuma  Fandau bata sakuba    Nabil wani dadi yaji dayaji abakin Inna dan yasan Baban sa baya wuce maganan ta Hadim kam da kuka ta tashi da gudu tana cangala kafa taje d'akin Jidda ta zari key dinta yanda take Afirgice ne yasa Jiidda tace " "lafiya Aunty?
Hadim tace "fita zanyi.
"wazai kaiki?
Hadim tace "nizan kai kaina.
Jidda tace "kawo najaki karkiyin tuki cikin b'acin rai kuma ayanda kafanki yake ina zaki iya tuki.
wulla mata key tayi suka fito saida megadi yabude suka fita Jidda tace "Aunty ina muka nufa.?
Hadim tace "polo zaki kaini gidan Habiba naji ance wanan kucakar tana gidanta.
"To Aunty mezaki mata karki je kikara jawo wani abun kuma bayan wanda ake ciki ma ba agama ba.

Hadim tace "gaskiya ne ba agama ba bakuma za agama ba inde muddin akace za a mayarmin wanan yarinyar tazama kishiya ta wllh baza agama ba.
Itade Jidda shiru tayi dan dama bata fiye magana ba

*Porlo Gidan Dr*
Gidan bakowa sai Fandau dan su Habiba sunfita ziyara dan dama uwar Dr yar meduguri ce
Har Habiban tace su tafitare Fandau tace zatayi bak'i dan ita Bagana kawai take son kani tana cikin chatting da Farida taji Hadim ta fado gidan
"ina babbar muna fukar Habiban ta kanta zanfara dan ance muna fukinka taburman ka bata san tayi gangancin jadani ba ko kigaya min tana ina?
Fandau ko daga kai batayi ba duk da faduwan da gabanta  yake ta dake tace "batanan idan tsakone ajiye idan tazo yata gani.
Hadim "tace ai yawuce karfin sako saide gaba da gaba   nida ita

Kekuna ina miki kashe da kiyarda ki shiga gidana gwara kiyi lefin da za amiki dauren rai da rai kidauwama agidan yari yafi miki dan da kishiga gidana amatsayin kishiya ta kwara adinka yankan naman jikin yafi miki sauki.

Fandau tameke tana murmushi tace "ba kiji anci kaji tsoron wanda ka kyutatawa ba kin kyutata min na aurin shiddams da ko ayar aikin gidan sa ban isa na shiga ba saide gashi na saka miki da halin mu irin na wanda aka kyutatawa mijin ya kamuda da sona ko jiya tare muka kwana dama nasan baza kiso zamatani ba sai dole jinki wani mawaki yace zamada da kishiya tilas ne badan uwar gidan tasoba  ina baki hakuri da rushe miki bajad danayi kintsara rayuwan ki daga ke sai mijiki da yaran aro amma kinyi gangancin barin zuciyar miji  harna samu wajen zama kekan kinsan baya yayinki yanzu dan bakisan inda ya kwana ba ajiya wllh jiya....
Daga hannu Hadim tayi zata mari  Fandau ta rike hannun Hadim da daya hannun ta dayan kuma ta fara shafa fuskan ta tana  murmushi tace "haba Halima kiduba wanan fuskan fa kinsan darajan sa awajen Shiddams amma kike gangancin tabashi ai atake kokuwa ya kacame da sauri Jidda ta dauki waya takira Nabil tace "YaShid kazo gidan dr na folo Aunty Hadim da Fandau suna fada bakowa sani  ai Nabil baikarasa jiba ya fita da gudu ya fada mota escort dinsa suka rufa masa baya

Abin mamaki ance alaman karfi yana ga mai kib'a tode A bangaren Hadim ba haka bane kodan bata da lafiyan kafane dan Fandau tana tureta tayi baya jikake dum ta yunkura zata tashi Fandau tayi saurin hawa ruwan cikin tunkarfin ta tafara jigganta ita ma Hadim akwancen ta fara dukanta amma tako ina Fandau tafi kwaranta dan ma hannunta yana mata ciwo Hadim kira take ke Jidda bazaki daki wani abu ki maka mata ba ki dauko wancen flawer ki doka mata ko sanda.
Jidda tace"Aunty ban iyaba yazanyi
Sakanin polo da
 G R A bawani nisa dan haka abin baiyin nisa ba yashigo da gudu shima yayi mamakin ganin Fandau  akan Hadim dan shi atunanin sa zata sumar masa Fandau kafin yazo har yana aiyana irin matakin da zai dauka akanta saida yaso yayi dariya ya karasa idan fuke cid'ak ya dauke Fandau kamar yanda ake daukan jariri ai Hadim dingi sawa tayi ta karasa gaban su tace "my ayanzu na keson kacikawa yarinyar sakinta kaji yada dalilinta aka hada fada cikin friend dina kuwa?
Wani kallo Nabil yayiwa Hadim yace  "yanzu idan da za ace inyanke kigiyar ki 2 da yarage na Mata daya zaizo Wllh zanyanke wani irin fusga  Hadim tayiwa Fandau  datake rugume ajikin Nabil Nabil yace idan kin kuskura kika sake tabata wllh zansa abitar minke idan kinnusu inason zanyi magana daku. wani ruwan ashir Hadim tazuba tace kasa afitar dani fa kace tayi kan Fandau daya ga abinnata bana gare bane kawai yakira escort dinsa yanuna musu Hadim dayan yace sir Madam cefa.
Nabil yace "kunfini saninta ne wani irin kuka Hadim tasa wai yau Nabil da yake kishinta har zaisa k'artai su fita da ita cewa tayi kumarni zan fita da kaina Jidda tameka mata sandan ta da dingisa tafita
had'a fuskan su yayi  yace "she mata jarumace wani irin wasani yafara da kita saida tabari ya gala baita fiye da jiya harda kuka sannan ta tun kudashi tayi hanyan wajen ta nacawa "ga matarka data damu dakai har take fada akan ka nabar mata ai ni yanzu sai nazaba na dirje ta murda kofan zata fita cikin kuka yace "idan kinfita adakin nan wllh na hakura dake  Fandau na tabatar da ba kya sona kuma natsik.......

*kas masoya inganin korafe kofafen ku akan rashin samun posting akan lokaci nima ba haka nasoba naso nagarasa nafuta amma kuyi hakuri ankusa gamawa*

B JATTKO
[3/12, 8:50 AM] Hauwa: *DAMATA*

     


       

           

             
                 *NA*


*BATUL ADAM JATTKO*




*46*



🌈Kainuwa writers asso🤝🏻

Da sauri Fandau ta katse shi da cewa "ka tsinke me?
 cikin wahala idon yayi jajir yace"na tsinke da al amarin ki ba kya yafiya  baki da tausayi kina da halin irin na masu daurin kai."
Fandau a jiyan zuciya ta sauke jin abinda ta zata ba shi bane  dan haka ta bude tafita ta rufo kofan

Shiko Nabil maran sa ya dafa yadin ga shafawa yana neman mafita to ya zaiyi ne yanzu ya Fandau take son yayi ne kawai wani tunani ya fado masa  yanda tashiga damuwa jiya da Baban yace ya saketa gashi yanzu mata tsorata da yadauko magana a garkace tabbas tana son ka wana ka kawai take sonyi murmushi yayi yace inko haka ne tunda taki na lallami ka gwada wani daman kawai  yana kwancen saida yaji  yadan samu nusuwa ya meke dan yafita,

Fandau tana fita taji ana knocking tabada izinin a shigo wazata gani cin karo tayi da fuskan yar uwar  ta Bagana duk sukayi kan junan su dan duk yanda suka canza ba zasu kasa kane juna ba "Baganata.
"YaFandau
Suka rungumi juna suna murna sai kuma suka saki kuka  saida su kaci  kukan Bagana tace "YaFandau  dama afiran muna k'ashe kince zaki bani mamaki  YaFandau gashinan kin bani Mama tagaya min duk abinda yafaru dake yar uwata,
Kinga abu muma kin bar barmu cikin kukan rashiki gorin nede muka sira dashi dan Baba yarufe bakin YaFandau nasan kaddara ne da rabon yaran nan amma munyi kuka nida Mama.
Fandau taja hannun Bagana suka zauna  cikin kuka Fandau tace "Wllh nima kullum keda Mama ne araina haka zan zauna nayita fira ni kadai nayi muryarki, nayi na Mama amma Abu FUJJI kullum yana bani hakuri haka,
Yawwa ina yaran dan shine yagaya min kin haifu Tajjudee da kuma mesuna ta suna ina Bagana ta daga kai ta kalli inda Shatiman yake  yarike hannun Judee  Fandau tabi inda Bagana ta nuna mata wani hadeden gaye tagani yana d'auke da wasu kyawawan yara baye ba Macce sak larabawa yaran dan dama Shateema sadaka yallah ne dan yanzu haka baisan inda iyayen sa suke ba ankawo shi wajen Malam tun baifi shikara 5 ba awajen Mama ya girma  ga dama Bagana ma fara ce tas dan ba abinda ta bari na Mama farin ar wani kore yasa Fandau ce tabiyo Malam
Fandau hannun ta narawa ta meka hannun Shattema ya meka mata mesunan ta wanda Bagana take kira da *Isseta* wato yar uwa ayaren shuwaa
Yameka mata Fandau ta rungume yarinya  tasake jan yaron mata rungume
Yaran sai kamshi suke kana gani kaga yan gayu

Fandau tace " yanzu Bagana wannan yanan kike ke Allah yabawa Allah Mungode maka da wanan ni ima da kamana.

Bagana tace "YaFandau mugode masa kam godiyar mu ga Allah ba zai taba karewa ba tun randa akacemn    wai Fujjirat yarmu ce Maaf da Bilal na mune nake ta godewa Allah  yanzu kawai jira muke ayi agama,
Abamu yaran mu,

 Akkaam ne awai ban gani ma dan ta gida muka biya Mama tace wai YaShid yafita dashi.

Fandau tace "ka marya yaya yafita dashi?

Kafin Bagana taba ta amsa
Shattema yace ni barin kowajen zama bazan samu ba kenan.
"Fandau tace "lah YaShatteem wllh ina murnan ganin yarana ne zanzo kanka namaka godiya yanda ka mayar min yar uwa babbar yarinya haka
Shateema murmushi yayi yace "Aidama my sweet  big girl ce.
Dariya sukayi
Yace" to ya bayan saduwa.?
Tace"kaide bari YaShattee abubuwa sun faru dayawa.
Shateema yace "eh harda na alkairi a ciki ai.
Kafin ta bada amsa sai ga Nabil yafito,
Yana cewa "sister kune Shateema yameke ya meka masa hannun suka gaisa
Bagana tace "kai YaShid ashe kana gidan.
 "Eh zance nazo  dama Malam yace na shawo kanta ta ta yarda mukoma muyi manage amma tace bata sona.

Bagana da tasan cikin abin da Mama ta gaya mata tace "haba YaShid yazata ce bata sonka amma banji dadi ba"

"A a sister kar ki samu damuwa aini yayan naki ai mai tsadane ayu yake so zan samu mata 4 zai iya.

"Gaskiya kam koni zan samo maka.
"no sister kibari na zabo kinsan bantaba zaba da kaina ba shiyasa na ke samun matsala kinga aure na nafari Bani da lokacin na tsaya nayi nazarin macce saboda lokacin ina tsaka me wuya aharkan wasa Ummi ta zabanin Hadim na 2 ma Hadim ta za bamin shiya so yanzu zan zabi kalan da nake so da kaina.

Bagana da Shateema dariya sukayi
Fandau taci kunu
Bagana tace "yanzu kuma wane kala zaka zabo ne.

Nabil yadan daga kansa alaman tunani yace "kinga nayi yayin fara kajera nayi baka doguwa,
Yanzu kuma fara doguwa nake so amma mejiki sosai.
Bagana tace "yayi za musha biki kenan.

Yace "sosai dan inason naga ammin cud'a yada akeyiwa kowane ango dan ni sabone tunda nake ba ataba min kamun ango ba ita ma Hadim ina London aka kaimin haka ita ma Ummu Akkaam kinga banga lalleba.

Daure faska Fandau ta sakeyi ya kalle ta ta gefen ido  yace "yabaki ce komai ba   babbar sister.?

Shateema yace "Gaskiya wannan ai cin faska ne akeson yiwa Auntyna.
Bagana tace "a a my neelly itafa tace bata son mu.

Nabil yace "bari na tafi sister za kijine idan na gama nazari dan mata sunanan burjik.

"Yawwa Yayana Allah yabaka sa a.

Ya shafa kan Tajuddin Yafita

Bagana ta juyo tace "Mama tace min guduwa kikayi dan shi yana ganshi anan kuma ina mutanen gidan?

Fandau tace "kanwar sace ta kirashi wannan yar rinin hankalin ce tazo ta faramin ihu dan ita bata san wacece Fandau duk karamin iskancin ta yana tafin hannun na, zan nuna mata ni cikekiyar yar cikin gargar ce ba taka haye nayiwa Barno ba, aini yanzu ba abinda nake jira irin ka ronmu da kita.
Bagana tace "Gaskiya ba tasan ke wacece ba ta sameki araha shiyasa ni har mamakin matan nan nake wai Hadim da ake yaban kirkin ta ako ina yanda take kyata da sadaka ita ce tayi irin wanan abin.
Da ganan Fandau ta kwashe komai ta gaya musu sun jijina sosai
Har Shattema yayi musu salama

Sai ga Amsatu Hadiza suma fa d'awa Fandau sukayi sukayi ta kuka da murna haka yan uwata mata suka cika gidan har manyan sun YaZahra da su YaKaka abin da Fandau bata taba tsammani ba kenan dan bata zaci abin zaizo mata da sauki awajen yayin nata haka ba  tazaci zasu mata gorin da fad'an su na manyan ce Sai nanan suka da ita lafiyeyen abinci Fandau tasa me aikin su jummai ta musu sai  yamma suka yayi shirin tafiya,
Fandau ta rakosu mamakin ta sai taga YaKaka YaBintu Baana har da motan kuma su suka tuka abin su sai sauran kuma wanda ba azo daukan suba suka kwashisu saura YaMainuna su Nana    suma ba jimawa dan gidan Maimuna  yazo ya dauke su sai Bagana zasu koma ciki itama Shateema yadan no kai ko parking bai yiba yace tayi sauri ta shiryo yana da wani uzuri
Fandau tace "kai YaShattee da kabari sai dare wllh bamu gama ba.

"yanzu wuni guda amma baku gama ba fira yawuce na awa 2 ai yazama na shirme  kai Tajud shigo ina Isseta.?

Bagana tace "tana bacce bari na dauko ta.
 tashiga
Fandau kamar tayi kuka dan basu sake sosai sunyi fira ita da yar uwar ta ba sai bayan sun shiga mota Fandau ta kama murfin motan Shateema yace "kar ki damu gobe sai tazo ai.

Fandau tace "Allah zata zo?
 yace insha ALLAH.
Tarufe musu motan suka ja

Hadim acikin mota kuka kawai take yanzu wannan yarinyar da na renawa ita takoma haka ashe dama mekyu ce tunowa tayi ita yaushe rabonta da Nabil tunda sukazo ko awaya ta kirashi a fisge yake amsawa tunowa tayi da maganan Fandau nacewa _jiya kinsan inda ya kwana ne_

Wani irin kuka tasa tace wayyooo ALLAH nayi kuskure ni Hadim yiwa kaina kishiya da kaina amma ai Nabil bamuyi da kaizaka min haka ba ai
Jidda tace "Aunty kiyi Hakuri yi addua.

"Jidda narasa ta ina zan fara addua an mezan cewa Allah  Jidda kishiya fa ake shirin yimin akuma kwacemin yarana nikam idan suka kwace min yara.

"Aunty kiyin Hakuri kunyi kuskure duk kanku amma kikar bi kaddara ki zauna da ita yafi miki nake gani yara kuma tunda kowa yasan kina son su tsakani da Allah kici gaba da nuna musu so su shaku dake yanda da kansu indan sun tashi baza su nuna miki ban baci ba tsakanin ki da uwar tasu kuma idan an hadaki da yarinyar nan wllh kibita ahankali dan yanda naga idanunta a tsai tsayen nan idan baki sauko ba kowa acikin ku bazaiji da dadi ba tunda kinga yanda YaShid yake sonta duk wannan jinyar da yayi akanta yayi kibi Ahankali kin san komai na Duniya yanda ka dauke shi haka yake zuwa maka.

"Jidda yazan shi yazan iya zama da my star na da wata wane irin rayuwa zamuyin
Zan kunyata agaban kawayena yanzu haka dazu wanan Faridan matar Amjad kinji abinda take fada kuwa wai har da cewa alwalan kifi yakarye yawanci kawayena da nake jida su narasa su kiga yanda muke da Aminan Bilal amma d'azu itama harda yadamin magana balle Habiba kinga  yanzu zancen yagama bazuwa cikin kawayena.

"haba Aunty keta kawaye kike su sunfi karfin amusune kishiya ko yanzu yanda yan mata suke daukan wanka su zaga gari ai nake gani mata suragewa kansu kishi yafi,
Kicire batun wani kawaye ki kwaci kanki kine mi yaya ku shirya tunda guntun sonki aran sa kar wannan karamar yarinyar ta miki illa dan naga alamar ta.

"Jidda illa sonawa ai yanzu ne kawai kujira makokina kawai.

Jidda tace "baza ki gane ba Aunty shifa kishi saukine dashi awajen me ta wakali. Ai kwara ke zuwa tazayi ta sameki nifa da zuwa zanyi na tarar  kede kiyiwa kanki fadan alkairi kawai.

"shikenan yanzu Jidda za ace na zauna da wata wllh da ba a gidan Nabil bane zan iya zama da wata amma da shi bana jin zan iya.

Jidda juyowa tayi ta Kalli Hadim batayi magana ba dan dama ita bata fiye magana ba gyaran parking tayi ta fita tabar Hadim  aciki

Fandau ganin har  magari ba akawo ma ta Akkaam ba gashi dama dasa fe ma bata bashi nono ba dan yana bacci ta fito nonota ya ciko yakamata sai ciwo yake mata sosai Mama takira tace akawo shi mama "tace yo ina naga Daudan da tun safe ubansa ya dauke shi wai zai kaiwa FUJJI yafita dashi amma bari nakira shi.
"Mama dan Allah yakawo shi yanzu bai shaba da safe yanzu gashi sai ciwo yake min.

Tana gama waya da Mama ta fata jin hayaniyar su Haris
Suka shigo da gudu Fandau tace "banace kudena shigowa gida da gudu ba kuma nace kuyin sallama. to suka ce tare da komawa kuma suka shigo da sallama ta amsa tare da ware hannun ta suka fara rige rogen Fadawa
bayan ishai suna cikin fira ba sai sukaga Nabil ya shigo da FUJJI da Akkam yana hannun sa sai BilAL da Maaruf suma suna binsu abaya  duk kaya irin da kayan yan ball ne amma dogon wandone duk kan su da fulan facing cap dayan ke  jane da fari sai yafiyiwa Fujjirat kyu an fito mata gashinta ta fujin fulan da gudu tayi wajen Fandau tana cewa "Aunty kirki Fandau ta dagata tana mata wasan da tasaba yi mata  ta na sauke ta ta ciren mata fulan tace "FUJJI na kidena sa irin wanan fulan na mazane kuma kidena sa Wanan rigan shima na yan ball ne."
Ita Fuj bata magane metake nufiba dan hankalin yatafi kan Nol
Nabil Marmushi yayi yace "kika sani ko ita ma zatayi  gadon babanta ta zama yar ball ko baki san mata suna ball ba ko anan Nigeria mata sun ciyo mana cup na Duniya balle akace jinin Shiddams ai inde FUJJI tana da ra ayin ball zan mata jagaba duk Duniya asan da zamanta balle yaran nan nawa maza ai dolen su ma su gajeni.

Dr yace "kade tsaya a mazan.
"wllh inta na ra ayi sai tayi."
Fandau tace
" Allah yasauke yarana su zama yan ball.
Nabil yace "ai kin gama ya gama ai asalin sayin da ga ruwa ne tunda uban su yabuga ai ko basu buga ba sunan su yan Ball shiyasa basan sasu makaranta ba saina kowan balls wannan ra ayinane.
"ai bansan dan ball bane na aure ka.
 Nabil murmushi yace"Kaddaran haifan y'ay'an ball ya kaiki shiku ma imani da shi yana cikin cika cikan musulumci.
Habiba tace "kai oga daga zuwa sai akama musan yan zance ba ko gaisuwa.

Nabil yace "irin abinda kuka koya mata kenan ai keda mijin naki rashi kunya yanzu idan na matsa mata ma inaga dukana zatayi dan dazu anan  parlour na samu ta danne min mata tana dukanta.
Habiba tace" ayya wllh nima banji dadin abinba saide wllh nide ban koya mata rashin kunya ba Allah yaki yayen gaba.

Nabil yace "Ameen yawuce ai dama ita my one ai dan ni takeyi yanzu kuma ni Fandau tace bata sona na hakura yanzu saide ayi zumunci  kawai.   Dr baisa bakiba dan shi Nabil baya kulashi har yanzu

Habiba tace "au haka akayi.

Nabil yace "ai baki ma sani ba ai dake da mijin ki ku kuka hada komai kuma kuke zugata ina ga kuna tunanin ban sani bane to nasani kuma ku kuka hadata da BilAL din ma tona bar masa yanzu Mama tace nakawo Akkam ne yasha mukoma da baza ku gan muba.

Dr yace "ashe muna da amfani tunda har za aneme mu dan mu shayar.

Nabil daure fuska yayi dan yanzu  gaba yake da Dr

Itako Fandau tashi tayi ta shige d'aki dan taji haushi magana Nabil naya hakura da ita
Fujjirat ta bita Nabil maya bisu har su Nol suka bi bayan su suka shiga

Dr yace "ban ce kashiga har d'aki ba.

Ko juyowa banyi ba yashige ciki

Fandau tana shiga tazauna abakin gadon tana tunani yanzu shikenan da gaske  Nabil ya hakura da ita karfa garin jan jaji ta rasa damar ta har suka zo kusa da ita bataji ba dan bata rufe kofan ba balle  taji k'aran budewa

Acinyar ya daura mata Akkam yasa hannun sa cikin riganta kawai sai jin hannun tayi a kan boobs dinta wani irin yar taji ajikin ta da saurin ta ture hannun sa tace "me haka?
"ido yakanne mata me kikaga abincin mu za abamu.

"kuma abincin da kai kake bashi.

"Ai dan ba abani dama bane da zan bashi.

Tace "yanzu dama kasamu kena.

"Eh mana da ban gankiba yanzu ko nagan ki.
 su Nol wasa su kawai suka kama

Shiko Akkam tunda yajishi cinyar uwar sa ya fara laluman nono ita kuma ta kasa fitawa ta bashi shiko Nabil wani mugun sha awar tane yake d'awai niya dashi yakasa tashi da ga dur gusan dakyar ya bude baki muryar sa can k'asa yace "ki bashi zamu tafi.

 Tace"wai kana nufin da Akkam zaka tafi.?

Yace"Eh

"tace yaron da yake shan nono zaka dauke shi agaban uwar sa ko da yake ba yanzu kuka fara wanan zalincin ba kuka kwace jaririn daya fado atake ma balle d'an wata 6.

 Yace "ai naga yana shan madara sosai badan Mama bama da bazan kawoshi ba
Fandau ya kike son nayi narasa ki kince ba kya sona sai nabar miki yarona wanda nasan kiyar yar uban su zai iya shafar su,
Koba haka ba kiji tausayina mana ki bari indin ga ganin yarana akusa konaji saukin wasu abubuwa shikenan kullum hankali na arabe su Maaruf suna wajen Inna kullum sai naje na  duba su ga FUJJI awajen Hadim suna gida ita ma sainaje sannan ga Akkam yana wajen ki kuma bakya son gani na Ni kuma bazan iya hakura da ganin d'ana ba shiyasa nake son na had'asu waje daya dan su hada kansu nima na samu nusuwa ko yakika ga.

Sai taji wani mugun tausayin sa dan yana maganan ne cikin kalan tausayi

Tace"ni nace maka bana son ganin ka.?

"Dazu mekika ce dana ce inason ki cewa kikayi bazaki karbi tayina ba tunda ban baki son lokacin da kike nema ba Fandau idan idona da gangan jikina bai sa kingane ina son kiba wllh fada abaki bazai fa shimtar dake ba amma
tunda bakya sona bazan iya tur sasa kiba dan ke mace ce dama d'aya tak kike dashi gwara na barki ki auri wanda kike so nikuma namiji ne inada dama wajen na auran mata har hudu iya adalcin da zanmiki da nuna miki so da sanyi yanuna son Gaskiya nake miki bawai sha awa da kike zargina akai ba to na goya miki baya ki auri wanda kikeso dan bazan bari ki cutu .
Fandau tace
"ashe son nawa baiyi nisa ba tunda gashi zaka iya hakura dani.

"baki ji ance hakuri yaza ma dole ba ai hakuri yana magani komai Fandau kin min komai arayuwa,  ko yaran nan nasa agaba ina gani nasan jinin kine ajikin ki suka fito zai iya ragemin zafin dan haka dole kema nabaki abinda kike so ai  awai wata yarinyar da ta dade tana bin bayana yar kono ce zan iya auranta na had'a ta da Hadim inaga su. Ishe ni rayuwa.

Shiru Fandau tayi kwai kode da gaske yake inko haka ne yazanyi

Afili kuma tace "ni kuma meye matsayi na awajen ka.?

"ai ke ta musamman ce matsayin ki awajena yazuce duk ida kike tunani  ko cewa kikayi na hakura da Hindu ta kano zan hakura.

Tace "ni bawan nan ba matsayin aurena.?

Nun farawa yayi yana jinjinawa iya takun sa na bugan cikinta yace "bayan sakin da namiki bisa umarni na maida ki agaban Malam shi ya sani najen na nemi yardan ki danaje na tadda kina waya da wancen dan iskan to kinga har yanzu kina matsayin matata saide idan kince na sallame ki zan iya bin umarnin ki dan ni ba abin da nakeso irin nabi zabin ki nasa ki cikin farin ciki kamar yanda kika sani alokacin da muke tare wanda nasan yanzu ma koda bama tare idan naga yaran ki zaki ciga ba dasani.

"waida gaske auren zakayi auren huce haushi kenan.?

Yace "Eh hakane dan Gaskiya da na taba mata 2 nagani bazan iya zama da daya ba."
Ajiyan zuciya ta sauke ta sa Akkam a nono amma sai saiga Nabil yazu bawa wajen ido  har Akkam ya tsaki  nono tana dubawa yayi bacci zata kwantar dashi saiko ya dauke shi ya meke tare da jan hannun sauran yaran har yajuya tace "da gaske tafiya min da shi zakayi.
"Eh wannan damar kine har yanzu kina da sauran dama ta zama da yaran ki kiyi nazari kafin gobe damar ta kucce miki dan rabuwa da yara ba kara min asara bane kiyin nazari yana gama fadan haka yaza hannun yaran sa suka fita a parlour ko yatarar da su Dr suna kallon ya zuce su ko Habiba da take cewa agaida gida bai kalla ba

Fandau ta sha kuka
Amma tana gayawa Dr da Habiba suka ce plan ne ta zuba basa ido fada suka mata sosai akan ita tabari yagane tana sonsa dan yariga yagano tane kawai
 !
 Fandau kasa bacci tayi dan kuka ta shayi

*WASHE GARI*

  Habiba bata je ko ina baBagana  tazo gidan  kamar yanda shateema ya mata alkawari suna cikin fira  Fandau tace " yawwa ni Bagana jiya ina son na tambayeki bayan tafiyar su YaMainuna sai Shateema yaza kuka tafi abin yabani mamaki wai Yabintu da YaZahra  Yakaka naga har da motan su duk dama nasan maza zajen su masu kudine amma harda mota haka.
Dariya bagana tayi tace "yo ai na gasa yazame musu yanzu Yazaina tace itama sai ta tsiya yanzu haka rabin kudin ta yana wayen Shateema ita ma Aisha ta hurawa mijinta wuta ina ga ma yatsiya mata bata koya bane yasa batazo da shiba,

Kawai dan sungan ni da mota kowa gasa yatashi....

Katse ta Fandau tayi da cewa kema kinada mota.?

 Bagana tace "ai nina fara yi sun zata Shateema ne ya tsiyamin.

"waya tsiya miki?

Bagana "tace wata rana Shateema ya kaini gida da yamma yace aiki yamasa yawa na hau napep na koma nace to shine dana gashi wayan tacewa Mama zanje na hau napep shine Shiddams yana wajen ya dinga tsoka nana da wai kamar ni big girl acikin napep  shine  yasa aka kaini gida washe gari kawai sai ga motoci kuda 2 masu tsada wai nawane daga Shiddams shine fa kowacce ta tashi amma ai masu isa su hau irin nawa ba wai dan ma boye dayan nayi gudun magana.

Fandau tace" Haba sai kibani dayan yar uwa.

Habiba dariya tayi tace" yanzu ke har kina matar Shiddams ai kinfi karfin mota daya sonawa nake cemiki za kisha mamaki duk sanda kika zama cikekiyar macce agidan Shiddams kyutan gidan da mota da kujeran makka wllh ba wani abu bane jin Shid kike baki san waye shi ma wllh shugaban kasa saide ya nuna masa mulki baki ga yanda Hadim ta ke bajinta a kawayen ta da yan uwan ta mota kuwa ita take canja wa kannen ta duk wanda ya fito sabo su suke fara hawa acikin meduguri.

"Bagana tace "rabu da ita Aunty B kuma tana son daman ta ya kufce mata ko dan jiyan nan saida yarura min pic din yarinyar da tamutu akansa amma yaki amsa mata amma yanzu yace zaije ayi maganan auran ta zaiyi wai sunata Hindu yar kano ce....  Fandau ta katse ta "na shiga ukku kinji Aunty da ma nace muka kamar da gaske fa yake kuka ce min plan ne kinji ko har yana fada.

Bagana tace" da gaske ne mana ga pic dinta tanuna musu wata gayiran budurwa

Ita ma Habiba shiru tayi tana son gaskan tawa tace " inaga fa da gaskene.
Bagana tace "da gaskene.

Fandau tace "yanzu yazan yi kar fa yayi auren yace baya sona shiyasa yace daganan zuwa gobe ne *dama ta* idan nayi wasa ya kufcemin shikenan shikenan aunty wata kilama yatafi kanon.

"Bazai tafi ba kibari Abban Nol yazo zai samo miki mafita kinji.

Shiru Fandau tayi gaban ta yana faduwa

Ganin tabar zancen yasa Habiba tace Allah Bagana ayi magana Gaskiya wanan *Issetan* taki nayiwa *Haris* kamu kinsan da FUJJI muka ce sai naga yanzu FUJJI tanawani mahaukacin girma kiga har taso wuce ummuna a tsawo tafi karfin mu...
Fandau mekewa tayi ta shige d'aki tana shiga ta fara safada marwa yanzu yazanyi idan narasa mijina wazan so kamar sa da saurin ta wawuri wayar take ta danna dialing no nashi

Alokacin Nabil suna kan hanyan gidan Dr din zai kai Akkam yasha kona ce zai barshi dan Fandau ta hada shi ta Mama Mama tanuna masa b'acin rai sosai yabata hakuri yace zai mai dashi
Yau ma kamar jiya shiga irin daya sukayi saide yau farin rigane bakin wado fulan ba b'aki ne sai tambarin Chelsea club din su ajikin fulan da rigan har agogo medauke da tambar ne a hannun su har Akkaam suna baya FUJJI tanata zuba masa surutu su ma su Maaf runa gwarancin su yana biye musu ahaka yaji wayan sana family yayi ringing dole ya dauka duk da basuna amma sallaman da yadoki kunne sane yasa yayi saurin mekewa da ga dan kishingid'an da yayi muryar sa yana kwaruwa yace "eh a am Mata ya akayi nasan Akkam kike mema ko?
"a a har da kai dan Allah kana ina?

"da gaske mata harda ni kike son gani?

"Eh amma idan kazo ka kirani a waje bana son Aunty tasan kazo zan fito.

"to ai gamu ma ina hango gidan kifito.

Tace" ok.
Mayafin ta tazara ta cilla ta wundo  dayake su Aunty B suna parlour ciki tafita kamar me zuwa babban parlour amma sai tafi ta kofar baya ta dauki mayafin ta tafita tana fita ko ta hango motacin nasu   tsayawa tayi dan bata san wada yake ciki ga gashi duk b'akin glass ne motan tsakiyan taga yatsaya daidai gunta kofan yabude yace "kishigo ciki ko ba musu ta shiga kofan yakoma
Shiru ne yabiyo baya
Can yace "to yanzu  afara bawa Daudana abin cinsa dan nasan ma shine dalilin ne man nawa ko.?

Tace" wai dama da gaske kake auren zakayi?

"ba kyason nayi ne ai dama saida na nemi sha awaran ki kuma na baki damar ki idan kince ba kyason bazan yiba amma bazan iya zama da Hadim kadai ba sai kisa momin mafita.?

 Cikin masifa tace "To wai ne cemaka nayi bazan koma ba ko duk kora da hali kake son yimin.

 yace "da gaske kike zaki koma  dani wllh  inde zaki koma har abadan bani ba kara aure ke da Hadim kun isheni ita ma tayi nadaman abinda tayi baki ga yanda take kuka ba jiya muka shiya har ta koma gidan ta nabar ta dan Allah Fatina da gaske ne.

"da gaskene Nabil bani da wani zabi sai kai duk da baka cancan ci nasoka amma ba yanda zanyi umarni zuciya tane kai......
Bai san sanda ya rungumota ba yana mata godiya har da kwallan sa.
Yace "nami ki alkawarin zama dake amana duk wannan zargin da kike min na nayaudare ki ko ban miki adanciba ba ki bani dama nan da 1week bazaki fada ba, acikin sati 1 tal zaki gane irin matsayin ki awajena,
kuma kicire wani Hindu aranki ni ba wata hindu dana taba sani na sauke pic din tane kawai a media kinriga kinrufe zuciya ta da tarin sonki.
 ya dago yabawa driver umarni da yajuya kan motan zuwa gargar
tace "amma ya tsaya na sauka dan Aunty bata sani ba nafito kuma itan Yaya yasani wllh zai min fada....
"Waye kuma yaya?

"Abban Nol.
"ai dama na gama gane plan dinsu shiyasa wancan dan iskan na neme shi narasa akarin nan amma zan dawo kansu sun cutar damu.

"mesu kayi na cuta mu kuma dan sun temakeni.

"Ni awajena ba temako bane raba ma aurata tsawon watanni 10 fa har jinya nayi badan demako Malam ba da yanzu sun miki asaran san talelen miji, har kina cewa sun temake ki
ai wllh sai sun gane basu da wayo baga shi na shawo kan abina ba ai sun san ni me sa ane.

Dariya tayi tace "kaji yaban kai wai san talele,
Nide sauke ni.

"ai ba inda zan sauke ki sai gaman Sayinna dan shine yace naje na nemi yar danki kuma na samu ayau agidan ki zaki kwana.
"dan Allah kar kasa naji kunya awajen mutanen da sukamin karam ci kaga yanda Dr yabar aikin sa da karatun yaran su yazo suka zauna dani.

"kar kiji komai matar Shiddams kike yarinya sai kinga dama ma zasu ganki balle kiji kunyar su,
 ai zuwa da sukayi na muna firci ne ba.

Daganan ya kawar da zancen ta cewa bari nakira Hanif yaje yashare mana gidan muna Shagari yaciro wayan yana bada umarni a share gidan.

Itade Fandau shiru tayi dan tasan abin kunyar tariga ta sake afkashi

Ya katse mata tunani da cewa yanzu wadanan yaran duk ka yaran kine kina yar misisiyar nan wllh abin yana bani mamaki wai yawan nan duka naki ne duk girman gadona fa jiya muda su da my one wllh amatse muka kwana agadon mu 6.
Wani kululu kishi ne yatsaya mata ta hade rai ta juya kanta
"sai asanan yagane ahe zata iya kishin Hadim dinma yafara basar wa yana wani janta dawasa har suka karasa gargar dakyar Fandau ta fito tana jan mayafin ta tana rufe fuskan ta dayake da safene Nabil yana tambayan almajiran ina Malam suka ce yakoma ciki  Fandau zata shige cikin gidan bangaran su yayi saurin kama hannun ta da ALLAH yatemaka ba kowa awajen
Yace "sai mun fara shiga wajen Malam tukun.
 tace "ai nasan yanzu Baa yana bacci tunda antashi akaratu  sai anjima.
Ina bai saya bata amsa ba kuma bai saki hanun nata ba yaran suna binsu abaya suka shiga har parlour Malam zaunar da ita yayi ya yace mari kiga ai  taso sa zanyi ta dauka wasane dan idan  Malam yana baccin hantsi ko matan sa basa tayinsa ai sai gashi ya haye sama ba ta gaskan tashi ba saida taji yana knorking din kofa ba ajima ba ko sai gashi sun sauko tare dariya malam ayi yace lalle da shirin ka kazo.
Fandau ta sauko akan kujeran tazube k'asa jikinta na rawa kanta a k'asa dan ita duk duniya ba wada yake mata gwar jini irin Baban ta tana mugun tsoron shi dan koda bata zuwa koda ai gaishe shi sai taga yana wajen zatayi sanda ta shiga satan apple dan abincin tane shima Malam yana son apple dan haka awai ranan asirin ta yatonu aka ganta aka gaya masa yakirata yace kullum tana zuwa tana dauka idan tana so amma ita da sunan gaida Baban sai tayi wata ma bata ganshi ba
Bayan sun gaisa malam yace ta tashi  tashiga ciki anjima za akira taro.

Yauma taron aka kira na gaggawa dan yau harda baban Hadim dayayin ta da mamar ta da iyayen Nabil kamar na wancen karon da BilAL da Dr  da farko dan gidan Malam ne yabude taro da addua a malam yace "Jaji kaine mahaifin Halima matar Muhammad ko?
Baban Hadim yasun kuyar da kai yace "Sanyina nine wllh da baka kira ba ma yau mukace zamuzo mubada Hakuri  akan abinda yafaru wllh ban san komai ba sai jiya.
Malam yace "Masha Allah tunda kaji abinda yafaru wanda ba Halima kad'a ba duk kansu masu nefine shiyasa zamu taru mu gyara abin tunda duk na gidane

Yanzu ta kanka zan fara Habubakar kasan tun alokacin da kace Fatima bata da idda nace maka tana da shi kace kasani kayine dan  yayi hankali to tun adaren nasa shi yamai da auren  anzu haka matar sace saide sakin da yamata yasa igiyar auren yazama saura  2 dan tun alokacin dan ka bukaci nabaka daman kane amma banso kayi wasa da saki ba Malam ya musu nasiya sosai.
Baban Nabil yace "hakane duk abinda mukayi na cewa auran Fatima da BilAL shirine dama Nabil ya dago kai ya zaggawa BilAL da Dr harara BilAL yayi murmushi

Malam yace "Halima matso kusa  Hadim ta matso dama Nabil da Fandau suna kusa dashi Malam yace  "yawwa Halima kamar yanda Fatima take y'ata haka kema kike ina son kuyin zama na amana atsakanin ku zaki karbi amana ko?
Hadim jitayi mutumin yamata mugun kwarjini wanda ta sha gaisawa da shugaban nin kasa she daban daban bata tabajin wani ya mata wanan kwar jinin ba gaban ta yana baduwa ta gyada kai alaman eh
"malam yace "bude baki zakiyin kimin magana zaku zauna lafiya.

Hadim bakin ta yana rawa tace "eh insha Allah.

Malam yace "to Alhamdulilah
Fatima ga yayaki Halima karnaji wani matsala yata so tawajen ki kiyi koyi da hali irin na Aisa kinu namin ke jinanin tane zakiyi.?
 cikin in ina Fandau tace "Eh Baa
"to Masha Allah,
Muhammad ga matan ka kazama adali a tsakanin su.

Dan zumudi yace "insha Allah nagode  Malam.
 Malam yace "Yawwa sai batun yara Halima na miki jajen abin da yafaru dake na rashi mahaifa to hakan baya nufin bakida yara  kina dasu ko a musulumce  yaran nan kina da hakki  na sharan da su tunda suna da gadon ki kema kina da nasu koda ace yanzu zai yuwu ace zaki haifu dawani wanda ba baban su ba to ba aure tsakanin su,
  a yanzu  ace kanin ki da kuka sha nono daya yace yana son Hajara to ba aure tsakanin su nono ya hada shi kuma da ma atsakanin d'a da uwa nono aka ambata yaran yanzu zasu gajeki zaki gajesu,
 ita ma haka tana da hakki tana mahaifiya agare su wanda ita tafiki hakki a kan su,
 dan haka inason na raba muku yaran dake da yar uwar ki amma kezaki fara zama dan haka kizabi 2 wanda kika bari sune na yar uwar ki
Hadim gaban tane yake faduwa yanzu shikenan Fandau taza ma matar Nabil yanzu shikenan yaran nan kowa yasan na Fandau ne to ma kita wane irin zama zatayi da kishiya kawai sai ta fashe da kuka

Sukuma mutanen wajen tunanin su karam cinda Malam yayi ne yasa ta kuka saida tayi kukanta me isarta

Cikin tashewa murya tace ina neman almarma a hadamin da Fujjirat  sai abani ko BilAL ko Maaruf.

Malam yace "amma naso ace yan biyun kika zaba sabo da bai kamata araba suba amma yanzu ma ki hada kirike su duka na baki,
Ita yar uwar ki tarike Daudan ta tunda ALLAH zai bata wani tunda tana da lafiya Allah yabata masu albarka kema Allah ya raya miki yabaki ikon tar biyar tar dasu sai kuma ab.......
Fandau wani irin kuka tasa wanda ta katse Malam

Cikin kukan ta fara magana Baa dan Allah ga Akkam din ahada mata dashi dan Allah abani Fujjirat wlllh ita nake so dan Allah Aunty kiji tausayina  kar kiraba ni da FUJJI wllh duk burina akanta yake.

Dak wajen kowa yayi shiru
Sai Nabil yace "Malam dan Allah aduba lamarin nan wllh ba ayiwa Fatima adalci ba ita Hadim ta dauki yan biyun ta barwa Fatima Fujjirat da Akkaram din.

Shiru Malam yayi Can yace "to Halima zaki iya barin Fujjirat din ne kinji abinda yar uwar ki tace ta baki harda Dauda.

Hadim da gaba daya haushin Nabil da Fandau ya kamata a gaban din bin mutane Nabil zai nuna yafi son ra ayin Fandau kwafa tayi aranta
Afili kuma tace "Baa nima wllh FUJJI nake so koda zan bar mata dukka yaran ne.
Wani irin kuka Fandau tasake fashiwa dashi dan tasan anga ma bawa Hadim zabinta.

Nabil yace "da zakice zaki bar mata da nakine ai nata ne dan haka wanda ta keso shi za abata.....

Itama Hadim kukan tasa cikin kukan tafara magana" yanzu ni za kayiwa  gorin akan yaran toni bana soma dan dun daga yanzu an faramin gori.......
Shiru tayi da dililin wani wutan mari da yaziyar ci fuskanta.......

*to  masoya waya mari Hadim Hadim zatayi Fandau almarman da tanema ta bar mata*
*B JATTKO*
[3/12, 8:50 AM] Hauwa: *DAMA TA*


                *NA*


*BATUL ADAM JATTKO*

WATA DAGACIKIN MASOYA TAMIN ABIN *AL SHERI* NA GODE ALLAH YASAKA DA ALKAIRI YABAR KAUNA


Wanan shafin nakine *UMMU MARMYA*


🌈Kainuwa writers Asso🤝🏻

*47*

Baban Hadim yasake d'aga hannu zai zaf ga mata wani marin Malam ya dakatar dashi da cewa "Jaji agabana ake nuna min Halima yar kace.
Baban Hadim sunkuyar da kai yayi  kamar mene man gafara yace "Sayinna Allah ya fuci zuciyar ka tuba nake.

Malam ya tumfasa yace" Muhammad Nabil kace ban yiwa matar ka adalci ba ko?
Shiru Nabil yayi dan su butan baki yayi saida yafada yagane da fa Malam yake
Cikin muryar nadama yace "kayi hakuri duk abinda kazar tar akanmu daidai ne.

Inna Zainab tace "Sayinna bawan da ya isa yaja da maganan ka kayi duk yanda ka ga dama.

Malam yace "Halima ki dauki yaran ki kuma ba maganan gori cikin duk wada yanu na miki yaran ba kece uwar su ba ki sanara dani.
yajuya kalli Abdulrahaman dansa yace" karufe min da adua.
Bayan an shafa
Kowa ya tashi
Malam yace "ban da Hadim da Fandau da Nabil bai gama dasu ba
Fandau har yanzu kuka takeyi
Malam yayi gyaran muryar yace "Fatima kin tabayi abu agidan nan namiki fad'a ko nanuna b'acin raina akai?
Fandau tace "A a.
"dakikayi wannan abin na zabawa kanki mijin aure da guje mana a matsayin mu na wanda shari a ta bamu daman zaba miki  amma ke baki bi yanda shari a ta zartar ba ke kin mana adalci?
Tace, "a a
 Yasake cewa"dakin bani *DAMA TA* na zaba miki da abinda ya faru dake tun farko zai faru.?

Gergeza kai Fandau tayi
Malam yace 'baki zaki bude kiyi magana.

Cikin kuka Fandau tace "a a
"da ki kazo nace miki wani abu.

Tace "a a.
"to dan me ke da na zartar da hukunci akanki zakice banyi daidai ba keda nake mahaifi awajen ki bakimin adalci ba nabarki sai ke kikeda iko akan hukunci na.

"Baba kayi hakuri bazan karaba nayi nadama kuma nayar da duk hakuncin da kayanke.

"idan kina son nagane kinyi nadama ki karbi hakuncin na kuma idan kin yarda da ni Modu nine wanda na yanka miki hak'ika to kar,
Naji koda wasa Kinyiwa Halima gori akan yarannan bazan hanaki nuna musu soyayya ko mu amullah dasu ba  dan yaran kine keki ka haifesu saide nabawa Halima rukon su sannan ban yarda kiyi amfani da *damarki* na kece uwa kisa rashin jutuwa tsakanin su da uwar goyon su ba maganan zaman lafiya duk kan ku kun min alkawarin zaku zauna
Lafiya dama ko?
Duk su kace Eh.
Daga nan ya musu nasiya sosai Hadim da Fandau yabasu adua shiko Nabil kullum yana cikin bashi saboda yanayin sana arsa ya sallame su

Suna fita Duk sukayi cikin gida Allah sarki Hadim har ita part din Mama sukayi anan suka tarar da su Ummi da sauran matan gidan anan ma duk Fandau akabawa hakuri Bagaji ita ma yanzu ta sauko harda ita ayan bawa Fandau hakuri Maman Hadim godiya tayi ta musu dan tasan dayawa har yanzu wasu basu san yara bana Hadim bane gashi kuma an bar mata kayanta
Suna cikin firan suka ji ana ta busa algaita na gidan sarauta Inna tace "SHEHU yazo muna gidan dawuya musamu hanyar fita  matan gidan suka ce "SHEHU bayayi wa gidan nan wanan shiyar dan yana girmama Malam saide wani sarkin

Malam yana parlour  ciki yaji ana busa *kakaki*  wani babban almajiran sa ne yashigo yace "Sayinna munyi b'aki suna neman izinin shigowa.
Malam yace "b'akin inane.
"wasu fararene amma fada ne har da sarkin su sun zo da wasu manyan motoci da sojojin Niger.

Malam yace" to amusu iso babbar parlour baki nawajen gani nan zuwa.

Haka ko ahayi
Malam yana shigowa sarkin ya meke alaman girmamawa saiko fadawa ma suka mek'e
Bayan Malam ya zauna suma suka zauna maimartaba yamek'awa Malam hannu suka gaisa  sannan yacire rawanin sa dan Malam yagane shi waye aiko yana cirewa Malam yace "Barumi kaine yau agidan nawa yau Aisa ya zatayi  hakurin danake bata yau yayi rana yau ga dan uwanta Barumi yazo.

Mai martaba yayi murmushi yace" Sayinna  ina yar uwar da yarona.

Malam yace "yara mata Aisa ta haifa sunanan Zainab da Fatima musha zuwa Niger ace bakanan sai Inna Munari kawai muke taddawa kuma made yanzu tsawon shekaru 7 kenan bamu jeba Amar dan Inna Munari da yake kawo mata ziyara bai zoba.

MaiMartaba yace" Ayyya Inna tarasu Amar shine galadima bashida lokacin zuwa,
 Ashe AISHA ta  haifu  ban san ta haifu ba d'ana Shattema nake tambaya ashe ita ma AISHA ta samu nata Amar bai gaya min ba.

Dasauri malam yakalli sarki yace "wane Shattema?

Sarki yace"Shattema naka daya.

Malam yace " dama Shattema dan kane.?

Maimartaba yace" da nane ni na aiko shi nanne dan tsiratar da rayuwan sa kamar yanda kasani kakana shine sarkin Maine babana shi kadai ne awajen iyayensa kuma Allah ya daura masa larura na makanta shiyasa yan uwan kaka na suka sa rai da su zasu gaji sarauta amma tunda babana yayi aure aka haifeni suke bakin ciki dani dan zan iya gadan Kakana tun ina yaro suke meman hallaka ni shine Kakana ya bawa Babana shawaran yafita dani ya kaini almajiran ta shine dalilin kawoni wajen asali Baban ka M Lawan Gargar har muka tashi dakai anan gidan naku to bayan nasa mu saukan Qur ani na koma na samu mahaifiyata tarasu saka makon haifuwar Aisa matar ka Aisa ta tashi awajen wata Innar mu Munari wanda awajen aka aura maka ita,
Wannan kiyyar da dan gin babana suke min shi yafitar dani acikin Maine  na koma gemi amma sai na shiga karatun boko wata rana nakawo wa babana ziyara yake cemin kazo nemana a sannan AISHA ta kusa zama budurwa shine nacewa baba duk sanda Allah ya sake kawo Zannah ya aura masa kanwata dama ziyaran ma asace nake kawowa babana kakana ko bana ganin sa dan yana jikin fada koda naji labarin mutuwan kakana a radio ban zoba dan ina tsoran suce nazo abani sarauta ne kawai na maida hankalina akan karatuna wanda nasamu uban gida mai sona shi yawuce min gaba nasamu degree na  sannan nayi auren fari awanan lokacin Allah ya daukaka uban gidana yazama, governor kuma shima asalin sa dan Maine ne
Mukuma sarautan
Maine wanda suke son ne suka samu
Dan Babana baya gani makaho ne wanda ba adau lokaci ba yabi baban shima bayan auren ku da Aisa ina  sane da Aisa ALLAH bai bata haifuwa ba shine na dauki d'ana Shateema na aiko shi da wani yarona buzu yakawo shi almajiranta wajen ka Shateema shine babban d'ana yana da yan uwa.

Malam ya girgiza kai yace "to Barumi ya akayi ka zama sarki yanzu akwai lokacin da naje Niger wllh wulakanci yan fadan nan suka min sosai ni kuma gidan baban ka kawai nasani da gidan Inna munari da nake tambayan dangin shine akace nace fadan.

Maimartaba yace "Innan tarasu  yan fada ko dole su maka wulakanci dan sun san kaine mijin Aisa suna tsoron kazo kace zaka nemi sarautan sune tunda mu acan miji yana gadan sarautan matar sa,
Yanda akayi nagaji sarauta kuma ziyara nakawo musu dan har ga Allah inason zumuci da yan uwana lokacin ina minister na kawo musu ziyara amma sai suka sa aka jefeni wannan haushin ne yasa nayi amfani da kujera ta a karfin mulkin siyasa na karbi sarauta na ayanzu haka nabar harkan siyasa sarauta kawai nake naji labarin ita ma AISHA ta gamu da irin laluran baba na makanta wanda ciwone idan bai samu kulawa ba yake zama makanta wandan kadan sa mukayi amma idan ankula dashi za awarke."

Malam ya nunfasa yace " Alhamdulilah anan ya kwashe abinda yafaru duk yaga yawa sarki abinda yafaru
da Fandau  har auren Bagana da Shateema atake Malam yasa aje adauko Shateema da iyalin sa

Ai Malam da kansa yayiwa Maimartaba iso har d'akin mama Aisa tana ganin dan uwan ta duk da yawan shekarun saida ta gane shi dan ba rawani ahaka yaje aiko Mekewa tayi tace "Ya Barumi Dasauri ya karasa inda take yakama hannun ta ya zaunar da ita yace Aisa yar uwata cikin Ummana nine Barumin ki ban guje miki da gandan ba sai dan ina son na tsira da lafiyana kema shiyasa nasa Baba ya aura miki wada bazai taba sha awan zaman Niger ba balle yane mi sarauta su gama da dake amma duk da haka bamu tsira ba saida sukayi abin da nazo na karbi sarauta suka huta."

 da ganan ita ma ya kwashe komai ya gaya mata agaban ki shiyoyin ta da kuma su Ummi da Maman Hadim da ita kanta Hadim din azuciyar tace ba banza ba Fandau ta keda kalan yan sarauta  ashe ita gada tayi uwa da uba Nabil yajijina kai yaji dadin samun asalin Mama dama abin yake shirin yi kenan idan komai ya daidai ta zai dauki su Mama ajen neman dangin ta sai gasu dakan su
Malam yaga batar masa Nabil da sauran mutane Fandau jin abin take kamar amafarki wai dangin Mama  kawai sai ta tashi taje ta fad'awa Barumi ta sa kuka  ana cikin haka Bagana da Shateema suka shigo  cak Maimartaba ya meke ganin Shattema ma yazama cikeken namiji daga gani naira yazauna masa wanda ko yan uwan sa na can ba abinda zasu nuna basa hatta Afwan wanda yabiyo bayan Shateema ka rasawa yayi wajen sa ya rungumo shi yana "cewa aboki nagode haka kaza marmin da d'ana ina ma da Hjy Kare mukazo taga Shattemanta da kullum take min maganan sa.
Shateema "cikin firgici yace "Sayinna waye wannan shiwaye tunda nake ba wanda ya taba rungumana sai Mama Aisa.
Malam yace  wannan dan uwan mamar ka Aisa ne ciki daya kuma shine mahaifin ka ai Shateema bai san san da yasake raruman  mutumin da akace baban sane kuka yasa har Mama da Bagana da Fandau kowa kuka Shateema yace "kaine dan uwan mama dan ga kaman ku daya da ita amma idan kaine babana meyasa kaman ta dani kabawa wani buzu yakawoni.

,"ban manta kaba d'ana buzun da yakawo ka gashi can a waje tare muke dashi yayan maman kane kamar ku daya kuma su buzaye ne akwai kannen ka maza Afwan yana aikin a India Dr ne sai Zannah shikuma shi yagajeni asiyasa shi nabar wa kujera na na minister mata na 3 mahaifiyar ku itace uwar gida inada yara dayawa yanzu haka Afwan yataso gobe zai sauka ananan sai mu iba mutafi kuga dangi.

Inna ZAINABU tace "yo ashe ba abanza ba Aisa take da dattako ahen jinin sarauta ce.

Mazan suka tashi suka fita sai Nabil ne kawai azaune  Har su Ummi sukayi sallama suka tafi
Hadim tace my star ka tashi mutafi Nabil ya Kalli Fandau yace "gawan zata b'ata mana lokaci nan malama tashi zamu tafi.
Tadaga ta kalle shi tace "Allah yakiyaye"

Nabil ya zoro ido yace "ban gane ba kina nufin ba tare zamu tafi ba.?

"tace ai yanzu nacewa Abban Nol yagaya wa Aunty anan zan kwana.

Nabil yace "ke kuma me gamin ki da gidan wata Aunty bayan da naki gidan.
Hadim tabe baki tayi zuciyar ta yana bugawa wani kallo da taga Nabil ya nayiwa Fandau kamar bakowa awajen sai su
Hadim Tace "Bagana nemo min Maaf acikin gidan yayi wani wajen zanu tafi.

Bagana tace "ai Aunty yaron nan bayaji ko kadan yana ta faman dukan yaran mutane har Tajjudee ma bai ba riba kije kine mi kayan ki dan idan nasa mu yana dukar mana yara bazan bari ba.

Itade Hadim fita tayi  Nabil ko yakafe sai Fandau ta tashi sun tafi.
Bagana tace "Mama kishiga cikin maganan nan mana.

Mama tace "Bagana rabu dasu sunfi kusa yanzu tare suka zo ko sallama bata muku ba a gidan Mutarin.

Nabil yace "Mama nifa ba gidan Mutari zan gaita ba gidan ta.

Dariya Mama tayi tace wane gidan kuma ban da abin ka haka akeyi.
Yace "Mama me? ake to.
"kabari akai ta idan ansa ranan tareya haka akeyi.
,"hama Mama wane irin tariya bayan ba musulumci bani kar kibata kofa mana.

Mama tace "Malam karami kaje matar ka tana jiranka Fandau sai anshiya.

Komawa yayi yazauna yace" tagama shirin ita Hadim bari nasa akai ta,
ita kuma ta gama mutafi ko nan da dare ne .
Mama tace " ajaf shirin lokaci guda zatayi ne sai nanda kaman sati idan anyi dawuri ma kenan."
atsorace Nabil yace "Mama kina tufin ma yanzu zan tafi da *mata* ba wannan din wane irin shiri ne ni  gidana da komai idan wani abu zata dauka anan ta fada inshiyar mata da kaina yanzu amma banda horon kwana  ni daya mama kinsan yanda nayi missing dinta kisa ta tashi ko na hada d'a Sayinna.

Itako Mama shiru tayi shida magana ita da jin kunya me ake da girma cikin turawa kwata kwata a d'abiyun Nabil ba na tsaren kanuri ko Shateema da ya girma aga banta ba zayi wanan rashin kunyan agaban ta ba.

"Mama kinyin shiru my one tana wajen tana jiran mu.

Dabara mama ta masa dan tasan zai iya zuwa ya hada da Malam kuma ba ruwan Malam zai ce ta bishi
tace "kaga yanzu dan uwana yazo inaso idan dare yayi mugana ajunan mu suma Bagana da Shateema anan zamu kwana dan haka gobe sai kazo kutafi.

"To Mama  bari nasa agai my one sai mu kwana ayi firan dani.

Mama tace "a a baza ayi haka dani ba shima Shateeman inda yana da wata matar ai bazan rike shima dan bai dace ba matar ka baza taji dadi ba,
 ai adalcin da akecewa kayi fa dama irin wannan ne kar kanuna fifiko tsakanin matanka zai iya kawo fituna da gaba dole asamu wacce tafi kwanta mata arai amma ka danne kar nuna afile ko ita wanda ka fison kar ka bari ta gane ita kafi so dan kar tayi anfani da damarta ta dagawa yar uwar ta kai.

Nabil yace "tabbas Mama da wacce ta fiso amma mama kimin adua kar ta gane dan kar ta mana girman kai.

 Bagana dariya tayi sosai

Itako Fandau gaban tane ya fadi towayafi so kenan cikin su

Mama tace "wannan damar kace kai zaka zama namiji duk da nasan dama kai namijine yanzu
 kaide kaje goben kadawo akwai karin nasiha da zan maka.

"Yanzu  Mama haka zan bar matata na tafi anya ba ashigar min hakki ba wllh badan keba bazan barta ba.

"yawwa to nagode d'an albarka kaje.

Cikin takunsa na isa ya taka har inda Fandau take ya sugunnan ahankali yace "kinga kinjawo mana ko da ina cewa ki tashin nan kika tashi da ba tace kizaun ba dan ma bani kadai nayi asara ba har dake,

Asali ma ni inada wanda zata mayemin gurbin ki,
 kece da asara dan wata k'ila nabaki y'ar da aka kwace ayau dako biyu zan baki har da bonus,
 amma yanzu me zan samu narage zafi nafa sa araina yau...
Dassuri Fandau ta meke dan gani take su Mama sunajin meyake cewa amma ko taku daya batayi ba caraf ya cakke kugunta a tsorace ta juyo ta Kalli inda mama da Bagana suke basu suke kallo ba amma da ganin yanda sukayin shiru sun san me akeciki
Fisgewa tayi zata kwace jikin ta ya juyo ta ita yana mata tani irin kallo  hannun yasa yarike hannayen ta bakin sa yakai setting nata yace "nace mezan samu my baby.
Idon tane yaciko da kwallah dan wanan tozar cin nasa da meyayi kama agaban uwata.

Girgiza mata kai yayi yace "to me ba anmiki yanda kike soba bazaki bini ba me na kukan kuma.
Ahankali tace dan Allah ka cikani.
Lumshe ido yayi yace '' Wow ko kinsan har da irin wannan muryar naki nayi missing.
Bakin sa yake kaiwa kusa tasan zai iya yin abinda yafi haka dan haka cikin karfi ta fisge tage kusa da mama da ta sunkuyar da kai Bagana ko danne danne dake awaya tana mamakin Nabil da rashin kunya

Yace "Mama kingan ta ko wai bazata rakani ba.

Mama har zata ce rakashi sai tatuna da rashin kunyan sa idan yafita wajen ma ba fasawa zai yiba ga kofar gidan su da jama a daranan Allah kar yaje yayi wani abun,
tace "a a bar rakiyan nan kasan Fandau tana da kunya me damuwan ka darakiya kaida gobe zan baka ita gaba daya.

"kallon Fandau yayi yace "Mata wai kunya kikeji?
Fandau ko kallon inda yake batayi ba
Ya juyo kan Mama yace kigaya mata ba kunya tsakanin miji da mata hakafa tayi tamin abaya ma sai fa kin koya mata wasu abubuwa abaya na mata uzuri da auren na rashin shirine baki bata nasiyan aure ba  amma yanzu nasan zaki gaya mata komai bana son wani kunya.

Mama da abin yade na bata mamaki tace "ai shine nake son ka barta amata komai akoya bata komai.
Yace "shike nan Mama ki mata kafin goben.
Amma nima anjima da daddare zan kawo Akkam ya dauki Akkaam da yake zaune cikin keken sa zai fita
Fandau tace "Mama kice ya barmin Akkaram.
Mama da sota ke  kawai taga ya tafi tace "ba anjima zai kawo shiba.
Juyowa yayi tare da kanne mata ido yayi mata murmushi ya fice.

Bagana tace "Mama wannan rawan kan YaShid dinnan anya zai iya zama da mata 2 awajen daya.
Mama tace" akwai  de matsala saide muca ALLAH ya kawo musu zaman lafiya.

"Amma Mama da alamun kamar yafison ya Fandau fako.
Mama tace gaya miki yayi.?
"A a kawai alamu nagani.
Mama ta daure fuska tace "to karna karajin haka abakin ki
Nabil yasa mu Hadim da yara amota tacika fam yana shiga
 yace "
Sorry my one.

"Yanzu  abu Fuj ina ka tsaya.

wllh Mata ce wai tamin rakiya taki
Hadim ajiyan zuciya ta sauke cikin muryar tausayi tace" yanzu my tsar  shikenan munza ma mu 3 kishiya ta tabbata akaina kenan ko?

Jawota yayi yace " *hukuncin Allah* wannan mukaddari shiku ma hakkunne akan kowane me imani Halima bamu tsara rayuwar muda haka ba muntsara ne iya mu amma kaddara ta daura mu akan wanda Allah ya tsara mana yazamuyi kuma ke kika fara kawo wannan shawaran da naje na gana  da ita nagano yar gidan Zannah ce saida na koma nace miki abin nen bazai yuwu ba amma kikace Zaiyuwu  kika nace akayi abinnan kinga yanzu yazaga yo ta inda yafi karfinmu dole muzauna da ita  murungumi kaddara shiko kaddara mekyu da marar kyu  duk kar bansa imani ne kidena sa komai aranki ba abin da zai faru da zaman mu zanci gaba da sonki zannu na miki tattali fiye da da idan gidana ya gyaru kece idan ya b'aci kece wannan yarinyar yanda kika horata haka zatayi idan kika so kuzauna lafiya nasan zaku zauna idan kika so fitina zakuyi wanda nasan kece da asara dan idan Kuna zaman lafiya yaran baza su kane wacece uwar ba koda zasu gane sai sunyi wayon da baza su iya nuna miki ban banci ba amma idan ba azaman lafiya nasan tunsuna yara zasu gane kuka bayan mahaifiyar su zasu koma inde kuna zaman lafiya ba abin da zaku nema kurasa.

Goge hawaye ta tayi tace, "to yanzu kana nufin kana sonta fiye dani koyan da kake nunawa kafi sonta kaduba yanda karukice da batanan kadinga gayamin magan ganu shine nake ga zaman bazai min dadi ba.

Goge mata hawayen yayi yace "waya kaya miki na fison ta da na rasa ta nariki ce ai inda ke narasa da saide arasani haba Hadim dimata dama nasoki balle yanzu da kika rikemin yara kike nuna musu so ai yanzu inde naga kun zaun nafiya zan soki fiye da da.

"towa kafi so acikin mu.

Shiru yayi can yace "Gaskiya yanzu bazan iya cewa ga wacce nafi soba abin da nasani ku dukka matana ne saide ance zuciya ta fison mekyutata mata to idan na zauna daku duk wacce tafison kwanciyar hankali na inaga ita ce.
Hadim ta sauke Ajiyan zuciya ta dauki Akkam da yake kuka tace "ALLAH Abu FUJJI wannan ma yashi ga raina ina son sa.

Dariya Nabil yayi yace "to komu koma wajen Baban ki zannah ya hada miki dashi dan naga yafi sonki fiye da Fandau din ma.
Ita ba dariya tayi tace "wllh kuwa ni ma haka kurum naji ina mutu kar sonsa dan yanzu bazan ce maka gawan da nafi so tsakanin shida Babana ba Gaskiya da can jin labarin Zannah nake yanzu naga halin nasa da akecewa Zannan barno katan barno afili,

Yanzu fa da zance inason har Akkaam din saiya hadamin dako naji dadi toma meyasa bance har shiba.
Nabil dariya yayi yace "zaki iya mana ai kin kware da mugunta kina gani tace abata FUJJI kika kijin tausayinta har kuka ta miki tana cewa Aunty kiji tausayina amma ki kak'i.

Tace"haba taya zanji tausayin ta bayan nice abin tausayin ai da gaiya nakafe nima FUJJI nake so tunda nasan kafi sonta ko ta dalilin ta nima sona zai karu.
Yace 'Gaskiya kam bana jin zan sake son wani fiyeda Ummuna.
drive yaja suka tafi

Da yamma Fandau sugama waya da Habiba ta kaya bata har sunwuce kaduna.
Fandau tace "haba Aunty kuma sai kibar ni.

Ni na isa na fito da matar Shiddams nasan de naga ma miki abinda zan miki sai fatan Allah yakawo zaman lafiya  akwai sauran abubuwan ki kije gidan Aunty Maimuna nan ne zakifi sakewa kiyi gidan ku gidan jama a ne shiya sa yar sundan ma acan ta sauka kiyi kitafi tana jiranki.

Fandau tace "yanzu Aunty sai yaushe.?

Habiba tace "Sai kunzo London zance.

"umm Aunty agaida min Haris da Kairat Nol muyin fad'a.

YaMainuna ce takira ta tace tazo tawuri mai mata aikin tazo dan Wata aka dauko a sudan wada zatayi wa Fandau aiki Habiba ce ta biya kudin komai
Fandau ta gayawa Mama zata tafi gidan YaMainuna mama tace ga wanan ki tafi dashi gaba daya zaki shanyen ai gwara kawai kije da ga can rashin kunyan mijin ki yayi yawa ita de Fandau ta dauki jarkan ta shige d'aki dan ta shirya ta rasa meyasa ta ko ina ana ta dura mata abubuwa gashi maran ta sai ciwo yake mata

Yar sudan ta murjen jikin Fandau sosai rami aka tona mu sammanin aka sata ciki aka fura wuta t
Da wasu ingan tattun itacuwa ake gasa Fandau dashi aka rufeta da barko sai kamshi yake ta shi sai ta kakayi kwanaki ukku ana mata gada ma Fandau da laushin fata abin yasake karuwa sai wanda yagani ita kanta me kyaran da akace matar Shiddams ce sai tasake azama wani irin shek'i da sansi take kowa ya kalleta sai yasake kallon ta arana na 4 Mama ta kirata tace duk abinda za ayi yau tazo ta koma gidan da
"Mama aikin fa ba Agamaba.

"ko ba agama ba kisan yanda zakiyi rasshin kuyar Nabil ya ishini bazan iya daukan magan ganun da yake fada ba yau har da Malam ya hadani jiya ma Ummin sa yaturo min wai tazo taji na boye masa mata ko ina shirin hana shine na gaya masa  harda kuka yayi wa Malam abin ya isheni yanzu nazo akiran Malam  yace zaikira Maimunan ma.

Fandau tana kashi waya ta gayawa Maimuna suka gayawa yar sudan tace "ai wannan aikin da na mata ya isheta ai namata aikin mekyu saide abin da nake so dake wanan aikin da namiki kisamu duk bayan wata 6 ana miki dan maku meduguri kuna da abubuwa muma anan ake kai mana wasu Gaskiya an miki aiki duk da dama fatan ki mekyu ne.

Wow wani Lalle da aka zubawa Fandau da kitso abin sai wanda yagani bayan tayi sallahn isshai ne wata me makeup ta zezara mata kwalleyan da ko mama baza ta gaji da kallon ta ba
Ta ko ina sai
  ta kifta sai kamshi take bazawa ta tsaya agaban mirror ta na kallon kanta tace yanzu dama haka nake da kyu lalle a aurena na farko nacuki kaina da ta tuna yanda aka kaita daren farkon kamar wata sobon kamu ita kanta sai da taji kamar kar ta yafewa kanta

YaMainuna ta shiro tace "Fandau kizo mutafi Baa har yayi waya wai ga Nabil agida ai nikam yau sai na ga Nabil dinnan ido da ido

Agidan ta samu yan uwanta mata dayawa sunzo rakata ALLAH sarki Bagana sun tafi Niger da Shateema dan da harda Mama aka shiya tafiya sai Malam yace abari Fandau ta koma gidanta sai shi yakai maman da kansa inyaso sai suzo dasu Shateema dan bayan da ba ayi da shateema maba yatare can yaki shi yafi son Nigeria ba arage shi da komai ba

Mama tayiwa Fandau nasiya haka YaMainuna tayi ta zagawa da ita d'akin matan gidan wada yanzu sun sauko gaba daya suma sunmata nasiya BaGaji ko harda neman yafiya
Sai d'akin Malam shima nasiya yamata sosai san nan yadauko Qur ani da sallaya ya bata kamar yanda yake yiwa dukan yaran idan idan za akaita d'akin miji
Yace" kibi mijin ki rike Qur ani ki kula da ibada daga kar she yadauko alkebba kamar yanda yake yiwa sauran yaran ya rufa mata dan sai anbiya dasu fada kowace amaryar agidan zannah sai ankaita gidan SHEHU SHEHU yasa akai ta shiya sa Nabil da yazo shi zai kai matar sa abashi aka ce A a yayi zuciya ya tafi abin sa
YaMainuna tace "Baa gobe munshirya walima zamuyi wa yar uwar mu.

Malam yace "a ina zakuyi waliman ?

"a gidan ta zamuyi.
Malam yace "a a Maimutatu sau nawa take kaya muku bana so inde gidan da abokiyar zama to kugama duk abinda zakuyi agida inde ba taron suna ba ban hana ba.?

"Eh Baa wannan dinne yazo akureren lokaci bamu zaci za ayi tariyar yanzu ba ne.

"to ku hakura tunda ba sabon aure bane kuma ta adua ainda  kuke ya isar.

YaMainuna tace "to Baa Allah yakara maka yawan rai.
Ta gyarawa Fandau alkebba akan lifayan ta ta kama hannun ta suka fita
Zasu shiga mota Fandau yace
 tace"Yamuna ba zan shiga wajen Mama ba?
"a a Fandau kuka zaki mana ai kungama.

Gunsu matar SHEHU tayiwa Fandau nasiya tare da bata turaruka da wasu abubuwa ta hada mata bayi 2 tace zasu koya mata wasu abubuwa da zai mata amfani sannan aka rakata bangaren SHEHU yamata nashi nasiyan tare da yimata kyuta
Aka kwashesu sai gidan Nabil da yake shagari quarters gida ne nagani na fad'a dan an shafti jeji inya ganin ka fadin yanda gidan yake b'ata lokacine
Part din Hadim aka fara yi da ita
Hadim uwar yan mata ta tarasu suna zaune su yasmin Hadim ta karbe su bayabo ba fallasa da sukace amana dariya tayi tace "amana na karba Aunty muna tun agaban Baa.
Addua sukayi suka ce to inane part din nata dakan ta tashi ta kama hannun Fandau ta raka ta har bedroom  tace "bari akawo muku abinci.

Suka ce laki barshi wllh munci a gida kuma da muka je sheuri sai da kuka kara.
Tace "aiko dan ku akayi dan haka sai kun tafi dashi.
Zahra tace "Wllh zaki hadamu da aiki dan wllh kowacce gidan ta zata wuce dare yayi.
AISHA tace "akawo kawai sai akai gidan ai zaiyin amfani suda suke da almarai.
Bayan tafiyan su Fandau zama tayi agan gado meyafi wandan dadi na bari ana farko *DAMA TA* ya kufcemin gani cikin yan uwana ankawoni cikin mutumci
Tana wannan taci anbude kofa dama fuskan ta arufe yake amma daya ke liffayan shara sharane tana ganin su gaban tane taji yabadi tunowa da ranan da ta fara ganin su ahaka ta gan su randa Sani ya kaita London ahaka suka shigo shigan su iri daya hannun su sakale da na juna suna tabu ahankali suyi matukar kyu koda yake dama sarakan kyune dan Fandau kyun Hadim har tsoro yake bata
Ahaka suka karasa suna jifanta da murmushi tana kallon su tacikin mayafin sai da suka zo kusa ta sunkuyar da kai zama sukayi abakin gagon Hadim ce ta fara magana tace amarriya ko me dan kiraki mani kinga tarishi ya maimaita kansa ko nice de Halima Jaji nashiko miki da mikina Muhammad akaro na biyu kamar yanda muka maki mamaki awancen karan yau ma zamu sake jefaki..............


*kashhh* 🤦‍♀
*Sister kuyi hakuri bana jin dadi ne wllh*
*B JATTKO*
[3/12, 8:50 AM] Hauwa: [3/9, 3:08 PM] BATUL ADAM JATTKO: *DAMA TA*




                  *NA*

*BATUL ADAM JATTKO*

Wanan shafin nakune group na masoyan Fandau da Nabil  khulud na baku wannan duk ka 🤣🤣🤣

🌈Kainuwa writers Asso🤝🏻

*48*

Cikin wani salon mamakin domin mun jijina miki kedin me sa a ce ba k'aramin sa a kikaci ba kin samu mijina  kuma nima na yarda na karbe ki abokiyar  zama dalilin karamcin da Baban ki yamin shiya nunamin Duniya ba komai bane shi tunda har ya danne barin cikin yar da ya haifa yabawa yar wani hakan yanunamin wannan hadisin da ake cewa kasowa dan uwan ka abin da kasowa kanka,
ina fatan zamuyi zama na fashimtar juna my star ba kace komai ba.

Murmushi yayi yace my one inada abinta cance amma naga bakuwar tamu kamar ta nacikin bak'unta ne saida safe zamuyi zama na musamman.
Hadim tace" ummm to yanzu saide nace muku saida safen ku ko,
 auna manta ban fa siyi baki.

Nabil yace "Gaskiya ne dan yanda aka ja faska aka rufen nan inaga saikin siya.

Hadim haurawa tayi kan gadon ta dan d'aga mayafin ido ta zaro tayi saurin sakin mayafin tana karanta Innalillashi azuciyar ta ita da kamshin da take ji ajikin Fandau tun sanda zata rakota d'aki ma yake sawa gabanta yake faduwa balle
Yanda taga fuskan ta tasan ta sha gyara duk da bawani tarkacen makeup ne afuskan ba dan ko janbaki ba asamata ba dan meyin makeup din haka tace lips dinta kalan yayi daidai da makeup dinta dan shima ja ne  gashi sai sheki suke
yanzu wannan zan bari da mijina nashiga ukku amma sai ta dinka karanto adua sai ta sauke ajiyan zuciya
Nabil yace "yade my one?
Murmushi tayi tace "wllh my star amarriyar tayi nayi kuskuren bude fuskan ta batare da biyaba yanzu de kai zaka biya.
Dariya yayi yace "ai nasan my one tana jidani baza ta yanka min abin da bazan iya ba me ki keso na bada.?

Hadim tarasa mezata ce kawai sai ta Kalli hannun sa tace "zobin ka zaka bamu.

Yakalli tsadeden zoben yatsan sa wanda yake iri daya dana yatsan Hadim ma ya ciro ya meka mata ta karba  ta janjo hannun Fandau zata sa mata a ya tsanta wani irin laushi taji wanda Hadim bata ta b'a sanmanin akwai shi fatan mutum ba ga Lallen nan yagama hawa kan hannun  Nabil zubawa hannun ido yayi  Allah Allah yake Hadim ta fita dan idan ta matsa zai iya kof sawa agaban natama zoben taga ya karawan hannun nata kyu dayake na farin daham ne
Da ganan ta sauko a gadon tameke  hannun ta yaruko yace "ya haka yana kallon fuskanta tace" da akayi me?
"naga kin meke baki budemin fuskan da nabiya ba.

Azuciyarta tace bazan iya budewa naga ka kalli wanan fuskan nata ba
Afili kuma
Tace" ai dan ansai da maka abu balalle abude kagani ba zaka iya budewa da kanka musamman amarriya ai angonta yaka mata ya bude ta dan abata matsyin ta na amarriya ko.
"to yanzu ina zaki da kika meke.?
Hadim tace "kasan nabar yara banason wani yafar ka bai ganni ba.
 yace "ok muje na rakaki.
Suka fice
A parlour ta tsaya tace "ka koma rakiyan ya isa Allah ya tashemu lafiya.
 Yace "nide sai na kaiki har wajen yaran ki naga kwanciyar ku.
Haka suka tafi har bedroom din Hadim  sai da ta kwanta  yayi adua yasha feta sannan ya da go fuskan ta cikin damuwa yace "my one ke ta musamman ce wllh ina tunanin yanda zan iya kwana ba tare da inajin nun fashin ki ajikina ba bawai bana son kasan cewa da Fandau bane a a kedin dake na shak'u ki min adua naza ma adali a tsakanin ku kinji.
Wani irin sanyi Hadim taji aranta wanan magan ganun nasa shi yake samata shakku na cewa Nabil bai dena jida ita ba
Tace "nima haka Abul Fuj wllh har tunanin nake yanda zanyi na lallashi zuciya ta bayan nasan zaka kwana rungume da wata.
Rungumo ta yayi yana goge mata hawaye
Yace"ki tashi kiyin sallah kiyin adua zaki samu nusuwa kuma kibar wayan ki abude zan kiraki anjima.
Tace"to ka tashi ka tafi kaga kar mushiga hakkin wata dan dare yayi saida yayi kissing dinta ya saketa yajuyo yabi yaran da ad'ua duka yayi kissing dinsu yaja blanket ya rufefi yace "my one kirufe idon ki bana son kiga fitana.
Murmushi karfin hali tayi ta rufe idon yadago hannun ta yamata kissing yace gobe amiki lalle kinji kanta ta g'ada
Yace" sai dasafe ya fita
Da sauri sauri yake taka mata kalan jiyake kamar ba zai karasa ba
Har yanzu tana nan inda suka barta k'arasawa yayi yana murmushi yana dafa hannun yace" yar Mama kinga ma guje gujen ki yau gaki ad'akin Muhammad Habubakar damasak tsawon  watanni 10 kenan ina fama da rashinki  hawa yayi yace "wai wannan din wane irin turaren ne Wllh tun a general parlor na fara jin kamshin sa.
Cikin tattausan muryar ta tace "wanda katsa akayan lefene.
Janyi hannun sa da yayi niyar bude mata fuska yayi yada murmushi ya dafe kai alaman mantuwa yace ,"gori najiran ranansa wllh kokarin samun ki yasa na manta da ana wani lefe arayuwa amma kada kisamu damuwa za amiki lefen da ba atabayi wa kowacce irin macce ba ai wannan bai kai gori ba da kanki zaki hadawa kanki lefe dan banason lefe ya toyemin wani jin dadin.

Ahankali yasa hannun ya daga mayafin shima ido yazaro yaja wani nunfashi
Cikin in ina yace " Alhamdulilah mata kece haka Allah na gode maka da kanin baiwa da matar da ganin ta yake karamin nusuwa Masha ALLAH
Mata me zaki cewa wanan ranan?
 Tace "inajin sa kamar bazai wuce ba Nabil nasha wahala da narasa ka arayuwa dan Allah kar ka k'ara bari murabu koda na kwana dayane wllh kafi hasken rana haskaka zuciya ta burina narayu da kai.

Ai baisan san da yajawo taba "yace Rabbi soyayyar mu kai ka hukunta kuma kaine majibi cin lamuran mu ALLAH ka amince narayu da da abin kaunata
Mata bar batun rana daya ke kashi fuska ke hasken farin wata ce mesa nishadi haka sukayi ta musayen kalaman soyyyya daga nan yace "muje muyi alwala muyi sallahn godiya ga Allah tare da rokon sa yabar mu cikin aminci ko a wajen shiga bathroom ma cewa yayi kishiga ki fito dan yasan idan yadake ya shiga da ita sallahn da yayi niya bazai yuwuba dan haka saida tafito ya shiga bayan sun idar ya dafe kanta yamata adua dama yasan tasan komai dan haka yace " me zakici.?
tace "naci abinci yanzu de inason cin tufa idan awai. Yameke yana cewa "ni na isa ina shirin ajiye maiyar apple agidana na kasa ajiye wa. Yanufi wajen
 bude fridge filet ya dauko ya sa apple din aciki ya ajiye ya fita kichen yadauko dan kara min wuka yayiwa apple din kananan yanka ya yajawo ta jikin sa ya ware liffayan ta wani irin yar yaji ajikin sa da kyar ya daure ya dinga bata abaki tana ci "mata wacece ta miki wanan kalle.?
"Ummu Salma ce yar gidan YaMuna.
"wacece YaMuna?
"YaMainuna ita ce babba a matan gidan mu tafi YaBunu ma.
"ok da ita Ummu Salma din zamu koma ta namiki wanan lalle acan ta iya.

Tun yana dan shafa hannun har ya zarce sauran gurare itako
Abin nasa ma tsoro ya bata asanda ya mata fatale da kaya ganin yanda sandan girman sa yaringa wani irin zungurin ta da sauri ta ja jikinta ta koma gefe dakyar yabude idon sa yace "mata Wayyyo mata   me kika yiwa fatan jikin ki da kika janye naji kamar kin rabani da rushina yana maganan yana Matsowa kusa da ita
tace "Allah Abul kaam bazan iya yanda kake soba kagan kafa kaji tausayina.
,"nima kiji tausayina wllh sonki ne yamai dani haka da tsantsan bukatan ki shi yasa asanda bama tare idan na tuno ki har kuka nake idan ina tare  dake ne kawai nake jin wannan yanayin ko bakya sona ne.
Ina sonka Habibi ba zan iya daikan ka bane.
Mekewa yayi ya dauketa cak ya daura ta bed bawata wata  kawai ya haye mata tace "habibi kar ka shigeni ahaka Wayyyo Allah.
Cikin dashewar murya yace ki rikeni gyam kuma ki rufe idon ki
Saida ta rafe idon yanemi kofa yarasa sai a nan yagane me take tsoro ashe amatse take hade  bakin su yayi sannan yayi addua saduwa sannan ya nemi hanyan ahankali sa ansa ma yasamu wajen da lema wani azaba taji duk da baikai daren suna farko ba amma sai da tasa k'ara  ai Nabil kuka kurun yakeyi wuwu ita ma tanayi saide ita nata na azabane sai sun batu yake "Wayyyo Allah mata kasheni zakiyi Duniya akwai mata Awai muna mata Gaskiyar su Usman da suka ce da matar dare da matar rana wayooo mata kimin adalci kibar ni haka.

 itako ta kanta ma take Nabil bai sarara ba harsai da yaji ta sake masa gaba daya ya mirgina gefe yana maida nunfashi sai kuma yaji wani irin zazzabi ya rufeshi yana ganin yanda take fitar da nunfashi amma yarasa ko d'aga hannun sa ya  daura bata yana son ya ja bargo yarufe su amma ya kasa
Fandau da kyar ta daidaita kanta taja ta sauka tana taku ahankali ta shige bayi da kyar ta daga kafanta ta shiga cikin bathtub din ta saki ruwan zafi ruwan yana ratsata ta lumshe ido dama YaZaha ta fada mata zata sha wahala dan wani hadin dorrot da suka bata sun ce ko yatsa da kyar yake shiga sai yafi wata Budurwan hadeta gashi ko tagani
Tagama ta fito daure da towel sai dan karami tana gode kanta dashi abin mamaki ayanda ta barshi ahaka ta sameshi ko rufuwan baiyin ba itade taja jakan kayanta da tazaro wani rigan bacci ta da aka gama hadeshi da turaru kan wuta tasa tun kafin ta hau gadon taji hakoran sa suna hadewa tsayawa tayi kallon sa taga yana karkarwa da sauri ta karasa hawa tace "habibi  me? Meyake damun ka dakyar ya daga hannun sa ya kamonata zafin taji rau a gigice ta matsa daf dashi ta jasa jikinta zafi sosai yake bugan ta cikin kuka tace" habibi kayi magana mana me yasa meka.?
Hannunta yakama yadaura a wuyansa ahankali ya bude bakin sa yace "kasala ne yafi damuna na kasa tashi ga kuma jikina zafi.
Fandau tace yanzu Habibi ya zanyi.?

" kibar kuka dauko k'a yana ki samin.

 da sauri tadauko kayan ta sa masa
Tace "sannun YaShid yazan maka?

Yace "daukomin wayata.
  da sauri tameka hannu ta jawoshi yace kimin dialing din Dr Hafeez da dauri ta shiga contact din tsabar gigita ta sha wuce no din ta kyar ta samo saida taji yana ringing har sai da tayi calling so 3 taji anyi picking  cikin muryar bacci taji ana cewa "Shiddams meyake faruwa ?
Kara masa wayan tayi akunnen sa
Yace "wllh nine jikinane ya mutu da kyar nake motsashi ga zazzabi?

Yanzu Shid zazzabi har yakai kakirani karfe ukku na dare haba kawai sauron Barno ya tabaka gaka bature....

Nabil Yace"Ni ba sauro bane daganan ya kwashe yanda yakeji ya gaya masa da abinda yafaru itako Fandau shine da fad'a itace dajin kunya.

"tsaki doctor yayi yace kana da karfin sha awa kasan haka tun kana saurayi meyasa kake son tarawa kanka sha awa wllh idan kana bari (mani) yana taruwa maka  da yawa wata rana ba k'aramin lila zai maka ba dan haka shawaran da zan baka kacire tsoron Hadim ka kara aure  kawai dan wannan rashin lafiyan nata ne da kadade ba ka samu nusuwa ba shine katara sha awa wanann zazzabi na lafiyan da kasamu ne nasan kafin ka samu nusuwa kana fama da ciwon mara sosai to yanzu lafiya ka samu kuma nanda awa 1 zaka ware.

Shiru Nabil yayi yana gaskanta Dr to ko da yamman nan da abin ya matsa masa saida ya rage zafi da Hadim amma shi kansa yasan tun daren da yafara sanin Fandau bai taba jin sha awar wata macce ba idan yanemi Hadim jiyaje sha awan sa ya karuwa bawan gamsu mararsa yayi ta masa ciwo Ya Allah kasa na nuna adalci a tsakanin mata na ita wanda nake son kar ta gane ita nake so itama Hadim Allah kar kasa ta gane abaya take
Dr yace"ko kasauka ne? yace inajin ka yanzu yazanyi na dan samu sauki.?
"nagaya maka yanzu zakaji kaware amma kafinnan a kashe maka AC karufu dan kasamu gumi ya zubo maka ko kasamu tea mezafi kacika cikin ka dashi.
Nabil yace ok ya cire kunen sa ita kuma ta kashe ta ajiye wayan  tace "meyasa  ka kasance me tona asirin aure.
Murmushi yayi yace "ba tona asirin mu nayi ba likita ne fa
Ki rufeni.
Tarufe shi ita ma tashiga ahankali
Ba ajima ba taji bacci ya kwa sheshi itama haka
Juyi zatayi ta bude ido taga alamun kamar gari yawaye da sauri ta d'aga ta kalli agogo jikin gadon yanuna mata karfe 9 na safe har ya gota salati tayi tashiga toilet agurguje tayi alwala saida tayi sallah ta meke taje ta tab'a jikin nasa taji bawani zazzabi baccin sa yakeyi cikin kwanciyar hankali itama ta kwanta tayi daidai idon sa take hura masa iska shiru bai tashiba hannun tasa tana shaho fuskan sa ahankali ya bude idon sa cikin jin bacci sosai yace "my Mata bacci. yarufe idon tare da jawota jikinsa
"Ka tashi kayi sallah rana tayi.
Da sauri yabude idonsa yace *"Yasalam!*
[3/9, 6:08 PM] BATUL ADAM JATTKO: Ya sauko yayi hanya batdroom yafito yana goge jiki kayan baccin nasa yasa yayi sallah dashi kafin ya idar har Fandau ta shiga tayi wanka tana zaune awajen mirror tana shafe shafe ya zo bayanta yana kalonta ta cikin mirror suna hada ido ya sakar mata murmushi
Tace "Abul kaam ya jikin?
 ina kwana?
Karasawa yayi inda take yasa hannu yana shafa kanta yace "wannan kitson fa wayamiki?
Tace "Umma Salma ce?
"kai wanda ta miki kunshi amma wannan dole muje da ita.
"nace yajiki bakace komai ba?
"Eh ai baki iya Gaisuwan ba shiyasa nak'i na amsa miki.
Tace"kamar ya.?
Yace bari na koya miji yanda ake gaida miji.
Ya d'agota ta meke shi yazauna amazaunin nata ya daurata kan cinyar sa idon sa cikin nata yasa fuskan sa cikin kirjinta yana goga hancin sa a boobs dinta wani irin laushi yaji ai take yafara wani irin gurnani dama towel ne ajikinta  ai yana sulbilewa ko ya sake  rekicewa cak ya dauketa ya dan ganasu da gado Fandau dole ta bari yayi yanda yakeso dan aunty Habiba tace kar ta nuna masa ragonta gurnani da alkawarirrika ta ma rasa wanda zata dauka yana mirgina wa ta duba agogo yanuna 11 na rana amma sai taga yana lumshe ido ya jata jikin sa ba ajima ba taji saukan nufashin sa yayi bacci ta dago kanta yana bacci wani irin son sane yake nunkuwa azuciyar ta yanzu wanan balaraben shine mijina ni Fandau da samarin Anguwar mu suke kira da yanga acikin Summa daga hannun tayi tana yiwa Allah kirari da godiya akan baiwar da yamata
ahankali takai bakinta kan nasa ta dinga lasa har bacci itama yayi gaba da ita yanzu ma ita tafara farkawa jin kamar ana knorking
Ahankali tafara raba jikin su

Aban garin uwar gida Hadim kuwa Nabil yana fita taji wani irin kuka ya taso mata dan tasan ayan da taga Fandau ba namiji me lafiya da sai ganta bai rudeba da taga shedan yana son samata rashin nusuwa kawai ta tashi ta shiga bayi tayi alwala tazo tayi ta jera nafila daganan tayi addua ta kwanta saide taji Nabil bai kirata ba
Da safe su Yasmin ne suka hada
break kamar yanda suka saba suka jera a babbar parlour amma har 11 basu fitoba abin yabawa Hadim mamaki ya har b'uya tayi tasha kukanta batare da kowa yakani ba takira wayan sa ba adadi ga Fuj sai kuka ta ke mata taki cin komai ita ina Abul haka ta rungume ta tafara kuka itaba su yasmin suka bata hakuri Jidda tace

 Aunty "dama ance amarriya ko ta buzuzu ne sai anyi dokinta amma kidaure zai wuce.

Hadim tace "ai ni bawani abubane dama FUJJI ce taki cin komai wai ita Abunta yazan mata Ashuwa ce  ta jata taje take faman lallamin ta har taci abincin daga nan suma sukaci Hadim de cakala kawai take tana kora ruwan tea dan kar yaran sugane suna cikin cine wayan Hadim ya fara ringing ta dauka Dr Hafeez tagani picking ta reda sallama ya amsa yace "yajikin nasa nakira wayan baya picking shine na kira naji ko lafiya.
Hadim tace "waye ba lafiya.
Dr Yace "Shiddams yaki rani wajen 3 nadare bashi da lafiya shine nakira naji.....

Ai tun kafin ya karasa Hadim ta meke tace "ok
Bari inazuwa.
Ta kashe wayan tare da Mekewa da sauri ta haye saman tafara knorking
Fandau
Da kyar tasamu taraba jikin nasu ta dauko shijab dinta har kasa tasa wani irin yinwa take ji dan haka dakyar take tafiya tana hada hanya ta karasa ta bude Hadim tagani ,"lah Aunty kece ina kwana.?
 Hadim" tace  ina yake meyasa meshi.?
Fandau tace Ayyya yana bacci zazzabi ya sauka ai
Hadim rab'awa tayi ta gefen Fandau ta wuce da ganin yanda gadon yake
Ayamutse tasan anyi aiki amma sai ta haye gadon ta d'ago sa idon sa arufe yakamo hannun Hadim fuskan sa cike da annashuwa yace "mata kibar ni wllh idan na bude ido ina kallon ki bazan iya kyaleki ba sai na wuni ban gaji ba gashi ina tausaya miki ke jarumace.
 amma sai me hannun yakeji kamar bana Fandau din saba ai da yashafo dantsen hannun da sauri yabude idonsa ya daura akan na Hadim da yaciko da kwalla
Cikin  in ina yace "my one kece?
ajiye kannasa tayi ta ahankali zata sauka ya kamo hannun ta amma sai yarasa mema zaice kurawa juna ido sukayi
Sai asannan Hadim ta gane bakomai ajikin sa sai bargon da yarufe rabin jikin sa tace "dama dr Hafeez ne yakira yace baka da lafiya amma da nazo banga alaman haka ba kana da bako ababban falo sai ka fito tana gama fadan haka ta kwace hannun ta tameke tana tafiyan ta akarkace dan kafa har yanzu bai ware ba
Tana fita tayi part dinta ta fad'a gado tana kuka Wayyyo ni Halima bazan iya zama haka ba zuciyata zata fashi saide yara ba mana gida kawai

Dago kansa yayi kalle ta yace "mata ya akayi baki tasheni ba kika bude kofa ta shigo har d'aki.

Itama Fandau cikin fushi tace "na dauka zata tsaya a parlour tace nakira mata kai  amma sai naga tashiko min har bedroom har kan bed dan isa koda yake ta isane idan anyi la akari da rayuwan da mukayi abaya ai zatayi wanda yafi haka ma.
Kallon ta yayi yana tabe baki ya jawo towel asaman gado ya daura ya meke yaje daf da ita ya d'ana mata yatsan sa abakin ta yace ni zaki zunburo wa ai wanda ta shigo miki zakiyiwa in banda sokuwa har kina tsaye macce ta shigo miki har bedroom har gado ta daga miki miji ta daura acinya duk kina tsaye?

Itako Fandau lips dinta take murzawa tace "Allah kai mugune kafara muguta ko.
"neni mugun sonawa na taba miki mugunta.?

"so dayawa kasha d'ana min wanan hannun naka a lebena har marina fa kashayi da duka ad'akin uwata.

"marin namiki a London akan kince Shateema yafini kyu kuma zaki aureshi ne ban manta ba dukan dana miki ma akan kishine.
Yana magana yana cire mata shijab dinta
Yace "amma kin manta mugunta da na taba miki.
Tace wanne cikin rigan ta yasa hannu yakamo books dinta  yace "na taba cizon nan harki kace inba maye ba wazai ciji mutun anan wazai tsosi nan kin manta.?
Fad'a fasa tayi tana dukan kirjin sa "Allah banaso.
"ni kuma Allah inaso kinsan ni mayen kini idan maitar ta motsa har gurnani nake nafi maye ita maita kamar kura nake dan...... .
"Allah kadena.
Lebin ta yakaiwa hannun yace "waike wani irin lips gariki daga d'an wanan shafawan har ya dan ja.
 kafin tayi magana har ya hade bakin su ya sungume ta sai kan godo
Da taga yazarce kuka tasa masa "ALLAH habibi na gaji yunwa fa nake ji. idon sa ya d'aga yakalli agogo yaka yaga1 har ya gauta
Shi yama manta dawani abinci aduniya tabbas zata ji yunwa wannan aika tuwa da tayi shikan sa saida ta tuno masa yaji cikin sa bakomai
Yace, "ai ke dince ce da zafinki kika shigo  gashi har na manta da cikinmu,
Shiga bathroom ki watsa nima zanje na daya d'akin.
Zunburo baki tayi
Tace " nede saide muyi tare ai haka ka koya min.

Dariya yayi yace "naga alama kema fa fitinan kanki ce harija ce ko kinsan fa awajen wankan baza abarki ba amma kike nema tashi yayi yasauka yana gyara towel din sa ya dunkufo zai dauke ta da sauri ta rarafa ta sauka ta daya gefen dagudu tayi hanyan toilet din tana shiga ta rufo dariya yayi ya sauke ajiyan zuciya yace Allah kasa kar son wannan bawar taka yamin illah shima yafita ya shiga daya d'akin  yariga ta shiryawa yashiko itama ta sha kyu cikin wani arnen material ja dinkin yadace da kayan kayan ya dace da jikinta wani siririn sarka tasa silvar iri daya da agogon tana daura agogon ya shigo
Da sauri yak'ara so" Wow Mata wllh idan kina min wanan salon gayun sai ki.... Ya dauketa yana juyata "kayi sallah Allah kaga har kusan karfe 2 wllh idona ya fara ganin 2-2 hanyan fita yayi da ita saida suka je parlour karshe tace nide ka tsauke ni ko ta kanta bai biba da Allah yasa Hadim bata man parlour saisu Jidda jin taku yasa suka d'aga kai amma ganin yada suke duk sai suka sunkuyar da kansu itama Fandau ta naganin su tayi saurin durowa murmushi yayi ya kamo hannun ta suka tsauka ahaka suka karasa yana mata magana k'asa k'asa saida sukazo daf dasu suna suka ce "YaShid ina wuni?
"Lafiya.
Yace tarida jan hannun Fandau suka zauna kujera sannan suka Kalli Fandau suka ce Aunty Fatima ina wuni?

Cikin wani salon yanga da tsare girma tace "kuna lafiya.
Dan Habiba ta jamata kunne akan kanne nasa duk yaran Hadim ne kar ta kuskura suga fuska awajen ta su rena ta dan duk sun girmeta ta ja ajinta sosai kafin ta gama sanin halin kowa
Duk suka sake kallon ta dan yanayin maganan kadai zaka gane me ajice
Nabil yace "ina my one.?
Zee tace "tana bacci.
Yace "ok ina su Fujna?
"yanzu YaHanif yafita dasu zai zaikai su gidan (zoo).
"to breakfas  fa?
Zee tace "YaShid saide na rana ai
Yana dining
"ok asamo min ruwan tea kuma akai part dina ajera ak'asa.
To suka ce tare da mekewa

"mata yunwa ko yasa hannun sa acikinta yana shafawa
Itade bata ce komaiba
Ahaka suka zo suka samesu
Su kace YaShid mugama
Hannun fandau yakama suka shiga part nasa
Gana ce ta tashi tayi tsalle tace" woww ya Allah ka bani irin wanan mijin da zamuyi wannan rayuwan.
Zahara tace "Wllh nima Ameen kai.
Zee tace "amma fa daganin yar girman kaice har dawani kuna lafiya.
 ta fad'a tana kwaikwayo muryar Fandau
Jidda tace "wllh baki iya muryar ta ba.
Yasmin ko tashi tayi take kwada tafiyan Fandau ita masuka ce wllh baki iya ba Ashuwa tace bari kuga haka take itama ihu su ka mata wllh baki iya ba Falmata tace "ai wllh sai na shiga jikinta ta koyamin irin wanan tafiyan da maganan.
 Zee tace caf ni wllh bata isaba wannan eya yarinyar  wllh dagani bata kai Hamida dasu Salma kannen muba.
Gana tace wllh ni kam sai nagoya haka kurum yarinya tunjiya ta dannan miji ad'aki sai yanzu yanzu ma yinwan cikin sune yafitar dasu dan kitchen din part din bakobai aciki.
Falmata tace "tun d'azu nake son tafiya Iya tana kirana amma dan naga wacce isheshiyar ce shiya sana zauna.
Jidda tace "Allah sarki Aunty Hadim

Suna shiga jikin sa narawa ya had'a tea me kauri yabata yabata tana kafa kai ta shanye nan tanan saiga kumi ya karyo mata
Daga nan shima yasha haka yajata jikin sa tawani narke sai shakwaba take zuba masa ahaka yayi ta dura mata abincin knocking akayi yabada izinin shigowa Fandau zata sauka amma yareke ta Gana ce tace "YaShid da  akwai bak'o fa.
Yace wai tun wanda my one ta fad'a.?
"Eh shine yana parlour bak'i.

Bayan sun gama ci ya kamo ta yace "muje muga bak'on ko.
Haka suka sake ratsa su Jidda suka wuce
Suko suka daura da Gulman

Zaune suka sameshi akan kugera da jarida ahannun sa sunayin sallama ya dago tare da Mekewa ya mekawa Nabil hannun yana murmushi
Yace Fatima ko?

Yazauna "nasan baku sanni ba amma ansanar daku zuwana nine Dr Afwan Barumi Niger naso nazo tun su Baba suna k'asan amma ban samu dama ba sai jiya bayan ankawoki. da sauri Fandau ta meke kusa dashi taje Ayya Ya Afwan gashi ko kamarku da YaShatee murna tayi sosai suka gaisa sai
Yace "ai Mama sai da tayi tayi nayi hakuri zuwa gobe nazo nace sai nazo naga Shiddams da muke ganin sa a TV  wai yau shine mijin yar uwata tun awaya bro yagaya min amma nakasa yarda saida
Nazo wani yayan kine Barnoma ya kawoni yajima yace zaije yadawo.

Sunjima sosai suna fira har Barnoma yazo da zasu tafi Fandau tace "sai yaushe?
 yace " ai kafin nabar k'asan nan nadinga zuwa kenan dan acikin gidan nan a yaran matan da suka shigo dani nan nagani inaso.

Bayan fitan sa suna shirin shiga part dinsu wayan Nabil yayi ringing ya duba Girema ne yace "Grem ya akayi ne.?

"Yashid daya daga cikin turawan nane bashida lafiya yanzu haka muna hospital yace yana son ganin ka.

"nawani company ne.?
 " *FUJJIRAT* *GROUNDNUT OIL*.
"ok gani nan.
Kissing din Fandau yayi a goshi yace  "kishiga ciki zanje ganin marar lafiya kinji.

Shagwabe fuska tayi tace kuma sai yaushe baku gaisa da Aunty ba ya kamata ace kun gaisa.
"Mata karki damu kisame ta kice mata nafita kuma nima zan kirata Wllh wani ma aikacine bashida lafiya yana maganan yana d'aga hannun alaman driver yazo da sauri ya taso suma ascots din duk sukayi shiri ya juya ya sake mata kissing yace " inason ki my Mata.

"Nima haka Mijin Mata.
"ki shiga kinga gardawan nan suna kalle min ke ahaka.

''Kana kishi nawa kasa gardin yayi ta yawo dani har London ina gardine yakaini.

Girgiza kai yayi yace, "mata wllh kina da neman magana ai Sani amincece nane ko yanzu zan iya bashi amanan ki.
Fandau tace "yawwa waini ina yake ne.

"yananan gobe yace zai kawo miki ziyara shida matar sa.
Ya juya yayi inda motan yake aka bude masa ya shiga saida taga fitansu sanan ta shige ciki su Yasmin kuwa suna Gulma ta window ita tama Hadim daya ke tana sama tana kallon komai baya tayi tana adua meyake shirin faruwa dani YAALLAH dole araba gida inba shaka ba mutuwa zanyi.

Suko yan Gulman tashi sukayi suna gwada tafiya, ta sukayi hanyan parlour
 Itako saida suka ga zata shigo ko wacce ta daidaita tafiyan waisu adole sai sunkoyi tafiyanta
Wu cewa zatayi ta shige part dinta Yasmin tace "am Aunty Amarya na biyo ki zan tayaki fira.

Tace "ayya ba damuwa duk suma meke banda Jidda da Zee
Yasmin tace "Aunty kinga yan iskan nan zasu biyomu ko.
Fandau ta juyo tayi musu murmushi duk suka shige
Zee tace "aikin banza dan Allah dubesu kanwar bayar su

Sai dare sosai Nabil ya shigo alokacin kowa ya kwanta part din Hadim yayi dan yasha kira ba ta dauka yanzu ma yaje sai knorking yake bata bude ba tana jinsa  yayi part din Fandau umm bidirin na yau ma ba magana dan da safe sun magara sosai tariga shi tashi tan har ta gama makeup din ta sannan ya bude ido yana kanin ta yace "wai yarinya nan mekike so dani ne.?
Tace"danayi me? yace "zokiji abin da kika min.

Mekewa tayi cikin kwarewar tafiyar ta tana dososa tana jifan da tattausan murmushi ta shiko sai wani lumshi ido yakeyi saida tayi daf da gado saita canza hanya tayi parlor da gudu
Yace "niko
Ya tashi yayi toilet shima

Itako Fandau kitchen dinta tashiga amma tasamu komai sabone idan ta tsaya cewa dasu zatayi amfani zata b'atawa kanta lokaci
Dan haka tayi babban kitchen din dama ko parlor ba kowa dan yan Gulman tun dare su kace bata gobe suna da school
Tashiga tafara aikin cikin kwanciyar hankali
Hadim tana saukowa taji mosin ana saukowa a saman Fandau daga jin takun tasan na Nabil ne dan haka tayi kitchen da sairin ta saide yaganta kuma dama gunta zaije dan haka yabita
Tana shiga shima ya shiga jawota yayi   jikin saya sauke ajiyar zuciya yace "haskena nayi missing naki sosai Allah rayuwan Nabil a hade yake da nake  bana gane hakan sai najima ban ganki ba Wllh jiya dakyar nasa mu bacci.

Hadim d'aga idon ta tayi ta kalle shi ido cikin ido tace ban ga alamun rashin nusuwa a gare kaba kaida ka manta dani...
"haba my one ahe zan manta da kaina kece farin cikina farar macce lantar kin gida kinfi 1000 kyu nede awajena bani da tamkarki shiya sa naki ranki my one macce me idon zinariya dole kyuwun ki asashi alayi.
"Nabil kasani wasiwasi Wllh kwana 2 kanuna halin ko inkula a gareni kasamu yarinya.

,"haba wacce yarinya ce zata sa na manta da sarauni yar mata kefa duk a family dani kike kama kinga soyayyamu daga Allah ne bawata yarinyar da ta isa na manta ki saboda ke kyakkyawan ce kuma kowa yana son abu mekyu har wannan yarinyar me ta isa tamin zaki damu kanki akanta kinsan yanda na matsu kuwa kwana 2 nan shiyasa nace ban yarda da satin da kikace kin bamuba dan garin naji d'adi ai shine gari yau zan dawo gareki mezaki tana damin dan natara.......
Fandau da take sugunne ta meke dan tagaji dajin magan ganun nasu yana rungume ta ita  ta cikin mirror sukayi ido 4 da ita bai san sanda yasaki Hadim ba tayi luuuu.....

*to masoya da fatan zaku cigaba dayi min uzuri afuwa insha Allah mun kusa*

*BJATTKO*
[3/13, 10:12 PM] Hauwa: [3/13, 2:37 PM] BATUL ADAM JATTKO: *DAMATA TA*

           
                    *NA*
*BATUL ADAM JATTKO*


🌈kainuwa writers Asso🤝🏻
*49*
Cikin zafi yatarota yace"mehaka my one.
Tace"kai zan tambaya sai jinayi ka sakeni kawai.
Hadim bata san da
Fandau na awajen ba saida Fandau din tazo daidai dasu tace, "Aunty antashi lafiya.?
Da sauri Hadim ta juyo dama tunshigan ta taji kamshi turaren Fandau
Tace"lafiya ummul kaam.
Daga nan Fandau ta wuce.

Bayan tafita Hadim tace "kai dama tanan nan kake da wanan magan ganun.?
"Eh tananan?
Tace "amma Wllh banji dadi ba.
Yace"mena rashin jin dadi menayi?
"haba Modu  kafa fadi kalamai wanda tamkar na kushene akanta tabbas koni akayin wa bazan ji dadi ba.

"Mena fad'a  kawai dan nace inason ki shine namata lefi.
Murmushi tayi tace "Ummm Mamman kenan ka mayar ni k'aramar yarinya ne najima da gane kana mutukar son yarinyar nan ban sake gaskan kaba sai a wanan kwanan 2 nata Nabil yaushe rabon ka dani tunjiya da nasame ka a godon ta acikin wani yanayi tare da sakin baki kana fadin kalamai na so agare ta kasan ka b'a tamin rai amma baka nemeni ba kafice sai dare da  ka shigo kabuga kofa kaji shiru juyawa kayi ban ganka fa baka kirani ko awaya ba sai yanzu duba time  12 katab'a kaiwa irin wanan lokacin ad'aki sai a duty wanda ka kira da yarinya ba abinda zata iya maka,
Jan hannun sa tayi suka zauna akan kujera  tace inason ka gane cewa nasan Fandau ba yarinya bace ai ta tashi a sawun yarinta tun adaren da kara bata da budurcinta nasan kai kanka kaji kunyar gayamata haka shine da kagan ka tsorata ko zaka kadani
ka gama moran ta har kana cewa ta bar inka bade ido ka ganta baza ka kyaleta ba yanzu kazo kana kushe ta baka so zaman lafiya ba matar da yara 4 suka fito ajikin, kakira ba abinda zata ma
Ni yanzu abinda nafiso dakai kar kabar ni cikin kunci nima nasa mu kulawan ka kuma bana son idan muna tare kana kawomin maganan Fandau dan inada rauni akai, yanzu de kaje ka lallashi ta ko wllh kayi missing
books dinta da Heep's.
Duk jikinsa amace ya akayi ma yayi hakane shi dawane idon zai Kalli Fandau shafa kumatun tashi Hadim tayi kamar tasan abin da yake tunani tace "kar ka damu kaje ka bata hakuri nasan kai jarumine saide ka zama na miji kar ka fadi kalamai na kushe akaina kamar yanda nima bana son gaba ka k'ara kawo min abin da ya shafi kushi agareta yin hakan zai janyo girman kai a tsakanin mu ko wacce kanuna mata   so kamar ba wata a gaban ka idan kana tare da ita.

"na gode da shawaran ki my one wllh ki yarda da gaske ke ta daman ce wllh inason ki fisabidillashi musamman yanzu da kike son zaman lafiya na kike son yarana wanda nasan sonda kike min ne yasa kike sonsu bazan boye miki nasha gaya miki ita ma Fandau inason ta amma namiki alkawari ba zan k'ara wani kalman kushi akan dayan ku ba nima nafison haka idan muka kasance dake kidauka ke dayace  kawai dani.

Hadim tace "saide inada shawara yanzu yaushe ne tafiyar mu.?
"Da jibi nace dan wllh an matsamin sosai  sai Baba yace zamuje Damasak ziyara gobe harda ku suga Fandau  dan basu san zancen ba.

Hadim tace "shikenan yanzu suma za aje ace musu yarannan bani na haife suba ko.?
Nabil yace "zasu sani dan tafiyar da Inna danja za aje.
Shiru Hadim tayi ita arayuwan ta bata son taji ance yaran nan ba ita ta haife su ba saide yazatayi d'an wani baya amsa sunan wani suma kansu yaran watara sai sunsani gawani mutuwar sonda take musu yanzu har Akkaram tarike bata son Nabil yayi maganan sama dan karya ce zai maidawa Fandau tunda yanzu kusan sati bai sha nono ba ai anyaye shi kawai wata 7 amma har yafara takawa
Katse mata tunanin yayi da cewa "me shawaran naki.?
tace "akan tsaren zaman da zamuyi ne ni aganina bai kamata ace muntafi duk ba yaka mata atafi da dayar mu tayi wata 6 sannan idan aka dawo akoma da daya yafi dan kishin dawani zanman rashi jituwa ko Wacce za ta dinga jinta kamar ita daya ce nakega hakan yafi ai.
Shiru yayi yana tunanin bazai iya barin Fandau ya jeyayi har wata 6 ba amma afile yace "kema kinsan hakan bazai yuwuba dan ina komawa zan sa su Fuj school tunda suna da baki kinga bazai yuwu adinga yawo dasu ba.
Hadim tace"sai su zauna awajin ta nima idan inacan suna wajena kaga hakan ba wani *dama* aka bata na kula da yaran ta ita ma nima kaga idan ina can zan hada harda Akkam da wanda zamu samu gaba na rike hakan zaisa yaran mu su tashi kansu ahade.
Yace "wanan shawaran naki  yayi yanzu dawa za afara zuwa.?
Hadim tace da ita yadace kufara zuwa.

"yanzu my one kinyar da natafi na barki har tsawon wata 6?
"My star to yazan yi kaima kakira abin da yafaru damu da kaddara ne.
Shikan dadi yaji na zai fara zuwa da Fandau  afile kuma yadinga gayawa Hadim kalaman so anan kichen din ta hada musu break yace wai ina su Fujna wllh inaga su Ashuwa ne fuka fita dasu Akkam yana bacci bari na dauko sa.
 tafita shiku ma yace "haka kawai sun ma yarmin da yara gantalalu bari nakoma dasu jibi su samu nusuwa suma da sauri Hadim ta dawo tace Haba ai ba yanzu za a  ta fimin da yara ba zai zan tafi inyaso sai nabar su asasu a school din amma bayanzu ba.
"Shikenan my one ai yanda kikace shi za acigaba dayi Modun ki bai taba kaucewa shawaran kiba ai cikin shawaran ki nake."
 dariya tayi tare da ficewa shima yaci gaba da cin abincin sa yana tunanin ko me Fandau takeyi yanzu har Hadim tashigo da Akkam a hannun ta
Tameka masa yace "yaron nan fa dake yake kama k'auri sukaji suna waigawa sukaga girkin Fandau ne yakama da wuta Hadim ta kashe gas din
Tace "yakamata kuma ka koma wajen matar kafa.

Yace "ita me yahana tazo ta cigaba da abinda takeyi.
Haka de har Hadim tace zata je tayi wanka shima mekewa yayi muje nima kimin dan naga alama kwana 2 kin maidani maraya.
"a a rufamin asiri kaje ta maka duk da nasan da aiki agaban ka.

Yace "umm to shikenan de amma kiyi shirin tarbata yau fa.

"Aida naba ka 1week  ina son bata damar da mamu bata ba tana budurwa akkin tashi sai kayi kwanaki 7 a wajenta.

"To ai  kince tare zamu tafi  da ita kinga dole nazo muyi na bankwana.
'a a wllh nayafe.
"yace nagode wa ALLAH da yaza bamin ke amatsayin uwar gida me adalci.

Itade sun guman Akkrama tayi ta haye  a bin ta

Tana zaune tana shan tea ya shigo da wayan ahannun ta tana chatin da kawayen da yan uwanda dan yanzu Faridan Amjad ta zama babban amini yar ta
Cikin murmushi ya karasa inda take ya zauna yace "Mata dama ba bacci kika koma ba shine baki fito kinbani break ba sai my one ta tausaya ta bani Gaskiya my one tana da kirki wata da kwana da miji ita da ciyar mata.

"ai kaima kace my one  tuda take daya awajen ka kaga ita ya dace ta maka komai musamman wanda ka kwana da ita yarinya ce me ta isa tayi maka da zaka sa ran zata baka breakfast.
Shide yarasa mezaice mata sai binda tada kallo yake dan yanda take kurban tea yana son yagane yanda fuskan ta yake ciji damu wace ko rashin sa amma yakasa tan tancewa
"Inason yin wanka mata fita zanyi.
Tace "ok.
 "To kitashi kuje kimin wankan.

Da gowa tayi tana kallon sa tace "kabari sai na gurma yanzu ban isa yiwa babba kamar kaba  kaje lantar kin gida ta maka ai mekyu da mekyu ta dace.
Cikin shan kunu yace "idan na fashin ceki kina son gayamin magana ne saboda reni yana son shiga tsa kanimu ko.?

Tace"A a yi hakuri ba reni tsakanin mu zan kiyaye gaba afuwa.
Tsaki yayi ya shige yana cewa girmana kikaga zaki iyayin fin haka ma.
Fandau cikin ta kaice ta ke bin kofan da kallo wato wannan shine hakurin da akecewa tayi ko amma meyasa zai mata haka dan yana son matar shibai gamata yana kusheta gaban taba
Har yafito yagama komai da yasa kayan tana kallon ta gefen ido ko kallon inda take baiyi ba saida yakusa fita yajuyo yace "kishiyar gobe zamuje damasak ziyara.
yana gama cewa haka yafita ita ko tace wannan kaine nade taburman kuyar ai

Tana nan ajaune sai bayan la asar yan matan gidan suka shigo mata yanzu kam tana dan sakewa dasu dan tana cin dariyan su dan basu boye mata Gulman ta da sukayi ba sudin ga gwada tafiyan ta da maganan ta agaban ta tun tana dauka raini ne yanzu ta gane tsabagen sangar tane irin na yan hutu sakalcin su yana bata dariya gashi dama duk kannen sane abokan wasan tane
Gana tace wai Aunty kirki meyasa bakya son zama a man parlor ne mutafi mu mar Hajiya Aunty ita kad'ai a parlour suka tadda Hadim acikin yara suna ta bata surutu FUJJI ce tazo da gudu Oyoyo Aunty kirki  ta fada mata sai kuma Fandau ta kasa yi mata wasan take mata nada Fuj tace "baki d'agani ba bance miki nice FUJJI kiba.
"Sorry Fujin mum kinga yanzu kinyi nauyi bazan iya d'agaki ba saide kije mum ta dagaki.
Zun buro baki tayi
Tace "Aunty kirki bata da karfi ai su  uncle Grem da mum da Abulna suna d'agani.
Su Maaf ko ball sukeyi sai Akkaam a cintar Hadim ta na bashi abincin sa
Fandau tace "Hajiya Aunty Allah yanzu karfi da yaji kunyaye min d'a kun hana nagan shi.
"tayi dariya tace "aikan gwara da na yaye din da yanda kuke barin kanku da yinwa shima haka zaku barmin shi shiba da amarcin ba a masa shoron wunwa yaude nasa azuma muku kayan abinci a part din ko zaku safa dan karna je ansamo min wani baby a masa shoron yinwa.
Duk dariya sukayi tare da jijinawa Hadim Falmata tayi shewa tace "se hajiyarmu ana cikin haka Basheu yashigo dan gidan Zannah kusan sa an Fandau ne gaishe su yayi tareda dan k'ada key din hannun sa yanayiwa BilAL wasa
Hadim tace "gashi ban gane kama kuma nasan tunda masu gadi suka bar kashigo to sunga na gidane.
Kafin yayi magana Fandau tace "kaninane.
Cikin fara a Hadim tace "Ayyya wllh ban gane ba kinsan yaran Baban ne masha Allah bazan gane ba sai ahankali shiyasa yanzu zan juri zuwa gidan dan nasan yan uwana  zauna mana dan uwa.
Basheu ya zauna yana cewa wllh kuwa munada yawa.

Hadim tace "ai kunkai 30 amma ko.?
Basheu yace "wllh mu maza ma 26 ne sai mata 18 idan aka had'a kinga mu 44 daidai.
Hadim tace "Masha ALLAH toni ma yanzu nashiga ciki kaga munza ma 45 kenan.
Dariya yayi yace "hakane Aunty amma fa wanan da tace muku ni kanin tane to ni wanta ne itace yar raini amma su Hassana da su Hafsa yaya suke cemin.
Fandau tace "su Hafsa kace kaje ka tambaya duk nafiku. Hadim tace kinfishi tunda gaki da aure.

Basheu yace "saide tace hakan.
Hadim tace "ya sunan ka.? yace"  MUSTAPA amma ana kirana da Basheu.
Hadim tace "Ayyya dan uwa zanje fa ayi family meeting dani dariya sukayi
Basheu yace "nifa da bak'o nazo Yariman Niger yana waje.
Fandau tace YaAfwan meyasa bai shigo ba.
Yasmin tace wai wannan tsadedden guy najiya.?
Ashuwa tace"wllh shine. " Zahra tace "wai wannan mejin kan.
Kafin su sake magana har sun shiko sosai suka kaisa da Fandau da Hadim tace "amma kanin Shateema ne ko.?
"eh inji Fandau  ana Afwan yace "zamu wuce.
Fandau ta tashi rakashi saida suka fita yace "sister wllh batun yarinyar na da gaske nake naga baki dauki abin da serious ba.
Fandau tace "nagane Wacce  kake nufi Jidda ce amma naji suna cewa tana da saurayi Aliyu amma bari na bata magana kashiga parlour bak'i zan turota.
Afwan yace" *Hauwa Jidda*
Sunan yayi kice mata waccen Aliyu ba na Gaskiyan bane ga *Aliyu Harda*
[3/13, 4:22 PM] BATUL ADAM JATTKO: Gata na Gaskiya nan.
 Fandau tana shiga tace "Aunty waifa yayana yanace yana son kizama surukar sa gashi can parlour bak'i yana jiran Jidooo.
Gana tace"wai dan Allah da gaske.
Fandau tace "hakane  ai duk basu san sanda suka fadawa Jidda ba suna mata murna amma ta daure fuskan taki cewa komai kuma bata tashin ba Hadim tace kitashi kidan gyara kije mana.
Jidda tace ai aunty da gaske kike naje nayaudare Aliyu kenan Hadim tace "haba jida wannan fa saurayine Aliyu yana da mata kin ko san halin *Yana* matar sa Allah kullum muna miki  adua Allah yaza ba miki mafi alkairi gashiko Allah yakawo miki Dr Afwan  wanda a India zai ajiyeki ai daga nan suka mata cah har ta tashi ta tafi

Nabil sai dare yashigo suna zaune a parlour su Fuj suka masa Oyoyo zama yayi yana biyewa shimen yaran Yace My one mezan cine.?
Hadim tace "Ummul Akkaam ki saukowa da dan sarauta naki abin kinsan idan sarauta yamosa maya hawa dining.
Fandau dan kar Hadim ta gane wani abu tameke ta dauko su yasmin ko dama suna gaishe shi suka wuce d'aki
Saida ta zuba masa tajuyo ta kalli Hadim tace "Aunty ni zan shiga ciki.
Hadim tace " to aida can din kika kaimasa nima tashi zanyi yanzu
Fandau de kowaigowa batayi ba ta haye da tafiyan na daukan hankali Nabil ajiyan zuciya yayi afili
Hadim tace" yawwa my star naga alert fa shine nace muraba da yar uwata ko? Nabil yace " a a kibar kayan ita ma za a bude mata nata account din kuma za abiyata kudin kamar yanda ake biyanki
 millions 40 duk wata ita ma haka munyi da oga da na bude mata ma da anyi da ita.
"Allah my star shiyasa na keson Chelsea  suna sonka dayawa matan Amjad Fa dayan suke r'abawa.
"ai Ajd kikace nida shi wayafi bautawa club.
Hakade sukayi ta fira
Hadim tace to katayani da d'akan yaran mu shiga ko dan bacci nake ji nima
Yana  zaune tafito awanka dan shiyayi tana fitowa tace "wai dama baka tafi ba.
Yace "ina."
" tace wajen Mata mana.
Dariya yayi yace "to natafi.
Yafita ta kaita sallaman nashi yabata mamaki ga kuma kishi haka ta kwanda ko shafe shafen batayi ba

Da sallama yashiga amma da alama tana bacci  hawa yayi tare da rungume ta yace "mata kinji yanda nayi missing naki ne wuni daya kamar shikara.

Da saurin Fandau ta meke zaune dayake wutan akashi yake ta nuna kamar bata gane ba cikin yanayin tsoro tace "Subahanallashi waye.?

Yaja bedside lame yace "yace wakike tsammanin zai tsalleke duk security gidannan ya shigo miki har bedroom.?

Tace "saikai kaikuma banyi tsammanin kaba saboda ai garin naji dadi shine gari banyi tsammanin zakazo garin da ba abinda aka isa amaka ba.?

Dariya yayi yace "mata ki min afuwa nayi kuskure da bansan ta ina zan fara baki Hakuri ba nasan kinsan masayin ki awajena basai nayi zaman gaya miki ba saide kitake dan kibani wahala ki manta da komai hakan bazai sake faruwa ba kinji Mata nasan ke me Hakuri ce.

"kaji nace kamin lefine ai abinda yake cikin zuciyar ka kafa d'a hakan yamin nima ina shirin komawa gidan iyayena kuma zan koma idan na girma na samu abinda zan baka sai nazo.?
"Mata amma nace kiyi hakuri ai.
"bazan hakura ba.

"yanzu yakike son ayi.?
,"inaso katashi ka tafi inda kake jin d'adi.

Mekewa yayi yace "wannan me saukine amfanin mata 2 kenan wata idan ta kunta ta maka wata ta faranta maka.
Saida yaje bakin kofan fita tace "kasan kafison matar kani kuma kadage saina koma?
Yace "sosai ina son matata ko na taba cemiki bana sonta ne.?

"toni na hakura ka mayar ni gida  awai.

"Kina da k'afa ai koni na dauko ki ai gani nayi an kawoki.
"to shiyasa kake wulakan tani kenan.?
"kai sorry Mata kar my one tarufemin kofa gwara naje.
Yana gama fadan haka yafude kofan yafice abinsa

Kuka Fandau takeyi sosai tace da kafa nafa yace kena yana tufi mana tafi ai ko dasafe sai natafi
Wani zuciyar yace mata kin manta gidanku ba a yaji daganan taci kukan ta ta gaji tukun ta sauko tafara jera nafila dan kwana 2 nacin sa yasa bata samun yin nafila da yazame mata jiki kawai sai ta tsinci kanta da adua Allah ya sasanta tsaka ninta da mijinta
Shiko abude yatarar da da bedroom din Hadim sosai sukayi da Hadim kafin ta barshi dan ita ta kafe sai yaceka kwanakin da tayi alkawari shikuma yace bai dace ba tunda ita Fandau da ita za ayi tafiya
Yayi kokari sosai wajen nunawa Hadim tana ransa dan yanuna bata kauna zalla
Washe gari tun asuba Baban sa yakirashi yace "tafiyan safe zasuyi tunda yace bazasu kwana ba ya gayawa Hadim ta shirya yara dan ita duk gandan ko kichen bata shiga amma ita take kula da harkan yaranta bata yarda wani yamusu ba bata son ko t'abasu masu aiki suyi ko su Jidda ne suka musu wanka sai tace kaza bayi bata sake musu Nabil yagama shiryawa tace "kagayawa Ummul Kaam ta shiya dawuri kuwa.?

Yajuyo ya kalleta yace "ina naganta kije ke kigaya mata.?
Hadim tace "baza kaje kugaisa ba.
"idan tafito ma zaisa kawai.
Azaune akan sallaya tana karatun Qu ani Hadim ta samu Fandau tazauna Fandau ta kai aya tarufe Qua nin tana murmushi tace "Hajiya Aunty antashi lfy.
Hadim tace "Eh kefa

 "lafiya lau.
"Masha ALLAH.
"ki gama shiryawa yanzu zamu tafi.
"ina zamu Aunty.
"Zamuje Damasak garin su megida.

Agidan su Nabil aka hadu inna matazo ba abinda kake gani sai jeren motoci haka suka shiga garin Nabil yana da taren masoya wanda idan yaje ko da yan uwa baya samun ganawa saide yan uwa idan yana meduguri suzo   su Hadim anbi dangi Inna duk inda akaje saita bada labarin abinda yafaru itako Hadim harda kukan aboye bayan sunzo duk agidan Inna suka sauka saicen dare suka watse kowa yayi gidan sa yau Nabil ko mukwanan lafiyan baije yayiwa Fandau dinba ita ma Hadim agajiye take bata masa zancen ma dagari yawaye jirgin safe zasubi  Hadim ta gama yiwa Nabil shiri sa tace "my star yanaji shiru Fandau bata fitoba gashi lokaci yakusa yana daure igiyar takalmin sa yace ki dubota mana.
Hadim tace "kai baza kajeba nifa na fashinci jiya ma har muka tafi banga kunyi magana ba bayan mun dawo haka meyake faruwa kaman bakwa jituwa.

"tabe baki yayi yace "nide ban ma kulata ba balle na mata nefi.

"bangane baka kulata ba inko hakane da lefin kenan Mamman katuna kayiwa Zannah alkawarin gina adalci a tsakanin mu.

"kigaya min mena mata na rashi adalci shikaran jiya naje na mata saida safe jiya da tafito lokacin tafiyan mu meyaka mata tamin data ganni tun ba d'aki daya muka tashi ba amma kinga ba ta gaidani ba to yazan mata ko ke haka kikemin kikoya mata yanda ake tattalin miji.

"To zan bincika dan nide nasan kanwata me biyayya ce inaga kamata wani lefinne kuma idan na bincika naga da lefin ka nima zan shiga yajin aiki.
Tana gama fad'a tafice awance tasamu Fandau

,"ai baki shirya ba kina kwance.?
Cikin turo baki Fandau tace Aunty yau ma wani wajen za asake fita.?
"Hadim tace "kina tufin bakinsan yaune tafiyan kuba.
"Aunty wane tafiyan kuma.?

"London zaku tafi.
Gaban Fandau ne yafadi wani irin zama zamuyi da wadannan bayin ALLAH  yanzu tafiya har wani k'asan bani da matsayin da zaigaya min saide matar sa tazo ta gayamin kuma sai asanda za ayi tafiya shiyasa jiya muka dinga bin yan uwan sa ashi sallama yakeyi nikuma da nakeda yan uwan birjik tunda nazo inda banda gidan YaMuna ba inda naje.
Hadim tace "kinyi shiru time yatafi fa me dame zaki dauka na tayaki shiri.
"wai Aunty to yanzu banyi sallama da kowa ba kuma su YaZaha baza suji dadi ba wllh nide anya za ayi tafiyan nan dani kuwa.
Hadim ta zauna abakin gadon ta dafa Fandau tace" Sister to yaza ayi tafiyan ne ya matso ki musu waya kibasu hakuri nima duk zan bi gidajen su amadin  ki in basu hakuri.
Fandau fadawa jikin Hadim yayi tace Aunty bansan mezan cemiki ba yanda kika dauki dangina ashe wai Basheu da Abor mota kika siya musu wllh bakiji godiyar da jiya sukeyi ba Aunty ki nada baiwar kirki wanda ba kowace macce ALLAH yabawa ba.
"yanzu Fandau dan
nayiwa yaran Baba Zannah abu har sai anamin godiya wllh baku daukeni yanda  na dauke kuba sam.
"Aunty kirkinki kawai na fad'a Allah de yabarmu tare.
"Ameen  nacewa Basheu din yamin les na sauran Wanda basu da mota ya turomin .
Fandau kam rasa bakin magana tayi

 sai Hadim din dince ta tashi shiya mata kayan bata musa mata ba dan wani kiman ta take gani  Hadim acikin whadrrop din Fandau taci karo wasu magun guna  wanda da gani tasan na matane  Tajiyo ta kalli Fandau tace kai yar uwa haka kike harka kin bar yayar taki a kasa nima ki daurani network bana ta kwasa ta zubawa jakan da take shiya kayan Fandau
Fandau sun kuyar da kanta tayi cikin kunya Hadim ta zo kusa da ita ta zauna tace "yar uwa da gaske nake dan Allah Mama ce ha hada miki wannan kayan wllh ina bukatan su danni bani koda kawaye anan narenasu sai turawa maganin bature yana k'a idodi kashinan yajanyo min matsala shine nake son yin amfani da namu na nan.
Fandau ta sauke ajiyar zuciya tace "wasu Mama ce ta had'amin wasu kuma YaMuna ce kisamesu.
"ok zan samesu amma sai kun kusa zuwa."
"ah Aunty ba dake zamu tafi ba.
"Eh nafison nabaku *DAMAR* ku kud'an ci amarci daga ke sai shi zaku tafi ko Akkam ba dashi za ajeba dan Gaskiya na shiga hakkin ki daga farkon auren ku shiyasa nace inason yanzu na gyara kurena.
Nabil ya shigo yace My one ya akayi kinsan time yayi kika zauna haka Hadim ta kama hannun Fandau ko wanka batayi basu ka tafita a airport  Hadim ta rungumo Nabil shima yaji tausayinta yana goge mata hawaye yace "My one kawai mutafi abin mu Hadim sakin sa tayi ta karbi Akkaam ahannun Fandau tarike hannun  Maaf da BilAL tasa su ta sake jan Fuj ta shige mota ta bawa drive umarnin yaja suka Bar wajen ita ko har akusa rufe jirgi Fandau bata da niyar shiga shiko ma dan girman kan yakasa mata magana yana so saita shiga ya shiga kawai sai yazo yakama hannun ta Ascort din shi suka dauki ja kansu suka shige dama shi ajirgi wajen zaman sa na musamman ne har nan yajata ya kuma kulle wayen ya dauki glass ya maka a fuska  yaja laptop dinshi ya kunna bai sake ko kallon inda ta keba  har 12 narana a gogon 9ja yanuna bai kulata ba bai bude wajen ba balle ma aikatan su zo suyin maganan abinci ko bacci ta kasa saboda yunwa  can taga yazuge jaka ya dauko takeaway yabude wani kamshin taji tasan dambun kazane ya sake sa hannun ya dauko wani karamin flask tare da ciro cup yazuba coffee yana ci yana kurban coffee bai ko kalle inda takeba yace "idan zaki ci kici mana kinwani zubamin ido sai kinsa na kwaru.
Abin ya bata mamaki me yake nufi shifa yamata lefi kuma yafita daukan zafi ita ma hankalin ta ta maida kan wayan ta  wayan sane yayi kara ya dauka tanajin muryar ta gane Mama ce tace "Nabil haka kuma zamuyi da kai ashi dama matar kake nema kwana 2 ko awaya.
"haba Hajiya Mama yaza kimin wanan fassara wllh ban samu zama bane shekaran jiya wani ma aika cinmu ne bashi da lafiya sai da naga yatashi k'asan su nasamu nusuwa jiya kuma mukaje Damasak kinga yanzu ma muna cikin jirgi zamu koma.
"zaku koma shine bako sallama da an kawo min ko Dauda da Hajara ai.
"Mama ai su suna gida dan bada My one muka zama ba nida Ummul kaam ne.
"Ayya yanzu ina ita Fandau din.?
Yajuya yakalli Fandau shi take kallo amma sai yace "Mama tana bacci ne.
"to ALLAH ya sauke ku lafiya.
Fandau ba karamin haushi taji ba ga idan awayan tane ko takira ba zai shiga ba tunda suna sama dan nashin ma international ni yasa kuma dasafe ma bata da kudi awaya dan ita tunda taje da dan kudin da Habiba ta sa mata take amfani a wayan da ya k'are ko bata da ko asi
 Har kusan 3 na yamma yanwa yana cinta shiko  yayi bacci yasa tayi sanda ta dauki guntun naman daya bari ta fara ci ita da take son tadan taba yanda bazai gane ba amma sai jinta tayi yace "kuma sai Kinga makerin *kwanon*
[3/13, 5:57 PM] BATUL ADAM JATTKO: Itade dan kunya tarasa mezata ce shikuma ya mayar da kansa ya rufe idon sa
Basu jitun ba har suka zauka sai yau Fandau ta ga matsayin Nabil a London yanda akazo taran sa

Angama shirya musu komai na abinci ita ko dama yinwa take ji gardawan duna fita ta na hawa kan dining shikuma ya haye sama da taga ma tashiga d'akinta nada tashiga bata gansa ciki ba tayi wanka tashiga rama sallolinta tana idarwa ko adua ba ta tsaya yiba ta bi lafiyan godo dan ita amma abin mamaki bata ga Nabil ba har wahegari saida daji yunwa ta shiga kichen dinta akwai komai saide ta jin bakinta take bata sha awan komai sai kawai ta daura ruwan tea tayi hadin kauri  tasha tashiga  taci wani uban makeup ga ta tsuke cikin kananan kaya tafito man parlor tana tafiyan ta na daukan hankali a falon ko tasamu Nabil yana waya "haba my one kema kinsan duk inda bake dushune haskena idan ankawo yaran ki kirani zamuyi video call dasu tana lafiya a a kikira awayan ta mana.
Hadim tace " ai bata  kirani ba bani da no. nata tasa sim  ne.?
Yace"ban sani ba.
"to dan Allah kabata wayan zamuyi magana.

"yace girman kine My one yi miki abinda kika so kinci sa ako gata nan.

Me kawa Fandau wayan yayi ranta ab'ace ba abin da take tunawa sai _My one inda bake duhune_
 Ahaka har ta k'arasa ta karbi wayan
 tace "Allah ya demaki Auntyna yakike ya yaran.?
"lafiya sister kun sauka nafiya.?
"Eh Aunty.
"ya baki nemeni ba na tambayi  My star   baki sa sim bane yace bai sani ba nace bangane bai sani ba yace na tambaye ki yanzu zaman da na fuskan kunayi kuka cigaba dayiko.
Fandau shiru dayi danme zata moyewa Hadim ai bayan ita Hadim har matsalan da tasamu ta gaya mata komai ai gwara ita ma tadauki Hadim ayanda ta dauketa kawai sai tace "Aunty toni yazan masa shine fa yadena min magana.?
"kin masa wani lefine.?

"nide bansani ba.
"to kinsan abinda nakeso dake ki samesa ki tambaye sa idan da lefin da kika masa kibashi hakuri  Nabil yana da saukin kai amma gawan da baisan halin saba bazai gane ba kuma duk girman lefi idan kika bashi hakuri yana da saurin yafiya kuma kinga ni zaman mu dashi mutane suna ga kaman na mallake shi magana ta kawai yake amfani dashi to wllh kawai sanin halin sane kinga idan yamin lefi koda zan shikara ina fushi wllh banza zaiyi dani saima yafini dauka zafi saide ni na koma nabashi hakuri kije kibashi hakuri zan sake gaya miki sauran halayin nasa idan ki kasa sim bari naji ta Akkaam yayi kashi.
Fandau tace, "to Aunty na gode.
Tana sauke wayan ta je inda yake ta sugunna tace" YaShid antashi lfy.
Saida yawani sha mur yace"bakiga alama ba ko kinga a lamun rashi lafiya ne.

Tace, "Allah kaifa kanin lefi amma....
,"saurara malama da namiki lefin ban baki Hakuri ba kike neman gayamin magana tambayi My one na tab'a bata hakuri akan namata wani lefi har zakice inje sai kin girma nadawo da ga karshe ma kikace na maidaki gigan ku   dan kinga na damu dake ko.
,tace"to kayi hakuri kaji.

"shine kika ebo makeup kika za gani maye ko kije sai kin girma saiki zo ki ban hakuri.
Idon ta ya cicciko da kwallah ta dan lonkwabo da kanta tace "to ga wayan. Zai karbi wayan tattausan fatan hannunta yagogu da nasa ai bai san sanda ya fusgota jikin saba
Ya sauke wani wawan ajiyan zuciya a file yace "YAALLAH idan ka dauke yarinyar nan arayuwata bansan yazanyi ba  rayuwata saida sa hannunki *mata*.
dukan kirjin sa tafara Allah ban yarda ba kaida kace nayi yarinta ba abin da zan baka.
,"bariki ga abubuwan da zaki mani mata kafin tayi magana ya hade bakin su ya sungume ta yayi sama saboda wannan parlour general ne masu aiki suna iya shigowa
Washigari yace" zamu fita fa dan na siya miki sim card da sauran  abubuwan da kike bukata tana kwance  a cinyar sa tace "suna sayar da garin kunan tsamiya kuma du a kayan fruit din da ake kawowa ba kwaiba  da sauri ya dagata  yace "da kaske kike AISHA tazo kena kawai sai ya d'agata sama ya fara juyi da ita saida ta gaji tace "dan Allah ka saukeni
Wacece  kuma AISHA.
"yace mesunan Mama mana ai nasan nemam kunun tsamiya awajen ki da albarka yake zuwa My one zata sha albishir. ya dauki wayan sa da sauri ta warce tace "ya daga cewa ga abinda nake so sai ka fassara ni da wani abu dududu yau shi nayi wanda kwana 1 dayin wanka na taro sai kace wata akuya.
Yace nide Bani waya na nagayawa My one  tashi tayi da gudau dawayan da zasu fita siyayya rin kayan da yasa shi yakawo mata tasa yanda suke shiga da Hadim
Fandau ta kalli kayan ta tabe baki tace "bazanyi wanan shigan ba.
Yace "dan me kinsan kudin da na kashi akansu guda 100 nasa aka bugo fa.
Tace"saboda kauyan cine kuma kowa da nasa salon.
"kede awai kice bazaki yi shigan Hadim ba sabo da kishi.
"Eh kace hakan ma lefine dan nayi kishin abinda nake so ai naga wani ba akan kishi idon sa rufewa yake yaka ma dukan yarinya har gaban uwarta.
"Shikenan mata duk abinda zakice yau bazanyi fad'a ba dan ranan farin ciki ne agida ana  birthday din Fuj  anan kin bani wani cikon na 5 cikin shikaru 4 kinban farin ciki ai ni yanzu ko kwai kika cewa da gashi ajiki saide nace yalas.
Liffaya tayi ya mata kyu ahaka suka fita yasha yawo da ita   sun jidi kaya wane lefin wata tana zuwa kida ta sa sim Habiba ta bara kira tana dauka tace my auny habiba tace" bawani sai yanzu kika ga daman kira bayan kuntafi ko sallama.
"kiyi hakuri Aunty kuna raina wllh kafin mudawo bani da kudine awaya da muka zo kuma sai yanzu nasa sim daga nan de suka gaisa harda su Nol ta kashi ta kira Mama itama sun sha fira ta kiya Bagana da sauran yan uwan ta Hadim  da Farida dade sauran mutane na suke cewa ta kirasu  washe gari Nabil suna da wasa kuma anshirya dashi anan club suka hadu da su Farida da sauran su Nabil ya gaba tar da Fandau koda zai shiga Drssing room da ita yashiga bayan bawan da yata ba shiga da matar sa dokane da d'akuna ne ajeri kowa da no nasa d'aki me number 12 suka shiga komai na ball awai duk no 12 takalma da riguna gassunan daya wa alankayi "isauri kisamin kinga mun kusa makara haka ta sa masa kayan wajen daure kalmine ta kasa ya daure kayan sa yana mata dariya tanacewa "wannan ta kallmin amma na karfeni kafin yabata amsa an farayi masa knocking ya nagani time saura kad'a a hura wasa ya tashi da sauri ya kama hannunta haka ya kaita ma zaunin ta sannan yace "mata addua tana masa da saurin ya fad'a file sunga gama duk wani shirin su aka fara wasa ita Fandau bata dauki wani ball abin kallo bane kawai ita matan da suka nutsu suka mayar hankali kan kallon ita kuma take bi da kallo su Farida ko kifta ido ba ayi ji anyi wani uban ihu duk wajen yarude cikin tsoro ta waiga jin ana ambatan Shiddams  sai kawai taga anyi sama dashi ana cillashi itama jitayi ana rungume ta tako ita matan turawa dasu Zahra  can aka sake mayar da hankali kanwasa ba ajima ba aka sake shima shiddams din ne yayi nasara da aka sake kuma abokan hamai yane suka samu daganan aka fito hutu shiddams yana haki sai faman zuba masa ruwa ake har ogan wayen Shiddams din yayi anawani shafashi ya same yana taku cikin sauri ya karaso inda Fandau take yakama hannun ta sukayi wani d'aki d'akin ya kayatu sasai zubewa yayi a kan gadon yana maida nunfashi saida ta tausaya masa d'aga kanshi tayi ta daura acinyar ta tace "wai haka kake shan wahala dan me baza ka bari ba ko magana bai mata ba yafara dannan Kafansa dan namasa kafan tashiga yi can akayi knocking a falo yace taji ta bada izini ashigo abinci ne kala kala aka shiko dashi Fandau ta dauko tashigo masa dashi dak'er yata shi ya fara ci yaci sosai sanan ya dauki wasu magun guna yakora sanan ya tashi ya hau wani injin ya fara wana shi ba ajima ba ya sauko garau dashi yana mata dariya yace "mata kar ki damu muje time yakusa awannan ma su suka samu nasaran daya  aka tashi 3 1
Fandau taga alert na kudi dayawa har million 40 a storace tanunawa Nabil yana yani yace kudin kine ita ma Hadim nata yaje mata amma kowane wata haka zaki cigaba da gani.
Tace "menayi za abani wanan uban kudin.?
Yace "gumin mijin kine mata kinga ko ai kema gumin kine.
Tace "to yanzu mezanyi da wanan kudin.
"ke kika sani itade My one duk aikin alkairi takeyi dashi ke kuma bakida yan uwan da zaki musu alkairi.
Tace "akwai duk su Hafsa sai na tsiya musu motoci dan naga yanzu shisu ke gasa.
Nabil yayi dariya yace "ai wannan Hadim ta regaki duk ta tsiya musu saide ki duba wani abin alkarin kimusu.

Fandau tayi kawaye Habiba ma tazo har lokacin komawar su gida yayi lokacin Cikin Fandau watan sa 6 daidai
Hadim sai murnan zuwan me gida ake YaMuna takira yar sudan ta gyarata sai Mama itama ta mata ita kanta tana jin canji ajikinta
Da sukazo Nigeria Fandau ta zaga dangi yan uwanta ji suke kamar su maida ta ciki har Niger taje anyi bikin Jidda da Afwan sunta fi India su yasmin duk anyi auren su
Da suka zo tafiya Fandau da Nabil basu ji dadin rabuwan suba
Dasu kaje can ma haka kullum suna nane da waya abin har yadan fara damun Hadim amma ta danne dan musamman ta ta tuno Fandau tana da ciki watan su 1 yatsiri tafiya Nigeria acikin watan saida yayi sati 2 yazo  daya dawo da  wata 1 yasake siran tafiya saida yasake cin sati 2 yadawo har de Fandau ta haifu dan ta namiji Zannah yamasa huduba da Haruna SHEHUN Barno suna kiransa Emir ita da yan uwan ta sun sha shagali suna sosai da gaiya Nabil yaki yazo saida Fandau tayi kwana 4 suka zo lokacin watannin Hadim yakusan cika dan saura wata 1 kuma yayi hutun wata 1 dan haka daya tashi tafiya  Da Fandau aka tafi amma da yaran Akkam kawai aka bare su dan ansasu school ne awanan zuwan Nabil shiru kake ji yanayin de waya da Hadim ya nagaya bata galamai na kwantar da zuciya idan yafara Fandau take kai auran mijin wata ko matsala
Amma da Fandau ta gama nata takoma na Hadim ya shigo sai aka sake komawa gidan jiya mama sosai ta masa fad'a tace meyasa ida Halima ce baka zuwa kana son kasa han kalin mutane yakoma gidan ka ko ka kawo rashin jutuwa atsakanin matan ka ko ta fada sosai yace "zai kiyayi
Amma yana koma ya kasa hakura yace zai tawo
Ranan da zaizo Nigeria Hadim da yara sun rako shi airport sunkusa tashi Hadim tace "Mamman ina so idan kaje katawo da ita muzauna tare nakega kaman yafi ba kamin adalci arayuwa ba nason sai Duniya ta gane haka ka dawo da ita idan ba haka ba bazan kara zuwa k'asan ba.

"My one yanzu kece zakice ban miki adalci ba kinsan de wannan tafiyan nace miki bata da lafiya ne amma idan maki abince ba shikenan zan iya bari. Hadim ta kama hannun yaranta ta tura su mota tajuyo tace masa nace" kazo ta ita kawai  ta fad'a mota ta ha abinta

*to masoya insha Allah pg gaba na ban kwana da Dama ta ne*
```MASOYA INA  NEMAN ADUAN KU DAN ALLAH AKAN JINYAR YAKE DAMUNA```
[3/16, 4:49 PM] Hauwa: *DAMA TA*



                 *NA*

*BATUL ADAM JATTKO*

*godiya agareku masoyan wanan labarin da yau nakawo karshe sa nagode da SOYYAYAR ku gareni*
JATTKO GROUP
DAMA TA 1.... 4
KAINUWA FANF
MASOYAN FANDAU  GROUP
HUGUMA GROUP
 ZAUREN BENAXIR  TABITAL PULAAKU
AISHA GARKUWA
LADIES VISION
MRS OMAR GROUP WANI SANADI GROUP

*Da sauran group din dama ban fad'a ba ina godiya da SOYYAYAR ku da kuma yabawar ku*

Inakuke UKTEE'S
Ga B JETTKON
ta dawo me kuka tanada min
Kowa yabar gida gida yabar shi
Gimbiya Nana kanan
Aunty zeenmu
Sameera kawas 👍🏼
Zahra Musa gambo
Mmn Abeeee
Mmn Amata Maryam pharmacy
Yaganan kolomi
Hjja Bintunmu
Aunty Yabah
Mmn Heesham
Yar autan UKTEES
Fatima A JETTKO


  *Nunccy* tawa amana🤝🏻

Godiya ta musamman gareki Aunty sis

Kainuwa writers
Wannan shafin nakune bani da space dinda zan irgoku daya bayan daya muna nare

*50*

Kafin yayi wani yunkuri har taja da sauri murmushi yayi  a fili yace "My one kinkawo shawa had'akun shine yafi sauki dama ban san mezan ceba  musamman Maman Fandau da tafi kowa samin ido sai nace naza daukan tane kawai zata ga Dr shikenan.

Fandau tana zaune abin Duniya ya isheta yawan zuwan Nabil yana damunta  har kunyan Hadim take gashi bai gaya mata dawuri ba da saide ya samu batanan ta kaiwa Bagana ziyara Niger dan duk nacin Shateema sai da sarki ya janyeshi dan yace dole shine maga jinsa

Koda taji ya sauka drive da security sa suna rawan jikin zuwa taran sa bata shirya binsu ba tsawa ma ta dakawa wani drive da yanace da Madam bada ke za ajeba

Da han zarin sa yashigo "mata mata  yana Kwala mata kira turus yayi ganin ta kwance akan kujera da saurin ya karasa inda take ya dagota bude idon tayi tana masa murmushi ba wai dan ta ji dadin zuwan sa bane sanin halin fushisa yasa bata nuna masa bata so zuwan nasa ba

"mata wllh na tsora ta nadauka jikin naki ne"

"a a na warke kona ce dama lafiya kalau abin da yasa shekaran  jiyan nace maka kaina yana ciwo dan ka kashe wayan ne fa waya cikin dare Gaskiya muna shiga hakkin baiwar Allah  shine har zaka iba kazo da made me neman kukane kawai amma ciwon  bai kai azo dubiya har daga k'asan England ba Wllh.

"ikon Allah mata nayi lefi dan nanuna kulawa ta agareki ba wai ina son nuna ban ban a tsakanin ku bane ke da ita duk dayane kamar yanda na saba gaya miki ina yawan zuwa inda kikene dan nasan ke Akullum kina bukatan temako na yanzu fa Emir wanan sa 7 amma gaki da wani cikin shi yasa bawai rashin adalci bane dan idan tan kade za ayi ayi rereya wllh My one tafiki sona yanzu da ita nasowa baza ta min Wannan tarban wulakancin ba.

"wulakanci kuma.

"Eh mana tunda
 bakiyi murna da zuwana ba.

"nayi murna mana saide bana son na kasance me son kai ne.

 "yanzu kam komai ya kare dan tare zamu tafi anrushe maganan wani a dafi da wata abar wata.

Fad'a masa Fandau tayi tana jin dadi Allah Habibi hakan yafi wllh ina rashin ka sosai nafi san ka kusa dani yanzu yau shene tafiyan.?

"cikin satin nanne dan ba hutu aka ban ba bamu da wasane kawai.

Fandau da taje sallama gida ta cewa Nabil ya tafi ita zata zaga dangi shima yana da zuwa gaisuwa Damasak dan haka yatafi
 Fandau tasamu BaAlta tace ta mata iso wajen Baba tana da magana dashi BaAlta awaya ta kira Zannah ta gaya masa da yagama ya shigo ya bada umarni Fandau ta k'araso
Azaune ta sameshi afalo kwarjinin sa da kamalan sa yananan
Zubewa tayi tace Bah ina kwana.? cikin harshin barbarci ya amsa ganin tayi shiru yasan da magana yace "me yake tafe dake.

Tace "Allah ya temaki Bah inason gaya maka wani magana amma kar kamin wani fassaran shine nake tsoron na kawo maka nasan kai ne ka dai maganin abin akan Fujjirat ne yar gidan Aunty Halima ayan da na fuskan ta akwai rauni a tarbiyar yarinyar, gashi ita kuma macce ce rayuwan, ta yana karkashin wani watarana inda namiji ne duk yanda yayi adone.
Shiru tayi  har saida malam yaca "ina jinki rauni wane iri kenan.?

"Bah yarinyar uwar da uban suna mata wani irin so wanda ita kuma tun daga yanzu ta gane anfi sonta tanayin yanda taga dama yar shekara 4 irin tabaran da takeyi abin zai baka mamaki a wancen zaman da nayi da yarinyar dan tayi lefi na dan mareta uban ta a gaban yan aikin gidan ya mareni kuma ya gayawa uwarta sai cewa tayi adawo ta ita asamu malaman ta amusu bayanin karatun wata 6 zatanayi kawai wata 6 zatayi anan Nigeria idan taje can sai tana daurawa dayake yana da kima a idon su haka sukace idan zai dauki nauyin malami da zasuna tafiya tare ayi wata shidan dasu sun yarda haka yadauki dauyin malamai 4 sukazo dasu ake koya mata anan kuma ta zagi wanda taga dama su kansu iyayen bata bariba amma sai susata agama suna lallamin ta kuma makarantan maba wanani na kirki suka sata ba dan duk malaman, yahudawane har wakan coci suke koya musu da nayi magana haka sukace wai idan ta girma tasan addinin zata dena danace susata amakarantan da Ummulkkairi yar gidan Ya Muktar take suka ce a a wai wanda Fuj nake shine makaranta mafi tsada akasan wanda hkairat takeyi har Qur ani suke ware yaran musulmi suke goya musu.

Malam yayi shiru ya tausayawa Fandau wato tana son Yar ta ta samu ingan taccen raruwa duk da ba agunta take ba awannan karan yaka mata ya bata *damar ta* dan haka yace "yanzu ya ki keson ayi Fatima.

"tace awai wani makaranta wanda wani balarabe yabude tun safe yaran suke zuwa amma sai yamma suke tayi tahfiz ne akwai karatu sosai inason ka samu Baban nata ka kaya masa yasatan idan ta tar biyan tu da ilimin addini nasan zata nusu.

" yanzu yaushene tafiyan naku.?
"gobeni idan Bagana ta haifu ta can zan wuce Niger din.
"to zan kirashi na bashi shawaran yanda kikace.
Tace "nagode Bah.
Tameke tafita
Fandau saida ta zaga Gargar sosai tayiwa wanda tasaba yiwa alkairi
Suna zaune da Mama tace "Mama Abul Kaam yace kin tura masa sunan wanda zasuyi hajji bana amma baifi mutum 7 ba ina cikon na goman.?
Mama tace"toni wazan cene idan gida Niger ne na bincika kowa yaje yanzu gashi anan Nabil ya karasa kai wanda basuyi ba wanda na basa 7 din mafa su YaGajine nace kowace ta kawo mutun 2 akasamu na hada da Nura wanan yaron da yake min hawala.
"shikenan Mama asa da aunty mero da mijn ta sai Dan gwaza driver yajima yana bauta agidan nan.
"yawwa wllh kinyi tunani mekyu Mairo tana da karamci.
"yawwa Mama anan wajen ki zan bar Emir.
 Mama ta Kalli Fandau dama taga alamun kamar tana da ciki Allah mai iko har yaushe aka haifi Fandau zatayi haihuwa na 6 yanzu afili kuma tace "kede wllh anyi wata uwa Allah yayiki ba kyason zama da yaro wayan cen ma yar albarka Halima take fama dasu wanndan dinma bazaki rikeba tsakanin ki da d'a sai haifuwa kawai.
Shagobe fuska tayi itafa arayuwan ta reno wahala yake bata har mamakin Hadim take da take wuni tana shidiman yara.

"Mama nono fa kawai zai manta ba baki shi duka zasuyi ba nasani yanzu ma idan naje sai anyi rigima da Hajiya Aunty.

Dariya mama tayi" yo karku ban mana inde wadan nan yaran nakune masu takewa mutum sallaya da gado da takalmin nima an bani katuwar Budurwa idan naje zan dauka.
"mama dama da gaske anbaki Lau din ne.
"Eh nina ce abari idan Bagana ta haifu naja sai muzo tare.
Lau yar gidan Barumi ce kanwar shatima.

*London*
 Suna sauka su Hadim sunzo taran su FUJJI tana ganin Baban ta da gudu ta jeta ta fad'a masa d'agata yayi yana juyata su Maaf ko ta kansu bai biba har Akkam da yaka ta faman d'aga masa hannu Fuji tace "Abul sai kadin ga tafiya wajen wanan ummul Kaam din kana barin mu meyasa baza ka zauna awajen mum na ba.?
Saida jikin kowa yayi sanyi Fuj zaran zance awajanta ita ko Fandau daukan Akkam tayi tana cewa" a a akai yaron Ummu yazama lukuti ita Hadim dan ta badar da zancen tace "ina  mai Barnon.?
Fandau tace" Emir yana wajen Mama.
Cikin murna Hadim tace "Allah yar uwa to da magana.
Itade Fandau gaba tayi ta shige mota sai.
Hadim tace "shine my star baku gayamin ba nasan zaman da zanyi daku ai ana shide Nabil kama hannun BilAL yayi suka shiga

Fuj bata hakura ba da suka je gida ma sai sake cewa tayi "Abul meyasa kazomin da wannan. ta nuna Fandau
Nabil yace saboda ita ma Momyn kuce.
"no Dad muguwar muce.
 Hadim tace" daughter kidena fadan haka itama Momyn kuce.
Cikin tsawa Fuj tace mum Akam boy ne ta buga kafa tayi sama Hadim ta tashi ta bita wanda Fandau tasan ma lallashin taje yi
Nabil ya fara kame kame
"kin gane Mata shiyaro yana da riko amma idan tayi wayo zata dena.
Fandau tace "ayya
Sai dare Nabil ya gayawa  Hadim yanason mayarda Fuj Islamic school
Hadim fada ta fara kamar ta ari baki Nabil yace "My one nayi tunani akai sosai ba sai macce tayi boko take wayewa ba wayewa yanayine kawai yanzu kiduba Ummul Akkam ba ta taba shiga class wai dantayi boko ba amma gashinan kanta awaye yake duk inda me karshe boko zata shiga itaba zata shiga balle FUJJI da zata tayi cikin wayewan me akayiwa bokon ne duniya nefa kuma ayanzu haka Fuj tana da dukiyar da hatta jikokin ta bazasu ga talauci ba rayuwa ga  companyn ta da kullum kara albarka yake dan haka gwara mune ma mata yanda zatayi ta gyara lahiran ta.
My star bazaka gane bane yanzu Duniya ba gaskiya idan Fuj batayi ilmin boko ba yazata kula da dukiyar ta.
"ai shikan sa makarantan na bincika ana bokon amma Arabic yafi yawa sosai dan haka zata samu wanda zata juya dukiyar ta ni Boko nayi nake sarrafa dukiya ta degree dina akan ball nayi mena sani aboko.
Hakade dakya ta yarda shima saida yace umarni Zannah ne tace "shikenan nasan shawaran Bah watarana zai zama me *AMFANI*  agaremu.
Zan iya cewa Alhaji Nabil yasamu kwanciyar hankali cikin iyalin sa kowacce tana kaffa kaffa da yar uwar ta hadin kai ba amagana

*BAYAN SHEKARA 20*

Cikin wanan shekarun  20 din abubuwa da dama sun faru cikin su awai na babban rashi da akayi na Zannah wanda yanzu dan sa Bunu ne akai sai rashin sarkin maine Barumi wanda yanzu Shateema ne akai  haka Hadim tara sa iyayenta uwa da uba  Maman Fandau tananan bawani alamun tsufa atare da ita sai ma najin dadi da yabai yana Shateema yaso tafiya da ita Nabil ya hana dan yanzu Nabil yayi rytare yazo gida
Fandau hafuwa ajere a gere saida tayi guda 10 Allah ya tsayar mata kuma duk ka 8 mazane sai yar auta   Fatima sunan Mamar Hadim ne suna kiranta Ammatee Ammate shekaranta 14 yanzu ita ma tazama budurwa fara ce sosai kamar Hadim sak dan har kajertan na su Ummin Nabil ta dauko gata acike take ta ko ina Maaruf da BilAL su suka gaji Nabil suna England da zama suma kafan su yana da tsada sosai Akkam  shima yana England yana kula da warkokin Nabil

Wani tsadedden mota naga yayi parking aciki haraban gidan a hankali ta saukar da kafanta saida ta bata lokaci kafin ta fito da gangan jikin nata wani burmemen shijab ne ajikin ta har kasa doguwa ce ba fara bace amma kalan ta yafi na fari daukan hankali Ahankali ta zakaya ta bude bayan ta dauki jakan da sauran tar kacen da jakan bai dauka ba cikin nusuwa ta fara takawa masu aiki ne suka fara cewa Yasaiyada barka dazuwa amsa musu take cikin gajiya *FUJJIRAT* kenan gwararriyar lacture a Ramad meduguri a fannin Islamic hayani yanda takeji tunkafin ta shiga gidan shi yanuna mata akwai taron samari na family agidan tunda su BilAL suna kasan gidan baya rabuwa da taron samari dan haka kawai ta janza hanya ta zagaya ta baya ta shiga bedroom dinta ta wuce saida ta wasa ruwa tasa doguwar riga ta dauki shijab dinta iya guiwa tasa dan ita tanada cikan kirji books da Heep's ga gidan su gidan tara samari dan haka kullum tana cikin shijab bame ganin su Maaruf yace kannen FUJJI ne saide ace sunyi kanwa ta 3 da iita gaku suna jida kudi dan haka duk abonkan su ba sa an su bedroom din Hadim ta shiga bata ganta ba ta fito parlour Fuhad kanin ta taga azaune yana danne danne a laptop tasan hayani yane ya koroshi a general parlor cikin murmushi yace .
"auntes dama kina ciki  ai da nasani dana shiga kin dauramin karatu .
"a a Fuhad yanzu na shigo ina mum na.?
"Tana part din ummul kaam  tasan idan tace zata ze part din Fandau dole tabi ta wayen yan hayaniyan dole ta waje ta fita ta zagaya zaune ta same su har Abul dinta
Naga Nabil yazama kato haka Hadim ma Fandau ta murje dayake ba jikin kibane dasu ba amma nayi mamakin ganin su duk kamar basu suka ciwannan shekarin ba musamman Fandau  ko Ammati yar auta baza kace ita ta haife taba  cikin nusuwar ta durkusa ta kaida su  Hadim tace "yawwa gwara da Allah ya kawoki FUJJI ki fitar da kwanin ki acikin su dan kinga su BilAL kannen ki har anyanke rana bana son ace su maza ma sunyi sunbar ki.
Shiru Fuj tayi  to yanzu ita waza ta fitarne duk maneman tafison Shamsudeen dan gidan BilAL maina amma shikuma sai jan aji sai kace ba shiya nace ta yarda dashi ba
Nabil yace "yafi mukude nasan yanzu da zannah yananan baku isa ta kai shekara 26 agida ba  kannen bayan ta suna da yara Tajuddin na miji ma yayi aure harda yara 2.
Ahankali Fuj tace "Mum shamsudeen din yafi ko tana fadan haka ta tashi da sauri ta shige bedroom din Ammati

Su Fuj tunsuna yara da sukayi wayo Hadim da kanta ta gaya musu dukan tarishin su ko da suka san ba itace uwar su ba ba abinda yaragu ason ta sukeyiwa Hadim saima ganin kimanta da suke dan sunfi son ta ma akan Fandau komai mum dinsu

*ARANAN AUREN*
*BIKI BIKI*
*AMFANI SOYYYYA*
*AURE*
Arannan naga iyaye yan Duniya ga Naira da Naira ya hadu gaba daya patyn bikin bawan da ba ayi da iyayen ba irin ta asan da akayi ba a magana Fandau komawa tayi kamar itace amarriyan su Jidda sai tsokanan ta suke Ummul kaam amma ke za acud'a ko

Hadim da kanta ta kai Fujjirat dakin miji kuka ko ba amagana da kyar aka rabasu
Tazo ko a gida tasa Nabil agaba tana kuka yanzu shikenan bazan ji motsin Fuj ba.
Fandau sai dariya take tace "inban da abinki Aunty yau fa amare 2 kika karba nayaran ki to me dan kinfitar da guda 1
Nabil yace "my one kawai kije ki karbo yarki nifa wanan dare nake jiye mata. Ma ga Shamsudeen jimgege dashi.
Dariya Fandau ta kara yi tace aini dadina da kobe zaurin zuwa ni adaren farko uwan wani har sumarni yayi.
Nabil yace "bakomai lada zata samu amma fa afili azuci ko addua yake Allah yasa yabita asannu.
Hadim ko fiton kujera ta dauka ta dinga jifan Fandau dashi Nabil yana karewa
Hadim tace "wllh mugun bakin ki akanki dake da yarki aike ba akwai aiki agaban ki.
Tana gama fadan haka ta haye sama dama girkin Fandau ne Nabil ya kama ta suma sukayi nasa part din
Wanka Fandau tayi tafito ta sameso yana aiki a laptop ta ja tarufe tace "time dina ya shigo dan kasan bana yarda da sakin wannan *DAMAN TAWA*
"Gaskiya ne yan mata wai ke mesirrin ne kinaga duk kin sake zama wata yarinya wllh da keda yan matan dazu awajen bikin banga wani ban banci ba.

"haba kai kake manin haka amma wace Budurwan za asamu haka.

"Bani ka dai ba har abokaina sun sha gayamin basu yarda ba wai kece ki ka haifi su Maaf ba shiyasa Akullum nake tunawa da ranan haduwar mu dake zanje lawan Bor
Na sinci dami a kale ashe itace farin cikina ina godiya da my one dan ita ce dalilin haduwar mu naso nayi wasa da *DAMA TA* na kin shawaran ta Allah yasoni da rahama
*AMFANI SOYYYYA AURE*
 kinbani yara masu albarka gashi yanzu muna shirin taran jikoki ina yarona. yana magana yana kunce igiyar rigan wankanta zatayi magana ya kifa fuskan sa kirjin ta

*Nima yanzu ya kamata nabar su haka gudun kar Gulma yayi yawa shi yasa ma ban leka gidan amarin ba*

Alhamdulilah

Sai kunsake jina jikin
*AMFANIN SOYYYYA*
wanda nasan zai k'ayata ku yabaku taurayi fiye da dama ta

(Subhanallahi wa'bihamdika Astagfirullah wa'atubu Ilaika)


*B JATTKO*

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *