Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Tuesday, May 12, 2020

SAIFUDEEN COMPLETE HAUSA NOVEL

adsense here
SAIFUDEEN COMPLETE HAUSA NOVEL
[4/22, 12:42 AM] Paexer: _Saturday/03/02/2018_
 *«»«»«»SAIFUDDEEN«»«»«»*



```By Billy giro😊```


*Dedicated to»»»Zarah gwandu*

```Bismillahi rahamanir rahim```.
  _Zan fara da sunan Allah ina kuma fatar na kammala da yardar shi_.
      _Allah yasa haka amin._

.

*«»Page«» 1* 
 _Kuka yake sosai gurfane a gun wani kabari,wanda yanayin kukan nasa ze tabbatar maka cewa haqiqa yayi babban rashi,musamman yanda idanuwan sa suka kumbura sukayi wani irin jajur ta yanda duk wanda ya kalle sa dole se nashi idanun sun ciko da qwallah sbd tausayi_.
 _A nn gurfanen da yake ne wani yazo shima se kukan yake ya tada shi ya rungume shi sosai a jikin sa,se rarrashin sa yake yana bashi magana,amma sam ya kasa daina kukan har se da yaja shi suka fita daga maqabartar_.
             
      *Baya Kafin faruwar hakan*.
          ««»»»«»»
Tsaye yake gaban mirror d'aure da farin towel a qugunsa yana taje sumar kanshi,wanda kallo d'aya zaka mishi kasan cewa hadadden guy ne shi,first class da sam bai aje kanshi kusa ba.
Sosai yake matuqar ji da kanshi sbd Allah yayi shi me tsananin kyau tamkar shi yayi kan shi.
 Shiyasa sosai kyawawan en mata ke rubibi akan sa amma sam baya kula su,mace d'aya kawai yake kulawa wato "Sophie"wata classmate d'isshi da sukayi karatu tare a London wacce yanzu haka tana nn Nigeria ta biyoshi.
  Bayan ya gama taje sumar kanshi ne ya tafi da cumb d'in yana qara kwantar da sajen fuskar shi dake kwance luf kan farar fatar shi tas wacce tamkar ka kwanta jini ya fito.
Sai da ya feshe jikin sa da body spray snn ya nufi kan bed inda ya ajiye kayan sawar shi da ya ciro,ya zauna tare da cire towel d'in jikinsa ya cillar gefe,ya janyo guntun wandon sa fari qal ya saka snn ya saka dogon wandon sa na suit silk fari,rigar ciki baqa yayi stocking da black belt,ya saka necktie fari,sucks baqaqe da takalmi baqaqe snn ya saka er samar shi fara,ya fesa turare kana ya d'auki briefcase d'issa ya fito bai zarce koina ba se 6angaren iyayen shi.
  Ya sami mahaifiyar tashi ta fito daga kitchen tana jera breakfast kan dinning.
A natse ya gaida ta fuskar sa ba yabo ba fallasa,byn ta amsa yace am going.
  Da sauri ta kalle shi tace"breakfast fa gashi har na kammala had'a komai ka d'an tsaya mana kaci ko kad'an ne"
  Yace"No umma ina sauri ne"
  Ba tare da ya jira me zata ce ba yasa qafa ya fita abin shi.
  Ta bisa da kallo kawai tana mamakin yau ko Abban sa bai je ya gaida ba ko lafiya,nan se ga Abban na shi ya fito cikin shirin sa tsaf na fita,ta kalle sa tace kaddai kaima fita zakayi hakan nn baza ka ci komai ba kmr yanda saifuddeen ya fita.
 Komai be ce da ita ba se d'an murmushi yayi had'e da girgiza kansa a lokacin da yaji tashin motar saifuddeen,kana ya qarasa gun dinning yaja kujera ya zauna yana fad'in"Halan me saifuddeen  yace maki da zai fita?
  Umma da ta janyo plate zata fara serving nashi tace"ce min yayi sauri yake"
   Abba yace"haka dai ya gaya miki amma ba wani sauri da yake da akwai dalilin da yasa baya so mu had'u"
   Umma tace"shi saifuddeen d'in?
  Yace"shi d'in yaron da ko kad'an baya so in masa zancen aure amma jiya se gashi na ganshi da wata baturiya a office d'inshi yanda na gansu abun takaici matsayin sa na musulmi yana biye mata kan lalaci irin nasu na turawa.
  Numfashi umma ta fitar snn ta zauna a hankli tana kallon Abba wacce da alama tasan  saifuddeen na tare da Sophie ba yau ba amma se tace "kana nufin yanzu saifuddeen duk jiji da kanshi yana kula en mata.
   Abba yace"Hm Mamn yusra knn ae duk namijin da kika ga baya kula mace to ba lafiyar sa qalau ba,amma irin kulawar da ake so shine namiji ya nemi mace da son aure ba irin shirritar da naga saifuddeen ya d'auko da wacce sam aure bazai ta6a shiga a tsakanin su ba,dan haka wlh sam bazan yarje masa wnn shashan cin ba,ni aure zan masa ko yana so ko baya so!
  Yana kaiwa nn ya fara cin abincin da umma ta zuba mishi.
  Umma dake kallon sa tayi shiru bata sake cewa komai ba,se abinci ta zubawa kanta ta fara ci cike da tunanin yanda zata shawo kan saifuddeen ya rabu da Sophie,dan ko kad'an bata son huld'ar sa da ita shiyasa ma bata so Abba yasan da ita ba.

Se da yamma liqis saifuddeen ya sake dawowa 6angaren su umma,sanye da qananun kaya a jikin sa,rigar fara ce tas me guntun hannu,rubutun jikinta baqi ne manya da aka rubuta *Being human*,wandon kuma fari ne tas tree quarter wanda duk da cewa fuskar sa ba annuri amma yayi matuqar kyau se qamshi ke fita a jikin shi sbd mutum ne shi da sam baya wasa da turare yana son qamshi sosai a  rayuwar shi,shiyasa jinin sa ya had'u da Sophie dan haka take itama ko yaushe cikin qamshi take.
  Umma dake zaune kan doguwar kujera hannun ta riqe da littafin addu'o'i ta kafe idon ta a kansa har ya qaraso ya zauna a kusa da kujerar da take zaune,still fuskar nn tasa ba annuri ya kalle ta yace"umma i will back to England"
  Umma tace"meyasa?
 Yace"kmr yanda suke buqata"
 Tace"kmr ya u mean zaka kar6i tayin su ka koma can da aiki ka bar asibitin mahaifinka saifuddeen?
  Yace"eh"
  Da mamaki tace"why?
 Muryar sa a hnkli can ciki yace"Abba  yasa min ido umma ni kuma bana so"
 Umma ta numfasa tace"saifuddeen knn idan Abban ka bai sa ido akan rayuwar ka ba to wa kake so ya kula da rayuwar ka ya nuna maka hanyar da ta dace kabi iye"
  Shiru yayi kmr beji me tace ba taci gaba da cewa"saifuddeen kaifa musulmi ne bai kamata dan kayi karatu a qasar turawa ba kazo kana yin irin halayen su marassa kyau snn kuma a maka magana kaji haushi,ka sani fa ko kad'an Abban ka bai ji dad'in yanda ya same ka office kaida Sophie ba dan nasan ba makawa ita ce ya ganku tare tunda yace min baturiya.
 A qufule yayi d'an guntun tsaki yace"umma bafa wani abu ya ganmu munayi ba fa,just ya samu tana kan laps d'ina muna magana shine kawai se  ya balbale ni da fad'a wai kar ya qara gani na da ita,wat kind of this umma.
 Umma dake kallon sa tace"Hum Saifuddeen yanzu kai a ganinka ba komai bane Abbanka ya ganka da mace kan qafafuwan ka,saif ae ko matar ka ce dole ka d'anji kunya bare Sophie wacce.....dafe kansa yayi sbd mgnr ta ishe shi,yace"umma plz a daina zancen nn haka is enough ni yunwa nake ji tun safe banci komai ba"
  Ba yanda umma ta iya se ce masa tayi olryt me kake so kaci?
  Yace"abu me d'an nauyi da zan iya ci.
  Nan umma ta tashi a hnkli taje gun dinning wacce dama ta kammala girkin ta na yamma,ta d'ebo masa,tuwon semo ne da miyar agusi wacce taji naman rago sosai tayi kyau har ta gaji se qamshi ke tashi,ta had'o mishi ruwa da lemu ta kawo mishi ya kar6a tare da mata godiya snn ya fara ci.
           »»»
Da dare umma da Abba suna zaune a falo suna kallon labarai,Abba ne saman kujera umma kuma tana zaune a qasa manne jikin kujerar yayinda wata yarinya da bazata wuce shekara biyar ba wato wacce ake kira da yusra tana kwance kan qafafuwan ta tana bacci,umma na fmn shafa jikinta a hankli.
Abba yayi gyaran murya yana me kallon umma yace"Maman yusra wata magana nake so muyi"
  Umma ta kalle sa tace"tou Allah yasa ba wani abu bane Alhj"
  Yace"ba wani abu bane so nake ki amince na had'a auren saifuddeen da zarah.
  Umma ta numfasa tace"cabd'i Saifuddeen da zarah fa kace Alhj?
  Yace"Eh haka nace ko anyiwa zarah miji ne ban sani ba?
  Aa ae kasan baza ma a fara ba baka ji ba amma dai kasan sam saifuddeen bazai ta6a yarda ya auri zarah ba ko.
  Abba yace"Zarah bata da wani aibu da saifuddeen zai ce bazai so ta ba tunda gwargwado dei tayi karatu har gaba da primary"
  To Alhj kasan fa zarah gabad'aya a qauya tayi rayuwar ta zuwan ta birni jefi jefi ne.
  Abba yace"ae shiyasa nace ta dawo nn da zama dmn ki wayar mata da kai,na kuma sata a university taci gaba da karatu sannu sannu  har su zo su saba ita da saifuddeen kafin nasa lokacin auren su.
  Umma tace"gaskiya Alhj kawai da ka bashi za6i ya kawo wacce yake so dan bana tunanin saifuddeen ze ta6a sakarwa zarah fuska har sukai ga sabawa da juna bare har ace aure ya shigo tsakanin su abun da kmr wuya.
  Yace"Maman yusra ba wani za6i da zan bashi Zarah nake so ya aura,dan haka abunda kawai nake so dake shine gobe ki shirya kije Rimin dako kizo da Zarah in yaso se kiyiwa inna bayanin komai nasan in taji baza ta qi ba inshaa Allah,ban sani ba ko dai ke ba kya son Zarah ta auri saifuddeen ne.
  Umma tace"ba haka bane Alhj ae Zarah in taji nasan ba qaramin farin ciki zatayi ba dan dai sosai tana son zaman birni,a duk lokacinda naje ji take kmr ta biyoni.
  Yace"to ai duk kece tun tana qarama ba yanda banyi ba kan tazo nn tare damu ta zauna kika qi alhali yarinya naso.
  D'an murmushi umma tayi tace"uhm Alhj knn ae de yanzu komai ya wuce Allah ya nuna mana gobe lafiya se inje inzo da ita d'in"
  D'auke da murmushi Abba yace "Amin ko ke fah".
[4/22, 12:42 AM] Paexer: _Sunday/04/03/2018_ *«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*






By
  *Billy giro😊*


*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 2*
 Washe gari tun da safe guraren qarfe 7 na safe umma ta kammala shirin tafiyar ta ita da yusra,driver yaja su suka tafi garin Rimin dako wato wani kauye dake cikin karamar hukumar 6agwai dake nan cikin jihar kano.

Awar su biyu kan hanya snn suka isa garin.

Gida ne d'an qarami suka paka motar su a gun,umma ta shiga daga ciki janye da yusra a hannunta ta sami wata yarinya da bazata wuce 17 yrs ba tana duqe a gaban murhu tana hura wuta da iskan bakinta,wacce tana ganin umma tazo aguje ta rungume ta cike da murna tana fad'in"oyoyo innan bunni shannun ki da zuwa"
  Kasancewar su Fulani ne Hausar su bata bi dede ba.
  Umma dake kallonta d'auke da murmushi tace"Yauwa Zarah ina mutan gidan suke ne naji shiru kmr ba kowa?
 Zarah da ta kama hannun yusra washe da baki tace"eh kawu baya nn yaje gurin kiwo,dije kuma taje d'ibar ruwa(cewa da er kawunta wacce suke tsara)
 Taci gaba da cewa mama asabe (wato mahaifiyar dije) yanzu ta siga bayi,inna kuma cewa da kakarta tana daga shiki kindirmo take damawa.
 Murmushi umma tayi zasu qarasa daga ciki Zarah ke tambayar ta"Nusaiba fa naga yusra kawai aka zo da ita"
 umma tace"eh Nusaiba bata nn  tana Kaduna ta kai musu hutu.
  Ta qarashe mgnr ne dai dai sun shigo d'akin inna,wanda d'an d'akine da aka yishi kmr bukka se mutum ya duqa yake iya shiga.
  Wacce ake kira da inna tana zaune a tsakar d'akin qwarya a gabanta tana dama kindirmo kmr yanda zarah tace.
"A'ah Maraba maraba da mutan birni yau kune a garin?
cewar inna wacce tayi maganar ne washe da baki tana kallon umma.
 Yayinda umma ta zauna kan d'an qaramin gadon karan da ke cikin d'akin tana fad'in mune inna ya muka same ku.
  Tace"lafiya lau ya mutan birni kowa lafiya?
  Duk suna lafiya Alhj ma yace a gaida ki da jiki da kuma lafiyar qafafu.
  Inna tace"wlh Alhmdlh jiki yayi sauqi qafafu kuma se sauqi suke tunda na fara shafa wnn maganin da kika kawo min kwanaki.
  Tace"to Allah ya qara sauqi inna"
 Inna tace"Amin yayinda take kallon yusra wacce tazo gurinta d'auke da murmushi ta zauna kusa da ita tana kallon yanda inna ke dama kindirmo,inna dake kallonta tace"ko kin iya in baki ki qarasa damawa"
  Da sauri yusra ta gyad'a mata kai alamar eh,inna ta lakaci hancinta cikin yanayin wasar jika da kaka tace"to naqi d'in salon ki mana dagwalgwale mu kasa sha.
   A shagwa6e yusra ta kama ludayin ita se inna ta bata ta dama.
 Umma dake kallon su tayi murmushi bata ce komai ba se kallon d'akin take sam bata son ganin d'akin nn haka,so take taga komai na zamani a ciki,wacce tuni ba yanda bata yi ba kan inna ta bari a gyara musu gida a sauya musu komai na zamani amma tace a'a ita bata son rabuwa da abubuwan gado.
  Inna ce ta katse mata shirun da cewa"ni kuwa ina Nusaiba?
  Umma ace"ae Nusaiba tana Kaduna ta kai musu hutu"
 Inna tace"Ayyo wnn karon bamu keda hutun ba knn,to fad'ima je kawowa innar ki ruwa mana tasha.
  Umma tace"Aa inna ni bana jin qishi kindirmo de zan sha snn tare nike da audu driver yana waje a qofar gida Zarah d'auko kwanon shan ruwa a zuba masa snn ki d'auki tabarma da ruwa a kofi ki kai masa kafin a gama abinci naga yanzu aka d'aura.
  Nan Zarah ta d'auko kwanon shan ruwa me kyau me marfi da kuma silver cup shima me marfi,taje waje ta d'auraye ta kawo ma inna kwanon shan ruwan ta ajiye snn ta nufi lungun ganbu riqe da kofin silver da akwai randa a lungun gambu nn cikin d'akin,dake d'auke da tsafta taccin ruwan dad'i da aka killace dan ruwan sha kawai,ta d'ibar mishi ruwan snn ta d'auki kindirmo da inna ta zuba mishi ta d'aura kwanon aka,ta fita riqe da sabuwar tabarmar da ta d'aukar mishi da kuma ruwan da ta d'ibar mishi a cup.
  Nan umma ke snr da inna dalilin zuwanta.
  Sosai inna taji dad'i wacce ba musu ta amince da zancen dan ita farin cikinta ne jikarta tayi aure birni.
  Koda zarah ta dawo aka snr da ita har tsallen murna ta dinga yi zata koma birni da zama,se dai ba'a gaya mata cewa aure za'a mata ba idan an kwan biyu.

 Bayan sllr la'asar
tuni Zarah ta kammala had'a komai nata na tafiya har ban kwana taje tayi da en uwa da abokan arziki.
 Da zasu tafi har kuka dije tayi zainab zata tafi ta barta.

Koda suka isa kano se kiraye kirayen sllr magrib ake,kae tsaye umma ta kaita d'akin da zata zauna wato d'akin Nusaiba.
 Byn sunyi sllh umma ta kaita gurin Abba suka gaisa.

 Washe gari da safe umma da kanta taje ta kira zarah suzo suyi breakfast,suna tafe kafin su qarasa gun dinning ta nuna mata saifuddeen dake zaune shi kad'ai kan dining yana cin breakfast d'insa.
(dan shi haka yake idan yana jin yunwa baya iya jiran kowa)
Tace yayanki ne in munje ki gaida shi amma fa baya son surutu dan karki jashi da srt yaji haushin ki.
  Zarah tace"to,amma waye si da baya son srt inna,ko sine wannan da keyin karatu a waje?
 Tayi mgnr ne tana mae kallon umma"
 Umma tace mata"eh shine"
 Tace"inna ya ma shunan si ni mantawa nake?
  Shiru umma tayi bata bata amsa ba sbd sun qaraso gun dining se jawo mata kujerar da ke dubin saifuddeen tayi,ba musu Zarah ta zauna kmr yanda umma ta mata nuni,wacce tana zama ta karkatadda kanta tana leqen fuskar saifuddeen da kansa ke duqe gabad'aya hankalin sa na gun cin abinci bai ko ji motsin isowar su gurin ba,se jin mgnr ta yayi kmr daga sama tace"hai shannun ka ka tasi lafiya,fad'ima shuna na kaifa ya shunan ka"
  Da saurin sa ya d'ago sexy eyes d'insa yana kallon ta fuskar sa a yatsine,a ransa yana mamakin wnn abar fa daga ina!
  Zarah da ta saki baki still kanta a karkace se kallon sa take tayi,a ranta tace"Aradu sina da kyau wnn"
  Se gashi mgnr ta fito a fili
  Saifuddeen dake kallon ta cike da tsana yace"of course!but to hell wit u mayya!mtsw!yayi tsaki tare da kallon umma  yace"umma where did u get this abar,wata iri da ita haka tazo ta zaunawa mutane kan dining kuma kin barta baki koreta ba.
  Kallon sa kawai umma tayi bata ce mishi komai ba,haushi duk ya cika shi yana kallon Zarah se duk yaji abincin ma ya fita ranshi nn ya ture plate d'in abinci gefe ya d'auki ruwa a cup yakai bakin sa,nn se ga Abba ya qaraso shida yusra janye a hannun shi wanda kai tsaye ya nuna Zarah yace da saifuddeen ka sani wnn da kake gani er uwar ka ce!
  Ba shiri saifuddeen ya furzadda ruwan da yasa a bakin shi be riga ya had'iye ba,kmr yaga kashi fuskar sa a ya mutse ya nuna Zarah yace"haba Abba wnn ce er uwata wacce ko er aikin gidan nn bata isa ta zama ba se dai ko mabaraciyar kan titi.
  Kul!
Cewar Abba wanda a fusace yace"kar in koma jin wnn kalmar ta fito a bakin ka,Zarah er uwar ka ce ta jini ko kana so ko baka so.
  Shiru saifuddeen yayi yana kallon Abba kana ya ajiye cup d'in da ke riqe a hannun shi ya bar gurin cike da jin haushin yanda Abba ya alaqanta shi da Zarah dan shi sam be yarda akwai wata alaqa shida ita ba,kawai de Abba ya fad'a ne dan ya 6ata masa rai.
  Jiki sanyaye Abba ya zauna ya kalli umma wacce tayi saurin d'auke idonta akan shi nn ya maida duban sa gun Zarah yace"kiyi haquri Zarah halin saifuddeen ne se shi kuma be san waye ke ba shiyasa"
Muryar ta a hnkli can ciki da alama taji zafin yanda saifuddeen ya mata tace"ba komai Baffa"

Nan sukayi breakfast har suka gama ba wanda ya sake cewa uffan.
  Suna gamawa Abba ya fita shida yusra acewar zasu je granny house kasancewar yau weekend ne ba aiki.
 
Saifuddeen kuwa yana zuwa d'akin sa kae tsaye kan sofa yaje ya zauna ya dafe kansa idanuwan sa a rufe,Zarah kawai yake gani,a ransa yana mamakin ina umma ta kwaso ta da har ake alanqanta shi da ita ace wai er uwar sa ce ta jini wacce kaf dangin su yasan babu kucaka irinta.
  Lallai idan har er aiki ce aka kawo zai yi maganin abun dan bazai ta6a barin ta ta zauna gidan ba,se dai a nemo wata da ta cancanci zama er aikin gidan.
[4/22, 12:42 AM] Paexer: _Monday/05/02/2018_ *«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*




By
   *Billy giro😊*






*Dedicated to»»»Zarah gwandu*







*«»Page«» 3*
Tun daga lokacin saifuddeen bai sake komawa 6angaren ba har se a washe gari snn,koda yazo ya sami driver ya sauke su umma knn sun fito daga anguwa gurin tela sbd sabbin d'inkunan da za'a ma zarah.
 Yana tsaye hannayen sa duka cikin aljifan wandon sa,da suka qaraso zarah ta duqa har qasa tana gaishe shi yayi kmr be jita ba ko gefen ta ma yaqi ya kalla se umma yake ma sannu da zuwa wacce ta amsa tare da nuna mishi Zarah dake durqushe still bata tashi ba tace"baka ganin Zarah na gaida ka"
   Kallon Zarah yayi tare da dalla mata uwar harara ae kuwa ta tashi sum sum ta wuce ya bita da wani irin kallon tsana.
  Umma ta girgiza kanta d'auke da d'an murmushi tace"saifuddeen wai meye aibun Zarah ne,naga ni banga wani abun nuna qyama a gare ta ba jiya jiya da fara ganin ta duk kabi ka d'aura mata karan tsana"
 Fuskar sa a yatsine kmr umman ce Zarah yace"kawai umma ni bata min ba,i dnt wnt see her any more,plz ki nemo wata er aikin da ta cancanci zama a gidan nn not dis one"
Umma dake kallon sa tace"saifuddeen ka daina kallon Zarah a er aiki ita ba er aiki bace fa"
  Yace"to waye ita?
  Tace"very soon zaka san wace ce ita"
 Daga haka taja hannun yusra suka wuce ba tare da ta jira me ze ce ba,
"very soon"
 ya fad'a yana me kallon ta har ta shige.
  In a shrug way ya kad'a kafad'un sa yayi gaba.
 Umma kuwa tana shiga kae tsaye d'akin Nusaiba ta nufa gun Zarah,ta same ta zaune kan bed kanta qasa,ta qarasa gurinta ta zauna tare da dafa ta.
 Zarah ta d'ago ta kalle ta idanuwanta cike tap da qwallah tace"inna ni bazan sake gaida shi ba tunda baya so"
   Umma tace"No Zarah yayanki ne kiyi haquri kici gaba da gaida shi kinji"
  Muryar ta kmr zata fashe da kuka tace"to inna baya so fa"
  Umma tace"halin shi ne haka amma idan kika ci gaba da gaida shi ze daina kinji"
  Tace"sikenn naji zanci gaba da gaida shi d'in tunda kince,yause ne Nusaiba zata dawo to?
 Umma tace"ae nusaiba na jin kinzo ta fasa qarasa hutun ta acan tana nn dawo wa jibi jibin nn inshaa Allah,idan ta dawo zan baki kud'i ta rakaki kasuwa ki siyo kayan kwalliya dama sauran abubuwan da kk buqata ko".
   D'auke da murmushi Zarah ta gyad'a kai cike da jin dad'i zata zama er bunni ga sabbin d'inkuna za'a mata snn kuma za'a je da ita kasuwa ta siyo kayan kwalliya,lallai kuwa zata yi ja gira tayi kwalliyar en bunni,in ma dan qauyan cin ta ne saifuddeen ke nuna mata tsana ko gaisuwar ta baya amsa to ze daina.

Bayan kwana biyu da faruwar haka ne Nusaiba ta dawo wato 'ya ga umma wacce bazata wuce 15 yrs ba,amma kasancewar girman jiki ne da ita zaka d'auka shekarun su d'aya da Zarah dan ta cimma Zarah da komai.

A washe garin rnr da Nusaiba ta dawo ne umma ta basu kud'i su tafi kasuwa.
  Nusaiba tayi kwalliyar ta acan acan ta zamani ta kuma yi kyau sosai dan ta iya kwalliyar kuma kwalliyar na mata kyau.
  Zarah kam powder kawai ta shafa a fuskar ta se kwalli da red lip-stick da tasa a lips d'inta, dan tunda taga kwalliyar da nusaiba tayi tasan in tayi tata kwalliyar tantagaryar baqauya zata fito,amma duk da haka se tayi kyau hasken ta ya qara fitowa sosai sbd fara ce sol.
   Gudun kar ta saka kayan da basu dace da fitar birni ba tace da Nusaiba ta za6ar mata kayan da zata sa,Nusaiba kuwa ta za6ar mata wata atamfa Holland ja da akayi zanen manya manyan leaf a jikinta milk in colour,ta had'a mata da wani hijab milk me hannu da ta gani a cikin kayanta da bazai wuce iya guiwa ba.
  Ita kuma ta shirya cikin black arabian gown snn tayi rolling da d'an kwalin arabian gown d'in.

Koda suka fito garin luf luf dashi ba rana se iska me dad'i dake ta kad'awa.
Saifuddeen na zaune a farfajiyar gidan can kusa da flowers kan kujerar shan iska shida wani abokin sa da sukayi krt tare,ipad a hannun shi da alama wani abu yake dubawa ta yanda yake scrolling da 'yan yatsun sa.
  Tare Nusaiba da Zarah suka gaida su,abokin ne ya fara amsa musu,saifuddeen kuma gaisuwar Nusaiba kad'ai ya amsa wato ya amsa gaisuwar ne had'e da kiran sunan ta har yana tambayar ta ya mutan kd tace mishi lafiya qalau.
 Bayan sun wuce abokin nasa ke cewa"A ina kuka sami fine yellow girl like nucy?
  Ba tare da Saifuddeen ya kalle sa ba yace"ae Nusaiba d'in ce baka gane ta ba?
  Abokin sa ya kalle sa had'e da girgiza kansa yace"ae kasan wacce nake nufi tafi nusaiba haske wnn d'ayar da kaqi amsawa gaisuwa@Fulani girl"
  Still Saifuddeen be kalle sa ba se ta6e bakin sa da yayi had'e da fad'in"oho ni ban san a ina aka samo ta ba"
  Ae da ganin ta er uwar ku ce kan yanda kuke kama kaida ita.
  Abokin nasa ya fad'a.
 Saifuddeen ya tsaya cak da abunda yake tare da sauke qafar sa dake kan d'aya yana kallon abokin nasa da fuskar sa da ta sauya lokaci d'aya,ya nuna kansa da yatsa cikin muryar 6acin rai yace"ni d'in zaka ce wae munyi kama da wnn abar!
   Abokin nasa yayi dariya tare da dafa shi yace"wnn abar fa kace to maida wuqar ni da wasa nake maka,kawai so nake inji wace ce?
A fusace Saifuddeen ya buge hannun abokin nasa ya kuma nuna sa yace"to wlh kar ka sake min haka jamil bana so"
A hnkli jamil d'in  yace"to naji yi haquri gaya min wace ce?
  Tsaki Saifuddeen yaja ya tashi ya bar gurin dan jamil ya gama 6ata masa rai shida yau yake jin er fara'ar sa amma jamil yazo ya 6ata masa komai.
  Jamil ya bisa da kallo d'auke da murmushi har se da ya daina ganin sa snn ya girgiza kansa yace"hm Saifuddeen halinka se kai"
  Nan ya tashi yaja motar sa ya bar gidan cike da tunanin sanin wace ce Zarah dan shi haka kawai yaji lokaci d'aya tayi mae,lallai bazai yi qasa a guiwa ba da wuri ze bayyana soyayyar sa gare ta bazai tsaya zurfin ciki ba ya rasata kmr yanda ya rasa Nusaiba aka riga shi.
  Dan yaso Nusaiba sosai amma ko Saifuddeen bai ta6a gayawa ba bare Nusaiba.
                *«»*
Bayan sun dawo da kasuwa Nusaiba ce zaune a d'akin umma,umma na duba kayayyakin da suka siyo kayan kwalliya ne da turarukka se inner wears da kuma kayan bacci kala biyu.
Nusaiba dake danne danne a waya tace"umma ashe dama yaya saif yana nn?
  Umma tace"eh yana nn me ya faru?
  No umma ba komai kawai na d'auka ko yayi tafiya ne naga tun jiya da safe dana dawo bangan shi ba har se d'azun da zamu je kasuwa.
  Umma tace"to ai kinsan halin yayan naki ba kasaifai yake shigowa 6angaren nn ba se cin abinci ke kawo shi ko kuma idan ze fita,kwana biyun nn ma ko cin abinci ya daina shigowa se idan ta mishi dad'i.
  Nusaiba tace"hm yaya saif manya ne zanso inga mtr da zai aura dan nasan se ya darje ya za6o dai dai dashi"
   Murmushi umma tayi tare da fad'in yayanki da baya ko son a masa zancen aure wai bai tashi ba tukuna.
   Tace"to umma may be gimbiyar tasa na can waje tana karatu ita yake jiran se ta kammala tukun musha biki.
   Murmushi kawai umma tayi bata sake cewa komai ba.
  Se duba kayan taci gaba dayi bayan ta gama duba kayan ta maida su a leda ta miqawa Nusaiba tare da fad'in"to gashi naga kayan sunyi se ki maidawa zarah nata ne ita kad'ai kin sani,kinada naki dan haka kowa ya tsaya kan nashi bana so inga wani na aiki da kayan wani dan nasan halinki ga me da kayan kwalliya ko kinada naki se kinzo har d'akin nn kinyi kwalliya da kayan kwalliya na na rasa wane irin ruwan ido ne dake"
   Cikin turo baki Nusaiba tace"kai umma jefi jefi ne fa kawai nake d'an zowa d'akin nn ina yin kwalliya ko shi sbd mirror d'inki yana fitowa da mutum sosai amma bawai ruwan idon kayan kwalliya nake ba,bare Zarah da kwana biyu tafiyar ta zatayi"
Umma tace"Waya gaya miki Zarah kam tazo knn nn zata ci gaba da zama tare da mu.
  Cike da murna nusaiba tace"da gaske umma!
   Umma ta gyad'a mata kai d'auke da murmushi.
  Tsalle Nusaiba ta daka tace"kae amma wlh naji dad'i dama zaman gidan nn ni kad'ai ya ishe ni yusra ce tayi qarama ba fira take taya mutum ba.
  Nan ta kwashi kayan cike da murna ta fita umma ta bita da kallo d'auke da murmushi a fuskarta har ranta tana jin dad'in yanda Nusaiba bata d'auki kanta kowa ba,duk yanda d'an uwanta yake,talaka ne ko baqauye bata nuna masa qyama se ma qoqarin take ta shigar da shi a jikinta sam halin su ba iri d'aya ne dana Saifuddeen ba.
[4/22, 12:42 AM] Paexer: _Tuesday/06/02/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*






By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*




*«»Page«» 4&5*
Nusaiba na zuwa d'akin su ta tarar da Zarah ta cire kayan jikinta ta sauya wasu,taje ta rungume ta cike da murna tana er qaramar rawa a jikinta"
 Zarah ta d'ago ta tana kallon ta d'auke da murmushi wacce hkn ya bayyanar da dimples d'inta tace"lafiya dai me kike ma murna haka Nusaiba?
  Nusaiba tace"umma tace min kinxo knn baza ki koma ba zaki ci gaba da zama tare damu shine nake murna"
  Murmushi Zarah tayi amma aranta addu'a  take Allah yasa zata iya zaman gidan to,dan yanda Saifuddeen ke mata be mata dad'i ko kad'an,sam bata son wulaqanci shi kuma ta fahimci saren saren wulaqanci ne dashi,amma in dan qauyan cinta ne sannu a hnkli zatayi maganin abun.
   Tana nazarin ne d'auke da murmushi a fuskarta,hakan yasa Nusaiba bata fahimci komai ba se miqa mata ledar kayan ta tayi tare da fad'in"umma tace sunyi kyau mun iya siyayya kiyi amfani da duk abunda ke ciki u are free duka naki ne kin sani"
  Murmushi kawai zarah ta koma yi snn ta zauna a hankli kan bed kmr wacce qwai ya fashewa ta bud'e ledar ta ciro kayan kwalliya ta kalli Nusaiba tace"in tambaye ki.
  Nusaiba ta zauna kusa da ita tace"fad'i man ina jinki"
Muryar ta a hankali tace"yanzu idan kika koya min irin kwalliyar ki zan iya,ko se d'an bunni kawai ke iya irinta?
 Nusaiba dake kallonta tace"Of course zaki iya mana ae komai sa kai ne"
  Tace"to ina son kullum ki riqa koya min har in iya,nima na zama er bunni a daina wulaqanta ni ana min kallon er qauye"
  D'auke da murmushi Nusaiba taja karan hancinta da ya tafi tsaye har baka kmr jinjirin karas,tace"wake miki kallon er qauye ae ba wanda ya isa dan ke ba baqauya ba ce"
  Murmushi kawai Zarah tayi tasan Nusaiba fad'a kawai tayi amma ita baqauyce sosai ta sani.

The following day ne mai d'inki ya kawo ma Zarah d'inkunan ta ciki har da hijabin uniform na islamiyya school.
  Islamiyyar ba nisa da gidan a qafa suke zuwa su uku,wato zarah,Nusaiba,da kuma yusra,dan makarantar har da ajin yara akwai bata manya kad'ai bace,kuma safe da yamma ake zuwa kasancewar ana hutun makarantar boko.

Ranar wata assabar da yamma zarah da nusaiba sun shirya zasu tafi islamiyya su biyu sbd yau yusra bata jin dad'i tun da safe ta tashi da jin zazza6i.
  Falo suka bar mami tare da yusra tana jiran Saifuddeen yazo ya duba mata ita dan Abba baya nn yayi tafiya zuwa Abuja.
  Koda zarah da nusaiba suka fita se gashi sun had'u da saifuddeen d'in shida jamil wa enda shigowar su knn gidan sun fito daga cikin mota.
  Jamil kallon zarah yake dake sanye cikin hijabin uniform d'inta blue mai hannu dake kai mata har qasa,fuskar ta fayau ba kwalliya se powder da kwalli da ta shafa,haka nn d'an bakinta d'an daidai me kmr an shafa janbaki se qyalqyalin lip gloss yake,bai d'auke idon sa a kanta ba har suka qaraso gurin su suka gaida su,ko wnn karon shi ya fara amsa musu,snn can ciki Saifuddeen ya amsa gaisuwar Nusaiba wacce yake jin itama ya kusa daina amsa gaisuwar ta idan har yaci gaba da ganin ta tare da zarah.
   Yana jin jamil yana tambayar Nusaiba ya sunan baquwar tamu tace mishi Zarah.
  "Nyc name"
 Ya fad'a
murmushi kawai nusaiba tayi suka wuce Saifuddeen ya ta6e baki jamil yace"lafiya"
  Yace"surutun naka ne naga yayi yawa har da wani tambayar suna,kaci sa'a Nusaiba ce ta fad'i sunan da yarinyar ce se kaji voice d'in nata wani iri ba dad'i,rnr fa kawai ina zaune ina cin abinci kan dining,ban ta6a ganin ta ba ma se a rnr,kaina a duqe banji motsin isowar su gurin ba ita da umma,kawai kmr daga sama naji muryar ta tace"hai shannun ka,Fad'ima shuna na kaifa ya shunan ka"
   Yayi mgnr ne fuskar sa a yamuste,jamil kam se murmushi yayi yana mae qara jin son zarah a cikin ranshi,dan yasan halin abokin nasa idan baya ra'ayin abu qara 6ata abun yake.

Shiga sukayi daga ciki suka sami umma,jamil ya durqusa cike da ladabi ya gaida umma ta amsa cike da fara'ar ta har tana tambayar sa ya mutanen gida yace mata duk suna lafiya,snn ya zauna kan kujera yana kallon yusra dake rungume a jikinta yace ashe yusra ba lafiya"
  Tace"eh wlh ka ganta gata nn se fama nike da ita jikin nata duk yayi zafi"
  "Oh no"
Jamil ya fad'a cikin yanayin tausaya wa,kana yakai hannu yana ta6a jikin nata a lokacinda Saifuddeen ya kar6e ta yana duba ta.
  Ledar magunguna da alluran da ke hannun sa ya ajiye gefe a kusa dashi yace da jamil ya 6alle allura ya had'a mishi.
   Nan fa yusra na jin zancen allura ta ajiye kuka bata so har tana neman guduwa daga jikin Saifuddeen,lalla6a ta yake kmr er cikin sa dan sosai yake tausayin yaro qarami idan bashi da lafiya,cikin lallami har ya samu ya mata allurar se kuka take ta mishi yana ta rarrashin ta har tayi bacci kan jikin shi,nn ya shiga shafa bayanta a hnkli har sai da baccinta yayi nisa snn ya bawa umma ita suka fita.
  Kae tsaye 6angaren shi suka tafi.
  D'akin tsaf tsaf very neat koh mace albarka se wani irin daddad'an qamshi ke tashi.
  Jamil ya zauna kan sofa tare da sauke idon sa kan wani qaramin frame dake ajiye kan bedside drawer photon Sophie da Saifuddeen ne a jikin frame d'in sunyi kyau sosai kmr masu gasar kyau dan se ka rasa gane shida ita wa yafi wani kyau duk da cewa ita baturiya ce amma ita kyaunta daban ne a cikin turawa.
  Jamil ya maida duban sa gun Saifuddeen wanda ke tsaye gun fridge yana tsiyaya musu lemu a cup yace"ni kuwa Saifuddeen har yanzu shiru banji inda aka kwana zancen ka da Sophie ba.
  Sai da Saifuddeen yazo ya zauna kusa dashi riqe da cup biyu a hannun shi d'auke da lemun da ya tsiyaya musu a ciki.
 ya miqa masa d'aya snn yakai d'aya a bakin sa ya kur6a kad'an snn a hankli ya sauke numfashi yace"jamil ban san ya zan tunkari Abba ba ina tsoro kar yaqi amincewa da zance na"
Jamil ya kur6a lemu snn yace"tunda umma na da sauqin kai kayi mata magana mana se ta tuntu6e shi ko Allah zai sa ayi nasara"
   Hum jamil kasan na gaya maka rnr Abba ya ganni da Sophie at my office,just ganin ta da yayi kan laps d'ina muna magana yayi ta fad'a har yace se na rabu da ita.
  Be bar maganar ba sbd abun ya masa zafi ya gayawa umma wacce na fahimci tun rnr da na kawo mata Sophie dmn ta gaishe ta naga alamar sam bata ra'ayin Sophie,to ta yaya kake ganin zan shawo kan wnn al'amarin?
 Jamil ya numfasa tare da ajiye cup d'in hannun sa kan stool d'inda ke ajiye a gaban su snn yace"ba mamaki idan Abba yaji aurenta zakayi ze amince kawai ka same shi ka gaya mishi"
  Saifuddeen yayi d'an guntun murmushi me nuna alamar da kmr wuya yace"hum jamil na san halin Abbana yana da tsauri sosai,shiyasa a duk lokacinda ya min zancen aure gabana har fad'uwa yake dan bansan ya zai d'auki abun ba idan nace masa ga wacce nake son in aura,bare idan yaji cewa ta gudo ne bada izinin iyayen ta ba matsalar zata fi yawa shiyasa kawai nake ce masa tukuna"
 Shiru jamil yayi a ransa yana jin kmr ya bawa Saifuddeen shawara ya haqura da Sophie kawai ya za6i d'aya daga cikin en matan da ke rubibi akan shi tunda dukkan su musulmai ne kuma suna da kyau dede gwargwado.
   Amma kuma sanin irin yanda suke qaunar juna da kuma sanin halin abokin nasa yasa dole zai bar shawarar a ranshi dmn fitar da ita wani babban abune da zai sa suyi fad'a.
  Yace"is she still at d hotel ko ka samar mata gida?
   Inafa ae bata so ka sani ita se nn d'in take so tazo ta zauna tare dani sam ta kasa fahimtar cewa mu da su ba d'aya bane,se da qyar na samu ta yarda zata ci gaba da zama a hotel d'in kafin na samar mana mafita,shine kullum se damuna take taji shiru wae ko dai tazo muje tare mu sami Abba.
  Ya qarashe mgnr ne d'auke da murmushi a fuskar sa sbd zancen Sophie wacce da ta san halin Abba da koda kuskure bazata fad'i haka ba.
 Shima dai Jamil murmushi yayi dan dukkan su sun san waye Abba snn qasar Hausa ne nn ba kmr qasar turawa ba,da akwai banbancin al'ada dama komai.
  Nan ya jingina bayan sa a jikin sofar da suke zaune ya lumshe ido a ransa yana jin dad'i shi kam Alhmdlh yasan inshaa Allah Zarah bazata masa wahalar samu ba.

Bayan mako Biyu da faruwar haka ne Nusaiba ta shigo d'akin umma wacce dawowar su daga islamiyya knn.
 Ta sami umma zaune kan bed tana qoqarin buga waya,taje ta zauna kusa da ita cikin yanayin damuwa.
Umma dake kallonta tace"lafiya Nusaiba me ya faru?
  Cikin yanayin damuwar da take d'auke dashi tace"umma wae meyasa yaya saif kwata kwata baya amsa gaisuwar zarah,ko yaushe cikin mata kallon tsana ko ta mishi wani laifin ne?
  Umma tace"ba laifin da ta mishi kin san halin yayanki se shi,tunda tazo gidan nn haka kawai ya d'auki karan tsana ya d'aura mata"
  Tace"umma halan baki gaya masa cewa Zarah er uwar mu bace"
   Umma tace"Abbanku ya gaya mishi se dai bana jin ya yarda ganin yake kmr er aiki ce,Abbanku ya fad'a ne kawai dan ya 6ata masa rai.
  Nusaiba tace"umma to shine kika barshi yana ta kallon ta a er aiki"
 Umma tace"Aa na gaya mishi ba er aiki bace kawai dai ra'ayin ta ne baya yi ya ganta baqauya"
  Tace"gaskiya umma yaya ya canja halin shi beyi ba,ni bana jin dad'in abunda yake mata, ae ko ba er uwar mu bace ya kamata a matsayin ta na musulma ya riqa amsa gaisuwar ta shikenan dan tana baqauya ya wani d'auki karan tsana ya d'aura mata se kace bada qauye akayi birni ba.
  Umma tace"to yayanki dai ne kisan irin mgnr da zaki fad'a akanshi"
  Cikin turo baki tace"to umma kuma meye laifina a nn ae gaskiya na fad'a"
  Bance ba gaskiya kika fad'a ba,kawai abinda nafi so dake shine ki tayani mu taya yayan naki da addu'a Allah ya sauya masa halin shi ya daina halayen sa da basu dace ba.
   Nusaiba tace "amin"
Kafin umma ke cewa"snn abu na biyu da nake so da ke shine duk wani abu da zarah tayi na qauyan ci wato a yanayin saka suturar ta,kwalliyar ta ko mgnr ta duk ki riqa lura cikin hikima da dabara kina gyara mata ta yanda zata fahimci abun ta riqa gyarawa da kanta.
   Nusaiba tace"Ae umma sosai zarah ke son ta zama er birni dan da kanta ma tace na riqa koya mata kwalliya gashi kuwa har ta fara iyawa,cikin ma muna zuwa islamiyya bama samun isasshen lakaci.
  Umma tace"yayi kyau amma kar ki ga wae ke ke koya mata abubuwa kizo ki rainata bayan kuwa yayarki ce ta girme ki har da shekara biyu.
  Nusaiba tace"haba umma ae kinsan bana da wnn halin"
  Umma tace hakane na nasani Allah ya miki albarka,idan kinje d'akin naku ki turo min yusra tazo inji me aka musu yau"
  Nusaiba tace"to"
snn ta tashi ta fita.

Da dare Abba ne zaune a falo shida umma dasu Nusaiba,zarah ce kawai bata gurin.
   Se fira suke tayi abinsu suna kallo,se can Abba ya lura cewa Zarah bata gurin,a nn ya kalli nusaiba yace"wae Nucy ina zarah ne?
  Nusaiba tace"Abba ae Zarah kunya take ji idan kana zaune a falo bata fitowa ta zauna ayi fira da ita.
  Abba yace"ikon Allah ai ni se yanzu na fahimci duk zaman da mukeyi falo bana ganin ta,je kira min ita tazo maza"
  Nan Nusaiba ta tashi da hanzarin ta taje d'akin su ta sami zarah zaune kan rug kusa da gefen gado ta lanqwashe qafafuwan ta tana duba littafan ta na islamiyya.
  Taje kai tsaye ta kama hannunta tare da fad'in"zo muje Abba ne ke kiranki"
  Da sauri zarah ta kalle ta tare da d'an ware idanuwan ta na alamar ni?
Nusaiba tace"of course tashi muje"
  Nan zarah ta tashi suka tafi wacce suna isa falo ta durqusa cike da ladabi ta gaida Abba.
  Cikin sakin fuska ya amsa snn yace"Zarah meyasa kowa na falo amma ke kin shige d'aki ke kad'ai baki fito anyi fira tare da ke ba?
  Cikin yanayin jin kunya tace"ba komai Baffa"
 Abba yace"ba wani ae Nusaiba ta gaya min wai kunya ta kikeji shiyasa ba kya zowo ayi fira dake ko"
 A hankli zarah ta d'ago idanun ta ta kalli nusaiba se kuma tayi saurin sauke idanun nata qasa ganin iskancin da nusaiba ta mata na kashe mata ido d'aya tana son sata dariya"
Abba dake kallon zarah yace"ki sani ni Abbanki ne kuma nn gidan ku ne ki saki jiki ki zama er gida kinji na gaya miki"
  A hankli zarah ta gyad'a masa kae yace"yauwa inace dai kina jin dad'in zaman gidan nn ba me takura ki?
 Nan ma gyad'a masa kai tayi alamar ba me takura ta.
   Yace"gud to tashi ku tafi kuyi shirin bacci dare yayi,Nusaiba d'auki yusra ku tafi"
  Nusaiba ta d'auki yusra da tayi bacci kan qafafun umma suka wuce.
  Nan Abba ya kalli umma yace"Zarah tace bamai takurata alhali kuma na fahimci duk lokacinda muke cin abinci saifuddeen baya son kallon inda zarah take kuma koda kuskure suka had'a ido se ya mata wani irin kallo na harara da saurin ta take d'auke idonta akan shi da alama tsoron sa ma take ji"
  Umma tace"nima haka na fahimta amma kar kace masa komai musa musu ido kawai dmn da haka da hakane se kaga abun ya juye sun fara shiri da junan su har soyayya tazo ta shiga tsakanin su.
  Abba yayi murmushi tare da fad'in"da nafi kowa farin ciki idan soyayya ta shiga tsakanin su dmn ina son Zarah ta kasance mtr saifuddeen Allah de ya yarda"
umma tace"Amin"
  Kafin suke tashi suka bar falon.

Su Zarah kuwa suna zuwa d'akin su Nusaiba ta shimfid'e yusra kan bed d'inta.
  Snn ta kalli zarah dake duqe tana tattara littafanta na islamiyya,bata bar ta qarasa ba taje ta kama hannun ta suka zauna kan bed tana kallon ta tace"Zarah meyasa baki gayawa Abba cewa yaya saif ko gaisuwar ki baya amsa ba se ma kallon banza da yake miki idan kika gaida shi.
   Murmushi kawai zarah tayi tare da fad'in ba abinda zan gaya ma Abba bane wnn nida kaina zanyi maganin abun.
  Daga haka ta tashi  taje ta qarasa tattara littafan ta ta saka a cikin jakar islamiyyar ta snn takai jakar inda ya dace.
  Nusaiba kuwa tun d'azu ta bita da kallo da d'an murmushi a fuskar ta kmr me son cewa wani abu se kuma bata ce komai ba ta tashi ta cire kayan jikinta ta fad'a bathroom.
  Bayan ta fito ne itama zarah taje tayi wanka.
  Da ta fito tayi shirin bacci cikin riga da wando soft silk,milk in colour snn ta saka hular baccin ta black ta net ta tura gashinta gabad'aya ciki kmr yanda taga Nusaiba nayi,dan Nusaiba ce ma ta bata hular sbd sun manta da suka je kasuwa basu siyo ba.
 Bed ta hau zata kwanta Nusaiba dake kishingid'e kan bed d'in riqe da littafin addu'o'i tace"zaki kwanta gashi kin manta baki sa abu d'aya ba"
 Nan Zarah ta shiga kallon jikinta tana son tuno mene ne taga dai har safa bata manta ba suna sanye a qafar ta,dan haka taga nusaiba nayi duk zata kwanta se ta saka socks a qafafuwan ta shine itama tace tana so Nusaiba ta bata,kuma sune ta cika mantawa dasu.
  Nan ta nuna ma Nusaiba qafafuwan ta tace"kin gani ban manta ba yau"
 Nusaiba tace"um um basu bane"
  Zarah tayi shiru d'an yatsan ta kan lips d'inta tana kallon silin tana son tuna me ne ne.
Can ta kalli Nusaiba da sauri tace"brush ne kuma da naje wanka nayi ban manta ba"
 Girgiza kanta nusaiba tayi alamar a'a snn ta dunqule en yatsunta na right hand tana moving da babban yatsan ta kan sauran tana zuwa da hannun nata a jikinta kmr me fesa turare.
  Zarah dake kallonta tayi rolling eyes d'inta tare da d'an buga kanta a hankli,snn ta tashi taje ta saka turaren ta dawo ta kwanta,a ranta tana mamakin su birni in za'a kwanta bacci wai har da turare ake sawa,hm lalle sudai komai nasu na daban ne shiyasa suke ganin mutumen qauye wani iri wanda ko fita anguwa ze yi ba lalle bane ma ya saka turaren.

Ranar Thursday ta kasance basa zuwa islamiyya.
 Guraren 11 suka shirya zasu je granny house,acan acan dasu sunyi kyau kayan su iri d'aya swiss less ne sky blue n baby pink yana cikin kayan sllr bara da Abba ya musu,sbd duk shekara tare yake musu d'inki iri d'aya.
   Zarah hijab ta saka iya guiwa klr wanda ya dace da kayanta kmr yanda Nusaiba ta za6ar mata dan kaf cikin kayanta bata da gyale ko d'aya.
 Nusaiba kam tafi ra'ayi da gyale shiyasa duk kayanta gyale sunfi yawa ko yanzu gyale ne ta yafa a jikinta,fuskar nn tata taci kwalliya kmr wacce zata je gasar kyau,haka ma zarah tayi er kwalliyar ta ta en birni da ta d'an fara iyawa kuma ba laifi tayi kyau dan Nusaiba ta d'an gyaggyara mata.
  Tare zasu je da yusra wacce ke sanye cikin riga da wando en kati masu kyau se d'an qaramin veil dai dai ita da aka yafa mata aka.
 Umma na Kitchen tana suyar meat roll wacce tana yin shi ne sbd a kaiwa hjy sbd tana son shi sosai.
 Suka je suka same ta acewar zasu tafi,umma ta saki baki tana kallon en matan nata se yaba kwalliyar tasu take,kana ta miqa musu meat roll d'inda ta d'ibarwa hjy a d'an wani small midi tray da akayi wrapping ta basu tace"to gashi ku kaiwa hjy ina gaida ta,a dawo lfy"
suka ce to kafin suke barin kitchen d'in.
 Sunzo zasu fita falo se ga saifuddeen ya shigo kad'an suci karo da zarah da sauri ta d'an ja baya snn a hankli ta sadda kanta qasa tana gaida shi.
  Harara ya dalla mata tare da kallon d'an space d'inda ta bashi,ya daka mata tsawa yace"ke dan kin raina ni wnn d'an space d'in ne ze ishe ni na wuce!da Allah ni matsa min er iska!ae ko zan ra6i mace in shafi jikinta ba irinki kucaka ba,an saba iskanci a qauye shine aka zo nn birni ma anayi.
 Ya nuna ta da yatsa yace"to bari kiji in gaya miki koda kuskure kika qara min irin haka marin ki kawai zanyi wlh! and u better leave this house tunda bana ubanki bane,very stupid!
  Zarah wacce tunda ya soma masifar shi tayi saurin matsa mishi snn da daga baya ta fita sum sum janye da hannun yusra qwallah tap a idonta dan sosai taji zafin kiran ta da yayi er iska,ita sam bata lura gurin da ta bashi baya isar shi wucewa ba,kai bare masifa ce kawai irin tashi ze wuce tsaf ba tare da ya shafe ta ba ma.
 Saifuddeen kuwa yana kai qarshen zancen shi yasa qafa ze fice Nusaiba tayi saurin tare shi tana kallon sa cikin marere ce fuska tace"haba yaya abunda kake yi be kamata ba Zarah fa er uwar.....da saurin sa ya dakatar da ita ta hanyar d'aga mata hannu ransa a 6ace yace"keep ur mouth shut!wlh kar in koma jin kinyi gigin alaqanta ni da ita and 6ace in daina ganin ki a nn very stupid!
  Qwallah ne suka ciko a idon Nusaiba jikinta a sanyaye ta ra6a ta gefen sa ta wuce.
  Saifuddeen ya bita da kallo yana fad'in"dan kin rainani ni zaki zo kisa a gaba kina gaya min abunda ya dace akan wata banza can wacce ba mamaki compassion ne kawai irin nasu Abba suka tsinto ta wani gun suka kawo a wani ce munada relative da ita.
  Mtsw yaja tsaki ya nufi hanyar kitchen sbd kiran da yaji umma ta mishi tana tambayar sa shida waye.
 Sai da ya shiga  kitchen d'in snn yake gaya mata shida Nusaiba ce dake son 6ata mishi rai kan wnn banzan yarinyar.
  Murmushi kawai umma tayi tare da girgiza kanta,a ranta tana addu'a Allah ya sauya mishi halin shi.
  Saifuddeen kuwa yace"wow meet roll kike yi umma"
  Kafin tace komai yasa hannu a cikin matsamin deep frayer ya d'auki d'aya dan shima yana son shi sosai.
  Ba shiri ya saki yana yarfi da hannu kmr qaramin yaro ya kalli umma yace"umma kice min it's very hot"
Murmushi umma tayi snn ta zari tissue ta saka mishi a ciki tana fad'in ae punishing d'inka ne nayi ka kami er qanwar ka se fad'a kake mata"
 Saifuddeen da ya kar6a yace"umma Nusaiban ce ta cika katsalandan ai banso na mata fad'a ba,bata ji ne to"
Nan yakai meat roll d'in a bakin sa yaci yace"uym umma yayi dad'i sosai a ajiye mana nida jamil kinsan shima yana son shi"
  Tace"to"
kafin yake tambayar ta ina Abba ya kira sa ne yace yana son ganin shi.
  Tace mishi yana d'akin sa.
  Nn ya bar kitchen d'in ya tafi sama zuwa d'akin Abba.
[4/22, 12:42 AM] Paexer: _Wednesday/07/02/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*



By
    *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*





*«»Page«» 6*
Nusaiba kuwa tana fita ta hango jamil ya tsaida zarah yana tambayar ta me aka mata take yin kuka.
 Ae kuwa se ta had'iye nata kukan snn ta qarasa gurin su ta d'an saki fuska ta gaida shi.
 Jamil kam be iya amsa gaisuwar ba se tambayar ta yayi  me aka ma zarah take yin kuka dan yaga zaran taqi tace dashi komai.
  Nusaiba tace"ba komai cin karo ta tashi yi ita da yaya saif shine ya mata fad'a bayan kuma bada gangan bane"
  Tsaki yayi cike da damuwa snn yace"na rasa me yake damun saifuddeen wlh hatta baquwa ma baya raga ma wane irin abu ne wnn mtsw....
Plz Zarah kiyi haquri kinji"
 Ya fad'a cikin muryar rarrashi yana me kallonta,
a hankli ta gyad'a masa kai alamar ba komai.
  Ya kalli Nusaiba yace"ina zaku je ne?
  Tace"Granny house zamu je"
  Yace"muje na sauke ku to"
  Tace"Aa wlh da ka barshi driver ze kaimu ka ganshi har ya fitar da mota mu kad'ai yake jira tun d'azu "
  Ta qarashe mgnr ne d'auke da d'an murmushi a fuskarta,shima jamil yayi murmushi yace"to a gaida hajiya"
   Tace"to zata ji"kafin suke wucewa"
  Ya bisu da kallo har sai da suka shiga mota suka wuce,snn ya sauke numfashi a hankali tare da ciro wayar sa a aljihu ya kira saifuddeen,bai d'aga kiran ba se qatse kiran da yayi hakan ya bashi cewa yana tareda Abba ne.
  Nan yaje ya jingina a jikin motar sa yana jiran fitowar sa.
  Jim kad'an se gashi ya fito yana cin meat roll har ya cinye wancan ya sake kar6o wasu biyu a gurin umma.
  Ya qaraso gun  jamil yana fad'in"ae na d'auka office kaje baka same ni ba ashe nn kazo"
  Jamil yace"ae kam office naje ban same ka ba nasan kana nn gida shine na biyoka"
  "To da ka biyo ni me zan maka?
  Ya fad'a yana ci gaba da cin meat roll d'inshi.
  Jamil yace" Sophie ce ta same ni office tana kuka wai jiya kunyi fad'a na baka haquri"
  D'an ta6e bakin sa yayi yace"Sophie ta kasa fahimta ne jamil,ita lallai fa se munje mun sami Abba snn ta gaji da zaman hotel gurina zata dawo da zama a nn gidan,kullum se ta dame ni da zancen nn tun ina lalla6ar ta har jiya ta ban haushi na mata fad'a.
  Jamil yace"saifuddeen dole ne ta dame ka ta fa bar iyayen ta cikin tashin hankli ta gudo ta bar su sbd kai"
  Yace"to ae nima cikin tashin hankali nake ban san ta ya zan tunkari Abba da zancen ba kullum cikin tunanin neman mafita nike ta bar ni inji da abu d'aya mana haba,ae tunda nace zan aure ta zan aure ta ko a 6oye ne.
  Jamil dake kallon sa yace"ko a 6oye ne?
  Of course dan na tabbatar ko na gayawa Abba bazai barni na aure ta ba gwanda kawai na aure ta a 6oye,se ka shirya next coming week zamu je a d'aura mana aure nida ita.
   Jamil yace"hum amma dai da wasa kake ko?
Hararar sa saifuddeen yayi yace"na ta6a maka wasa irin wnn"
 Jamil yace"baka ta6a ba amma baka gudun Abba yaji"
 Sai dai in kaine munafikin.
 Saifuddeen ya fad'a.
  Jamil yayi shiru yana me kallon saifuddeen yasan tabbas tunda ya fad'a ze aikata d'in yace"to bada ni ba ka nemi wani abokin nikam ina jin kunyar Abba rnr da asiri zai tonu bansan da wane ido zan kalle shi ba dan haka tun yanzu ba hannu na ba qafa ta.
  Kallon sa saifuddeen yayi tare da ta6e bakin sa yace"and so what ae ba dole sai da kai za'a d'aura auren ba,da kaina zan nemo dattijawan da zasu zama waliyan mu.
  Jamil yace"Allah taimaka,nidai a ina ka sami meat roll d'in nn se ci kake ka hana min"
  Yace"rnr auren mu da Sophie zaka ci har ka ture in kaje amma,a gidana na G.R.A da zan siya can za'ayi party Sophie ta tare a can.
  Da haka yasa qafa ze ficewar shi,jamil ya riqo shi da sauri yace"ina zaka je kabar ni da had'iyar yawu wae"
  Murmushi saifuddeen yayi tare da janye hannun jamil daga riqon da ya mishi yace"je gun umma tana kitchen ka kar6o mana namu gabad'aya"
  Yace"Aa muje tare dai"
 Da mamaki saifudden yace"au kaji min gidan baqon ka ne,Allah idan bazaka je ba ni tafiya ta zanyi inada abun yi patients na jira na.
 "Gud abun er rashin nasifa ce"jamil ya fad'a kana ya shiga ciki ya kar6o nashi kad'ai,ya fito yana ci ko gefen saifuddeen be kalla ba yaje ya shiga motar shi ya wuce.
  Saifuddeen dake kallon sa yayi murmushi tare da girgiza kansa snn shima yaje ya shiga tashi motar ya wuce,dan wanda yaci ma ya ishe shi.

Su zarah kuwa a cikin mota kafin su isa,sosai Nusaiba ta bata haquri,hkn yasa koda suka isa gidan hajiya fuskar su wasai kmr ba abunda ya faru.
 Wacce ake kira da hjy ta tarbe su da murna tana musu lale marhabin.
  Nan take kuma se tasha toka tace"ae na manta fushi ma nakeyi dake Nusaiba tunda kika dawo kaduna nake ta sauraren zuwan ki inji labarin ya kika baro mutan kaduna amma shiru har aka share sati biyu.
  Da sauri Nusaiba ta ajiye saqon da umma ta basu taje ta rungume hjy tana fad'in"haba dai hjy yi haquri kin san islamiyya muke zuwa shiyasa snn kinsan baquwa mukayi marmarinta akeyi kafin azo kanki"
 "au lallai wnn baquwar ina take ne in ganta dame ta fini"
  Hajiya ta fad'a tare da janye Nusaiba daga jikinta tana kallon zarah wacce tayi qasa da kanta d'auke da d'an murmushi a fuskarta tana wasa da en yatsun ta snn muryar ta a hnkli ta gaida ta cikin harshen fulatanci.
  Hajiya ta amsa tare da kama hannun ta suka zauna kan doguwar kujera ta dafa kanta tana kallon ta d'auke da murmushi  tace"zarahn inna,jonta ka inna muyi accinni amin ma,no inna 6andu mako dama ko?
 Zarah tace"eh owad'i dama sosai "
 Hjy tace"to Allah 6eddu dama"
 Zarah tace"Amin"
   Nusaiba dake kallon su tana jin abinda suke cewa amma maidawa ne kawai bata iyawa.
  Yusra dai kam komai bata ji se kallon su kawai da take fuskar ta a shagwa6e ta tafi jikin hjy wai se ta gaya mata me suke cewa,dan haka take da umma ba halin umma tayi waya da fulatanci tana kusa se ta ajiye mata rigima ita se an fassara mata me aka ce.
Hjy ta d'auke ta ta d'aura kan qafafuwan ta tace"to zan fassara miki amma meye alhaki na tunda mamar taki taqi ta koya miki nima bazan koya miki a banza ba"
  Yusra tace"kawai ki fad'a zan baki koma me kike so"
  Hjy tayi murmushi snn tace"to abunda muka fad'a shine:-ce mata nayi zaran inna,yanzu dai inna ta haqura ta bar mana ke,to ya kika baro inna jikin nata yayi sauqi?
  Se tace min"eh taji sauqi sosai"
  Nace to Allah ya qara bata lafiya
  Tace Amin.
 Shine kawai abunda muka ce ba gulmar ki akayi ba.
  Ta fad'i hakane tare da lakato hancin yusra,yusra tayi dariya tare da qara lafewa a jikinta.
  Zarah da Nusaiba kuwa murmushi kawai sukayi nn Nusaiba ta bawa hjy  saqon da umma ta basu,hjy ta kar6a washe da baki ta bud'e se sama umma albarka take dan har ranta tana jin dad'in yanda tayi sa'ar suruka kmr umma wacce ko yaushe cikin son kyautata mata take.

 Se guraren 8pm snn suka dawo gida.
  Sun samu saifuddeen zaune shi kad'ai a falo yana jiran fitowar umma daga kitchen da taje had'a mishi ruwan Lipton.
  Sau d'aya da suka kalle shi suka kauda kai suka wuce ko gaida shi basu yi ba da zarah har Nusaiba wacce ke rungume da yusra kan kafad'ar ta tayi bacci.
   Har suka shige saifuddeen kallon su yake yana mamakin wane irin klr raini ne su ganshi su wuce ba tare da sun gaida shi ba.
  Ya kalli umma ransa a 6ace wacce isowar ta knn ta fito daga kitchen yace"umma wae ni yaran nn zasu raina su shigo su wuce ba tare da sun gaida ni ba kuma sun ganni ba wai basu ganni ba.
  Umma dake kallon sa tace"suwa knn?
  Yace"Nusaiba da wnn banzar yarinyar mana bansan gidan uban wa suka fito a wnn lokacin ba"
  Zama umma tayi tare da ajiye mug d'inda ke hannunta tana kallon sa a natse tace"kayi haquri zan musu magana basu kyauta ba,amma kai  d'in ne ka cika masu tsauri saifuddeen,ita Zarah kwata kwata ma baka amsa gaisuwar ta"
   Saifuddeen yace"ko bana amsa gaisuwar ta shine dan tsabar raini zasu shigo su wuce ni ba tare da sun gaida ni ba kmr statue ne ni,har su kalle ni su kauda kae,to daga yau ko gaisuwar Nusaiba d'in bana so,tunda akan wnn banzar yarinyar zata d'auki yin fushi dani.
  Daga haka ya d'auki mug d'inda umma ta ajiye masa ya tashi ya fita ransa a 6ace.
  Umma da ta bisa da kallo ta girgiza kanta kana ta tashi ta nufi d'akin su Nusaiba.
  Fuskarta a d'aure take kallon su kowannen su yana qoqarin cire kayan jikin sa tace"kan me zaku shigo ku wuce ba tare da kun gaida yayanku ba"
   Dukkan su shiru sukayi.
Tace"daku nake magana ko bakwa jina ne kun min shiru"
  Nusaiba fuskar ta a d'aure tace"hln da mutum ne a falo mu bamu ga kowa ba"
  Umma tace"bana son shashan ci Nusaiba wnn ba tarbiyar da na baki bace tun wuri ki sauya dan bazan d'aukar miki wnn shashan cin ba.
  Ke kuma zarah shine har da biye mata ko!?
   Zarah da ko kad'an bata son fad'a kmr zatayi kuka tace"inna ko na gaida shi fa ba amsawa yake yi ba"
  Umma tace"Amma zarah ae na gaya miki ko baya amsawa kici gaba da gaida shi da sannu zae riqa amsawa kinji yi haquri"
   Zarah ta gyad'a kanta yayinda Nusaiba ke cewa"umma se kinji irin zaginta da yake yi a d'azun da zamu fita dan kawai sun tashi cin karo ita da shi har da cewa ta bar gidan nn tunda bana ubanta bane,dana masa magana kan ya daina hkn be dace ba se ya dawo kaina yana ta min masifa.
  Umma ta numfasa a ranta tana fad'in"ya ta iya da halin saifuddeen tunda gado yayi abun se addu'a"
  Snn a fili tace"Duk abun da yayi dai yayanku ne kuyi haquri kuci gaba da mishi biyaya kunji,zan mishi magana ya rage masifar nn da yake muku.
  Dukkan su gyad'a mata kai sukayi alamar sunji snn ta fita daga d'akin.
[4/22, 12:42 AM] Paexer: _Thursday/08/02/2018_ *«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»» Zarah gwandu*



*«»Page«» 7*
Washe gari Friday Abba,saifuddeen,jamil dukkan su suna cikin tsadadden farin yadi an dawo daga sllr juma'a suna zaune kan dinning suna cin abinci su duka har su umma dasu Nusaiba wa enda sun ci kwalliya tamkar zasu je gurin biki dan haka rayuwar gidan take,rnr Friday kwalliya suke yi sosai a kuma yi abinci na gani na fad'a iri iri daban daban sbd daraja ta wnn rnr.
   Ba kad'an ba hakan na matuqar birge jamil shiyasa duk rnr Friday a gidan yake yin lunch dan matar mahaifin shi kam sam ba ruwanta da wnn,tun rasuwar mahaifiyar shi tsawon shekaru biyu rabon da ayi abincin kirki a gidan kullum kusan abu d'aya ake yi wato jellof rice.
 Cin abincin suke amma gabad'aya hankalin jamil na kan Zarah,se kallon  ta yake tana cin abinci a natse haka duk wani motsi nata a natse take yin shi wacce tana yin hakane gudun kar tayi wani abun qauyanci,saifuddeen ya balbale ta da masifa dan ba qaramin aikin sa bane,shi kam jamil dake kallon ta se yaba irin natsuwar ta yake a ranshi yana fad'in ita dai komai nata a natse take yinshi,haqiqa irin klr macen da ya jima yana nema ce,duk da cewa baqauya ce amma tana da dama a cikin qauyawa sam baya ganin tana abubuwan qauyanci,ko dan yana sonta ne.....to koma dai yaya ne shidai yana sonta a haka,ba kuma zai yi sakaci ba garin kallon ruwa kwad'o ya masa qafa.
lallai yau idan suka kammala cin abincin nn zai yi qoqarin snr da ita abunda ke ranshi koma ya sami umma ya snr da ita,dmn shidai cikin sauri yake son ayi komai.
Sbd jamil mutum ne da Allah ya d'aura mishi lalurar son aure sosai amma rashin samun macen da ta dace dashi yasa beyi auren ba se yawaita azumi da yake gudun afkawa zina.
  Amma yanzu ji yake a ranshi kmr matsalar shi ta kusa zowa qarshe dmn zarah 100% ce a tsarin macen da yake so ftr shi Allah yasa Zarah ta so shi.
 Wayar sa ce ta soma ruri koda ya duba mahaifin sa ne,a mutunce ya d'aga kiran cike da ladabi kmr mahaifin nasa na kusa,dan jamil mutum ne mai girmama iyayen shi sosai.
  Bayan ya gama wayar ne yake snr da su Abba ze tafi Abban shi yana son ganin shi.
   Umma tace"ae da ka bari ka kammala cin abinci indai ba kiran gaggawa bane"
  Yace"Kd zamu tafi yanzun jikin kaka ce ya tashi"
   "Subhannallah ciwon sweetheart ya tashi yi sauri tashi muje"
Cewar saifuddeen wanda ya tashi da sauri riqe da tissue yana share bakin shi.
  Yayinda umma da Abba cikin jimami suka mata fatar samun sauqi tare da musu addu'ar Allah kiyaye hanya snn suka fita.
  Suna fita yusra tace"nidai mama tun yanzu idan kakar yaya jamil ta rasu zan biki kd gaisuwa"
  Dukkan su ido suka saki suna kallon yusra mama kuwa da hanzarin ta buge mata baki tace"ba bakin ki ba yusra kin kuwa san me kike fad'a!
  Kuka yusra ta fashe dashi ta sauka kan kujerar ta ta tafi jikin Abba.
  Abba ya d'auke ta ya d'aura kan jikin shi yana kallon ta yace"yusra kin kuwa san meye mutuwa,idan mutum ya tafi fa baya dawowa shikenan idan muka je kd baza ki qara zuwa gurin ta ba,dan ko kinje ma baza ki ganta ba ta tafi knn.
  Yusra tace"to ae kaka ta tsufa in ta mutu aljanna zata je,a islamiyya malamin mu ya gaya mana ba abinda yakai aljanna dad'i duk abinda kake so zaka samu a can.
  Abba yace"to shi malamin naku ce maki yayi idan mutum ya tsufa in ya mutum aljanna zai je?
  Aa yadai ce mana idan kana yawan alheri ma zaka shiga aljanna kuma kaka mai yawan alheri ce a kd in naje gidan ta duk abunda nake so baza ta hana min ba bani take kuma me yawa.
  Abba dake kallon ta yace"to ae yusra ba'a yiwa mutum ftr mutuwa dan haka kar ki koma kinji"
  Kai ta gyad'a masa alamar taji,yayinda umma tayi murmushi tare da girgiza kanta tace"su qurci dangin hauka wai ita fa ganin tayi duk akayi rasuwa se ince bazan je da ita gaisuwa ba shine yanzu tun wuri ta gaya min kar ma ince bazan je da ita ba.....ni daina kallona"
Umma ta fad'a tare da hararar yusra dake kallon ta.
  Ae kuwa da sauri yusra ta 6oye fuskarta gabad'aya cikin jikin Abba.
  Nusaiba da zarah kam murmushi kawai sukayi suna kallonta.
  Abba kuwa lalla6ar ta yayi ta tashi ta koma kan kujerar ta suka ci gaba da cin abinci.
  Bayan sun kammala ne Abba ya zari tissue yana share bakin sa yace da Nusaiba"Monday ne hutun ku ze qare ko Nusaiba?
  Tace"eh Abba dama ina son in gaya ma da akwai abubuwan da nike so a siya min kafin Monday"
 Kafin Abba yace komai umma tace"ke Nusaiba bana son iya yi,me zaki siya keda ba boarding school kike yi ba,sa'an nn ba hutun first term ba.
Ba abinda kk buqata u have everything,kwalin biro qwara biyar fa kawai kika ta6a a ciki,socks da akwai su sabbi dal har qafa uku,books ba kya ma da buqatar su,idan ma lokacin buqatar su yazo school ke baku to me kuma zaki siya.
 A d'an shagwa6e tace"Allah umma da akwai,sweets,chocolate biscuit,juice duk inada buqatar na zuwa school,kuma naga karon nn ba'a siya ba har yanzu.
   Umma tace"wnn ae yusra keda buqatar su ke kin wuce gurin baza a qara siya miki ba.
   Kmr zatayi kuka tace"haba dai umma"
  Kana ta kalli Abba alamar yace wani abu mana.
  Nan Abba ya kalli umma d'auke da murmushi yace"Maman yusra ki barta kawai ta rubuto duk abunda take buqata har na yusra d'in duk se a siyo"
  Umma tace"Alhj ka manta irin yanda  Nusaiba ke fama da period pain,in ta fara abun ba sauqi kai da kanka ma kace na kula duk wani zaqi ta daina sha,3months knn da farawar ta amma still ba sauqi har tea ma hkn nn take shan sa ba sugar"
  Shiru Abba yayi yana kallon umma snn ya kalli Nusaiba wacce tayi saurin sadda kanta qasa idon ta tap da qwallah ita bata so a hanata.
  Yace"kinji ko er baba mamanki ta fimu gaskiya amma za'a siyo miki kad'an se kisan yanda zaki riqa d'auka kina ci not any time ba....promise?
  Ya fad'a yana me kallonta,da sauri ta d'ago bakin ta a washe tace"eh Abba i promise u"
  Ta fad'i hakane tare da kai d'an yatsan ta akan nashi suka qulla alqawari kmr yanda ya buqata.
  Kana ya kalli zarah yace"kefa Zarah me kike so?
  Kanta qasa muryar ta a hankli tace"ba komai Baffa.
 Yace"da akwai mana tunda kin gama secondary ya kama ta kije high school mkrntr gaba da secondary,ko kinfi so mu wanke ki mu kaiki d'akin mijinki"
  Da sauri ta rufe fuskar ta da tafukan hannyen ta tace"Aa baffa ni bana son a min aure karatu nake so nayi"
  Yace"gud Zarah zakiyi karatu sosai kuwa tunda kina so,and u Nusaiba anjima da dare bayan sllr isha'i se ku shirya keda zarah da yusra muje kowa ya siyo abunda yake so.
  Godiya sukayi umma tace"au ni kuma na zama er gadin gida knn?
  Abba dake kallonta yayi murmushi snn yace"inafa na isa ganin nayi qwalama ce siyayyar yara amma idan zaki je se ki shirya muje mu dukan mu"
  Umma tace"Aa ni bana da buqatar komai da wasa nake"
  Murmushi Abba yayi snn ya fita acewar ze je gidan hjy suka mishi Allah kiyaye tare da miqa saqon gaisuwar su zuwa ga hajiya.
 
8:30pm saifuddeen ya dawo gidan be sami kowa a falo ba hakan yasa ya haura sama zuwa d'akin umma ya mata knocking ta fito wacce tana fitowa tace"Aa saifuddeen kaine kun dawo?
  Yace"eh umma amma ni kad'ai na dawo"
  Umma tace"subhanallah knn jikin sosai ya tashi"
   Aa da sauqi sosai fa asthmar ta ce ta tashi kuma ta d'an kwanta mata.
  Umma tace"to Allah ya qara sauqi"
  Yace"amin"
Snn yace"umma abincin mutum biyu nake so za'a samu?
  Yayi mgnr ne tare da d'an sosa bayan kanshi hakan yasa umma ta kalle shi da kyau snn tace"kaida waye?
  Yace"nida wani baqo na ne"
 Cikin kallon tuhuma tace"hm kaida Sophie dai ko?
 Cikin fuskewa yace"haba umma wace Sophien kuma abokina dai.
   Gaban rigar sa ta nuna tace"wnn abun fa a ina ka same shi ko abokin naka ne ya maka"
  Kallon gaban rigar tashi yayi,kiss💋ne rand'am a jikin rigar wato fararen kayan shi da still yake sanye dasu bai sauya ba duk jan jan bakin Sophie ya 6ata su .
  Ransa a d'an 6ace ya lumshe idon shi kana ya ware su akan umma yace"oh umma me kuma yakai idonki a can plz,Sophie ce ta min kuma bawai da wata manufa ba"
  Rai 6ace Umma tace"in banda iskanci da wace manufar ma to zata maka kiss iye ita mtr ka ce ko me! ta nuna shi da yatsa tace bari kaji in gaya maka saifuddeen muddin kace zaka biyewa lalaci irin na turawa to wlh zamu sa qafar wando d'aya nida kai,sam bazan yarje maka wnn iskancin ba tun wuri ka sauya...karatu a England hauka ne ae ga jamil nan naga tare kukayi karatun amma shi sam baya iskancin da kakeyi.
 Cikin yanayin damuwa Saifuddeen yace"oh Allah! umma wlh abinda kuke tunani bashi bane,nifa ba yaro bane nasan abunda nakeyi"
 Umma tace"shikenan tunda kai ba yaro bane kaci gaba da yin abunda kake in dai dai ne,and 6ace in daina ganin ka a nn kafin Abban ka ya dawo ya ganka da wnn abun kunyar a rigar ka.
 Kallon umma kawai saifuddeen yayi ba tare da yace komai ba ya wuce kmr yanda tace.
  Tabi sa da kallo har ya fita a ranta se addu'a take mishi Allah ya shirye shi.
  Tana jin lokacinda yaja motar sa ya fita daga gidan,ta girgiza kanta kawai snn ta koma daga ciki.

Washe gari da safe guraren qarfe goma da mintina su zarah suka dawo daga islamiyya sbd dama da safe 8 suke zuwa su dawo by 10.
 Da shigar su d'aki Nusaiba ko hijab bata iya cirewa ba ta fad'a kan bed dafe da marar ta dake mata masifar ciwo tana kuka.
 Se sannu Zarah ke mata wacce ta ajiye jakar islamiyyar ta snn ta cire hijab ta linke tasa a wardrobe da niyyar zata je ta snr da umma halin da nusaiba ke ciki se ga umma ta shigo d'akin.
  Kafin tace komai idonta ya sauka kan Nusaiba dake kwance kan bed tana juyi a hnkli sautin kukan ta na fita kad'an kad'an.
   Sai da ta girgiza kanta snn taje ta zauna kusa da ita tana kallonta tace"jiya da kuka dawo shopping kinsha alawa da yawa ko,alqawarin da kikayiwa Abbanki knn?
  Cikin muryar kuka tace"Allah umma ni kwata kwata bansha ba pringles kawai naci ki tamvayi zarah ma kiji.
  Umma tace"to naji tashi kisha magani ki kuma yi gaggawar kimtsa kanki kinsan yanda abun ke zo maki.
   Ba musu ta tashi zaune  tare da cire hijab d'in jikinta,umma ta bud'e bedside drawer ta ciro magani,da kwai ruwa ajiye cikin jug kan bedside drawer d'in ta 6alle mata maganin tare da tsiyaya mata ruwa a cup ta bata tasha snn ta miqe da qyar tana tafiya sannu a hankli har ta shiga bathroom.
  Umma da ta bita da ido ta maida duban ta gun Zarah tace mata"ina ce dai ke kam al'adan ki baya baki wahala kmr haka ko?
 Sai da Zarah ta sadda kanta qasa snn tace"yana min amma ba sosai ba kad'an kad'an"
  Umma tace"to Allah sauwaqe muje ki kaiwa yayanku breakfast tun d'azu nayi jiran shigowar sa ko ze shigo amma naji shiru gashi jiya yace min yana da baqo.
  Nan suka fita suka bar yusra na cire uniform d'in jikinta.
  Koda Zarah ta tafi 6angaren Saifuddeen se sallama take tayi har da knocking amma shiru ba amsa se kid'an music dake fitowa a hnkli.
  Kmr ta juya se kuma ta kae hannun ta kmr da tsoro ta 6ird'a handle d'in qofar,se gambun ya bud'e a hnkli ta shiga had'e da sallama a bakinta"
 Bata qarasa sallamar ba da sauri tasa hannu ta rufe bakinta,ta kuma bud'e ido a tsorace ganin Sophie hakan nn ba komai a jikinta daga ita se d'an pant sun fito daga bathroom ita da Saifuddeen tana rungume a jikin shi,yana sanye da d'an guntun wandon da da ya manne sosai a jikin shi hannun Sophie gabad'aya akan wandon nashi tana shafa shi,yayinda shi kuma hannun sa ke kan qirjin ta yana shafata snn bakin su a had'e gam suna kissing d'in juna.
  Zarah da tayi mugun gani ihu ta saki tare da sake breakfast d'in da umma ta aiko ta dashi dake cikin basket ta fita aguje.
[4/22, 12:42 AM] Paexer: _Saturday/10/02/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*







By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 9*
Yusra ce ta shigo d'akin bata qarasa gurin su ba se tsaye kawai tayi tana kallon su kmr yanda umma ke kallonta,zarah dake rungume jikin umma taji alamun shigowar mutum se dai bata san waye ba nn ta janye jikinta a hankli daga jikin umma,ta juyo ta kalli yusra bata ce mata komai ba se tashi tayi ta fita daga d'akin,yusra ta bita da kallo har ta fita snn ta qarasa gun umma tace"umma halan me Anti zarah da anty nucy suka ma yaya da ya dake su?
   Umma tace"ya dake su?
  Yusra tace"Eh a gabana ya mari anti nucy gata can ma se kuka take tayi.
  "oh Allah me kuma Nusaiba ta mishi da zai mare ta muje in ganta"
  Umma ta fad'a tare da jan hannun yusra suka je d'akin su Nusaiba.
  Kan bed ta zauna tana kallon Nusaiba dake kwance kan bed tana kuka kuncen ta duk yatsun saif ne da suka kwanta.
  A hnkli umma ta shafi kuncen nata tace"laifin me kika masa?
  Cikin kuka Nusaiba tace"ba abinda na mishi,wai ya d'auka ko nice naje 6angaren shi shine ina fitowa daga bathroom se jin saukar mari nayi bansan hawa ba bansan sauka ba.
 Umma da tayi shiru tana kallonta tace"Ayya sorry kinji k'yale shi,kana takai hannun ta a hankli tana share mata hawaye.

Saifuddeen kuwa yana isa kd kai tsaye gidan Abban kd ya nufa ginin gidan sak irin nasu dake kano komai iri d'aya.
  Zaune yake a falo yana jiran fitowar hjyr gidan da ya aika mai akin gidan ta kira mishi ita.
  Jim kad'an se gata ta fito wacce kallo d'aya zaka mata kasan cewa jini d'aya ce da umma wato yayar umma ce uwar su d'aya uban su d'aya.
  A natse Saifuddeen ya gaida ta ta amsa tare da zama kusa dashi tana kallon sa da kulawa ganin irin yanda yake cikin damuwa sosai,
tace"saifudddeen lafiya me yake faruwa?
  Kallonta yayi d'auke da idanuwan sa da still suke jajur yace"sosai ina cikin damuwa umma,Abba nake son gani ko yana nn?
 Cikin yanayin damuwa ta numfasa snn tace"eh yana nn bari na kira maka shi"
  Nan ta tashi jiki sa6ule ta haura sama zuwa d'akin shi.
  Ba 6ata lokaci se gashi ya fito,Saifuddeen ya zame qasa ya zauna tare da gaida shi.
  Abban kd da sak kmr sa d'aya da Abba tamkar an tsaga kara,ya zauna a natse tare da amsa gaisuwar da Saifuddeen ya mishi,snn da kulawa yace"ina jinka Saifuddeen gaya min meye damuwar ka Maman Salma ta gaya min kana cikin damuwa"
  Saifuddeen kansa qasa yace"eh Abba wlh nayiwa Abba laifi ne ya yanke min tsastsauran hukunci shine nake son dan Allah ka taimaka min ka bashi haquri ya janye min nayi alqawarin zan kiyaye bazan sake aikata abunda na aikata ba.
  Abban kd dake kallon shi ya numfasa snn yace"me ka mishi tukun inji?
  Saifuddeen bai 6oye mishi komai ba ya gaya mishi duk abinda ya faru.
   Abban kd ya jinjina kansa yace"cabd'i lallai Saifuddeen karatun da ka koyo a England knn,to ka sani sam baka kyauta ba ka kuma d'auko abunda kaf dangin mu ba wanda ya ta6a aikata hakan,kuma hukuncin da Abbanka ya yanke maka shine dai dai, ba kai ba wnn arniyar snn auren ka da zarah ba fashi dmn baza mu zuba maka ido ka kunyata mu a idon duniya ba.
  Saifuddeen ya kalle sa kmr zai yi kuka muryar sa na rawa yace"Abba wlh da Aure nake son Sophie na jima ina son snr da Abba amma kullum ina tsoro kar yace bazai amince ba"
  Abban kd dake kallon sa yace"Saifuddeen dukkan mu nida Abbanka a England mukayi krt amma ba wanda ya d'auko baturiya yace ita zai aura,asalima iyayen mu ne da kansu suka za6a mana matan da muka aura,wanda gashi yanzu Alhmdlh har kullum cikin farin ciki muke da godiyar Allah kan za6in da suka mana,dan haka ina son kayi haquri ka ajiye auren wnn baturiyar gefe ka amince da za6in Abbanka dmn shine mafi alhairi a gare ka.
   Shiru Saifuddeen yayi idanun sa suka qara yin jajur suka ciko tap da qwallah,dama yasan da kmr wuya ya samu auren Sophie da amincewar su, shiyasa kawai ya tsara ya aureta a 6oye ba tare da sun sani ba se gashi kwana d'ayan da tazo ta mishi ya lallata komai,yanzu ba yanda zai yi tunda Abba ya mai iyaka da ita.
 Kana cikin muryar kuka yace"Abba naji zan fita harakar Sophie amma dan Allah a bar ni na za6o wacce zan aura da kaina"
   Shiru Abban kd yayi lokaci me tsawo se can yace"shikenan gobe zanje kano na sami Abban naka muyi magana"
  Godiya Saifuddeen ya mishi snn ya tashi ya fita.
  Bai zarce koina ba se gidan kakar jamil,ya faka motar shi a gefen gate d'in gidan snn ya ciro wayar sa a aljihu ya kira jamil.
  Koda jamil ya fito ya leqa motar ya ganshi ya had'e kanshi da sitarin motar,
nn ya zagaya ya bud'e motar ya shiga ya zauna yana  mai kallon shi yace"lafiya dai Saifuddeen baka ta6a zowa ka tsaya a qofar gida ba se yau"
  A hnkli Saifuddeen ya d'ago yana kallon sa yace"ina cikin damuwa ne bana son in shiga ya jikin kaka"
  Jamil dake kallon yanda idanun Saifuddeen sukayi jajur yace"taji sauqi sosai amma me yake damunka ban ta6a ganin ka a cikin irin wnn yanayin ba se yau.
  Saifuddeen yace"jamil Abba ne ya min iyaka da Sophie yace baya so ya sake gani na da ita har abada,a waya ko a bayan idon sa na sake kula ta bazai ta6a yafe min ba.
  Cikin damuwa Jamil yace"subhanallah me ya faru har hakan ta faru ko zuwa kuka yi kaida ita da niyar mishi magana?
  No,it's all my fault da na amincewa Sophie kan matsa min da tayi ita tana son se taje tamin kwana d'aya,byn naje da ita se gashi da safe umma ta aiko wnn banzar yarinyar ta kawo min breakfast ta shigo mana d'aki haka kawai ba sallama ba knocking shine ta ganmu taje ta snr bansan jakar ina ce ba ita.
  Jamil da ya fahimci Zarah yake nufi ya numfasa yace"kayi haquri amma yanzu ya za'ayi and ita Sophie meyasa ta nemi hkn byn ka snr da ita cewa this coming week zakuyi aure.
 Bari kawai ta mugun 6ata min rai,kawai naje in ganta tace se ta bini yanzu gashi ta 6arar mana da komai snn tasa Abba ya min mummunan hukuncin da yake neman had'a aure na da wnn banzar yarinyar bagidajiya er qauye da bansan ta yaya ma za'ayi na iya rayuwa da ita ba"
  Da kmr rashin fahimta jamil ya kalle sa yace"ka..min..bayani...ban...gane ba,wa..ce ce Abba ke shirin had'a ka da ita ba dai Zarah ba ko?
  Rai 6ace Saifuddeen yace"ita man wacce nake tunanin ko tsinto ta akayi,wae ashe dama can Abba ya kawo ta ne da niyyar had'a mu aure,kaji min!abu se kace wasan kwaikwayo,kai ko a wasan kwaikwayo ma wnn sam beyi ba,it doesn't making sense a had'a ni da wnn,na rasa me yake damun Abba da yayi wnn tunanin,da ya ta6a accident se ince ko ya sami matsala ne a qwaqwalwar sa ba'a sani ba but...se yayi shiru yana mai kallon jamil da ya dafe kansa sbd mugun sara masa da yayi.
  A hankali ya dafa shi yana kallon sa yace"jamil?
  Da qyar jamil ya iya d'ago kanshi idanun sa har sun canza kala zuwa launin ja ya kama hannuwan saifudden cikin yanayin begging lips d'insa na rawa yace"Ni ina sonta Saif dan Allah ka taimaka min Abba ya bani auren ta tunda kai baka so"
   A hnkli Saifuddeen ya zare hannayen sa daga riqon da jamil ya mishi yana kallon jamil kmr yaga wani zautacce yace"jamil wae ka fahimce wacce nake nufi kuwa?
 Jiki sa6ule jamil yace"na fahimce ka mana wnn baquwar da kukayi zarah wacce suke fita tare da Nusaiba"
  "Ya salam"
Saifuddeen ya fad'a yana mai kallon jamil cike da mamaki yace"me ka gani a tare da wnn bagidajiyar da har zaka sota jamil?
  Jamil yace"komai na gani a tare da ita,ba abinda ta rasa a tsarin irin macen da nake so na aura.
  Saifuddeen ya leqa fuskar jamil d'in snn yace"amma dai da wasa kake min ko?
  Wlh da gaske nake gaya maka saif tun rnr da na fara d'aura idona a kanta naji ta kwanta min arai,har ma jiya na yanke shawarar muna kammala cin abinci zan snr da umma se gashi Abba ya kirani jikin kaka ya tashi ba dan haka ba da na gaya mata wlh.
  A sanyaye  Saifuddeen ya numfasa ganin yanda jamil ke magana seriously idanun sa tap da qwallah se duk gabad'aya ya cika da mamakin jamil d'in.
 Girgiza kansa kawai yayi snn yace da jamil"kar ka damu tunda har kana sonta kmr ka same ta ne dmn gobe ma Abban kd zai je kano ya roqa min Abba ya barni na za6i wacce zan aura da kaina.
  Jamil dake kallon sa ya sauke ajiyar zuciya a hnkli snn yace"nagode sosai Saifuddeen and idan har Abba ya amince ka kawo macen da kake so,plz ka za6i salima dmn a cikin en matan da ke son ka duk tafi su sonka tsakani da Allah snn mace ce har mace bata da wani abu da d'a namiji ze kalla yace baya so son kowa ce qin wanda ya rasa.
  A hankli Saifuddeen ya girgiza kansa yace"ni Sophie kawai zan iya rayuwa da ita a matsayin mata ta kuma inshaa zan aure ta da izinin Abba bama a 6oye ba.
  Jamil yace"ta yaya saif?
  Yace"jamil kafi kowa sanin irin qaunar da Sophie ke min,akaina ta gudo ta baro iyayen ta snn aikaina zata iya musulunta dmn ta aure ni,da haka ne nake tunanin idan ta musulunta Abba ze barni na aure ta.
 Jamil yace"hakane tabbas Sophie ba abinda baza ta iya ba akan ka ina maka fatan alhairi Allah yasa ayi nasara"
 "Amin"
Cewar Saifuddeen.
[4/22, 12:42 AM] Paexer: _Friday/09/02/2018_ *«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*






By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 8*
 Umma na falo zata haura sama se ganin Zarah tayi aguje tazo duk a tsorace jikinta se rawa yake.
 Da sauri umma ta riqo ta tace"lafiya Zarah me yake faruwa?
  Komai zarah bata iya ce ma umma ba,se janye jikinta tayi da sauri zata haura sama zuwa d'akin su se ga Abba ya sauko da saurin sa wanda ya fito knn daga d'akin sa ya hango lokacin da zarah ta shigo aguje.
 Bai bar ta wuce ba yace"mene ne zarah lafiya a ina kika fito haka?
  Kuka kawai ta fashe masa dashi snn ta tafi aguje zuwa d'akin su.
  Abba ya kalli umma yace"a ina ta fito?
  Umma tace"6angaren Saifuddeen na aike ta ta kai masa breakfast shine ta dawo haka.
  6angaren Saifuddeen?Abba ya tambaya.
  Se dai kafin ma umma ta bashi amsa tuni ya fita da saurin sa ya nufi 6angaren Saifuddeen.
 Shigar sa d'akin yayi dai dai da lokacinda Saifuddeen ya rufawa Sophie white bedsheets a jikinta yana ce mata tayi sauri taje ta 6uya a bathroom.
Cak Abba ya tsaya cike da tsananin mamaki yana kallon su wanda duk a tunanin sa ko Saifuddeen ya balbali zarah da masifar sa ne dan an aiko ta 6angaren shi se ya samu abunda be ta6a tsammani ba.
  Ransa a mugun 6ace ya nufo su,Sophie ta fice da sauri jikinta na rawa ta shige bathroom ta rufe.
  Tas!tas!!taji saukar marikan da Abba ya yiwa Saifuddeen wanda har sai da yayi taga taga kmr ze fad'i.
Abba ya nuna shi jikinsa na wani irin rawa sbd tsananin 6acin rai yace"maza ka sameni a falo yanzun nn!
  Yana gama fad'ar haka ya fita.
  Sophie na jin fitar sa ta fito da sauri tazo gun Saifuddeen idanuwan ta tap da qwallah take shafa kumatun sa da sukayi jajur duk yatsun Abba sun kwanta akai.
 A fusace Saifuddeen ya ture ta daga jikinsa ya nufi wardrobe ta biyo shi da sauri,ya dakar mata tsawa kan kar ta kuskura ta ta6a shi.
  Kuka Sophie ta fashe dashi ta zube qasa tana ta bashi haquri be kulata ba har ya ciro tufafin sa ya saka,zai fita har yakai bakin qofa ya tsaya ba tare da ya kalle ta ba yace"u better leave this house b4 i came back.
  Daga haka ya fita ba tare da ya jira me zata ce ba.
  Koda yaje 6angaren su umma be sami Abba a falo ba kai tsaye ya haura sama zuwa d'akin su Nusaiba,Nusaiba ta fito daga bathroom knn se saukar gigitaccen mari taji a fuskarta,ba shiri ta dafe kuncen ta,ta saki ido cikin mugun tsorata tana dubin a ina marin ya fito,se ganin Saifuddeen tayi a gabanta wanda shine ya mare ta d'in,ransa a 6ace yace"uban me yakai ki 6angare na da har zaki shigar min d'aki without permission iye!
  Da sauri ta girgiza kanta cikin kuka tace"wlh Allah bani bace ni ko lafiya ma bana da"
  Yace"wat! bake bace u mean wnn banzan yarinyar ce taje 6angarena ta kuma shigar min d'aki haka kawai,lallai yau zanyi maganin ta wlh!
  Ina take gaya min!?
 Ya tambayi Nusaiba tace"ni ban sani ba"
  Ya tambayi yusra tace mishi umma tazo ta tafi da ita.
  Fuuu! ya fita a fusace ya nufi d'akin umma.
  Da shigar sa ya sami Abba a d'akin yana snr da umma abin baqin cikin da ya gane ma idon sa.
 kallon da Abba ya mai yasa yayi saurin sadda kansa qasa,snn cikin kakkausar murya Abba yace"falo nace kaje ka same ni dan uwar ka ba a nn ba very stupid get out! in daina ganin ka a nn shasha sha kawai mara kunya fitsararre.
  Sum sum Saifuddeen ya fita gabad'aya ransa a dagule ko kad'an baiji dad'in faruwar hakan ba wanda yanzu bai san wane iri hukunci ne Abba zai yanke akanshi ba.
  A hnkli yake tafiya har Abba yazo ya wuce shi yaje ya zauna kan doguwar kujera,kana Saifuddeen ya qarasa ya zauna qasa wanda gabad'aya jikinsa a sa6ule yake,tsoron sa d'aya kar Abba ya masa iyaka da Sophie.
  Kansa qasa yana sauraren me Abba zai ce dashi,Abba be ce dashi komai ba har se da umma ta qaraso ta zauna.
  A hnkli Saifuddeen ya d'ago ya kalle ta ya d'an marairaice fuskar sa alamar ta taimaka ta bawa Abba haquri plz.
  Shaye da toka umma ta dallah mai uwar harara ae kuwa yayi qasa da kanshi muryar sa a hnkli yace"Abba dan Allah kayi haquri"
  Muryar Abba daji kasan sosai ransa a 6ace yake yace"bari kaji in gaya maka Saifuddeen wlh kaji na rantse kar in sake ganin ka da wnn yarinyar har abada,a waya ko a bayan idona ka sake kula ta bazan ta6a yafe maka ba!.
   Take Saifuddeen ya runtse idanun sa gam lokaci d'aya jijiyoyin kansa duk suka taso yana jin kansa cikin wani irin yanayin dashi kansa be san ma yazai fisalta ba dmn ko mutuwar Sophie yaji baya jin ze sami kansa a yanayin da ya tsinci kansa a yanzu.
    Kana ya bud'e idanun sa tare da had'e tafukan hannayen sa yana kallon Abba muryar sa na rawa yace"Abba dan girman Allah kayi haquri ka janye min wlh bazan iya ba"
    Abba ya kalle sa da kmr mamaki yace"baza ka iya ba!to kasani wnn d'in ko zaka iya ko baza ka iya ba dole se ka kar6e shi umarni ne,sati mai zuwa rnr juma'a zan d'aura auren ka da zarah!.
  Kamar saukar guduma Saifuddeen yaji mgnr ya miqe zumbur yana kallon Abba wanda yana gama fad'ar mgnr ya ficewar shi ya haura sama.
  A rud'e ya rarrafa gurin umma dake qoqarin tashi ya kama hannayen ta yace"umma na shiga uku wace ce kuma zarah!?
  Umma tace"Zarah dai da ka sani baquwar gidan nn"
   Saifuddeen da sam bai kawo ita Abba ke nufi ba,ba shiri ya saki hannun umma tare da girgiza kansa snn cikin wata irin murya da shi kansa bai san yana da ita ba yace"never!wlh nasan Abba ya fad'a ne kawai sbd 6acin randa na saka shi a ciki"
ya tashi a kid'ime kmr wani zautacce yace"umma bari naje na same shi na bashi haquri,na amince zanyi rayuwa ba Sophie kmr yanda yake so bazan sake kulata ba har se da izinin shi.
  Tashi umma tayi tare da riqo hannun sa tana kallon sa lokaci d'aya duk ya haukace.
  Tace"Saifuddeen sam 6acin randa kasa Abban ka a ciki ba shine dalilin da yasa yace zai had'a auren ka da zarah ba,asalin zuwan Zarah a gidan nn dmn ya had'a auren ku ne amma a niyar sa se tayi karatu,wanda yanzu ya janyo auren kusa ne sbd ya fahimci kana neman ka kunyata mu ne a idon duniya!.
  Da sauri ya girgiza kansa lips d'insa na rawa cike da son yace wani abu,umma tayi saurin dakatar da shi ta hanyar d'aga masa hannu tace"bazan saurare ka ba Saifuddeen,kasan halin Abbanka sarai idan ya fad'i magana bazai ta6a canzawa ba.
 Tana gama fad'ar haka ta wuce,ya bita da kallo idanuwan sa sunyi jajur a ransa yana fad'in"wnn karon zai canza dmn bazai ta6a yiyu na aure ta ba wlh"
 Daga haka ya bar 6angaren bai zarce koina ba se 6angaren shi,be sami Sophie a 6angaren ba ta tafi kmr yanda yace dmn sosai tana gudun zuciyar shi shi kansa ya sani shiyasa yake matuqar sonta.
  Sakwaf yaje ya zauna kan bed ya sauke idon sa akan wata farar kyanwa wacce ba d'igon komai a jikinta ko inan ta duk fari ne du6u du6ul da ita er qarama ta dunqule guri d'aya se bacci take tayi abunta.
  Kyanwar Sophie ce wacce take matuqar ji da ita idan tana bacci sam bata son wani abun da zai tashe ta shiyasa bata je da ita ba ta barta.
   Saifudddeen dake kallonta ya maida duban sa gun hoton su dake ajiye kan bedside drawer yana kallon fuskar Sophie gabad'aya yau ta mugun 6ata mishi rai dan kusan duk ita taja komai,dmn sam ba'a son ranshi yazo da ita gidan ba se dan matsa mishin da tayi kan lallai ita se tazo ta mishi ko kwana d'aya ne,yanzu ga abunda kwana d'ayan yaja musu,take kuma takaicin sa ya koma kan zarah a lokacinda ya maida duban sa gun basket d'inda ta 6arar,ba kad'an ba yaso ya samu damar damqar ta ya mata hukuncin da ko a mafarki baza ta sake fatar ta ganta a gidan nn ba bare hanyar 6angaren shi.
  Kana yayi wani irin murmushi me ciwon gaske wai shi Abba ze had'a auren sa da ita,mummunan mafarki knn dan muddin Abba yace dagaske yake zai had'a auren sa da ita se dai a nemi yarinyar a rasa.
 Hm Kaiyh! it's better ya gaggauta zuwa ya samu Abban Kd dmn ya bawa Abba haquri.
  Abban Kd
cewa da Abokin tawaicin Abba wato en biyu ne shida Abba,Shine Hassan Abba kuma Hussain.
 Nan ba 6ata lokaci Saifuddeen ya d'auki makullin motar sa ya tafi se zuwa kd.

Umma kuma koda ta koma d'akin ta ta sami Abba zaune kan sofa zarah na zaune qasa a gaban shi ta sadda kanta qasa yana snr da ita auren su da yake son zai had'a ita da Saifuddeen wanda yana magana ne cikin natsuwa da kuma neman amincewar ta.
  Ganin bata iya ce masa komai ba ya kalli umma yace"kiyi magana da ita idan ta amince to idan kuma bata amince ba kar ki mata dole"
  Nan ya tashi ya fita umma ta zauna kan sofa d'in tana kallon zarah da still kanta a qasa
tace"Zarah meyasa Alhj na maki magana kikayi shiru ko ba kya son auren ne?
  Da sauri zarah ta d'ago idanun ta dake cike tap da qwallah tace"eh inna"
  "Oh my God!"
Umma ta fad'a snn a hnkli ta kama hannun Zarah ta zaunar da ita kusa da ita tana kallon ta muryar ta a hankli tace"meyasa zarah?
  Zarah tace"inna ni gaskiya bazan iya auren me irin halin shi ba"
  Umma dake kallon ta,ta numfasa tace"Zarah kiyi haquri ki amince da buqatar Alhj sanin kanki ne bai cancanci kice masa a'a ba"
  Zarah ta kalli umma cikin muryar kuka tace"na sani inna shiyasa ma na kasa ce masa komai amma a gaskiya bana son auren haka shima nasan baya so komai zai iya faruwa idan aka had'a aure na dashi.
  Umma tace"ba abinda zai faru se alheri Zarah"
  Hawaye ne suka silalo akan kumatun zarah dake kallon umma tace"nidai inna dan Allah a'a,tare fa na gansu shida wata meyasa baza a had'a shi da ita ba"
  Umma tace"Zarah Saifuddeen da wnn baturiyar sam auren su bazai ta6a yiyu ba,ke Alhj ke son Saifuddeen ya aura asali ma shine ya tura ni musamman rimin dako naje nazo dake garin nn sbd yana son had'a auren ku,kinga kuwa idan baki amince ba bazai ji dad'i ba, haka nima bazan ji dad'i ba,inna ma baza taji dad'i ba sbd tasan da zancen tun rnr da naje nazo dake.
  Shiru zarah tayi tana kallon umma d'auke da hawayen da ke kan fuskar ta bata share ba,tayi qasa da idanun ta snn tace"inna d'an iska ne fa bashi da hali nagari me yasa kuke so na aure shi"
 Da kulawa umma ta kalle ta snn tace"Zarah kiyi haquri idan kika aure sa kmr kinyi jahadi ne,inshaa Allah zai rabu da duk wasu banzan d'abi'un da yakeyi kinji"
A hnkli zarah ta gyad'a mata kai tare da saurin share hawayen da suka zubo mata.
  Umma taja ta zuwa jikinta se qara rarrashin ta take cike da tunani fal a ranta,haqiqa ita kanta ba son auren take ba sbd wani dalili da yasa ta hango abubuwa da dama a cikin auren amma tunda Abba yana so ba yanda zatayi.
[4/22, 12:42 AM] Paexer: _Sunday 11/02/2018_ *«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*




*«»Page«» 10*
 Washe gari guraren 11 Abba ne zaune a falo shida Abban kd da yazo yana lalla6a Abba kan yayi haquri ya bar Saifuddeen ya kawo wacce yake so.
  Abba dake kallon sa a natse yace"Ahajin Kd kafi kowa sanin inda aka fito can baya tun iyayen mu na raye sam rayuwa bata min dad'i ba sbd qin bin umarnin mahaifin mu da nayi se bayan nabi za6in sane snn naji dad'in rayuwa hakan yasa na kwad'ai tu da son nima na za6arwa Saifuddeen wacce zai aura dmn yaji dad'in rayuwar auren sa kmr yanda nake jin dad'in rayuwa da maman yusra.
              «»
  D'an taqaitaccen labarin shine:-
  Su Abba asalin en kano ne tun kakannin kakannin, mahaifin su Abba shaharren d'an kasuwa ne,ta hanyar kasuwanci ne suka had'u shida mahaifin su Umma har suka zama aminai sosai,wanda shi asalin sa d'an rimin dako ne amma a kano yake kasuwan cin sa.
  Amintakar tasu ce tasa har sukayi sha'awar had'a 'ya'yan su aure dmn qara damkon zumunci.
  Bayan kowannen su ya yanke shawara da iyalansa ne snn suka snr da 'ya'yan su.
Umma da yayar ta hjyr kd kai tsaye suka amince da buqatar mahaifin su ba tare da sun ko ta6a ganin su Abba ba amma sukayi biyayye dmn sun san mahaifin su bazai ta6a had'a su da abunda zai cutar da su ba.
  Su Abba kam Abban kd ne kawai ya amince amma Abba fafau yace shi kam yana da wacce yake so,kai koda baya da ma bazai iya auren bagidajiya ba,ba yanda mahaifin su bai lalla6a shi ba amma fir yaqi amincewa da auren har mahaifin nasu yayi fushi dashi amma hkn besa Abba ya saduda ba,ya auri wacce yake so,Abban kd kuma ya auri za6in mahaifin su wato hjyr kd,umma kuma ta auri wani wanda mahaifin su ya had'a ta dashi a cikin dangin su wato d'an qanin shi.
  Dukkan su suna jin dad'in rayuwar auren amma banda Abba wanda yake ganin yayi auren soyayya amma rayuwar auren se ta zamo masa wani iri ba dad'i,gabad'aya dangi ba me zuwa gidan shi sbd mtr shi sam bata da mutunci kowa bata gani da gashi har shi kansa da ya aure ta bai isa yasa ta abu tayi ba se idan taga dama, kullum cikin fad'a suke sbd masifar ta,har suka samu qaruwa zaman nasu ba dad'i tun Abba na 6oye halinda yake ciki har yazo baya iya 6oyewa gabad'aya ya shiga nadama da dana sani rashin amincewa umarnin mahaifin su da yayi,da qarshe ma ya saki mtr tashi and still rayuwar tashi bata mishi dad'i sbd mahaifin su yaqi sake mishi be daina fushi dashi ba.
   Haka yayi ta rayuwa be sake wani auren ba har aka kwashe wasu shekaru.
  Kwatsam umma tana zaman jin dad'i ita da mijinta se Allah yayi mishi rasuwa ya barta da yaro d'aya da kuma tsofon ciki.
   Tofa tunda Abba yaji labari ya kwad'aitu da son auren ta dmn ya samu mahaifin su ya daina fushi dashi ya kuma samu albarkacin biyayyar iyaye.
  Hkn yasa ya sami Abban kd ya snr dashi wanda ba kad'an ba yaji dad'in hakan dan ko kad'an baya jin dad'in fushin da mahaifin su keyi da Abba duk da dai ya jima yana jin haushin Abba kan qin amincewa umarnin mahaifin nasu da yayi amma ganin irin rayuwar da ya shiga se duk ya bashi tausayi.
   Koda Abban kd ya snr da mahaifin su buqatar Abba se yaji dad'i duk wani fushi da yake yi da Abba ya ajiye snn da kanshi yaje rimin dako ya snr da aminin sa wato mahaifin su umma,wanda beyi fushi ba ko nuna jin haushin Abba na qin amincewar da yayi tun farko yace ba komai indai zainab cewa da umma ta amince to ya amince.
  Se bayan umma ta haifu har ta yaye abunda ta haifa wato Zarah snn aka yi aure tare da amincewar ta.
    Alhmdlh tun daga lokacin Abba ya soma jin dad'in rayuwar auren shi.
    Wannan kenan.
Mu dawo inda muka tsaya.
             «»
 Abban kd ya jinjina kansa yace"hakane nima a gaskiya zanfi so Saifuddeen ya auri Zarah amma ganin yanda duk ya je min cikin damuwa yasa nace to zan zo na same ka muyi magana akan kayi haquri ka barshi ya kawo wacce yake so ba wai dan ina son hakan ba dmn yaran yanzu basu san irin matan da suke d'aukowa ba,kyau kawai suke bi ba ruwan su da hali.
  Abba yace"sosai kuwa bare shi saifuddeen yaro ne me jin kansa wani  bazai gane abinda nake nufi ba se idan anyi auren yaga lallai za6in iyaye shine za6i.
  Abban kd yace"tabbas kuwa,inda shi Saifuddeen d'in ma da son samun sa ne wnn baturiyar yake so mu barshi ya aura"
  What!
Abba ya fad'a
  Abban kd yace"qwarai haka ya gaya min da aure yake sonta.
   Abba yace"kaji min sha sha shan yaro,ae ko giyar wake nasha bazan barshi ya auri wnn yarinyar da ke neman lalata mishi rayuwa a banza ba,zan had'u dashi sha sha sha shida nace ya fita harakar ta wato har maganar ta ma yaje ya maka"
  Abban kd yace"Aa da ya same ni ne kan nazo na baka haquri,na nemi jin me ya aikata har hakan ta faru shine ya gaya min.
  To bayan naji bayanin sa ne har yake gaya min da aure yake sonta nace masa a'a wnn bazai yiyu ba ya haqura,se yace min to shi gaskiya baya son zarah dan Allah abar shi ya kawo wacce yake so nace masa to zan zo na same ka muyi magana.
   Abba yace"Zarah kam ba fashi se ya aure ta,idan kuma yaqi tofa bamu bashi se dai ya nemi wasu iyayen bamu ba.
  Abban kd yace"Aa hakan ma bazai faru ba da kaina zan lalla6a shi ya haqura da auren zarah d'in nn gaba zai fahimci abunda muke nufi.
  Nan ya kira Saifuddeen a waya yace yazo yana son ganin shi snn ya nemi Abba da ya basu guri dan ya fahimci Abba fad'a kawai zai masa ba lalla6ar sa zai yi ba.
  Abba bai musa masa ba se murmushi kawai da yayi ya tashi ya basu guri.
 Jim kad'an sae ga Saifuddeen ya shigo sbd dama yana cikin gidan.
  A natse ya zauna qasa gaban Abban kd tare da gaida shi.
  Abban kd ya amsa yana mai kallon sa snn cikin natsuwa yace"Saifuddeen mun zauna nida Abbanka munyi magana wanda a gaskiya sosai na gamsu da bayanin da ya min,dan haka ina son kayi haquri da za6in da ya maka inshaa Allah idan ka masa biyayya se kaji kmr kafi kowa sa'ar rayuwar aure.
  Saifuddeen yace"Abba ba wai naqi za6in Abba bane ni yarinyar ce bana so sam bazan iya rayuwa da ita ba wlh,Sophie nake so  wacce na tabbatar idan kuka amince na aure ta kae tsaye zata yarda ta musulunta"
  Abban kd yace"Saifuddeen dani har Abban ka Zarah muke son ka aura ba Sophie ba wacce na tabbatar itama iyayen ta  basa son auren ka da ita,snn sanin kan ka ne baza su ta6a barin ta ta musulunta ba dan haka ka daina min zancen ta kwata kwata bana son in sake ji "
  Shiru Saifuddeen yayi wanda gabad'aya ya rasa ina zai sa kansa.
  Can yace"to Abba ai ita zarah d'in ma jamil ke sonta a shirye yake idan kuka amince masa zai aure ta wlh"
  Abban kd dake kallon sa yayi shiru cikin jinjina kan sa yace"Jamil ke sonta kace?
 Eh jiya da naje kd yake gaya min"
 To ita zarah d'in tana son sa?
 Bai gaya mata ba tukun amma shekaran jiya sosai yaso muna kammala cin abinci ya snr da umma se uzurin tafiya kd ya gifta mishi sbd jikin kaka da ya tashi.
  Yace"to Allah ya bata lafiya ya kuma bashi wata wacce tafi zarah sbd zarah taka ce mun riga mun gama yanke hukunci se ka bashi haquri kaji.
  Komai kasa cewa Saifuddeen yayi se tashi yayi ya haura sama zuwa d'akin umma,ya samu zata fito knn sbd kiran da Abba ya mata a waya yana son ganin ta,
tayi tsaye tana kallon yanda duk jijiyoyin kansa suka taso idanun sa sun qara yin jajur cike tap da qwallah cikin murya me cike da jin haushin abinda ke shirin faruwa dashi yace"wae umma me yasa ake son cutar dani kan dole sai na auri banzar yarinyar da sam ba ajina bace,why umma! why!!
  Ya qarashe mgnr ne kmr wanda zai fashe da kuka.
 Umma ta rungume shi cike da son lallashin sa da sauri ya d'ago tare da had'iye kukan da yake ji cikin wata irin kakkausar murya yace"wlh umma komai zai iya faruwa idan aka ce lallai se anyi auren nn na rantse kuwa!
  A natse umma ta d'aura hannayen ta kan kumatun sa ta girgiza kanta tana kallon sa a hnkli tace"Aa saif ba abinda zai faru se alheri ka daina fad'ar haka kaji"
  Zeyi magana knn tayi saurin rufe masa baki tare da kwantar da kansa kan jikinta tana shafa kan nasa a hnkli kmr wani qaramin yaro tace"kayi haquri iyayen ka ne su idan kayi musu biyayya zaka ga ribar hakan biyayyar ka baza ta ta6a tafiya a banza ba kaji.
 Nan tayi ta bashi magana tana rarrashin sa har ta samu ya haqura ze yarda ayi auren amma ya nuna mata haka ne kawai sam a zuciyar sa ba haka bane ji yake kmr yaje ya sami zarah ya mata gunduwa gunduwa kowa ma ya huta.
   Bai dai ce komai ba kawai ya fita daga d'akin ya fice zuwa 6angaren shi.
  Da shigar sa d'akin sa kawai yaga jamil wanda ya taso da saurin sa yazo yana tambayar sa ya ake ciki?
   Saifuddeen dake kallon sa ya had'iye yawu da ciwon gaske snn yakai hannayen sa kan kafad'un jamil ya dafa shi yace"suna nn kan bakar su,haka nima bazan ta6a yarda nayi rayuwa da wnn yarinyar ba,mtr ka ce kai zaka aure ta"
  Jamil da idanun sa suka ciko tap qwallah ya girgiza kansa yace"no saif kayi biyayya kawai shine mafi alheri"
  Ya fad'a ne tare da qoqarin fita daga d'akin sbd kukan da yake ji sosai.
  Saifuddeen ya riqo shi yace"haqiqa jamil na fahimci kana matuqar sonta ni kuma ko ganin ta bana sonyi bare har na iya rayuwa da ita a gida d'aya wae a matsayin miji da mata sam bazan iya ba ni hajiya zanje na sama nayi magana da ita dmn gaskiya idan akayi auren nn zan iya aikata abinda ban ta6a aikatawa ba.
 No saif kayi biyayya na gaya maka shine mafi alheri a gare ka.
  Jamil alherin sa shine kar ayi baka san yanda nake ji bane komai zai iya faruwa fa idan akayi aure nn zanyi gunduwa gunduwa da ita ne na ma tabbatar.
 Jamil yace"ba abinda zae faru se alheri biyayyar da kayiwa iyayen ka baza ma ta bar ka akaita wani mummunan abu ba,ba kad'an ba ina matuqar son zarah ta kasance mata ta amma bazan ta6a baka shawarar kaci gaba da jayayya dasu Abba ba burina shine kayi biyayya a gare su ni kuma zanyi ta addu'a Allah ya bani irin Zarah koma wacce ta fita.
  Lokaci d'aya jikin Saifuddeen duk yayi sanyi sbd tausayin jamil dmn yanayin yanda yake magana dole ka tausaya mishi muryar sa a hankali yace"jamil naji zanyi biyayya na aure ta amma na d'an wani lokaci daga baya zan sake ta ka aure ta"
  Cikin rashin fahimta Jamil yace"kmr ya Saifuddeen ban gane ba Abba fa yana son kayi rayuwa da ita ne a matsayin matar ka ta har abada"
  Na sani jamil amma ita da kanta zata sa na sake ta ba tare da Abba yaga laifi na ba.
  No saif kar ka cutar da zarah dan Allah ka barta kawai.
  Jamil babbar cutuwa shine naci gaba da rayuwa da ita bayan bana sonta,har abada baza ta ta6a jin dad'in rayuwa dani ba,kai ke sonta dakai zata ji dad'in rayuwa dan haka nayi maka alqawarin zan sake ta ka aure ta.
  Jikin jamil ne yayi sanyi tabbas a yanda yasan halin Saifuddeen in ya tsani abu ya tsane sa ne,ba makawa zarah zatayi rayuwa marar dad'i a tare dashi,shi kuma burin sa zarah tayi rayuwa me dad'in gaske na har abada amma ya zai yi tunda qaddara ta fad'a mata,sam baya son dalilin sa Saifuddeen ya aikata abunda iyayen sa zasu zo suna fushi dashi dmn ya tabbatar ze muzgunawa zarah ne har ta nemi saki da kanta.
  Sanyin da yaji kan kumatun sa ne ya bashi tabbacin cewa hawaye yake,se jin yayi Saifuddeen yasa hannu yana share masa hawayen yace"trust me bazan cuce ta ba tunda baka so amma dai zan sake ta ba tare da Abba yaga laifina ko nata ba i promise u"
  Jamil yace"but ta yaya zaka saketa ba tare da Abba yaga laifin ka ko nata ba?
  U are a Dr and me too da akwai hanyoyi da dama wa enda idan na gayawa Abba d'aya daga ciki ko a addinan ce auren yana da buqatar a raba shi sbd zaman cutuwa ne kawai zamu tayi rayuwar mu baza ta ta6a qaruwa ba.
  Jamil ya jinjina kansa yace"hakane amma kmr yadaurar Abba ne mukayi"
  Kar ka damu Abba ne zai yafe mana kuma gwanda haka akan na aikata abunda za'a zo ana yin dana sani.
  Jamil yayi shiru can yace"shikenan nagode zan tafi yanzu ne dawowa ta daga kano ko gida banje ba.
  Ka gaida su umma
Saifuddeen ya fad'a yana mai kallon jamil har ya fita.
  Shi har yanzu mamakin sa yake ta yanda akayi har ya fad'a son wnn abar.
  Ya ta6e bakin sa yace"lallai so makaho ne"
  Kana yaje kan sofa ya zauna idon sa qyar kan photon su shida Sophie,can ya jinjina kansa,ae dolen sa ne ma ya azabatar da zarah dmn kusan ita ce silar rabuwar sa da Sophie,kawai dai ya 6oye wa jamil ne dmn baya son ya tada hankalin sa,amma shi ba wani abunda zai gaya wa Abba da za'a raba auren ba tare da laifin d'ayan su ba dmn ko ya fad'a Abba consultant Dr ne da bazai raba auren ba har se yayi bincike da kansa ya gano gaskiya,dan haka bazai ma fara ba asirin sa ya tonu,muzguna mata zai yi ta yanda dole da kanta zata nemi saki.
  Wayar sa ce tayi qara koda ya duba Sophie ce wacce tun rnr da abun ya faru tayi ta kiran sa yafi a qirga amma be d'aga ba kmr yanda Abba ya hane shi,ko yanzu ma be d'aga kiran ba jiki sa6ule ya ajiye wayar kan sofa ya dafe kansa cikin tsananin damuwa,ba kad'an ba yana mutuwar son Sophie and he can't life with out her,amma dole hakan zai yi ta haqurin jure hukuncin Abba har na tsawon wani lokaci kafin sannu a hankli ya samu ya lalla6a Abba har ya barshi ya aure ta.
[4/22, 12:42 AM] Paexer: _Monday 12/02/2018_ *«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 11*
Washe gari shigar sa office knn ko zama beyi ba se ga Sophie ta shigo,tsaye yayi yana kallonta lokaci d'aya duk ta rame idanuwan ta duk sun kumbura da gani tun rnr da abun ya faru take kuka har yau dan still qwallah ne tap a idon ta tana kallon shi.
 Kafin tace komai yazo ya ra6a ta gefen ta ya fita,ta bisa da kallo hawaye na silalowa a hankli kan kumatun ta,Saifuddeen bai ta6a fushi da ita irin haka ba se wnn karon,gashi ta biyoshi har office d'insa dmn ta bashi haquri amma ya fita ya bar mata office d'in.
 A hankli ta zube gurin tana kuka.
  Saifuddeen kuwa da fitar sa kai tsaye office d'in jamil ya tafi Jamil da har ya zauna ze fara duba wasu files ya tsaya yana kallon saif har ya qaroso yaja kujera ya zauna muryar sa cikin yanayin damuwa yace"plz jamil kaje ka sami Sophie tana office d'ina ka mata bayanin komai and ina son ka kwantar mata da hankali ta yanda baza ta shiga damuwa sosai ba snn kuma ka gaya mata ko bayan ta koma England zan dawo gare ta very soon inshaa Allah zamu yi aure.
  Jamil ya numfasa yace"Aa Saifuddeen kar fa a gaya mata abunda bazai yiyu ba taje tayi ta faman jiran ka a banza......Bakin ka ya sari d'ayan kashi,da Allah ni je ka gaya mata nasan tana can ta soma kuka.
 D'an guntun murmushi kawai jamil yayi snn ya tashi ya fita.
 Saifuddeen kuwa cike da damuwa ya had'e kansa da desk.
  Can jamil ya dawo jikin sa duk a sa6ule ya zauna Saifuddeen da ya d'ago yace"what! ta fahimce ka ko kuwa?
  A hnkli jamil ya lumshe idon sa tare da ware su akan shi snn yace"ta fahimce ni dmn sosai na kwantar mata da hankli amma duk da haka se da tayi ta kuka ita bata so ta tafi England tafi so ta zauna tayi ta jiranka har ko yaushe ne dmn tana tsoron yanda zata je ta fuskanci iyayen ta wa enda ba lallai bane su barta ta samu damar sake had'uwa da kai ba har kuyi aure.
   Saifuddeen ya numfasa snn yace"kira ta awaya ka gaya mata ta tafi kawai komai zaiyi normal inshaa Allah da izinin iyayen ta ma za'a yi auren kar ta damu.
  I have already told her but still dai ta tafi tana kuka,she dnt wnt miss u,and ga short note d'in da ta rubuta ta bani tace na baka.
  Saifuddeen ya kar6i takadar ya ware ya fara karanta content d'in da ke ciki"
_Dear,am very sorry 4 wat i have coused for us,of course i should punished my self 4 that,bye take care of ur self and my kitty._
                    _Miss u!_
 Saifuddeen da ya gama karantawa yasa hannu ya goge en guntayen hawayen da suka gangaro ta gefen idon sa kana ya tashi ba tare da yace da jamil komai ba ya fita.
 Jamil da ya bisa da kallo ya girgiza kansa cikin yanayin tausayawa sbd yanda suke matuqar son junan su dole ka tausaya musu musamman yanda suka dad'e cikin qaunar juna.
  Zarah ce ta fad'o mishi a rai wacce basu ko fara soyayyar ba,asali ma ko cikakken wata d'aya beyi da fara ganin ta ba amma da Saifuddeen ya gaya mishi Abba zai had'a shi aure da ita,wani irin yanayi ya tsinci kansa a ciki da baisan ma ta ya zai fisalta ba,wanda shi kansa yana mamakin yanda akayi soyayyar zarah ta kama shi lokaci d'aya haka da yawa duk da kasancewar ta baqauya amma shi sam qauyancin nata bai dame sa ba burin sa kawai ya mallake ta,kuma inshaa Allah zai mallake ta kmr yanda Saifuddeen ya masa alqawari,kul ba dad'e kul ba jima ze iya jira koma yaushe ne.
           «»
Saifudddeen na ganin abun kmr wasan yara amma se shiryen shiryen auren ake da gaske ba kama hannun yaro dan kaf dangi da abokan arziki kowa ya sani,amma shi kam in banda jamil bawani abokin sa da ya sani dan hana jamil yayi ya snr da kowa acewar sa ba auren da zai snr da frnds d'insa ba ne wnn,auren takaici da har kullum mamakin Abba yake da har yayi tunanin had'a shi da wnn yarinyar,gabad'aya takaici da kewar Sophie duk suka tara mishi har ma ko yaje asibiti baya iya wani abun kirki yake dawowa.
  Nusaiba kam duk da tasan halin yayan ta ko kad'an baya son zarah amma tayi farin ciki sosai dmn ganin take zai daina duk wani abun da yake yiwa zarah su koma son juna,duk qyamar da yake yiwa ba qauyen mutum dai se gashi baqauyar ce zata zamo matar shi,kai ba kad'an ba tsarin Abba ya birge ta dmn sam bata son halin yayan nata na tsanar da yake yiwa qauyawa abun na damunta sosai.

Saura en kwanaki da d'aurin auren ne Saifuddeen ya fito 6angaren su umma riqe da invitations d'inda Abba ya bashi na d'aurin aure dmn ya bawa abokan sa.
  Umma na kallon sa ta windown falo gabad'aya ya keta su ya zuba su a cikin dustbin ya kakka6e hannun sa yayi ficewar shi,bata yi mamaki ba dan dama tasan abunda zai faru knn,girgiza kanta kawai tayi snn ta kalli Abba da ya haura sama se waya yake abun sa cike da fara'a.
  Bin sa tayi zuwa d'akin nasa bayan ya ida waya ne ya kalle ta da fara'ar sa  yace"ya akayi ne Maman yusra?
  Tace"plz Alhj ka zauna ina son zamuyi magana"
  Ba musu ya zauna kan bed itama ta zauna tana kallon sa a natse snn tace"nasan baka so amma kayi haquri abu ne da ya zama dole,kasan mahaifiyar saif dole ne tasan da auren nn amma naga ga dukkan alama baka snr da ita ba se ma harkokin gaban ka da kake.
   Take duk wani farin cikin sa ya 6ace 6at ransa a 6ace yace"da wane dalilin zata sani mtr da sam bata qaunar shi tun yana d'an wata shida da ta barshi ta tafi ko da kuskure bata sake waiwayar sa ba.
  Umma tace"Alhj kar fa ka manta kaifa ka sake ta ba wai ta tafi ne ta barshi ba.
  Nasan ni na sake ta amma sam bata son Saifuddeen na gaya miki dmn a lokacinda ta sami cikin sa ba irin abinda bata yi ba dmn cikin ya zube amma Allah da ikon sa bata yi nasara ba har ta haife shi,a tunani na renon cikin sa da tayi na tsawon wata tara da yanda tasha wahala a gurin haifuwar shi zai sa ta so shi amma sam hakan besa ta damu dashi ba,masu aiki kawai ta barwa suna hidima dashi,nono ma se ta ga dama take bashi,har na gaji da baqin halinta na sake ta.
  Umma tace"amma dai duk da haka haqqi ne akanta a snr da ita"
  Yace"maman yusra kinfi kowa sanin bana son Saifuddeen yasan wace ce mahaifiyar sa dmn baqin ciki ne kawai a gare shi,a gurin hajiya ya tashi tun da yayi wayo ya fahimci cewa hjy kakar sa ce,ya fara damuna ina mahaifiyar sa,ban ta6a gaya masa ba sai dai kawai nace tayi tafiya da haka har Allah yasa mukayi aure nida ke,a gabanki na kawo shi nace masa gaki kece mahaifiyar sa da yake damuna kullum,kina kallon yanda ya rungume ki cikin tsananin farin ciki da jin dad'i wanda tun daga lokacin ya d'auka kece mahaifiyar sa da ta haifeshi har yau baisan bake kika haife sa ba and still bana so ya sani dan haka kar ki qara min zancen wnn banzar matar bana so.
 Kayi haquri inshaa Allah hakan bazai sake faruwa ba.
  umma ta fad'a tare da tashi ta fita daga d'akin.
  kici6us tayi da Nusaiba tsaye a bakin qofar d'akin idonta tap da qwallah da alama ta ji duk abinda suke fad'i.
  Wani irin kallo umma ke mata da kmr mamaki snn taja hannun ta da sauri ta tafi da ita zuwa d'akin ta,
tace "Nusaiba uban me kikeyi a bakin qofar Abbanku kika la6e kina sauraren abinda muke fad'i iye!
  Da sauri ta girgiza kanta tare da share hawayen da suka zubo mata tace"wlh umma ba la6e nake maku ba,umman kd ce ta kira a waya ta tace na kai maki wayar tayi ta kiran wayar ki baki d'aga ba shine naje ban same ki a d'aki ba nazo d'akin Abba da niyyar maku knocking shi ne se.....
   Shine se kika ji muna magana kika tsaya kina sauraren mu ko!to bari kiji in gaya miki wlh kar inji mgnr nn ta fito kinji ko!
  Da sauri Nusaiba ta gyad'a kanta alamar taji snn ta fita daga d'akin kmr yanda umma ta umarce ta.
  Taje d'akin su tayi kwance kan bed kmr wata marar lafiya dan gabad'aya se taji tausayin yayan nata ya kama ta yazai ji idan ya gano umma ba mahaifiyar sa bace bayan yana mata kallon ita ce ta haifeshi....."Nusaiba lafiya me yake faruwa?
zarah ta tambaya wacce tana zaune kan bed koda Nusaiba tazo ta kwanta.
   A kafai ce Nusaiba tasa hannu ta share hawayen da suka sakko kan kumatun ta sbd ta bawa zarah baya bata iya lura da abinda take ciki,byn ta share hawayen ne snn tace"ba komai kaina ne naji ya d'an sara min shine na kwanta"
   Muryar ta a sanyaye ta mata sannu.
  Snn taci gaba da duba littafan ta na islamiyya da take dubawa sbd dama aikinta knn idan bata yin komai,wacce duk ta d'an fad'a sbd zullumin auren da za'a mata da wanda bata san ya rayuwar ta zata kasance ba,wanda tun rnr ta ganshi da Sophie suna wnn iskancin wani irin tsanar sa take ji a ranta ko ganin sa bata son yi asalima bata sake ganin sa ba d'in tun daga rnr dan kwata kwata ya daina shigowa cin abinci,gidan su jamil yake zuwa can yaci.

Saura kwana d'aya asa lalle suka tafi Rimin dako ita da Nusaiba da kuma Nadiya wato 'ya ga umman kd wacce shekarun su d'aya da Nusaiba sune suka zama en matan amarya tare da dije dake can.```
  ```A washe gari aka sa lalle snn suka dawo kano akayi  sauran bukukuwa rnr juma'a aka d'aura aure and by 10pm aka kai Amarya ba kad'an ba zarah tayi kuka har ta gode Allah shike nn da gaske dai an d'aura auren nn har gata a d'akin ta an kawo ta,tana zaune kan bed kanta qasa fuskar ta a rufe da gyale kmr dai kowace amarya,su Nusaiba,nadiya da dije se sheri suke ta mata kmr yanda en matan amarya keyi tana jinsu bata tanka su ba dan ita kad'ai tasan irin baqin cikin da take ji a ranta an had'a ta da miji d'an iska dako qaunar ganin sa bata yi su har sunga gurin barkwanci.

Bayan kowa ya watse tana nn zaune kan bed ita kad'ai still fuskar ta a rufe se ci gaba take da kukan ta dan se kukan ma ya dawo mata sabo.
  Qofar d'akin taji an bud'e da qarfi har sai da ta tsorata ba shiri ta miqe ta sauka daga kan gadon tana kallon  Saifuddeen da shine ya banki qofar d'akin ya shigo yana mata wani irin mugun kallon da yasa ta soma ja baya,shi kuma se matsowa yake inda take har ya had'e ta da jikin gina,yana kallon ta fuskar nn tashi kmr wani zaki ba annuri ko kad'an,zarah kuwa gabad'aya ta kame jikin gina tana kallon sa a tsorace,wacce ba shiri ta saki qara sbd yanda yasa qafar sa ya daki qafar ta da qarfin tsiya se mutsustsuka qafar yake d'auke da takalmin sa masu masifar ciwo snn yakai hannun sa a bayan wuyan ta ya lotsa akaifun sa ciki sosai ya riqe mata jijiyoyin wuya gam tamkar ze 6alla mata wuya.
  Ae kuwa take idanuwan zarah suka yi jajur se faman qoqarin qwatar kanta take amma ta kasa.
[4/22, 12:42 AM] Paexer: _Wednesday 14/02/2018_ *«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*


*«»Page«» 12*
Saifuddeen kuwa se qara matse mata wuya yake yana mai ci gaba da mutsustsuka qafar ta,Zarah dake ta qoqarin qwatar kanta ta saki qara cike da jin zafi cikin kuka tace"wae kai wane irin mugu ne me na maka!
 A qufule yasa hannun sa da yatsun sa biyu ya mugun matse mata baki snn cikin kakkausar murya yace"ke! dan ubanki har tambaya kike,to bari kiji ba'a ta6a babbar jakar da ta shigo rayuwa ta ba ta lallata min duk wani tsarin na rayuwa ta ba irin ki,wacce ko d'aura min ke akayi a qafa bazan ta6a janki ba wlh se dai na tsinke na yar,dan haka tun wuri kiyi gaggawar cire cewa kin zo gidan nn ne dmn aure never!
Kisa a ranki cewa kinzo fursun ne inda zan azabtar dake na miki hukuncin laifin da kika aika ta a gare ni,dmn bazan ta6a barin ki ba wlh se na hukunta ki hukunci mafi tsanani da se kinyi nadamar zowar ki duniya!
 Supid!!
 Ya fad'a tare da jefar da ita gefe ta fad'i da qarfi har sai da goshin ta ya daki gefen bed da sauri ta dafe goshin nata tare da fashewa da wani irin kuka yayinda d'ayan hannun ta ke riqe da qafar ta da ya mutsustsuke duk tayi wani irin jajur,wuyan ta kuma ji take kmr still bai janye hannun sa ba sbd zafin bala'in da take ji,wacce tana jin yanda jini ke d'an silalowa a hankli daga bayan wuyan nata,ga bakin ta dake mata sululi sbd matsar da ya masa.
  A ranta se Allah ya isa take ta mishi tana ci gaba da kuka a nn har bacci ya kwashe ta a gurin bata sani ba.

Washe gari da qyar ta iya jan qafar ta taje ta d'auro arwala tayi sallah.
  Bayan ta idar ta koma kwanciya,byn wuyan ta da qafar ta duk sun kumbura tana jin kanta kmr wata mara lafiya haka dai ta samu bacci ya d'auke ta.
  Se guraren 9 ta tashi tayi wanka ta shirya,zuwa qarfe 10 da rabi se ga su Nusaiba sun zo mata da breakfast d'inda umma ta basu su kawo.
 Dama yunwa take ji tayi zaune taci se da ta qoshi,nan fa sukayi ta fira abinsu
  Se bayan mutane sun fara zowa ne snn suka tashi zasu sauka downstairs zuwa falo a nn Nusaiba taga yanda zarah ke taka qafar ta da qyar tana d'ingishi,nadiya da dije sam basu
lura ba sbd suna gaba su suka fara fita.
 Nusaiba da ta gani ta jata baya kad'an tana kallon qafar snn tace"6ter what's wrong,me ya sami qafar ki haka tayi jajur?
  Zarah ta ta6e baki tace"yayanki mana mugu shine duk ya mutsustsuke qafar"
  Me kika mishi?
Nusaiba ta tambaya
 Zarah tace"hm meko mugunta kawai"
Snn ta yaye gyalenta dake yafe tun daga saman kanta tace"duba bayan wuyana ma ki ga duk ya kumbura sbd matsar da ya min"
  Nan Nusaiba takai hannun ta a hankli ta ta6a gurin tana dubawa tace"kai oh my God!
 lallai yaya saif Allah tun wuri kar ki barshi yaci gaba da miki haka"
  Zarah tace"hm basshi Allah ya isa ne zai kama shi dan bazan ta6a yafe masa ba wlh"
   Nan ta maida gyalen ta ta yafa har zuwa goshin ta da ya d'an yi ja duk ta rufe bata so mutane su gani,haka ma da suna saukowa daga staircase se taka qafar ta take a hnkli dan kar mutane su fahimta,amma duk da haka se da nadiya da dije suka fahimta har ma suka tambaye ta me ya sami qafar ta tace musu abune ya fad'o min a qafa shine naji ciwo.
  Komai basu ce ba se sannu da suka mata snn suka qarasa gurin mutane dake zazzaune a falo duk mafi yawan su en rimin dako ne wato maman dije da sauran en uwa,wa enda a nn garin suka kwana gurin umma.
 Take gida ya cika tamkal se yinin biki ake Saifuddeen kam tun da safe ya fita gidan be sake dawowa ba har yamma tayi kowa ya watse se su Nusaiba kad'ai wa enda suma tafe suke sun fito zarah ta rakosu bakin gate,odar da akeyi ne yasa suka tsaya mai gadi ya bud'e gate d'in,se ga jamil ya kunna motar sa a cikin gidan shida saifuddeen wanda motar shi ce ta sami matsala shine jamil ya kawo shi ba dan yaso ba sbd yarinyar da Saifuddeen yake tare da ita tana nn zaune a seat d'in baya se k'as k'as take tana cin chewing gum ta wani ci uban ture kaga tsiya,qafar ta kan d'aya tana faman danne danne a waya wacce tana d'aya daga cikin en matan da ke matuqar son Saifuddeen da se yanzu ne ya fara lokacin su,jamil kam abun har mamaki ya basa.
 Su Nusaiba kam fita kawai sukayi sbd driver na waje yana jiran su ba tare da sun tsaya kula da wa enda ke cikin motar ba kawai dai sunga Saifuddeen da jamil basu kula da wacce ke baya ba sbd duhun glass d'in motar bazai barsu su iya ganinta kai tsaye ba se idan sun kula.
Zarah na tsaye har sai da suka shiga mota suka wuce snn ta koma daga ciki,idon Jamil qyar a kanta ganin yanda take d'ingishi ya kalli Saifuddeen dake qoqarin bud'e qofa ze fita yace masa"halan me ya sami zarah a qafar ta har take yin d'ingishi?
  Wani banzan kallo Saifuddeen ya mishi snn yace"oho mata in ma kayi wani banzan tunani ne to ka ma watsar dan kasan wnn abar ko duniyar nn kaf za'a ban bazan neme ta ba wlh"
  Ya buga tsaki tare da bud'e ganbun motar ya fita Jamil ya bisa da kallo d'auke da murmushi shi sam bai ma kawo wani tunani ba dan yasan halin abokin nasa bazai ma ta6a kula ta ba.
  Yana kallon sa har suka shige shida yarinyar sa,ya girgiza kansa kawai
snn yaja motar sa ya bar gidan.
  Saifuddeen kuwa koda suka shiga sun sami zarah tana kashe kayan kallo sau d'aya ta kalle su ta kauda kai taci gaba da aikinda take,Saifuddeen ya riqe waist d'insa yana kallon ta yace"ke dan ubanki gidan ku ba'a koya maki tarbiya bane da baza kizo ki durqusa ki gaida mutane ba!
  Kafin zarah tace komai wacce yake tare da ita ta wani ya tsine fuska tana kallon zarah tare da fad'in"No dear ka barta kawai ni bana ma son gaisuwar ta,zo mu tafi"
   Taja hannun sa suka haura sama zuwa d'akin shi,
zarah ta bisu da kallo ta6e da baki tace"an dai yi asara ga kyau amma ba kyan hali,Allah sa ma kaf karuwan duniyar nn zaka kawo a cikin gidan nn ni ina ruwana"
  Nan ta ida kashe kayan kallon ta haura sama zuwa d'akin ta.

Washe gari da safe tana kwance kan dardumar sallah tana bacci se ga Saifuddeen ya shigo d'akin riqe da qaramin bokiti a hannun sa cike da ruwa,a tsiyace ya kwara mata su gabad'aya kan fuskarta,ba shiri ta farka tare da sakin ihu cikin mugun tsorata ta miqe a rud'e tana waige waige a tunanin ta ko tayi gamo da aljanu ne suka jefo ta rafi.
  Saifuddeen dake kallon ta ya kwad'a mata gigitaccen mari yace"kalle ni nn nine kije ki bud'e qofa se faman danna doorbell ake duk an hana min bacci.
 Zarah dake dafe da kuncen ta tana kuka tace"amma wlh se Allah ya isa min bazan ta6a yafe maka ba....wani lafiyayyen marin ya koma kife ta dashi ya nuna ta yace"mind ur tongue ban tashe ki dan ki gaya min mgnr banza ba,maza kije ki bud'e qofa nace ko yanzun nn nayi gunduwa gunduwa dake,kinzo se sharara bacci kike tunda an gaya miki nn gidan ubanki ne da zaki kwanta ki huta.
 Da har zata ce bazata ba tayi shiru tana kallon farar kyanwar da ta shigo a tsorace taja baya dan mugun tsoron kyanwa take.
  Saifuddeen da ya fahimta ya d'auki kyanwar yace"zaki je ko sai na cillo miki ita"
  Da sauri ta girgiza kanta muryar ta na rawa tace a'a zanje wlh.
 Nan ta fita da sauri sauri se fmn d'ingishi take har ta iso bakin qofa ta bud'e.
  Mai gadi ne tsaye a bakin qofar wanda har ze juya yaji an bud'e qofar ya tsaya,se da ya gaida ta snn yace"dama ruwan gidan ne suka d'auke gashi ina so zan bawa flowers ruwa"
 "to an gaya ma ni wani abu na sani na gidan nn ne"
 Zarah ta fad'a ranta a 6ace tana kallon sa kmr shine Saifuddeen.
  Mai gadin bai ce komai ba se haquri da ya bata ze juya se ga Saifuddeen,da saurin ta ta bar gurin dan still yana riqe da kyanwar a hannu sa.
  Tambayar mai gadi yayi mene ne,mai gadi ya gaya mishi.
 Nan ya fita yaje ya duba ruwan suka kawo.
  Da ya dawo kai tsaye d'akin zarah ya nufa da niyyar gindaya mata sharuddan gidan,but yana 6ird'a qofar d'akin ya jita a rufe.
  Zarah na jin sa tayi banza dashi se jiqaqqin tufafin jikin ta ta cire wato kayan bacci riga da wando da kuma qaton hijabin sallah da ke jikinta,se ta zamo daga ita se inner wears,half vest ce baqa da pant baqi mai kmr bomb short dan ya rufe mata d'uwawu sosai har zuwa gurin cinyoyin ta kad'an.
  Sanyi take ji sosai har tana kakarwa amma bata nemi wani abu ta rufa jikinta ba,dan jin inner wears d'in jikinta take kmr suma sun d'an jiqe,tayi gurfane kan guiwoyin ta tasa tufafin da ta cire tana tsane ruwan da sauri tana matsewa a cikin bokiti.
 Saifuddeen da yaje d'akin sa yana kallonta ta jikin laptop d'in shi se kallon ta yake kmr da mamaki,sbd gashin da ya gani da ita sosai mai sul6in gaske baqi wulik dashi ya zubo har saman gadon bayanta ga black half vest da black bomb short d'in jikinta sun qara fito da hasken fatar ta sosai se tayi kyaun duba kmr wata wayayya.
  Ta6e bakin sa yayi snn ya rufe laptop d'in tare da cillar da ita gefe.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Thursday 15/02/2018_ *«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*






By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*




*«»Page«» 13*
Snn ya maida duban sa gun wacce yazo da ita jiya a nn ta kwana tana kwance rufe da blanket se fmn sharara bacci take,hannu yasa ya yaye blanket d'in,ba wata sutura a jikin ta bai damu ba se tashin ta ya shiga yi.
 A hnkli ta bud'e idon ta tare da jan blanket ta rufe jikinta snn ta tashi zaune tana kallon sa tace"ya akayi ne dear?
  Yace"wanka zakiyi kiyi ki bar gidan nn kafin mutane su fara shigowa bana son qananun maganganu"
  Tace"to da akwai abinda zanci idan na fito dan ni yunwa nake ji sosai"
  Fuskar sa a d'aure yace"kin girka ne da zaki ci"
  Ta marere ce fuska tace"haba dear ina wnn yarinyar da zan shiga kitchen da kaina"
  Wnn qazamiyar ce zaki iya cin girkin ta.
  Ta yatsine fuska tace"kuma fa hakane bazan iya cin girkin ta ba gaskiya,bari naje nayi wanka idan na fito ko tea ne se nasha ko kanada buqatar na girka mana wani abu?
  "Bana buqata"
Ya fad'a a taqaice,bata sake ce masa komai ba se sauka tayi daga kan gadon taje ta fad'a bathroom.
  Zarah kuwa bayan ta gama gogen gogen ta,kae tsaye bathroom ta shiga tayi wanka se bayan ta fito ta shirya snn ta gyara d'akin.
 Kana ta kalli agogon bangon d'akin taga har sha d'aya tayi amma ba alamar zuwan su nusaiba gashi yunwa take ji,yau Sunday bare tayi tunanin ko sunje school,snn bata da waya bare ta kira umma taji ko lfy dan jiya da kansu suka gaya mata cewa zasu koma dawowa.
  Nan dai ta yanke shawarar idan har sha biyu tayi basu zo ba zata je kitchen ta sami abunda ta girkawa kanta.
  11:30 ta soma jin qarar doorbell ae kuwa ta sauka downstairs da saurin ta dan tasan inshaa Allah sune suka zo.
  Koda ta bud'e qofa kuwa sune.
  Shaye da toka tayi tsaye riqe da qugu tana kallon su taqi ta basu hanya su wuce,haquri suka bata tare da gaya mata dlilin jimawar su ba haka kawai bane.
"Snn kuma ga babban albishir Abba yace a kawo miki"
 Nusaiba ta fad'a tare da miqa mata waya sabuwa dal a cikin kwalin ta.
  Wani irin dad'i zarah taji ta kar6i wayar da murnar ta snn ta basu hanya suka shigo suka zauna,nusaiba ta kar6a ta fiddo wayar a kwali,irin wayar ta ce sak Tecno K9 se dai ta Nusaiba gold ce wnn kuma ruwan cement.
  Se da suka d'auki selfie da wayar snn suka baje kan rug suna yin breakfast sbd basuyi breakfast a gida ba shine suka zo da nata har nasu gabad'aya.
  Koda Saifuddeen ya fito zai fita ya gansu se 6arkar firar su suke Nusaiba na nunawa zarah yanda zatayi amfani da wayar.
 Nusaiba,Nadiya da Dije tare suka gaida shi bai kalle su ba se kiran sunan Nadiya yayi tare da amsa gaisuwar ta ya fita.
  Rashin amsa gaisuwar dije da yayi shine ya fahimci cewa er uwar Zarah ce dmn rashin iya hausar su iri d'aya ne suna bud'e baki zaka san su Fulani ne.
  Nusaiba kuma tuni ya daina amsa gaisuwar ta tun daga rnr da suka wuce ita da zarah basu gaida shi ba.
   Bata damu ba dan dama tasan ba amsa gaisuwar ta ta zai yi ba,dije kuma ita sam bata lura cewa gaisuwar Nadiya kad'ai ya amsa ba,bare ita Nadiyar wacce a tunanin ta ko dan sun jima basu had'u bane ya kira sunan ta.
  Nan dai suka ci gaba da harakar su har sai bayan sunyi sllr zuhur snn sukayi shirin komawa gida zasu bi driver da ya kawo wa zarah abincin ranan ta wanda dama yazo ne da niyyar komawa dasu sbd Nadiya da dije duk yau zasu koma.
  Tana dawowa daga rikan su ta hango Saifuddeen zaune kan dining yana cin abincin da umma ta aiko dashi.
 Kae!
Ta fad'a snn taje da hanzarin ta ta d'auke abincin,wani lafiyayyen mari saifuddeen ya mata har sai da ta saki plate d'in ba shiri,fuskar sa cike da mamaki yace"ke! ni sa'ar ki ne da zaki zo ki samu ina cin abinci ki d'auke"
  Zarah dake dafe da kuncen ta idanun ta cike tap da qwallah cikin muryar kuka tace"abinci na ne fa da inna ta aiko min kuma idan na d'iba mai gadi nake kaiwa sauran gashi kazo kana ci"
  "Inna"
Ya fad'a fuskar sa a yatsine.
  Ya shiga kallon kulolin abincin tabbas kulolin umma ne kuma d'and'anon abincin na umma ne snn kuma yaga lokacinda driver ya kawo abincin haka na nufin umma take cewa inna knn.
  Ya kalle ta a fusace tare da d'aura mata wani marin yace"dan ubanki umma kike kira da wnn qazamin sunan iye!?
  Tambayar ki nake ki gaya min ko yanzun na sake sauke miki wani marin wlh!
  Kuka zarah ta fashe dashi tare da ja baya,
yace"to wlh bari kiji in gaya miki kar in koma jin kin kirata da wnn sunan,ki bari in kinje can qauyen naku kyaci gaba da kiran uwar ki da sunan ba tawa uwar ba,sakara kawai fice in daina ganin ki a nn.
  Matsawa kawai zarah tayi bata bar gurin ba dan so take ta d'ibi abincin taje dashi taci yunwa take ji.
  "Kitty! Kitty!!Kitty!!!"
Saifuddeen ya shiga kiran sunan wnn farar kenwar ae kuwa se gata tazo aguje,ba shiri zarah ta bar gurin har tana had'awa da gudu,shi kuma ya dire ma kitty plate d'in abincin da ya fara ci me cike da naman kaji take ta fara ci,snn ya d'auki wani plate ya sake d'ibar wani abincin ya soma ci.
 Se da akayi sllr la'asar snn zarah ta fito a tunanin ta ma Saifuddeen ya fita amma se ganin sa tayi kishingid'e kan 3seater qafar sa kan d'aya yana karatun jarida,kitty na kwance kusa dashi se baccin ta take.
 Gun dinning ta nufa koda ta bud'e warmers ba komai a ciki.
 Kallon sa tayi muryar ta a sanyaye tace"ina kuma ka kai sauran abincin banci ba"
  Ba tare da ya kalle ta ba yace"na baiwa maigadi ga sauran  na kitty nan a qasa se ki d'auka kici,shine rabon ki ba dan matsayin ki yakai can ba na taimaka maki ne kawai"
  Zarah ta kalli abincin da kitty ta rage a plate,wato ita zai had'a da kyanwa har yace taci raginta,hm wai me en birni suka d'auki qauyawa ne,amma ba komai da sannu zata nuna masa ko en qauye suna da  muhimmanci ba abun walaqantawa bane su.
  Ta kalle sa kmr tace masa wani abu amma tana tsoron tayi magana ya turo mata kyanwa,ta d'auke idon ta a kanshi ta duqa ta d'auki plate d'in,Saifuddeen ya kalle ta dan ya d'auka ko zata ci abincin ne se yaga ta tattara su gabad'aya har na kan dining ta tafi dasu zuwa kitchen,bata fito ba se da ta wanke gabad'aya kwanikan sbd anjima idan umma ta aiko musu abincin dare se ta bada a koma dasu.
  Ta fito d'auke da tsintsiya da faka ta share gurin dining d'in dan duk shinkafa ta zuba inda kitty taci abinci.
 Bayan ta share gurin ta mofe snn ta koma d'akin ta tayi kwance kawai cikin ta se faman qugi yake mata haka ta zauna da yunwar har sai da aka kawo abincin dare snn taci.

Washe gari ta fito tana share gidan se ga Saifuddeen ya fito cikin shirin sa  zai fita,
yayi tsaye yana kallonta fuskar nn tasa ba annuri yace"ke zo nn!
  Kallon kitty tayi dake biye dashi beko sani ba tace"ni bazan iya zowa ba kawai ka fad'i mgnr ka ina jinka"
  Wani mugun kallo ya mata tare da matsawa inda take,da sauri taja baya har tana qoqarin fad'uwa tace"dan Allah ka tsaya kar ka matso wlh tsoron kyanwa nake kuma gata a bayanka tana binka"
    Kallon kitty Saifuddeen yayi snn ya maida duban sa gare ta fuskar sa a d'aure yace"Allah yasa idan na matso mutuwa zakiyi bazan tsaya ba kuma kina d'agawa daga inda kk se na jefa miki ita wlh"
   Da sauri Zarah tace"naji zan tsaya wlh,amma dan Allah na roqeqa kar ka matso inda nake...bata ida ba se ganin sa tayi a gabanta kmr walqiya,zata gudu ya fizgo ta da qarfi se ihu take tana tsalle tsalle bata son kyanwar ta ta6a ta,marin da ya mata ne yasa ta tsaya cak tare da kamewa guri d'aya jikin ta se rawar tsoro yake,Saifuddeen yace"zaki daina wnn rawar jikin ko sai na qara miki wani marin"
  Da qyar zarah ta d'an iya controlling kanta muryar ta na rawa tace"na daina fad'i abunda zaka fad'a min ka tafi dan Allah"
 Sai da ya kama kunnen ta ya mird'e sosai snn yace"sharuddan gidan nn zan gaya miki dan haka ki saurare ni da kyau kiji"
  Daga yau d'akina ya zama dole shine farkon inda zaki fara sharewa snn ko zakiyi sauran share sharen gidan nn,snn mai gadi da kikeyiwa tsawa kan ya gaya miki ruwa ya d'auke,kiji in gaya miki yafi duk wani naki daraja a gurina,dan haka daga yau kece zaki ci gaba da yin duk wani aikin da yake yi a gidan nn and idan umma ta aiko da abinci kar ki kuskura kice zaki d'iba har sai ni,mai gadi,kitty munci ya ishe mu snn ko zaki ci abinda muka rage.
  Idan kuma kika sa6a d'aya a cikin wa en nn ko!!...yayi qwafa tare da ture ta gefe ya d'auki kitty suka fita.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Friday 16/02/2018_ *«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 14*
Binsa kawai zarah tayi da ido,duk da sharuddan sa sun mata tsauri baza ta bijirewa abunda yace ba,tasan jiranta kawai yake abu kad'an se yakai mata duka,kwana biyu kacal da yin aure amma marikan da tasha sunkai biyar bancin muguntar da yake mata dan haka bazata yarda taci gaba da zama jakar shi ba amma zata yarda ta zama baiwar shi na d'an wani lokaci.
  Nan ta share hawayen da ke kan fuskarta snn taci gaba da share sharen ta.
  Bayan ta idar ne taje tayi wanka ta shirya snn taje ta d'aurawa kanta breakfast taci,dmn ta gwammaci ta riqa dafa nata abincin taci yafi mata sauqi akan yanda yace,ko banza ma umma sati d'aya ne zatayi tana aiko musu da abinci.
  Haka ta yini ita kad'ai a gidan ba wanda yazo har dare kmr ba sabuwar amarya ba sbd anguwar nisa ne da ita sosai snn barikir shiya ce tsit tsit tsit ba kasaifai kake ganin mutane ba bare kuma hutu ya qare an koma school.
Bata wani damu ba tunda akwai kayan kallo sbd akwai ta da son kallo sosai abu ga baqauyen mutum lol.
 Ga kuma sabuwar wayar ta da ta yini tana danna na ganin cewa ta iya abubuwan wayar.
 Se bayan isha'i Saifuddeen ya dawo gidan tun fitar sa da safe,
 Cike ya sami dining jere da abinci,breakfast,lunch,dinner duk suna jere akai,koda ya duba ba wanda zarah taci a ciki.
  Ta6e bakin sa kawai yayi ya nufi zuwa d'akin sa yaga kota share mishi d'akin,se kuwa ya sami d'akin tsaf tsaf very neat se dadda d'an qamshi ke tashi.
   "Kin kuru"
Shine abinda ya fad'a snn ya cire kayan jikin sa ya fad'a bathroom yayi wanka ya shirya ya fito yaci abinci shida kitty da ya d'ibarwa nata daban,take ta cinye abincin kaf sbd farfesun kifi ne ya zuba mata,sake zuba mata wani yayi,bayan sun gama cin abincin ne ya kira mai gadi yace ya kwashi duka sauran abincin ya tafi dashi.
 10:30am na washe gari zarah ta shiga d'akin Saifuddeen zata gyara masa d'aki.
  Duk a tunanin ta baya nn ya fita zuwa gurin aiki amma se ganin sa tayi shida wata mace bata jiya ba,ihu ta saki tare da fad'in"innalillahi wa inna ilaihi raji'un!
dmn yanayin da ta gansu a ciki yama fi wanda ta ganshi shida Sophie.
   Ta fito d'akin aguje Saifuddeen ya tashi da zafin nama ya nemi towel ya d'aura ya biyota kafin ta shiga d'akinta tuni ya fizgota,gaban ta se wani irin dukan uku uku yake ta runtse idanun ta gam tare da kamewa guri d'aya tana jiran saukar mari.
   Bai mare ta ba se had'a ta yayi da jikin bango ya shaqeta yana tambayar uban me taje yi a d'akin sa.
  Zarah dake qoqarin  janye hannun sa daka shaqar da ya mata tace"to bakai bane kace na riqa share ma d'akin ka kafin komai....to shine dan ubanki zaki shigo min d'aki kai tsaye se kace d'akin awakai.
  Tace"to meye banbanci kaida ko bunsuru ma baya abinda kake....ihu ta saki sbd lafiyayyun marin kan da ya kai mata.
  Ta fashe da kuka tace"Allah ya isa wlh ka cuci su Baffa da suka same ka ta hanyar halal suka baka tarbiya amma ka zamo musu d'an akuy.....dukan ta Saifuddeen ya shiga yi iya qarfin sa yana ball da ita,sai ihu take tana neman guduwa sai da wacce yake tare da ita tazo ta rirriqe shi tana fad'in"haba my saif ya zaka biyewa wnn bagidajiyar yarinyar da sam ba tarbiya ne dasu ba!
 "Komai rashin tarbiyar ta ni sei na ladabtar da ita!"
 Saifuddeen ya fad'a a fusace tare da barin gurin ya shiga d'akin shi,yayinda Zarah kam tuni ta shige d'akin ta ta rufe.
   Taci kukan ta har ta gode Allah.
  Sai da ta tabbatar ya bar gidan snn ta fito ta share koina na gidan amma taqi share d'akin sa,se Quaker oats taje ta had'a wacce zaman ta birni ne ta fara iya shan shi tana kuma ganin yanda umma ke had'awa idan zasuyi breakfast shine ta iya dan tana son shi sosai.
  A nn falo tayi zaune ta kunna kallo ta fara sha,but ba shiri ta tofar da spoon d'in farko da ta fara sha snn ta tafi aguje zuwa d'akinta ta shiga bathroom se kwara amai take,byn ta samu ya tsaya mata tazo tayi zaune kan bed tare da dafe kanta wacce ba komai ne yasa ta amai ba se tuno mugun ganin da tayi a d'akin Saifuddeen wanda ita kad'ai tasan me ta gani.
 Se da ta sami natsuwa snn ta koma downstairs ta d'auki oats d'in ta tafi dashi kitchen kallon sa take yaji madara sosai da sauri ta rufe idonta ta zubar dashi cikin sink ta kunna famfo har se da ta tabbatar ya wuce snn ta bud'e idon ta ta rufe famfon,ta koma falo riqe da mopper ta goge gurin da ta tofar da oats snn byn ta mayar taje gun dining ta bud'e breakfast d'inda umma ta aiko musu dashi arish ne da soyayyan qwai se plantain wanda sai da Saifuddeen da farkar shi suka ci mai isar su snn suka fita.
  Rufe breakfast d'in kawai tayi taje ta kwanta kan 3seater taso ta d'an ci amma yanda zuciyar ta ta yamutse tasan ko taci amayar wa kawai zatayi.
   D'an kwanciyar da tayi ne bacci ya kwashe ta a gurin,Saifuddeen ya shigo da saurin sa ya haura sama zuwa d'akin sa da alama mantuwa yayi.
  Se da ya dawo snn ya lura da zarah kwance tana bacci,yatsine fuskar sa yayi kmr yaga kashi sbd still tana sanye da kayan bacci bata ko yi wanka ba,ya girgiza kansa kawai ya nufi gun dinning ya duba breakfast yaga yanda suka barshi haka yake,fita kawai yayi se ga mai gadi ya shigo d'auke da sallama a bakin shi,tashi zarah tayi ta amsa sallamar tana kallon sa da kmr mamaki kafin take cewa lafiya malam?
  Yace"yalla6ai ne yace nazo na d'auki abinci"
  Tace"haba kai kuwa malam fisabilillah se kace ba musulmi ba,ai da sae ka tsaya a waje kayi sallama se in kawo ma ko"
  Kiyi haquri yalla6ai ne yace na shigo kawai na d'auka,a tunani ba kowa a falon ai da bazan shigo ba.
  Tace"hm ae ko ba kowa kasan dai ba dacewa bane ka shigo....ya shigo d'in! er rainin hankali in ke ba haka kawai kike shiga d'akin mutum ba ko sallama,shi har ma yayi miki sallamar.
  Cewar Saifuddeen da ya koma dawowa wanda kana ya kalli mai gadi yace da Allah je d'auki abincin ka tafi daga yau idan ka shigo kar ka sake tsayawa sauraren wnn sha sha shar...
ba mamaki ma ubanki na can yana neman ko gadin ne ya samu be samu ba amma sbd kinzo birni shine har kinada qwarin guiwar da zaki tasa mai gadi a gaba kina gaya masa mgnr banza.
   Shaye da toka Zarah ta miqe tsaye cikin 6acin rai ta kalle sa tace"kaga malam wlh duk abunda zaka min kamin amma kar ka sake sako ubana a ciki,d'an akuya kawai da bai san darajar iyayen shi ba!.
Ta dalla mishi harara tare da buga wani uban tsaki ta wuce.
  Cak Saifuddeen ya tsaya galala yana binta da kallo cikin mugun mamakin yanda akayi ta sami damar raina shi haka.
Haqiqa duk Abba ne yaja masa wnn rainin,ace baiga wacce zai had'a shi aure da ita ba se wnn bagidajiyar bafulatana,nn kawai idanun sa suka sauya zuwa launin ja,ya jinjina kansa kawai ya fita.
 Satin ta biyu a gidan,rnr friday se ga Nusaiba tazo ita da yusra sosai zarah tayi murna,sbd tun wancan lokacin basu sake dawowa ba,bcos zuwa makaranta be bar su ba in sunje tun safe sai 5pm suke dawowa sbd makarantar had'e take da islamiyya duk da haka saturday n sunday suna zuwa islamiyyar da ke nn kusa da gida snn thursday n friday da yamma extra lesson ake musu idan sun dawo daga school.  ko yanzu ma suna dawowa daga school ko abinci basu ci ba suka shirya suka zo by 4 zasu koma kafin me lesson d'in nasu yazo.
  Amma waya kam suna yin ta sosai shiyasa take d'an jin damar kewar.
 Dama ta kammala girki knn suka zo ta d'ebo abincin sukayi zaune a nn falo se ci suke suna fira.
  Suna kammala cin abincin ne Nusaiba taja zarah suka je d'aki.
Kan bed suka zauna Nusaiba na kallon zarah tace"6ter sati biyu kacal amma kinga yanda kika rame"
  Murmushi zarah tayi tana mai kallon kanta dama ya jikin nata yake balle ta rame,afkin jikinta hips ne se boobs da ko ta rame su basa wani raguwa.
 Tace"ae dole na rame Nusaiba ina tare da wanda baya da burin da ya wuce kullum yaga ya sauke wata sabuwar muguntar sa a kaina.
  Nusaiba tace"kina nufin yaya bai daina maki abubuwan da yake miki ba"
  Hm Nusaiba knn da wuri haka ae sai abunda ya qaru.
  6ter wato wani namijin se kin nuna masa ba kya jin tsoron sa snn fa zaku zauna dai dai dan haka daure ki riqa nuna masa kmr ba kya jin tsoron sa zaki ga ya daina ku dawo kuna zaman ku abun sha'awa kmr ba ku ba.
   Har abadah baza mu ta6a zama yanda kike tunani ba Nusaiba sbd ba kad'an ba yayanki ya tsane ni haka nima.
No 6ter yaya ba ke ya tsana ba kawai shidai haka yake baya son mutumin qauye,gashi kuma a cikin d'an qanqanin lokaci har kin fara waye wa sbd kina son kiga cewa ke waye d'in,da mukaje rimin dako lokacin sa lalle ae kinga se magana akeyi tayi inna se jin dad'i take,dan haka zamu ci gaba da inda muka tsaya amma ba'a fannin kwalliya ba tunda ba laifi kin d'an iya.
  Wane fannin zamuyi knn yanzu?
  Zarah ta tambaya tana mai kallon Nusaiba tare da gyara zamanta.
  Nusaiba tace"tun zuwanki gidan nn wane irin kaya ne kike sawa?
  Atamfa kawai nake sakawa kuma ko kwalliya ma bana yi sbd gabad'aya tunda akayi auren nn naji komai ya fita raina duk da ina son kwalliyar en birni sosai.
  Nusaiba tace"to ba ma kwalliyar ba dai dmn kayan da nake son ki riqa sawa basa da buqatar heavy makeup ko simple kikayi daidai ne bare natural beautyn ki ma ko bakiyi kwalliya ba zakiyi looking good.
  Murmushi zarah tayi tace nidai gaya min wane irin kaya ne.
  Ba wasu kaya bane face qananun kaya.
  Da sauri zarah ta gwalo idanun ta tare da dafe qirji tace"qananun kaya fa kika ce Nusaiba,dan Allah rufa min asiri kayan en iska ne fa ina ni ina saka su amin kallona er iska,masu sawa dai Allah shirye su idan suna da niyyar shiryuwa.
  Dariya Nusaiba tayi sosai snn tace"wa ya gaya miki se d'an iska kawai kesa qananun kaya,wayewa ce fa kawai kuma naga kema kina son ki waye d'in ko?
  Sosai ina so amma ba irin wnn wayewar ba gaskiya dan bazan iya sa qananun kaya ba.
  Haba 6ter kmr bakiyi boko ba ai qananun kayan sune zasu fito dake.
  Nusaiba ban fa ta6a sawa ba ta ya ma zan fara.
  Ae da sannu zaki fara har ki saba da kayan kizo kina mishi yanga.
 Zarah ta 6ata fuskar ta tace"ni kam bazan yi ba ae abinda kake so zakayi wa yanga na ganin ka birgeshi,ni kuma bana son shi ko kad'an,ba kuma zan ta6a son shi ba har abada koda kuwa maza sun qare a duniya.
  Nusaiba ta dafa ta tace"Ki fahimce ni 6ter wato so nake ki jawa kanki girma ya daina ganin ki er qauye har yana miki wulaqanci.
  Shiru zarah tayi burinta knn dama in haka ne kuwa zata qoqar ta.
  Tace"shike nn zanyi"
 Dad'i Nusaiba taji wacce ba girma kad'ai take son jawa zarah ba burinta soyayya ta d'arsu a tsakanin su.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Saturday 17/02/2018_ *«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 15*
 4:10pm suka fito zasu koma.
 Jamil suka samu jingine a jikin motar sa da ya faka a nn gaban parking lot.
  Gaida shi sukayi snn suka wuce.
  Zarah da ta raka su har se da taga wucewar su snn ta dawo,jamil da ya bita da kallo tun wucewar su har dawowar ta,
ya tsaida ta yace dan Allah ta kira mishi Saifuddeen idan yana ciki yayi ta kiran shi a waya be d'aga ba.
   "To" tace mishi ta wuce ba tare da tasan Saifuddeen d'in yana nn ko baya nn ba dan tunda suka shiga d'aki ita da Nusaiba basu sake fitowa ba yusra ma can ta same su sai da zasu koma ne snn suka fito.
   Da shigar ta kae tsaye d'akin sa ta nufa tana mishi knocking se can ya bud'e qofar,kallonta yake fuskar sa a d'aure mai d'auke da alamar bacci yake ta tashe shi yace"wae ke jakar ina ce daqiqiya ba na hanaki zowa ko kusa da qofar d'akin nn ba!
  Kallon sa tayi tare da kauda fuskarta gefe snn tace"da ka hana min ai baka gaya wa abokin ka cewa in ya zo ya riqa shigowa kawai ba se ya aiko ni ba.
  Nan kawai ta wuce abinta zuwa d'aki Saifuddeen ya bita da kallo tare da yin qwafa snn ya fito ya sami Jamil ransa a 6ace yana fad'in"kan me zaka tsaya a waje kmr wani baqo baka shigo ciki ka same ni ba har da aika wnn sakaryar.
  Jamil dake kallon sa yace"kaffa ka manta nn gidan auren ka ne ba kamar gida ba da zanje 6angaren ka kai tsaye.
   Saifuddeen ya ta6e bakin sa yace"hm!wai shirmen banza auren da kanka zai koma in huta da jaraba ni har yanzu mamakin ka nake wlh wai baka ga abin so ba se wnn abar,har kana jiran na sake ta ka aure ta,ba mamaki ma tausayin ta ne kawai kake ji se ka aure ta kazo kana yin dana sani.
  Jamil yayi murmushi tare da girgiza kansa yace"Saifuddeen knn har abada ni bazan ta6a nadamar auren zarah ba inshaa Allah,sai dai in ko kaine zakayi nadamar sakin ta.
  Wani mugun kallo saifuddeen ya mishi tare da daka qafar shi da qarfi kan yatsun qafar jamil"
 Ah!....jamil ya fad'a cike da jin zafi ya duqa tare da kai hannu yana shafa yatsun qafar shi idon sa kan Saifuddeen yace"amma saif ka cika mugu wlh da zafi fa"
 Hararar sa saifuddeen yayi yace"ae kaine cikakken mugu kan me zanyi nadama akan na saki wnn abar har abada wlh bazan ta6a yin nadama ba.
  Jamil ya d'ago d'auke da murmushi yace"kaga nidai banzo dan wnn ba dalilai biyu ne suka kawo ni zan fad'a maka nayi gaba"
  Saifuddeen ya kalle sa alamar yana jinsa.
  Jamil yace"na farko dai Sophie ce ta turo text"
  Me tace?
Saifuddeen ya tambaya a natse yana me kallon sa da kulawa.
 jamil yace"kawai tace tana kewar ka sosai snn ya kitty"
  Shiru Saifuddeen yayi be ce komai ba har se da jamil yace me za'a ce mata?
  Kawai duk abinda kace mata yayi dmn bana son nida kaina in riqa fad'a har ya zamo na bata kulawa byn Abba ya hana ni,ina jinka fad'i na biyun mene ne?
  Jamil dake kallon sa yace"kd zan tafi gun kaka ban sani ba ko zaka tafi naji kana magana kan zaka je ka duba jikin ta"
   A sanyaye saifudden yace"Naso inje amma damuwar rashin Sophie ya motsa min bazan iya zuwa yau ba sei dai gobe da safe zanje inshaa Allah.
  Jamil yace"ba matsala zan jira ka mu tafi tare amma da safe ne tafiyar zaka iya?
  Zan iya but yaushe zaka dawo?
  Sunday da safe
  Ok shikenan nima zan kai Sunday d'in  se ka biyo min muje a motar ka.
  "Olryt"
Cewar Jamil snn sukayi sallama saifuddeen ya koma daga ciki jikin sa duk a sanyaye.
9:00pm
 Kallo take tana cin abinci,tana ji se doorbell ake ta fmn dannawa amma tayi biris se ci gaba take da cin abincin ta,dan tasan ba kowa bane face en matan Saifuddeen dake samun sa har gida.
  Har sei da aka gaji da danna doorbell  aka bud'e qofar aka shigo sbd dama qofar ba'a rufe take da key ba.
  Qananun kaya ne a jikinta riga da wando da suka bayyana tsiraicinta kan yanda suka matse ta sosai snn taci uban kwalliyar nn crazy makeup,ga kitson attachment dake saman kanta tsorayen sun sauka har tsakiyar gadon bayan ta kmr wata arniya,d'an qaramin veil ne akanta da ta d'auro shi tun daga bayan qewar kanta tazo dashi kan goshin ta tayi rolling d'insa.
  Ba jaka a hannun ta bare purse wayar ta ce kawai se key d'in motar ta dake saqale a d'an yatsanta,ta riqe waist d'inta tana kallon zarah tace"hm!wai dama da akwai mutum a falon nn ne ina ta faman danna doorbell kika yi banza dani baza ki gaya min na shigo kawai qofar a bud'e take ba.
  Kallon ta kawai zarah tayi yau ma wata sabuwar fuskar ce ba wa enda ta saba gani ba kuma,ita abun mamaki ma yake bata iyayen su basa raye ne ko me da suka barsu suna yawon iskanci har suna zowa su kwana a gidan wani qaton banza hankalin su a kwance.
   Allah kyauta.
Ta fad'a a cikin ranta snn ta maida duban ta gun abincin ta taci gaba da ci.
  Da mamaki take kallon zarah kafin tace komai se ga Saifuddeen yana saukowa sanye da white bathrobe a jikin shi da alama fitowar sa knn daga wanka.
  Yana qarasowa ta riqo hannun sa tare da nuna masa Zarah tace"my beloved halan kurma aka ajiye maka a cikin gida,na jima ina danna doorbell tana zaune a falon nn bata bud'e min ba snn byn na shigo ina mata magana kallona kawai tayi ta kauda kai taci gaba da cin abincin ta.
  Saifuddeen ya kalli zarah dake ci gaba da cin abincin ta tana jinsu amma ko gefen su taqi ta kalla.
 yace"iskanci ne tana dik jinki"
    Nan ya tafi ze d'auko abu a fridge zarah na ganin sa tafe ta d'auka ko wani abu ze mata ta tashi da sauri riqe da plate d'in abincin ta ta koma bayan kujera ta tsaya,tsaki yayi tare da girgiza kansa snn yaje ya bud'e fridge ya d'auko fresh milk ya wuce sama zuwa d'akin sa tare da wacce tazo gurin shi.
Ta6e da baki Zarah ta bisu da kallo har suka shige ta girgiza kanta snn ta koma kan kujera ta zauna taci gaba da cin abinci tana mai ci gaba da kallo,Tom and jerry ne ake a tashar MBC 3 se dariya take kwasa kmr wata qaramar yarinya.

Da safe bayan saifuddeen ya kammala shirin sa na zuwa kd ya tafi d'akin zarah kitty na biye dashi.
  Da shigar sa d'akin kae tsaye gun fridge ya nufa ya d'auko ruwan gora da sukayi mugun sanyi ya nufi gun zarah dake kwance kan bed tana bacci gabad'aya ta rufe jikinta da blanket fuskarta ce kawai bata rufe ba.
  6alle gorar yayi ya shiga zuba mata ruwan kan fuskarta,zarah ta tashi a firgice cikin fasa ihu tana neman guduwa daga kan gadon,Saifuddeen ya riqe ta yana ci gaba da qwara mata ruwan har se da ya qarar da ruwan gorar a kanta,se kuka take tana zagin sa tana mishi Allah ya isa.
  Marin da ya saukar mata ne yasa tayi shiru tare da cusa fuskarta gabad'aya cikin cinyoyin ta ta saki wani sabon kuka.
  Yasa hannun sa ya d'ago ta da qarfi yace"kalli nan kin ganta!ya nuna mata kitty da ya riqo a hannun sa"
   Zarah ta kalle ta tare da saurin kamewa a jikin gadon sosai kmr zata shige ciki,jikinta se rawa yake haka ma muryar ta tace"eh na gani dan Allah kar ka liqa min ita wlh bazan sake zagin ka ba"
  Sake kittyn yayi tare da d'aura d'ayar qafar sa kan gadon ya ranqwafa sosai kusa da zarah yana kallon ta yace"zanyi tafiya se gobe zan dawo ban gaya miki ba se dan kisan cewa ke zaki kula da kitty kuma ki tabbatar kin kula da ita yanda ya kamata"
  Yana kaiwa nn ya juya ze tafi tayi saurin riqo rigar shi ya mata wani irin mugun kallo tare da kama hannun nata da ta riqo rigar shi ya mird'e hannun kmr ze karya ta,ta saki ihu tana fad'in yi haquri dan Allah dama zan gaya maka ne wlh bazan iya kula da ita ba tsoron ta fa nake ka sani.
  Yace"Right tunda kina tsoron ta ki barta kar ki kula da ita kinji"
 Yayi qwafa tare da fita d'akin kitty na biye dashi.
  Zarah ta taso da gudun ta ta rufe d'akin da makulli.
  Bata fito ba se da ta tabbatar ya bar gidan wacce duk a tunanin ta ya tafi da kitty amma se hango ta tayi kwance kan 2seater tana bacci.
  A tsorace taja baya da sauri riqe da tsintsiyar da ta d'auko zata yi shara.
  Fuskar ta kmr zatayi kuka tana kallon kitty tace"Oh oh wato da kika bishi baije dake ba.
  Mugu kawai azzalumi wlh ka cuce ni da ka bar min ita ni yanzu ya nasan zanyi.
 Ta jefar da tsintsinya tana kallon falon taso ta share shi amma bazata iya ba dan baza ma ta iya qarasawa daga cikin falon ba,bare tayi zancen fita ta share harabar gidan da kuma ban ruwan flower dan duk ita keyi sbd suna cikin ayyukan da gateman keyi da saifuddeen yace duk ita zata riqa yi abu d'aya ne bata yi shine bud'e gate.
 Ba yanda ta iya haka ta d'auki tsintsinyar ta mayar.
  Snn ta had'awa kanta breakfast  taje d'akinta ta rufe da makulli.
  Se byn ta gama breakfast har tayi wanka zuwa 12 snn ta fito.
  Tsoro tsoro take saukowa daga staircase tana leqen kitty still bacci take haka ta lalla6a da saurin ta ta shiga kitchen ta rufe bata fito ba har sai da tayi girkin ta da tasan ze kai mata har dare ta zuba a kula ta kuma d'auki duk wani abu da tasan zata buqata dan bata son in ta shiga ta koma fitowa.
  Dama ta d'ibarwa kitty nata a plate d'inta,da ta fito ta ajiye mata abincin nesa da ita,tsoro da gudun kar qamshin abincin ya farkar da ita bata riga ta shige d'aki ba.

 Guraren 9 duk taji zaman d'akin ya isheta ta fito sanye da kayan bacci.
Kmr dai d'azu tsoro tsoro take saukowa tana leqen kitty amma se bata ganta ba,bata damu ba kawai dai tayi mamakin ko ina ta shiga ne oho,nn dai ta basar taje tayi zaune kan 3seater ta kunna kallo.
  Can hankalin ta gabad'aya ya tafi gun kallo ta soma jin kukan kitty.
  A tsorace ta tashi tana dube dube ta ina kitty zata fito.
  Ae kuwa se ta hango ta tafe tana saukowa daga staircase,nn ta kwasa aguje zuwa kitchen ta shiga ta rufe da key.
  Da sauri ta janye daga jikin qofa sbd kukan kitty da taji gab da bakin qofar kitchen d'in har tana sa nails d'inta tana kokawa da gambun kmr zata tsaga shi ta shigo.
  Kuka zara ta fashe dashi ta tafi da gudu zuwa store ta rufe.
 Amma duk da haka sosai take jin kukan kitty a kunnen ta,gabad'aya ta rud'e jikin ta se rawa yake ita ya tasan zatayi,lokaci d'aya ta tsaya sbd tunanin da ya fad'o mata ba makawa yunwa kitty keji shine take wnn kukan haka sbd abincin da ta zuba mata a d'azun ta ganshi bata wani ci sosai ba naman kawai taci.
  Nan ta d'auko kifin gwangwani,ta bud'e ta zuba mata a plate kmr yanda taga Saifuddeen na mata.
 Amma kuma ta rasa ta ya ma zatayi ta fita har ta bata kifin,ta san kyanwa da mugun son kifi bare yunwar nn da taji tana tsoron kar tana bud'e qofa tayi super zuwa cafkar kifin,ae kuwa da an kwashi gawar ta a gurun dan ta tabbatar tana yin super to lallai zubewa kawai zatayi somammiya.
 Safa da marwa ta dinga yi a kitchen d'in kmr zatayi kuka tana neman mafita ga qarin kifin duk ya cika mata hanci kmr tayi amai take ji dan ko kad'an bata son warin kifi shiyasa ma kwata kwata ko cin kinfi bata yi.
   Can ta shiga store da saurin ta ta d'auko sweeper tazo zata bud'e qofa gaban ta se wani irin dum!dum! yake hkn ta jure sannu a hnkli jikinta na rawa  har ta bud'e qofar,hannun ta a baya ta 6oye plate d'in kifi tasa sweeper se kora kitty take cike da qarfin hali har ta fitar da ita waje tare da tura mata plate d'in kifi ta rufo qofa da sauri,kana ta zube qasa a gurin ta had'e kai da guiwa tana faman sauke ajiyar zuciya.
   Can ta tashi ta leqa kitty ta jikin door ta ganta se cin kifin ta take tayi.
  "Alhmdlh"
 ta fad'a snn taje kan kujera ta kwanta tana jiran idan kitty ta gama se ta bud'e mata qofa ta shigo dan ita qarin kifin ne da bata so yasa ta fitar da ita waje.
  Bacci ne ya kwashe ta a gurin batare da ta sani ba.
 Har se washe gari snn ta farka sbd mugun sanyin da taji na ratsa dukkanin ilahirin jikinta har da mafarkin gata a cikin qanqara se ruwan sama ake.
  Da tashin ta kan agogon bangon falon ta fara sauke idanun ta qarfe goma na safe.
  "Kae!"
Ta fad'a tare da saurin tashi taje ta leqa window hankalin ta ne ya tashi ganin da gaske dai ruwan sama akayi gashi ta bar kitty a waje.
Dafe da qirji tace"na shiga uku wnn wane irin bacci ne haka nayi,se kuma tayi shiru tuna cewa in tana al'ada fa se a hankli bacci take me nauyin gaske da take jimawa kafin ta farka.
  Tausayin kitty ne ya matuqar kamata ta fita da saurin ta riqe da sweeper tana dube dube ta ina zata ganta ta korata ta koma ciki kafin Saifuddeen ya  dawo ya nemi halaka ta.
 Bata ganta ba se plate d'inda ta sa mata kifi ta gani cike tap da ruwan sama,kafin tayi komai se odar mota ta jiyo mai gadi ya fito d'akin sa da sauri yaje ya bud'e gate.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Sunday 18/02/2018_ *«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*






By
  *Billy giro😊*


*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 16*
Tsaye tayi a gurin kmr wacce aka dasa,tana kallo har motar da aka bud'ewa gate ta kunno kai ta shigo,jamil ne da Saifuddeen suka fito a ciki.
  Se dai Jamil na hango ta ya koma cikin mota sbd kayan baccinta riga da wando ne,da tsayin wandon iya guiwa,en dogayen fararen k'aurin ta suna a bayya ne.
  Kanta ta sadda qasa dan se taji kunyar ganin ta da yayi,snn a hankli ta 6oye sweeper a bayan ta,idanuwan ta qasa tana kallon qafafuwan Saifuddeen dake qarasowa kusa da ita gaban ta se dukan tara tara yake tana tunanin abinda zata ce masa ba tare da yaga laifinta ba.
   Saifuddeen na qarasowa gurinta yasa hannu ya tallabo fuskar ta yana kallonta fuskar sa a d'aure yace"uban me kika fito yi a waje kin wani tsaya se kallon mutane kike.
  Shiru tayi ta kasa ce masa komai ya kalli sweeper da ta 6oye a bayan ta yace"shara zakiyi ne ko me?
Still ta mishi shiru
Cikin d'aga murya yace"ki bani amsa ina tambayar ki kin min shiru!
  Girgiza kanta tayi snn cikin inda inda tace"A'a..wnn farar kyan..war...nake nema...ban...ganta ba"
  What!
Saifuddeen ya fad'a da qarfi har sai da taji tsoro taja baya da sauri.
   Ya riqo ta a fusace yace"dan ubanki gaya min a ina kika kaita!
  Tace"ni ba inda na kaita kawai dai ban ganta ba.....wani irin mari ya saukar mata yace"ki fito da ita yanzun nn wlh ko na kakkarya ki.
   Kuka ta fashe dashi se ga jamil yazo da gudun sa yana fad'in haba Saifuddeen meye haka!.
   Saifuddeen yace"wai gaya min take kitty ta 6ata bata ganta ba,this can never happen!
  Kitty!! kitty!!kitty!!!
  ya shiga kiranta yana zaga gidan hankalin sa duk a tashe kyace uwar sa ce ta 6ata.
  Duk girman gidan haka ya zagaye shi yana ta faman kiranta be ganta ba.
   Ya dawo gadan gadan cike da niyar shaqar zarah har se ta fad'i inda ta kaita.
  Se kuma ya tsaya cak idon sa akan flowers da yaga suna motsi irin motsin da ba iska ne ke kad'a su ba ta6a su ne ake suna yin motsin.
  Be tsaya wata wata ba yaje da hanzarin sa yasa hannun sa ya ware flowers d'in,kitty ce ta 6uya a ciki duk ta jiqe,jikin ta se wani qyarma yake tana son fitowa amma ta kasa sbd gabad'aya bata da wani qarfi.
  Hannu biyu Saifuddeen yasa ya d'auko ta,ya miqe tsaye tare da ciro farin handkerchief d'insa a cikin aljihu ya rufa mata,snn ya sata gabad'aya cikin   suit jacket d'issa ya rufe ya rungume ta kmr jariri.
  Yazo a fusace gurin zarah yayi tsaye yana kallonta d'auke da idanun sa da sukayi jajur,kana ya fizgi hannun ta da qarfi ya tafi da ita.
  Jamil ya bishi yana fad'in"saif tsaya mana meye haka wae!"  Saifuddeen be saurare shi ba se ci gaba yake da jan zarah wacce keta qoqarin qwace hannunta,amma bata iya qwatar hannun nata ba har ya tafi da ita gun swimming pool ya jefa ta da qarfi ta fad'a ciki.
 Wani irin Ihu ta saki me qarar gaske sbd masifar sanyi ne da ruwan,ta taso da qarfi cikin jan numfashi kmr zata shid'e,yayinda jamil ya dafe kansa tare da fad'in"innalillahi wa inna ilaihi raji'un!
 snn cike da mamaki ya saki ido yana kallon Saifuddeen wanda ko a jikin sa,yana jefa ta ya juya abin sa ya tafi.
  Ga zarah se wahala take a cikin ruwan tana neman shid'ewa bata iya fitowa.
  Hakan yasa gabad'aya hankalin jamil duk ya tashi wanda a rud'e ya shiga kiran Saifuddeen yazo ya taimaka ya fidda ta zata shid'e bata iya fita amma Saifuddeen ko jiyowa beyi ba har ya shige.
  Nan Jamil yaje aguje ya d'auko sweeper wacce zarah ta saki a lokacin da Saifuddeen ya fizge ta.
  Ya tafi da saurin sa  ya miqa mata sweeper d'in yace ta kama ya fidda ta.
 Da qyar zarah ta iya kamawa,da hakan jamil ya tafi da ita sannu a hankali har gurin matattakala ta tattaka ta fito,jikinta se wani irin qyarma yake ba sauqi ko tsayuwa bata iya yi se zubewa tayi kan guiwoyin ta,kanta qasa ta kame hannuwan ta sosai a qirjinta tana fmn rawar d'ari.
 Cike da tausayi jamil ya cire suit jacket d'isshi ya rufa mata yana kallon ta idanuwan sa tap da qwallah yace"tashi muje kafin sanyin nn ya miki illah ki samu ki shiga ruwan zafi kinji.
 Gyad'a masa kai zara tayi tare da share hawayen da suka zubo mata snn ta tashi.
Koda suka zo bakin qofar shiga falon se ga Saifuddeen ze fito wanda still yana rungume da kitty a jikinsa riqe da makullin motar sa zai kai ta veterinary hospital.
 Kallon sa jamil keyi cikin qunan rai yace"mahaukaci kawai marar imani akan kyanwar banza zaka nemi illata rayuwar d'an adam da bata da laifi ko d'aya.....kaga dakata da Allah! da akwai marar imani mahaukaciya banza irin wnn!
 Saifuddeen ya fad'a tare da nuna zarah snn yace"kalli wancan plate d'in kaga shi zai tabbatar maka cewa da sanin ta komai ya faru dmn kitty baza ta ta6a d'auko plate d'in abinci da kanta ta fito dashi ba,itace munafukar da ta wurgo ta tare da plate d'in abincin ta rufe qofa ta barta ta kwana a waje tasa duk ruwan da akayi a daren jiya suka qare a kanta,very stupid! wlh duk wani abu ya sami kitty ki kuka da kanki!
   Daga haka ya wuce ya var su tsaye a gurin.
Jamil ya kalli zarah ita ma ta kalle shi idanuwan ta tap da qwallah ba tare da tace masa komai ba ta shiga daga ciki.

Sha biyun rana tana kwance kudundune cikin blanket sbd zazza6in da ya saukar mata tana ji se knocking ake ta mata a qofar d'akin ta ta samu da qyar ta tashi taje ta bud'e qofa.
Wata ta gani da baza ta wuce 22yrs ba tsaye a bakin qofar,da fara'ar ta tace"sannu ni qanwar yaya jamil ce ga wnn magunguna ne yace na kawo maki kowanne da akwai yanda zaki sha shi a rubuce"
  Zarah ta kar6i ledar magungunan,muryar ta a hankali mai cike da jin zazza6i tace"nagode"
  Murmushi kawai yarinyar ta mata snn ta wuce taje ta sami jamil a waje yana jingine jikin motar sa yana jiran fitowar ta.
  Tana qarasowa ya tashi daga jinginen  da yake tare da fad'in"hope she is doing ok sanyin be riga ya kamata ba dai ko?
  Tace"inafa har zazza6i ya kamata ai,se ma kaji irin yanda jikin ta yayi zafi da zata qarfi ledar magunguna a hannu na naji hannun ta kmr garwashi.
  Oh no!to kin mata bayanin yanda zata sha magungunan?
  Aa kawai dai nace ta duba kowanne da akwai yanda zata sha.
  No zainab ba haka ba plz koma kiji idan taci abinci se ki 6a66alla mata magungunan ki bata tasha,idan kuma bata ci abinci ba ki samu abunda kika d'an dafa mata me sauqi taci kinji zanje na dawo.
  "Ok to"
 Ta fad'a snn ta koma daga ciki.
  Zarah wacce ana bata magungunan ta kaisu kan bedside drawer ta ajiye,ta kwanta knn ta koma jin knocking,ba yanda ta iya haka ta taso ta bud'e qofa.
  Zainab tace"yi haquri se damunki nake tayi,yaya ne yace na dawo na miki bayanin yanda zaki sha magungunan.
  Hanya Zarah ta bata tare da fad'in to shigo daka ciki.
  Zainab ta shiga ta d'auki ledar magun gunan ta ciro su snn ta kalli zarah tace"kinci abinci na 6alle miki magungunan kisha?
  A hnkli Zarah ta girgiza kanta alamar bata ci ba
 zainab tace"Ok to me zan dafa miki?
  A'a ki barshi nagode ko tea zan had'a na sha...No abu me d'an nauyi ya kamata kici idan akwai indomie zan dafa miki kina so?
   "Eh"
zarah ta fad'a nn zainab ta ajiye mayafinta ta fita.
  Tana cikin dafa indomien ne jamil ya kirata a waya acewar tazo ya dawo yana a farfajiyar gidan.
  Taje ta same shi ya miqa mata er qaramar farar ledar pharmacy dake hannun shi yace"allurai ne a ciki plz ki mata a hankli kar ki jiwa matar mutane ciwo"
  A hnkli Zainab ta lumshe idanun tare da ware su akan shi snn tace"haba dai yaya se kace ba aikina ba kuma ko dan kai ae dole na bita a hankli gudun kar nayi laifi.
  Yace"to iyayen surutu jeki ki mata ina jiranki kizo mu tafi"
  Tace"ai bata ci abinci ba shine nake dafa mata yanzu"
Ya girgiza kansa tare da fad'in"Allah sarki zarah,kawai to ki tsaya ki mata duk abunda take so snn idan kin kammala se ki kirani nazo na maida ki gida.
  Ok to.
 Zainab ta fad'a snn ta koma daga ciki.
  Bayan ta gama dafawa zarah indomie har ma zarah d'in taci snn ta shiga had'a allurai,zarah se kallonta take ita wa zatayi wa allura to dan dai taga kmr tayi qarama da iya allura har ta ma mutum.
  Murmushi zainab tayi tana mai kallon zarah sbd yanayin fuskar zarah kad'ai ya isa ya bayyana abinda ke zuciyar ta,tace"kar ki damu ni ma'akaciyar asibiti ce karatun da nayi knn fannin nurse.
  D'an murmushi zarah tayi dan haka kawai taji ta birge ta.
  Bayan zainab ta mata allura ne ta tambaye ta ko da akwai wani abunda take so ta mata kafin ta tafi,tace"ba komai nagode.
 Murmushi Zainab ta mata cikin kad'a kanta alamar ba komai snn ta kira jamil yazo ya tafi da ita.

Tun fitar Saifuddeen se bayan zuhur ya dawo gidan rungume da kitty a jikin shi wacce ta d'an walwale ba kmr d'azun da ya fita da ita ba.
  Kae tsaye d'akin sa ya nufa d'ayan hannun sa riqe da ledar takeaway d'in da ya siyo.
  Har dare be sake fita gidan ba se aikin faman jinyar kitty yake.
  Zarah kuwa tunda zainab ta bar gidan ta kwanta bacci koda ta tashi zazza6in ya d'an mata sauqi,sai dai sosai mura ta kamata da dare ko baccin kirki bata iya yi ba da qyar taga safiya.
  Koda akayi kwana biyu muryar ta duk ta shaqe bata wani fita sosai,ga masifaffen ciwon kai da mura ta sako mata,ko yaushe tana kwance ko girki bata iya yi se idan Zainab tazo duba ta ne take mata girki dama duk wani abunda take so snn ta tafi.
  Washe gari ta kasance Wednesday Alhmdlh ta d'anji sauki ba kmr sauran kwanaki ba dan yau da kanta ta fito kitchen tana girka abincin da zata ci.
  Tana kitchen d'in ne ta soma jin qarar doorbell,a tunanin ta ko Zainab ce tazo amma koda taje ta bud'e qofa se taga Jamil.
  A natse ta gaida shi ya amsa tare da tambayar ta ya jikin nata tace mishi taji sauqi.
    Snn yace Saifuddeen fa ko yana nn?
  Gyad'a masa kai tayi alamar eh sbd d'azu kafin ta fito taji shigowar shi.
 Yace"plz kira min shi kice masa gani nazo ina magana"
  "To"
Tace tare da bashi hanya ya shigo yaje ya zauna,har takai gun staircase zata haura sama se kuma ta dawo ta durqusa kanta qasa tana riqe da en yatsun ta snn muryar ta a hankli tace"yaya dan Allah idan ba damuwa in yazo ina son gobe ya barni in tafi gida naga su umma,ina gudun na tambaye shi yace bazan je ba.
  Jamil dake kallonta yace"ok ba damuwa in yazo zanyi magana dashi.
  Godiya ta mishi snn ta tashi ta haura sama zuwa d'akin Saifuddeen.
  Knocking d'in farko ana biyu ya bud'e qofa.
 Farar singlet ce a jikin shi se dogon wando jeans fuskar sa ba yabo ba fallasa yake kallonta,tun rnr da ya jefa ta sweeming pool be sake sata a idon sa ba se yau wanda yasan ta kamu da rashin lfy ne sbd yana ganin shiga da fitar da zainab keyi a gidan suna had'uwa har su gaisa and yasan ba kowa ke turo ta ba face jamil.
Sau d'aya zara ta kalle sa ta kauda idonta tare da gaya mishi yaya Jamil keson ganin shi.
  Daga haka ta wuce ba tare da ta jira me zai ce ba.
  Ya sauko ya sami Jamil ya zauna yana me kallon sa fuskar sa a d'aure yace"lafiya?
  Murmushi Jamil yayi snn yace"Buddy knn yanzu akan kitty kake fushi dani haka,baka d'aga waya ta snn idan naje office d'inka baka saurara ta and yanzu nazo ka wani d'aure min fuska har da fad'in lafiya knn me ya kawo ni gidan ka ko?
    Saifuddeen dake kallon sa yace"wa ya gaya maka akan kitty ne,nifa ka 6ata min rai ne sosai,wai kan wnn banzar yarinyar zaka zazzage ni har kana gaya min magana marar dad'i a kanta,abinda be ta6a faruwa a tsakanin mu ba tun muna yara har girman mu,a gskiya kasani tun wuri ka ajiye dmn bazan d'aukar maka ba wlh.
  Jamil ya numfasa tare da fad'in"calm down yi haquri raina ne ya 6aci ba kad'an ba and kai d'in ne baka kyauta ba wlh dmn na tabbatar Zarah bazata wurgo kitty kamar yanda kace ba may be ta bar qofar a bud'e ne har kitty ta fita bata sani ba.
  Hm jamil knn shi kuma plate d'in abincin fa ko shima qafafu yayi ya biyo kitty suka fito tare.
   Jamil yace"kaga Saifuddeen koma dai mene hukuncin da kayi wa zarah is hard,marin ta fa kayi ina kallo snn kaje ka jefa ta a cikin ruwa masu masifar sanyi wanda hakan ya janyo mata zazza6i da mura still har yanzu kana jin muryar ta bata fita sosai duk sbd wata banza can kitty.
  Hararar sa Saifuddeen yayi tare da fad'in kar ka sake.
Jamil yace"Kaji zafi ne sbd na kira kyanwar masoyiyar ka banza,ni kuma fa da kake kiran zarah banza a gabana ka san irin zafin da nake ji kuwa.
  Cikin d'aga kafad'a Saifuddeen yace"Oho maka ka bari idan na sake ta ka aure ta qauna yasa ka had'iye ta in ka iya amma ba yanzu da take qarqashin ikona ba dole kayi haquri da duk wani abunda kaga na mata.
   Jamil yace"Shikenan Allah ya nuna min ta dawo qarqashin ikona ta huta da qiyayyar da kake nuna mata.
  Saifuddeen yace"ko dai ni na huta da jarababben auren ta ba.
  Jamil dake kallon sa girgiza kansa kawai yayi.
 Snn ya numfasa tare da fad'in"ka dai rage wani abun dan gashi yanzu kan shakkun ka tana son zuwa gida but she can't ask u.
  Ta6e da baki Saifuddeen ya kalle sa yace"Au shine se ta gaya maka,to tafi ruwa gudu duk inda zata je ita ta sani Allah yasa ma in taje kar ta dawo".
  Murmushi kawai Jamil yayi yana kallon sa be ce masa komai ba.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Monday 19/02/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 17*
"Ke!
kawo masa lemu!"
Saifuddeen ya fad'a cikin d'aga murya ta yanda zarah zata iya jiyo shi har kitchen.
  Snn ya tashi tare da cewa Jamil bari naje na sako riga muje gidan Hjy na kwana biyu banje na ganta ba.
  Jamil yace"Ok to"
Kafin Saifuddeen ke wuce wa ya haura zuwa sama,nn se ga zarah tazo d'auke da qaramin tray da juice da kuma cup akai ta ajiye kan stool snn ta tsiyaya mishi lemun a cup ta bashi,ya kar6a tare da fad'in"nayi magana dashi yace kije,gobe da safe se ki shirya zan turo Zainab ta kai ki inshaa Allah"
  Cikin nuna jin dad'i ta masa godiya snn ta wuce.
  Washe gari koda 11 tayi ta kammala shirin ta tsaf cikin wani dakakken lace dake cikin kayan lefen ta,lace d'in baqi ne da akayi zanen manyan flowers baby pink in colour se lace d'in ya mata kyau sosai sbd d'inkin riga da skirt ne da yayi d'as a jikinta.
  D'an kwali riqe a hannun ta ta rasa ta yanda zata d'aura sbd ba iya d'aurin d'an kwali tayi ba gashi da girma.
  Ba yanda ta iya se kan bed taje ta shinfid'a shi ta kama gefe da gefe ta linka snn ta d'auka ta d'aura ba tare da tayi wani style ba amma baya se yayi kmr tush sbd yanda tayi rolling d'in d'an kwalin a kan parking d'in sumar kanta da tayi a tsakiya,yayinda jelar gashin nata se reto yake har yana ta6a gadon bayan ta bata kama shi ta dunqule a ciki ba,se gyale ta d'auka ta yafa a kanta baby pink in colour tsadadde me kyau irin na matan manya.
 Tasa takalmi snn ta d'auki jaka ta fita da sauri sbd doorbell da ake ta fmn dannawa bata son 6atawa Zainab lokaci.
  Sai dai koda ta bud'e qofa ba zainab bace kmr yanda take tunani Jamil ne wanda tana bud'e qofar ya sauke idanun sa akanta se kallonta yake bako qyaftawa dmn ba qaramin kyau ta mishi ba,duk da bata wani qware da yin ja gira ba kmr yanda Nusaiba ke koya mata amma yanda ta jata d'in tayi kyau ba laifi,snn ta shafa powder dai dai bata yi yawa ba bata yi kad'an ba,ba abinda ma yafi birge shi kmr shafin kwallin ta,dmn kwallin ya hau kan idonta dai dai yanda ake so wanda hakan ya bayyanar da ainihin kyawon idanuwan ta manya dasu farare qal,kana ya tafi da idanuwan sa a hnkli kan d'an madaidai cin bakinta da ta shafawa janbaki pink me haske wato klr flowers d'in less d'in ta snn tayi lining with dark pink lip pencil liner.
 Se duk yaji ya qara sonta kan yanda ta yafa gyalen ta tun daga saman kai dmn shi dai ko kad'an baya son irin yafin gyalen da yaga en matan yanzu nayi yafi son yaga mace cikin mutunci da kamala.
  Can ya tsinkayo muryar ta tana gaida shi,ya kauda fuskar sa a hnkli a ransa yana fad'in subhanallah! tare da yin istigfari dan be san ma ya shagaltu da kallon ta haka ba.
Snn ya amsa mata gaisuwar tare da fad'in"kiyi haquri Zainab baza ta sami zuwa ba tana asibiti aikin safe take dashi yau,but muje mu sauke ki Saifuddeen yana a waje yana jiran mu.
  To tace tare da binshi a baya suka fita.
  Jamil da kanshi ya bud'e mata gidan baya ta shiga shi kuma ya zagaya ya shiga gaba gurin me zaman banza.
  Tsaki Saifuddeen yaja tare da jan motar ransa a 6ace.
 Kallon sa kawai jamil yayi ba tare da yace masa komai ba har suka isa.
  Basu shiga ciki ba zarah kawai suka sauke suka wuce.
  Koda ta shiga falo ta had'u da Abba ze fita umma ta rako shi.
  A natse ta durqusa har qasa ta gaida su.
  Cike da fara'a suka amsa mata gaisuwar snn ta tashi se kallon ta suke ganin yanda tayi kyau kmr ba ita ba.
  Abba yace"ina Saifuddeen d'in yake da kika shigo ke kad'ai?
  Tace yanzu suka wuce shida yaya jamil kmr sauri suke da akwai inda zasu je.
 Ok to inace dai lafiya lau kuke zaune ko?
 Tace"lafiya lau"
  Mashaa Allah Abba ya fad'a snn ya kalli umma yace"to ni zan fita se na dawo"
  Tace"a dawo lafiya"
 Ya fita su kuma suka haura sama zuwa d'akin umma.
  kan sofa suka zauna umma na kallon zarah da kulawa tace"har yanzu dai murar nn bata rabu dake ba kina shan magani kuwa?
  Zarah tace"Eh inna ina sha ae kinji murya tawa ta d'an sake ba kmr farko ba.
  Haka ne ina ce dai bada ruwan sanyi kike wanka ba har murar nn ta kama ki.
  Tace"A'a inna ni da ruwan zafi nake wanka,wnn sanyin ina zan iya wanka da ruwan sanyi,na kamu da ita ne kawai.
  Umma tace"to Allah qara sauqi"
  Ameen su Nusaiba fa yau da wuri suke dawowa koh?
  Eh da wuri suke dawowa qarfe biyu tun jiya take zancen yau idan sun dawo gidan naku zasu tafi  in yaso su dawo kafin me lesson d'in nasu yazo se gashi kinxo.
  Eyyah jiya da muka yi waya se bata gaya min ba amma kuma ni dama na matsu da inzo gida duk kad'ai ci ya min yawa,satin nn uku naji kmr watanni har so nake ma inje rimin dako in ga inna itama ina kewar ta sosai.
  Umma tace"Rimin dako kam ba yanzu ba duka duka yaushe ne akayi auren da har zaki je,ki dai bari zuwa wani lokaci snn.
  A d'an shagwa6e tace"amma inna kinsan halin shi bazai ta6a cewa in tafi ba,ko yanzu da nazo seda na tambaya dan na fahimci ba zai ce nazo d'in ba tunda shi kullum yana zowa yana ganin ku baya da wata kewa.
  Kar ki damu da zarar naga lokaci yayi da kaina zan mishi magana se muje gabad'ayan mu ko?
 Murmushi tayi cike da jin dad'i.
   Snn ta cire mayafin ta ta ajiye suka tafi kitchen tana taya umma girki.
   Bayan su Nusaiba sun dawo ne har ma sunyi wanka sun ci abinci tana zaune ita da Zarah su biyu a d'aki se fira suke a cikin firar su ne Nusaiba ke cewa"ni kuwa 6ter ya plan d'in mu shiru har sati d'aya banji kin fara bani bayani ba.
   Zarah tace"inafa ni ban fara gwada wa ba tukun zazza6in mura be barni ba kullum da ciwon kai nake fama yanzu haka ina d'an jin shi se dare yayi na kasa bacci.
  Ikon Allah wnn wace irin mura ce haka yaya ya siyo miki magunguna kuwa?
  Hm Nusaiba knn yaya jamil dai ya tura qanwar sa zainab ita keta kula dani tana duba ni dama girki duk ita ke min in tazo dan ko fitowa bana iyayi daga d'aki se d'aki.
   Da mamaki Nusaiba ke kallonta tace"kuma shine se baki fad'i yanayin da kike ciki ba kika ce mura ce kawai ke damunki ashe har kwantawa kika yi.
  To Nusaiba duk a dalilin muguntar yayanki ne fa,bansan ta yaya zan fad'i abun ba dmn ko kad'an bana son su umma su san yanayin da nake ciki da yayanki duk da dai sun san kafin aure ba qaunata yake ba.
    Nusaiba ta girgiza kanta tare da fad'in"Oh Allah wane muguntar kuma ya miki har hakan ta faru?
   Zarah tace"A dalilin wnn farar kyanwar ne da yake kira kitty,ze yi tafiya ya kawo min ita wai na kulata da ita har ya dawo nace masa bazan iya ba sbd ina mugun tsoron ta kuma ya sani amma ya tafi abinshi ya bar min ita.
 Nan ta gayawa Nusaiba duk yanda akayi.
  Nusaiba tace"Hm lallai yaya,ya ubangiji Allah ka sauya mishi wnn halin,kiyi haquri inshaa Allah shida kansa ze dawo yana nadamar abubuwan da ya aikata miki.
  Shi ya sani ni ina zama dashi ne kawai sbd biyayya duk abunda ze min Allah ya fishi wahala bata kisa,idan kuma na mutu a dalilin muguntar sa shikenan haka Allah ya qaddara zan zama tarihi.
  Nusaiba tace"baza ma ki mutu yanzu ba inshaa Allah har se kun zama cikakkin masoyan gaske kun haifi 'ya'ya har ma da jikoki.
  Ta6e baki Zarah tayi snn tace"hm da kin tashi kinyi abinda ke gabanki ma da yafi kafin me lesson d'inku yazo".
   Ta qarashe mgnr ne tare da kwanciya sbd headache d'in da ke damunta.
   Nusaiba dake kallon ta tayi murmushi kawai snn ta tashi.
   Har bayan sllr isha'i tana gidan bata koma ba umma ta shigo d'akin ta sami Nusaiba tasa yusra a gaba tana mata homework,zarah kuwa na kwance kan dardumar sallah,umma tace da ita"tashi ki tafi gida gasu Saifuddeen nn sunzo suna jiranki a falo.
  Muryar ta a hnkli can ciki tace"wlh inna kaina ke min ciwo sosai,in na tashi har ji nake kmr ze tsage dan Allah a barni zuwa gobe se in koma"
  Umma dake kallon ta a hnkli takai hannu tana ta6a goshinta zuwa jikinta duk yayi zafi sosai.
  Ga handkerchief  manne a hancinta duk murar ta dawo mata sabuwa se fmn sharewa take.
  Umma tace"wai murar nn ce ke sako miki ciwon kan nn da zazza6i.
  Zarah tace"eh wlh inna haka nake fama duk dare se ta dawo min sabuwa abun ba sauqi ko baccin kirki ma bana iya yi kullum ina shan magunguna amma kmr ba nasha in dare yayi.
   Bari naje to na sami Alhj.
 Umma ta fad'a tare da fita d'akin.
 Kae tsaye downstairs ta sauka sbd Abba yana can tare dasu Saifuddeen.
  Tana saukowa ta tsaya sbd shima ya kawo knn zai haura sama.
 Yace"ya akayi ina Zaran take ne?
 Tace"Zarah na can kwance tana fama da ciwon kai kasan mura take fama da ita kwanakin nn ashe ko baccin kirki ma bata iya yi yanzu haka jikinta duk yayi zafi,shine take son a barta ta kwana a nn gobe idan jikin nata ya mata sauqi se ta koma.
  Shiru Abba yayi snn ya juya yana mai kallon Saifuddeen da jamil ke magana dashi qasa qasa yana fad'in"kaji abunda ka jawa er mutane ko,tun rnr har yanzu se wahala take da mura kwata kwata baka damu ba se nine nake tura zainab tana duba ta bayan kai ya kamata ace kana kula da ita.
  Saifuddeen yace"kaji min na kula da ita sbd me,ajiye ni tayi ko ka manta duk ita ta janyo wa kanta ba uban da ya aiketa,kuma ko gobe ta sake wanda yafi wnn zan mata ta dad'e bata mutu ba.
  Kallon sa jamil yayi se yayi shiru be ce komai ba sbd Abba da umma da suka qaraso gurin su.
 Abba yace da Saifuddeen kai dan ciwon ba a jikin ka yake ba shine zaka barta tana ta faman wahala haka tsawon kwanaki kuma hankalin a kwance.
  Muryar sa a natse cikin ladabi yace"to ya zanyi ne Abba magunguna da allurai ba wanda bata sha ba snn idan na fita aiki bana barin ta ita kad'ai a gidan zainab nake turawa tana kula da ita,murar ce kawai taqi ta rabu da ita amma ina iya qoqarina.
  Abba ya numfasa yace"ae na d'auka ko ka zuba mata ido ne kawai amma tunda hakane ka tafi se gobe kazo ka tafi da ita sbd yanzu tana can kwance bata jin dad'i.
  Shikenan Abba,Allah ya bata lafiya kana ya kalli jamil da duk ya cika da mamakin sa yace muje na sauke ka ko.
  Abba yace"tukuna je dubata kafin ku tafi mana.
   Cikin nuna jin kunya ya sosa bayan kansa tare da fad'in ae ba se na duba ta ba Abba ko Zainab zan turo ta duba ta.
  Daga haka ya fita ba tare da ya jira me Abba zei ce ba,shima jamil ya tashi ya musu sai da safe snn ya fita.
  D'auke da murmushi Abba ya girgiza kansa ya kalli umma yace"wae yaron nn fa hankali ne ya fara,kuma ni ganin nake kmr ciki ne da Zarah shine laulayin yazo mata da mura.
  Umma tace"ciki Alhj da wuri haka duka duka yaushe ne auren ko wata d'aya fa ba'a yi ba.
   To maman yusra in banda abinki ae shi ciki ba dole se yakai wata d'aya yake fara nuna alamomin sa ba,duk da anyi auren nn baya so amma kmr kar ayi kwana biyu se naga ya saduuda dan haka ba abin mamaki bane ko cikin ne kinsan yaran yanzu.
  Umma tayi murmushi tare da fad'in"to Allah yasa hakane"
 Abba yace"Amin amin muje naga ya jikin zarah d'in yake.
  Nan suka haura sama zuwa d'akin su Nusaiba.
Saifuddeen kuwa koda ya fita dariya yake ji sosai ganin yanda jamil duk ya cika da mamakin sa,ya shiga mota knn se ga jamil shima ya shigo yana kallon sa yace"kaji tsoron Allah"
   Saifuddeen ya tashi motar d'auke da dariya yana fad'in"au da kai nake tsoro to".
  Jamil dake kallon sa yace"u better change ur life wlh yanzu kasa su Abba sun yarda da gaske kana bata kulawa bayan kuwa ba haka bane,kawo ta da mukayi ma da d'aukar ta da muko zo yi,duk da masifa da komai ka yarda amma shine harda wata kunyar munafurci kake masa sbd kawai baka so kaje ka ganta ba damuwar ka bace koh.
Saifuddeen da still dariya na kan fuskar shi yace"kaga ba wani munafurci a ciki ko wai rashin damuwa da ita,ni hikima ce tasa nayi hakan amma se nn gaba ko zaka gane.
  Jamil yace"kai ka sani Allah ya shirye ka.
 Saifuddeen ya kalle sa kawai d'auke da murmushi kana ya maida hankalin sa gun tuqi.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Tuesday 20/02/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 18*
Washe gari da qarfe goman safe tuni Nusaiba da yusra suka wuce zuwa school.
  Abba na zaune shi kad'ai kan dining cikin shirin sa na fita yana breakfast se ga umma ta sauko daga upstairs tazo taja kujera ta zauna tare da ajiye cup d'in da ke hannunta.
  Abba dake fuskantar ta yana kallon ta yace"ya akayi naga kin dawo da oats d'in kmr bata sha ba?
D'auke da murmushi umma tace"hm ina ga dai Alhj zancen ka ne juna biyu ne da Zarah kasan duk son nn da take yiwa oats,ina ce mata gashi da saurin ta tace min um um bata sha,arish da qwai kawai zata ci shine na bar mata na dawo da oats d'in.
  D'auke da jin dad'i Abba yace"haqiqa dana fi kowa farin ciki idan ciki ne da zarah dmn kinsan bani da babban buri irin na fara ganin en jikokina kafin na bar duniya.
   Umma tace inshaa Allah kuwa baza ka bar duniya ba har se ka gansu.
  Amin amin Allah yasa.
Abba ya fad'a fuskar sa fal fara'a.
  Snn yace"jiya ina Allah Allah na tambaye ki da Zainab tazo ta duba ta me tace?
  Bata ce komai ba kawai dai tayi mata allurai snn ta bata wasu magunguna kuma Alhmdlh da safen nn se jikin nata yayi sauqi,but ko za'a mata pregnancy test ne mu tabbatar da abunda muke zargi.
  Yace"A'a ba se anyi ba ae me bayyana kansa ne in shine,zancen makarantar ta dai kin gaya mata cewa an samar mata addimission?
  Aa ban snr da ita ba tukun.
 To ki snr da ita idan Allah yasa taji sauqi se ta fara zuwa zanyi magana da Saifuddeen ya samar mata driver da ze riqa kaita yana d'auko ta sbd shi aiki yake zuwa ba lallai bane fitar su ta zama d'aya.
   "hakane"
Umma ta fad'a snn daga haka basu sake cewa komai ba,se breakfast da suka ci gaba da yi,suna kammalawa Abba ya fita.

Duk da zarah taji sauqi a nn ta yini har se bayan isha'i snn Saifuddeen yazo d'aukar ta su koma gida.
  Kafin su tafi sei da Abba ya zaunar dasu,shi yana zaune kan doguwar kujera 3seater shida umma su kuma suna zaune a gaban su kan rug kansu qasa Abba yace da Saifuddeen"idan Allah yasa zarah ta qara jin sauqi zata fara zuwa makaranta a BUK na samar mata addimission se ka samar mata driver da ze riqa kaita yana d'auko ta idan kuma kana ganin zaka iya lalurar da kanka shikenan ba se ka nemi wani driver ba.
  Yace"A'a Abba gwanda a samo mata driver zai fi dan ni bani da wnn lokacin"
  Yace"shikenan amma kasan irin drivern da zaka samar mata wanda ze riqa tafiya da ita a hankli tunda kaga yanzu ba ita kad'ai bace.
   Da saifuddeen har zarah d'ago kai sukayi suka kalli Abba se kuma basu ce komai ba suka sake sadda kansu qasa.
  Saifuddeen yace
       "to"
cikin jin zancen wani iri.
Zarah kuwa bata ko wani fahimci me Abba ke nufi ba.
  Umma tace"kina ji ke kuma zarah koda Allah yasa kin fara zuwa makaranta ki kula da irin abokanan da zaki riqa huld'a dasu mace ce ke kuma matar aure dole se kin kula da mutuncin kanki sosai snn kuma ki maida hankali sosai akan karatun ki sam kada kisa wasa kina jina ko"
  Eh inn...mama.
Wacce tayi saurin canza sunan ne sbd wani irin mugun kallo da Saifuddeen ya mata a kafaice ba tare da su Abba sun lura ba.
  Abba yace"shikenan Allah muku albarka ku tashi ku tafi.
   Nan suka musu sai da safe snn suka fita.
 Motar jamil ce fake yayinda jamil d'in yana ciki zaune a mazaunin driver yana jiran fitowar su,zarah ta bud'e  gidan baya ta shiga,Saifuddeen kuma ya shiga gidan gaba 6anagaren me zaman banza ya zauna snn jamil yaja motar suka tafi.
  Da isar su zarah ta bud'e ganbun motar ta fita Saifuddeen ya bita da kallo har se da ta shiga daga ciki snn ya kalli Jamil yace"mutuniyar ka fa ciki ne da ita.
 A razane jamil ya kalle sa yace"wake da ciki Zarah!
  Saifuddeen yace"Eh haka Abba ya fad'a nasan a tunanin sa zazza6in murar da take ne ya d'auka ko laulayi ne,shine da ya min zancen school d'inta yake ce min nasan irin  drivern da zan samar mata wanda ze riqa tafiya da ita a hnkli sbd ba ita kad'ai bace.
   Yayi dariya snn yaci gaba da cewa"kae Abba knn shi ko ce masa akayi na kama hannun wnn abar da niyyar wani abu ya shiga tsakani na da ita ze yarda bare har in kai ga mata ciki Allah sauwaqe har abada wlh.
  jamil dake kallon sa ya sauke nannauyan ajiyar zuciya snn yace"plz saif kasan irin yanda zaka faro magana wlh kasa na razana ba kad'an ba har se da kaina ya mugun sara min.
 Ta6e baki Saifuddeen yayi yana me kallon sa a wulaqance yace"u have gone mad!
a tunanin ka da kaji farkon zancen se ka d'auka ko na mata cikin ne da gaske shine har da su razana da wani ciwon kai to hankalin ka ya kwanta ni har abada bata a gabana,kaida jarabar sonta ya same ka se kayi tayi har Allah yasa ka same ta.
  Ya buga tsaki tare da bud'e ganbun motar ya fita Jamil ya bisa da kallo tare da yin murmushi snn yaja motar sa ya bar gidan.

Washe gari ta kasance saturday bayan zarah tayi share sharen gidan da ban ruwan flowers har ma tayi breakfast taci.
  Taje d'aki ta bud'e akwatinan lefen ta tana neman tufafin da zata sa idan tayi wanka.
  Wasu qananun kaya ta ciro riga da wando skinny,rigar milk ce wandon maroon,ta kaisu kan bed ta ajiye,snn ta wuce zuwa bathroom.
 Can se ga Saifuddeen ya shigo d'akin,wanda da shigowar sa ya sauke idon sa akan kayan da ta fitar zata sa,d'an ta6e bakin sa yayi tare da kauda idon sa a kan kayan snn ya kalle ta har ta fito daga wanka tana kwance a rigingine kan bed d'aure da d'an guntun towel a jikin ta tana bacci qafar ta kan d'aya.
  A hnkli ya qarasa gurin ta yayi tsaye fuskar sa ba yabo ba fallasa ya kafe idon sa se kallon santala santalan cinyoyin ta yake har zuwa tafin qafafuwanta da suke tas basu da wani datti bare qwarzane very smooth kmr na jarirai,snn sun lanqwasa cike da kyau kmr sirdi en dai dai.
Kana ya rankwafa gab da ita yasa hannun sa a hnkli kmr da tsoro ya shafi gashin kanta dake barbaje kan pillow.
 Sanyin ruwa yaji a tare da sumar wato ma da fitowar ta wanka ne bacci yayi awon gaba da ita.
  Mamaki yake a ransa wane irin bacci ne wnn kaddai mgnr Abba ce ciki ne da yarinyar nn"
  Nan yakai duban sa gun hannayen ta da ke kan cikinta ta saqale en yatsun ta,yakai hannun sa a hnkli ya kama d'ayan hannun ta ya zare shi daga saqale sun da tayi ya riqa en yatsun ta kan tafin hannun sa se kallon su yake,sam bai ga wani alamar ciki a tare da ita ba,ya sakar mata hannu snn ya matsa sosai zuwa fuskar ta yasa en yatsun sa biyu ya gwale mata ido,da yake bata da wani nauyin bacci sosai,ta tashi firgigit tana kallon shi snn da sauri taja blanket ta rufe jikinta har zuwa wuyanta tana kallon sa tace"meye haka?
  Komai be ce mata ba se kumatun ta ya kama da duka tafukan hannayen sa biyu yana kallon cikin qwayar idonta,still be ga alamar da yake nema ba,nn ya tuna cewa mura take ba makawa magungunan da take sha ne suke sata bacci.
  Fuskar sa a d'aure yace"Ke kinsha magani ne yau da safen nn?
   Zarah dake kallon sa da kmr mamaki tace"eh nasha duka kowanne"
 yace"to ki daina shan su haka, wawiya kawai tun d'azu umman kd tazo kin zo se bacci kike sbd ba uwar ki ce tazo ba ko"
  Kallon sa kawai zarah keyi ta fahimci ga alama be san ma ya take da su umma ba shi ne yake ta wnn haukar,dan ita a hauka ma ta d'auke shi shiyasa har ya qaraci masifar sa ya fita bata ce dashi komai ba se tashi tayi ta nemi wasu kayan atamfa riga da skirt tasa snn ta fito zuwa downstairs se murna take da ganin umman kd dake zaune kan doguwar kujera,Saifuddeen na zaune gefe kusa da ita riqe da lemu yana tsiyaya mata a cup.
 Taje ta durqusa har qasa tana gaida ta cikin harshen fulatanci.
   Itama cikin harshen fulatanci ta amsa mata tare da kama hannun ta ta zaunar da ita a kusa da ita,ta d'an bawa saifuddeen baya,fuskar ta a sake tana kallon zarah da kulawa se magana suke cikin harshen fulatanci,Saifuddeen kallon su kawai yake baya jin komai,kawai dai ya fahimci sun san juna ba yau ba hkn na nufin knn dai zarah er uwar su ce da gaske nn dai ya basar da zancen ya miqawa umman Kd lemu ya tashi ya bar musu gurin.
  Da zata koma se da ta zaunar da su tana basu shawarwarin yanda zasuyi haqurin zaman aure su zauna lafiya a tsakanin su ba tare da wani yaji kan su ba.
  Da zarah har Saifuddeen kansu qasa sunyi shiru se sauraren ta suke har ta gama advising nasu snn ta tashi suka raka ta har mota bayan ta tafi kowannen su ya kama gaban sa.
Bayan kwana d'aya rnr Monday da Asuba zarah na bacci sam bata ji kirayen kirayen sllr da ake tayi ba,se saukar ruwa taji masu masifar sanyi  saifuddeen ya kwara mata su kan fuskar ta.
 Ta tashi a firgice tare da jan numfashi da qarfi snn da sauri ta zame daga kan gadon ta zauna qasa dirshan tare da rirriqe gefen gadon sosai,se goga goshin ta take akai sbd wani irin masifar abu da taji ba sauqi yana yawo a cikin goshin ta har zuwa qwaqwalwar ta kan yanda ruwan sanyin suka ratsa aguje cikin hancinta a lokacinda ya kwara mata su.
 Saifuddeen dake kallonta da sauri ya nufe ta ya d'ago kanta yana kallon yanda jini ke fitowa ta hancinta sauri sauri,ba shiri ya d'aga kanta sama ta yanda jinin zei daina zubowa,ta fizge kanta ta maida qasa jinin naci gaba da zuba.
A fusace ya sake d'aga kanta da sauri yace"kina hauka ne ba kya ganin yanda jini ke fita wae.
  Bata damu ba se koma fizge kanta tayi ranta a 6ace tace"ae kaine mahaukacin,mugu kawai marar imani wlh se Allah ya isar.....ihu ta saki tare da saurin miqewa tsaye taja baya sbd yanda ya d'aga hannun sa ze kai mata mari,ransa a 6ace ya nuna ta yace"wlh mind ur tongue kika sake zagi na se nayi gutsu gutsu da bakin ki er rainin hankli,maza kije ki san yanda zakiyi jinin nn ya tsaya kiyi sllh snn kiyi duk wani abun da zakiyi kafin 8 driver zai zo yakai ki school idan kuma kika 6ata masa lokaci yayi tafiyar sa....yayi tafiyar sa mana ni ba inda zanje da sassafen nn.
  Tana kaiwa nn ta shige bathroom ta barshi tsaye sake da baki yana mamakin wae ba inda zata je da sassafen nn karatun be dame ta ba knn lallai kuwa ze nuna mata yafi ta zama d'an iska dan in shi zai sake mata zancen school zata gani dama ba damuwar sa bane.
  Yayi qwafa snn ya fita daga d'akin ya wuce zuwa masallaci.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Wednesday 21/02/2018_
*«»«»«»SAIFUDDEEN!«»«»«»*




By
  *Billy giro😊*


*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 19*
Zarah kuwa tana shiga bathroom gun wash basin taje ta tsaya tare da d'an rankwafadda kanta har se da jinin ya tsaya mata snn ta wanke fuskar ta ta cire rigar baccinta dan duk ta 6aci da jini ta d'aura towel snn ta fito riqe da rigar baccinta da ta cire ta goge jinin da ya diddiga a d'aki snn ta koma bathroom ta saka rigar a cikin washing machine tayi arwalla ta fito.
  Tana ida sallah a nn gurin tayi bacci se 8 snn ta tashi.
  Koda 10 tayi tuni ta kammala duk ayyukan ta har ma tayi wanka ta shirya cikin qananun kayan ta riga da wando na rannan da d'auko bata sa ba.
  Tayi tsaye a gaban madubi tana kallon kanta se murmushi take kan yanda kayan suka mata kyau sbd basu da wani tsiraici a tare da su.
  Rigar milk ce high neck mai d'an dogon hannu da yakai zuwa guiwar hannun ta,yayinda rigar ta kame jikinta dai dai har zuwa waist snn aka baje rigar like umbrella ta d'an sauka har zuwa cinyoyin ta,se wandon jikinta skinny da ya kasance maroon,gashin kanta kuma ta taje shi yayi kyau ta sake shi ya sauka duka baya bata sa ribbon ta d'aure ba,se zuwa tayi da saurin ta ta bud'e akwatinan lefen ta ta ciro packet na skinny hair ribbons pieces ne kala kala,ta zari d'aya wato klr wandon jikin ta maroon.
  Taje gaban mirror se kallon ribbon d'in take tana d'an jan shi sbd jikin nashi roba roba ne like band,plain ne circle me fad'i fad'i da akwai d'an cliff a qarshen mahad'ar circle d'in da in ka bud'e zeyi sauqi gun d'aurawa kmr yanda Nusaiba ta mata bayani,nn ta bud'e ciff d'in ta d'aura a gaban kanta ta tafi dashi har zuwa bayan kanta snn ta maida cliff d'in ta rufe ya kama kanta sosai yanda ya dace snn a nn gaban kanta ta jashi yayi baya kad'an se gaban kan nata ya wani kwanta sosai baya kuma ya qara sauka ya baje kmr wata baindiya.
  D'an qaramin ihu ta saki tare da yin tsalle ganin yanda tayi kyau kmn ba ita ba babban burin ta knn ta waye ta zama er birni a daina mata kallon er qauye ana wulaqan ta ta.
 "Na fara kamo hanya"
  Ta fad'a ciki rausayawa tana me kallon kanta ta jikin mirror d'auke da murmushin da ya bayyanar da dimples d'inta sosai.
   Kana taje ta d'auki wayar ta dake kan bedside drawer ta d'auki selfie dmn ta turawa Nusaiba ta watsApp ta gani anjima da dare idan ta hau online,sbd se dare take hawa kasancewar bata da wasu frnds daga nadiya ce se Nusaiba kuma dukkan su se byn isha'i suke hawa sbd zuwa school be barsu ba.
  Fitowa tayi abunta ba wani shamaki kmr dama ta saba sa kayan sbd burinta be bar taji wani d'ari d'ari sosai a ranta ba.
Had'uwa tayi da Saifuddeen zata sauka downstairs se gashi shima yazo ze sauka cikin shirin sa na suit navy blue in colour,ta cikin kuma milk,se belt d'insa baqi haka ma takalmin sa,yana riqe da briefcase dake hannun shi.
 Sau d'aya ta kalle sa ba kad'an ba yayi kyau musamman yanda ya taje sumar kanshi ta kwanta luf har zuwa sajen fuskar sa duk ya kwanta baqi me sul6i da ke qara fito da hasken fatar sa sosai,se wani daddadan qamshi ke tashi a jikin shi.
  Kmr yanda ta kalle sa sau d'aya haka shima sau d'aya ya kalle ta amma se da yayi 30seconds kafin yake d'auke idon sa ya maida gun kitty da ta nufo shi aguje sbd kiran da ya mata.
 Zarah na jin ya kira kitty kafin tayi komai se ganin ta tayi girshi tazo aguje ae kuwa a tsorace ta fasa ihu tana neman guduwa  zuwa downstairs,ba shiri tana taka stairs qafar ta ta zame,da sauri Saifuddeen ya saki briefcase d'isshi ya  fizgo ta da qarfi ta fad'o se kan jikin shi.
  Fuskar sa a d'aure yake kallon yanda duk ta cukuikuye shi ya tura ta da qarfi har se da ta fad'i zaune,snn cikin 6acin rai ya shiga kakka6e jikinsa yana fad'in wayiwa kawai mahaukaciya baki ga abin tsoro ba se kyanwa,da na barki kin fad'a kin kakkarye kowa ma ya huta,mtsw!yaja tsaki tare da d'aukar briefcase d'isshi ya sauka kitty na biye dashi har suka fita.
  Zarah da ta bisa da kallo ta miqe tsaye tare da fad'in"masifaffe me ya hana kabar ni na fad'a d'in na kakkarye,mtsw!ban gode ba ma.
  Ta fad'a cikin dallawa qofar fita hararar kyace saifuddeen d'in na gurin.
 Kana ta sauka taje tasa kaset d'in Tom&jerry da ta samo gida gun yusra se kallo take tana kwasar dariya se kace yarinya qarama.
  Har saifuddeen ya dawo gidan tana nn zaune a falon se aikin kallo take tayi,tuni tom jerryn da tasa ya qare ta koma tashar Hausa movies tana kallo.
  Bai ce da ita komai ba haka itama se kallon juna kawai da sukayi ya haura zuwa sama yayi wanka ya sanya farar jallabiya ya fito ze tafi masallaci sllr la'asar,yana saukowa downstairs ya tsaya yana kallon ta se dariya take har da su zamewa daga kan kujera sbd wani gun da akayi me ban dariya a cikin film d'in da take kallo.
  Tsaki yayi tare da girgiza kansa snn ya fita da sauri dan baya son jam'i ya wuce shi.
  Zarah da bata ma san yana yi ba se kiraye kirayen sllh ne ya dawo da ita hankalin ta,ta tashi ta kashe kallon taje zuwa sallah.
  Washe gari da qarfe sha d'aya na safe ta fito kitchen riqe da plate a hannunta soyayyar doya ce me had'e da qwai akai.
  Tana sanye cikin qananun kaya inda rigar komai iri d'aya ce da ta jiya banbanci kawai shine rigar baqa ce dake zagaye da manyan fararen stones kan waist d'inta har baya,se qyalqyali suke kmr diamond,snn wandon jikinta skinny ne fari,haka skinny hair ribbon d'inta ma fari ne da ta jashi ya d'anyi baya gaban kanta ya kwanta yayi kyau,gashi tayi kwalliya abunta ba laifi tayi kyau se qamshi ke tashi a jikinta.
  Jamil ta gani shida saifuddeen zaune a falo takardu a gaban su suna d'an wani aiki da laptop.
  Ta gaida jamil ya amsa snn ta wuce ya bita da ido se kallon ta yake har ta haura sama zuwa d'akin ta.
  Kana ya maida duban sa gun aikin da suke amma kuma ya kasa ta6uka komai se sauke numfashi yayi a hankli tare da kallon saifuddeen wanda duk hankalin sa na gun laptop yana aikin da ke gaban shi.
Ya kira sunan sa a natse,saifuddeen ya d'ago ya kalle shi yace"mene ne?
   Ba komai kawai ina so inji ne ko ka fara lalla6ar Abba kan zancen auren ka da Sophie gashi tace ta yarda zata musulunta.
 Saifuddeen dake kallon sa a hankli ya numfasa snn yace"jamil a kullum muka had'u da Abba ji nake kmr na d'auko masa zancen but ganin ba a jima da yin auren nn ba yasa dole nake yin shiru har se nn da d'an wani lokaci tukun.
  Jamil dake sauraren shi yayi shiru haqiqa gaskiya saifuddeen ya fad'a lokaci bai yi da ze fara yiwa Abba zancen ba shine dai ya matsu da ganin cewa zarah ta dawo gare shi amma dole ya haqura har se lokaci yayi.
  Can yace"haka ne kam kar ka fara masa zancen yanzu,duk da cewa ba mamaki idan yaji zata musulunta ya yarda,matsala d'aya ita ce iyayenta ta yaya kake ganin zasu yarda su barta ta musulunta har ma su yarda kuyi aure,dmn kasan fa iyayen ta turawa ne masu tsauri tunda ta koma a tsare take koina basa barin ta ta fita.
Saifuddeen yace"wnn ba matsala bane da akwai abunda nake shiryawa,burina kawai naga cewa na rabu da wnn abar a lokacin ne komai zai fimin daidai.
  Kallon sa kawai jamil yayi shidai ko kad'an bai ga wani abun qi a tare da zarah ba,se ma wani qara jin son ta da yake kullum,yasan qauyan ci abu ne me wucewa,gashi a yau ma ya fara gani dan yau dressing d'in ta gabad'aya ya tafi da imanin sa har ya shigar dashi mamaki,ya kuma ji kmr ace ita mallakin sa ce halak malak,da yinin yau gabad'aya kallon ta kawai ze zauna ma yi har se ya gode Allah.
  "Subhanallah"
Ya fad'a a hankli kana ya maida hankalin sa gun aikinda suke suka ci gaba dayi.
kullum haka zarah taci gaba da yin dressing d'inta na qananun kaya hankalinta a kwance kmr dama can ta saba sasu har de yanda suke mata matuqar kyau.
  Rnr lahadi da dare bayan isha'i ta fito riqe da plate a hannunta ta gama cin abinci,taje kitchen dmn wanke plate d'in kmr yanda take kullum da zarar ta kammala cin abinci take wanke wa.
  Wata ta samu a kitchen d'in wato d'aya daga cikin en matan saifuddeen tana yin girki,ba yau ta saba gani ba hakan yasa bata ko wani damu ba se zuwa tayi gun sink ta d'ibi morning fresh tana wanke
plate.
 Wacce ke cikin kitchen d'in tayi tsaye tana kallon zarah.
Leggings ne a jikinta iya qauri,coffee brown in clour se rigar jikinta handless light brown wacce kan cikinta da akwai zare guda biyu da aka tsuke rigar ta d'an baje ta sauko zuwa rabin cinyoyinta,kanta ba d'ankwali se qaton ribbon da ta tufke kanta dashi kalar wandon jikinta,ta saki jelar gashin ta wacce duk wani motsi da tayi haka jelar gashin nata ke motsawa abun sha'awa.
  Da Allah malama kallon ya isa haka!
  Zarah ta fad'a tare da dalla mata harara dan tana kule da duk irin kallon da take mata.
  Komai bata ce da zarah ba se wani shu'umin murmushi da tayi,zarah tayi tsaki tare da kai plate a mazaunin sa ta fita.
  Ita kuma ta sauke numfashi a ranta tana tunanin lallai nn gaba idan yarinyar nn taci gaba da dressing haka saifuddeen zai zo ya daina kula su.
 Hum
Ta fad'a tare da jinjina kanta kana ta maida hankali gun girkin da take.
  Zarah kuwa tana fita falo taje ta zauna ta kunna kallo se ganin saifuddeen tayi yazo ya kashe kallon,da saurinta ta kalle shi shaye da toka awa wata qaramar yarinya yanda tasha toka d'in.
 Ganin yanda ya nufo ta gadan gadan yasa ta tashi da sauri zata bar gurin,se jin tayi ya fizgo ta da qarfi yana kallonta fuskar sa a d'aure yace"bari kiji in gaya miki daga yau bake ba kallo a gidan nn,wawiya kawai kin gwammaci ki zauna ki wani saki baki se dariya kike kina kallo,to kisani rnr Monday dolen ki kije school ko kina so ko ba kyaso!
very stupid! tafi in daina ganin ki a nn!
 Ya ingiza ta da qarfi har se da ta fad'i,da saurinta ta tashi tare da dalla mai harara tace"ae gwanda ni kallo kawai nake ina yin dariya ba wani aikin haramun ba,kaifa kullum se ka tara karuwai kuna yin iskan ci bako tsoron Allah....wayyo!
 ta saki ihu tare da saurin guduwa sbd cafko ta da yaso yi.
 Kitty! Kitty!!
 Ya shiga kira,zarah da har takai gun staircase zata haura sama ta dawo aguje taje bayan shi ta la6e tana fad'in"dan Allah yi haquri ce kar ta tazo wlh Allah bazan sake ba su6utar baki ne"
  Tana kai qarshen zancen ta se ga kitty tazo da gudu dan ba daina kiranta yayi ba,ihu ta saki tare da rirriqe shi ta bayan shi tana ta bashi haquri baza ta sake ba,be saurare ta ba se fizgo ta yayi ya dawo da ita gaban shi cike da niyyar kai mata mari,se kuma yayi tsaye yana kallon yanda ta fashe da kuka snn ta cukuikuye shi sosai kmr me neman shigewa a qirjin sa.
  Se yayi shiru yana kallon ta har ma zuwa yanayin dressing d'in ta se ya ganta kmr wata baby doll yanda qananun kayan suka mata kyau.
 Can muryar sa a hankali yace"is ok na haqura jeki baza ta miki komai ba"
  D'agowa tayi ta kalle shi idanun ta taf da qwallah snn ta kalli kitty dake kusa dasu tana kallon su,da sauri ta qara qanqame shi tace"bazan iya ba"
  Yace"olryt cika ni to zan d'auke ta se ki tafi.
  Tsoro tsoro ta sake shi,yana d'auke kittyn ta tafi da sauri har takai staircase ta juyo ta kalle shi cikin d'aga murya tace"mugu Allah ya isa!
  Nan saifuddeen ya ajiye kitty yace"oya! kitty je ki cinye ta ki mata gunduwa gunduwa har qassan ta ma kar ki raga,kan kace me tuni zarah ta haura sama aguje zuwa d'akinta ta banko qofa da qarfi ta rufe.
Saifuddeen ya girgiza kansa d'auke da murmushi snn ya d'auki kitty se shafa jikinta yake ya nufi kitchen.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: *«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*


*«»Page«» 20&21*
Ranar monday da kanshi ya kaita school sbd ya fahimci ba serious bace dole se ya mata haka,zarah kuwa dama haka taso shiyasa ta zille a wancan satin dan tasan idan driver ne kaita kawai zai yi ya ajiye ba kmr yanda saifuddeen ya mata ba dan shi se da ya had'a ta da en course d'in su snn ya tafi.
 Da suka gama lectures dama saifuddeen ya bata numbar driver  acewar idan sun kammala se ta kira shi yazo ya maida ta,tana kiran shi kuwa ba jimawa yazo ya maida ta gida.
  Da isowar ta bathroom kawai ta fad'a tayi wanka byn ta fito ta shirya cikin qananun kaya,riga polo sky blue in colour tayi d'as ajikinta,had'e da black tummy skirt akai,yunwar da take ji bata bar ta yi wata kwalliya a fuskar ta ba se d'an qaramin black veil da ta d'aura a kanta,snn taje kitchen ta dafa indomie tayi zaune a falo tana ci tana kallo.
  Jin shigowar motar saifuddeen yasa ta kashe kallon taje d'aki taci gaba da kallonta a can sbd dama da akwai kayan kallo a d'akin nata kawai dai tafi ra'ayin kallo a falo.
  Tana kammala cin abinci se ga saifuddeen ya shigo d'akin wanda kae tsaye ya d'auki remote ya kashe TV,ba tare da ya ajiye remote d'in ba yasa qafa ze fita,tayi saurin shan gaban shi cikin marere ce fuska,shaye da toka ya mata wani irin kallon da yasa dole taja baya ba tare da ta iya ce masa komai ba tana kallo har ya fita daga d'akin.
  Fuskar ta a murtuqe se gunguni take kana taje ta ciro handouts d'in da aka musu lectures akan su yau,tayi zaune tana dubawa.
  Haka ta kwashe satin aikinta knn duk ta dawo school bata da aikin yi se na duba handouts dan har tibin falo ya d'auke remote ba yanda za'ayi tayi kallo,gashi yau Saturday basu da lectures bata je school ba duk zaman gidan ya ishe ta ba dad'i kallo kawai take so tayi bata iya dube duben handouts d'in nn yau.
 Ba yanda ta iya dole ta d'auki wayar ta ta soma yin game can dai taga ba abinda zei fishshe ta bane ta bud'o qur'ani ta soma karantawa cikin zazzaqar muryar ta me dad'i.
  Can tayi nisa a cikin karatun nata taji qarar door bell,takai aya snn ta sauka zuwa downstairs ta bud'e qofa.
   Cike da murmushi ta tsaya tana kallon su,Nadiya ce da Nusaiba da kuma wani guy wato yayan nadiya me suna ma'aruf wanda shine zai auri Nusaiba.
  Da munar ta ta musu iso suka shigo suka zauna.
  Ma'aruf se kallon zarah yake wanda ya juye baki cikin harshen fulatanci yana magana da ita wae tayi kyau sosai saifuddeen ya iya kiwo shima zai zo yayi aure nn aga irin nasa kiwon,murmushi kawai zara tayi,haka ma Nadiya,Nusaiba kuwa turo baki tayi tana kallon shi.
  Da wasa ya harare ta yace"ki ma daina wani turo baki ni na gaji da jiran se kin kammala school muna komawa gida magana zan yiwa su Abba azo ayi aure mu tafi can Lagos ki qarasa karatun ki.
   Nusaiba ta ta6e baki tare da fad'in"cabd'i kaima dai da wasa kake ni ba wanda ze min aure se na kammala school tukun".
 "Ko"
Ma'aruf ya fad'a d'auke da murmushi a fuskar sa yana me kallonta kana ya maida duban sa gun zarah yace"zarah idan mai gidan naki yana nn kira min shi mu gaisa.
  Nan zarah ta tashi ta haura sama zuwa  d'akin saifuddeen ta shiga mishi knocking.
  Sai da ya jima kafin yake bud'e qofa,ransa a 6ace ya kalle ta tare da fad'in"kai! innalillahi wa inna ilaihi raj'iun! wae kidahumar ina ce ke da se mutum yana cikin bacci kizo ki tashe shi,lafiya mene ne!?
  Idan ka sauka qasa ka gani.
 Zarah ta fad'a fuskar ta a d'aure ta kuma wuce ba tare da ta jira me zai ce ba.
  Girgiza kan sa kawai yayi tare da riqe waist d'in sa ya bita da kallo har ta 6ace ma ganin sa snn ya koma daga ciki,dmn ya sanyo tufafi dan guntun wando ne kawai a jikin sa ko vest babu ma.
   Zarah kuwa tana sauka kae tsaye gun fridge ta nufa ta d'auko musu ruwa da lemu ta kawo musu,nn se ga saifuddeen yazo sanye da farar jallabiya wanda cikin sakin fuska sosai ya bawa ma'aruf hannu suka gaisa,snn ya zauna yana me amsa gaisuwar su Nadiya da suka gaida shi kafin ma'aruf ke cewa"manyan qasa ka ga yanda ka qara kyau kuwa hm lallai zarah ta iya kiyo.
 Ta6e da baki Saifuddeen yace"hum kai dai baka rabuwa da shirme,ya aiki ya kuma Lagos?
  Lafiya qalau wlh gauran ci kawai ke damu na bani da me dafa min abinci kullum se na siya ga qanwar nn taka tace baza ta yarda ayi aure ba se ta kammala karatu ko tausayi na ma bata ji.
  Ya qarashe mgnr ne yana me kallon Nusaiba da suka tashi zasu haura zuwa sama.
  Saifuddeen ya kalle ta snn ya kalle sa yace"she is right tausayin ka na me zata ji to kai baka tausaya matan ba,wacce secondary school kawai take yi yanzu bata ko kammala ba ina zancen aure,kaima de ka fad'a ne kawai dmn kaji dad'in bakin ka dan ko ta yarda ni bazan yarda a mata auren wuri ba feature life d'in ta ya lallace ta zama child mother da wuri gsky se tayi karatu me zurfi snn ko zamu baka ita.
  Haka ma zaka ce yayi akwai Allah"
  Ma'aruf ya fad'a cikin yanayin da yasa saifuddeen yayi dariya dan ma'aruf mutum ne me barkwanci da ban dariya.
  Kana suka d'auko wata firar suna yi.
  Su Nadiya kuwa suna isa d'aki Nusaiba se kallon zarah take da ke sanye cikin qananun kaya riga da skirt,rigar milk ce round neck me guntun hannu snn zuwa tummy aka saki umbrella da ta d'an sauka zuwa mazaunan ta,skirt d'in jikinta kuma coffee brown ne strait da ya tafi har zuwa ankle yayinda aka d'an tsage bayan shi kad'an,ta yafa d'an qaramin top veil klr skirt d'in hasken fuskar ta ya qara fitowa sosai se tayi kyau duk da simple make up ce akan fuskar ta.
Haka ma takalman da ke qafar ta simple ne gold masu d'an tsini klr en kunnen ta.
  Murmushi Nusaiba tayi dan zara ta birge ta duk yanda ta fad'a mata tsarin yanda zata riqa sa kaya su fito da ita bata yi kuskure ba haka take yi.
  Cikin d'aga gira zarah tace da Nusaiba"kallon fa?
  Nusaiba tace"wlh kyau kika yi sosai.
 Zo muyi selfie.
  Ta fad'a tare da kama hannun zarah ta zaunar da ita kusa da ita a nn kan sofa yayinda nadiya ke zaune d'ayan 6angaren,suka saka Nusaiba a tsaka wacce ta ciro wayar ta ta d'auke su selfie dukkan su kowannen su ya d'aura qafa d'aya kan d'aya se sukayi kyau sosai musamman yanda suka saki murmushi.
  Take Nusaiba ta turawa kowaccen su  hoton a wayar ta kmr yanda suka buqata,snn zarah tace"to ku tashi muje kitchen ku dafa abunda kuke so dan ni dai yanzu ba girki nakeyi ba tunda na fara zuwa school,da na dawo indomie kawai nake dafawa dan ta fimin sauqi.
   Nadiya tace"Au shi yaya saif fa ko biye miki yake kuyi ta cin indomie d'in?
  Kafin zarah tace"komai Nusaiba ta riga ta da cewa"Aa ae kinsan yaya saif ba ko yaushe abinci ya dame shi ba shiyasa take cin karanta ba babbaka.
  Lallai yaya saif babba ne.
  Nadiya ta fad'a wacce ta miqe tsaye tare da cire mayafin ta ta ajiye snn ta nufi  bathroom dmn yin arwala sbd kiraye kirayen sllr zuhur da aka soma yi.
  Bayan ta shige bathroom d'in ne Nusaiba ta kalli zarah tace"wae kinji wani qamshi dake fita a jikin ki mai dad'in gaske kodai.... Da sauri zarah ta harare ta tare da fad'in kodai me?
  D'an murmushi Nusaiba tayi snn tace"maida wuqar ni bada wata manufa nake nufi ba ina nufin ko yaya ya gaya miki ra'ayin sa ne dan mutum ne mai son qamshi sosai.
  Zarah ta ta6e baki tare da fad'in"hm Allah sauwaqe wlh ni yayanki sam baya a gabana bare har ya gaya min ra'ayin sa nabi kawai dai turarukkan da umma ta bani ne a kwana ki da naje tace na riqa amfani dasu kullum idan nayi wanka.
  Nan Nusaiba ta jawo jakar ta da sauri tace"ae kin ma tuna min umma ta bani saqon wani turare tace na kawo miki da dare ake amfani dashi idan anyi wanka za'a kwanta se ki fesa a jiki.
  Kana ta ciro turaren ta miqa mata,zara ta kar6i turaren tana dubawa se ganin hoton cartoon d'in mace da namiji tayi a jikin turaren rungume da juna se shinshinar qamshin jikinta yake tamkar ze had'iye ta.
  Da sauri tasa tafukan hannayen ta ta rufe hoton snn kana ta maida tafukan hannayen nata ta rufe fuskar ta cikin jin kunya kmr umman na kusa.
  Nusaiba dake kallonta d'auke da murmushi tace"lallai ma kunya su en cartoon d'in,to kar6i wnn ledar ki duba a kasuwa na siyo miki da umma ta aike ni.
  Ta fad'i hakane tare da miqa mata wata leda snn ta tashi ta wuce zuwa bathroom sbd Nusaiba ta fito.
  Zarah da ta bita da kallo ta d'auki ledar ta ware tana dubawa,kayan shiga swimming pool ne kala biyu,bra da d'an guntun skirt iya cinya me had'e da bomb short a jikin shi,sky blue in colour,se d'ayar klr kuma white yayinda bra d'in take d'auke da wani material lace like net da aka shinfid'a a gaban ta se tayi looking like half vest amma tsaf ake hango qoqannin bra,yayinda skirt d'in ya kasance shape d'in sa iri d'aya da tummy amma guntu ne sosai iya cinya kuma a ware yake ba'a d'inke ba d'aura shi ake kmr zani,da akwai en zareruwa guda biyu gefe da ake d'aurewa.
  Hm zarah ta fad'a tare da maida kayan cikin leda se ga Nusaiba ta fito daga bathroom har ta d'auro arwala,suna had'a ido da zarah ta kashe mata ido d'aya tare da fad'in"ya kika ga kayan sunyi?
  Zarah tace"inafa nikam bazan iya sa kayan nn ba kin sani gwanda kawai ki maida su inda kika siyo se a d'auko wa enda zan iya sawa yafi da ayi asara"
 Nusaiba tace"kinga sis wa en nn fa kayan shiga swimming pool ne bawai wa enda zaki sa ki zauna bane.
  Meye kuma haka?
Zarah ta tambaya.
  "Zo kiga"
Nusaiba ta fad'a bayan ta kama hannun ta suka je gun window ta nuna mata swimming pool da suke hangowa.
   Tace"amfanin kayan se idan zaki je gurin se kisa ki shiga kiyi wanka abunki"
  Gwalo ido zarah tayi tana kallon ta tace"ga bayi se naje can nayi wanka awa wata mahaukaciya kowa na kallona"
   Kafin Nusaiba tace komai se dariyar Nadiya suka ji wacce ta sallame sllh knn ta taso tazo gurin su ta dafa zarah tare da fad'in"kinga zarah ae wayewa ce wanka a gurin ba wanda zai d'aukeki mahaukaciya snn wanka ne na shan isk dmn kawai jin dad'i,ba kmr irin wankan da akeyi bayi bane snn kinga gurin a ke6ance yake har ki gama wankan ki ba me ganin ki,da akwai qofar da zaki bi ki wuce ba se kinbi qofar falo ba,kin fahimta?
  Eh na fahimta
 Zarah ta fad'a ba wai dan zata iya abunda suka ce ba ta fad'a ne kawai dan ta huta dasu.
  Tace"yanzu dai ku gaya min me kuke so naje na dafa muku kafin yaya ma'aruf yace ku fito har de ke nadiya da zaku koma kaduna.
  Nadiya tace"ai se gobe zamu koma ko kina so mu kwana a nn"
 Tayi mgnr ne cikin tsokana.
  Da sauri cikin marere ce fuska Zarah tace"eh wlh ina so dan Allah.
  Hm um! rufa mana asiri da yaya saif haka ma umma baza ta bari ba cewar Nusaiba kafin nadiya ke cewa"lallai dai kam da dai baya nn.
  Zarah tace"haba dai ko yana nn meye ruwan sa daku tunda ba'a kanshi zaku kwana ba,kuma inna nasan yanda zan bi da ita ta yarda kunji dan Allah"
  Murmushi kawai sukayi ganin yanda duk ta wani marairai ce musu suka ce"shikenan kira umma muji idan zata yarda d'in to.
  Um um tukun ni nafi so se na gama girka muku abinda zaku ci snn,kar yaya ma'aruf ya bar gidan nn bai ci komai ba.
  Nadiya tace"cabd'i ina gimbiyar tasa zata yarda ta bar shi da yunwa ae ko ni er rakiyar sa a qoshe nake sbd albarkacin sa da na samu har ji nake kmr cikina ze fashe.
   Nusaiba ta harare ta tare da fad'in me kk nufi.
  Nadiya tace"ae kema kinsan gaskiya na fad'a dmn dani kad'ai ce zanzo baza kimin liyafar da kika mishi ba se dai idan nazo abunda na samu anyi a gidan shine zanci.
   Kallon up and down Nusaiba ta mata tare da fad'in"ae kam kin san shi kad'ai keda wnn matsayin.
  Daga haka bata jira me nadiya zata ce ba taje zuwa sllh.
  Nadiya da ta bita da kallo tayi murmushi kawai haka ma zarah wacce taje bathroom ta d'auro arwala tayi sllh bayan ta idar,ta d'auki wayar ta dake kan bedside drawer ta kira umma.
 Da qyar kmr zatayi kuka ta samu umma ta yarda ko shi se da sa bakin Abba dan suna tare shida umma shine yace ta barsu kawai su kwana tunda kwana d'aya ne.
 Ae kuwa sosai Zarah taji dad'i haka ma su Nusaiba dan suna son kwana a gidan.
Har bayan la'asar ma'aruf na gidan be tafi ba suna can balcony shida saifuddeen kan resting chairs se fira suke tayi kmr wasu mata,dan haka suke suna jimawa basu had'u ba amma duk rnr da suka had'u tofa suna jimawa tare suna yin fira.
 Se 5:30
  Suka koma daga ciki kmr yanda ma'aruf ya buqata yana son zasu tafi dan shi sam bae san da zancen a nn gidan su nusaiba zasu kwana ba sbd basu gaya mishi ba se yanzu yake ji da suka zo suka same su a falo yace"su tashi su tafi Nusaiba kece mishi ae su a nn zasu kwana.
   Kafin ma'aruf yace komai saifuddeen yace"what! uban me zakuyi a nn gidan idan kuka kwana"
     Sis ce ta buqata ae.
  Cewar Nusaiba da tayi kicin kicin da rai.
   Saifuddeen da ya fahimci zarah take nufi ya kalli Zarah irin kallon kin raina ni ko.
 Tayi qasa da idon ta kawai dan bata son ma'aruf da nadiya su fahimci wani abu.
Shi kuma saif ya maida duban sa gun Nusaiba zatayi magana knn ya mata wani kallo dako be fad'a ba tasan me yake nufi sum sum suka haura sama ita da Nadiya suka d'auko mayafin su da hand bags d'insu suka fita.
   Nan Ma'aruf yayi sallama da saif shima ya fita.
  Kmr jiran fitar sa yake da sauri cike da mugunta ya fizgo zarah cikin damqo gashin kanta ya riqe sosai har se da ta saki er qara tare da saurin kai hannayen ta kan nashi cike da son qwace kanta.
 Bai barta ba se had'awa yayi da hannayen nata duk ya riqe guri d'aya tare da jelar gashin ta,with deep voice yace"kin raina ni ko munafuka wato so kike su san me yake going a gidan nn to bari kiji wlh duk naji wata magana ta fito wae ina kawo en mata a gidan nn ko se nayi gunduwa gunduwa dake naba kitty ta cinye wawiya kawai.
  Ya tura ta da qarfi har sai da ta fad'i zaune yasa qafar sa yayi ball da ita snn ya wuce zuwa sama,Zarah da ta bishi da kallo qwallah tap a idonta ta mishi Allah ya isa yana jinta be juyo ba yayi tafiyar shi nn ta had'e kanta da guiwa ta shiga yin kuka.

_Thursday 22/02/2018_
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Friday 23/02/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*




*«»Page«» 22&23*
Tuna cewa sun d'aura girki yasa ta sassauta kukan ta tashi cikin share qwallah ta nufi kitchen.
  Ta samu ruwan zafin da suka d'aura dmn yin tuwon semo har sun tafasa ta kashe wutar gas cooker d'in ba tare da tayi tunanin tayi iya ko nata ba,har miyar agusi ma da suka d'aura duk ta kashe tayi ficewar ta zuwa d'aki ranta ba dad'i.
  Washe gari da safe guraren qarfe goma ta fito kitchen riqe da cup d'in tea zata haura sama zuwa d'akin ta tana sanye da wani material me  kyau turquoise green in clour d'inkin doguwar riga da tayi d'as a jikin ta,high neck me dogon hannu wacce ta baje sosai tun daga kan waist d'inta,snn tayi d'aurin d'ankwali simple iya yinta se yayi kyau ba laifi har de yanda ta jashi yayi baya kmr yanda taga Nusaiba nayi.
  Sam bata ji motsin saukowar mutum daga staircase ba se ganin mutum tayi a gabanta,har se da ta d'an tsorata ta ja baya da sauri tare da kallon wacce tasha gaban ta wato d'aya daga cikin en matan saifuddeen,da ta fito zata tafi riqe da makullin motar ta saqale a d'an yatsan ta se jujjuya shi take tana fmn cin chewing gum.
 Shaye da toka Zarah tace"lafiya meye haka?
  Riqe waist d'inta tayi tare da sakar mata murmushi snn tace"yi haquri and idan baza ki damu ba plz ina son zamuyi wata magana ne game da mijinki saif.
  Tsaki Zarah taja snn ta ra6a ta gefen ta zata wuce,da sauri ta tare mata hanya tace"Haba sis ki tsaya ki saurare ni mana magana ce fa mai mihimmanci".
  Ke kika san wnn ni da Allah bani hanya na wuce.
   Zarah ta fad'a tare da mangare ta gefe zata wuce.
  Bata ji haushi ba ta riqo hannun ta a hankali cikin sanyin murya tace"yi haquri dan Allah ki saurare ni kinji sis"
    Kallonta ta zarah tayi kmr baza tayi magana ba can ta kauda fuskar ta gefe tace"fad'i ina jinki kuma ni sauri nake idan baki tashi ba nayi tafiya ta.
 Tace"to sis a tsaye d'in zamuyi magana da munje mun d'an zauna ko?
  Mtsw zarah tayi d'an guntun tsaki snn ta yarda suka je suka zauna.
   Yarinyar na kallon ta tace"am sorry bansan ya zaki d'auki maganar ba,gashi a gaskiya na kasa haquri bansan wa zan tunkara da zancen nn ba face ke dmn ke zaki fi sanin komai akan abunda nake son ji game da saif,so nake naji plz shin tunda kukayi aure da akwai wani abu da ya ta6a shiga a tsakanin ku na kwanciyar aure keda shi ko kuwa dama kinsan cewa baya da lafiya bazai iya amfanuwa da mace ba se dai kullum cikin wasa kawai.
   Zarah dake kallonta cikin girgiza kai tace"Hm lallai iyayenki sunyi asara wlh,ta nuna ta tace to bari kiji in gaya miki ni ba asararriya bace irinki da har zaki zo ki tunkare ni da wnn banzan zancen naki.
  Mtsw taja tsaki tare da tashi zata bar gurin,yarinyar ta riqo hannun ta da sauri tace"kinga sis matsalan nn fa har ke ta shafa gwanda ki tsaya mu san yanda zamu warware matsalar, ki daina jin haushi na ke kikayi sakaci ae da kika bar mijin naki yana kula en mata.
   Zarah ta fizge hannunta cikin dalla mata harara tace"jaka kawai asararriya ki tafi can ki nemo sauran en matan nashi ku warware matsalar kuda yake gaban ku.
  Daga haka ta wuce ba tare da ta jira me zata ce ba.
  Yarinyar ta bita da kallo wacce duk a tunanin ta ta d'auka ko zarah sokuwa ce ganin kai kawon da take a gidan amma sam bata damu ba bayan tasan gurin mijinta take zowa har su kwana tare amma ko oho,ashe rashin so ne dan dai yanzu ta fahimci Zarah ba son saifuddeen take ba kmr yanda shima ta fahimci ba son zarah yake ba akayi auren.
 Numfashi ta fitar a hankli tare da jinginawa a jikin kujerar da take zaune,ta lumshe ido tana tunanin tun lokacinda ta fara d'aura idonta akan saifuddeen ta kwad'aitu da son kasancewa tare  dashi burin ta knn kullum amma duk tazo bai wuce yayi romancing d'inta ba yana jin kansa yanda yake so ze ture ta gefe ya hau baccin sa,kwanaki har camera tasa a d'akin nasa a 6oye dmn taga ya yake yi da sauran en matan nashi amma taga duk kanwar ja ce romancing d'insu kawai yake kmr dai yanda yake mata,kuma ta fahimci kowaccen su tana mamakin hakan amma kwarjinin sa yasa ba wacce ta iya masa magana,haka itama tasha yunqurin son ta tambaye shi wai lfy amma se ta kasa.
 Qamshin turaren sa da taji ne yasa ta bud'e idanunta,fuskar sa a d'aure ya mata wani kallon me kuma kk yi zaune baki tafi ba.
  Haquri ta bashi tare da saurin tashi ta fita.
 Snn shima ya fita yaje ya samu jamil dashi ne dalilin fitowar shi.
  Jamil dake jingine jikin motar sa yabi yarinyar da ido har taja motar ta ta fita,kana ya girgiza kansa ya kalli saifuddeen yace"haba saif is not gud wlh ba girman ka bane ace wai kana kawo en mata har gidan ka su kwana.
  Cikin yanayin 6acin rai saifuddeen yace"dama wane girman ne dani to yanzu,ae tunda aka had'a aurena da wnn banzar yarinyar aka 6arar min da girma,kuma dan Allah ka daina sa ido akan abunda be shafe ka ba bana so.
  Jamil yace"ae gwanda kaso dan gaskiya nake gaya maka in zaka daina ka daina.
  Bazan daina ba jamil!kuma idan zaka fad'i abunda ya kawo ka ka fad'a kona tafi abuna dan nagaji da wnn banzan surutun naka da kake min.
  Kallon sa kawai jamil yayi kmr bazai ce komai ba se can ya bud'e ganbun motar sa ya ciro wasu takardu ya miqa masa ba tare da yace masa komai ba ya shiga motar sa yayi tafiyar shi.
  Saifuddeen da yasan takardun mene ne be damu da tafiyar sa ba se komawar sa yayi daga ciki yana me duba takardun da zeyi signing akai kan wani clinic da suka had'a hannu zasu bud'e shida jamil.
  Koda zarah ta gama breakfast ta fito ta same shi zaune a falo ya gama signing d'in takardun yana waya da jamil.
 Sau d'aya ta kalle sa ta wuce zuwa kitchen,ta fito zata koma sama se jin tayi ta fad'i ba shiri kan yanda saifuddeen ya jefo mata d'ayan takalmin shi daga can inda yake zaune,takalmin yayi super ya kad'e mata qafar ta da take shirin takawa ta fad'i har ta buga bakin ta kan stairs dan gab take da shirin hawa.
 Ae kuwa ta saki qara tare da saurin ta6o bakin ta,se ga saifuddeen yazo ya zauna kan stairs tare da kai hannu ya tallabo fuskar ta yana kallon gefen bakinta dake fitar da jini yace"gud gobe ma idan kika sake zagina uban wnn zan miki wlh,er rainin hankali.....kai kuma mugu azzalumi Allah ya isa wlh!
  Zarah ta fad'a tare da tofa mishi jinin da ya taru a bakin ta kan farar rigar sa.
   Da saurin sa ya kalli rigar tashi snn cikin hanzari ya tashi ze damqo ta,amma kan kace me tuni ta zura aguje ta haura sama ta shige d'akin ta ta rufe.
   Be bita ba se kallon rigar sa ya sake yi rai 6ace ya jinjina kansa tare da yin qwafa snn ya nufi d'akinsa ya cire rigar ya sauya wata.
  Se da ta tabbatar ya bar gidan snn ta fito tayi zaune a falo tana waya dasu Nusaiba.
  Washe gari da safe saifuddeen ya dawo daga masallaci be zarce koina ba se d'akin zarah ya same ta kwance wacce tana yin sllh ta koma kwanciya se bacci take ta rufa jikinta da blanket gabad'aya har fuskar ta ba'a gani duk ta rufe.
 Yasa hannu ya yaye blanket d'in daga kan fuskar ta yana kallon bakinta da ya d'an kumbura kad'an ta gefe,kana ya maida duban sa gun gorar ruwan da ke ajiye kan bedside drawer ya d'auki gorar ruwan ya bud'e ya d'an zuba ruwan a hannun sa snn ya yayyafa mata kan fuskar ta.
  Rae 6ace ta bud'e idanunta a hankli tana kallon shi,shima fuskar nn tasa ba annuri yake kallonta snn yace"wawiya uban me kike yi har qarfe shida da rabi baki tashi ba,wlh ina gaya miki idan driver yazo ko kin kammala shiri ko baki kammala ba haka zaki bishi ku tafi,kisa wasa kuma ki gani.
  Yayi qwafa snn ya fita yaje d'akin shi ya bud'e laptop d'in sa yana kallonta,yanda ya barta still tana nn kwance abunta se can ta tashi ta bud'e windows d'in d'akin ta yaye curtains kmr yanda taga Nusaiba nayi a gida idan sun tashi daga bacci haka take yi sbd iskan safiya ya shigo,d'umin bacci ya fita,yana kallo har ta gyara d'akin tsaf ta fesa room fresh,ta kuma ciro kayan da zata sa ta ajiye kan bed snn ta jawo towel zata cire rigar baccin da ke jikinta nn ya rufe laptop d'in ya kwanta tare da lumshe idanun sa ya hau bacci se qarfe takwas saura ya tashi lokacin zarah ta kammala shirinta tsaf har tayi breakfast taci aikin gidan ne bata samu tayi ba.
  Ta fito da sauri ta shiga mota dan har driver yazo yana jiran ta,wacce garin rufe ganbun mota ta had'a da gefen gyalenta ta rufe bata sani ba har ana hango gyalen ya fito a waje.
   Saifuddeen dake can d'akin sa laptop a gaban sa yana ganin su,yayi tsaki tare da d'aukar wayar sa ya kira driver da har ze tashi mota yace ya bawa zarah waya wacce tana kar6a se jin tayi yace"bagidajiya shiga motar ma ba'a iya ba,da Allah bud'e ganbun kija gyalen ki ki matsa can er qauye kawai yayi tsaki tare da tsinke wayar.
   Zarah da ta fahimci waye kan wayar tayi mamaki tana dubin ta ina yake,bata ganshi ba kawai ta miqawa driver wayar sa snn tayi kmr yanda yace.
  Shi kuma yana kallo har se da suka fita gate d'in gidan suka hau hanya snn ya rufe laptop ya koma bacci se 9 ya tashi ya shiga bathroom zuwa wanka.
   Zarah kuwa se 4 ta dawo gidan,tana shiga d'aki wayarta ta soma ringing se da ta cire mayafin ta ta ajiye snn ta bud'e jakar ta ta ciro wayar,da sauri ta d'aga kiran sbd umma ce me kiran,wacce suna gama gaisawa take tambayar ta ko ta dawo daga school tace mata eh,tace"to gasu inna nn zuwa da yayanki tunda safe suka zo nace musu kina makaranta shine suka jira har se kin dawo.
  Sosai Zarah taji dad'i har tana tsallen murna.
 Wacce suna kammala waya ta sauko downstairs da sauri ta d'auko tsintsinya ta share falon duk da ba wani datti ne dashi ba se dan ganin bata samu ta share shi da safe ba.
 Ta mofe shi tas snn ta fesa room fresh take gidan ya d'au qamshi kmr yanda take yi kullum idan ta gyara.
 Tana kammalawa ba jimawa taji qarar doorbell har sun iso.
  Da murnar ta ta bud'e musu qofa tare da qanqame yayanta wanda dama haka take tarbon shi duk ya dawo daga zariya dan can yake karatu tun kan secondary school har yanzu da yake high school ABU,d'an wayayye dashi fari sol kmr ita kama ce kawai basa yi dan shi mahaifin su ya d'auko.
  Cike da murmushi yayan nata yaja karan hancin ta cikin harshen fulatanci,yace"wae baki san kin girma bane zarah"
  Kafin zarah tace komai inna tace"yo ina zata san ta girma wnn kam,ko kunya bata ji ta barni tsaye ta rungume ka kai akeyiwa maraba.
  Zarah dake kallonta d'auke da murmushi tayi saurin sakin yayan nata taje jikin inna tana mata oyoyo.
 Da sauri inna ta janye ta tare da kutsowa ciki tana fad'in ni kinga karki kada ni bani guri in zauna wad'an nn qafafuwan nawa ba qarfi ne dasu ba.
  Nan Zarah ta kaita gun doguwar kujera 3seater ta zauna shima yayan nata ya shigo ya zauna ta kawo musu ruwa da lemu suka sha.
 Inna se kallon falon take ganin irin had'uwar da yayi.
  Tace"barikallah fad'ima kinyi qosin miji wnn irin gida haka awa aljannar duniya,hai kiran min si mu gaisa d'an albarka.
   D'an murmushi Zarah tayi tare da fad'in"ae inna baya nn ya fita.
   Wacce ta fad'i haka ne kawai amma yana nn,tace musu hakane dan tasan ba qaramin wulaqanci ze musu ba in yazo,ba kuma zata so hkn ba ga inna har da wani sa mishi albarka.
   Ya school Ammi tace kin fara zuwa ko?
  Yayanta ya tambaya.
  Zarah tace"eh na fara zuwa tun wancan satin"
 Yace"to Allah ya taimaka"
  Tace"amin"
 Nan inna itama tasa bakin ta tare da mata fatan alheri,snn kuma ta shiga yi mata nasiha kan yanda zatayi haquri da zaman rayuwar aure,duk da sosai tayi mata nasiha a can Rimin dako lokacinda aka je sa lalle.
  Zara dai tayi shiru se sauraren ta take amma a ranta se Allah Allah take kar saifuddeen ya fito har se sun bar gidan.
  Bai fito ba kuwa har suka tashi tafiya.
  Sun fito zarah ta rakosu inna ta hango mota ta shigo tace"yauwa ga d'an albarkan nn ma ya dawo.
  Murmushi yayan zarah yayi ya kalli inna yace"inna baki gane shi ba ae wnn drivern da Ammi ta turo ne yazo ya tafi damu.
  Inna tace"Ayyo ban gane si ba ai ca nake d'an albarkan ne ya dawo.
  A'a bashi bane cewar zarah snn yayan ta yace"idan ya dawo se ki gaida mana shi...eh kice munzo bamu same si ba muna gaida si kinji koh.
 Ita kuma inna ta fad'a.
 Zarah tace dasu
   "to"
wacce tana tsaye har sai da suka shiga mota suka wuce snn ta juya zata koma daga ciki,se hango saifuddeen tayi tsaye a bakin qofar shiga falo riqe da waist d'in sa yana mata kallon lallai ma.
Tana qarasawa sosai cikin d'aure fuska yace"uban waye yabawa wa en can qazaman izinin shigo min cikin gida,tambayar ki nake su waye!
  Ya daka mata tsawa zata ja baya sbd tsoro,ya fizgo ta da qarfi har se da ta fad'o kan jikin sa,da saurin sa kuma ya ture ta tare da kai mata mari snn ya nuna ta yace"bari kiji in gaya miki nn ba irin gidan ubanki bane da kowane kucaki ke shigowa dan haka wlh duk na qara ganin su a gidan nn se na illata ki er iskar yarinya wuce in daina ganin ki a nn very stupid!
  Ya fad'a yana kallon ta a fusace,yayinda ta wuce ciki da sauri tana kuka.
 Kana shima ya koma daga ciki yayi tsaye a falo fuskar sa a yatsine wai duk falon ya 6aci da warin fulani se masifa yake tayi,ya yaye curtains d'in windows ya d'auko room fresh ya feffesa.
  Snn ya fito se qwalawa me gadi kira yake wanda yazo aguje da sauri ya durqusa a gaban sa yana fad'in gani yalla6ai.
   Saifuddeen yace"kana jina!
wa en nn qazaman mutanen da suka fita yanzun nn kar in qara ganin qafar su a gidan nn,idan kuma ka sake kuskuren barin su suka shigo wlh a bakin aikin ka!.
 Da sauri me gadin ya shiga bashi haquri yana fad'in"inshaa Allah hkn bazai sake faruwa ba yalla6ai sunyi na farko sunyi na qarshe bazan sake barin su su shigo ba ko yanzu dan naga drivern Hjy ne ya kawo su shiyasa.
 Saifuddeen da ke kallon sa cikin daka tsawa yace"naji da Allah tashi ka tafi ban neme ka wani  dogon surutu ba
sha sha sha kawai da be san aikin sa ba,kana barin kucakai suna shigo min cikin gida..mtsw!
 yayi tsaki tare da komawa ciki,jim kad'an ya fito riqe da makullin motar sa ya bar gidan shida kitty da kusan ko yaushe da ita yake fita.
  Be dawo gidan ba se bayan isha'i,kitty na biye dashi kmr jela suka nufi d'akin shi.
  Dama sunci abinci a waje,cire kayan jikin sa kawai yayi ya fad'a bathroom yayi wanka,yana fitowa yayi shirin bacci,snn ya janyo laptop d'insa ya bud'e yana kallon zarah dake zaune kan bed ta had'e kai da guiwa,bazai iya fahimtar me take yi ba is she crying or no hkn yasa ya maida abun baya yaga tun lokacinda taje d'aki cikin kuka ta hau kan gado tare da had'e kanta da guiwa she is still like that bata sake d'agowa ba har yanzu.
    Nan ya rufe laptop d'in ya nufi d'akin ta,inda jelar shi kitty na can ya bari kan sofa tayi bacci.
   Qarar bud'e qofar da yayi ne yasa zarah ta d'ago fuskarta ta kalle shi hawaye na gangarowa a hankli kan kumatun ta.
  Tana kallo har yazo ya zauna kusa da ita,zata tashi knn ya kama hannun ta ya maida ta yana kallon idanunta da duk sun kumbura kan kuka.
  Fuskar sa ba yabo ba fallasa snn muryar sa a natse yace"wa enda suka zo su waye a gurin ki?
   Komai bata ce dashi ba se fizge hannun tayi ta miqe tsaye,ba shiri ta dafe goshin ta snn ta tafi suuu zata fad'i sbd wani irin jiri da ya d'ibe ta,saif ya tashi da saurin sa ya tarbo ta ya zuba mata ido yana kallon yanda ta dafe goshin ta sosai snn ta runtse idanunta gam can yaji gabad'aya ta saki har hannun ta dake kan goshin ta ma duk ta sake,ta some mishi a hannu.
   Nan ya d'aura ta kan bed ya kwantar snn ya d'auko ruwan gora a fridge ya yayyafa mata har kusan sau ukku snn ta fitar da dogon numfashi amma idanuwan ta a rufe bata bud'e ba haka kuma ba alamar zata bud'e dan ko motsa su ma bata yi ba.
  Saifuddeen dake kallonta ya dafa goshin ta yaji yayi zafi sosai be sake yayyafa mata ruwa ba se tashi yayi ya tafi zuwa d'akin sa jim kad'an ya dawo riqe da d'an small syringe d'auke da ruwan magani a ciki,ya zauna tare da kama hannun ta na hagu ya soka allurar sannu a hankli kan jijiyar hannun har se da ruwan maganin suka qare snn ya zare yana d'an murza mata hannun.
  In seconds ta sauke ajiyar zuciya a hankli,ya kafe idanun sa se kallon fuskar ta yake can yaja blanket ya rufa mata jikinta snn ya kashe wutar d'akin ya fita.
  Se sha biyun dare ya koma dawowa yana mird'a qofar d'akin nata ya jita a rufe da key knn ta farka ta rufe d'akin.
   Da ya koma d'akin sa ya duba laptop ya ganta zaune qasa kan rug kusa da sofa fresh milk a gaban ta da cup tasha ta d'aura kanta kan sofa se bacci take wutar d'akin a kunne.
 Washe gari koda ya dawo daga sllr asuba ya sami d'akin nata a bud'e ta cire key.
 jikin wardrobe ya same ta daga ita se towel d'aure a jikinta,girshi ta gan shi da sauri ta ciro hijab a cikin wardrobe tasa,snn fuskar ta a d'aure ta kalle sa,kafin tace komai ya ta6e bakin sa cikin girgiza kae snn a hankli ya soma tako zuwa gurin ta yana fad'in"Allah wadarai meye a jikin naki to har na 6oyo,baki ga en matan da ke zuwa gurina bane tamkar su sukayi kansu,full option ba kmr ke da kallon ki ma asara ne.
  "Look this"
Ya fad'a tare da kama d'ayan mamanta yace"boob ne ko abu da kama"
  Qara zarah ta saki tare da saurin buge masa hannu dan sosai ya kama mamman ba tare da tasan ma ze kama ba kae tsaye taji hannun shi,wacce tana buge mishi hannu ya manna ta da qarfi jikin wardrobe tare da kama hannayen ta gabad'aya ya maida su baya ya riqe da d'ayan hannun sa,d'ayan hannun sa kuma ya kama wuyan hijabin ta yace"zan miki zir wlh a nn gurin inga tsiyar da kk 6oyo na kuma yi abunda naga dama,er rainin hankali a banza dai an bani bare da igiyar aurena shine har kina da qwarin guiwar da zaki buge min hannu sbd kin raina ni ko!
  Wani kallo zarah ta mishi ranta a 6ace se qoqarin qwatar kanta take.
   Yace"all right ni kk ma wnn kallon lallai yanzun nn zan nuna miki ke qaramar er rainin wayo ce zan tu6e ki na kuma fitar dake a cikin gidan se kowa a anguwar nn kaf ya gama ganin ki.
   Nan kawai ya fizge hijabin ta ya cire ya jefar snn ya kama towel d'inta ze fizge da sauri zarah ta fashe da kuka cikin girgiza kai tana fad'in"a'a dan Allah kayi haquri bazan sake ba".
  Kafin yayi komai qarar wayar sa ta katse shi kuma Abba ne me kiran dan ringing d'inda ya sa mishi daban nn ya sake ta tare da tura ta da qarfi har se da ta fad'i zaune snn da sauri ta riqe towel d'inta da taji ya kunce ze sa6ule mata.
  Saif be fita a d'akin ba se kallon ta yake yana waya da Abba kana yazo gab da ita ya durqusa tare da d'aura mata wayar a kunnen ta.
   Jin Abba ya kira sunan ta yasa tayi saurin share hawayen fuskar ta kmr wanda yana kusa bata so ya gani snn ta saisaita kanta muryar ta a hankli ta shiga yin waya dashi har suka gama.
 Saif ya maida wayar sa a aljihu ya kalle ta tare da kallon bathroom ya kuma kalli agogon bangon d'akin ko be fad'a ba tasan me yake nufi,ba musu ta tashi se bayan ta shiga bathroom ya miqe tsaye a hankli yana kallon hannun sa da ya kama mammanta dashi a ransa yana mamaki ba yau ya fara ta6a nonon mace ba amma ya akayi da ya ta6a nata yaji wani abu daban kmr be ta6a ta6awa ba.


Am sorry plz gobe bazan sami damar yi muku ba sbd wata exam da zan rubuta ina neman addu'ar ku plz👏🏻.


*Dedicated to »»»zarah gwandu*
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Sunday 25/02/2018_
*«»«»«»SAIFUDDEEN!«»«»«»*




By
   *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



 *«»page 24«»*
 Nan de ya basar ya fita daga d'akin.
  Zarah kuwa bayan ta kammala shirin ta,dama komai ta fito zata fita,ta sami saifuddeen zaune a falo ya jingina bayan sa a jikin kujerar da yake zaune idanuwan sa a lumshe kitty kan laps d'in sa se shafa jikin ta yake a hankli wanda ba abinda yake tariyo wa se rayuwar shi shida Sophie da tun secondary school suka had'u da juna har zuwa university,primary school kawai yayi a Nigeria.
 Qamshin turaren zarah ne ya dawo dashi duniyar tunanin da yake ya bud'e idanun sa da duk sukayi jajur suka canza launi.
  Zarah da tayi tsaye ta kasa wucewa sbd tsoron kitty ya sakar mata wani mugun kallo.
  Kallon da ya mata ne yasa dolen ta ta nufi qofa zata fita se  kawai kitty ta nufo ta aguje tare da yin kukan su na kyanwa.
 Ae kuwa a tsorace ta fasa ihu bata riga ta bud'e qofa ba taje da gudu tayi tsalle ta hau kujerar da saif yake zaune tana neman 6uya a bayan shi.
 Da sauri Saifuddeen ya miqe yana mamakin me kitty keyi haka wacce da gudun ta zata hau kujera cike da son cafko zarah da gabad'aya ta cukuikuiye saif se ihu take.
  Cikin daka tsawa yace"kitty stop it!"
   Se kuwa ta tsaya cak bata hau kujerar ba se ma ja baya da tayi.
  Nan ya fizgo zarah ya dawo da ita gaban shi yana fad'in"ke kuma ki min shiru ko in 6a66ala ki a nn gurin wlh munafuka me kika mata da har take binki kin qara mata wata muguntar ko"
  Zarah bata iya bashi amsa ba se qara rirriqe shi tayi cikin kuka tana ihu sbd yanda kitty ta sake yunqurin cafko ta.
  Nan saif ya kore ta ta bar gurin,snn a natse ya kafe idon sa akan zarah dake rungume jikin shi duk ta cukuikuye shi bata ma san ya kori kitty ba se kuka take tana fad'in ita wlh bata mata komai ba dan Allah ya kore ta.
   Be ce mata komai ba se d'agota yayi tare da nuna mata kitty da idon shi.
  Nan ta juya taga kitty can nesa dasu near kitchen ta kame guri d'aya se kallon su take.
  Saifuddeen yace"kayan jikin ki ne fa idan baki je kin canza su ba zata sake biyoki dan yunwa take ji"
 Da sauri zarah ta kalli kayan jikinta atamfa ce me hoton kifi da aka d'anyi su manya jefi jefi a jikin atamfar se tayi kyau ba laifi.
 Ta juyo ta kalli saif idonta tap da qwallah tare da qara rirriqe shi.
  A hankli ya lumshe idanun shi tare da ware su akanta yace"No jeki kawai baza ta miki komai ba"
 Kallon kittyn tayi ta kuma kalle shi tana son wucewa amma kuma tana tsoron kar se ta kama hanya kitty ta bita.
  Saifuddeen da ya fahimci bata iya wucewa ga lokaci se tafiya yake driver na waje yana jiran ta,ya kama hannunta ya tafi da ita har bakin qofar d'akinta,byn ta shiga ya dawo downstairs ya zauna kan kujera tare da jingina bayan sa snn ya lumshe idanun sa a hankli yana jin yanda qamshin turaren zarah me dad'i ke tashi a jikin shi.
Sosai turaren ya masa dad'i sbd cool qamshi ne dashi ba me irin hawa kai d'in nn bane,se ma natsuwa da mutum ke tsintar kanshi a ciki.
   Kmr wanda aka tsakura ya bud'e idanun sa da sauri ya kalli kitty still tana can kame guri d'aya.
  Murmushi ya sakar mata kmr wata mutum ya tashi yaje ya d'auke ta yana bata haquri,snn ya shiga kitchen ya d'auko mata kifin gwangwani ya bud'e ya zuba mata a plate d'inta ta soma ci.
  Zarah kuwa tana canzo kaya da saurinta ta fita taje ta sami driver ta shiga mota suka wuce.
   Da ta dawo tayi wanka ta shirya cikin qananun kaya snn ta girka abinci taci,tana kammala cin abinci,ta d'auko handouts d'inta tayi zaune tana dubawa kullum abun har ya zamar mata jiki sbd rashin abin yi ba kallo gata ita kad'ai a cikin gida,mostly yanzu saif in ya fita tun safe se dare yake dawowa amma duk wani abu da ta keyi a gidan yana gani dan duk ya dawo se ya duba a laptop d'in shi.
  Rnr Saturday da safe ta fito daga baya gurin shanyi sanye da kayan bacci riga da wando da kuma hular net a kanta tana riqe da bokiti a hannun ta.
  Tana shigowa falon ta tsaya da saurin ta tana kallon d'aya daga cikin en matan saifuddeen wato wnn wacce ta ta6a tare ta a ranar.
 Tana tsaye gun dining ta gama tsiyaya ruwan Lipton a cup,ta ciro wani magani a cikin aljihun wandon jeans d'inta ta 6alle qwaya d'aya ta saka a cikin ruwan Lipton d'in tare da saurin motsewa seyi take tana kallon gun staircase kar saif ya fito ya ganta dan shi take had'awa tea shine ta saka mishi desire tablet a ciki,dmn samun cikar burin ta dan ta fahimci ba wani rashin lafiya dake damun sa iko ne kawai irin nashi da ya maida su tamkar qwalama tatta6asu kawai yake ya bari amma sosai yake sakar musu kud'i kmr yayi wani abun dasu.
  Gyaran muryar da zarah tayi ne yasa ta d'ago a tsorace tana kallon bakin qofar falon,tana ganin zarah ce ta wani sha toka dan kar ma ta ga damar ta,hakan be hana zarah qarasawa gurin ta ba shaye da toka itama ta kalli ruwan Lipton d'in snn ta kalle ta tace"asararriya me kika sa masa a cikin ruwan Lipton d'in zaki kashe shi ne ko me?
  Ina ruwan ki da abunda na sa masa munafuka kin la6e kina kallo na to lafiyar sa nake nema masa ba wani abu ba.
  Zarah tace"Babbar qatuwar munafuka ta wuce ki dashi bazai nemi lafiyar da kansa ba se ke kuma har kina dube dube gudun kar ya ganki,wlh idan baki je kin zubar ba yana zowa zan gaya masa ne ehe.
   Naqi na zubar d'in kin dad'e baki je kin gaya masa ba.
  Kallon ta Zarah tayi tare da jinjina kanta taje ta zauna kan kujera ta d'aura d'ayar qafar ta kan d'aya tana fad'in"nida ke shege ka fasa ina nn har se yazo wlh.
   Komai kasa ce ma zarah tayi se kallon ta da take tana jin kmr taje ta shaqe ta.
 Ganin saifuddeen yana saukowa yasa dole ta d'auki ruwan Lipton d'in taje kitchen ta zubar a sink.
  Koda ta dawo har saifuddeen yaja kujera ya zauna fuskar sa ba yabo ba fallasa se kallon zarah yake wacce ita ma ta d'an kalle shi kawai snn ta tashi ta d'auki bokitin ta ta wuce.
  Yarinyar ta bita da kallo kana tayi d'an murmushi ta d'auki mug ta shiga tsiyaya masa wasu ruwan Lipton tana fad'in"hm gaskiya dear yarinyar nn da aka had'a ka da ita bagidajiya ce sosai,wae fa tea ta samu zan had'a maka daga kawai taga na zuba nescafe ta d'auka ko wani mugun abu ne har dasu min masifa wai nasa maka magani zan kashe ka,shine taje ta zauna tana jiran fitowar ka wae zata gaya maka ne idan banje na zubar ba,ni kuma abun nata se ya ban dariya naje kawai na zubar dmn na huta da ita dan bana son se ka zauna tazo ta cika min kai da banzan surutu.
  Tun farkon zancen ta har ta gama qyar saifuddeen ke kallon ta dan duk abunda ya faru yana can zaune gaban laptop yana ganin su.
 Komai bai ce da ita ba se miqa mata desire tablet d'in yayi wanda ya fad'i ne garin maida shi aljihu bata sani ba.
  Ras gabanta yayi mugun fad'uwa ta kasa kar6ar maganin se sadda kanta tayi qasa cike da jin nauyin sa,ya dakar mata tsawa yace"kar6i nace!
  Da sauri jikinta na rawa ta kar6a yace"6alle gabakid'aya ki zuba a ruwan Lipton d'in ki motse kmr yanda kikayi da farko.
  Da sauri ta kalle shi cikin mamaki se kuma ta shiga rarraba idanunta tana kallon saman falon har idanunta suka sauka kan abinda take zargi wato CCTV camera,bakinta na rawa ta kalle shi cike da son bashi haquri ya watsa mata wani irin mugun kallo snn yace"ki 6alle ki zuba nace!
  Ba musu ta 6alle gabakid'aya ta zuba ta kuma motse.
 Yace"oya drink it right now! in yaso kije can waje ki nemi banzan gardin da ze iya taimakar ki.
   Gwalo ido tayi tare da saurin marere ce masa tana bashi haquri.
  With deep voice yace"wlh ko ki sha ko na d'ura miki shi  yanzun nn very stupid kar6i!
  Ya d'auka ya miqa mata,jiki sa6ule  zata kar6a tasha suka ji qarar doorbell,ajiyar zuciya ta sauke a tunanin ta ko ta sami ku6uta ne se ganin tayi ya kalli qofar kawai ya maida duban sa gare ta kmr wani zaki yanda yasha toka yana jiran ta qar6a tasha.
  Ba yanda ta iya idanunta tap da qwallah ta kar6a takai bakinta knn suka jiyo zarah se ihu take a d'aki.
 Nan saifuddeen ya tafi da saurin sa ya haura sama zuwa d'akin zarah.
 Da shigar sa yayi turus cike da jin haushi yana kallon abunda take yiwa ihu,d'an qaramin spider ne ya korota a bathroom,wacce har ta tu6e ta ganshi shine ta fito aguje tana ihu,tana ganin saifuddeen ya shigo ta shiga nuna mishi spider d'in tana fad'in"wnn abun ne gizo-gizo bansan a ina ya fito ba dan Allah ka fitar min dashi tsoran sa nake wlh"
  Tsaye kawai saifuddeen yayi riqe da waist d'in sa ya kafe idon sa a kanta yana kallonta daga ita se towel riqe a hannunta bata d'aura ba se kare qirjinta tayi ya tafi har zuwa rabin cinyoyinta ya rufe ba'a ganin tsiraicinta se pant d'inta da yake d'an hangowa ta gefe kad'an,amma rabin mammanta duk a waje,tsoro be bar ta fahimci yanda take ba bare ta gyara se nuna masa spider take tayi tana roqon ya fitar mata dashi.
  Saifuddeen dake kallonta ya had'iye yawu sbd wani yanayi da yaji kansa a ciki.
 Ya riqo hannun ta tare da nuna mata qirjin nata da idanun sa yace"ae se ki kama wnn tukun ko zan iya abunda kk so"
  Zarah ta kalli qirjinta cikin sauri taje zuwa gyara towel d'in ta saifuddeen ya riqe towel d'in tare da fad'in"ae naga so kike in gani meye kuma na rufewa ko kin d'auka ban fahimci duk tsoron kitty da kikeyi na iskanci bane kinayi ne kawai dan ki riqa liqe min a jiki ko zan taya ki,shine kinga ba riba kika dawo kan spider towel a hannun ki kina min tallan jiki kinqi ki d'aura sbd yayi sauqin sa6ulewa na gani ki samu ido rufe na biya miki buqatar ki koh,to bari kiji even Sophie ma bata ta6a samun wnn abun da kk buqata a gurina ba and bazan iya cutuwar ta ba sbd ita kad'ai keda ni ba wata kucakar macen da ta isa.
  Kana yayi qasa da muryar sa yana kallonta cikin shafo fuskar ta yace"but kin bani tausayi zan taimake ki na rage miki wani abun kar ki fara kawo min qarti a cikin gida dan jarabar ki zata fi haka ma nasani.
  Zarah da gabad'aya ya gama cika ta a fusace ta buge masa hannu da ya shafo fuskar ta ya tafi dashi har zuwa saman mammanta yana shafawa.
 A kasale saifuddeen yayi d'an murmushi yace"kinji haushi ne dan nace bazan biya miki buqatar ki duka ba,ki gode Allah ma da na matse zan taimake ki.
   Ya qarashe mgnr ne tare da fizge towel d'inta da qarfi ya jefar.
  A rud'e zarah taje zuwa fasa ihu tana neman kare qirjinta da hannayen ta se jin bakin sa tayi a nata ya kuma jefa ta kan bed ya mata rumfa se mutsu mutsu take tana son qwatar kanta ya riqe mata hannuwa and still bakin sa a nata be barta ba har se da ya gama jagwalgwala ta son ranshi snn ya tashi yana me gyara buttons d'in rigar shi,yayinda ita kuma da saurin ta tasa blanket ta rufe jikinta cikin kuka tana mishi Allah ya isa.
Yayi murmushi tare da fad'in a ranki nasan gode min kike kina samin albarka kinji dad'i na sosa miki inda ke miki qaiqaiyi,idan jarabar taki ta sake motsa miki u are free zan qara matsewa na taimake ki,se ki riqa zuwa d'akina kina samuna kmr yanda kika ga sauran en matan nayi.
  Zarah dake kallon sa rai 6ace tace"Allah sauwaqe ai ko en matan banda asara banga abunda yasa suke faman bibiyar fankon namiji marar amfani irin ka da bazai iya ta6uka komai a kan mace ba se shirme.
  Saifuddeen da har ya juya zai fita daga d'akin,ya juyo ya kalle ta d'auke da mamaki a fuskar shi kana ya jinjina kansa d'auke da shu'umin murmushi,lallai kuwa yanzun nn ze nuna mata shi cikakken namiji ne da se tayi nadamar gaya mishi wnn mgnr.
  Nan kawai ya shiga cire kayan jikin sa idon sa akan ta yana mata wani kallo da ko be fad'a ta sani,zarah dake kallon shi se jin tayi gaban ta ya shiga dukan uku uku,ta tashi da sauri zata shige bathroom ya fizgo ta da qarfi ya maida ta kan bed ya haye ruwan cikin ta ya zaune se ihu take tana dukan shi ta koina,amma ko a jikin sa har ya gama  cire kayan jikin sa ya dawo kanta ze raba ta da d'an pant d'inda ke jikinta,ae kuwa duk inda hankalin ta yake ya tashi a rud'e ta shiga girgiza kanta cikin kuka tana fad'in"Dan girman Allah kayi haquri wlh Allah su6utar baki ne bazan sake ba,fir yaqi saurarrar ta se ma bakinta da nashi ya had'e.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Monday 26/02/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 25*
Snn ya shiga sarrafa ta son ranshi yayinda zarah keta kuka tana kokawar qwatar kanta,amma ina ta kasa tana ji se ci gaba yake da mata abubuwa da suka fi qarfin tunanin ta,wanda yayi enjoying sosai har yana gab da jefa qwallo a raga se kawai ya ture ta da saurin sa cikin buga tsaki ya kalle ta ransa a mugun 6ace yace"tafi can qazama kawai,kuma baki tsira ba wlh qazantar na tafiya se na koya miki hankli very stupid!
  Yana qarashe zancen ya nemi kayan shi ya saka snn ya fita daga d'akin se tsaki yake tayi.
  Zarah kuwa tunda ya ture ta ta nemi blanket ta rufe jikinta se bayan ya fita ne ta duba jikinta dmn taga wace irin qazanta ce ya gani a jikinta nn taga ashe On ne ya zo mata,bata yi mamaki ba duk da tasan cewa lokaci beyi ba da sauran kwanaki,amma tsoran da taji kad'ai ya isa yazo mata,wacce yanzu haka jikinta rawa yake tana jin kanta wani iri ba qarfi a jikin nata kmr an sa6ule mata jijiyoyin jikinta dan taji tsoro sosai fiye da tsammani.
  Hawaye ne suka silalo zar kan kumatunta ta share hawayen tare da had'e kanta da guiwa snn a hankali takai hannu kan boobs d'inta dake mata wani irin zafi kan yanda ya luguiguita su son ranshi cikin rashin tausayi.
  Kana ta janye hannunta a kan qirjin nata tare da d'ago fuskar ta se ga wasu hawayen agurguje sun sauko kan kumatun ta tsoron ta d'aya ce matan da yayi bata tsira ba se ya aikata mugun nufin sa a kanta ba kuwa zata barshi ba da yardar Allah.
 Jin yanda sanyi duk ya mamaye inda take zaune yasa ta share hawayen da ke kan fuskar ta ta miqe tsaye tana kallon gurin white bedsheets ne shinfid'e a kan gadon dik yayi sha6e sha6e da jini sam bata ta6a rushing kmr haka ba wnn wane irin tsoro ne taji da yawa haka tana ji ma jinin har ya fara bin cinyoyinta da sauri yana sauka daga kan jikinta se kace wacce ta haihu,blanket d'in da ke jikinta ma dik ya lalace,nn ta cire blanket d'in ta d'auki towel ta d'aura snn ta cire bedsheets ta goge jinin da ya zuba a qasa ta had'a da blanket ta tafi dasu bathroom ta saka a washing machine har ma towel d'in da ta d'aura duk ta cire ta had'a ta zuba arial ta kunna machine d'in snn taje zuwa wanka.
 Saifuddeen kuwa yana komawa d'akin shi kai tsaye kan sofa yaje ya zauna tare da dafe kansa at all ya rasa me ke masa dad'i be ta6a jin son kasancewa da mace ba lokaci d'aya kmr zarah har Sophie kuwa wacce duk iskanci sa da ita sau d'aya ma be ta6a yarda wani abu ya shiga tsakanin sa da ita ba,bazai manta ba akwai wani lokaci har kuka ta mishi amma be amince mata ba se rarrashin ta da yayi sbd yafi son se sunyi aure snn ko wani abu ze fara shiga a tsakanin su.
  Beji tausayin ta ba ma se yanzu da yaji irin yanda yake matuqar son kasancewa da zarah,dashi kad'ai yasan irin abunda yake ji.
  Tsaki yayi tare da ciro joystick d'in shi cike da takaici yana kallo yana jin kmr ya gundule abun ya yar,meyasa ze ji son kasancewa da wnn abar er qauye ma da sam ba ajin sa bace.
  Nan kawai ya cire kayan jikin sa ya fad'a bathroom dmn ya watsa ruwa ko zai ji sauqin abunda yake ji.
  Se bayan ya fito har ya shirya snn yake tuna wacce ya bari a falo,koda ya sauko downstairs be ganta ba,d'an shu'umin murmushi yayi dan yasan abunda zai faru knn ba samun ta zeyi ba ta gudu amma dolen ta zata dawo sbd komai nata bata samu ta d'auka ba haka ta tafi ta bar jakar ta har da makullin motar ta duk suna nn ajiye a d'akin shi,wacce sosai taso ta tafi da abunta amma se ta sami d'akin nashi a rufe ya kuma zare key,wanda ya rufe d'akin nasa ne a lokacinda ya tafi da sauri zai je d'akin zarah ya biya d'akin nasa ya rufe ya tafi da key sbd yasan dole zata gudu shi kuma so yake se ya hukunta ta ta yanda ko a mafarki baza ta sake yunqurin masa abunda tayi niyyar aikata mishi ba.
 Komawa yayi ya d'auko makullin motar sa ya tafi zuwa gidan su jamil dan yana tunanin shine d'azun ya danna doorbell kafin zarah tayi ihu sbd yaga missed calls d'in sa sunfi a qirga.
  Be wani jima sosai ba ya dawo wanda har a washe gari be sake sa zarah a ido ba wacce tana can d'aki kwance kmr wata marar lafiya har yau ta kasa jin qarfi a jikinta kuma ko kad'an bata son ta fito suyi arba dashi dan ko kayan da ta wanke jiya,bedsheets towel da blanket se da taji ya fita snn ta fito ta bawa mai gadi ya shanyo mata,snn yau da suka bushe ya linke ya kawo mata an kuma yi sa'a saif d'in baya nn ya fita dan har ma ta samu tayi share sharen gida dama komai be dawo ba haka ma rnr Monday har tayi aikinta ta wuce school basu had'u ba.
 Da suka gama lectures kai tsaye gida tasa driver ya kaita wato can gurin su umma.
  Da shigar ta ta had'u da Saifuddeen ya fito kitchen riqe da meat roll a hannun sa yana ci suna had'a ido tayi saurin janye idanunta ta haura kawai zuwa sama.
  Nan se ga umma ta fito daga kitchen ta sami saif tsaye yana bin guri d'aya da kallo,da har zata tambaye shi me yake kallo se taga ashe zarah ce wacce har ta shige d'akin umma bata yarda ta juyo ba dan bata ma ga lokacinda umma ta fito daga kitchen ba.
   Umma bata ko san da zuwan nata ba ganin ta kawai tayi haka ma saif wanda yaje yayi zaune abun shi kan doguwar kujera 3seater yana ci gaba da cin meat roll d'in shi.
  Umma kuma ta haura sama zuwa d'akin nata de de zarah zata fito tana ganin umma ta shigo tayi tsaye tare da sadda kanta qasa ta gaida umma muryar ta a hankali.
  Umma bata amsa gaisuwar ba se kama hannunta tayi ta tafi da ita suka zauna kan sofa tana kallon ta da kulawa tace"lafiya zarah me yake faruwa kinxo gida baki ce min zaki zo ba kuma da alama dawowar ki knn daga makaranta kika yo nn,kaddai kice min har saifuddeen ma bai san zaki zo ba dan naga kallon da yake miki knn ko?
 A sanyaye zarah ta d'ago ta kalli umma se kuma tayi qasa da idanunta muryar ta can ciki tace"inna ni bazan iya auren nn ba na gaji dan Allah kice ya sake ni"
  Umma dake kallonta da mamaki tace"kina da hankali kuwa zarah,kin san me kike fad'a duka duka yaushe ne aka yi auren nn da har zaki fara zo min da wnn zancen iye,idan ma fad'a kukayi na gaya miki fa ita rayuwar aure dole se da haquri dukkan mu nn haquri muke tayi zarah ba wai dan muna jin dad'in rayuwar auren d'ari bisa d'ari ba,dan haka ko mene ne kije kici gaba da haquri,kuma kar in sake ganin kin d'auko qafar ki kinzo ba tare da izinin sa ba wai dan kunyi fad'a kinji ko!
 Cikin muryar kuka Zarah tace"ni inna ba fad'a mukayi ba kawai dai bana son in koma gidan har abada wlh na gaji da auren.
  Shaye da toka Umma tace"kinga bana son shirme,tashi idan kina jin yunwa kije ki d'ebo abinci a dining kici,idan saif ze tafi ku tafi tare.
 Zarah dake kallon umma qwallah ne suka ciko tap a idon ta tace"inna dan Allah ki fahimce ni wlh ba shirme nake gaya miki ba,har yanzu baya son auren nima haka muna zama ne kawai.
  Umma tayi shiru tana kallon ta can ta numfasa muryar ta a natse tace"ki dai ce kece ba kya son auren dmn tunda akayi auren nn saif be ta6a kawo min wani zance ba se ke,har kina cewa nasa ya sake ki zarah ba kya ko tunanin idan Alhj yaji ya zai ji shida yake farin ciki nn gaba kad'an ze fara ganin en jikokin sa.
  Hawaye ne suka silalo a hankli kan kumatun zarah ita kam ya tasan zatayi yiwa umma bayani ta fahimce ta ko kad'an bata son komawa tana jin tsoron muguntar da saif zai aikata a kanta idan ta fita On,qila ma kashe ta kawai zeyi dan ta fahimci mugun mutum ne shi marar tausayi,mammanta da ya mammatsa son ranshi gasu nn har wani girma suka qara.
 Umma dake kallon ta tasa hannu ta share mata hawaye cikin muryar rarrashi tace"tashi  muje ki samu abunda kika ci ku tafi bana son Alhj ya dawo ya same ki gidan nn bansan me zan gaya masa ba dan in ya ganki dole zei fahimci kina cikin damuwa ne,kin bayyana ta a fili se kace wani abun aka miki bayan kuwa rigima ce kawai kike son d'auko mana,saif be fara ba se ke da nake tunanin zakiyi haquri ki zauna.
 Komai zarah bata ce da umma ba se tashi tayi had'e da jakar ta dake hannun ta,dan abunda take ciki ma bazai bar ta iya cin abinci ba komawa gida kawai zatayi ta shiga tunanin wata mafitar.
  Nan sun fito knn se ga saif yazo yace da umma shi zai tafi.
  Umma ta kalli zarah wacce tayi saurin d'auke idon ta akan saif da ya kalle ta tace"Ayya gashi kuwa har nace da zarah tayi sauri taci abinci ka koma da ita.
  Kafin saif yace komai zarah tace"Ni a qoshe nake amma ya tafi kawai zan nemi adai dai ta"
  Umma tace"Aa ki bishi dai ku tafi tunda baza kici abincin ba ko ba gida zaka je bane saif?
  "Gida zanje"
Ya fad'a a taqaice ba tare da ya jira me umma zata ce ba ya sauka zuwa downstairs da niyyar yana sauka fita kawai zeyi yaja motar sa ya tafi.
  Amma kuma kusan tare suka sauko kawai dai shine gaba suna baya.
 Da saukowar su umma taje kitchen da sauri ta d'ebowa zarah meat roll a leda snn ta raka su har mota tana tsaye har suka fita gate d'in gidan kana tayi murmushi tare da girgiza kanta haka take ganin fushin masu ciki ne kawai ke damun zarah shine ta d'ebo qafa wai ita auren ya ishe ta.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: Thursday 01/03/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 26*
Suna isa gida da saurin ta zata fita mota se jin tayi ya riqe mata hannu ta kalle shi fuskar ta a d'aure haka shima tasa fuskar a d'aure yace"uban me kika jeyi gida without my permission?
 "Ina ruwan ka"
ta fad'a tare da saurin fizge hannun ta zata fita ya koma fizgo ta ya riqe hannun ta gam yana kallon ta kawai se kokawar qwatar kanta take cike da son yin kuka dan kuka take ji sosai shine ta matsu taje d'aki ta samu tayi ko zata ji sauqin damuwar da take ciki.
  Ganin ta kasa qwatar kan ta yasa ta kalle shi qwallah tap a idon ta kmr zasu zubo tace"ka sake ni dan Allah"
  Saifuddeen dake kallon ta shaye da toka yace"gaya min se yaushe ne qazamin baqon naki ze tafi?
  Dam taji gabanta ya fad'i dan gobe ne kad'ai baza ta shiga tsarki ba,amma ta daure cikin shan toka tace"ban sani ba"
  Ihu ta saki sbd marin da ya saukar mata.
 Snn ya matse kumatun ta sosai  yace"i will slit ur mouth right now wlh! gaya min kwana nawa kike yi!
  Shiru zarah ta mishi se kuka da take yi.
Yayi tsaki tare da sakin ta yace"oya fita in daina ganin ki a motar nn.
 Jiki sa6ule zarah ta bud'e ganbun motar ta fita,saifudden ya bita da kallo yana fad'in"ko baki fad'a ba dole dan ubanki zan kama ki ne ae er rainin hankli bazan qyale ki ba wlh se na koya miki hankali very stupid in ni sa'an ki ne da zaki riqa gaya min duk mgnr da ta fito bakin ki.
  Nan de ya qaraci masifar shi ya fita daga cikin motar ya rufe ya shiga ciki.
 wanda kai tsaye da shigar sa d'aki gun fridge ya nufa ya bud'e ya d'auko ruwan gora masu sanyi ya tsiyaya a cup snn yaje kan sofa ya zauna tare da kafa ruwan a bakin sa be janye ba se da ya shanye ruwan kaf snn ya jefar da kofin har se da qarar fashewar kofin ya tashi kitty dake kwance kusa da shi kan sofa tana bacci,wacce tana ganin shi da saurin ta tazo jikin sa be kula ta ba se ture ta yayi gefe,ya dafe kansa yana me d'an murza gashin kansa a hankli yana jin kmr bazai iya haqura har zara ta fita on ba,dan kmr kar ya ganta yaji komai ya dawo mishi sabo sbd tun rnr da yaso kasancewa da ita be sake sa idon shi akan ta ba haushin
kansa da haushin rashin samun kasancewa da ita be bar ya d'auko laptop d'in shi ba bare ya duba ya ganta.
  Zarah kuwa da taje d'aki kuka tayi me isar ta se bayan ta gama snn ta shiga tunanin ko dai rimin dako zata je da sunan ganin gida tayi zaman ta can se wanda ya gani,kuma ba makawa idan ta gayawa kawunta yanda akayi auren ba me so a cikin su da wahalar da take sha a gidan bazai goyi bayan ta dawo ba ze mata tsaye har se an raba auren.
  Murmushi tayi tare da share hawayen kan fuskar ta,take kuma se jikinta yayi sanyi ta shiga tunani to ya ma zatayi a bar ta taje rimin dako d'in kafin jibi,dan tasan umma ce mata kawai zatayi ai inna bata jima da zuwa ba,kai koma dai yaya ne zata kira umma gobe da safe in yaso ta ajiye mata kuka ko Allah ze sa ta bar ta taje.
  Haka ta ajiye zancen se a washe gari bayan tayi sharen sharen gidan har ma tayi shirin ta tsaf na zuwa school,dan tafi son se taje school tayi ban kwana da en sabbin qawayen ta da suke course d'aya snn idan ta dawo ta tafi.
  Nan ta kira umma a waya se bayan sun gaisa snn ta marere ce murya sosai tace"inna dan Allah yau ina son zanje rimin dako inga mutanen gida ina kewar su"
  Umma tace"ae na gaya miki zaki je zarah amma ba yanzu ba ko,tunda kinga inna da yayanki basu jima da zowa ba snn kuma gashi kina zuwa makaranta ki bari idan anyi hutu se kije kinji.
  Muryar ta kmr zatayi kuka tace"dan Allah inna ki barni inje wlh ina kewar su sosai"
  Umma tace"shikenan naji amma ba yau ba se zuwa weekend se kije kiyi ko kwana d'aya ne ki dawo.
  Kuka zarah ta saki a hankali snn tace"ae inna komai ya gama faruwa a lokacin"
  Umma tace"me ya gama faruwa a lokacin wani abu aka ce miki za'ayi a rimin dako?
  Zarah da bata san ma ta fad'i haka ba da saurin ta tace"Aa ina nufin ni nafi son inje kafin lokacin,koda anjima ne da yamma se na tafi ko a motar tasha ne.
  Umma tace"Aa zarah ki dai yi haquri zuwa weekend se nasa driver yakai ki"
  Wayyo Allah inna wlh bazan iya jira har lokacin ba yau nake so in tafi.
  Cikin fad'a umma tace"ha'a! wae lafiyar ki zarah tsakanin jiya da yau duk kin bi se rigima kike ji,idan har ma qunci kike ji a ranki kiyi tayin addu'a ko ki d'auki al'qur'ani ki karanta bawai kizo ki ajiyewa mutane rigima ba,har ina gaya miki magana kina min gardama,to bari kiji baza kije ba se weekend na gaya miki.
  Daga haka umma ta tsinke wayar.
 Nan Zarah ta saki wani sabon kuka shikenan ae muguntar saif zata hau kanta kafin lokacin,sam bata son ya 6ata mata rayuwa snn wai ko zata bar gidan ae ya shammace ta da yawa,ba mamaki ma kwashe kwashen en matan sa da yake ya kasowa kansa wani ciyon yazo ya liqa mata.
  Da saurin ta tayi shiru tare da share hawayen ta,lallai dole ne tana shiga tsarki baza ta sake fita ba rufe d'akin ta zatayi da makulli,da akwai kayan tea a d'akin ta riqa shan tea kawai har se rnr da za taje rimin dako,idan drivern da ze kaita yazo snn ko zata yarda ta fita.
  Tayi nazarin ne tana me kallon key d'in qofar d'akin.
  Hakan ya ganar da saif abunda take niyyar aikatawa wanda yana can d'akin sa a gaban laptop yana kallon duk abunda yake faruwa har wayar da tayi da umma duk yaji.
  Ya saki shu'umin murmushi tare da girgiza kan sa yana fad'in"komai tsulla tsullan ki se na koya miki hankali ba dai da kika tsokalo ni ba,in kukan me zakiyi kuwa bazan barki ba har se na cimma burina,nida ke zanga wanda zeyi nasara akai.
  Nan ya rufe laptop ya kwanta tare da kai hannun sa kan tsakiyar cinyoyin sa yana shafa gurin cike da murmushin mugunta.
 Zarah kuwa tana gama nazarin ta ta gyara fuskar ta kmr ba wacce tayi kuka ba snn ta fita ta samu driver ya kaita school.
  Washe gari Wednesday tunda asuba tsarki ya kamata dan kusan ko yaushe da asuba tsarki ke zo mata taje tayi wanka.
 Bayan ta ida sallah ne zata koma kwanciya da niyyar shikenan baza ta sake bud'e d'akinta ba har se rnr da zata je rimin dako,se kuma ta shiga tunanin kuma fa rashin zuwan ta school zae yi saurin fahimtar da saif cewa ta shiga tsarki shine ta shiga wasan 6uya dashi,ba kuwa zata so ya fahimta ba,tunda kwana biyu ya rage a shiga weekend gwanda kawai taci gaba da zuwa school in yaso idan ta dawo se ta riqa rufe d'akin ta tunda tana rigon shi dawowa gida.
   Nan ta fasa komawa baccin,ta hau gyara d'akin har bathroom duk ta wanke,koina ya zama neat se qamshi d'akin keyi sbd room fresh d'inda ta fesa.
 Bayan ta gama da d'akinta ne ta sauko downstairs shima ta gyara koina har kitchen,snn ta fita ta share filin gidan ta bawa flowers ruwa.
  A gajiye ta koma d'aki ta fad'a bathroom ta sakarwa kanta shower ko zata sami sa'ida dan ba kad'an ba sharar filin gidan na wahalar da ita fad'i ne dashi sosai shiyasa idan tayi yau gobe bata yi.
  Tana fitowa tasha fresh milk me sanyi snn tayi shirin zuwa school driver na zowa ta fita suka wuce.
  Se a snn saif ya rufe laptop d'in shi d'auke da murmushi wanda tun dawowar sa daga sllr asuba yayi zaune yana ta kallon duk abunda take yi tun daga kan sllr da tayi har gyare gyaren gidan dama komai duk akan idon sa yana kallo kmr me kallon film.
  Bacci yayi abun shi har se 9 snn ya tashi yayi wanka ya shirya ya fita.
  Qarfe shida da rabi nayi ya dawo gidan dan yasan confirm zarah ta isa dawowa dmn wa dalilin ta kad'ai ya dawo sbd ya koya mata hankali acewar shi,bayan kuwa sha'awar ta ce ta dame shi ko aikin kirki ya kasa yi tunda yaje asibiti se tunanin ta yake tayi yana ayyana yanda zai kasance da ita.
  Amma koda yayi wanka yaje sllr magrib yana dawowa kae tsaye d'akin ta ya nufa se be same ta ba ya duba har bathroom bata nn dama ko ina a cikin gidan duk ya duba be ganta ba.
  "Kaddai yarinyar nn wayo ta min"
ya fad'a tare da komawa d'akin shi ya duba laptop d'in shi yaga tunda ta fita da safe bata dawo gidan ba,lallai kuwa tunda bata dawo ba bata ma san shirin sa ba bare har ta mishi wayo.
  To ina ta shiga? ya tambayi kanshi tare da d'aukar wayar sa ya kira drivern da ke kaita school ya tambaye shi ina yakai zarah da ya d'auko ta school?driver yace ae shi tunda ya kaita da safe har yanzu be koma school d'in nasu ba,kmr kullum idan ta gama lectures kiran sa take yaje ya d'auko ta amma tun d'azun yaji shiru har yanzu bata kira shi ba.
  Tsaki saif yayi tare da fad'in"shikenan se baka je ka duba ta ba,ka sani ko wayar ta ce ta sami matsala"
  Drivern yace"Dan Allah ayi haquri yalla6ai yanzun nn zanje na dubo ta  wlh tunanin hakan sam be zo min ba....ka barshi bana so zanje da kaina,saif ya fad'a tare da tsinke wayar ya tashi ransa a 6ace ya d'auki makullin motar sa ya tafi se school d'in su zarah,duk inda yake tunanin ya ganta be ganta ba hakan ya koma jan motar shi ya tafi sai gida gun su umma,da shigar sa Nusaiba ta sauko downstairs knn zata je kitchen ya riqo ta da saurin sa tare da fad'in yauwa Nusaiba ina wnn yarinyar tazo gidan nn?
  Nusaiba tace"indai 6ter kake nufi bata zo ba tun d'azun ma se kiran ta nake a waya naji wayar ta a kashe da na tambayi umma se tace min maybe bata da caji ne dan da safe ma sunyi waya da ita.
  Yace"shikenan kar ki bari umma taji wai nazo neman ta kiyi shiru da bakin ki"
  Yana qarashe zancen ya fita ba tare da ya jira me Nusaiba zata ce ba ya tafi se gidan su jamil.
  Be shiga ciki ba se kiran sa yayi a waya,jamil yana fitowa yace"lafiya baka shiga ciki ba?
 Saif yace"ba wnn ba mutuniyar ka ce ban gani ba tun safe da taje school bata dawo ba,na tambayi drivern da ke kaita yace tun safe da ya kaita be koma ba jiran yake idan sun gama lectures takira shi ya d'auko ta amma har yanzu shiru bata kira shi ba,da kaina naje school d'in su na neme ta koina ban gan ta ba,na kuma je gida gun su umma bata can.
  Gaban Jamil ne yayi mugun fad'uwa yace"ka mata wata muguntar koh shine ta gudu?
  Mtsw saif yayi tsaki tare da fad'in" kaga ni ba abunda na mata da safen nn kawai dai bansan meyasa bata dawo ba,ban kuma zo dan ka gaya min mgnr banza ba nazo ne muje ka tayani neman ta kafin su Abba suji.
  Rai 6ace jamil yace"bawani ka mata wata muguntar dai ne dan haka kawai baza taqi dawowa ba.
  A qufule saif ya kalle shi kafin yace komai wayar sa ta hau ringing koda ya duba d'aya daga cikin en matan shi ne keta kiran shi wato wacce ta zuba mishi desire tablet a ruwan Lipton,tun d'azu da safe yake ta ganin kiran ta yaqi ya d'aga a tunanin sa ko haquri zata bashi shine yaqi ya d'aga dan baya ko son ya saurare ta,har text ta turo mishi amma duk yaqi dubawa dan ba kad'an ba so yake se ya hukunta ta snn ko ze bata kayan ta dake hannun shi.
 Tsaki yayi tare da d'aga wayar cike da son ya balbale ta da masifa,amma jin bayanin da ta koro ya sa shi yin shiru yana sauraren ta ransa a mugun 6ace,dan gaya mishi take zarah na hannun ta ita tasa akayi kidnapping d'inta,idan har yana son ta maida ta tofa lallai se ya kawo mata motar ta da jakar ta yanzun nn ko kuma ya sami gawar zarah an jefar idan har ma wnn be dame shi ba to kuwa da kanta zata je gidan su ta sami mahaifin shi ta gaya mishi abunda ke tsakanin su dama wanda be ta6a shiga a tsakanin su ba,idan ka shiryi kar6ar zarah d'in se ka duba text d'inda na turo ma.
Tana kaiwa nn ta tsinke wayar.
  Nan saif ya hau duba text d'in da saurin sa.
  Jamil da yaji duk abunda yarinya ta fad'a sbd muryar tana d'an fitowa ana jin me ake cewa,rae 6ace yace da saif wace ce wnn er iskar!?
  "Farida ce"
Saif ya fad'a a taqaice tare da bud'e ganbun mota ya shiga,shima jamil ya zagaya ya shiga yana me tambayar saif me ya had'a ku da zata mana wnn iskancin?
  Saif yaja mota ransa a 6ace yana fad'in banni da er iska ni zata raina!yayi qwafa tare da fad'in zan mata abunda take so tukun na samu er mutane ta dawo.
  Jamil dake kallon sa yace"ba dole ta raina ka ba ta gama ganin girman ka a banza,wlh duk wani abu ya sami zarah se na gayawa Abba duk abunda ya faru,ko ze raba auren ta huta da muguntar ka.
  Shaye da toka saif ya kalle shi cikin doka mai harara yace"kar ma ka jira har se munje ka kira shi yanzun ka gaya mishi in ya raba auren se ya baka auren ta,jarababbe kawai da bega abun so ba se wnn abar.
 Yayi tsaki tare da kiran farida a waya yace mata gashi nn ze kawo mata kayan ta su had'u gurin da tace.
 Yana gama fad'a be jira me zata ce ba ya tsinke wayar ya nufi gidan shi ya d'auko jakarta da makullin motar ta ya bawa jamil yace ya hau motar shi kuma se yaja tashi motar su tafi gurin da tace.
  Ba musu jamil ya kar6a suka tafi,gurin can bayan gari ne daji sosai duhun duhun ba wani haske se na motar su.
 Suna fakawa Saif ya kirata a waya yana fad'in"gamu a gurin mun kawo miki kayan ki ki sako er mutane ko kuma wlh na sako police a harakan nn.
  Yana kai qarshen zancen sai ganin Zarah sukayi wasu qarti sun tunkud'o ta da qarfi daga bayan wata babbar bishiya har seda ta fad'i.
  Saif da jamil kowannen su da sauri ya fito daga cikin motar da yake suna rigangan isa gurin Zarah,saif ne ya fara isa ya kama hannun ta ya tada ta,da saurin ta ta fizge hannun nata shaye da toka taja baya bata son ya koma da ita,dan d'auke tan da akayi ya mata dad'i a tunanin ta shikenan ta ku6uta daga muguntar shi,su kuma har ta tsara yanda zata tsere daga hannun su ta gudu zuwa rimin dako.
  Sannu basu ji maki ciwo ba?
 Cewar jamil wanda duk ya damu sosai.
  Kafin zarah tace masa komai,saif ya fizgi hannun ta a fusace ya kaita mota ya tura ta gidan baya ya maida ganbu da qarfi ya rufe.
  Jamil da har ransa yaji zafin yanda ya fizge ta ransa a 6ace yace"haba saif meye haka dan Allah ae se ka ji mata ciwo"
  Sai me to idan na ji mata ciwo,baka ganin yanda taja baya wai ita bata so mu tafi bansan uban me zata tsaya wa yi tare da mugayen mutanen ba.
  Jamil yace"ba dole ba kafi su zama mugu ai dole taji tsoron komawa gurin ka.
   Jamil!!
Saif ya fad'a da qarfi cikin murya me cike da 6acin rai snn ya nuna shi yace"wlh idan ka koma gaya min maganar banza zan barka a nn!
  Tsaki jamil yayi tare da bud'e ganbun mota ya shiga 6angaren me zaman banza.
  Saif da ya riga shi shiga ya fizgi motar  da qarfi suka bar gurin.
 Ba wanda ya sake cewa uffan har yakai jamil gida snn ya wuce gidan shi,suna isowa da sauri zarah ta fita mota ta shiga ciki har tana had'awa da gudu gudu dmn ta samu ta isa d'aki ta rufe da makulli kafin saif ya cin mata dan tun cikin mota sun sauke jamil kafin su iso yake gaya mata yau se ta gane kuskurenta.
  Amma kash duk saurin ta tana rufe qofar zata sa key taga wayam ba key a jikin qofar ya zare key d'in tun da safe kafin ya fita.
  Kafin tayi komai se jin kanta tayi qasa ya banko qofar da qarfi ya shigo,key a hannun shi yasa ya rufe qofar ya kuma zare key d'in ya cillar dashi can saman wardrobe.
  A rud'e zarah ta shiga ja baya tana neman tashi dmn ta gudu zuwa bathroom,se kawai ya nuna mata makullin bathroom d'in gashi a hannun shi,tana gani shima ya cillar dashi zuwa saman wardrobe snn ya shiga 6alle buttons d'in rigar shi.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Thursday 01/03/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*


_Ga wnn kad'an ne a tunani na ma baza ku samu na dare ba_


*«»Page«» 27*
Lokaci d'aya idanun ta suka ciko tap da qwallah,ta had'e tafukan hanneyen ta se haquri take ta bashi be kula ta ba har ya gama 6alle buttons d'in rigar shi ya fara tako zuwa inda take,a rud'e ta shiga ja baya tana girgiza mai kanta.
  Jin ta had'a bayan ta da jikin bed yasa ta juya da sauri ta miqe tsaye,se jin tayi ya kama kafad'un ta ya zaunar da ita da qarfi kan bed d'in,tare da d'aura d'ayar qafar sa a kan gadon ya rankwafa gab da ita  ya tallabo fuskar ta yana kallon yanda hawaye suka sauko aguje kan kumatun ta.
 Muryar ta na rawar kuka tace"dan Allah kayi haquri wlh ban ta6a yi ba kar ka lalata min rayuwa na roqe ka"
 Shaye da toka yace"ni kuma kinsan na ta6a yi koh"
 Cikin langwa6ar da kai tace"Ae kai namiji ne"
Yanayin yanda tayi mgnr cikin marerecewa se ya bashi dariya amma yasha toka yace"Au mu maza se aka ce bama jin ciwon mu lalata rayuwar mu kan inda bata dace ba,ko kin manta u are not my type sam ba ajina bace ke ina kuma jin ciwon yanda zan fara d'aura joystick d'ina akan ki abunda Sophie ce kad'ai ya kamata ta fara samun wnn damar,not u er qauye wacce ba dan zan koya miki hankali ba na nuna miki ni cikakken namiji bane da ba abunda zai sa na had'a jikina dake.
  Da sauri tace"Wlh kai cikakken namiji ne wasa nake da nace maka fanko.
  Yace"what! yaushe na zama abokin wasan ki"
 Da sauri cikin girgiza kai tace"ina nufin qarya nake na fad'a ne kawai.
 Wata dariyar ya koma ji yanda duk ta rud'e amma still ya koma shan toka yace"ae tunda har kika furta bazan d'auki raini ba se na koya miki hankali,ita wacce ta gaya miki ni fanko ne da kanki se ki mata bayanin ainihin waye ni tunda abunda take son ji knn.
  Ya qarashe zancen ne tare da kai hannu ze zuge zip d'in wandon shi.
zarah ta fasa ihu tare da saurin rufe idanunta.
  Se kawai ya fasa zuge zip d'in se hannun sa yasa ya janye hannuwanta da ta rufe fuskar ta dasu yana kallon ta yace"ba kya so ki ganni?
 Da sauri cikin gyad'a masa kai tace"eh wlh bana so"
  Yace"to ni ina son inganki.
  Ta gwalo ido cikin girgiza kai kafin take marerece masa tace"wayyo dan Allah kayi haquri"
  Be saurare ta ba kai tsaye ya soma cire kayan jikinta d'aya bayan d'aya se ihu take tana son hana shi.
   Amma yanda ya kwantar da ita ya daddanne baza ta iya komai ba tana ji har ya raba ta da komai nata,ya kami boobs d'inta se matsar su yake son ranshi tare da had'e bakin sa da nata dan baya son jin kuka da ihun da take ta mishi.
   A hkn ya samu ya sa6ule kayan jikin shi yana ci gaba da wasa da koina na jikinta cike da son yaga ya fitar da ita hayyacin ta dmn ya samu ya same ta yanda yake so amma fir be samu hakan ba,se kuka da take tayi tana son qwatar kanta,tana ji da saurin shi jikin sa na 6ari ya fara yunqurin shigar ta,nn wani irin qarfi yazo mata ta qwace hannayen ta da ya daddane,ta rirriqe shi snn ta kame jikinta sosai ko yaya ya kasa wucewa ta rufe qofar bam,haushi ne ya kawo masa iya wuya be san lokacinda ya shaqe ta ba yace"zaki saki jikin ki ko se na burma ta qarfin tsiya na miki kaca kaca a nn gurin"
   Komai bata iya cewa ba se wani irin tari da yazo mata kan yanda ya shaqe ta,ba tare da ya damu da yanayin da ta shiga ba yasa iya qarfin sa zai shige ta,tayi kukan kura tare da tunkud'a shi gefe ya fad'i da saurin sa ya taso cikin mugun 6acin rai taja baya da sauri tasa blanket ta rufe jikinta,tana kallon inda ta bari yayi stain,shima ya kalli gurin tare da fincike blanket d'in da ta rufe jikinta yaga On ne ya dawo mata.
  Take idanun sa sukayi wani irin jajur ya fizgo ta a fusace  yace"me zan gani qazamin baqon ki ne wai ya dawo!to wlh bari kiji yanzun nn zan mayadda shi inda ya fito bazai hana min abunda nayi niyya ba se na koya miki hankali.
  Nan kawai ya kama ta ze kwantar,ta fashe mishi da kuka
tare da cukuikuiye shi tana bashi haquri.
  Ya tsaya tare da karkatar da hankalin shi yana sauraren door bell da ake ta fmn dannawa be damu ba se komawa yayi kanta ya d'ago ta daga kan qirjin sa jikinta na wani irin rawa hawaye sha6e sha6e kan fuskar ta har suna d'iga kan qirjinta,ya kafe idon sa a gurin snn a kasale cike da sha'awa ya d'aura hannun sa a hankali kan d'ayan mammanta da hawayen ke d'iga akai,da saurin ta taje zuwa ture hannun shi sbd masifar zafi da boobs d'in ke mata,shaye da toka ya mata wani kallon da ya dakatar da ita,se kuma fuskar sa ta canza yayi shiru kmr me wani nazari yana zuwa da hannun shi a hankli under mammanta yana sauraren yanda zuciyar ta keta halbawa sbd tsoro,kmr da alamar tausayi ya d'ago fuskar shi yana kallonta,ta kame guri d'aya bata son ta6a tan da yake dan se shafar qirjinta yake tayi amma idanun sa na kan fuskar ta da ta rufe idanunta hawaye duk ya jiqa eye lashes d'in ta sunyi wara wara abun sha'awa se duk ya shagala yana ta kallon fuskar ta and still hannun sa na kan mammanta be daina shafawa.
 Qarar phone d'in shi ne ya farkar dashi ya ture ta da sauri ya d'auki wayar dan Abba ne me kiran.
 Koda ya d'aga kiran cikin fad'a Abba yace"maza zo bud'e mana qofa tun d'azun se fmn kiran ka muke tayi a waya kaqi ka d'aga,ga doorbell muna ta fmn dannawa byn gateman ya shaida mana kuna ciki.
  Haquri saif ya bawa Abba acewar gashi nn yanzu ze zo ya bud'e.
 Nan suka tsinke wayar yaga missed calls ba dama,na Abba,Nusaiba har ma da na umma,amma duk beji lokacin da sukayi ta kiran nashi ba yayi mamaki dan duk yanayin da yake ciki tare da mace baya hana yaji ringing d'in waya se gashi akan wnn abar hakan ya fara faruwa dashi,ya kalle ta fuskar sa a d'aure wacce tuni ta rufe jikinta da blanket ta kame guri d'aya,bai ce mata komai ba se sauka yayi daga kan gadon ya nemi kayan shi ya saka snn ya kalli zarah da ta had'e kanta da guiwa she don't want see him nude yace"Da Allah yi sauri tashi kisa kayan ki gasu Abba nn shigowa kuma zan gaya musu cewa baki da lafiya dan haka u better pretend.
  Yana qarashe zancen kawai be jira me zata ce ba ya d'auko key a saman wardrobe ya bud'e d'akin ya fita se zuwa downstairs ya bud'e wa su Abba qofa,ya hango su jingine jikin mota tsaye suna jiran fitowar shi ya qarasa gurin su tare da fad'in umma,Abba lafiya me yake faruwa ne haka?
  Abba yace"uwar ka ce take faruwa ina zarah a ina ka ganta?
  Be ce da Abba komai ba se wani kallo da yayiwa Nusaiba na kin raina ni ko!?
  Tace"wlh yaya hankali na ne ya kasa kwanciya nikam"
  Yayi guntun tsaki tare da fad'in"Abba bafa wani abu bane kawai na manta ne sam ta gaya min cewa daga school idan sun gama lectures zata je gidan wata qawar ta kuma se gashi koda taje gidan bata jin dad'i shine ta kashe wayarta ta kwanta dmn ta d'an samu relief,yanzu haka da muka dawo tana d'aki kwance still she is not feeling fine"
  Abba ya numfasa tare da fad'in ae hankalin mu ne gabad'aya ya tashi da Nusaiba ta gaya mana kazo neman ta baka ganta ba,gashi ba'a samun wayar ta a kashe kai kuma se kiran ka ake kaqi d'agawa.
  Saif yace"kuyi haquri Abba na manta wayar ne a d'aki sbd gabad'aya am occupied naga cewa taci abinci tasha magunguna.
  To ae shikenan bari mu shiga muga ya jikin nata yake.
   Umma ta fad'a kafin suke shiga daga ciki suka zauna a nn falo,Saif ya haura sama zuwa d'akin zarah koda ya shiga har ta saka tufafin ta dan dama doguwar rigar atamfa ce,da kanshi ya d'auki hijab ya bata tasa ya riqo hannun ta suna fitowa daga d'akin ya kama kafad'un ta ya tafi da ita jikin shi kmr de wata mara lafiya a haka har suka sauko downstairs gabad'aya zarah se mamakin sa take ga kuma kunya da taji wacce suna isowa ta janye jikin ta daga nashi zata zauna kan rug,Abba yace"A'a zo nn zarah ki zauna inji ya jikin naki yake"
  Yayi mgnr ne tare da nuna mata kusa dashi kanta qasa ko kallon su bata iya yi taje ta zauna a kusa da shi d'in,ya dafa goshin ta se kuwa yaji zafi kmr da gaske d'in bata da lafiya haka ma kukan da tasha ya nuna fuskar ta kmr wata mara lafiya.
   Sannu ya mata tare da kallon saif yace"tana yin amai sosai ne?
  Yace"A'a bata amai zafin jiki kawai ne kuma da zarar tasha magani tayi bacci koda zata tashi komai ze dawo mata normal.
   Abba yace"to shikenan zo maida ta ta samu tayi baccin mu zamu koma Allah ya sauwaqe"
  Kmr da gaske yaje da kulawa ya kamata umma da Nusaiba se sannu suke mata,snn ya haura da ita sama su kuma suka fita.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Friday 02/03/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 28*
Suna isa d'aki ya tunkud'e ta daga jikin shi yana kallon ta fuskar sa a d'aure yace"cika ni kin wani liqe min a jiki matsoraciya kawai next time ba qazamin baqon naki ze dawo ba ko uban sa ne se na koya miki hankali,in gidan ku ba'a koya miki yanda zaki fiddowa babba magana ba ni nn zan koya miki.
  Yayi qwafa tare da zuwa gun wardrobe ya miqa hannun sa ya d'auko makullin bathroom snn yazo ya zare na qofa ya fita dasu.
  Binsa kawai zarah tayi da kallo snn taje jiki sa6ule ta kwanta a hankli kan gadon tana jin kanta kmr wata marar lafiya,duk ta qarar da d'an qarfin ta a gurin kokawar qwatar kanta daga saif,numfashi ta sauke a hankli cike da godewa Allah da ya ku6utar da ita yasa On d'in nn ya sake dawo mata duk da dai silar dawowar shi tsoran da taji ne,and tana ji a jikin ta kmr ta ku6uta daga muguntar saif knn,indai har Allah yasa On d'in be d'auke mata ba har lokacinda zata tafi rimin dako.
  Tana nn a nn kwance gurin bata sani ba bacci yayi awon gaba da ita.
  Ba ita ta farka ba se 11 ta samu da qyar ta miqe zaune dan jin jikin nata take kmr wacce aka yiwa duka,ta kafe idanunta tana kallon jikinta a ranta tana tunanin ya akayi bacci ya d'auke ta bata shirya kanta ba gashi duk jikinta ya lallace,fuskar ta a yamutse kmr me qyamar kanta ta tashi tare da cire bedsheet d'in gadon ta nufi bathroom bata fito ba sai da tayi wanka,tana d'aure da towel taje ta bud'e wardrobe ta ciro kayan bacci ta saka,taje da niyyar zata kwanta se jin take jiri na d'an d'ibar ta dan yunwa take ji sosai tun fresh milk d'inda tasha da safe ta bar gidan bata sake sa komai a cikin ta ba sam tama manta se yanzu take tunawa kan yanda cikin ta ke faman qugi ba sauqi.
  A hankali ta shafi cikin ta yanda take jin yunwar nn abu me d'an nauyi ya kama taci amma bata jin zata iya fita ta girka wani abu a cikin daren nn,da akwai Freshmilk a fridge taje ta bud'e ta tsiyaya a cup tasha me isar ta snn taje ta kwanta se bacci.
  Washe gari guraren goma saif ya fito cikin shirin sa na suit chocolate brown,ta cikin ce kawai milk amma tun daga ta sama,wando belt har takalmin duk chocolate brown ne,yayi kyau sosai se zuba amshi yake.
  Yana riqe da makullin motar shi ya fita,se hango drivern da ke kai zarah school yayi tare da gateman suna zaune guri d'aya se fira suke tayi.
  Drivern na hango shi ya taso da sauri yazo gurin shi cike da girmamawa ya d'an russunar da kanshi ya gaida shi,saif be amsa gaisuwar ba se cewa yayi"me ya faru ko ka sake tafka min wani shirmen ne kuma?
 Yace"yalla6ai tun kafin takwas nazo amma bata fito ba har yanzu kuma wayar ta a kashe,dana kira taka wayar kuma se ba'a d'aga ba.
  Saif da be ga kiran nashi ba ya ciro wayar shi ya duba yaga missed call lokacin yana bacci kuma mostly silent yake saka wayar shi idan ze kwanta.
  Ya kalle sa kawai ba tare da yace masa komai ba ya koma daga ciki ya haura sama zuwa d'akin zarah.
  Koda ya shiga ya same ta kwance ruf da ciki ta rungume pillown da take kwance akai se sharar bacci take kanta ba hula duk gashin kanta ya baje a saman pillow snn qafafuwan ta a hard'e d'ayan kan d'aya.
  Da har ya kalli fridge da niyyar d'auko ruwan gora masu sanyi dmn ya kwara mata ta tashi se kuma ya fasa ya kafe idon sa kawai yana ta kallon ta ya rasa meyasa yaga ta mishi kyau har yana jin wani abu na fizgar shi bayan ba wasu kaya masu sha'awa ne a jikin ta ba face riga da wando na bacci,kawai dai wandon a iya guiwa ya tsaya haka kayan d'as suke a jikin ta masu laushi da hoton katun katun a jiki.
 Tsintar kanshi yayi da zama saman gadon a hankli kmr wanda baya son ya tashe ta snn kmr da tsoro yakai hannun sa kan sumar kanta dake barbaje kan pillow,har ransa wani abu yake ji idan yaga sumar ta tamkar be ta6a ganin suma me tsawo ba a rayuwar shi wani irin kyau take mishi se yaga kmr ba nata bane dan sosai sumar keda santsi da laushi kmr baby hair da aka haifa yau yau d'in nn,gashi baqi sosai abun sha'awa,se jin yake kmr kar ya daina ta6awa amma dolen shi ya janye hannun sa da sauri sbd motsin da tayi ta gyara kwanciyar ta tare da sauke nannuyan ajiyar zuciya kmr me mafarkin an kama ta ta kufce.
 Yana nn zaune idon shi akan ta har se da baccin ta ya koma yin nauyi snn yakai hannun sa a hankli ya yaye mata sumar kanta da ta zubo ta rufe mata fuska,nn hannun sa ya d'an shafi gefen fuskar ta se yaji jikin ta da zafi kmn garwashi musamman saman goshin ta dan a hankali ya tafi da hannun sa yana ta6a jikinta har zuwa wuyan ta duk jikin nata zafi koina.
  Nan kawai ya d'aga ta cak kmr wata er baby ya zaunar da ita,da sauri zarah ta bud'e idanunta a d'an tsorace tana kallon shi,fuskar sa a d'aure yace"ya kin bar driver tun d'azu yazo yana ta fmn jiranki?
  Muryar ta can ciki ta marasa lafiya tace"bana jin dad'i ne bazan iya zuwa school ba"
 Me yake maki ciwo?
Ya tambaya fuskar sa ba yabo ba fallasa.
 Tace"kaina ne...
Se tayi shiru amma da alamar bashi kad'ai bane but she can't tell him.
  Saif da ke kallon ta yace"and what?
 "Ba komai"
Ta fad'a zata sauka kan gadon ya riqo ta se bin jikinta yake da kallo har ya sauke idon sa akan qirjinta yana kallon yanayin boobs d'in ta sunyi luhu luhu a jikin rigar snn nipples d'in ta sun bayyana a jikin rigar sosai.
  Ko bata fad'a ba ya fahimci suna d'aya daga cikin abunda ke mata ciwo dan muguntar da ya mata a kan su yasan dole ne zasu mata ciwo.
  Sam zarah bata lura da inda yake kallo ba sbd in seconds ne ya mata kallon,shiyasa kai tsaye se jin tayi hannun sa dumu dumu a cikin rigar ta yana ta6a mata boobs snn ya kama rigar ta da d'ayan hannun sa ze yaye ya gani,ranta a 6ace ta riqe rigar tare da saurin riqo hannun shi zata fitar daga cikin rigar ta,bata sami damar hakan ba se kuka ta fashe dashi sbd matse boobs d'inta da yayi.
  Yana kallonta hankalin shi a kwance yace"da zafi?
 Da sauri ta gyad'a mishi kai yayinda hawaye ke sauka a hankali kan kumatun ta.
  Nan kawai ya zare hannun sa a hankli daga cikin rigar ta ya shiga share mata hawayen yana fad'in"amma shine na samu kin kwanta akai"
  Shiru ta mishi dan ita bata ma san ta kwanta akai ba kawai dai a lokacin da ta gyara kwanciyar ta taji kmr an zare mata qaya.
  Bai damu da shirun da ta mishi ba se koma kai hannun sa yayi ze yaye rigar ta dmn yaga yanda mamman ta sukayi bcos da akwai maganin da yake son kawo mata but yafi son se yaga yanda maman sukayi tukun,amma se ta riqe rigar sosai taqi barin shi,ya girgiza kansa tare da ta6e bakin sa yace"wane dare ne kuma jemage be gani ba,ke kika sani idan suka ru6e ae se a yanke a yar kin ma huta da kayan nauyi.
  Zarah da duk haushin sa take ji ta kalle sa shaye da toka tace"ko na huta da muguntar ba,dan gwanda su ru6e akan kaci gaba da ta6a min.
 Tayi tsaki tare da tashi ta shiga bathroom ta banko ganbun qofar da qarfi ta rufe.
   Saifuddeen da yayi mgnr ne dan kawai ta barshi ya gani,yayi murmushi kawai snn ya tashi ya bar d'akin.
  Ya fita had'e da kiran jamil a waya,jamil na d'agawa yace"plz jamil idan zainab na free ka turowa mutuniyar ka ita bata jin dad'i naso na duba ta sbd ta raina ni taqi ta bari"
  Jamil yace"yawan masifar ka da muguntar ka yau da gobe ai dole yasa ta raina ka sbd sanin kanka ne farko ba haka take ba kai ka janyo wa kanka rainin"
   Saif yace"kaga jamil ba wnn na tambaye ka ba,ka turo mata zainab nace"
 Yayi tsaki tare da tsinke wayar ba  tare da ya jira me jamil d'in zai ce ba,ya nufi motar shi zai shiga knn se ga drivern zarah yazo da saurin shi yace"yalla6ai na ci gaba da jiran ta ne zata fito?
   "Aa"
Ya fad'a a taqaice snn ya shiga mota yaja ya fita daga gidan.

Kafin sllr juma'a ya dawo yayi wankan juma'a ya shirya cikin farin yadi ya fita.
Se bayan ya dawo snn ya tafi d'akin zarah,ya same ta ta ida sllh,qur'ani a hannunta tana karatun suratul kahfi,wacce a bayyane take karantawa cikin zazzaqar muryar ta me dad'in sauraro,har saif ya sami kansa da tsayuwa yana ta sauraren ta,har se da ta kammala karantawa zata rufe qur'ani kawai ta ganshi yazo gabanta tare da rage tsawon shi suka rufe qur'anin tare snn ya kar6i qur'anin ya ajiye a hnkli gefe kan dardumar da take zaune akai.
 Wani irin fad'uwar gaba ta samu kanta da shi idanun ta qasa taqi yarda su had'a ido wacce ko kad'an bata so ya kama ta dumu dumu haka ba.
  Saif dake kallonta ya d'ago fuskar ta ga mamakin sa hawaye ya gani cike tap a idonta har suna tserar sauka akan kumatun ta.
  Ya riga yasan dalilin kukan muryar sa a natse yace"ki cire tsoro a ranki zan barki bazan sake takuraki ba amma se idan zaki min abu d'aya"
  Da saurin ta ta kalle shi muryar ta a sanyaye tace"koma mene ne zan maka fad'i ina jinka"
  Se da ya d'an d'au lokaci snn yace"Ina son gobe naje dake gurin Abba ki nuna masa cewa da yardar ki nake son zan auri Sophie idan kika min haka har na sami auren ta ni kuma na miki alqawarin zan sake ki kije ki auri duk wanda kike son ki aura.
  Har ranta taji wani irin dad'i ta share hawayen fuskar ta tare da fad'in"shikenan gobe da yaushe zamu je dan tafiya zanyi bana so inyi dare"
  Kumatun ta ya kama a hankli yana me qara share mata hawaye yace"kar ki damu akan lokaci zamu tafi har ki samu kiyi tafiyar ki in time"
 Ya qarashe mgnr ne cikin sakar mata murmushi.
  Nan ita ma ta tsinci kanta da sakar mishi murmushi snn ta bisa da kallo har ya tashi ya fita daga d'akin.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Sunday 04/03/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 29*
Saif da ya fita har ya kai qofar d'akin shi ze mird'a handle,se yayi tsaye yana dawo da hoton fuskar zarah a lokacinda ta sakar mishi murmushi,se duk yaji yana son sake ganin murmushin nata har dei yanda dimples d'inta suka lotsa yafi matuqar birge shi.
  Nan kawai ya fasa shiga d'akin nashi ya juya zuwa d'akin ta,da shigar shi ya samu ta miqe tsaye daga kan darduma a tsorace cikin fasa ihu ta nufo shi se nuna mishi spider take da ya fito under bed tana fad'in"ka ganshi ko gashi nn har yau be fita daga d'akin nn ba dan Allah ka fitar min dashi kar ya ta6a ni ina jin tsoro.
  Kallonta kawai saif ya tsaya yana yi,yanayin jin tsoron ta ma abun sha'awa da son kayi ta kallo,shi se yanzu ma ya fara fahimtar son ta da jamil keyi,lallai kuwa idan ya sake ta ze yi qoqarin ganin cewa jamil d'in ne ya aure ta ba wani ba.
  Ihun da ta saki ne  tare da fita aguje daga d'akin ya farkar dashi shagaltar da yayi yana kallon ta,ya tafi da sauri kan dressing mirror ya d'auko insect killer ya fesa mishi take ya mutu,yasa faka da sweeper ya fitar mata dashi.
 Zarah dake tsaye bakin qofa ta mishi godiya snn ta koma daga ciki,ta d'auke qur'ani takai shi inda ya dace snn ta linke darduma tasa a wardrobe had'e da hijabin sallar ta da ta cire shima ta linke.
 Nan se ga saif ya dawo d'akin wanda kae tsaye corner of bathroom ya tafi ya ajiye faka n sweeper a mazaunin su.
  Da har zai fita daga d'akin se kuma ya tsaya yana tambayar ta ko zainab tazo ta duba ki?
  Zarah tace"eh tazo ta min allura ta kuma bani wasu magunguna nasha"
  Yace"muga magungunan,ba musu ta d'auko mishi ta kawo mishi byn ya duba magungunan ya kalle ta yace"baki gaya mata qirjin ki na maki ciwo bane?
  Shan toka tayi kafin take sadda kanta qasa snn ta girgiza masa kai alamar a'a.
 Saif da ke kallon ta be ce mata komai ba se miqa mata magungunan yayi ya fita daga d'akin.
  Ta maida magungunan knn ta soma jin doorbell nn ta fita ta sauka zuwa downstair ta bud'e qofa,se ganin Nusaiba tayi riqe da er wata doguwar silver food flask a hannun ta 5pieces amma ba wani tsayi ne da ita ba sbd cute pieces of bowls d'in qananu ne basu da girma sosai.
  Zarah ta d'an yi far da idanun ta d'auke da murmushi na alamar kece.
Nusaiba tace"eh surprise,nazo duba ki ne ya jikin naki?
  Alhmdlh naji sauqi zarah ta fad'a had'e da kar6ar food flask d'in da ke hannu Nusaiba suka shiga daga ciki,Zarah na mai tambayar ta yusra fa jiya da kuka zo ban ganta ba yauma gashi kin zo min ba ita.
  Nusaiba da har sun qarasa cikin d'aki ta zauna kan sofa tare da yaye gyalen ta ta ajiye snn tace"yusra ae satin nn kaf a gidan hajiya tayi shi daga sunan zuwa weekend fa tace ita bata tashi dawowa ba,shine umma ta tattara mata tufafin ta har ma da uniform d'inta ta aika mata se idan za'a kaini school a biya a d'auke ta mu tafi.
  D'auke da murmushi zarah tace"ina ma nn tazo na samu me tayani zama da safe se muyi shirin mu,mu fita tare a sauke kowa a school d'in su.
 Cabd'i ae school d'in su da taku ba kusa ba kwata kwata ma basu had'a hanya ba.
  To ae duk a cikin gari d'aya ne,kawai dai zamu shirya kan lokaci ta yanda za'a kai kowa akan lokaci.
  Hmm duk da haka dai zaman ta a gidan nn bazai yiyu ba dan naga yaya saif ya fara tsunduma a sonki,se ma kinji wani dad'i da naji a raina a lokacinda ya fito dake manne a jikin sa yana wani nan nan dake,da gani ya damu sosai akan rashin lafiyar.
  Zarah dake kallon ta ta ta6e baki snn d'auke da murmushi tace"hm Nusaiba knn nida yama alqawarin gobe idan munje.....
  Se tayi shiru taqi qarasa zancen dan se taga kmr ba mgnr da ya kamata ta snr da Nusaiba bace.
  Nusaiba tace"alqawarin me ya miki gobe,ko tare zaku je rimin dako?
  A'a ae ko me za'a bashi nasan bazai je wnn qauyen ba bare ni bana ma son yaje...me kika kawo min a kula?
 Zarah ta fad'a cikin basar da waccan mgnr.
  Nusaiba da har taso tayi wata magana se kuma tace"Bud'e kiga umma ce ta bayar a kawo miki.
  Zarah dake zaune kusa da Nusaiba a hankali ta shiga 6alle bowls d'in d'aya bayan d'aya tana duba abubuwan da ke ciki.
   Abincin marmari ne irin wanda masu ciki keso.
 Bowl d'in farko da ta bud'e alala ce yayinda na biyu ta sami sauce d'in qoda wanda zata had'a taci da alalar,na uku kuma d'an wake ne with cucumber salad da dafaffen qwai a gefe,and the 4th one mai da yaji ne a ciki na had'in d'an wanken,then d last one danbun shinkafa wanda yayi kyau har ya gaji se qamshi ke tashi.
  Murmushi zarah tayi me d'auke da nuna jin dad'i snn tace"wlh kmr inna tasan banyi abinci ba gashi yunwa nakeji na kasa zuwa na girka.
  Nusaiba tace"lallai ma so kike ki kashe mana baby"
  Cikin jin zancen wani iri zarah tace wane babyn.
  Ta6e baki Nusaiba tayi tare da mata wani kallon up & down kafin take cewa"hmm kinji ki 6ter ae ko zaki 6oyewa kowa banda ni,bare tunda naga umma na miki wnn had'e had'en kalolin abincin nasan cewa ciki ne da ke.
 Dam kawai zarah taji gaban ta ya fad'i wacce da saurinta ta kai ma Nusaiba duka cikin dalla mata harara tace"Allah sauwaqe ni wlh banda komai"
 Dariya Nusaiba tayi tace"karki maida ni qaramar yarinya mana ko kin manta jiya da yaya saif ya fito dake a gabana Abba ke tambayar sa kina yin amai sosai ne yace a'a zafin jiki kawai ne da zarar kuma kinsha magani kinyi bacci shikenan komai ze dawo miki normal,ko kuma duk dai ba zancen me ciki akeyi ba a gurin.
  Ta qarashe mgnr ne tare da tsare ta da ido.
  Zarah tayi murmushi had'e da girgiza kanta tace"Au Allah sarki baxa ki gane ba ne,kuma ae in cikin ne ba abu ne me 6oyuwa ba bayyana zai yi,bare ma ina roqon Allah kada ya kawo qaddarar da zai sa na sami ciki da yayanki,wnn...hum um!Allah raba 'ya'yana da uba irin shi.
  Daga haka ta sauko ta zauna kan rug tare da lanqwashe qafafu ta had'a d'an waken ta ta soma ci.
  Nusaiba da ke kallon ta tayi murmushi kawai,haka ma saif wanda yana can d'akin sa yana kallon su a laptop yayinda yake jin shima dai koda ace ya d'auki hukincin da yaso d'auka akan ta na kiran shi fanko da tayi,har akayi akasin ciki ya shiga,to lallai da kanshi ze mata allurar zubar da shi dan ya riga ya tsara a rayuwar shi babu wata uwar 'ya'yan shi face Sophie da tuni suka aje akan 'ya'ya biyu kacal zasu haifa.
   
Washe gari koda qarfe goma tayi tuni  sun shirya har sun fito,zarah na can tsaye gefe riqe da er traveling bag d'inta a hannu ta shirin tafiyar ta rimin dako.
 Sbd so take daga can gida idan sun gama magana da Abba umma tasa driver ya kaita kmr yanda ta mata alqawari.
  Saifuddeen kuma kitty ce a hannun shi tsaye a gurin mota yana qwalawa me gadi kira,mai gadin na zowa ya bashi yace"ba jimawa zanyi ba ka kula min da ita.
  "To a dawo lfy"
Mai gadi ya fad'a wanda yana rungume da kittyn ya tafi da sauri dmn bud'e musu gate,se a snn zarah ta yarda taje ta shiga mota dan dama ganin yana riqe da kitty ne yasa tayi tsaye can gefe tana jiran har se ya bada ita tukun.
  Wacce byn ta  shiga har ta rufe ganbu saif ya kalle ta yace"zan gaya miki abu d'aya shine bana son wawanci a harakar nn i mean kar ki gayawa kowa wai nace zan sake ki,kawai idan kin min yanda nace  zan cika maki alqawarin ki.
  Gyad'a masa kai kawai zarah tayi yayinda shi kuma yaja motar suka fita daga gidan.
   Da suka isa tare suka fito cikin motar suka shiga daga ciki,Nusaiba ce ta fara ganin su wacce ta dawo daga islamiyya knn zata haura sama tayi tsaye tana kallon yanayin shirin su tamkar wasu couples d'in da ke qaunar juna sunyi kyau sosai se zuba qamshi suke,ba abinda ma yafi bata shawa kmr klr kayan su iri d'aya.
 Zarah na sanye da atamfa super Holland navy blue da akayiwa zane me ratsin sky blue wato klr gyalen ta dake yafe tun daga smn kai,haka ma takalmin qafar ta klr ne,amma hand bag d'inta klr navy blue ce.
  Yayinda shi yake sanye da tsadadden yadin shi sky blue hadda hula qubbe klr kayan a saman kanshi kmr wani na Allah kan yanda kayan suka kar6e shi sun fiddo mishi da kamala sosai,dan ba kasaifai yake saka hula ba ra'ayin sata ne kawai ya biyo mishi yau,wanda dashi har zarah ganin kawai sukayi sunyi to match d'in ba wanda yasan klr da d'ayan ze sa.
 D'auke da murmushi Nusaiba ta gaida su had'e da kar6ar travelling bag d'in da ke riqe a d'ayan hannun zarah nn se ga Abba da umma suna saukowa daga staircase,Abba ne zeyi tafiya zuwa kd shine umma ta rakoshi.
 Wa enda sun qarasa saukowa ne cikin fad'ad'a murmushin da ke kan fuskar su,suna masu amsa gaisuwar su zarah.
  Abba da har ransa yaji dad'in yanda ya gansu haka abun sha'awa yace da zarah"ya jiki zarah kinji sauqi?
  Zarah kanta qasa cike da ladabi ta gyad'a masa kai alamar taji sauqi.
  Yace"to Allah ya qara baki lafiya ni zan tafi kaduna ne yanzu,idan kinje Rimin dako ina gaida inna sosai dama mutanen gida gabakida'aya kinji"
  Sake gyad'a masa kai zarah tayi zata basu hanya dmn su wuce dan kan hanya suke tsaye,a kafaice saif ya riqo hannun ta da sauri had'e da kai d'ayan hannun sa ya d'an sosa bayan kansa irin na jin kunya d'in nn yace"plz Abba muna son zamuyi magana da kai ne"
  Abba ya kalle sa da kulawa kafin yake gyara babbar rigar sa yace to muje inji.
  Nan umma da Nucy suka haura sama,yayinda Abba ya qarasa daga cikin falon ya zauna kan doguwar kujera 3seater su kuma su saif suka zauna kan rug suka sadda kansu qasa.
  A natse Abba yake kallon su yace"ina jinku mene ne?
  Saif yace"Abba dama...se kuma yayi shiru yana d'an sosa bayan kansa.
  Abba wanda ya d'an shiga tunanin ko zai gaya masa cewa zarah na d'auke da ciki ne,yayi murmushi yace"kayi maganar ka mana saifuddeen ina jinka kar kaji komai.
 Saif ya kalli zarah snn ya kalli Abba yayi qasa da kansa yace"dama Abba mgnr aure na ne da Sophie,tace ita a gurin ta ba matsala ta amince kuma Sophie d'in ma ta amince zata musulunta indai har ka yarda zan aure ta.
  Abba dake kallon saif d'auke da murmushi,yana jin zancen sa lokaci d'aya fuskar sa ta canza cikin 6acin rai
yace
"Ga d'an rainin hankali kan wnn banzar maganar ne kasani a gaba wai zaka gaya min sbd ka maida ni sha sha sha wanda ban isa in gaya ma magana ka bi ba,har ni zan rantse kan har abada kar ka sake kula wnn baturiyar ashe har yanzu baka ajiye zancen ta ba ko!.
A sanyaye saif yace Abba kayi haquri ka taimaka min dan Allah.....ka min shiru very stupid! wlh ko bayan raina ban yarda ka auri wnn baturiyar ba koda ace zata musulunta kuwa ni bana ra'ayin ka aure ta har abada ba kai ba ita,dan haka kar ka sake zo min da zancen ta idan har baso kake na maka abunda baka ta6a tsamani ba,sha sha sha kawai fitsararre get out! in daina ganin ka a nn!.
  Ba musu saif ya tashi ya fita d'auke da idanuwan sa da duk sukayi jajur suka ciko tap da qwallah
  Nan ita ma zarah kafin Abba yace da ita komai ta tashi sum sum ta miqe ta haura sama da sauri sbd kukan da taji yazo mata.
  Umma dake tsaye ta bita da kallo kawai,wacce saukowar ta knn daga sama kan jin fad'an Abba wanda kana ta nufi gurin shi ta zauna a natse ta soma magana dashi.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Tuesday 05/03/2017_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 30*
Kan yayi haquri ya bar saifuddeen ya auri Sophie.
  Abba da duk ransa a 6ace yace"plz Mmn yusra kar ki qara 6ata min rai,akan me zan barshi ya aure ta,baturiya ce fa fitsararriya mara kunya wacce bayan tana samun sa a office be ishe ta ba har nn gida ta fara biyoshi tana qoqarin lalata min yaro a banza.
  Shiru umma tayi snn tace"Amma Alhj tunda har ta yarda zata musulunta plz ka bar shi d'in ya aure ta ko dan musuluntar da zata yi.
 Hm maman yusra na fahimci dan ba ke kika haife sa ba shiyasa kika kasa hango abunda nake hangowa ko.
  Cikin mamaki da rashin jin dad'in mgnr sa umma tace"haba Alhj wace irin magana ce kake gaya min haka"
  Kiyi haquri maman yusura ba wai ina nufin in 6ata miki bane ya kamata ki natsu kiyi tunani idan na barshi yayi auren wace irin tarbiyar kike ganin yaran su zasu d'auko,ko kin manta gado a cikin jini yake duk abunda uwar su tayi shi zasu zo sunayi ko ma fiye,ba lallai bane su kasance masu kirki.
  Amma Alhj musulunta fa tace zatayi ko dan haka inshaa Allah,Allah bazai bar yaran su d'auko wata banzar dabi'a ba....a'a maman yusra ni na tabbata hauka kawai yakeyi iyayen ta baza su ta6a yarda su barta ta musulunta ba,dan haka ya isa dan Allah bana son sake jin wata magana.
  Daga haka be jira me umma zata ce ba ya fita.
   Umma da ta bisa da kallo tayi shiru har ranta ita kanta ba son auren take ba,da dai wata ce a cikin Hausa fulani ba baturiya ba amma saif d'in ne ya bata tausayi,cikin baya son zarah aka tursasa mishi auren amma gashi yanzu ya saduda suna zaune abin su qalau be ta6a kawo wani qorafi ba,ko dan hakan taso Abba ya tausayawa mishi wnn karon a bashi dama shima.
   Tashi tayi ta leqa ta window ga mamakin ta ta hango motar saif ajiye be tafi ba wacce tunanin da tayi knn dan bata ji tashin motar sa ba fitar Abba kawai taji.
  Nan ta fita taje ta same shi a cikin mota ya had'e kansa da sitari se kuka yake kmr wani qaramin yaro,cikin rarrashi ta d'ago fuskar shi tare da share mishi hawaye snn ta kama hannun sa suka koma daga ciki sukayi zaune a nn falo kan doguwar kujera tana kallonsa cikin yanayin damuwa tace"saif kayi haquri kaji kasan halin mahaifin ka idan ya fad'i magana baya canzawa,kuma tunda har kaga auren nn yaqi yiyuwa tayu ba alheri bace a gare ka.
 Saif dake jin wani qololon baqin ciki a ranshi ya girgiza kansa yace"No umma ki daina fad'ar haka musulunta fa tace zatayi a kaina,ta yaya baza ta zama alheri a gare ni ba,kawai dai Abba ne bazai barni na aure ta ba.
 umma na rasa meyasa kwata kwata Abba baya son farin ciki na....haba saifuddeen ka daina fad'ar irin wnn magana haka ae duk duniya babu me son ganin farin cikin ka irin shi....No umma zan de fi yarda duk duniya shine baya son farin ciki na,akan kawai yayi farin ciki fa nake nuna muku muna zaune qalau nida wnn abar bayan kuwa ko kad'an ba haka bane sam bata cikin tsarin rayuwata ina yin haka ne kawai dmn a tunani na farin cikin ganin nayi mishi biyaya muna zaune qalau nida ita zesa ya barni na auri Sophie amma se gashi a banza umma.
  Umma da taji wani abu a ranta tayi shiru tana kallon shi snn tace"me kake son gaya min saifuddeen,kana nufin kaida zarah babu wata kulawa a tsakanin ku kana nuna mana ne kawai?
  Of course umma ni bana son wnn abar dmn duk ita ce silar lalata min komai,abinda yafi sauqi ma a gare ta idan taje wnn qauyen kar ta dawo bana son sake ganin ta a gidana.
 Umma dake kallon sa komai bata ce dashi ba tana kallo har ya tashi ya fita,a ranta tana tunanin knn ko cikin da suke zargin zarah na d'auke da shi kusan hasashen banza ne suke dmn yanayin maganar sa kad'ai ya nuna mata da kmr babu wata alaqa da ta ta6a shiga a tsakin su,ashe rnr ba fushin masu ciki ne ya d'ebo zarah tazo tana fad'in ita ta gaji da auren ba zancen gaskiya dai tazo tana gaya mata.
  Nan ta numfasa a hankli zata tashi se ganin saif tayi ya dawo ya zauna yana kallon ta yace"plz umma bana son Abba yasan gaskiyar zaman da mukeyi nida ita,na fison naci gaba da bin sa a haka har Allah yasa wata rana ko zai janye rantsuwar da yayi ya barni na auri Sophie.
   Umma tace"saif bana tunanin Abbanka zai ta6a janye rantsuwar da yayi haka kuma zarah idan taje wnn qauyen ba dawowa zata yi ba ta tafi knn kmr yanda ka buqata.
  Yanayin fuskar sa kmr wani qaramin yaro yace"No umma na canza shawara ne,akan samun auren Sophie wlh zan iya jure komai,ki barta kawai ta dawo na d'ora inda na tsaya ko Allah zai sa nayi nasara.
 Aa dawowar zarah baza ta amfane ka da komai ba dmn babu nasara a cikin yaudarar Abban ka da kake son yi kawai kaje ka sake wani tunanin.
  Daga haka ta tashi ta barshi nn gurin ya bita da kallo cike da damuwa a ranshi.
  A 6angaren Zarah kuwa a lokacin da ta haura sama kae tsaye d'akin su Nusaiba taje ta zauna kan bed tare da had'iye kukan da take ji wanda ita kanta bata san dalilin zuwan kukan ba kawai dai tasan bata ji dad'in da Abba yayi fad'a ba,dmn da tasan mgnr 6atawa Abba rai zatayi da baza ta biyewa saif ba sai dai ta bar tsarin ta akan idan taje rimin dako baza ta dawo ba wanda ko yanzu kuwa hakan ne kad'ai mafitar ta.
 Nusaiba da itama duk fad'an da Abba keyi ya iso kunnen ta tazo tayi zaune kusa da zarah cike da mamaki tace"lallai 6ter me yake damunki da har kika yarda yaya yaje dake gurin Abba kan neman alfarmar auren wnn baturiyar,ko ba kya son sa ae ya kamata kiyi kishin sa a matsayin sa na mijinki.
  Shiru kawai zara tayi tana kallon ta taqi tace da ita komai har umma tazo ta same su.
 Zarah na ganin shigowar ta ta sadda kanta qasa tace"inna dan Allah ayi haquri shi ne yace na raka shi bansan maganar zata 6ata ran Baffa haka ba.
  Umma tace"ba komai maganar ta wuce,and u Nusaiba idan har zaki je d'in to kiyi ki shirya dmn  Alu driver na zowa bazai tsaya jiranki ba sai dai suyi tafiyar su shida zarah.
A'a umma Allah yanzun nn zan shirya.
  Nusaiba ta fad'a wacce tayi saurin bud'e wardrobe ta ciro kayan da zata sa snn ta kalli umma cikin marairai ce fuska tace"plz umma tunda rnr sunday 6ter zata dawo nima zan d'ebi kayana mu kwana a can se mu dawo tare.
 Umma tace"A'a bazai yiyu kiyi missing d'in islamiyyar yamma ba snn kuma gobe tazo baki samu zuwa ba kwata kwata.
 Ba tare da Nusaiba ta musa ba ko nuna rashin jin dad'in ta ta tafiyar ta kawai zuwa bathroom dmn ta d'an watsa ruwa duk da tayi wanka da safe da zata je islamiya.
 Umma kuma zama tayi a hankli kusa da zarah tana kallon ta kawai ta kasa ce mata komai bata san meyasa ba haka kawai se tausayin ta take ji.
   Inna lafiya?
  Zarah ta tambaya wacce ke kallon umma a natse.
  Umma ta sauke numfashi a hankali tare da fad'in"ba komai kawai dai idan zaku tafi da akwai turarukkan fesawa da turarukkan d'aki na tsintsiya da kuma tokunan wanka da nake son baki kije dasu a matsayin en tasarabar ki da kika kai musu.
Byn haka zaku biya gurin hajiya ku d'auki yusra dan nasan tana buqatar zuwa itama d'azun ma na kira hajiya na snr da ita.
 Snn da akwai shawarar da nake d'an yi a raina idan na yanke shawarar to wata qil gobe zanje rimin dako d'in wata qil kuma bazan je ba sai dai na tura Alu driver ya d'auko ki.
  Gyad'a mata kai zarah tayi wacce bata ko san umma taje d'in duk da bata san dalilin son zuwan nata ba,amma gwanda ta tura mata Alu driver kawai dan shi tana iya liqewa tace baza ta dawo ba tunda yanzu bata san makomar akqawarin da saif ya mata ba,ga rayuwar gidan nashi ta ishe ta gabad'aya,gwanda kawai tayi zamanta a mahaifar ta inda ake ganin mutuncin ta,daga nn idan ta samu yanda take so yayan ta ya sake nema mata wata makaranta taci gaba da karatun ta koda kuwa school d'inda yake karatu ne zata iya kasancewa a garin dan so take tayi ilimi sosai ta waye dmn ta samu damar cika burin ta akan saif so take ko yaya se tasa yayi nadamar tsanar ta da yayi.
  Koda Alu driver yazo har Nusaiba ta kammala shirin ta tsaf,umma ta bawa zarah abubuwan da tace snn ta rakasu har mota tana musu Allah kiyaye hanya.
 Da fitar su gidan basu zarce koina ba se gidan Hjy suka d'auko yusra snn suka kama hanyar rimin dako.
 Cikin mota tsif ba mai cewa komai tsakanin Nusaiba da Zarah kowa da abunda ke zuciyar shi musamman Nusaiba da ta rasa gane kan yayanta da zarah,ita da take ganin kmr sun fara qaunar juna se gashi sun wani je sun sami Abba kan neman alfarmar auren wata banzar baturiyar can har zarah d'in ta yarda suka je wai,sosai abun ya bata haushi da har yanzu yayanta ya kasa fita hararkar wnn baturiyar bayan umma da Abba duk ba me son alaqar sa da ita.
  A hankali ta sauke numfashi tare da kallon zarah cike da niyyar mata magana se taga karatun qur'ani take a wayar ta hakan yasa tayi shiru bata ce mata komai ba,se bud'o qur'anin tayi ita ma a wayar ta ta soma karantawa har suka isa rimin dako.
  Dije suka samu a tsakar gida tazo aguje cike da murna ta tarbe su tare da kar6ar kayan da ke hannun su suka shiga ciki yayinda inna washe da baki ta shiga musu sannu da zuwa.
  Basu sami yayan zarah ba baya nn ya koma school amma kawun ta yana nn wanda da kanshi yazo har d'akin inna shida innan dije suka musu ya hanya ya kuma suka baro su umma.
 Suka ce suna nn qalau sun ma ce a gaida ku.
  Kawun zarah yace"to muna amsawa ya kika baro mijin naki?
  Ya tambayi zarah a cikin harshen fulatanci wacce sai da ta sadda kanta qasa snn ita ma a cikin harshen fulatanci tace mishi yana nn qalau.
   Nan bayan sun gama gaisawa snn suka bar d'akin.
  Dije ta kawo musu abinci da kuma lafiyayar hurar da aka dama musu an saka qanqara tayi sanyi sosai,suka ci suka sha se fira suke tayi a tsakanin su su duka har inna wacce duk ta kalli zarah wani irin farin ciki take ji sosai a ranta ganin yanda zarah take ta qara kyau da ko ba'a fad'a ba tana cikin qoshin lfy.
  Se yamma snn su Nusaiba suka tafi ita da yusra.
 Rnr lahadi saif yayi ta bud'an idon ganin zarah ta dawo amma shiru har ya kwanta bacci bata ba alamar ta gashi a gaban shi umma ta tura Alu driver yaje ya d'auko ta amma har washe gari shiru.
 Bayan ya shirya zai tafi asibiti ya biya gida a tunanin sa ko ta dawo dare yayi shine bata sami komawa gidan nashi ba dan da shigar shi gidan ya sami motar da aka tura Alu driver yaje ya d'auko ta da ita.
  Amma da ya shiga ciki babu alamar zarah d'in ta dawo dan bayan yaje d'akin umma ya gaishe ta yana fitowa ya tafi d'akin su Nusaiba be sami kowa ba su Nusaiba basa nn sun tafi school ya bud'e har bathroom wai ko zarah na ciki amma be ganta a ciki ba,jiki sa6ule ya bar gidan ba tare da ya iya tambayar umma ina zarah d'in take ba.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Wednesday 07/03/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 31*
Tun yana ganin abun wasa wasa har aka share kusan sati bata dawo ba,duk ya shiga damuwar rashin dawowar ta da shi kan sa bai san dalilin hakan ba.
 Wanda tunda umma tace mishi babu nasara akan yaudarar Abba da yake son ci gaba dayi se duk yaji bazai sake yin hakan ba,zai dai yi wani tunanin akai kmr yanda umma tace mishi,shiyasa yake mamakin to meyasa duk ya damu da rashin dawowar zarah da kullum se ya duba laptop yana kallon previous video d'in ta da be zauna ya gani ba.
  Wani abun se ta bashi sha'awa wani abun kuma haushin kansa da tausayin ta yake ji dmn kmr kar yaga lokacinda ya bar mata kitty irin wahalar da tasha da qoqarin ganin cewa ta kula da ita,amma yana dawowa jin ta 6ata da kuma 6acin ran ganin tasha kashin ruwan sama be bar ya tsaya wani bincike ba kawai ya yanke mata hukunci,hukuncin da duk yaji ashe be kyauta ba,da ya duba abubuwan da suka faru a wnn lokacin da bazai yanke mata wnn hukuncin ba amma 6acin rai be bar yayi tunanin dubawa ba ma.
 A hankali ya sauke numfashi tare da rufe laptop d'in da ke gaban shi wanda yanzu gabad'aya ya gama duba previous video d'in ta ba wani next abunda ze gani kuma.
 Ya na rufe laptop d'in ya kwanta a natse tare da lumshe idanun sa,duk yabi ya rame kan damuwar da ke ranshi na tunanin mafitar samun auren Sophie da ya shiga yi kuma,wacce kullum cikin karanta saqonin da ta turo mishi a wayar jamil yake har kullum tana cikin damuwa da tambayar ya ake ciki dmn a tunanin ta amincewar da tayi zata musulunta shikenan ta kawadda duk wata matsala,take Abba ze amince ya bar su suyi aure se gashi taji shiru har kiran jamil take tayi a waya amma kullum abu d'aya ne,haquri kawai yake bata kan ta kwantar da hanklin ta,ta kasa samun ainihin abunda take son ji.
  Gashi sosai take gudun sake causing d'in wata matsalar,daa saifuddeen zata kira taji komai daga bakin shi amma sanin irin kashe din da Abba ya mishi kmr yanda jamil ya mata bayani can farko yasa take tsoron ta kira shi,wacce ko texts d'in da take turowa a wayar jamil iya kan saif ya karanta yace duk abunda jamil ya bata replay is ok,dan sosai yake gudun furcin da Abba ya mishi kan duk ya sake kula ta be yafe mishi ba,shiyasa wani lokacin har numbar ta ze zauna yayi ta kallo yana jin kmr ya kira ta amma tuna wnn furcin kesa dole ya fasa.
  Kana ya tashi ya sauka daga kan bed yana yawo a cikin d'akin wanda yanzu abunda yafi damun shi a gaba shine rashin dawowar zarah wacce rashin ta a gidan se yaji wani iri ba dad'i kmr dama can wani shiri sukeyi.
  A ranshi yana tunanin dole ne yanzu yaje gida yayi magana da umma baya jin zai iya ta zuba ido haka kawai duk da dai ya kasa fahimtar abunda yasa duk ya damu da rashin dawowar ta amma yafi yarda cewa tausayin ta ne ya fara kamashi snn yana son yaga cewa ta dawo taci gaba da zuwa school.
  Nan ba 6ata lokaci ya d'auki makullin motar sa ya tafi gida gun su umma.
  Da shigar sa falon ya sami umma da Abba zaune kan rug sun jingina bayan su da jikin kujera 3seater,fruit bowl ajiye a tsakiyar su an yanyanka fruit d'in sunyi sanyi se fira suke suna shan fruit d'in cike da nishid'i.
  Bayan ya gaida su yaje ya zauna a kusa da umma yana neman shigewa a jikin ta kmr wani qaramin yaro muryar sa a hankali yace"umma wai meyasa har yanzu yarinyar nn bata dawo ba bayan a gabana naga kin tura driver yaje ya d'auko ta.
  Kafin umma tace komai Abba yace"Au ikon Allah wai umman taka bata gaya maka yanda akayi ba,ae da Alu driver yaje se ya samu zarah bata jin dad'i baza ta iya dawowa ba a rnr shine ya dawo ba ita.
  Saif da yanayin damuwa ya d'an bayyana a fuskar shi yace"Amma Abba is gud ta dawo nn zata fi samun kulawa ina ne qauyen ni a gaya min inje"
 kar ka damu ae idan taji sauqi zata dawo inna na kula da ita sosai.
  Cewar umma wacce tasan zarah lafiyar ta qalau ba wani ciwo dake damunta,ta fad'i hakane kawai dan ta samu ta zauna kuma umma se bata matsa mata ba ta barta.
 Saif yace"No umma idan har qauyen yana wahalar ganewa ne plz a had'a ni da Alu driver se muje is gud ta dawo ko dan school d'in ta.
  Umma da ta d'auka yana yi ne dmn yaudarar Abba ta kalle sa kawai kafin Abba ke cewa shikenan ae Alu yana can tare da gateman suna fira se kaje ka mishi magana.
 Nan saif ya tashi ya fita se qwalawa Alu driver kira yake wanda yazo da saurin shi yace"gani yalla6ai"
 Kai tsaye saif ya jefa masa key d'in motar shi snn yace"oya muje ka kaini wnn qauyen inda ka kai wnn yarinyar amma mu fara zuwa gidan su jamil tukun dmn tare nake son zamu je dashi.
  Alu driver da ya fahimci zarah yake nufi yace"to"
Snn ya tafi da sauri ya budewa saif ganbun mota na baya,saif d'in ya shiga ya zauna yana me waya da jamil.
  Abba kuwa saif na fita ya kalli umma wacce tabi saif da kallo yace"kema kin lura da yanda yaron nn ya rame sosai ko?
 Ae dole ne ya rame Alhj sbd yana cikin damuwar auren Sophie da ka hana mishi.
  Abba ya kalle ta yace"ina fa ya isa yasa damuwa akan abunda yasan ba samun sa zai yi ba ae shi kansa yasan idan yasa damuwa akan hakan wahala kawai zai yi,ni nafi yarda cewa bai san sun shaqu da zarah sosai ba ne har se da tayi tafiyar nn yasan muhimmacin ta a kusa da shi gashi kina gani ma da kanshi yace ze je qauye ya d'auko ta wanda nn gaba se kinji ya daina zancen wnn baturiyar kwata kwata.
  "Uhm Allah taimaka"
Cewar umma wacce daga haka bata sake cewa komai ba se shan fruit d'in ta taci gaba dayi haka shima Abba.
Su saif kuwa koda suka isa rimin dako kawun zarah suka samu a nn qofar gida qarqashin bishiya gishingid'e kan tabarmar kaba yana shan iska riqe da radio a hannun sa ya kara a kunnen sa yana sauraro.
  Suka je cike da girgimawa suka gaida shi wanda se da ya kashe radio snn ya tashi zaune cikin sakin fuska yana amsa musu gaisuwar har yana tambayar su ya hanya ya kuma suka baro su Abba.
  Jamil ne ya iya bashi amsa saif kuwa se kallon yanayin gurin yake da ma qofar gidan yayi mishi kama kmr ya ta6a zowa amma bazai iya tuna yaushe ne ba.
  Wanda sam beyi mamakin nuna musu sani da kawun zarah yayi ba har yana tambayar su yasu Abba ya ajiye akan kawai Alu driver ya sani.
  Bai san cewa kawun zarah ya san shi ba tun yana yaro amma se bayan Abba ya auri umma ne take zowa dashi ko shi sau biyu kacal,dan saif d'in ne tun yana yaro tsanar qauye yake a cikin ranshi shiyasa duk umma zata zo se yace mata baya zuwa be sake yarda ya biyo ta ba se dai duk lokacin da zata zo ta kai shi gidan hajiya da haka ba a wani jima ba aka tura shi waje karatu shine fa tun lokacin be sake dawowa qauyen ba se yau,wanda ko kawun zarah ba tun sanin yarin ta ne yasa ya gane shi ba,zuwa d'aurin auren da sukayi ne.
   Nan suna gama gaisawa ya tafi dasu cikin gida.
 Sun samu su zarah suma suna zaune a qarqashin bishiya innan dije ta sata a gaba tana mata kalaba,wacce duk ta kasa zama guri d'aya se motsi take tayi tana jin kmr ta fashe da kuka dan ko kad'an bata son kitso mugun ciwon sa take ji,ko yanzu dan an tursasa mata kan dole ne yasa ta zauna wacce tana jin dije ta ta6a mata kai ta juyo da sauri ta kai mata duka.
  Dije ta fashe da wata irin dariya har tana duqawa,nn zarah ta miqe tsaye a fusace idon ta tap da qwalla tana kallon innan dije tace"mama wlh ki mata magana ta daina ta6a min kai"
  Innan dije tace" fad'ima ae ni nace ta kama min ayi a qarasa miki naga se ciwo kk ji duk kin gaji amma yi haquri zauna baza ta qara ta6a miki kai ba ni kad'ai zan qarasa miki.
 Kallon dije Zarah tayi wacce still bata daina mata dariya ba,ta dalla mata harara had'e da yin qwafa snn tasa ribbon ta dunqule kanta tace"ki barshi kawai mama nagode zan qarasa da kaina"
  Daga haka tasa takalmi zata bar gurin se kici6us tayi dasu saif wacce  sam bata san da zuwan nasu ba se ganin su kawai da tayi.
  Ae kuwa ta tsaya cak tana kallon saif da shima ita yake kallo,wanda sosai ramar sa ta bayyana da lokaci d'aya ta fahimci haka,amma ba tayi tunanin me ya kawo masa ramar ba dan tasan damuwar da yake ciki,kawai dai tayi mamakin me ya kawo su dmn sam bata kawo wae saif yazo ne dmn ya koma da ita ba duk da dai ta ganshi tare da jamil,wanda kansa qasa ya tsiri danne danne a wayar shi sbd baya iya kallon zarah dake sanye cikin kayan fulani riga da zani yayinda rigar a d'age take ana ganin lafaffen cikin ta a bayyane bata saka rigar da ake sawa a ciki ba sbd zafin da ake,da sam ta manta da yanayin dressing d'in nata sai da ta kama saif yana kalla mata ciki snn ta tuna,ta bar gurin da sauri ba tare da iya ce musu komai ba ta shigewar ta d'akin inna.
 Kawun ta dake tare da su a tunanin sa ko kunya ce irin tasu ta fulani yasa zarah ta kasa ce musu komai ta wuce,yayi murmushi tare da cewa"dije d'auko musu tabarma ki shimfid'a musu a nn qaraqashin bishiya baza su iya zama ciki ba zafi.
"To"
Dije tace wacce sai da ta gaida su snn taje ta d'auko sabuwar tabarma ta shimfid'a musu suka zauna snn ta kawo musu ruwa ta wuce yayinda ita ma innan dije tuni ta bar gurin bayan sun gama gaisawa da ita.
  Bayan wucewar ta ne inna ta fito tare da kawun zarah da yaje ya snr da ita tazo gasu saifuddeen mijin zarah,wacce washe da baki cikin fara'a sosai take musu maraba ya hanya suka ce"Alhmdlh mun same ku lafiya?
  Tace"lafiya qalau"
Yayinda lokaci d'aya saif na kallon ta ya fahimci ita ce wacce ya gani rnr sunje ita da wani har yace da gateman kar ya sake barin su su shigo mai gida.
  Wacce se yanzu yake ganin yanda sukayi kama sosai da zarah har ya shiga tunanin ko mahaifiyar zarah ce duk da dai ya ganta tsofuwa.
  Nan dai ya basar da zancen ya shiga snr dasu cewa sun zo zasu tafi da zarah ne da fatar taji sauqi.
  Inna tace"sosai kuwa taji sauqi bari naje na snr da ita ta shirya.
  Nan bata jira me zasu ce ba ta tashi ta tafi zuwa d'aki.
  Kawun zarah kuwa ya shiga qwalawa dije kira kan taje ta kaiwa driver ruwa shima yana a waje,nn ba 6ata lokaci dije ta fito taje ta kai mishi.
  Yayinda it kuma inna tana shiga d'aki ta snr da zarah abunda ke tafe da su saif.
 Zarah tayi shiru tana kallonta a ranta tana tunanin baza ta gaya musu cewa tazo dmn niyyar kashe auren ta ba ne,zata yarda d'in ta koma,ba mamaki komawar ta zata fi samun damar yin abunda take tunani akan saif.
 Nan kawai ta hau shirya kayan ta.
  Snn bayan ta gama ta cire kayan fulanin da ke jikin ta ta shirya cikin atamfa.
  Da zasu tafi dije ta riqa mata kayan ta ta raka ta har mota su inna da suma duk sun fito rakiya se Allah kiyaye hanya suke musu had'e da musu godiya akan alherin da su saif suka musu.
 Alu driver da jamil sune a gaban mota zarah da saif su ne a baya.
 Yayinda zarah tunda Alu driver ya tashi mota bayan tayi addu'a ta bud'o qur'ani a wayar ta ta soma karantawa a hankali cikin ranta,saif se kallon ta yake amma ita koda kuskure taqi yarda ta kalli ko gefen da yake,har suka isa garin kano kuwa bata yarda ta kalle shi ba se karatun qur'anin ta take tayi.
Da shigar su garin kano kae tsaye Jamil aka fara saukewa a gidan su,snn aka sauke su a gida.
 Saif ya kar6i makullin motar shi had'e da ciro 5k ya bawa Alu driver ya kar6a yayi godiya ya tafi snn su kuma suka shiga daga ciki.
Zarah ta wuce d'akin ta shima haka wanda da shigar shi ya d'auro arwala ya fito ya tafi zuwa masallaci dmn yin sllr magrib da ake tayin kiraye kiraye.
 Wanda bashi ya dawo gidan ba se 8:30,kai tsaye ya wuce d'akin zarah ga mamakin sa ya samu har tayi bacci,jiki sa6ule ya kalli takeaway d'in da ya siyo mata,ya qarasa gun bedside drawer ya ajiye takeaway d'in snn ya zauna a hankali kan bed tare da d'aura idon sa akan kalabar kanta da tayi kyau sosai wacce suna dawowa bayan tayi sllr magarib tayi zaune ta qarasa abunta dan kad'an yayi sauri.
  Mamakin ganin an qarasa kalabar ne yasa saif ya d'aura hannu sa a hankli yana duba kalabar se ganin yayi ta bud'e idanunta tana kallon shi.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Thursday 08/03/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 32*
Ya kauda fuskar sa tare da janye hannun sa a kan ta a hankali snn ya d'auko ledar takeaway da ya ajiye kan bedside drawer yace"tashi ga abinci kici"
  Kallon sa kawai zarah tayi bata ce masa komai ba se blanket taja ta tafi dashi zuwa qirjinta ta rufe dan rigar baccin da ke jikinta santsi ne da ita sosai tsaf ake ganin yanayin qirjinta.
  Saif kuwa ganin ba alamar tashi zata yi ta kar6a ba ya maida ya ajiye ya tashi ya fita daga d'akin,nan Zarah ta gyara kwanciyar ta dmn ci gaba da baccinta se kuma ta tuna abinci ba abun wulaqantawa bane gwanda ta saka shi a fridge in yaso da safe tayi warming ta bawa mai gadi dan dai bata da buqatar shi ita kam.
 Nan ta sauka daga kan gadon ta d'auki takeaway d'in taje tasa a fridge ta dawo ta kwanta.
  Saif dake d'akin shi yana kallon ta a laptop ya tsinci kanshi da rashin jin dad'in qin cin abincin da tayi,gashi ita kad'ai ya siyo ma abinci shi bai ko yi tunanin ya siyo ma kanshi ba duk da irin yunwar da yake ji kuwa.
  Nan ya rufe laptop d'in yaje bathroom yayi wanka bayan ya fito yasha fresh milk snn yayi shirin bacci ya kwanta.
 Washe gari koda yaje d'akin ta da niyyar tashin ta tayi sallah ya samu har ta tashi amma be ganta ba ta shiga bathroom.
  Nan ya fita ya wuce zuwa masallaci.
 Zarah kuwa bayan ta ida sallah,ta d'auko hand bag d'in ta ta ciro wayar ta wacce tun lokacinda suka iso tasa ta a ciki shine se yanzu ta ciro ta ae kuwa ta sami missed calls d'in umma har da na nusaiba sbd wayar a silent take shiyasa bata ji lokacinda suke kiran nata ba ga missed calls d'in ma tun jiya suke,ba kati a wayar ta se flashing da ta musu.
 Ba 6ata lokaci se ga kiran su d'aya bayan d'aya wa enda ba wani abu bane so kawai suke suji ko sun iso lfy.
 Byn ta gama waya dasu ne ta tashi ta hau share sharen gidan dmn idan ba kan lokaci tayi aikin ba,zata yi lattin zuwa school shiyasa take yin aikinta da wuri.
  Kmr kullum idan ta shirya ta fita ta kan samu driver har yazo yana jiran ta amma akasin yau da taga wayam bashi ba alamar shi,wacce kafin tayi komai se ganin saif tayi ya fito riqe da makullin motar shi yazo ya kama hannunta se kallon sa kawai take har ya tafi da ita gun mota ya bud'e mata gidan gaba byn ta shiga ya rufe mata ganbun snn ya zagaya 6angaren driver ya shiga yaja motar bai zarce koina ba se school d'in su ya sauke ta snn ya dawo to 10 ya shirya ya wuce aikin shi.
 Zarah kuwa bayan sun gama lectures taje ta siya kati ta kira driver dmn yazo ya maida ta gida.
  Amma a maimakon taga drivern,saif kuma ta gani yazo d'aukar ta.
 Komai bata ce ba dai ta shiga ya maida ta gida,yana sauke ta ya juya ya koma asibiti.
  Sai da ya d'an jima kafin yake dawowa rungume da kitty a hannun shi,kae tsaye ya nufi kitchen.
 Be qarasa shiga ba ya tsaya yana kallon zarah dake dafa indomie tana sanye da riga t-shirt mai guntun hannu da wandon jeans,wacce yanayin yanda wando ya kama ta se ya fiddo mata buttocks n hips d'in ta cike da sha'awa.
 Dan saif na sauke idanun sa a gurin take yaji wani abu ya tsirka mishi,a kasale ya lumshe idanun sa snn ya bar gurin da sauri sbd kitty da ke qoqarin sauka ta nufi gun zarah dan sosai take son indomie ko qamshin ta taji yanzun ne zata nufin gurin wanda ke cinta ta ajiye mishi kuka har se ya bata,amma bata yin hakan se idan tana jin yunwa dan tunda suka fita da safe sau d'aya taci abinci daga lokacin ta hau bacci se kan hanyar su ta dawowa snn ta tashi,shine yaso ya d'auko mata kifi ya bata taci,se ya sami zarah a kitchen wacce har ya bar gurin bata ma san yazo ba kawai dai taji qamshin turaren shi da ta duba kuma se bata ganshi ba kawai taci gaba da aikin ta.
  Tana kammala dafa indomien ta zuba a plate taje falo tayi zaune kan rug ta lanqwashe qafafu ta soma ci,can tayi tsaki ta kalli Tv,shikenan ya maida ita awa kurma ko me zata kira abun ma oho,ba Tv ba abokin fira gata nn dai se duk taji kad'aici a a ranta,d'an zuwan nn da tayi rimin dako se taji sat tamkar wacce aka sako daga kurkuku,komai tana yin shi cikin jin dad'i babu takurawa,koda yake rnr farko da aka kawo ta abunda ya fad'a mata knn,fursun tazo ba gidan aure ba haka ne kam amma da yarda Allah lokaci zai zo da zata fita daga wnn kurkukun fita ta ta har abada kuwa.
  Duk tana yin zancen ne a ranta,snn ta tashi ta d'auko ruwa a fridge ta dawo ta zauna taci gaba da cin indomie,tana idarwa ta tafi kitchen ta wanke plate had'e da fork spoon d'in da taci dashi dama pot d'in da ta dafa indomie duk ta wanke bata bar komai da datti ba kmr ko yaushe.
  Duk saif na kallon ta a laptop bcos yana shiga d'aki yaji yana son qara ganin ta,kitty dake lafe kan jikin shi a hankli ta soma mishi kukan yunwa amma be ajiye laptop d'in ba yaci gaba da kallo har se da zara ta tafi d'aki,wacce da shigar ta ta soma cire buttons d'in rigar ta zata cire rigar sbd indomien da taci duk zafi ya taso mata,tayi tsaki tana kallon smn d'akin wai ace ba fanka duk koina na gidan abun ma mamaki yake bata,gashi bata iya kunna Ac ma6allar ta mata nisa,remote d'in kawai take cimma kuma tasan idan ba kunna ma6allar aka yi ba aikin banza ne.
  Nan ta koma wani tsaki had'e da cire rigar ta....oh my God"
 Saif ya fad'a a hankli tare da saurin rufe laptop sbd ba bra a jikin zarah koda ta cire riga,dmn mammanta tsaf mamman fulani ne dake girke ajiye guri d'aya irin wa enda basa fad'uwa d'in nn da ko ba'a sa bra ba aka saka riga sam ba'a ganewa se idan nipples ne suka turo snn ake fahimta.
  Tunda saif ya furta"oh my God"
yana nn dafe da laptop idanuwan sa a rufe yana fidda numfashi a kasale kyace abunda yaji kmr be ta6a ganin qirjinta nata ba.
  Da saurin sa kuma ya bud'e laptop d'in ko zai sake gani,amma ya samu har ta d'auko white vest ta saka a jikin ta snn ta hau bedside drawer se tsalle take tana son kunna ma6allr Ac.
  Gabad'aya sei ya ganta kmr Sophien shi dan duk yawan dressing d'in ta jeans ne se vest take sawa.
  Zarah dake can d'aki tana faman tsalle tsalle na ganin ta kunna ma6allar
Ac,garin tsalle tsallen ta kawai taji qafar ta ta zame"
  "Wayyo!"
Ta fad'a da qarfi wacce a maimakon taji kanta qasa se jin kanta tayi cak kan hannayen saif ya tallabe ta kmr wata jinjira,da saurin ta ta sauka se kuma tayi saurin rirriqe shi ganin kitty ta shigo d'akin dan da ya shigo be rufe qofar ba a bud'e ya barta.
  A hankli saif ya runtse idanun shi kan abunda yaji na rirriqe shin da tayi a haukace yake jin sha'awar ta na neman taso mishi.
  Ya kalli kitty tare da korar ta ta fita daga d'akin snn ya samu ya janye ta a hankali daga jikin shi ya kunna mata Ac tare da nuna mata yanda zatayi amfani da remote snn ya fita daga d'akin.
  Ya samu kitty a qofar d'akin shi se kuka take tana kallon qofar d'akin zarah kmr me kiran shi ya fito,wacce tana ganin ya fito ta tafi aguje ya d'auke ta ya tafi da ita kitchen ya d'auko kifin gwangwani ya 6alle yasa mata a plate d'inta ta soma ci snn ya koma falo ya zauna tare da jinginar da bayan shi a jikin kujerar da ya zauna,ya lumshe ido cike da sha'awar zarah dake tsikarar shi.
 Wanda da qyar ya samu ya miqe ya tafi d'aki ya d'auro arwala ya tafi zuwa masallaci dmn sllr magrib da ake ta yin kiraye kiraye.


Sorry 4 dis one.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Saturday 10/03/2018_ *«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 33*
Washe gari bayan zarah ta dawo daga school har ma tayi wanka ta shirya taje kitchen zata dafa indomie,ta shiga store dmn ta d'auko c-pot kawai taga store d'in an siyo duk abubuwan da suka qare,su arish doya plantain duk gasu nn har indomie duk an kawo.
 Ta d'an yi mamaki take kuma se ta basar ta d'auko abunda zata d'auka ta fito,bayan ta d'aura pot d'in ta zuba ruwa ta bud'e freezer dmn ta d'auko tarugu ae sei ta riqe waist ta saki ido tana kallon firizar cike tap da su naman kaji,naman rago,naman sa,en ciki dama dai sauran abubuwa duk cike a ciki,dan har ma su tarugu tattasai fresh tumatur duk an zuba kowanne da nashi muhalli.
  D'auke da mamaki ta d'auki tarugu guda biyu ta rufe firizar zata koma store ta d'auko albasa,bata shiga ba ta tsaya a nn kitchen d'in tana kallon qwai da kayan tea duk an kawo kowanne ajiye a inda ake ajiyewa,ikon Allah"ta fad'a kafin take wucewa store d'in ta d'auko albasa wacce ta samu ita d'in ma an qaro akan wacce ta bari.
 Ta6e baki tayi a ranta tana tunanin ko dai an amince masa ne akan auren wnn baturiyar shine ya siyo komai kafin tazo dan ita kam dai tunda tazo gidan sau d'aya da ta samu irin kaya haka ba'a sake siyowa ba sai dai duk abunda ya qare a cikin kud'in ta take bawa maigadi ya siyo mata,qwandala saif be ta6a bata ba,ko kud'in kati,kud'in handouts dama er qwalamar da take ci a school duk kud'in sadakin ta ne dubu hamsin da aka bata sune take amfani dasu.
  Haka dai ta dafa indomie tana tunanin abun a ranta,bayan ta gama dafawa har taje falo ta zauna tana ci,ta kira Nusaiba a waya wacce tana d'aga wayar tace"hi 6ter ya kk?
 Lafiya qalau dama zan tambaye ki ne halan Baffa ya amincewa yayanki ya auri wnn baturiyar ne?
 Guntun tsaki Nusaiba tayi had'e da fad'in"6ter idan ba so kk mu 6ata ba dan Allah ki daina min zancen wnn baturiyar haushi nake ji wlh"
  Uhm zarah tayi murmushi mai sauti snn tace"sauyin abubuwa fa na gani a gidan nn wanda ya tabbatar min da kmr hakan shiyasa kika ji na tambaye ki ba wai dan in 6ata miki rai ba"
  Sauyin abubuwa?
Nusaiba ta tambaya snn tace"kmr name knn?
  Zarah tace"shiga kitchen nayi zan dafa indomie se na sami store duk an siyo kayan da babu haka ma da na bud'e freezer na ganta cike tap da naman kaji,naman rago,en ciki dama dai sauran su duka duk a cike,bayan kuwa tun zuwa na gidan da na samu irin haka sau d'aya wanda nasan duk aikin inna ne tasa aka min kuma shikenan daga lokacin duk abunda ya qare sai dai in sa kud'i na in siya koda kuskure bai ta6a kawo wani abu ko yace ga kud'i a siya ba,se yau naga ya kawo...af kin bar ni ina hauka wata qil ma bashi yayi ba su inna ne ko?
 Nusaiba wacce tayi shiru kan jin tausayin zarah,kana tayi dariya tare da fad'in"wae me kika maida yayana ne ni kam"
  Zarah da ita ma ta shiga yin dariya tace"ae gaskiya nake fad'a abunda be ta6a yi ba,kan me zanyi tunanin shine to,in dai har ba hasashen da nake yi bane....ta qarashe mgnr ne tare da kallon gefen da ta jiyo qamshin turaren saif taga kuwa shi d'in ne ya fito sanye da farar jallabiyar sa ze je masallaci wanda ya kalle ta kawai ya fita.
 Nan tace wa Nusaiba"Abunda kawai na fahimci yayanki yana yi na kirki shine ko kad'an baya son jam'i ya wuce shi da zarar an soma kiraye kirayen sallah take zaki ganshi ya fita zuwa masallaci,yanzu ma kirayen kirayen sllr nn da aka soma yi gashi nn har ya fita.
  Nusaiba tace"wlh kuwa haka yake abunda ke birge ni dashi knn son addini"
 Zarah tace"Allah sarki amma kuma se yake yin wasu halayen gasu nn dai...kinga ni yau ma duk na shiririce se yanzu nake cin abinci bari nayi sauri na qarasa kin san magarib tsuntsuwa ce zan koma kiran ki idan na idar da sallah.
  "Ok to"
Cewar Nusaiba kafin suke tsinke wayar.
Bayan isha'i ta fito daga wanka d'aure da towel a qirjinta,taje ta zauna gun dressing mirror ta shafa mai ta kuma feshe jikin ta da turare snn ta tashi ta nufi gun wardrobe zata ciro kayan bacci,kafin ta bud'e wardrobe d'in idon ta ya sauka a kan envelope dake ajiye kan bedside drawer wacce tun d'azun da ta dawo daga school tana shigowa d'akin ta ganta amma kuma nn take se hankalin ta ya d'auke bata duba ko mene ne a ciki ba kawai taje zuwa aikin gaban ta.
 Fasa bud'e wardrobe d'in tayi taje ta bud'e envelope d'in tana dubawa,kud'i ne a ciki rafar en dubu dubu sabi dal 100k
  "Kud'in dannan qirji"
 ta fad'a a ranta snn a fili tayi d'an guntun murmushi tare da d'auko wayar ta ta kira Nusaiba,Nusaiba na d'aga wayar tace"wane sherin ne kuma zakiyiwa yayan nawa "
  Zarah tayi dariya tare da fad'in"ba sharri se fad'an gaskiya wlh ina ga dai Abba ya amince masa kan auren wnn baturiyar kece dai baki sani ba gashi har kud'in dannan qirji ya ajiye min,sosai cikin dariya zarah ta qarshe mgnr wacce kafin Nusaiba tace komai se ganin tayi an kar6e wayar,ta kalli wanda ya kar6i wayar da sauri taga saif ne.
 Take dariyar da ke kan fuskarta ta 6ace,saif da ya kar6e wayar ya tsinke kiran yakai wayar kan bedside drawer ya ajiye.
 Snn yazo kan bed ya zauna a kusa da ita tare da d'aukar ta cak ya d'aura ta kan qafafuwan sa,da saurin ta zata sauka ya d'aga d'ayar girar sa cikin nuna mata kitty dake bakin qofar d'akin,ae kuwa a maimakon ta sauka se ma rirriqe shi da tayi.
Yayinda shi kuma ya kafe idanun sa akanta se kallonta yake d'auke da idanuwan sa masu cike da sha'awar ta da yake fama da ita tun jiya.
 Meye haka wai?dan Allah ka tashi ku fitar mun daga d'aki.
 Zarah ta fad'a cikin muryar ta dake rawar tsoro.
  Saif dake riqe da waist d'in ta yana fmn kallonta har baya son qyaftawa muryar sa a hankli yace"ki gaya min tukun me kika maida ni da bazan yi abun alheri a gidan nn ba sai dan zan auro Sophie"
Cikin shan toka zarah tace"ae kam dama,kuma ni kasan ba abunda zanyi da wani kud'in dannan qirji meye had'i na dasu ma,alqawari na kawai nake son ka cika min.
   Yanda take mgnr se abun ya bashi dariya yayi d'an guntun murmushi
tare da mirginadda ita ya kwantar da ita hankli kan bed had'e da mata rumfa ya shiga yawo da d'an yatsan sa a kan fuskar ta har zuwa lips d'inta yana shafawa.
 Snn idanuwan sa a lumshe se yawo yake da hancin sa a jikinta yana shinshinar qamshin jikinta musamman wuyanta da tsakiyar qirjinta da duk yafi jin qamshi a gurin se wani jan numfashi yake a hankli yana qoqarin zame mata towel.
  Zarah kuwa se qoqarin ture shi take tana fad'in"wai meye haka ka daina bana so".
 Ya tsaya ya kalle ta yace"kina son na kira kitty tazo kan gadon nn ne?
 Zarah da kmr har ta manta da kitty na qofar d'akin a tsorace ta girgiza kanta tace"dan Allah a'a kuma ka daina bana son abunda kake min"
  Yace"ni inaso kuma idan kk sake yunqurin hana ni kitty zan sa ta miki yaga yaga akan wa en nn kyawawan abubuwan da kk kuri dasu"
  Ya fad'a yana me shafar boobs d'in ta da suke a bayyane,sbd towel d'in ta da ya samu ya zame ya cillar gefe.
   Wanda a natse ya kai bakin sa akai yana mata wani irin salo mai wuyar fassarawa,ae kuwa take zarah taji abu ya tsirka mata,can ciki taja numfashi tare da saurin rufe idanunta dmn lokaci d'aya taji wata irin kasala ta saukar mata amma hakan be hana ta shiga ture kanshi tana fad'in ya daina bata so.
  Sam saifuddeen bae sauraren ta ba se abubuwa yake ta mata da harshen shi yana bin koina na jikinta.
 Zarah kam jin yakai inda bata iya barin shi ta samu ta ture shi da qarfi,ta tashi zaune tare da saurin had'e qirjinta da cinyoyinta dan ba halin taja blanket ta rufe jikinta saif na akai wanda gadan gadan ya nufu ta,zata sauka kan gadon ya fizgo ta ya rungume ta sosai,jikin sa na wani irin 6ari muryar sa na d'ad'd'aukewa yace"kar ki tafi dan Allah ki tsaya ki taimake ni zan iya mutuwa"
  A rud'e zarah ta rufe idanun ta sbd ciro joystick d'in sa da yayi,jikinta na rawa ta shiga tura shi cikin girgiza masa kai tana fad'in"ni bazan iya ba ka rabu dani"
 Cike da son ta taimaka mishi yace"No ba wnn abun da kike tunani bane,kmr yanda en mata na ke min zaki min,kin ta6a gani ai ko.
 Ya fad'a kamar wani qaramin yaro.
  Ba shiri Zarah ta gwalo ido fuskar ta kmr zatayi amai tace"me!Allah sauwaqe wlh bazan iya wnn qazantar ba kaje ka neme su suda zasu iya"
  Kmn zai yi kuka yace"nifa mijinki ne ki taimaka min,tuni na daina haraka da wa en nn en mata"
  "Naqi!"
Ta fad'a tana faman tura shi.
  Ya riqe ta yana kallon ta ransa a 6ace yace"kimin ko kuma wlh na miki wnn abun da ba kya so"
 Bata saurare shi ba se qwace kanta ta shiga qoqarin yi,tana fad'in"ka rabu dani bazan iya ba nace,nn kawai taji shi gadan gadan yana qoqarin shigar ta,ta samu da qyar ta miqa hannun ta kan bedside drawer ta d'auko flower vase ta buga mishi aka har se da qwalbar ta fashe.
  Take saif ya saki qara tare da dafe kanshi.
 Se kuma ta saki ido a tsorace jikinta na rawa tana kallon yanda jini ya fara fita da sauri.
  Ya d'ago ya kalle ta ya fizgo ta da qarfin tsiya ta d'auka ma shaqe ta zai yi amma se jin tayi ya had'e bakin sa da nata yana tsutsar lips d'in ta a haukace kmr ze raba ta dasu.
 Can ya zare bakin sa yana kallon ta se fidda numfashi yake snn da sauri ya riqe joystick d'in shi ya sauka kan gadon yana tangad'i ya fita daga d'akin yana jin idan ba wnn abun aka mishi ba ya samu ya fidda...,hm bazai ta6a samun sa'ida ba.
 Kan dole ya kira d'aya daga cikin en matan shi a waya,ba 6ata lokaci kuwa se gata tazo ta mishi kaman yanda ya buqata yana samun kansa yanda yake so ya sallame ta ta var gidan,to fa se a snn ya iya yiwa kan sa dressing snn yaje yayi wanka.
  Zarah kuwa saif na fita d'akin idanun ta tap da qwallah ta shiga kallon jinin saif da ya diddiga a jikinta,da kan bed,har ma fitar da yayi duk jinin ya diddiga kan tiles d'in d'akin.
Sam bata ta6a aika aika irin wnn ba duk da lokacinda tana qarama fad'a ne da ita sosai amma bata ta6a yiwa kowa rauni ba,dan sam bata yarda tayi danbe,sai dai kawai ta balbali mutum da masifa wacce duk fad'an ta se idan an tsakalo ta ne ba haka kawai take yi ba.
 A hankli tasa hannu ta share qwallar da suka zubo mata snn ta tashi ta d'aura towel ta hau gyaran d'akin.
 Washe gari suna cikin mota saif ze kaita school wanda ko jiya shi ya kaita ya d'auko ta.
  Suna tafe seyi take tana satar kallon inda taji mashi ciwo duk da yasa plaster a gurin amma jim kad'an se ta koma kallon gurin but in seconds se ta kauda ido dan bata son ya ganta tana kallon shi,kmr kar ta janye idon ta a kanshi taji yace"wash"
 Tare da dafe gurin,ta kalle shi da sauri suna had'a ido ta kauda fuskar ta gefe kmr me jin kunyar had'a ido dashi.
  Saif wanda da sanin sa yayi hakan yayi d'an guntun murmushi tare da kai lallausan hannun sa ya juyo fuskar ta yace"kin fara sona ko?
  Ture mishi hannu zarah tayi tare da fad'in"Allah sauwaqe har abada wlh"
 Saif dake kallon ta ya sami kansa da rashin jin dad'in mgnr ta,har ma fuskar sa ta nuna cikin kasa dannewa  yace"kamar yanda nima kika san har abada bazan ta6a qaunar ki ba,shiyasa ma nake gab da cika maki alqawarin ki in huta da ganin ki a gidana.
 "Kodai ni na huta da muguntar ka ba"
  Ta fad'a tare da kauda fuskar ta gefe duk ranta a 6ace.
  Saif ya kalle ta wanda se a lokacin yaga ashe jiya ya ji mata ciwo a gefen lips d'inta gurin yayi kwancin jini na alamar cizo snn kuma ya d'an kumbura kad'an.
 Da kulawa yakai babban yatsan sa yana shafa gurin a hankali,zarah ta ture hannu nashi da sauri cikin dalla mishi harara.
  Yayi murmushi tare da maida hanklin sa kan tuqi,wanda har ya sauke ta school bata sake yarda ta kalli ko gefen shi ba,dan sosai taji haushin maganganun sa.

Da yamma liqis har magrib na qoqarin gabatowa,still zarah na school zaune cikin class,bata kira driver ba kuma bata da niyyar kiran shi dan har yanzu driver  take kira amma saif ke zowa,but ba wnn ne damuwar ta ba irin Assignments d'in da ke gaban ta,da ta kasa yin ko d'aya a cikin uku,bcos ba easy bane kuma bata nn koda aka bada Assignments d'in tana Rimin daako har gashi gobe da safe za'ayi submit,wanda basuyi ba suna nn a cikin class d'in suma seyi suke tayi amma ita ta kasa yi duk haushi ya cika ta tana kallon takardun da ke gaban ta kmr ta fashe da kuka.
  Qamshin turaren saif da taji ne yasa ta d'ago fuskar ta a hankli taga shi d'in ne,d'auke da mamaki take kallon shi wanda yasa hannu ya shiga tattara takardun da ke gabanta ya saka a jakar ta,nn se ga wani yazo gun zarah riqe da duka assignments d'in sa da yayi yace"wato qanwa ba kya nn koda akayi lecture akan topics d'in nn shiyasa abun ya maki wahala,gashi kuma lokaci ya qure bare na zauna na fahimtar dake,shiyasa nace bari kawai na kawo miki nawa Assignments d'in kije da su gida kiyi gobe da safe idan mun had'u se ki bani ko.
  Kafin zarah tace"komai saif ya masa wani mugun kallon da yasa guy d'in ya bar gurin sum sum,shi kuma ya kama hannun zarah ransa a 6ace suka fita daga class d'in.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Monday 12/03/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 34*
Zarah na biye dashi se kallon sa kawai da take har ya tafi da ita suka shiga mota,amma har suka iso gida in banda sharara gudu da yake faman yi da mota ba abunda yace da ita,kawai dai suna isowa gida kamar yanda yasa ta a mota ran sa a 6ace haka ya bud'e ganbun motar ransa a 6ace ya fizgo hannun ta ya fito da ita.
zarah ta shiga qoqarin qwace hannun ta tana fad'in"wai meye haka dan Allah ni ka sake ni!
  Be kula ta ba har sai da suka shigo falo dai dai ta samu ta fizge hannun ta,shi kuma a fusace ya had'a bayan ta da jikin qofar fallon ya manne har sai da qofar ta rufe da qarfi.
 Da sauri zarah ta qara kamewa a jikin qofar kan yanda ya doka hannayen sa da qarfi a jikin ganbu yasa ta a tsakiyar shi yana kallon ta cike da 6acin rai,snn with deep voice yace"gaya min waye wnn d'an iskan yaron da yazo ya same ki har inda kk zaune?.
  Wani iri taji abun banbarakwai tace"Ikon Allah kai kuwa meye ruwan ka dashi ka ji min"
   Ubanki ne ruwana dashi very stupid zaki gaya min waye shi ko se nayi gunduwa gunduwa dake a nn gurin"
   Ni ban san waye shi ba ta fad'a had'e da qoqarin ture shi dmn ta wuce"
   Ba shiri ta fasa ihu sbd qafar sa da yasa ya daki qafar ta da qarfi snn ya fizgo ta cikin riqo kafad'un ta yace"waye shi nace ki gaya min!
  Kuka zarah ta fashe dashi tare da fad'in"ni ban san shi ba kawai dai na san d'an course d'in mu ne"
  Shine to har ze kira ki qanwa wai kuma har yana fad'in da akwai lokaci da ya zauna ya miki bayani dan uban shi,to bari kiji in gaya miki wlh duk iskancin da zakiyi ki bari idan na kwance igiyar aure na akanki,ki tafi can kiyi tayi da duk uban da zakiyi amma bawai kina gidana ba.
 Wawiya kawai wacce bata san darajar aure ba.
  Yayi tsaki tare da ture ta gefe har se da ta fad'i zaune snn ya wuce fuuu!ya haura sama zuwa d'akin shi.
  Zarah kuwa bata tashi ba se kuka taci gaba dayi a gurin riqe da qafar ta se can byn tayi me isar ta snn ta tashi ta tafi d'aki.
 Guraren 11 saif ya fito sanye da kayan bacci ya nufi d'akin ta,wanda a tunanin sa zai samu tayi bacci amma se ya same ta zaune kan bed ta had'e qirjinta da cinyoyinta idanun ta cike tap da qwallah tana kallon takardun assignments d'in ta ajiye a gaban ta.
   Ya qarasa a hankli ya zauna ze d'auki takardun dmn ya duba,da saurin ta ta riga shi d'auke takardun tare da sauka kan gadon.
  Beyi yunqurin riqo ta ba se binta kawai yayi da kallo har ta fita daga d'akin,taje downstairs ta kwanta ruf da ciki kan doguwar kujera 3saeter ta saki kuka a hankali.
 Saif da ya fito yana kallon ta duk da ya fahimci kuka take be qarasa downstairs d'in ba yayi tafiyar shi zuwa d'aki.
 Har sai guraren 12:30 ya kwatanci cewa tayi bacci snn ya fito.
 Ya same ta still tana nn kwance ruf da ciki tayi bacci gashin kanta duk ya rufe mata fuska,a hankali ya gurfana kan guiwar shi yayinda ya jigina d'ayar guiwar a jikin kujera gab da ita yakai hannun sa ya yaye mata sumar kanta da ta rufe mata fuska wanda se a lokacin yake tuna cewa kalaba ce fa a kanta duka duka yaushe ne a kayi ta,just 2dayz har ta tsefe,ya d'an ta6e bakin sa cikin ko in kula dan shi sam baya ra'ayin kitso duk da kalabar da aka mata ta mishi kyau,amma dai yafi son ganin gashi yasha gyara yana sheqi qamshi na fita akan a kitse.
  Wanda a hankli ya shiga shafa sumar kan nata amma idon sa na kan eyelashes d'in ta dake d'auke da sanyin hawaye,bata jima da yin bacci ba knn dan har en guntayen hawaye ya gani a gefen idon ta har sun gifta kan karan hancin ta,ya tafi da babban yatsan sa sannu a hankli ya share mata hawayen,snn ya karkatar da kansa a hankli yana bin karan hancin nata da kallo da ya kasa d'auke yatsan sa akai,se ma tafiyan tsutsa ya shiga yi da yatsan nasa akan karan hancin nata ya tafi har zuwa lips d'in ta yana shafawa.
  Wata kasala ce ta saukar mishi kan yanda yake jin laushin lips d'in ta akan d'an yatsan shi wanda hakan yasa ya lumshe idanun sa a hankli kafin yake ware su akan cheeks d'inta ya tafi da yatsan sa a gurin yana shafa dai dai inda dimples d'in ta ke lotsawa idan tayi dariya,ba akanta ya fara ganin dimples ba amma sosai yafi ganin kyawon nata but Why?
  Ya tambayi kanshi.
Be iya ba kanshi amsa ba se dire idanun sa yayi akan rigar baccin da ke jikin ta,fara ce me santsi sosai yayinda hannun rigar ya kasance d'an siriri kamar na vest,snn tsayin ta zai kai zuwa rabin k'aurin ta,wacce tsaf ta fito mata da kyawon surar jikin ta,nn saif ya shagala se kallon surar jikin nata yake,shape d'in hips d'inta masu kyau kmr na Sophien shi,kawai dai tafi Sophie bumbum,dmn na Sophie basu da wani cikowa da zaka kalla kayi sha'awa kmr irin wad'anan da yake kallo har yana jin abu na fizgar shi da yasa ya kauda idanun sa da sauri.
 Snn a hankli ya matsa ya kama lallausar qafar ta yana duba saman qafar wato kan inda ya daka mata qafar shi d'azun,gurin yayi ja abinda yayi tunani knn dan yasan takalmin sa masifar ciwo ne dasu.
  Samun kansa yayi yana me murza mata gurin a hankali......
 Nan qarar wayar sa da ya ajiye kan rug ya katse shi,koda ya d'auki wayar ya duba jamil ne me kiran amma kafin ya d'aga se kiran ya tsinke da kmr network problem dan kiran be isa tsinkewa ba.
  Duba lokaci ya fara yi tukun"
 "qarfe d'aya"
Ya fad'a d'auke da mamaki kan fuskar sa yana kallon agogon bangon falon yaga shima haka ne.
Kallon zarah yayi yana mamakin wane shagala ne yayi a kanta har 30 mnt be sani ba shida yake ganin kmr ma just 2mnt yayi a gurin.
 Yayi kasaqe yana kallon ta,kana ya shiga dialling numbar jamil d'auke da tunanin meyasa jamil zai kira shi wnn lokaci.
  Amma se bai sami jamil d'in ba har kusan sau uku bata shiga,nn kawai ya haqura da kiran,ya zauna kan rug yana me lanqwashe qafafun sa sannu a hankli kan tsamin da sukayi,snn daga nn ya d'auki assignments d'in zarah ya hau yi mata.

Washe gari tun da asuba qarar wayar zarah ta tashe ta sbd alarm d'in da saif ya sa mata,ta tashi da qyar se miqa take wacce a tunanin ta ko kira ne dan sam bata fahimci ba ringing d'in da take amfani da shi bane sai da ta duba taga alarm ne snn hankalin ta ya bata,amma se ta shiga tunanin ita da bata ma ta6a sa alarm ba ya akayi yau kawai ya tashe ta....se kuma da sauri ta katse kanta da wnn tunanin,tana kallon inda take ta yaya itada ke falo ta dawo d'aki har gata a kan bed.
   "Na shiga uku"
Ta fad'a cikin jin tsoro idan ba gamo tayi da aljanu ba suka maido ta d'aki.
 Se kuma tayi shiru hankalin ta yana d'an dawo mata,tana tuna jiya fa kmr a mafarki taji saif ya maida ta d'aki wanda sam bata ta6a kawo cewa ba mafarki take yi ba se yanzu da ta ganta a d'aki.
Hm ikon Allah duniyan cin sa me yawa ne abunda take ganin ana yiwa indiyawa a TV a d'auke su cak kmr wata er tsana shine ya kawo kanta dan dai jiya kusan kmr haka ta gani a cikin baccinta.
 Nan bata gama mamakin abun ba ta hango Assignments d'in ta da ya mata ajiye kan bedside drawer,da saurin ta ta matsa ta d'auko tana dubawa taga kuwa duka ba wanda beyi mata ba.
 Nan tayi murmushi me nuna alamar jin dad'i,duk da jiya ya 6ata mata rai amma zata masa godiya dan dai ya mata abunda ta kasa yi,duk da cewa ba kad'an ba taso ace ita tayiwa kanta Assignments d'in akan fahimtar ta,wanda hakan yasa taqi tambayar abokanan ta su ara mata se questions kawai da ta amsa a hannun su.
A hankali ta sauke numfashi ta tashi riqe da Assignments d'in taje ta saka a cikin jakar ta da take zuwa school da ita,snn ta fad'a bathroom ta d'auro arwala tazo tayi sallah.
 Bayan ta idar ne tayi duk wani aiki da takeyi a gidan,tayi breakfast snn tayi wanka ta shirya ta fito,a niyyar ta ta jira fitowar saif dan duk ta fito haka kawai take ganin shima ya fito,amma akasin yau da ta samu har drivern da ke kaita school yazo yana jiran ta.
 Taje ta shiga mota tana mai kallon gurin da saif ke ajiye motar shi taga motar bata nn,wata qil kiran gaggawa aka masa asibiti.
 Abunda take tunani knn a ranta kafin driver ke jan mota suka bar gidan.
 Wacce har satin ya qare driver ke kaita ya d'auko ta,ga alama saif tafiya yayi dan bata qara ganin shi ba har kwana uku yau saturday,ita kad'ai ke rayuwar a gidan bata san inda yaje ba bata kuma nemi ta sani ba.
  Washe gari sunday da safe bayan ta gama share sharen gidan har ma tayi wanka tana kitchen ta jiyo knn riqe da tea a hannun ta zata fito se kawai taci karo da saif,taja baya da sauri gudun kar tean ya zuba a jikin shi,bata ankara ba se jin tayi tean ya zuba a hannun ta,ta saki qara tare da sake kofin snn taje aguje gun sink cikin yarfi da hannu zata bud'e famfo dmn ta sakarwa hannun nata ruwa,saif ya kama hannun da sauri yana dubawa.
   Rai 6ace ta qwace hannun nata zata fita,ya riqo ta yana fad'in"sorry is not intentionally bada sani na bane"
  Kallon shi kawai tayi still ranta a 6ace,ta ra6a ta gefen sa ta wuce,wacce ita bama tean da ya zuba a hannun ta ne yasa taji haushin sa ba,haka kawai taji ta sami kanta da jin haushin sa da ita kanta bata san dalili ba.
 D'aki taje ta kasa zama se yawo take tana faman hura hannun ta dan sosai tean keda zafi,har ma gurin yayi ja.
  Nan se ga saif ya shigo d'akin wanda kae tsaye ya kama hannun ta ya tafi da ita suka zauna kan bed snn ya kama hannun ta da tea ya zuba akai,da akwai d'an tube cream da ya shigo riqe dashi a hannun shi,ya matsa kad'an yana shafa mata a hankali.
 Wani sanyi taji a cream d'in da ya ratsa hannun ta taji abun har cikin zuciyar ta,wanda hakan yasa ta lumshe idanun ta a hankali,saif yayi quri da idanun sa yana kallon fuskar ta har ma zuwa dressing d'in ta ba kad'an ba gown d'in da ke jikinta ta mata kyau.
  Amma hankalin sa duk yafi karkata akan fuskar ta da ya sake maida duban sa akai,nn zarah ta ware idanunta a hankali sukayi 4 eyes,inda a natse saif yace"sorry lalura tasa nayi tafiya ban gaya miki ba,kakar jamil dake KD ce Allah yayi mata rasuwa shine naje se yau na samu dawowa.
  Zarah dake kallon sa take se ta soma jin haushin sa da take ji yana tafiya a hankali,ta sadda idanunta qasa muryar ta a sanyaye tace"Allah yaji qanta yasa ta huta"
  Yace"Amin,anjima da yamma se ki shirya mu tafi gidan su jamil ki masa gaisuwa.
  A hankli ta gyad'a masa kai alamar taji.
 Yayinda shi kuma ya tashi ya nufi fridge ya tsiyayo  mata fresh milk a cup ya kawo mata,wacce dama tunanin ta knn ta nemi fresh milk tasha dan bata jin zata iya koma had'a wani tea,shiyasa bata musa masa ba ta kar6a tare da masa godiya snn ta bisa da kallo har ya fita daga d'akin.
  Kana ta kauda fuskar ta tana tunanin meyasa Nusaiba da inna basu gaya mata rasuwar kakar yaya jamil ba,gashi kusan kullum se tayi waya dasu koda yake basa ma tunanin bata ji ba.
  Nan kawai ta kai cup a bakin ta,ta hau shan fresh milk d'in saif ya kawo mata.

Da yamma guraren qarfe biyar suka tafi gidan su jamil,suna gab da qarasawa qofar shiga falo ne,se ga baqar kyanwa ta fito aguje daga cikin flowers,cikin mugun tsorata zara taje zuwa fasa ihu saif yasa hannun sa ya rufe bakin ta da sauri,tare da kai d'ayan hannu sa kan waist d'inta ya matso da ita sosai zuwa jikin shi yana kallon yanda duk idanunta suka ciko tap da qwallah snn jikinta na wani irin rawa,saif dake kallonta ya janye hannun sa kan bakinta tare da rungume ta a hankali zuwa jikin shi dan ya fahimci ta tsorata sosai fiye da yanda yake ganin tana tsorata idan taga kitty.
  Wani irin abu jamil yaji kmr zuciyar sa zata faso qirjin sa ta fito wanda fitowar shi knn daga 6angaren shi ya gan su a haka.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Tuesday 13/03/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 35*
 Ji yayi kmr ya juya ko zai fi samun sa'ida amma hakan ya jure da qyar ya danne abunda yake ji ya qarasa gurin su cikin yin gyaran murya,hakan yasa zarah ta d'ago da sauri cikin share qwalla.
 Kafin take sadda kanta qasa muryar ta a sanyaye ta gaida shi.
  Fuskar sa ba yabo ba fallasa ya amsa gaisuwar yana kallon ta snn ya kalli saif yace"what's wrong naga kmr kuka zarah keyi,and yanayin ta kmr she is not okay.
  Saif ya kalli zarah kafin yake maida duban sa gun jamil yace"eh wlh ta tsorata ne sosai kan wata baqar kyanwa da ta fito aguje cikin flowers d'in nn ta  fita.
  Jamil da ya d'anji sauqin abunda yake ji a ranshi har yana sauke numfashi,yayi d'an guntun tsaki snn yace"kyanwar gate man ce wlh bansan a ina ya samo ta ba,but am sorry zarah kiyi haquri kinji"
 Bata iya ce masa komai ba se gyad'a masa kae da tayi.
 Snn suka shiga daga ciki,sun sami mtr mahaifin shi da kuma qanwar shi zainab a nn zaune falo,byn sun gaisa snn zarah ta musu gaisuwa,daga haka basu wani jima ba suka fito dan saif ya fahimci tsoron da zarah taji still be sake ta,ta jure ne kawai,dan da zasu fita gate suna kawowa ta gurin d'akin gateman,ta riqe hannun saif sosai dan ganin take kmr fitowa kyanwar zatayi,yayinda saif da kulawa ya qara riqe ta a jikin shi har sai da suka fita snn.
  Jamil da ya raka su se a lokacin ya fahimci knn zarah tsoron kyanwa take,ba fitowar ta aguje kad'ai ne ya firgitata ba.
  "Amma kuma shine saif ya bar kitty a gidan shi".
  Ya fad'a tare da juyawa yana kallon saif da ya tashi mota suka wuce.
  Yayinda a ranshi yake tunanin dole zai san abun yi kitty ta bar wnn gidan,dan ko wnn kyanwar ba barin ta zai yi ba yanzun nn zai yiwa gateman magana yayi gaba da ita baya son sake ganin ta a gidan.
  Nan ya koma daga cikin gidan ya kalli mai gadi dake zaune kan bench a kusa da d'akin shi yace"kana ji na Audu ka d'auke wnn kyanwar daga gidan nn dan Allah bana son sake ganin ta dmn tana firgita baqi masu shigowa.
  Audu ya zame qasa cike da ladabi yace" inshaa Allah yalla6ai yanzun nn ma kuwa"
Daga haka ya tashi da sauri ya shiga d'akin shi ya d'auko kyanwar zai fita da ita.
 Jamil da har ze wuce ya tsaya yace"kaga ba ina nufin ka jefar da ita ba dmn ba'a san halin da zata shiga ba,ka bincika maqota kaji idan da akwai me ra'ayin ajiye ta a gidan shi ba matsala bane se ka basu,amma dan Allah su kiyaye kar ta dawo gidan nn"
  "To yalla6ai"
Mai gadi ya fad'a snn ya fita riqe da kyanwar a hannun shi"
6angaren su saif kuwa driving yake amma se yi yake yana kallon zarah wacce jikinta a sanyaye har yanzu sbd sam bata ta6a ganin baqar kyanwa ba a rayuwar ta,da ta ganta se ta d'auko ma aljana ce shiyasa duk ta firgita da yawa,wacce duk da taji cewa kyanwa ce besa tsoran da taji ya tafi lokaci d'aya ba shine take jin jikinta duk a mace kmr wata mara lakka.
  Saif dake kallon ta a hankli ya kama hannun ta,zarah ta kalle shi,muryar sa a natse yace"sorry kin tsorata sosai ko"
  Fuskar ta kmr yanayin shagwa6a tace"Ae kam ni bazan sake zuwa wnn gidan ba ma"
  No ae indai jamil ne tunda yaga kina tsoron ta inshaa Allah daga yau ta bar gidan knn.
  Meyasa?
 Ya kalle ta kawai snn yace"halin shi ne kawai haka"
  Tayi kasaqe snn tace"Allah sarki wlh har ya birge ni da yasan darajar d'an adam ba kmr kai ba"
  Ta qarashe mgnr ne tare da zare hannun ta daga nashi snn ta kauda fuskar ta tana kallon gefen hanya.
  Wani irin abu saif yaji fuskar sa a d'aure ya kalle ta kawai bai ce mata komai ba se tuqin sa da ya ci gaba dayi.
  kae tsaye gidan su umma suka wuce se bayan isha'i snn yace ta fito su koma,koda ta fito ta same shi jingine jikin mota Apple fruit drink a hannun shi yana sha,ya kalle ta fuskar nn tasa ba annuri duk haushin ta yake ji a ranshi.
Wanda ba shiri ya saki gorar Apple drink d'in da yake sha sbd sarqe shi da yayi,se tari yake tayi,zarah tayi tsaye kawai tana kallon shi har sai da tarin ya tsaya mishi.
 Ya dalla mata harara tare da fad'in"tafi can er qauye kawai mutum na faman tari ko sannu baza ki mishi ba kin tsaya se faman kallona da kike"
  Ta6e baki tayi snn tace"da dai wanda yasan darajar mutane ne dana mishi sannu har in kawo mishi ruwa ma yasha.
  Tana qarashe zancen taje zata zagaya ta shiga mota,se jin tayi ya fizgo ta ransa a 6ace yace"wlh kika sake yabon wani a gabana se nayi gutsu gutsu da wnn bakin naki wawiya kawai wacce bata san darajar aure ba.
  Nan kawai zarah ta sami kanta da fashewa da dariya se kuma ta rufe bakin ta da sauri tana son mayadda dariyar.
  Duk 6acin ran saif take ya neme shi ya rasa ya sassauta damqar da ya mata ya tsaya kawai yana ta kallon yanda dimples d'inta ke lotsawa dan still ta kasa had'iye dariyar.
 Samun kansa yayi da d'aura en yatsun sa biyu ya lotsa dimples d'in d'auke da murmushi a fuskar shi yace"kin raina ni ko"
 Girgiza masa kai tayi tare da kai hannyen ta ta saqalo su a bayan wuyan shi tana kallon shi d'auke da murmurshi a fuskar ta snn tace"ka ajiye zancen raini ae gaskiya na fad'a,snn ka daina fad'ar cewa wai bansan darajar aure ba dan dai ban auri wanda nake so bane,amma idan na aure shi zaka d'auka ma kmr nafi kowa sanin darajar aure.
  Saif dake riqe da waist d'inta yayi murmushi tare da lakato hancinta yace"nima ki daina ce min bansan darajar d'an adam ba dan dai ban auri wacce nake so bane.
  Far tayi da idanun ta tare da fad'in" Allah sarki"
Wacce daga haka ta janye jikinta daga nashi ta zagaya ta shiga mota.
  Nan shima ya bud'e gambu ya shiga.
  Abba dake can saman balcony yana hango su,d'auke da murmushi ya bisu da kallo har saif yaja mota suka fita daga gidan,wanda har ranshi dad'i yake ji sosai dmn duk a tunanin sa ko kalaman soyayya ne suke fad'awa junan su.
Yayinda su kuma tunda suka fita daga gidan suka hau hanyar komawa gidan su kowannen su shiru basu sake cewa komai ba asali ma zarah se gefen hanya kawai take kallo,amma shi kam saif se yi yake yana kallon ta,can ya kama hannun ta,ta juyo a hankli ta kalle shi ya d'an yi murmushi snn yace"idan na cika maki alqawarin ki waye kike nufin ki aura da kike so?
  Murmushi zarah tayi snn tace"wanda nake so yafi ka komai,mutumen kirki ne wanda ke daraja d'an Adam komai qasqantar shi ba sai dan yana son shi ba"
   Hararar ta yayi tare da kai hannun sa ze buge mata baki,tayi saurin kaucewa tana mishi dariya.
   Ae fa se ya tsurawa dimples d'in ta ido,yana ji kmr ma kar ta daina yin dariyar,wanda sam ya ma manta cewa tuqi yake.


Sorry 4 this one.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Wednesday 14/03/2018_ *«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 36*
Innalillahi wa ina ilahai raj'un!
 Zarah ta fad'a da sauri ganin tsirif ya rage ya dagi wani mashin dake gaban su.
  A rud'e cikin sauri saif ya samu ya kaucewa mashin d'in.
  Zarah ta sauke gauron numfashi tare da fad'in"Allah mun gode ma"
 Cikin harshen fulatanci.
 Saif ya kalle ta kawai bai ce mata komai ba yaci gaba da tuqin shi.
  Har suka isa gida wa enda da shigar su kowanen su ya nufi d'akin shi.
  Yayinda zarah da shigar ta d'aki wanka kawai tayi tasa kayan bacci ta kwanta take tayi bacci abunta.
  Akasin saif wanda tuni shima yayi wanka yayi shirin bacci amma har 12 still awake beyi bacci ba gabad'aya ya rasa me ke damun sa game da zarah se tariyo dariyar da take ta mishi yau yake.
  Can ya miqe ya nufi d'akin ta yaje gab da ita kan bed ya zauna a hankli yana kallon fuskar ta ita kam se baccinta kawai take tayi tana sauke numfashi cike da natsuwa.
  A hankali ya d'aura hannun sa gefen fuskar ta yasa d'an yatsan sa babba yana shafa dai dai inda dimples d'inta ke lotsawa,yana tuna Sophien shi in tayi dariya bata da shi,kawai dai tafi zarah kyau amma be ta6a shagala yana kallon ta ba idan tana yin dariya,kmr yanda yake shagala da kallon zarah but why?
  Sbd dimples d'in ta suna matuqar yi mata kyau idan tayi dariya.
Ya tambayi kanshi,ya kuma bawa kanshi amsa,duk a cikin ranshi.
 Wanda a natse yakai bakin sa a gurin ze mata kiss se kuma ya fasa sbd motsin da tayi tare da gyara kwanciyar ta ta bashi baya.
 Nan ya miqe jikin sa a sanyaye dashi kansa be san meyasa yaji jikin nasa haka ba,ya d'auki remote ya qara mata qarfin sanyin split dan yaji sanyin bai wadatar ba.
 Ya ajiye remote ya koma 6angaren da ta juya yayi tsaye yana ta kallon ta har sai da yaji sanyin split d'in ya wadatar snn ya fita.

2dayz later.
Sauri sauri zarah ke saukowa daga staircase,sbd sosai tayi latti kuma bata son ta fita bata sa wani abu a cikin ta ba shine take sauri zata je kitchen ta nemi abunda zata ci.
 Saif dake zaune kan dining yana shan tea kmr wanda aka tsakura ya miqe zumbur da sauri tare da fad'in"ke ina zaki je haka?
 Zarah da har ta kusa kai qofar kitchen taji maganar sa daga sama dan bata ko lura da cewa yana falon ba ta tsaya tace"sauri nake zan sha tea bana son fita da yunwa"
 Saif yace"ba wnn na tambaye ki ba ina zaki je da wa en nn kayan dake jikinki.
  Zarah ta kalli jikinta,er riga ce baqa mara nauyi mai siririn hannu kmr vest,wacce style d'in wuyan rigar duk ya fito da rabin mammanta a fili snn rigar tayi d'as a jikinta,kmr yanda leggings wato wandon da ke jikinta ya mata d'as da tsayin sa iya rabin qauri.
Tace"Hauka nake da zan fita haka doguwar riga fa zan d'aura akai.
 Tana gama fad'a ta wuce kitchen ta bar shi tsaye.
  A kasale ya koma ya zauna cikin sauke numfashi a hankli sbd abunda yaji dan yanda ta fito sauri sauri haka mammanta ke taya ta suna shaking da sauri wanda shi kanshi haka kawai yaga ya miqe zumbur yana watsa mata tambaya.
  Zarah tana shiga kitchen sharp sharp ta had'o tea ta fito wacce har zata wuce sei kuma ta tsaya tana kallon saif da ya talla6e goshin sa ya tsurawa tean da ke gaban sa ido da alama ba a kan tean hankalin sa yake ba ma.
  Nan taje taja kujerar da ke fuskantar shi ta zauna ta ajiye tean ta snn ta karkatar da kanta tana leqen fuskar shi cikin qyasta masa yatsu dai dai saitin kunnen shi,ya d'ago a natse yana kallonta ta sakar mishi murmushi tare da fad'in"kana tunanin gwanar ka...se tayi shiru cikin tunani ta kasa kawo sunan Sophie, tace"am meye ma sunan ta ni mantawa nake"
  Saif dake kallonta yayi d'an guntun murmushi,ba tare da ya gaya mata sunan ba se kallonta kawai da yake.
  Kafin yake sauke idon sa akan d'an mintsilin kofin da ta had'o tea a ciki da bai wuce kur6i d'aya ba.
 Yana kallo ta d'auki kofin ta kai bakin ta,zama d'aya ta shanye tean ta ajiye kofin da bata jin sauri ze iya barinta taje ta wanke ta barshi nn ta tashi da hanzarin ta,ta bar masa qamshin turaren ta ta wuce.
  "Ya salam"
 Saif ya fad'a a hankli cikin tallabe goshin sa snn ya lumshe idanun sa ba abunda yake gani kmr rabin nonuwan ta da kuma bayanta da ta tashi zata wuce ba qaramin tafiya sukayi da imanin sa ba,sosai wandon ya kama ta yanda ya kamata ba qarya ya fiddo mata komai ta yanda dole duk lafiyayyen namiji ya kalle ta se yaji yar a jikin sa musamman yanda ta tashi da hanzari jikinta na karkad'awa ta wuce.
  Can bayan minti biyu cool qamshin turaren ta ya sashi d'agowa a hankali ya kalle ta,ya ganta har ta shirya cikin arabian gown baqa tayi rolling da d'an kwalin arabian gown d'in kmr yanda taga nusaiba nayi se ta fito mishi kmr wata balarabiya wacce ba kad'an ba tayi kyau.
   "Muje ko"
Zarah ta fad'a tana me kallon saif wanda lokaci d'aya yasha mata toka,a sanyaye tace"ko ba kai zaka kaini bane?
  Ni zan kai ki amma se kinje kin sauyo wasu kayan,ko an gaya miki zuwa makaranta fashion ake hadda wani saka turare.
  Zarah da ko kwalliya babu a fuskar ta ta kalli jikinta tana mamakin meye fashion a nn jallabiya ce fa doguwa har qasa se d'an kwalinta da ta lauya akai,turare kuma tunda tayi wanka ta shafa shi a jikinta shikenan bata sake sakawa ba,mtsw kae wnn mutum masifar shi yawa ne da ita,shikenan dan tunanin wnn baturiyar ya motsa mishi yanda yake jin takura an hana mishi auren ta haka yake qoqarin ganin ya takura mutum,ae kuwa baza ka sami wnn damar ba.
  Tayi mgnr ne a cikin ranta snn tasa qafa zata wuce,cikin daka tsawa yace"ke! baki ji me nace bane ko so kk sai na 6ata miki rai!
  Zarah ta juyo ta kalle shi yanayin fuskar ta cike da jin duk ya takura ta tace"to ae gani nayi duk abunda ka fad'a ba haka bane ba wani fashion da nayi,turare kuma fa tun d'azu yake a jikina ba sake sawa nayi ba"
  To kije kisan yanda zakiyi qamshin turaren ya fita ki kuma sauyo wasu kayan idan ba haka ba ba inda zaki je.
    Zarah da duk ranta ya gama 6aci cikin muryar kuka tace"to ni kam wae ina ruwanka da yanayin shiri na da ma komai nawa,shikenan dan kana cikin takura se kace zaka takura mutum ni gaskiya bazan iya yanda kace ba,sai dai kar inje d'in"
  Ta qarashe mgnr ne tare da jefar da makullin motar shi dake hannun ta wacce ita kanta bata san ya akayi ya manta shi a d'akin ta ba se ganin sa kawai da tayi ajiye kan bedside drawer shine da zata fito ta fito masa dashi.
  Wacce tana jefar da makullin ta wuce a fusace zuwa sama.
  Saif da ya bita da kallo ya sauke numfashi a hankali yana tunanin gaskiya fa ta fad'a, meye ruwan shi da ita da har ze damu da dressing d'inta da kuma qamshin da takeyi...mtsw yayi tsaki dan se yaji haushin kanshi ya tashi jikin sa a sanyaye ya d'auki makullin motar sa da ta jefar yana tuna jiya da dare ne ya manta shi a d'akin ta bayan ya dawo daga gidan hajiya,da dawowar shi yaje d'akin ta kae tsaye ya samu ma ta yi bacci,wanda bai san ma tsawon lokacinda ya d'auka yana kallonta haka kawai ba,haka kuma be san ma ya manta makullin ba se yanzu da ta jefar yake tuna cewa ya shiga d'akin ne riqe da makullin a hannun shi,amma da ya fito babu makullin se bai fahimta ba.
 A hankli ya koma sauke wani numfashi snn ya haura sama zuwa d'akin ta.
 Koda ya shiga ya same ta har ta fincikar da top veil ta yar snn da sauri cikin 6acin rai take 6alle buttons d'in arabian gown d'in dake jikin ta,dan sosai gown d'in keda kyau har de yanda aka dazo aninnan tun daga kan shoulder suka gifta tsakanin boobs suka tafi har zuwa gefen waist.
  Yayinda zarah kad'an ma ya rage ta qarasa 6alle aninnan.
  Saif dake kallonta ya qarasa cike da son ya rarrashe ta ya riqo ta,ta qwace da qarfi tare da fad'in"ni ka rabu dani"
  A natse ya sake riqo ta ya manna ta sosai a jikin sa ta yanda baza ta iya qwace kanta ba,yana kallonta muryar sa a natse yace"sorry am just kidding u,ina miki wasa ne but am sorry yi haquri kinji maida buttons d'in se mu tafi in kaiki"
  Ya qarashe mgnr ne tare da kama hannun ta ya tafi da ita kan bed suka zauna ya shiga rufe mata buttons d'in da kanshi,wanda a cikin ranshi se fmn had'iyar yawu yake sbd rabin nonuwan ta da ke bayyane yana fmn satar kallon su har ya samu da qyar ya qarshe rufe mata buttons d'in duk yayi zufa sbd masifar abunda yake ji.
  Ya sauke numfashi tare da ciro farin handkerchief ya shiga share zufar,yana mai mamakin duk irin sanyin split d'inda ke ratsa d'akin,shi gashi zufa yake hadda sharewa.
  Kana yabi zarah da ido se kallonta yake wacce bata ma lura da yanayin da yake ciki ba se gun dressing mirro ta nufa tana lauya d'ankwalin ta.
  Bayan ta idar ne ta d'auki jakar ta suka fita yaje ya sauke ta school ya dawo zuwa 10 snn ya tafi hospital,wanda ya fita ne kawai amma  ba dan yana jin zai iya yin wani abu ba dan abunda yake ji ba dainawa yayi ba.
 Hakan yayi ta fama har lokacin d'auko zarah yayi yaje ya d'auko ta,kmr yanda kullum idan sun gama lectures driver take kira ta gaya mishi,shi kuma drivern se ya kira saif ya gaya mishi kmr yanda saif d'in ya buqata.

Koda suka dawo gida qarfe shida tayi,zarah ko abinci bata iya ci ba sbd test d'inda aka ce za'a musu gobe,se cire arabian gown d'in jikinta kawai tayi ta ciro handout d'in da zasuyi test akai ta hau yin karatu se safa da marwa take a cikin d'akin ta tana faman cramming.
  Saif dake d'akin sa yana kallonta a laptop ji yake kamar tana kashe shi ne dan yanda take safa da marwa a d'akinta haka abubuwan ta ke masa safa da marwa a ido,gashi baya jin zai iya daina kallonta,amma ya zama dole ya mata wayo ta sauya wasu kayan masu rufa mata jiki ko zai samu sa'idar abunda yake ji.
  Nan ba 6ata lokaci ya tashi ya nufi d'akin ta wanda kai tsaye ya nufi gunta tare da tsaida ta ya kar6e handout d'in hannun ta,muryar sa cikin lallami kmr wata qaramar yarinya zeyiwa magana yace"karatun me kike yi haka da dawowar ki baki je kinyi wanka ba,baki kuma ci abinci ba.
  Yanayin fuskar ta kmr me son yin shagawa6a tace"wai test zamuyi gobe kuma course d'in yana da matuqar wahala wlh,duk cikin courses yafi bani wahala shine nake son in d'an karanta snn ko zanje inyi wanka inci abinci se naci gaba,dan gobe tun da safe muke da shi qarfe 8 ga malamin ance mugu ne sosai sai ka dage sosai kake cin course d'in shi.
  Saif dake ta kallon d'an bakin ta dake mishi bayani yace"duk da haka dai je kiyi wanka kici abinci zaki fi jin dad'in yin karatun dai dai brain d'in ki ta huta da lectures d'inda kukayi ko.
  Gyad'a masa kai tayi tare da kai hannu zata kar6i handouts d'in ta yace"No barshi a hannu na ina son zan duba na koya miki yanda zakiyi karatun a sauqaqe idan kin kammala se ki same ni a downstairs.
   "To"
Tace mishi kafin yake fita daga d'akin ita kuma ta cire kayan jikinta ta fad'a wanka.
  Bayan ta fito ta shirya,taji anyi sllr magarib tayi sallah snn ta fito.
  "Oh my God! wnn abar zata kashe ni"
 Saif ya fad'a wanda dawowar sa knn daga masallaci.
  Yayi arba da ita ta fito sanye cikin irin qananun kayan da ta cire sak komai iri da'ya da rigar da wando duk irin wa enda yaje ya mata yawo dan ta cire ya samu sa'ida,kawai dai wa en nn farare ne tas kuma kmr ma sun fi mata kyau dan shi kam haka ya gani,wanda da qyar ya iya d'auke idanun sa a kanta yaje ya zauna,ita ma taje ta zauna a gaban shi kan rug ta lanqwashe qafafu,ribbon a hannun ta,ta tattara gashin kanta dake baje kan gadon bayan ta ta d'aure.
  Saif da ke kallon ta a ranshi yana tambayar kanshi meyasa komai nata yake birge shi ne.....sha'awar ta ce dake damunka is gud ko ta qarfi ne ka same ta ko zaka sami sa'ida ka huta da abunda kake ji kafin ka illata.
  6angaren zuciyar sa ne ke gaya masa haka,yayinda yayi shiru yana nazari a ranshi,lallai kam idan beyi haka ba yana gab da illata dan abunda yake ji ba sauqi,amma kuma yafi so da yardar ta komai zai faru dmn ze fi samun gamsuwa yanda yake so but yasan sam baza ta bashi had'in kai ba sai dai idan wayo zai mata.....mu fara ko?
 Zarah ta katse shi.
Ya sauke numfashi a hankli snn ya sauko daga kan kujera ya zauna kan rug suna fuskntar juna,wanda idanun sa na sauka kan qirjinta yaji duk ya daburce joystick d'in shi na neman 6allo zip d'in shi ya fito,sam baya jin zai iya koya mata wani abu idan ba samunta yaga yayi ba.
 A hankli ya share zufar da ta tsatstsafo mishi kan goshi yana kallon ta yace"kinci abinci kuwa?
  Tace"um um banci ba da har na fito da niyyar dafa indomie se naga har ka dawo daga masallaci shine naga bari ka nuna min tukun tunda ba wata yunwa nake ji sosai ba se idan mun kammala se naje na dafa d'in.
  Saif dake kallonta cike da sha'awa idanun sa har sun soma janza launi yace"A'a bari na kawo miki fresh milk zaki fi fahimtar abunda zan nuna miki"
  Nan ya miqe ba tare da ya jira me zata ce ba ya haura sama zuwa d'akin shi jim kad'an se gashi ya dawo riqe da cup ya tsiyayo mata fresh milk a ciki.
  Ya zauna snn ya bata ta kar6a had'e da mishi godiya.
  Wacce tana gama shan fresh milk d'in ta soma jin kanta gata nn dai.
   Mene ko kina jin bacci ne?
 Cewar saif wanda ke kallon ta idanuwan ta se faman lumsashewa suke.
  Tace"A'a ba bacci nake ji ba wani abu nake ji da bansan mene ne ba,amma bari in sha ruwa.
  Ta qarshe mgnr tare da miqewa tsaye aifa se ta soma jin abu na fizgar ta ba sauqi kamar ta fad'i.
  Saif ya miqe tare da rungume ta,ta d'ago fuskar ta da niyyar janyewa daga jikin shi,se kawai taji hannun sa kan mamman ta yana shafa su a hankali.
  Nan kawai ta lumshe ido tare da jan numfashi ta rungume shi sosai ta lafe a qirjinsa,hannun ta kan buttons d'in rigar shi ta shiga cire mishi.
  Saif da ya fahimci desire tablet d'inda ya saka mata a fresh milk ya kama ta yanda yake so,ya kama hannun ta suka tafi d'akin shi.
  Wacce koda suka isa d'akin nashi har ta gama 6alle mishi buttons d'in riga,se cire mishi rigar kawai tayi snn ta koma kan rigar ta zata cire,jikin sa na 6ari ya kama mata suka cire rigar.


To ga wnn nasan zai kai muku har jibi ku huta da fad'in na jiya ya muku kad'an.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Friday 16/03/2018_
*«»»««»SAIFUDDEEN!«»»««»*






By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*

_This page is dedicated to u sister's»»masoyan zarah_
    _Heart u all❤_

*«»Page«» 37*
Kyawawan mammanta ta suka bayyana qyam yana kallon su,ae kuwa wani irin 6ari jikin nasa ya qara yi a rud'e cikin kid'ima ya shiga sarrafa su cikin wani irin salo mai wuyar fassarawa,zarah ta lumshe idanunta qirjinta na tasowa tana fidda wani numfashi kmr me jan yaji wacce take taji qafafunta basa d'aukar ta tana neman sulalewa qasa,saifuddeen ya kwashe ta suka hau kan bed,nan kawai ta kai hannayen ta bayan kanshi,ta kami bakin sa a haukace ta had'e da nata se kissing d'in sa take ba sauqi,duk tabi ta qara rikita shi se abubuwa take ta mishi,yana faman ihu dan duk abunda yake so su ta shiga yi mishi,har yana wani irin numfashi kmr me neman shid'ewa,dan bazai ma iya fahimtar shin ya bar duniya ko yana cikin ta.
Har sai da ya dawo kanta ita ma yana neman fitar mata da hankali wacce har Allah Allah take aje ga babban aiki dan abunda tafi son ji knn,amma da kamar ma saif ya fita buqatar hakan dan shi tuni ma ya kama hanyar yana kokawar shiga qofar da yaji ta rufe bam kuma sharkaf da lema.
  Wanda hakan ne ya qara rikitar dashi,cikin sauri ze afka mata se kawai yaji gaban sa yayi wani irin mugun fad'uwa.
   Ya tsaya cak jikin sa duk a sa6ule,yana jin sam be kyautawa jamil ba idan har ya aikata hakan,snn ita kanta zarah ya cuce ta dmn jamil ne yafi cancanta ace ya sami budurcinta ba kamar shi da sha'awar ta kawai yake ba.
  Nan ya janye jikin sa daga na zarah ya zauna gefen bed tare da tallabe goshin sa,se ga zarah ta biyo shi tazo ta gurfana a tsakanin qafafun shi zata kai bakin ta a tsakiyar cinyoyin sa,saif dake kallon ta ya tada ta ya zaunar kan cinyoyin sa yana kallon ta cike da damuwa,wacce idanuwan ta a lumshe takai bakin ta kan nashi ta had'e,a hankli ya zare bakin sa tare da kwantar da kanta  kan kafad'ar shi,muryar sa can ciki a hankali yace"ya isa haka zarah yi bacci kinji"
  Zarah ta d'ago tare da girgiza masa kai tace"ni bana jin bacci kamin ina so bazan yi kuka ba"
  No zarah zakiyi kuka da zafi sosai in na miki.
Da sauri cikin girgiza kai tace"um um bazan yi kuka ba kamin ina so.
 Sake maida kanta yayi a kafad'ar shi cikin muryar rarrashi yace"kiyi haquri zarah ni sam ban cancanci na miki ba,masoyinki na gaskiya da ze aure ki nn gaba kad'an ya kamata ya same ki bani ba.
 Da sauri ta d'ago idanunta ta tap da qwalla tace"ba wani masoyi ni kai ne kafi cancan ta kamin ina so dan Allah ko da zafi ne ni kamin kawai".
   Saifuddeen da duk tausayin ta yake ji yayi shiru yana kallonta,wanda shima ba kanta jurewa ne kawai yake amma yasan dole ta fishi buqatuwa ita da ya d'urawa desire tablet irin me qarfin nn ma.
 Kana ya zame a hankli daga kan gadon ya zauna kan rug wacce still tana zaune kan cinyar shi,se faman shafa jikin shi take tare da koma kai bakin ta a nashi ta had'e,be hanata ba se romancing d'inta ya shiga yi sosai duk dan dai ya samu ya rage mata abunda take ji.
 Zarah da ta gama kai qololuwa da kanta ta kama joystick d'in shi tana qoqarin cusawa a jikin ta,ya hana ta,nn kawai ta fashe masa da wani irin kuka tana son ita se tayi.
 Ya rungume ta sosai a jikin sa had'e da share hawayen da suka zubo mishi,yana tunanin me zai ce mata ta haqura dan shi kam yasan ko kad'an be cancan ci ya same ta ba,muguntar da ya mata a rayuwar auren su kad'ai ya isa ace ya barta haka ba sai ya cutar da ita ta hanyar rabata da budrcinta ba kuma.
 Wanda idanun sa cike da qwalla yake kallonta se faman kuka take tana roqon shi.
  Yasa hannu ya shiga share mata hayawe yana fad'in"am sorry zarah ni ba namiji me lafiya bane bazan iya komai da mace ba"
  Wani sabon kuka ta fashe masa dashi tare da ture shi tana fad'in"kawai dai baza ka min ba sbd na gaya maka fanko a wancan lokacin  shine kake so ka hukunta ni dan ka ga ina so ko.
  Janyo ta yayi jikin sa cikin rarrashi yace"No zarah ki yarda dani gaskiya nake gaya miki"
  Girgiza masa kai tayi cikin kuka ita bata yarda ba,snn ta rungume shi sosai tana wani abu kmr me neman shigewa a jikin sa.
   Cike da jin tausayin ta ya janye ta a hankali daga jikin nasa ya tashi yaje ya tsiyayo ruwa a cup da kuma maganin da zata sha desire tablet d'in ya sake ta. 
   Ya kawo mata ba tare da tasan maganin mene ne ba,ranta a 6ace ta kar6a cike da takaici ta wullar da maganin ta kuma kar6e ruwan dake hannun shi ta jefar da kofin ya fashe,snn ta fad'a jikin sa da qarfi ta rungume shi sosai cikin fasa wani sabon kuka da ta shiga yin sa a hankali.
 Shiru saif yayi yana mai shafa gadon bayan ta a hankli cike da tunani fal a ranshi.
  Can bayan yaji ta d'an sassauta kukan da take,ya miqe tsaye riqe da hannun ta se kallon shi kawai take har ya nufi bathroom da ita,ya shiga da ita gurin wanka tare da sakar musu shower,ruwan na fara ratsata ta sauke numfashi me kamar ajiyar zuciya,snn ta kwanta a qirjinsa ta lafe sosai hannayen ta kan gadon bayan shi tana shafa shi a hankli,haka shima se shafa gadon bayan ta yake a hankli kafin yake sa shower gel yana cud'a mata jikinta ta  sannu a hankli cikin natsuwa kmr me wanke qwai.
  Kana ya matsa mata shower gel ita ma ta shiga cud'a masa nasa jikin da haka har suka gama wankan suka fito.
 Yasa d'an qaramin towel ya tsane mata gashin kanta snn ya zaro wani d'an dai dai a towel rack ya d'aura mata,suka fito shima da nasa towel d'aure a qugunsa,yayinda zarah ke liqe a jikin sa bata ko son taji skin d'in ta ya rabu da nashi dan desire tablet d'in be sake ta ba sosai take jin buqatuwa amma rashin samu da kuma zazza6in da ya taso mata ne yasa duk jikin nata yayi sanyi.
  Tana manne a jikin sa ya tafi da ita ya sake 6allo mata maganin da taqi yarda tasha d'azun,ya tsiyaya mata ruwa a cup ya bata,ta kalle sa had'e da qara mannewa a jikin sa cikin maqale kafad'a ita baza ta sha ba,dmn ji take bata da wani abunda zata yi lokacin sa irin taji yana biya mata buqatar ta.
Ya sauke numfashi a hankali yana kallon ta da kulawa snn muryar sa a natse yace"kina so in miki abunda kk so"
  Da sauri ta gyad'a masa kae alamar eh.
  Yace"to sha idan kina so in miki"
   Ba musu ta 6ude bakinta yasa mata maganin had'e da bata ruwa tasha ta kora maganin ta had'iye.
 Bai ko ajiye cup d'inda ke hannun sa ba yaji hannun ta kan qugun sa zata zare masa towel,ya ajiye cup snn ya kama hannun nata yana kallon ta yace"A'a ae sai gobe idan munje asibiti gurin doctor ya dubani snn ko zan iya yi miki"
   Idanunta tap da qwallah tana kallon sa cikin yanayin shagwa6a tace "uhum ni bazan iya haqura har gobe ba muje yanzu"
  "To shikenan"
ya fad'a kafin yake zuwa da ita kan bed ya zaunar had'e da zare mata towel d'in jikinta yasa mata tufafin ta snn shima ya maida nashi tufafin a jikin shi,ya kama hannun ta suka tafi d'akinta.
  Suna shiga kae tsaye ya bud'e wardrobe ya ciro qaton hijab da take yin sallah dashi me kai mata har qasa ya sa mata,snn ya shinfid'a mata dardamu.
 Ya kalle ta yace"ai kinga munyi arwala a bathroom ko?
  Ta gyad'a masa kai
Yace"to kiyi sllr isha nima yanzu zanje masallaci nayi sallah idan na dawo se muje ko"
  Nan ma sake gyad'a masa kai tayi ta bisa da kallo har ya fita daga d'akin snn ta hau yin sallah.
 Koda saif ya dawo ya same ta a nn inda tayi sallah bacci ya kwashe ta ko hijab ma bata cire ba.
  Ajiyar zuciya ya sauke dan dama yasan haka zata faru sbd maganin da ya bata bacci yake sawa sosai.
  Nan ya durqusa a hankli gab da ita ya cire mata hijab ya d'auke ta ya maida kan bed,wanda ya jima tsaye a kanta se kallon ta yake snn daga baya ya fita daga d'akin,yaje d'akin sa ya kwanta se juyi yake tayi kan bed ya kasa bacci gabad'aya ya rasa meke masa dad'i.
  Can ya tashi zaune ya d'auko laptop d'in sa da ke ajiye kan bedside drawer ya bud'e yana kallon zarah still se baccinta take tayi,yaji kamar ya tashi yaje d'akin ta ya rungume ta suyi baccin su.
  Daga nn yana kallonta be san lokacinda bacci ya kwashe shi ba,se asuba snn ya farka sbd kiraye kirayen sllr da ake tayi wanda kae tsaye idanun sa suka sauka akan laptop d'in shi,zarah na zaune kan bed riqe da handout a hannun ta tana karatu,ya bud'e ido d'auke da mamakin wane irin bacci ne ya kwashe shi haka,ya tashi daga jinginen da yake jikin sa duk yayi ciwo sbd yanayin yanda yayi bacci.
  Ya janyo laptop ya matso da ita a gaban shi dmn kad'an ya saura ta fad'i da alama cikin bacci ya ture ta bai sani ba.
Vedeon nata ya maida baya ya duba yaga bata ko yi wani baccin kirki ba ta tashi ta hau yin karatu shine har yanzu bata koma kwanciya ba.
Rufe laptop d'in yayi ya tashi ya shiga bathroom ya d'auro arwala,ya tafi d'akin ta.
Tana ganin ya shigo d'akin,ta ajiye handout ta tafi jikin sa tare da kwantar da kanta a qirjinsa,cikin muryar kuka tana fad'in"ka barni inata jiranka ko karatu ma ban iya yi da kyau ba"
  Beyi mamakin jin abunda take fad'i ba dan tunda yaga bata yi wani baccin kirki ba yasan jinin ta qarfi ne dashi maganin be yi mata wani aiki ba,dole se ya bata wanda yafi shi qarfi gashi jikinta ma duk yayi zafi sosai tana buqatar har allura ya mata.
 Nan ya janye ta a hankli daga jikin sa dan yanayin da yake jin kansa in yasa wasa yanzun zata iya kare mishi arwala.
   Wanda yana d'ago ta yasa lallausan hannun sa ya share mata hawayen da ya gani kan fuskar ta yana fad'in"to yi haquri bari naje nayi sallah na dawo.
  Da sauri ta koma jikin sa tana fad'in"ni wlh bazan yarda ba wayo zaka koma min"
   Saif yayi shiru can yace"shikenan kinga an kusa tada sallah muje bathroom kiyi arwala se muzo mu bi liman tunda muna jinsa har nn kuma masallacin a gaban mu yake."
  Ba musu ta yarda suka je bathroom byn ta d'auro arawala suka fito.
  Suna ida sallah ya kwantar da kanta a hankli kan kafad'ar shi yana ta6a goshin ta yace"muje d'akina in baki magani kisha ki samu kiyi bacci zafin jikin nn ya rage miki"
  Tace"um um ni sai mun dawo da asibiti tukun"
  No zarah yanzu ko munje asibiti baza mu sami likita ko d'aya ba se zuwa qarfe goma.
   Tace"to ae dama ina so inje school,idan ka kai ni se ka tsaya min har na gama test se mu wuce can"
   Yace"Aa keda baki da lafiya me zai kai ki school,ji idanun ki fa duk sunyi wani iri sun kumbura sbd rashin bacci,u have to rest magani kawai ya kamata kisha ki kwanta kinji.
  Tace"um um nafa gaya maka wnn malamin mugu ne idan banyi test d'in shi ba akwai matsala"
  Kar ki damu ba wata matsala ki gaya min wane malami ne,naje na same shi muyi magana ya miki excuse bayan kinji sauqi se ya miki test d'in...a'a ni gaskiya nafi so nayi tare da mutane.
  Shiru saif yayi be sake ce mata komai ba se binta yayi da kallo ta tashi ta d'auko handout ta dawo ta zauna tare da maida kanta kan kafad'ar shi ta kwantar dan jikin nata ba qarfi,tana yin komai ne cikin juriya,shi kansa ya fahimci hakan wanda yana kallo ta ajiya handout a gaban su ta bud'e acewar ya nuna mata yanda zatayi karatu a sauqaqe.
 Be musa mata ba ya shiga nuna mata,yayinda yake jin wani irin tausayin ta na fizgar shi dmn karatun ma da qyar take yin shi.
 
Sanin ko minti d'aya ka qara akan qarfe takwas malamin baya bari a shiga yasa tana ganin qarfe bakwai tayi tace mishi zatayi wanka,wacce koda ta miqe tsaye se jin tayi jiri yana d'an d'ibar ta hakan dai ta jure ta fad'a bathroom tayi wanka.
  Bayan ta shirya se ga saif ya dawo d'akin dan fita yayi  yaje d'akin sa shima yayi wanka.
  Wanda ya shigo ne riqe da cup a hannun sa ya had'o mata thick tea a ciki dmn tasha ko zata d'anji qarfin jikinta.
  Zarah da har ta d'auko jakar ta a niyyar su wuce,tana kallo ya kama hannun ta suka zauna kan sofa ya shiga bata tean har sai da tace ya ishe ta snn abunda ta rage yasha.
  Bayan ya kaita school bai tafi ba ya tsaya jiran ta.
 Suna gamawa ba 6ata lokaci tazo ta same shi,yana kallonta ta shigo motar a daddafe ta zauna.
  Da kulawa ya mata sannu tare da tambayar ta ya test d'in?
 Muryar ta a sanyaye can ciki tace"Alhmdlh"
  Nan tana kallo ya 6alle magani ya bata ba musu ta kar6a tasha,dan abubuwa take ji gasu nn ba dama ko baccin ne ma ta d'an samu tayi kafin su isa asibiti dan ita a tunanin ta da gaske asibiti zasu je bata san wayo kawai yake mata ba.
  Tana gama shan magani ta miqa masa ruwan gorar da ya bata,kafin ya kar6a ta saki gorar ba shiri tare da dafe marar ta da ta shiga yi mata wani irin ciwo na daban,da sauri saif ya kama ta ganin tana qoqarin zamewa daga kan kujerar da take zaune.
  Ya tafi da ita jikin sa se rarrashin ta yake cike da nadamar abunda ya aikata a gare ta,dan yasan duk aikin desire tablet d'inda ya bata ne,amma inshaa Allah wahalar tazo mata qarshe dan maganin da ya bata tasha yanzu me qarfi ne da yafi na farko wanda da zarar tayi bacci ta farka shikenan komai zai dawo mata normal.
 Tun tana jurewa har ta soma yi mishi kuka tana rungume a jikin sa se rarrashin ta yake tayi har ya samu tayi bacci,hakan yasa ya sauke ajiyar zuciya a hankli snn ya kada mata seat ya kwantar da ita.
  Kafin yake jan mota ya bar school d'in yana tafe duk rabin hankalin sa a kanta har suka isa gida.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Sunday 18/03/2018_ *«»«»«»SAIFUDDEEN!«»«»«»*






By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 38 & 39*
Suna qarasowa gida ya tsaya kawai yana ta kallon ta riqe da hannunta da ya kama yana d'an murza shi a hankli kmr me wani tunani a ranshi,can dai ya fita ya zagaya 6angaren da take,ya bud'e ganbu yasa hannuwan sa duka biyu ya d'auke ta snn ya tura ganbun da qafar shi ya rufe,ya shiga da ita ciki ya haura sama zuwa d'akin ta ya kwantar da ita kan bed,ya cire mata hijab,yaje d'akin shi ya had'o allura ya dawo.
   A hankli ya bud'e zip d'in skirt d'in ta ya d'an d'aga pant d'in ta kad'an ya mata allura,byn ya gama d'an murza mata gurin ne snn ya rufe mata jikinta ya gyara mata kwanciyar ta ya fita daga d'akin.

Tun lokacin bacci Zarah keyi har sai qarfe uku snn ta farka,se ganin ta kawai tayi rungume a jikin saif,ta tashi da sauri hawaye na tserar saukowa daga kan kumatun ta,sbd lokaci d'aya abubuwan da suka faru da ita suka shiga dawo mata.
  What's wrong zarah me kuma yake damunki?
  Saifudden ya fad'a fuskar sa d'auke da damuwa yana qoqarin janyo ta jikin sa,zarah da bata ko iya kallon shi ta fashe da kuka cikin sauri ta sauka kan gadon zata fita daga d'akin dan ta ma rasa ina zata sa kanta da wnn abun kunyar da ya faru da ita kmr a mafarki.
  Saif be bar ta fita d'akin ba ya taso da saurin shi yasha gabanta ya rungume ta yana fad'in"calm down zarah gaya min mene ne kinji daina kuka"
  Komai zarah bata iya ce masa ba se kuka ta ci gaba dayi a jikin shi.
  Nan ya tafi da ita kan bed suka zauna se rarrashin ta yake yana bata magana,dan ya fahimci dalilin kukan wanda dama yasan haka zata faru idan komai ya dawo mata normal,shine yake bata magana irin wacce zai samu ta sake ta maida komai ba komai ba.
 Amma har ya qaraci maganganun shi zarah bata iya daina kukan da take yi ba,ya d'ago ta daga jikin sa yana kallon ta kanta qasa taqi yarda ta kalle shi gabad'aya kunyar sa take ji ita kam har bata jin zata iya sake had'a ido dashi,dan abunda ya faru da ita ya riga ya gama bashe ta,da ta rasa ta yanda akayi hakan ya faru da ita.
  Saif dake kallon ta duk yaji damuwa a ranshi be san ta yaya zai fara gaya mata gskyr abunda ya faru cewa duk cin amanar sa ne.
 Nan ya sake maida ta jikin sa muryar sa a hankli yana fad'in"kiyi haquri dan Allah zarah ki daina kukan nn haka kar ki janyo wa kanki ciwon kai kinji,a hankli ta gyad'a masa kai ba tare da ta iya kallon sa ba.
  Yace"to tashi kiyi sllr azahar kinga har uku ta wuce kar sllr la'asar tazo ta same ki.
 Nan ba musu ta tashi ta nufi bathroom koda ta fito saif baya nn ya fita,se bayan ta ida sallah da d'an jimawa snn ya dawo,riqe da plate d'in abinci a hannu shi white rice ce with stew wacce sosai taji naman kaji se qamshi ke tashi,ya ajiye mata a gabanta a nn inda tayi sallah still tana zaune gurin bata tashi ba.
  Wacece bata kalle shi ba se abincin kawai ta kalla kafin tace komai saif dake kallonta yace"plz kar kice baza kici ba,bana siyarwa bane wnn a gurin umma naje na kar6o mana,bcos naga wancan lokacin da na ta6a siyowa miki abinci siyarwa baki ci ba,shiyasa nace may be ba kya son na siyarwa ne ko?
  Bata bashi amsar abunda yake son ji ba se godiya da ta masa.
  Ya kalle ta kawai snn ya tashi ya d'auko mata ruwa a fridge ya ajiye mata snn ya fita,shima yaje zuwa cin abinci dan tun tean da ta rage ya qarasa shanyewa be sake cin komai ba.

Har aka yi sati d'aya zarah bata iya had'a ido da saif,hakan yasa bata sake yarda ya kaita school ba kullum driver ne ke kaita ya kuma d'auko ta,amma hakan be hana saif kullum se yaje d'akin ta ba,dan so yake ko yaya ta sake ta manta komai amma ita kam ta kasa sakewa idan ma ta ganshi se taji komai ya sake dawo mata sabo duk abubuwan da suka faru suyi ta tariyo mata aka da har kullum ta kasa daina tunanin wae wane irin abu ne ya faru da ita awa mafarki da koda ace mafarkin ne yana d'aya daga cikin mummunan mafarkin da baza ta iya gayawa kowa ba.
  Dan duk ta tuna abun ma se taji qwallah sun cika mata ido.
 Yau ta kasance sunday guraren goma na dare ta fito daga d'akin ta,sanye da rigar bacci fara mai santsi er guntuwa wacce bata ko qarasa kai zuwa guiwar ta ba,ga hannayen ta en siriri kmr na vest,ta tufke gashin kanta da ribbon yayinda jellar gashin ta ke yawo a hankali sbd saukowar da take yi daga staircase zata je downstairs.
Tana qarasa saukowa kawai ta hango saif zaune a falo Tv kunne yana kallo,suna had'a ido tayi saurin janye idanunta ta juya zata koma,gashi ta fito ne da niyyar zuwa kitchen ta d'aura ruwan zafin tea tasa a flask dmn taje dashi d'aki sbd azumin da take son yi gobe Monday.
  Tunda ta juya cikin tako d'aya bata qara wani ba ta tsaya cak sbd kiran da saifuddeen ya mata.
  Ya taso ya qaraso gurin ta ya juyo da ita yana kallonta kanta qasa taqi yarda su had'a ido,se hawaye ya gani suna saukowa daga kumatun ta,a hankli cikin damuwa yace"oh Allah mene ne kuma zarah?
  Ni bazan iya ci gaba da zama a gidan nn ba,ina son kaci ka min alqawari na dan Allah in tafi.
   Zarah ta fad'a tana mai share hawayen da suka zubo mata.
  Saif dake sauraren ta,shi kam gaban sa ne yaji ya fad'i,snn lokaci d'aya yaji duk jikin sa a sa6ule,be iya ce mata komai ba se kama hannun ta yayi ya tafi da ita kan kujera suka zauna yana kallonta da kulawa yace"No zarah indai akan wnn abun ne da duk kika sa kanki a damuwa ni bazan sake ki ba,idan zaki cire damuwar ki cire,abu ne fa wanda dan ya faru tsakanin miji da mata ba komai bane,ni sau nawa ina nuna miki tawa buqatar bansa kaina a damuwa ba se ke,yi haquri kinji ki daina zancen nn dan Allah,ki gaya min duk abunda kk so zan miki.
  Duk yana mgnr ne cikin rarrashi.
 Zarah da still kanta ke qasa tace"ni alqawari na kawai nake so ka cika min dan Allah.
  Handkerchief ya ciro ya share zufar da yaji ta d'an tsastsafo mishi a goshi sbd maganar da tazo mishi da ita. Yace"meyasa zarah ko wanda kk so ne yake matsa miki?
  Girgiza masa kai tayi tare da fad'in"um um ni ba wanda nake tare dashi fa,kawai dai ina buqatar ka cika min alqawari na ne,bana son abunda ya faru dani ya sake faruwa dani ina jin kunya.
 Da saurin sa yace"No zarah nayi miki alqawarin bazai sake faruwa da ke ba"
  Cikin muryar kuka tace"kmr ya abunda ya faru dani fa ni kaina bansan ya akayi ba"
  Saif da duk ya daburce yace"to shikenan naji amma kinsan idan na sake ki yanzu Abba zai d'auka ko dan ya hana ni auren Sophie ne naji haushi na sake ki,kuma dama ae ce maki nayi se idan na samu auren Sophie snn ko zan cika maki alqawarin ki.
 Se a lokacin ta kalle shi qwalla tap a idonta tace"to ai ni da kai fa ba me qaunar juna meyasa baza ka sake ni ba"
  Yace"yanzu ke idan na sake ki me zaki cewa su umma? muryar ta a sanyaye tace"nima ban sani ba".
  Yace"To kin gani nima bansan me zan gaya musu ba kuma haka kawai baza ayi saki ba,dan haka idan har kina so in sake ki to kije kiyi tunanin abunda kikasan su Abba baza su ga laifin ko d'ayan mu ba,ko kina da wata hujjar ne yanzu?
 Ya fad'a cikin tsare ta da ido.
 A hnkli ta girgiza masa kai alamar a'a.
  Yaji wani dad'i a ranshi har yana sauke ajiyar zuciya.
  Yace"to kije ko yaushe kika sami hujja kizo ki gaya min,amma fa daga yanzu bana son in sake ganin ki a cikin damuwa ki sake kamar ba wani abunda ya faru idan ba haka ba ko kin kawo min hujja bazan saurare  ki ba bare har na rubuta miki saki.
 Gyad'a masa kai tayi zata tashi ya riqo hannun ta yana kallon er fincikar rigar da ke jikinta ta mata kyau sosai,cikin wata irin murya qasa qasa yace"ina zaki tafi me kika fito yi?
  Zan d'aura ruwan zafin tea ne nasa a flask sbd ina so zanyi azumi.
  Azumin ranko?
Ya tambaya yana me kallonta.
  Ta girgiza masa kai alamar a'a.
  Yace"to nima zanyi se kisa ruwan dani qarfe hud'u zan zo na tashe ki kinji"
   Bata yi magana ba se gyad'a masa kai da tayi.
  Snn ta tashi ta wuce ya bita da kallo har ta shige kitchen,ya sauke numfashi a hankli tare da jingina bayan sa a jikin kujerar da yake zaune,idanuwan sa a lumshe se wani irin qaunar zarah yake ji a ranshi,da ya d'auka ko birge shi ne kawai take.
  Wanda yana zaune a gurin idanuwan sa a lumshe har se da zarah ta gama abunda takeyi a kitchen ta fito riqe da flask,snn ya bud'e idanun sa ya bita da kallo har ta 6acewa ganin sa snn ya iya tashi ya kashe Tv da hasken falon ya haura sama zuwa d'akin shi.
 Qarfen hud'un asuba koda yazo tashin ta ya samu har ta tashi tana bathroom se yunqurin amanta yake jin yana fitowa a bathroom d'in,kae tsaye ya shiga bathroom d'in da sauri.
 Ya same ta gun washbasin kan ta a duqe riqe da brush a hannun ta tana ci gaba da yunqurin amai.
  Ya tallabo fuskar  ta yana kallon ta yace"mene ne?
  Ruwa tasa ta wanke bakin ta snn tace"ba komai brush kawai nakeyi.
 Saif dake kallon ta yace"wane irin brush ne kk yi haka,ki riqa sa brush d'in a hankli kinji.
 Gyad'a masa kai tayi tare da kunna famfo ta wanke brush d'in tasa a d'an wani cute case dake manne a jikin bangon bathroom d'in nasa brushes ta bud'e ta saka snn suka fito yana rungume da ita a jikin sa.
 A nn d'akin sukayi sahur zaune kan rug suna fuskantar juna,yayinda saif shan tea kawai yake amma hankalin sa na gun zarah se kallonta yake tayi musamman yanayin zaman ta duk yafi tafiya da imanin shi,wacce tayi zaman ne cikin matse cinyoyinta kmr zamanta tahiya sbd yanayin rigar ta dole se tayi irin wnn zaman,en kyawawan fararen guiwoyin ta a bayyane,duk tabi ta tsauwala sbd ta lura da kallon da saif keta yi mata.
 Wanda koda suka gama sahur ya bar d'akin duk a jiqe yake jin kansa shiyasa yana zuwa d'akin shi ya gaggauta yin wanka.

Washe gari shi yakai ta school ya kuma d'auko ta.
  Da shigar ta d'aki ta tu6e ta fad'a bathroom tayi wanka byn ta shirya snn ta tafi kitchen dmn girka musu abunda zasu ci idan ansha ruwa.
  Saif yazo yayi tsaye a bakin qofar kitchen d'in yana kallonta,zarah bata san dashi ba se qamshin turaren sa da taji,ta juyo ta kalli bakin qofar kitchen d'in ta ganshi sanye da qananun kaya ya cire suit da alama wanka yayi.
   D'an murmushi ya sakar mata haka ita ma snn ya qarasa gurinta tare da riqo waist d'inta ya d'an tafi da ita jikin sa yana kallon,tarugu tattasai da albasa da ta yayyanka tana d'an soyawa sama sama had'e da qoda da tayiwa gutu gutu,ya kalle ta yace"me zaki dafa mana ne?
  Zarah dake motsa abubuwan da take soyawa tace"taliya ce zan dafa had'e da wake naga lokaci ya tafi"
 Yace"wow that's my  best food but sauran abubuwan da kika d'aura mene ne?
  Ya tambaya had'e da kai hannun sa ya bud'e d'ayar tukunya wanda da saurin sa ya saki marfin yana yarfi da hannu.
 Zarah ta kalle sa d'auke da er dariya a fuskar ta.
  Saif da har ransa yaji zafi yace"dariya ma kike min kinji zafin wae,ya d'aura mata en yatsun sa kan kunci,se kuwa taji yatsun nasa da zafi,a hnkli ta kama hannun nasa tana dubawa har ma ta sami kanta da hura masa en yatsun nasa da taga sunyi ja.
 Kafin take kallon sa cikin yanayin murmushi tace"kai d'in ne da kaud'i in bashi ba me yakai namiji da bud'e tukunya.
 Murmushi kawai yayi ya koma kai hannun sa ze bud'e tukunyar yana fad'in "so nake inga abunda yake ciki"
   Tayi saurin riqe masa hannu tana fad'in"meye haka zaka sake qone kan ka fa"
  Saif ya kalle ta wanda shi kam ae qonewar yake so ya sake yi dmn ta sake hura masa iskan bakinta da yaji wani irin sanyi da dad'i na ratsa hannun sa har be so ta daina ba ma.
Wanda a hankli ya lumshe idanun sa tare da ware su a kanta yace"to gaya min meye a ciki?
 Tace"d'ayar tukunyar farfesun kaza ne d'ayar kuma wake nake tafasawa.
   Tayi mgnr ne tare da bud'e masa kowace tukunya ya gani.
 Ya kama hannun ta yana dubawa yaga ita kam ba abunda yatsun ta sukayi duk da irin laushin su kuwa dan har ma tafi shi laushin hannu.
 Zarah da ta fahimci dalilin kallon hannun ta da yake,a hankli ta zare hannun nata da ya kama,d'auke da murmushi tana fad'in mu d'in ne na daban aikin mu ne mun riga mun saba ba abunda wuta zata mana.
  Au haba ae kuwa yanzun nn zan gwada in gani,saif ya fad'a tare da rungumo ta ta baya snn ya kama hannun ta zai kai a wutar gas cooker.
 Da sauri cikin maqe hannu Zarah tace"Wayyo!
Ya saki hannun had'e da lakato hancin ta yana murmushi yace"matsoraciya nida da wasa nake miki to"
 Murmushi kawai tayi tana kallon sa har ya fita daga kitchen d'in,snn ta maida hankalin ta gun aikin da take yi.

Da aka sha ruwa bayan sunyi sallah,a nn falo sukayi zaune kan rug suna cin abinci a plate d'aya,abun se yayi musu kyau kmr dama can sun saba.
 Wa enda suna cikin cin abincin ne aka soma danna doorbell,saif ya tashi yaje ya bud'e qofa.
 Jamil ne,saif ya masa iso ya shigo ya zauna yana me amsa gaisuwar zarah.
Yayinda saif yaje ya zauna a gaban zarah suna fuskantar juna wato inda ya tashi.
 Invitation a hannun sa yana dubawa,snn ya kalli jamil da shine ya bashi invitation d'in yace"this coming Saturday za'ayi auren knn?
  Jamil yace"eh"
Allah kaimu
Cewar saif kafin jamil ke cewa amin.
  Wanda duk yana yin maganar ne da qyar cikin danne kishi,ganin tare ne fa suke cin abinci har ma wani dukan uku uku yaji gaban sa nayi.
 Can ya tsinkayo muryar saif yana cewa zarah taje ta kawo masa abinci,yace"A'a am ok"
 Daga haka ya miqe tsaye ze fita,saif yace"plz to ka d'an jira ni mana mu kammala cin abinci da akwai mgnr da nake son zamuyi"
  Jamil da baya jin zai iya kallon su suna cin abinci tare yace"ok zan d'an fita na dawo kafin ku kammala cin abincin.
  Saif yace"ok to"
Snn jamil ya tashi ya fita.
 Zarah ta kalli saif tace"katin d'aurin auren sa ne?
 Saif ya kalle ta yace"tukuna ae shi wacce zai aura ba a ko sake ta ba tukun"
  Wani iri zarah taji zancen tace"kmr ya ba'a saki wacce zai aura ba?
  Saif ya d'anyi murmushi yace"da gaske nake gaya miki ba a saki wacce zai aura ba yana jiran a sake ta ne snn suyi aure"
   Zarah tayi er dariya tace"uhm kaima dai da wasa kake se kace baya da aikin yi zai tsaya jiran wacce aka aura wae har se an sako ta,ae komai sonda yake mata gwanda kawai ya haqura tunda har yaga an riga shi ita.
  Saif dake kallonta yace"dan baki san yanda abun yake bane shiyasa,ita yarinyar tun lokacinda ya fara ganin ta yaji yana sonta,amma ita bata sani ba dmn bai ta6a gaya mata ba,yana shirin shigar da kanshi,kwatsam yaji za'a aurawa abokin sa ita,gashi abokin nasa sam baya son ta auren dole ne za'a masa da shi har yarinyar duk ba mai son juna,shine da yaji duk yabi ya rud'e ya gayawa abokin nasa irin sonda yake mata har ma ya buqaci ya bar mishi ita ya aura tunda shi baya so,duk da abokin nasa yayi mamakin sonta da yake haka yayi fafutuka na ganin cewa auren ya koma kan jamil,dmn shi kuma ya samu a barshi ya auri wacce yake so,amma se hkn be samu ba,duk jamil yabi ya damu,abokin nasa yace kar ya damu ya masa alqawarin ko bayan anyi auren ze sake ta ya aure ta dmn shidai baya iya zama da ita,ko zaman da zeyi da ita na d'an wani lokaci dan ba yanda zeyi ne kawai an turasasa mishi,amma burin sa bai wuce ya auri wacce yake so ba.
 Zarah tace"Hm lallai abu se kace film shine yaqi yin aure yana jiran ta,to idan yarinyar tazo tace bata son shi fa bayan an sake ta?
  Saif ya kalle ta kawai yace"bana jin cewa baza ta so shi ba sbd tana ganin kirkin sa.
  Amma ae ganin kirki daban so daban.
  Hakane amma  kirkin mutum nasa a so shi.
  Amma kuma na kasa fahimtar tsakanin sa da qanwar sa zainab yana ganin kirkin ta,amma baya sonta ita kuma sosai take qaunar shi har bata iya kula duk wani saurayi.
  Zarah dake kallon sa tace"zainab wnn da ke dubani idan bana da lafiya?
 Eh ita
Dama ba qanwar sa bace uwa d'aya uba d'aya?
  A'a er gwaggwan shi ce da ta rasu,wato er qanwar mahaifin shi,shine baban sa ya d'auko ta ya riqe ta a hannun shi tun tana yarinya a gidan su jamil ta taso.
 Allah sarki to meyasa baya son ta?
 Nima ban sani ba kawai dai baya son ta asalima be ta6a yarda ya nuna mata cewa ya fahimci tana son shi ba.
 Zarah tace"dan Allah to ka bashi shawara ya aure ta,zainab tana da kirki sosai kuma nidai naga dacewar su,ya daina jiran wacce ba lallai bane ya same ta,duk da dai yayi nisa baya jin kira dan da alama son wnn yarinyar ya zautar dashi tunda har ya tsaya jiran a sake ta ya aura,bata ko san yana yi ba ma,amma ko dan kirkin sa ina roqon Allah ya bashi ita se ya had'a su ita da zainab ya aura ko"
  Shiru saif yayi ya kasa ce mata komai,yana jin wani irin haushi a ranshi kan me ma ya d'auko mata zancen.
  "Ka bashi wnn shawarar dan Allah".
 Zarah ta fad'a cikin marere ce fuska tana kallon shi.
 Ransa a 6ace ya daka mata tsawa yace"da Allah yi min shiru naqi in bashi shawara!
  Jiki sanyaye zarah ta zuba mishi ido tana kallon shi,kana ta miqe tsaye sbd doorbell da taji ana dannawa taje ta bud'e qofa,ras taji gaban ta ya fad'i ganin d'aya daga cikin en matan saif ne tazo,wacce shine karon farko da ta ta6a jin faduwar gaba da kuma wani irin abu da taji a ranta.
  Saif da ya taso yana tambayar ta waye?
  Kallon sa kawai tayi bata iya ce masa komai ba se barin gurin tayi ta haura sama zuwa d'akin ta.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Wednesday 21/03/2018_
*«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*




By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 40*
 Da shigar ta d'aki ta hau tu6e kayan jikinta,duk haushin saif take ji a ranta da bata ma san dalilin tu6ewar da take yi ba.
  Bayan ta gama tu6ewa ta d'aura towel tayi zaune kawai kan bed tana tunanin shi kam wane irin mutum ne marar tsoron Allah asararre azumi fa yayi amma lokacin da suke yin bud'a baki karuwa tazo gurin shi suje su hau yin iskancin da suka saba,baya ko jin kunyar azumin da ya yini dashi
  Mtsw tayi tsaki tare da fad'in"Allah kyauta"
 Nan se ga saif ya shigo d'akin,sau d'aya ta kalle sa ta kauda fuskar ta gefe,be damu ba se qarasawa yayi ya zauna gab da ita tare da kai hannu ya juyo fuskar ta yana kallon towel d'in da ke d'aure a jikin ta da tsayin sa iya rabin cinya,ya kalle ta yace"ya haka kin tu6e ba mu ko kammala cin abinci ba?
  "Shan iska nake"
Ta fad'a fuskar ta a d'aure,had'e da janye hannun sa ta sake kauda fuskar ta gefe.
  D'an guntun murmushi saif yayi yana mamakin wane irin shan iska ne wnn duk irin sanyin split dake ratsa koina a cikin gidan.
  Ya sake juyo fuskar ta yace"to ae se ki cire towel d'in kiyi zir ta yanda zaki fi jin iska sosai ko.
  Zarah dake kallon sa duk haushin sa da take ji kawai ta sami kanta da yin murmushi,se kuma ta kauda fuskar ta,dan se ma taji kunya duk da dai yanayin maganar sa cikin zolaya ne da hakan ne ma yasa ta yin murmushi.
   Saif da ya fahimci kunya taji yayi d'an murmushi tare da kama hannun ta yace"to tashi muje mu qarasa cin abinci.
  Ta qwace hannunta cikin shan toka awa wata qaramar yarinya tace"ka tafi kawai ni bazan je ba kana min tsawa haka kawai ba dalili".
 A hankli ya janyo ta jikinsa cikin muryar rarrashi yace"sorry ni kaina bansan meyasa na miki tsawa ba"
  Zarah dake kallon shi a ranta tace"lallai wnn shi ya cika masifaffe,wato haka kawai ya mata tsawa da shi kansa baisan dalili ba,ba fad'a ba komai suna maganar su lami lafiya abu awa me aljannu.
  Ta ta6e baki tare da fad'in"to bari na kawo mana abincin mu a nn dan bazan iya zama falo haka ba kar yaya jamil ya dawo ya same mu.
  Ta qarashe mgnr ne had'e da miqewa tsaye,saif ya riqo hannun ta yana kallonta yace"kisa kayanki mana se muje mu qarasa cin abincin mu can yafi.
  Zare hannun ta tayi tare da fad'in"Aa ni wanka nake so nayi idan mun kammala cin abinci.
  Daga haka ta wuce ba tare da ta jira me zai ce ba.
  Ya bita da kallo yanayin tafiyar ta jikin ta na karkad'awa abun sha'awa.
  Kana ya kauda fuskar sa cikin sauke numfashi,yaso ace ta maida kayan jikinta ko zai samu natsuwar cin abinci,dan shi kam dai ya rasa wace irin jarababbiyar sha'awar ta ce ke damun sa da har ko yaushe take hana mishi sukuni,baya da halin ya tsura mata ido na minti biyu yanzu ne ya fara jin wani abu,azumin nn ma da sukayi da qyar ya samu yaga ya kai shi,bayan da sahur ma sai da yayi wanka,ko zuwan da yayi kitchen ya same ta duk a cikin juriya yake yin komai.
 Wani numfashin ya koma saukewa a hankli ya kwanta yana jiran dawowar zarah.
 Koda ta dawo still yana kwance idanuwan sa a lumshe,hannuwan sa duka biyu a bayan kanshi yayi pillow dasu.
  Ajiye abincin tayi kan rug snn taje ta zauna kusa dashi tare da d'aura tafin hannun ta a hankli kan goshin sa,ya bud'e idanun sa a kasale da har suka soma canza kala yana kallonta yace"har kin dawo?
  Gyad'a masa kai tayi tare da fad'in"har ma inata sallama baka amsa ba shine na d'auka ko baka jin dad'i ne"
  Lafiya ta qalau banji sallamar ki bane sorry.
 Nan ya tashi tare da kama hannun ta suka zauna kan rug.
  Wanda suna kammala cin abincin ya tashi ya fita.
  Nan ita ma Zarah ta tashi taje ta bud'e fridge ta d'an tsiyaya fresh milk a cup zata sha,se kawai ta tsaya shiru tana kallon fresh milk d'in,wacce kusan kullum haka take yi,tana son sha amma se byn ta tsiyaya a cup se kuma ta kasa sha ta mayar,sbd tuna cewa tana gama shan fresh milk ne wnn abun kunyar ya hau kanta.
 Ko yanzu abunda ta tuna knn ta mayar da fresh milk d'in bata sha ba.
  Ta kwashe kwanikan da suka ci abinci taje kitchen ta wanke snn ta dawo,kae tsaye ta fad'a bathroom tayi wanka snn bayan ta fito tayi sllr isha'i.
Tun lokacin da saif ya fita d'akin bai sake dawowa ba se 11.
 Be qarasa ciki ba se tsaye yayi a bakin qofa had'e da jingina bayan sa a jikin ganbu,qafafuwan sa a hard'e haka ma hannunwan sa rungume a qirjinsa yana kallon zarah dake kwance ruf da ciki,daga ita se half vest da bomshort d'an guntu sosai wanda da kad'an ma ya sauka kan cinyoyinta.
 Yayi minti biyu tsaye a gurin yana kallonta kafin yake sauke numfashi a hankli cike da kasala snn ya qarasa ciki ya zauna kan bed se kallonta yake tayi se kace wata er tsana a yanda yake ganin ta komai nata abun sha'awa,ya matsa gab da ita yana shafa sumar kanta da ta tufke da ribbon,jelar gashin na kwance a gadon bayanta,inda a hankli yake bin gadon bayan nata da ido har ya sauke idanun nasa kan arse dimples d'inta,kmr da tsoro yakai hannun sa a gurin yana shafawa a hankli ya tafi har zuwa santala santalan cinyoyinta yana jin kmr kar ya daina shafar su dan se yaji cinyoyin sun masa wani irin  laushi kmr yana ta6a boobs d'inta da duk su yafi qauna a jikinta da bazai ma iya fisalta irin laushin su ba shiyasa gabad'aya duk yake rikicewa idan yana shafar su.
  Hakan ya janye hannuwan sa kan cinyoyinta ba dan yaso ba se dan yana son ya gyara mata kwanciyar ta,sbd sanin illar yanayin kwanciyar da tayi na ruf da ciki yakan sa ciwon qirji,ciwon zuciya,baqin rai da kuma makamantan su.
  Yana gyara mata kwanciyar ta yasa blanket ya rufa mata jikinta har zuwa qirjinta dan ya fahimci kmr sanyin split ya fara ratsa ta da yawa.
  Bayan ya rufa mata jikin ta ne ya d'auke mata handout din da ya gani kan bed da alama karatu take tayi bacci,dan ko wutar d'akin ma bata kashe ba.
  Yasa mata handout d'in a cikin jakar ta ta zuwa school snn ya kashe mata wutar d'akin ya fita.
Washe gari koda zarah ta kammala shirin ta na zuwa school ta fita,se fmn jiran saif take be fito ba ga lokaci yana tafiya.
 Har tayi tunanin ko ta kira drivern da ke kaita yazo,se kuma taga shima wani qarin 6acin lokaci ne kafin ya iso gwanda kawai taje ta dubo saif d'in tukun.
   Nan ta koma daga ciki kae tsaye ta nufi d'akin sa tana mishi knocking.
  Se can aka bud'e qofar,ga mamakin ta ba saif ne ya bud'e mata qofa ba, d'aya daga cikin en matan sa ce wato wacce tazo jiya suna tsakar yin bud'a baki,ashe bata tafi ba a nn gidan ta kwana.
  Hm
Zarah ta fad'a a ranta tana me kallon saif da ya fito daga bathroom daga shi se d'an guntun wando,snn d'an qaramin towel riqe a hannun sa yana tsane ruwan jikin sa,wanda suna had'a ido da zarah yayi saurin janye idanun sa dan haka kawai yaji ya sami kansa da jin nauyin ta.
 Zarah da bata ma san abunda take ji a ranta ba da saurin ta ta bar bakin qofar d'akin,ta fita se waje a bakin titi tana neman adaidai ta,sanin baza ta samu ba yasa ta shiga kiran drivern ta.
  Kiran be ma fara shiga ba kawai taji an kar6e wayar had'e da tsinke kiran.
  Koda ta duba saif ne wanda har ya fiddo motar shi waje,yana sanye cikin farar jallabiya ya kama hannun ta se binsa kawai take da kallo har yasa ta a mota suka kama hanya,duk wani abu da takeji a ranta haka ta danne ta ciro handout d'in ta tana karatu da alama test zasu rubuta.
 Saif da still yake jin nauyin ta se satar kallon ta yake tayi,yana son tambayar ta ko suna da test ne,amma ya kasa tambayar ta har ya sauke ta school.
  Haka ma da suka gama lectures ya d'auko ta,zarah bata damu da kallon ko gefen sa ba shi kam se kallonta yake yana son ya mata magana amma ya kasa samun fuska har suka iso gida.
 Da isowar su ta fita mota ta wuce ciki.
  Saif ya bita da kallo kawai,wanda har satin ya qare zarah ba ruwan ta da shi,abun da yasha mata kai kawai takeyi d'an shirin da suka fara duk suka daina kmr basu ba,duk da  sosai ya shiga damuwa,amma se harakar gaban sa yake dan kullum da klr macen da zata shigo gidan ta kuma kwana se safe snn ta tafi,kuma shigowar su da fitar su duk a idon Zarah shiyasa ma ta fita harakan sa kwata kwata ko school ma driver tasa yaci gaba da kaita har suka kwashe sati biyu a haka.
   Yau Wednesday tana dawowa school tayi wanka ta shirya cikin qananun kaya kmr kullum duk ta dawo wankan qananun kaya take masu fito da ita,duk da tana cikin damuwar abun da saif keyi na kawo en matan da yaci gaba dayi,bata fasa ba se ma abunda ya qaru dan yau wankan qananun kayan sun fi na kullum d'aukar ta tayi masifar kyau a cikin su.
Da kullum Nusaiba ce ke qara d'aura ta akai idan sun had'u ta WhatsApp.
 Saif na zaune falo yana waya ta fito zata je kitchen ya kafe ta da ido yana kallon ta har baya son qiftawa,yana tuna can baya lokacinda yaje d'akin ta yaga ta fidda qananun kaya ta ajiye kan bed ya ta6e baki dan a shirme ya d'auki abun be d'auka zata ta6a yin kyau a cikin su ba,se gashi tun rnr da ta fara saka qananun kayan yaga sun mata kyau,har ma yayi mamaki a ranshi da yasa ya ya tsaya na tsawon sakwanni yana kallon ta.
 Wanda tun daga lokacin ne fa a hnkli ta d'an fara birge shi har zuwa yanzu da kalolin dressing d'inta ke matuqar birge shi da tsakalo mishi sha'awa,da kullum har Allah Allah yake ta dawo school yaga irin wankan qananun kayan da zatayi kuma,sbd kullum da kalar qananun kayan da zata sa ba maimaitawa take ba,shiyasa kullum sha'awar ta se abunda ya qaru,da ko en matan sa da yaci gaba da kulawa duk a dalilin shawa'ar ta ne yasa dole yaci gaba da kula su,inda asali tun farko yana kawo su gidan ne domin kawai abubuwa suyiwa zarah yawa taji duk zaman gidan ya isheta,ta nemi barin gidan da kanta,yanzu kuma da yake son fita harakar su,sha'awar ta sam taqi barin shi dan akan su yake d'an rage wani abu dan de kam baya jin sun gamsar dashi kmr ace zarah d'in ce ya samu,wanda kullum tsoron sa kar yaje daga haka ya fara aikata abunda be ta6a aikatawa ba dan ji yake ya kusa ma,amma dole yasan abun yi kafin hakan ta faru da shi.
  To meye abin yi....ka daina kula wa en nan en matan kwata kwata,ka dinga yin azumi dmn shine babbar mafita,zarah kuma kaje ka same ta cikin hikima da dabara ka mata wayo ta daina sa qananun kaya.
  Amma wayo wane iri me zan ce mata har ta yarda?
    Kace mata wnn abun da ya faru da ita ranar da ta shiga jin buqatuwa sosai duk yawan sa qananun kaya ne ke kawo shi,idan har tana son kar wnn abun ya sake faruwa da ita to fa lallai se ta daina saka su kwata kwata dan yana ma gab da sake dawo mata.
   Saif da duk zuciyar sa ce ka basa wnn shawarar yayi d'an shu'umin murmushi,dmn yasan tabbas idan ya gayawa zarah haka ta ajiye sa qananun kaya knn.

Nan ya sauke numfashi tare da lumshe idanun sa a hankali,yana jin yanda yake jin nn kam bazai iya haqura ba dole ko akan zarah ne zai je ya d'an rage wani abun kafin yake fara bin shawarar da zuciyar sa ta bashi.
  Nan kawai ya cillar da wayar sa ya tashi gadan gadan ya nufi kitchen.
  Zarah da ta d'auko c pot zata d'aura ta ganshi tafe tayi tsaye kawai tana kallon yanda ya shigo kitchen d'in hakan nn wani iri idanuwan sa gabad'aya sun sauya kala.
  Wanda a hankli ya qarasa inda take ya tsaya yana kallonta haka itama se kallon sa take,se kuma ta fara matsawa a hankli tana ja baya sbd yanda taga yana qara matsowa kusa da ita,jin takai jigin gina yasa ta tsaya ranta a 6ace tace wae meye hak.....bata qarasa fad'a ba se jin bakin sa tayi a nata,ba shiri ta saki c pot d'inta ke hannun ta tana qoqarin qwatar kanta amma ko yaya ta kasa,da lokaci d'aya taji ya yage mata rigar jikinta ya jefar ya shiga luguiguita ta son ranshi snn ya barta ba don ya samu yanda yake so ba se dan kukan da ta ajiye mishi,dan jin kukan nata yayi har cikin ranshi yana jin wani zafi a zuciyar shi.
 Ya rungume ta se rarrashin ta yake yana bata haquri,ta ture shi tare da tofa mishi yawu a fuska tace"qazami kawai Allah ya isa ban yafe ba.
   Handkerchief ya zaro ya share yawun snn ya fizgota da qarfi zuwa jikin sa bakin sa saitin kunnen ta cikin wata irin murya qasa qasa yace"yau ni ne qazamin bayan ranar kin gama tsotse koina a jikina har da nn ma,ya fad'a tare da kai hannun ta kan joystick d'in shi....ba shiri ta qwace hannunta cikin fasa kuka ta d'auki takalmin ta se dukan sa take dan bata ma san me zata masa ba taji sauqi.
   Sosai ta bawa saif dariya,ya qwace takalmin ya rungume ta sosai a jikin sa tare da d'aura mata kiss gefen kunci cikin murya me dad'i yace"sorry na rama ne kawai but i dnt mean to hurt u baby.
  Ture shi zarah tayi ta zauna tare da had'e kanta da guiwa tana ci gaba da kuka sosai a ranta taji ciwon abun da ya gaya mata wanda shikenan ae tasan wnn abun kunyar ya riga ya gama bashe ta ita kam.
  Jikin Saif ne yayi sanyi duk yaji bai ji dad'i ba ya durqusa kusa da ita cike da son ya rarrashe ta,be samu hakan ba sbd qarar doorbell da yaji ana dannawa,ya kalli rigar zarah da duk ya yaga ta ba halin ta mayar se dai a jefa dustbin.
Bayan t-shirt da akwai singlet a jikin sa,ya cire t-shirt d'in me guntun hannu ze sa mata taqi yarda.
  Muryar sa a natse yace"to tashi kije d'aki ina ga jamil ne kuma in ya shigo zamu jima"
   Kamar ma bada ita yake magana ba,ko d'agowa taqi tayi se kukan ta take ci gaba dayi.
  Hakan yasa kawai ya mayadda rigar shi snn ya tashi yaje ya bud'e qofa.
 Hajiya ce tazo.
 Ae kuwa cikin sakin fuska sosai yana murmushi ya bata hanya ta shiga,suka zauna bayan sun gama gaisawa take tambayar sa zarah fa?
  Yace"tana kitchen bari na kira miki ita"
  Yana zuwa kitchen ya cire rigar sa tare da durqusawa a gaban ta yana fad'in"sorry zarah tashi kisa rigar nn kinji Hjy ce tazo"
 Shiru zarah tayi ta daina kukan da take snn ta d'ago a hankli tana share hawayen fuskar ta,saif ya kai lallausan hannun sa yana taya ta se haquri yake bata wanda da kanshi yasa mata riga snn ya kama hannun ta suka tafi.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: Thursday 22/03/2018
*«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*




By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 41*
Koda suka isa falo se kallon ikon Allah hajiya keyi ita kam,tana kallon saif da singlet wanda yanzun nn fa koda ya tashi da riga ta ganshi a jikin sa amma se gashi rigar har ta koma jikin zarah,ko ina rigar zarah ta shiga a kitchen d'in ne? "ikon Allah"
 Hjy ta fad'a a ranta kafin take amsa gaisuwar zarah snn da kulawa ta kama hannun ta ta zaunar da ita kusa da ita tana kallon zarah wacce ta sadda kanta qasa ta kasa kallon ta se faman kame kame take tana gyara wuyan riga se kace wuyan rigar ya mata ruwa bayan kuwa rigar collar ne ma da ita,kuma kaf botiran rigar ba wanda saif ya rage da be rufe mata ba.
  Shiru Hjy tayi bata ce da ita komai ba se maida duban ta tayi gun saif wanda suna had'a ido yayi d'an murmushi cikin sauke idanun sa qasa yana d'an sosa bayan kansa irin na jin kunya d'in nn.
  Hjy tayi murmushi kawai tare da girgiza kanta.
  Snn ta kalli zarah d'auke da murmushin da ke kan fuskar ta,ta shiga magana da ita cikin harshen fulatanci.
  Saif dake sauraren su in banda karatu,da kuma Alhmdlh da yaji zarah ta fad'a a cikin maganar ba abunda yaji.
 Se binsu kawai yake da kallo har suka gama maganar su,snn zarah ta tashi a natse dmn kawowa hajiya ruwa.
  Nan Saif ya kalli Hjy yanayin fuskar sa kamar qaramin yaro yace"wai ni kam hajiya meyasa kowa ya iya fulatanci nn banda ni why?
  Hajiya tace"Sbd kai d'in na daban ne,tun kana yaro ba abunda za'a saka kayi se idan kana ra'ayi,kuma ko ubannan naka ae ba wani jin fulatanci suke ba dan ban wani koya musu ba shiyasa kaima baka iya ko bidib ba.
 Fuskar sa cikin nuna rashin jin dad'i yace"Hajiya kice kece baki koya min ba,ba wai rashin ra'ayi na ne ba,amma tukuna dai hajiya shin a ina kika iya fulatanci dan naga a sani na Alhj (cewa da marigayi kakan shi)sam ba bafulatani bane mutumin kano ne.
  Er dariya hajiya tayi tace"to kae in banda abun ka dan shi ba bafulatani bane nima haka,to bari kaji ni dama can asalin bafulatana ce koda mukayi aure dashi,kmr dai yanda ubananka sukayi.
 Saif yace"knn kakata ta gefen su umma da ta rasu bafulatana ce itama.....yo naji shashan yaro mutum da ranshi kana saka ta a layin matattu,ba bakin ka ba maza tofadda yawu dmn kuwa tana nn raye cikin qoshin lfy,rashin zumunci ne kawai ke damunka da tun kana yaro baka son zuwa rimin dako kae a dole tashin birni baka son zuwa qauye awa a kanka aka fara rayuwar birnin.
Saif da duk yaji zancen wani iri,yace"kmr ya hajiya tun ina yaro fa ban manta ba dana tambaye ki wace ce kakata ta gefen ummana kika ce min ta rasu bata raye.
  Shiru hajiya tayi tana tuna lokacin lallai haka ta gaya mishi amma ita a nufin ta mahaifiyar mom d'in sa ta ainihi ce take nufin ta rasu,ba mahaifiyar umma ba.
 Ta numfasa tace"hakane mana amma ai ko ita ta qauyen kakar ka ce kai d'in ne kawai ka qiya musu.
  Saif yayi shiru yace"Hjy ban sani bane wlh shiyasa ma bansan zarah er uwar mu bace daga sama kawai naji abun,ashe kakanin mu d'aya ma da ita,but hajiya ina son in sani ita kaka ta qauye yayar kaka da ta rasu ce ko qanwar ta?
 Shiru hajiya tayi snn da saurin ta tace"kaga na gaji da wa en nn tambayoyin naka abu awa d'an jarida,se tamboyoyi kake ta min ko ruwa baka bar nasha ba kinga zarah er albarka tsiyaya min ruwa nasha dmn na fahimci wnn sakaran so yake na bar gidan nn maqoshi na a bushe.
  Zarah wacce bata jima da ajiye ruwan ba ta zame daka kan kujera ta tsiyaya mata lemu a cup ta bata had'e da komawa ta zauna.
 Hajiya ta kur6a lemun yayinda saif ke fad'in"ba haka bane hajiya is gud nasan sauran en  uwana akan inzo inata wulaqan ta su ban sani ba.
   Hjy tace"Au kaddai lokacin da suka ta6a zowa wulaqan tasun kayi?
 "No Hajiya"
Ya fad'a yana me kallon zarah da ita ma shi take kallo.
 Snn ya maida duban sa gun Hjy yace"ni ban wulaqan ta su ba,ina magana ne kan kar hakan yazo ya fara faruwa cikin rashin sani.
  Hajiya tace"kaga nifa zowa kawai nayi in ganku na kuma ganku to sai watara nn ku,ta miqawa zarah kofi tare da fad'in"Allah yayi miki albarka kinji zarah kiyi ta haquri nasan halin saifuddeen se haquri.
 Ta qarashe mgnr ne had'e da miqewa tsaye
 Cikin rashin son ta tafi Saif yace"plz Hjy ki zauna yanzun nn fa kika zo be kamata ace har zaki tafi ba.
A'a sai dai wani lokacin idan na koma dawowa,Alu driver na can a waje yana jira na kar yaga na jima bayan ce masa nayi ba wani jimawa zanyi ba ina so zan biya wasu guraren kuma.
  Daga haka bata jira me zai ce ba ta nufi qofa.
  Ba yanda ze yi haka suka tafi zasu rakata.
  Suna kai qofa ya bud'ewa Hjy qofa ta fita shima ze fita knn ya tsaya yana kallon zarah da itama niyyar ta fita zatayi ta raka hajiya ya dalla mata harara yace"kina hauka ne ina zaki je da wa en nn kayan a jikin ki.
  A hnkli Zarah ta sauke idanun ta kan wandon da ke jikinta skinny ne gold in colour se shining yake irin me attraction d'in nn sbd yanayin material d'in sa kmr leather da ya kama jikinta sosai.
  Ita kanta tasan lallai be kamata ta fita haka ba hakan yasa bata ce masa komai ba,se Allah kiyaye ta yiwa hajiya a nn inda take tsaye.
  Shi kuma ya tafi har mota ya raka ta snn ya dawo.
  Ya samu zarah ta mayyad lemu a fridge zata je kitchen riqe da d'an small trayn da ta d'aura cup akai zata mayar.
 Ya riqo hannun ta had'e da kar6e trayn ya ajiye kan stool,ya tafi da ita kan kujera suka zauna ya kama duka hannayen ta biyu ya riqe a cikin nashi yana kallonta da kulawa yace"kinga Hjy taqi ta snr dani sauran en uwan mu da ban sani ba,gashi se naji ina son in sani musamman ma ummar ki ina so in santa dmn zuwan da mukayi qauye ban ganta ba kuma abunda na fahimta wnn mutumen da ya shiga damu cikin gida like kawun ki ne ko?wanda matar sa ita ce muka samu tana miki kalaba hakane?and se wnn tsohuwar ita kuma granny ko?to ummar ki fa?
Zarah da tun lokacinda ya fara zancen sa kallon sa kawai take,fuskar ta a d'aure ta kwace hannayen ta tare da fad'in"kaga ni ba er uwar ka bace gaba da baya,mahaifiya ta kuma bazan fad'a ba ka fara tambayar kanka waye taka mahaifiyar tukun.
 Daga haka kawai ta miqe tsaye zata bar gurin ya tad'e mata qafa ta fad'i kan rug kafin ta tashi ya tafi jikinta ya mata rumfa yana kallonta d'auke da murmushi yace"kin raina ni ko"
  Zarah da duk haushin sa take ji tace"wane rainin ae gaskiya na gaya ma kaf dangin ku ina kuka had'u da en qauye bare har mu zamo en uwan ku,Allah sauwaqe bama ciki wlh,kaje can wani gurin ka nemi en uwanka,mu mun gode Allah a yanda muke qauyawan.
  Saif da still murmushi na kan fuskar sa yana kallonta yace"hm kinji haushi ne akan abubuwan da na miki a baya,to kiyi haquri kinji a ajiye wnn mgnr ta wuce,ina so ki yafe min ki kuma snr dani sauran en uwan mu gabad'aya na ziyar ce su na kuma basu haquri akan rashin zumuncin da nayi a baya kinji.
  Yana magana ne sosai cikin kwantar da murya.
 Amma zarah se tsaki tayi tare da da qoqarin miqewa.
  Saif be tashi daga kan jikin ta ba bare ta iya tashi se kallon ta kawai da yake.
  Tace"kaga dan Allah ka barni in tashi yunwa nake ji"
  Hannun sa kan lips d'inta yana shafawa yace"to gaya min yanzun zan barki ki tashi.
  "Naqi"
Ta fad'a cikin turo baki.
 Cike da sha'awa saif ya tura d'an yatsan sa da yake shafa lips d'in ta a cikin bakin nata da ta turo,ba shiri ya zare sbd gantsara mai cixo da tayi,snn da saurin ta ta ture shi tana dariya ta miqe zata gudu,saif ya tashi zaune tare da fizgo ta ta fad'o kan jikinsa,tana kallon shi ya 6ata fuskar sa awa qaramin yaro ya nuna mata yatsan sa wai ta gani har cizon da ta mai ya fito.
  Kama hannun nasa tayi cike da ganin sha'awar yanayin shagwa6ar sa sosai ta masa kyau,idanunta akan shi tasa yatsan sa a cikin bakin ta tana tsotsa yatsan a hankli kafin take zare yatsan ta d'aura shi akan tafin hannun ta tana hura mishi iskan bakin ta.
  Saif ya lumshe idanun sa,har ransa yake jin dad'in iskan bakin ta dake sauka akan d'an yatsan sa,ya tafi da fuskar sa gab da tata har tsinin hancin sa na ta6a nata ze had'e bakin su....
Zarah tace"meye haka?
Ta fad'a tare da ture shi daga jikinta tana dariya d'auke da mamaki a fuskar ta,saif ya kalle ta a kasale cike da sha'awa yana kallon dimples d'inta dake lotsawa,zata tashi ya kamo ta yana fad'in"oya bring my shirt tunda baza ki gaya min abunda na tambaye ki ba.
  Cikin dariya ta ture hannun sa da yake qoqarin bud'e buttons d'in rigar  tace"na baka me kaifa ka yaga min riga ka biya ni tukun ko zan baka wnn.
  Be kula ta ba se qoqarin cire rigar yake wanda ba komai ne yasa yake son cire rigar ba irin yayi wasa da dukiyar fulanin ta.
  Ita ma ta fahimci abunda yake niyya tayi nasarar qwace kanta ta tafi da gudu zuwa kitchen ta kullo qofar da sauri tasa key.
  Saif da ya bita da kallo yayi murmushi cikin sauke numfashi.
  Se kuma da saurin sa ya miqe zumbur sbd ihun da yaji zarah ta fasa ya tafi da sauri dai dai ta bud'e qofa ta fad'o jikin sa ta rirriqe shi cikin yanayin jin tsoro ta nuna mishi store tana fad'in"inaga wnn farar kyanwar ce a cikin store naji abu ya fad'i.
  Saif dake kallonta a hankli ya sauke ajiyar zuciya cikin murya me natsuwa yace"Allah zarah har kinsa na tsorata da naji ihun ki na d'auka ko wani abu ne ya same ki,abu ne kawai ya fad'i a store bcos kitty da kk fad'a ae tuni bata gidan nn,tun rnr da muka je gidan su jamil kika musu gaisuwa a washe garin rnr da naje Hospital jamil ya d'auke kitty ya tafi da ita tana can hannun shi still yaqi ya bani har yau,kawai dai kullum yana zuwa min da ita Hospital,amma yaqi yarda na dawo da ita.
 Zarah da tayi shiru tana tuna lallai fa rabon da tasa kitty  a idon ta har ta manta,ta d'ago daga kan jikin sa tana kallon sa tace"meyasa to ya d'auke ma ita?
  "Oho masa"
Saif ya fad'a cikin d'aga kafad'un sa,wanda da sanin sa yaqi gaya mata gaskiyar dalilin da yasa jamil ya d'auke ta,sbd yasan yana gaya mata yanzu ne zata hau yabon halin jamil,shi kuma a ransa baya so haushi yake ji idan tana yabon jamil.
  Me zaki dafa?
Ya tambayi zarah.
 Tace"indomie "
 Bai ce mata komai ba se hannun sa yakai kan rigar jikinta ya bud'e mata button d'in farko da na biyu ya qara gyara mata collar rigar snn yace"ki dafa dani zanci"
 Gyad'a masa kai kawai tayi tana kallon sa ya juya ya  fita daga kitchen d'in,snn a hnkli ta sauke idanunta a kan buttons d'inda ya bud'e mata,ta d'aura hannun ta a gurin d'auke da d'an murmushi a fuskar ta.
 Kana ta wuce store ta d'auke abunda ya fad'i snn ta hau zirga zirgar dafa indomie.
  Koda ta gama dafa indomie d'in ta fito bata same shi a falo ba,har tayi tunanin ko taje ta kira shi se kuma ta fasa dan yanzu ko hanyar qofar d'akin nasa bata son zuwa sbd en matan da yaci gaba da kawowa,haushin abun take ji sosai.
Nan kawai tayi zaune kan rug ta ajiye plate d'in indomie a gabanta ta lanqwashe qafafu ta fara ci knn ta ganshi ya fito still yana nn daga shi se singlet da dogon wandon da ke jikinsa.
 Kae tsaye ya nufi fridge ya d'auko fresh milk,yazo ya zauna suka hau cin indomien tare har suka kammala snn ya tsiyaya fresh milk a cup ya bata,bata kar6a ba se girgiza kanta tayi alamar bata sha,bai ce mata komai ba shi kam yasha dan yasan tun daga rnr bata sake shan fresh milk ba.
  Yana kallo ta tashi riqe da plate d'in da suka gama cin indomie ta tafi dashi kitchen ta wanke duk wani abunda ta 6ata snn ta fito,still ya koma binta da kallo har sai da ta haura sama zuwa d'akin ta snn ya tashi riqe da cup da fresh milk a hannun sa ya tafi d'akin shi.
 Washe gari koda yaje ya tashe ta sllr asuba ya same ta kwance a tsakiyar tiles d'in d'akin se juyi take tana kuka.
  Da saurin sa ya qarasa gurinta yana riqa ta kawai yaji ta sake mishi gabad'aya ta some mishi a jiki.
 Oh my God!
Ya fad'a a rud'e yana kallon jinin da ke fitowa a qasan ta yana biyowa ta qafafun ta,da sauri ya tashi yaje d'akin sa ya d'auko laptop ya hau duba me ya same ta har hakan ta faru byn jiya da dare guraren sha biyu koda yazo d'akin ta ya same ta lafiya lau se bacci take.
  Bakin sha biyu d'in ya maida yana dubawa,har qarfe biyu duk lafiya lau take tana bacci to 3 ne ciwon mara ya tashe ta har zuwa yanzun qarfe biyar da wani abu da yazo ya same ta ciwon be sassauta mata ba se somewa ma da tayi.
  Rufe laptop d'in yayi ya dawo kanta riqe da ruwan gora da ya d'auko a fridge ya shiga yayyafa mata yana kiran sunan ta.
   Amma ina ba alamar zata farka ga jinin da ke fita a jikinta se qaruwa yake sosai awa me miscarriage,duk yabi ya rud'e,shi kam yasan bata da ciki bare yace ko cikin ne ke zubewa asalima duka duka yau satin ta d'aya da gama on,bare yace ko On d'in ne yazo mata haka.
  Gabad'aya ma ya rasa me zai yi se ciro wayar sa yayi ya kira umma ya gaya mata halin da ya samu zarah a ciki.
 Snn byn sun gama waya yaci gaba da yayyafa mata ruwa yana jijjiga ta yana kiran sunan ta still bata farka ba har se da umma tazo yaje ya bud'e mata qofa suna shigowa d'akin suka samu Zarah na motsi,saif ya tafi da saurin sa ya kama ta had'e da rungume ta a jikin sa yana fad'in"Zarah mene ne me yake faruwa dake haka gaya min kinji dan Allah"
 Duk yana maganar ne a rud'e kmr zeyi kuka.
 Zarah kam ko magana bata iya yi,se hannun ta takai kan marar ta,ta riqe sosai kmr me shirin ciro ta gabad'aya,wacce da qyar ta iya bud'e idanuwan ta dake rufe tana kallon saif lips d'inta na rawa tana son yin magana amma ta kasa,se rufe idanun ta ta koma yi.
  Umma tayi kanta da sauri tana kiran sunan ta.
  Nan mahaifiyar saif ta saki wata irin dariya wacce ke zaune a gaban boka tana kallon abunda yake faruwa a jikin qwaryar da bokan ke nuna mata.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Friday 23/03/2018_
*«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*




By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«» 42*
Tace"Gud boka tsafi ya dafa maka,aikin  ka na kyau,ina fatar se da cikin nata ya gama zubewa snn ka aikata lafira,dmn ko a lafira bazan ta6a yarda d'ana ya had'a zuri'a da wa en nn matsiyatan ba.
 Wata irin dariya bokan yayi snn yace"Ae ban kashe ta ba tukun Hjy zafin ciwon ne ya koma sumar da ita amma yanzun zan aikata lafira dmn tuni cikin ya gama zubewa.
  Nan kawai yayi wani irin ihun tsafi tare da saka hannayen sa duka biyu a cikin qwaryar tsafin ya shaqe wuyan zarah wacce take ta hau yin shure shure.....firgigit Abba ya farka daga mummunan mafarkin da yake,ya tashi zaune yana fad'in"innalillahi wa inna ilaihi raji'un!x3
  Snn da saurin sa ya d'auki wayar sa dake ajiye kan bedside drawer ya kira saif.
  Saif na cikin bacci ya soma jin wayar sa na ringing.
 Ya tashi cike dajin bacci ya kunna bedside lamp yana kallon agogon bangon d'akin qarfe uku na dare.
  Ya d'auki wayar a ransa yana mamakin lafiya Abba ya kirasa a irin wnn lokacin.
 Wanda ya d'aga kiran ne had'e da yin sallama,Abba ya amsa sallamar tare da fad'in"ina zarah take tana lafiya ba abunda ya same ta?
  Saif yace"eh..Abba tana..lafiya..me yake faruwa?
  Abba ya sauke ajiyar zuciya tare da fad'in"ba komai ka bani ita muyi magana"
  Saif da duk ya shiga tunanin wae me yake faruwa yace"to Abba bari na tashe ta"
  "Yauwa ina jiranka"
Abba ya fad'a kafin saif ke tsinke kiran ya tafi d'akin zarah,ya kunna hasken d'akin ya ganta kwance kan bed se sharar baccinta take tayi.
  Yaje ya zauna gab da ita yana kallonta se jin yake kmr kar ya tashe ta sbd da gani baccin yana mata dad'i sosai.
  Hakan dai ya shiga bubbuga pillown ta a hankli can zarah ta bud'e idanunta cike da jin bacci tana kallon shi fuskar ta a yamutse.
 Saif dake kallonta yace"ki tashi Abba ne yake son magana dake a waya"
  "Baffa"
Ta fad'a tare da miqewa zaune tana kallon shi,kafin take kallon agogon bangon d'akin snn ta maida duban ta gare shi tace"uku na dare ne fa yanzun me yake faruwa?
 Saif da ya shiga kiran numbar Abba ya kalle ta yace"nima ban sani ba na tambaye shi yace min ba komai,but kar6i waya kiji maybe ze gaya miki ne"
  Nan Zarah ta kar6i waya gaban ta se fad'uwa yake kaddai wani ne ba lfy ko ya rasu.
  A natse tayi sallama cikin girmamawa kmr tana a gaban Abba,byn Abba ya amsa sallamar yace"kina lafiya zarah are u ok komai ba abunda yake damunki"
  Tace"eh Baffa ina lafiya"
  Yace"mashaa Allah,Allah ya qara tsare lfyr ku keda abunda kk tare dashi,idan zaki koma bacci kiyi addu'a kinji"
 Tace"to Baffa Nagode"
 Daga haka ta bawa saif waya kmr yanda Abba ya buqata.
  "Ka kula da zarah kar ka barta ita kad'ai kasan ba ita kad'ai bace tana buqatar kulawa"
 Abunda Abba ya gayawa saif knn a lokacin da saif ya kar6i waya,saif dake sauraren sa yace"to Abba inshaa Allah"
  Nan suka tsinke wayar yana me kallon zarah da itama shi take kallo,yace"me Abba ya gaya miki?
  Tace"ya tambaye ni ne ina lfy,nace mishi eh yace to idan zan kwanta nayi addu'a"
  Shine kawai abunda ya gaya miki?
Girgiza masa kai tayi ta sadda kanta qasa tana wasa da en yatsun ta snn tace"ya min addu'a kan Allah ya qara tsare min lafiya ta nida abunda wae nake tare dashi.
  Saif dake kallon ta ya numfasa yace"olryt ki kwanta kiyi bacci inaga Abba mafarki yayi shiyasa duk hankalin sa ya tashi.
 Nima abunda nake tunani knn amma meyasa yake tunanin ciki ne dani.
  Ta fad'a tana me kallon sa kmr me tuhumar shi.
  D'auke da d'an murmushi saif yace"tun wnn murar da kikayi ne fa har kika kwana a gida ya d'auka ko ciki ne dake ashe har yanzu be ajiye wnn tunanin ba"
Cikin rashin jin dadi' tace"Eyyah gaskiya tun wuri kasan yanda zaka yi ka gaya masa gaskiyar cewar wnn murar duk muguntar ka ce ba wani abunda nake da nikam,Allah sauwaqe ma inyi ciki dakai.
  Ta qarashe maganar fuskar ta a d'aure,snn ta kwanta,se ganin saif tayi shima ya kwanta gab da ita had'e da rungume ta a jikin sa,da saurin ta ta tashi zaune tana fad'in"wae malam ni kam lafiyar ka kaffa ka manta ba gwanar ka bace kake a gabanta ni d'in ce dai er qauye da ka tsana.
 Sosai saif yayi murmushi cike da so yana kallon ta yace"baki ji abunda Abba ya gaya min bane,ce min yayi na kula da ke kar na barki sbd bake kad'ai bace kinada buqatar kulawa keda babyna"
  Nan ya shafo cikinta.
 Ta ture hannun sa cikin dalla mai harara tace"haqqin Baffa se ya kama ka wlh idan baka gaya mai gaskiya ba nidai ba ruwana.
 Nan kawai ta kwanta had'e da juya mai baya.
  Saif da still murmushi na kan fuskar shi ya kwanta gab da ita ya rungumota yana fad'in"zan gaya mae amma se idan tare dake zamuje mu wargaza masa farin cikin sa tunda kinfi son haka....da sauri ta juyo tace"Baffa bai haifen ba amma na tabbatar na fika son farin cikin sa.
 Ta doka mai pillow snn ta sauka daga kan gadon taje kan sofa ta kwanta.
 Komai saif bai ce da ita ba still se mumurshi kawai da yayi snn ya rungume pillown da ta doke shi dashi ya hau baccin sa.
  Koda asuba tayi zarah se ganin kanta tayi kan bed rungume a jikin saif.
 A maimakon taji haushi se murmushi tayi tana kallon shi har ma ta sami kanta da d'aura hannun ta a sajen fuskar shi tana shafa shi a hankli har zuwa lips d'in sa,nn kawai ya bud'e idanun sa ta janye hannun ta da sauri ta tashi zata sauka daga kan gadon.
  Se jin tayi ya fizgo ta ta fad'a gabad'aya kan jikin  sa tana kallon sa ya kama lallausan hannun ta ya d'aura kan sajen fuskar shi yace"ni mijinki ne ki shafa ni duk inda kike so,kmr yanda nima zan iya shafa koina a jikinki.
  Da sauri ta ture hannun sa da yakai yana shafa mamanta snn ta qwace daga riqon da ya mata ta sauka kan gadon ta wuce zuwa bathroom,saif da ya bita da kallo yayi murmushi snn ya sauke numfashi a hankli ya tashi ya fita daga d'akin yaje d'akin sa yayi arwala ya wuce zuwa masallaci.

Tuni zarah ta jima da ida sallah ta tashi tana linke darduma,saif ya shigo d'akin yaje a natse ya kar6i dardumar da ke hannunta yasa a wardrobe snn ya kama hannun ta yace"muje Abba ne yazo yana son ganin mu"
Kallon sa tayi haka shima ya kalle ta basu ce komai ba dai har suka sauka downstairs a nn falo suka sami Abba zaune kan kujera.
  Zarah da sam ta manta saif riqe yake da hannun ta,sai da taga Abba na kallon hannayen nasu d'auke da murmushi snn hankalin ta ya bata tayi saurin zare hannun ta daga na saif snn ta durqusa har qasa cike da ladabi tana gaida Abba.
   Wanda d'auke da murmushin farin ciki ya amsa gaisuwar ta tare da kama hannun ta ya zaunar da ita akusa dashi snn ya dafa kanta yana fad'in"Allah yayi miki albarka zarah, ya kuma kare ki da dukkanin sharrin maqiya,haqiqa naji dad'in yanda nazo na same ki lfy,ba kmr yanda mafarki na ya nuna min ba,sosai na tsorata shiyasa nayi gaggawar rubuta miki wnn addu'ar,ya zaro wata farar takarda a cikin aljihun jallabiyar sa ya bata yace"ki riqa yinta duk dare idan zaki kwanta bacci da kuma bayan sllr asuba idan kin sallame sallah bayan kin gama addu'o'in ki se kiyi ta daga qarshe,kariya ce daga dukkanin sharrin mutum da aljan,nayi wani mafarki ne da ya bani tsoro amma inshaa Allah hakan bazai faru ba ki kwantar da hankalin ki kinji,sam kada kisa damuwa a ranki,ban fad'a miki ba sai dan ina so ki dage sosai kada kiyi wasa da addu'ar.
  A natse zarah ta gyad'a masa kai had'e da mishi godiya.
  Yace"ba komai jeki abin ki"
 Bayan ta wuce ne Abba ya sauke numfashi yana kallon saif dake gurfane a gaban shi,ya zaro wata takarda ya bashi yace"wnn ma wata addu'ar ce a rubuce,ta farkon ita ce zaka karantawa zarah bayan tayi bacci,ta biyun kuma hannun ka na dama zaka dafa cikin ta dashi se ka karanta addu'ar sau uku yayinda sautin addu'ar ke sauka a hankli kan cikin ta snn ka tofa kana mai shafe cikin nata gabad'aya,ina fatar ka fahimce ni?
   "Eh Abba saif"
 ya fad'a wanda yayi shiru yana kallon addu'oin da ke rubuce a kan takardar da ya kar6a daga hannun Abba.
  Nan Abba ya miqe yana fad'in"ni zan tafi,anjima da qarfe goma ka same ni a gida ina son zamuyi magana.
  Saif yace"ok to"snn ya tashi ya raka Abba har sai da Abba ya shiga mota ya wuce snn ya dawo ya tafi d'akin zarah ya same ta zaune kan bed still da hijab d'in sllr ta a jikin ta har qasa tana duba takardar da Abba ya bata.
  Be qarasa gurinta ba se kallon ta kawai ya tsaya yana yi,haka ita ma ta d'ago tana kallon shi,ba wanda yace da wani komai se juyawa yayi ya fita daga d'akin.
  Yau be bar driver ya kaita school ba shi da kansa ya kaita,ya dawo zuwa 10 ya tafi gida kmr yanda Abba ya buqata.
  Bayan sun zauna Abba yace da saif"saifuddeen tafiya zanyi zuwa abuja da akwai taron da zamuyi a can na manyan likitoci,ga wnn ya miqa masa wasu takardu snn yace"takardun kadodarin ka ne da na mallaka ma,ya miqa masa wasu yace"wnn kuma takardun asibiti na ne da na mallakawa abunda zarah zata haifa ina fatar Allah ya kawo shi duniya lafiya ya kuma kasance rayayye me albarka.
 Saif da duk jikin sa yayi sanyi ya kar6i takardun had'e da mishi godiya.
  Abba yace"ba komai kana iya ka tashi ka tafi.
 Nan saif ya tashi jiki ba qwari yana jin kmr ya koma ya gaya wa Abba cewa zarah bata da komai amma kuma ya Abba zai ji a yanda yasa ransa sosai d'in nn haka.
 Nan ya juya ya kalli Abba bai ce masa komai ba dai ya koma juyawa ya haura sama zuwa d'akin umma.
   Ya same ta zaune kan bed riqe da takardu a hannun ta itama.
  Yaje ya zauna a hankli kusa da ita ya kar6i takardun yana dubawa duk takardun kadarori ne suma wanda ya mallakawa umma,Nusaiba,yusra har ma da zarah ya bata wani gidan sa dake G.R.A.
  Bayan saif ya gama dubawa ya kalli umma yace"umma me yake faruwa ne duk Abba ya rabe mana komai nashi bana tunanin da akwai wani abun kirki da ya bari a hannun shi se dai ko kud'ad'en banki da ya bari kawai,ki duba fa asibitin sa gabad'aya da yafi ji da ita ya mallakawa abunda zarah zata haifa.
  Umma dake kallon sa ta numfasa tace"nima dai ban san me yasa yayi haka ba,amma ita zarah halan tana da ciki ne da gaske da har zai mallakawa abunda zata haifa gudan asibitin shi?
  Saif da duk ya samu kansa da jin nauyin umma ya sadda kansa qasa yace"a gaskiya umma ban ta6a kusantar zarah ba bare tayi ciki,kawai dai tun lokacinda tayi fama da mura har ta kwana a nn gidan,shine ya d'auka ko ciki ne da ita,ban san ta yaya zan fuskance sa in gaya masa gaskiya ba umma,gashi bana so yayi tasa rai a kan abunda babu daga qarshe yazo yaji haushina idan ya gano gaskiyar komai,bazan so haka ba umma ina tsoron 6acin randa Abba zai shiga.
  Duk yana mgnr ne cikin damuwa da macewar jiki.
 Umma dake kallon sa tace"nima dai har kullum ina son in gaya masa gaskiyar abunda na fahimta zarah bata da ciki amma ganin yanda yasa cikin sosai a ranshi da har kullum muka zauna mgnr cikin yake hkn yasa na rasa ma ta yaya zan gaya masa.
 Shiru saif yayi se ga Abba ya shigo d'akin d'auke da sallama a bakin shi yana fad'in"to ni zan tafi bana son 11 tayi bamu fara hanya ba"
 Nan suka fito suka rako shi a bakin mota,wanda har zai shiga mota se kuma ya tafi da saif jikin sa ya rungume shi a hankli yana fad'in Allah yayi maka albarka saif,haqiqa nayi matuqar farin ciki da kayi biyaya a gareni har ya kasance zarah tana d'auke da juna biyu,ina fatar Allah ya biya maka dukkanin buqatun ka na duniya dana lafira ya kuma baka 'ya'ya masu yin biyaya a gare ka,snn ya d'ago shi yana riqe da hannyen sa duka biyu a cikin nashi yana kallon sa yace"abu na qarshe da zan gaya ma saif,ko bayan raina ka rabu da zarah zanyi baqin ciki,burina kayi rayuwa da zarah rayuwa ta har abdah,ka riqe ta amana duk rintsi kar ka bar wani abu ya raba ku kaji.
  A sanyaye saif yace"Inshaa Allah Abba bazan rabu da zarah ba har abada.
 Wani irin dad'i Abba yaji a ranshi har yana qara sawa saif albarka.
  Jamil da ya d'an jima da zowa yana tsaye a gurin wata irin zufa ce duk ta lullu6e shi da jin zancen da Abba yayiwa saif da kuma jin irin amsar da saif ya bawa Abba,ya samu da qyar ya danne abunda yake ji ya d'an russuna cike da ladabi ya gaida umma da Abba.
  Jiki sanyaye umma ta amsa mishi dan haka kawai taji duk ta tsinke da lamarin Abba,wanda shi kam da fara'ar sa ya amsa gaisuwar jamil har yana tambayar sa mutanen gida,jamil yace"mishi suna lafiya"
 Yace"ka gayawa Abban naka nayi tafiya ban samu na kira shi ba se na dawo idan Allah yace"
  Yace"to Abba Allah ya kiyaye hanya"
  Abba yace"Amin"had'e da shiga mota"
  Alu driver yaja motar suka wuce.
 Sai da motar ta fita daga gate d'in gidan snn umma ta iya komawa daga ciki.
    Jamil kuwa kallon saif kawai yake ya kasa ce masa komai se juya wa yayi ya bar gidan d'auke da zazza6in da yaji ya kama shi lokaci d'aya.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Sunday 25/03/2018_
*«»«»«»SAIFUDDEEN!«»«»«»*





By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«»43,44,45*
 Kallo kawai saif ya bisa dashi be tsaida shi ba se juyawa yayi ya koma daga ciki ya d'auko takardun sa kawai ya fito ya shiga mota tare da bud'e drawar motar ya saka takardun a ciki ya rufe.
  Snn yaja motar ya tafi se asibiti bai sami jamil a can ba,hakan yasa ya bar asibitin yaje gidan su jamil d'in.
  Wanda kai tsaye 6angaren sa ya nufa.
 Koda ya shiga d'akin nasa ya same   shi lullu6e da blanket qudundune se kakarwa yake kmr me jin sanyi.
  Da sauri saif ya qarasa gurin sa ya yaye blanket d'in yana fad'in"what happen jamil?
  A hankli jamil ya tashi zaune lokaci d'aya idanuwan sa duk sunyi jajur ya dafe kansa dake masa masifar ciwo,muryar sa da qyar yace"sorry maganar bazata yiyu ba yanzun kaina yana min ciwo sosai kuma ina jin zazza6i,ko anjima ne idan naji sauqi zan same ka a gida mu tattauna maganar akan clinic d'in mu ne dama.
  Saif da ya fahimci dalilin zazza6in nasa yayi shiru yana kallon sa,can ya tashi ya d'auko masa magani da ruwa ya bashi yasha,snn ya taimaka masa ya koma ya kwanta yasa blanket ya rufa masa jikin sa tare da fad'in"Allah  sauwaqe"
   Daga haka ya fita tunani fal a ranshi,wanda gabad'aya haka ya kasance asibiti jikin sa ba qwari se bayan yayi waya da Abba ne yaji cewa sun sauka lafiya snn ya rage jin abunda yake ji.
Da su zarah suka gama lectures yaje ya d'auko ta suka dawo gida.
 Koda tayi wanka ta shirya ta fito zata je kitchen ta sami saif shima yayi wanka sanye cikin qananun kaya na shan isa yana kwance rigingine kan doguwar kujera 3seater idanuwan sa a lumshe kmr me yin bacci ya kara d'ayan hannun sa a goshin sa,snn ya d'aura d'ayar qafar sa kan d'aya.
  Ta kalle sa kawai ta wuce zuwa kitchen wacce har ta gama girka abunda zata girka ta fito still yana nn yanda ta bar shi,hakan yasa ta qarasa a hankli inda yake ta ajiye plate d'in abincin kan rug itama ta zauna kan rug d'in,ta jingina gefen jikinta a jikin kujerar da yake kwance snn ta kama hannun sa a hankali dake ajiye kan cikin sa.
 Nan saif ya bud'e idanun sa ya tashi a natse tare da kama hannun ta ya zaunar da ita a kusa dashi yana kallon ta da kulawa muryar sa a hankli yace"ya akayi ne zarah?
 Zarah dake kallon sa muryar ta can qasa a hankli tace"ba komai kawai naga tun lokacinda na fito zanje kitchen na ganka a kwance har naje na kammala abunda nake na fito baka tashi ba,baka jin dad'i ne?
  Girgiza mata kai kawai yayi alamar a'a lafiyar shi qalau.
  Ta zuba mishi ido tayi shiru tana kallon shi sbd a lokacinda ta kama hannun sa taji jikin nasa da zafi kmr baya jin dad'i.
  Saif kuwa dashi kansa bai san abunda ke damun sa ba,ya kalli abincin da ta ajiye kan rug snn ya maida duban sa gare ta yace"da yawa kikayi abincin in zauna muci yunwa nake ji"
 Gyad'a masa kai tayi snn tace"eh da akwai wani a kitchen na zuba a kula.
  Nan saif ya zame daga kan kujera ya zauna kan rug tare da lanqwashe qafafu yana kallon abincin jallof rice ce da taji kayan lambu da qoda tayi kyau sosai se qamshi ke tashi dan zarah duk da rayuwar qauye tayi amma a gidan su lafiyayyen girki suke sbd duk wata umma se ta aika musu kayan abinci dama duk wani abunda zasu buqata,wacce tunda sukayi aure da Abba shine ke bata isasshin kud'in da zata samu ta yiwa en uwan ta hidima.
  Saif beci abincin ba se kallon sa yake tayi cike da sha'awa har sai da zarah taje kitchen ta d'auko wani spoon da abincin da tace ta zuba a kula ta kawo ta ajiye dan wanda ke cikin plate d'in na mutum d'aya ne bazai ishe su ba,byn ta d'auko musu ruwa da lemu a fridge snn ta zauna suka hau cin abincin.

 8:30pm tuni zarah tayi sallar isha'i har ta tu6e tana d'aure da towel zata shiga wanka se ga saif ya shigo d'akin d'auke da sallama a bakin shi,fasa shiga bathroom tayi ta juyo had'e da amsa mishi sallama tana me kallon takardun da ke hannun sa har ya qaraso gurinta ya kama hannun ta ya tafi da ita kan sofa suka zauna,ya bata takardun yana kallon ta a natse yace"takardun asibitin Abba ne da ya mallakawa abunda zaki haifa".
  Da sauri zarah ta kalle shi muryar ta na rawa tace"ba dai wnn hadaddiyar asibitin da kaje dani yau ba"
  Cikin lumshe ido ya gyad'a mata kai alamar eh.
   Da sauri ta girgiza kanta qwallah tap a idon ta tace"A'a dan Allah kaje ka gaya wa Abba gaskiya,kar mu barshi yana tunanin  abunda bashi bane,byn kuma rabuwa zamuyi kaga ya zama cutuwa.
   Saif dake kallonta a hankli ya kama kumatun ta yana kallon ta muryar sa a natse yace"zarah still kina nufin kina kan bakar mu rabu,ba kya so mu faranta mishi,tunanin sa ya zamo gaskiya?
 Shiru zarah tayi tana kallon shi sosai tana son su farantawa Abba amma bata jin zata iya rayuwa da saif dmn ta tabbata baqin ciki ne kawai zai kashe ta kan en matan da yake kawowa,da ta rasa meyasa yanzun abun ke baqanta mata rai sosai ba  kmr farko ba da ko kad'an abun be dame ta ba,nn ta kauda fuskar ta gefe tare da share hawayen da suka gangaro kan fuskar ta.
Saif ya juyo da fuskar ta,yana kallonta idanun sa kmr zasu ciko da qwallah yace"kar kice a'a zarah kiyi tunani kinji.
  Daga haka ya tashi ya barta riqe da takardun a hannunta.
   Tana riqe dasu ta tashi jiki sanyaye taje kan bedside drawer ta d'auki wayar ta ta kira umma.
  Umma na d'aga wayar,cikin muryar kuka zarah tace"inna kinji abunda baffa yayi"
  Naji zarah byn wnn ma har wani gidan sa dake G.R.A ya baki kyauta,se ki kirasa ki masa godiya.
  Bud'e ido zarah tayi had'e da dafe qirjinta tace"na shiga uku ya bani gida inna...se kuma cikin sauri ta girgiza kanta tace"A'a inna a mayar masa wlh ban can canta ba,kuma ni bani da wani ciki da yake tunani ki gaya masa dan Allah inna kar a cutar dashi akan tunanin abunda ba haka bane.
  Duk tana maganar ne kmr wacce ta rud'e.
  Umma tayi shiru can tace"naji zan gaya masa amma ki kirasa ki masa godiya"
  "To"
Zarah ta fad'a jikinta duk a sa6ule.
  Wacce bayan sun tsinke wayar tayi shiru cike da tunani fal a ranta.
 Har washe gari duk jikin nata ba qwari komai a sanyaye take yin shi.
  Suna tafe cikin mota saif zai kaita school se yi yake yana kallon ta,can ya riqo hannunta ta kalle sa a natse,yace kin kira Abba kin masa godiya?
  Gyad'a masa kai tayi alamar eh snn muryar ta a hankli tace"yaushe zai dawo?
   Cikin kafe ta da ido saif yace"gobe zai dawo,kina son zamuje mu gaya masa gaskiya ne idan ya dawo.
   A hnkli ta girgiza masa kai snn tace"na tambaya ne kawai"
 Nan ya sauke numfashi yana kallon ta kmr me son cewa wani abu sai kuma yayi shiru,ya maida hankali gun tuqin da yake,byn ya sauke ta school ya dawo by 10 ya tafi gidan su jamil ya dubo shi snn ya wuce Hospital cike da tunani a ranshi,dan ba wasa ba zazza6i  jamil keyi,wanda shi yanzu kam ba abunda yafi so irin ya farantawa Abba rai baisan ya zai yi da alqawarin jamil dake kanshi ba,gashi of course yasan dalilin zazza6in nashi.
 kamar dai jiya haka ya kasance asibiti ba wani aikin kirki  da ya iya yayi,har lokacin d'auko zarah yayi ya tafi school d'in su,ya fito mota knn ya ganta tazo da saurin ta ta fad'a jikin sa ta saki kuka a hankli.
 Take damuwa ta bayyana a fuskar shi ya d'ago ta yana fad'in"zarah lafiya me ya faru?
  Komai bata iya ce masa ba se kama hannun sa tayi suka tafi har inda aka laqa musu C.A ta nuna masa course d'in mugun malamin nn ne aka liqa musu sam bata ci wani abun kirki ba,saif da ta nunawa ya sauke numfashi snn yace"kar ki damu idan kika dage a exam inshaa Allah zakiyi passing kinji,zarah dake kallon sa a sanyaye tace"amma da qyar ko?
  Yace"A'a inshaa Allah baza ki fad'i ba zaki wuce"
 Tace"ni ba wucewa kad'ai nake so nayi ba so nake naci abun qwarai yanzu ace duk yanda na wahala a karatun 12 kawai naci amma wlh....se kuma tayi shiru tana tuna lokacin ne fa da wnn abun kunyar ya same ta kwata kwata a lokacin haka haka take jin kanta ba lallai bane ko ta rubuta abun kirki a test d'in.
  Saif dake kallonta a hankli ya janyo ta jikin sa yace"amma me,ae tunda course d'in naku micro biology ne baki da matsala ina tare dake tare ma zamuyi karatun exam na nuna miki komai yanda zakiji sauqin karatu kinji,ko kina so muje mu sami malamin na mishi magana?
  Da sauri tace"um um ban so ni nafi so naci akan kaina had'e da taimakon ubangiji.
  Murmushi saif yayi tare da lakato hancinta yace"Gud gal kin san me kk yi knn".
 Zarah ta sakar mishi murmushi ya kama hannunta suka wuce,mutanen gurin masu duba C.A suma se kallon su suke ko ba a fad'a ba sun san miji da mata ne ko dan yanayin soyayyar su kad'ai dasu basu ma san suna yi ba.
 Koda suka isa gurin da saif ya ajiye motar shi,suka samu wani ya faka  motar shi knn ya fito ze wuce,yana ganin zarah ya kasa zuwa koina ya tsaya se kallonta yake tayi,har suka shiga mota saif ya kalle ta fuskar sa a d'aure yace"d'an iskan ina ne wancan da ya tsaya yana ta kallon ki haka?
  Ta6e baki tayi tace"wae so na fa yake shine....what!
Saif ya fad'a da sauri ze bud'e motar ya fita.
  Zarah tayi saurin riqe shi tace"ba student bane malami ne fa,rae 6ace cikin d'aga murya yace"ko uban malamin ne fa!se na koya mai hankali d'an iska shi baisan matar aure bace ke.
  Nan ya fizge hannun sa daga riqon da zarah ta mishi ya bud'e ganbu zarah ta koma riqo shi tana fad'in"ka tsaya mana ka saurare ni tuni na gaya masa cewa ni matar aure ce kuma tun daga rnr be sake min magana ba.
  To uban me zai sa ya tsaya yana kallon ki bayan kin gaya mai haka.
 Tace"nima ban sani ba amma dan Allah kar ka ce masa komai malamin yana da kirki sosai"
  Wani irin kallo ya mata bai ce komai ba dai se rufe ganbun motar yayi da qarfi yaja motar a fusace tare da bankad'awa malamin qura suka wuce.
 Zarah kam se kallon sa take tayi tana mamakin meyasa ransa ya 6aci da yawa haka.
  Saif dake ta faman sharara gudu da mota ya kalle ta fuskar sa a d'aure yace"kallon fa?
   Ta kalle sa kawai snn a hankli ta kauda fuskar ta gefe har suka isa gida bata sake kallon shi ba.
  Haka shima dan duk haushin ta yake ji.
Suna shiga ciki kowannen su ya nufi d'akin sa.
 Saif yayi wankan juma'a ya shirya cikin fararen kayan sa ya fita,be dawo gidan ba se qarfe uku,yana shigowa a nn falo ya kwanta kan 3seater ya lumshe idanun sa kmr me jin bacci,can qamshin turaren zarah yasa ya bud'e idanun sa yana kallonta ta wuce gun dining d'as da ita tayi kyau sosai cikin shirin ta na atamfa super Holland,wacce tuni ta kammala musu abinci,shi kad'ai take jiran ya dawo. Ta zubo musu abincin a plate,da ruwa da lemu duk ta ajiye snn ta zauna a nn kan rug tana kallon sa tace"tashi muci abinci"
 Fuska d'aure Saif ya kalle ta kafin yake d'auke idon sa a kanta yace kici kawai bana ci"
 Muryar ta a sanyaye tace"meyasa da kaifa na dafa kuma tun d'azu kai kad'ai nake jiran ka dawo muci.
 K'ara d'aure fuskar sa yayi ya tashi yana kallon ta yace"har tambaya kike,mtsw wacce bata san darajar aure ba kawai,daga yau ina gaya miki wlh kar ki sake yabon wani da aure na a kanki ki bari idan na kwance igiyar auren duk uban da zaki yaba ke kika sani."
 Da haka ya tashi ransa a 6ace ya bar gurin.
  Zarah ta bisa da kallo idanun ta tap da kwallah snn ta tashi jikin ta duk a sanyaye taje ta rage abincin.
   Ta tafi d'akinta tayi zaune kan rug tana ci ba dan tana jin dad'in cin abincin ba se don yunwar da take ji,dan ko dad'in abincin ma ta kasa ganewa she is just eating.
 Washe gari da safe har ta shiga bathroom ta cire towel zata fara wanka se kuma ta fito da saurin ta zata d'auki ribbon ta d'aure gashin kanta da yake sake bata son ruwa ya ta6a shi,kawai taga saif gashi pant ne kad'ai a jikinta,ae kuwa ta fasa ihu snn da sauri tasa hannuwan ta duka biyu ta rufe qirjinta zata juya,bai barta ba ya riqo ta,hannun sa kan waist d'inta ya matso ta sosai zuwa jikinsa yana kallon ta idanunta tap da qwalla ta ture hannun sa tace"ni ka rabu dani ba fushi kake yi dani ba"
  Da sauri saif yasa hannu ya share mata hawayen da suka sauko kan kumatun ta yace"sorry na daina muje na taya ki wankan.
  Zarah dake rungume da qirjinta ta maqale kafad'a awa wata qaramar yarinya tace"ban so".
  Saif yayi murmushi cike da sha'awar shagwa6ar ta yana kallon ta ya d'an sha toka yace"kina so naci gaba da yin fushi da ke ne?
  Ta kalle sa tare da saurin girgiza masa kai.
 Yace"to yi haquri muje na taya ki wankan"
  Bata musa masa ba tana kallo ya d'auke ta cak ya tafi da ita bathroom.
  Jim kad'an ya fito ya d'aukar mata ribbon d'inta wanda hakan nn ya koma bathroom ba kaya a jikin sa duk ya cire,zarah dake cikin bathtub tana ganin sa da saurin ta tasa tafukan hannayen ta ta rufe fuskar ta,saif yayi murmushi kawai ya shiga bahon wankan da duk ruwan kunfa ne ba'a ganin jikin mutum in ya shiga.
  Cike da so ya janyo zarah jikin sa yasa ribbon ya d'aure mata gashin kanta ya had'a da jelar duk ya dunqule daga haka suka shiga yin kansu.
 Can bayan sun gama wanka Zarah ta samu da qyar ta qwato kanta daga hannun saif da ya hana su fitowa se romcing d'inta yake yana neman fita hayyacin sa,ya biyo ta gadan gadan,ta hau kan bed tana masa dariya riqe da towel a hannun ta zata rufa jikinta be barta ba se qwace towel d'in yayi ya jefar ya kada ita kwance ya mata rumfa tare da had'e bakin sa da nata,snn can ya shiga kissing d'in jikinta ta koina,cikin wani irin salo mai wuyar fassarawa,take zarah ta fara fita hayyacin ta dan yakai ga6ar da ko ita waye dole se ta russuna ta bada kai,dan kuwa sosai itama ta biye mishi suka hau romancing d'in juna tamkar zasu cinye kansu,d'akin yayi tsit baka jin qarar komai se sautin numfashin su dake fita a hankli,da dukkan su burin su suje ga babban aiki,inda saif a hankali ya fara shigar zarah se kuma ya tsaya be tafi ba,yana kallon yanda duk tabi ta rirriqe shi tana sauke wani irin numfashi mai cike da tsoro,kana ta sauke ajiyar zuciya a hankli ta janye jikinta ta tafi can gefe ta kwanta ruf da ciki zata ja blanket ta rufa jikinta se jin saif tayi ya kwanta kan jikinta yana shafa jikinta a hankali bakin sa saitin kunnen ta snn cikin wata irin murya can qasa mai cike da buqatuwa yace"No zarah is enough kar ki ce wnn karon ma bazan sami dama ba,ki taimaka min dan Allah na samarwa Abba farin cikin sa bazan miki da zafi ba kinji"
  Komai zarah kasa ce masa tayi se lumshe ido tayi tana sauraren yanda yake ta shafa jikinta yana ci gaba da begging d'inta.
 Tayi shiru kawai har ya gaji dan kansa ya tashi ransa a 6ace zai sauka daka kan gadon,tayi saurin tashi ta riqo hannun sa,ya fizge hannun nasa ya kwashi tufafin sa ya fita daga d'akin.
  A kasale ta bisa da kallo cike da buqatuwa,snn jiki sa6ule ta koma ta kwanta se yawo take da hannunta a hankli kan jikin bed d'in tana tunanin yanda zata je ta shawo kanshi.
  Can bayan ta jima kwance a gurin ta tashi ta nemi towel d'inta ta d'aura taje d'akin sa se knocking take ba alamar zai bud'e,tasan yana jinta fushin da yake yi da ita ne yasa ya share ta,hakan yasa kae tsaye ta mird'a handle d'in ganbun qofar ta shiga.
  A rud'e taja baya da sauri cikin bud'e ido tana kallon en matan da ke kan saif su biyu kowacce da irin salon da take mishi,gabad'ayan su sun fita hayyacin su musamman saif da ya kami d'ayar yana qoqarin afka mata,nan kawai zarah ta saki wata irin qara had'e da fashewa da kuka snn ta fita aguje daga d'akin.
  Ba shiri saif ya tunkud'e en matan da ke gaban shi ya d'auki guntun wandon shi ya saka snn ya bita.
Tana shiga d'akin kae tsaye gun dressing mirror ta nufa duk ta watse kayan da ke jere akai take abubuwan fashewa suka faffashe.
 Dai dai saif ya shigo d'akin ya tafi da sauri ze qarasa inda take cike da son ya rarrashe ta,ta nuna shi muryar ta sosai cikin 6acin rai tace"wlh kar ka kuskura ka matso inda nake!
 Ba musu ya tsaya cak yana kallonta yace"naji bazan qaraso gurin ki ba,amma ae kinsan laifin ki ne zarah duk abubuwan nn da suke faruwa sha'awar ki ce take hana min sukuni,har yasa bayan na daina kula su,na dawo kuma naci gaba da kula su,sbd ke duk yanda naso sam ba kya bari ya kk so nayi.
 Ba wani ae dama can halin ka ne,dan haka wlh ni na gaji ka rubuta min saki na ka bani.
 Cikin kwantar da murya yace"No zarah kiyi haquri daga yau bazan sake kula su ba nayi miki alqawari"
  Ni ba wani dad'in baki da zaka min, me hali ae bazai ta6a canza halin shi ba,kawai ni ka sake ni dmn bazan ta6a iya rayuwa da qazamin namiji irin ka me neman mata ba.
 Duk tana mgnr ne cikin kuka.
 Saif yace"No zarah abunda kk tunani bashi bane wasa kawai nakeyi dasu fa ban ta6a kusantar ko d'ayar su ba wlh,yauma da na tashi aikatawa kin kaini qololuwa ne..nima ka kaini qololuwa na gaji da ganin haramun da baqin ciki dan Allah ka sake ni in huta!
  Nan ta ciro takarda a cikin littafan ta na school ta kawo mishi had'e da biro,be kar6a ba se hard'e hannayen sa yayi a qirjinsa yana kallonta yace"da wace hujjar zan sake ki ko kin manta yanda mukayi dake.
  Zarah da ranta ya qara 6aci tace"hujja har kana tambaya,rayuwar gidan ka da nayi cikin qunci da  muzguna min da kake snn kullum cikin kawo karuwai su ba hujja bane,kaga malam tun muna mu biyu ka rubuta min saki na ko kuma na kira Baffa na gaya mae komai wlh.
  Yace"Kin dad'e baki kira shi kin gaya masa ba idan ma baki da kati akwai a wayana.
 Ya saki shu'umin murmushi.
Zarah dake kallon sa duk haushi ya qara cikata ta fasa wani sabon kuka ta jefar da biro da takarda,ta nufi bedside drawer ta d'auki wayar ta zata kira Abba,saif da ya bita da kallo a fusace yaje ya fizge wayar yayi jifa da ita lokaci d'aya duk ta tarwatse,ya nuna ta yace"wlh ya isa is enough!na rabu da Abbana cikin farin ciki har yana samun albarka,kinyi kad'an kice zaki lalata min,saki ne zan baki yanzu amma ki sani akan ki komai zai koma dmn baza ki ta6a nasarar sake had'a ni dashi ba,kinyi na farko to baza kiyi na biyu ba wlh.
  Daga haka yaje ya d'auki biro da takarda ya rubuta mata saki d'aya,snn  ransa a 6ace yaje zai bata,se kuma yayi tsaye shiru yana kallon takardar qwallah tap a idon sa yana jin bazai iya bata ba,gwanda kawai yaje ya samu ya rarrashe ta har ta haqura,nn ya dunqule takardar ya jefar.
  Ya nufi gun zarah da ta zube qasa sai kuka take tana kallon wayar ta da ya tarwatse,ya kama ta a hankali ya tafi da ita jikin sa ya rungume ta se rarrashin ta yake yana bata haquri.
  Zarah bata qwace kanta ba se kuka taci gaba dayi a jikinsa,ya tafi da ita kan bed suka zauna se shafa bayan ta yake a hankali yana fad'in"ya isa haka kinji yi haquri zan saya miki wata wayar na kuma yi miki alqawarin bazan sake kula wa en nn en matan ba koda kuwa sha'awar ki zata kashe ni.
  Nan zarah ta sassauta kukan da take har tayi shiru tana yawo da hannunta a hankali kan faffad'an qirjinsa,muryar ta a hankli can ciki tace"na amince ma kayi duk abunda kake so da jikina dmn bazan so ka mutu a dalili na ba,ba kuma zan so a dalilina kaci gaba da aikata zunubi ba,amm zan so mu maida tunanin baffa ya zamo gaskiya.
  Wani dad'i saif yaji a ranshi wanda a natse yakai lips d'in sa kan goshin ta ya d'aura mata kiss,zarah ta lumshe idanun ta a hankali tare da qara lafewa a jikin sa.
  Ringing d'in wayar sa ne yasa ta bud'e idanunta tana kallon shi,bai ga wayar ba sai nemanta yake dan tun zuwan farkon shi d'akin ne yazo da ita,can bayan sun d'auke blanket suka ganta har kiran ya tsinke se kuma aka sake kira.
  Abban kd ne mai kiran hakan yasa cike da ladabi ya d'aga kiran.
  Bayan ya ida wayar ya kalli zarah dake zaune kan bed yace"tashi ki shirya gida za muje Abban kd ne yazo yace yana son ganin mu yanzu"
  Nan ba musu zarah ta tashi ta nufi wardrobe,shi kuma ya tashi ya tafi d'akin sa,ya sallami en matan sa suka wuce snn ya shirya suka fito.

Suna tafe cikin mota shiru ba mai cewa komai har suka isa,koda suka fito motar duk hankalin su a tashe suna kallon d'inbin taron da ke qofar gidan da suka rasa na mene ne,kawai dai suna ganin taron suka samu kansu da jin fad'uwar gaba,snn yanayin taron kad'ai ya nuna cewa rasuwa ce dan dukkanin su sunyi zugum cike da jimami.
  Sannan koda suka qarasa zasu shiga falo se jin kukan mutane suke ba sauqi,hakan yasa saif yaji qafafun sa na neman kasa d'aukar shi,zuciyar sa ta shiga halbawa da sauri sauri hannun sa na rawa ya riqo hannun zarah,ta kalle shi jikin ta duk a sanyaye qwalla na neman cika mata ido duk da bata san ma waye ya rasu ba.
  Wa enda suna shiga falon hankalin su yayi matuqar qara tashi,ganin gawa ajiye a tsakar falon rufe da farin qyalle duk jini,ga su umma,Hajiya, Nusaiba,yusra,se kuka suke tayi ba mai kama wani,Abban Kd ne ya d'an fisu dama amma shima ya sadda kansa qasa se kukan zucci yake da yafi na fili ciwo.
  Cikin tsakanin tashin hankli saif ya gurfana a gaban gawar tare da zarah da yake riqe da hannunta,ya saki hannun nata jikin sa na wani irin rawa ya bud'e fuskar gawar da qyar.
   Kmr shed'ar sa zata d'auke yace"Inalillahi wa inna ilaihi raji'un!
Se kawai ya fasa wani irin kuka me tsuma zuciya ya fad'a jikin gawar yana jijjiga ta yana kiran sunan Abba.
zarah dake kallon fuskar Abba yau gashi kwance ba rai hawaye ne suka fito aguje kan kumatun ta,ta fashe da kuka snn ta tafi da gudu ta fad'a jikin umma wacce itama nn wani sabon kuka ya qwace mata ta had'a su su duka uku,Nusaiba,zarah yusra,duk ta rungume su se kuka suke tayi.
[4/22, 12:43 AM] Paexer: _Tuesday 27/03/2018_
*«»«»«»SAIFUDDEEN!«»«»«»*





By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«»46*
Sosai Abban kd ya shiga basu magana,har ya samu suka d'an sassauta kukan da suke snn a kafaice ya share hawayen da suka zubo mishi dan kuwa saif still yana rungume da gawar Abba se kuka  yake sosai bai daina ba,yaje ya samu da qyar ya 6an6are shi daga jikin gawar,ya rungume shi a jikin sa yana ta rarrashin sa yana bashi magana.
   Daga haka akayiwa Abba komai da akeyiwa mamaci aka kaishi makwancin sa.
  Ae kuwa kuka ya dawo musu sabo yayinda shi kuma aka baro shi can shi kad'ai a cikin kabarin sa,Allah sarki mutuwa knn Allah yaji qanka Abba,duk burin sa na son ganin en jikokin sa ashe bazai samu gani ba mutuwa knn mai yankan qauna,kana naka Allah na nashi,dmn kuwa duk burin uwa na son ganin abunda ta haifa tana ji zata haifu amma se Allah ya kar6i ranta ba tare da taga abunda ta haifa d'in ba,Allah knn mai iko kuma sarkin saraku nan da babu kamar shi.
  Bayan kwana uku da rasuwar Abba ne,zarah na zaune a d'akin su Nusaiba ta ida sllr isha'i,qur'ani a hannun ta tana karantawa a hankli cikin ranta,su Nadiya da dije ma sllr suka ida,suna zaune kan dardumar da suka ida sallah kowaccen su zugum shiru cazbi a hannun su suna ja.
  Nusaiba kuwa da alama ta riga su ida sllr tana kwance ruf da ciki kan bed sanye da qaton hijab me kai mata har qasa,wayar ta riqe a hannun ta se kallon futunan su take da sukayi da Abba,hawaye na faman zarya a idon ta.
 Umman kd ce ta shigo d'akin ta zauna a hankli kusa da ita tana kallonta tace"Ajiye wayar nn haka Nusaiba addu'a ya kama ta ki masa ba ki zauna kina ta kallon hoton shi kina kuka ba yi haquri tashi daina kuka kinji.
 Cikin kuka Nusaiba ta taso tazo jikinta tana fad'in"umma na kasa yarda Abba ya rasu a kullum gani nake kmr ze dawo.
 Ta qarashe mgnr sosai cikin kuka tana kallon hoton Abba dake jikin wayar ta yana murmushi kmr ya motsa yayi magana.
  Umma ta kar6i wayar snn ta share mata hawaye cikin muryar rarrashi tace"ya isa haka daina kuka je ma'aruf yana falo zasu koma kd ne"
  Nan Nusaiba ta tashi jiki sanyaye ta fita daga d'akin.
 Kafin umman kd ke cewa da zarah"idan kin kai aya zarah kije jamil yana a waje yana kiranki.
   Ba musu zarah nakai aya ta rufe qur'ani ta ajiye a hankli kan darduma snn ta fita.
  Koda ta sauka downstairs ta sami Nusaiba tasa ma'aruf a gaba tana mishi kuka shi kuma yayi shiru se kallonta kawai yake cike da jin tausayin ta ya kasa ce mata komai,sbd ko ya rarrashe ta ba shiru zatayi ba dmn tun da Abba ya rasu haka take bata awa1 bata fasa wani sabon kuka ba kuma in ta fara se ta gaji dan kanta snn take yin shiru.
  Zarah dake kallonta qwalla ne taji sun ciko mata ido tayi saurin fita daga falon taje ta sami jamil a waje,suka gaisa har yana mata ya qarin haquri,tace"mun gode Allah,snn a natse yace"saif ne dama still har yau bai ci komai ba ruwan drip ne kawai da na d'aura mishi ke amfani a jikin shi nayi nayi dashi ko ruwan Lipton ne yasha amma yaqi.
  "Za'a gayawa umma ne?
Zarah ta tambaya a sanyaye tana mai kallon shi.
 Yace"A'a zaki je ki duba shi ne ki samu ko kad'an ne yaci abinci dmn idan ya sake kwana baici komai ba zazza6in zai qara masa yawa"
  Tace"to bari naje na d'ebo masa abinci"
Yace"Aa ankai mana abinci yanzun,jeki kawai ki d'ibar masa a can.
  Tace"to snn ta wuce zuwa 6angaren saif Jamil ya bita da kallo har sai da ya daina ganin ta,snn ya d'auki motar sa ya fita daga gidan.
 Zarah kuwa tana isa 6angaren saif a hankli ta bud'e qofa ta shiga had'e da sallama a bakin ta.
 Taje ta zauna kan bed kusa da saif dake kwance idanuwan sa a rufe kmr meyin bacci da ko shigowar ta ma bai ji ba,sai da ta d'aura tafin hannun ta a hankli kan goshin sa ne snn ya bud'e idanun sa yana kallonta.
 Ya kira sunan ta a hnkli cikin muryar sa can ciki da bata ko fita sosai,snn ya yunqura zai tashi ta taimaka mishi ya tashi zaune,ya d'aura kan sa a kafad'ar ta,hannun sa kan waist d'inta ya zagayo dashi kan cikinta yana shafa cikin nata cikin muryar kuka yace"zarah Abba ya tafi ba tare da mun samar masa farin cikin sa ba"
   Shiru zarah tayi bata iya ce masa komai ba se hawaye da suka silalo a hankli kan kumatun ta,ta share hawayen snn ta kalli saif da shima hawayen ne suka silalo kan kumatun sa tasa lallausan hannun ta ta share mishi,snn ta kama kumatun sa tana kallon sa muryar ta a hankli tace"jikin ka yayi zafi sosai dan Allah kayi haquri kaci abinci kaji"
  Komawa yayi kan kafad'ar ta ya kwanta yana fad'in"i cnt eat zarah bazan iya cin komai ba"
 Um um kayi haquri dan Allah zaka iya.
Nan ta janye shi a hankli kan kafad'ar ta ya koma ya kwanta zata tashi ta d'ibar masa abinci ya riqo hannun ta yace"no zarah bazan iya ci ba fa ko kin d'ibar min is just wasted. 
  Zarah dake kallon sa cikin damuwa ta shafo cikin sa tace"kwanan ka uku baka ci komai ba fa,gaskiya yau in baka ci ba zanyi kuka"
  Saif dake kallonta hawaye ya gani kuwa har sun cika mata ido.
  Ya girgiza kansa alamar kar tayi kukan zaici.
  Da taimakon ta ya tashi zaune,dan ba wani qarfi a jikin sa,har sai da ma tasa masa pillow ya jingina bayan sa.
  Da akwai ruwan Lipton a mug ta tsiyaya mishi a cup ta bashi yasha kmr yanda ya buqata snn ta d'ibar mishi abinci d'an dai dai da tasan ze iya cinyewa,ta shiga bashi abincin da kanta har sai da yace ya ishe shi snn ta ajiye,ta bashi ruwa yasha snn tasa tissue ta share masa bakin sa.
  Ta miqe tsaye da niyyar zata gyara masa pillow ya kwanta,yace"Aa zanyi wanka ne je bathroom ki had'a min ruwa"
  Nan zarah ta cire hijab d'in jikinta ta ajiye sbd babba ne har qasa baza ta ji dad'in shiga bathroom dashi ba.
 Bayan ta wuce yakai hannun sa a hankli ya cire drip d'inda aka d'aura mishi snn ya cire kayan jikin sa ya bar d'an guntun wando kawai a jikin sa ya tafi bathroom,nn zarah ta fito ta bashi guri dan har ta gama had'a mishi ruwan se kayan bacci ta fidda mishi snn ta maida hijab d'in ta a jikin ta da niyyar zata tafi se kuma tayi zaune kan bed tana jiran fitowar shi gudun kar se ta tafi da akwai abunda yake buqata kuma.
  Se 10 jamil ya dawo gidan sbd a nn yake kwana tun lokacinda akayi rasuwar shine ke kula da saif.
  A mamakin sa koda yazo d'akin saif se ganin zarah yayi a d'akin ashe bata tafi ba,tana kwance kan faffad'an qirjin saif ya rungume ta suna bacci abinsu,da alama baccin ya kwashe su ne basu sani ba dan still zarah na sanye da qaton hijab d'inta mai hannu da ya rufe mata jikin ta gabad'aya se en kyawawan qafafuwan ta dake waje kawai.
  Jamil dake kallon su a hankli ya juya ze fita daga d'akin se jin yayi saif ya kira sunan shi cikin muryar bacci.
  Sai da jamil ya share en guntayen hawayen da suka fito mishi,snn ya juya yana kallon yanda saif ke shafa bayan zarah a hankli yana kiran sunan ta,ta tashi a natse tare da sauke idanun ta akan agogon bangon d'akin ta bud'e ido cikin mamaki tana kallon saif tace"qarfe goma har da en mintina yaushe mukayi bacci har haka,nn kawai bata jira me saif zai ce ba ta tashi da sauri tana fad'in"zan tafi sai da safe.
  Kallo kawai Saif ya bita da dashi,ita kuma ganin jamil yasa ta sadda kanta qasa cikin jin kunya ta fita,jamil ya kalli saif da ya gyara kwanciyar sa ze ci gaba da bacci yace"baza ka iya raka ta bane dare fa yayi ba kowa a harabar gidan nn zata iya jin tsoro.
  A hankali saif ya lalla6a ya tashi ya fita,jamil ya bisa da kallo qwallah tap a idon sa,har suna qoqarin zubowa bai bar hawayen sun zubo ba ya samu da qyar ya had'iye kukan da yake ya tafi bathroom dmn watsa ruwa.
 Saif kuwa koda ya fita ya samu zarah se sauri take har tayi nisa.
  Ya kirata ta tsaya ya qarasa gurinta tare da kama hannun ta yana kallon ta yace muje na rakaki ko"
  Duk da tasan jikin nasa bai yi wani qarfi ba bata musa mishi ba dan tsoro take ji shiyasa ma take ta sauri.
  Har qofar falo yakai ta se bayan ta shiga snn ya koma.
 Umma na zaune a falon kan kujera  riqe da qaton photon su dake manne a falon ta ciro tana kallo,su duka ne gabad'aya,ita da Abba,saif,Nusaiba da yusra dukkan su suna murmushi amma fuskar Abba kawai take kallo qwalla tap a idonta,har ma hawayen suka soma saukowa a hankli,jin motsi yasa tayi saurin share hawayen,snn ta ajiye photon a can d'ayar kujera ta juyar da fuskar photon.
  Snn ta miqe tsaye tana mai kallon zarah da ta shigo, muryar ta a hankali mai cike da damuwar rasuwar Abba tace"zarah a ina kika fito yanzun qarfe goma fa har da mintina"
  Zarah bata iya ce mata komai ba sai sadda kanta tayi qasa.
  Kafin umma ta sake tambayar ta se ga umman kd ta sauko tana fad'in"Gurin saif ta fito kinsan baya jin dad'i tun shekaran jiya har yau bai ci komai ba,shine jamil yace taje ko zata shawo kan saif d'in yaci abinci,ina fatar yaci abincin dai ko?
Umman kd ta tambayi zarah,zarah tace"eh"
 Umma tace"To ya jikin nasa?
  Zarah tace"yaji sauqi"
 Tace"to Allah qara sauqi jeki kwanta" 
 Umman kd tace"A'a bari tasha ko fura ce kafin ta kwanta,dan nasan koda ta fita bata ci komai ba ko kinci abinci a can?
  A hankali Zarah ta girgiza kanta alamar a'a.
  Umma ta kalle ta kawai ba tare da tace komai ba ta wuce,se umman kd ce ta kama hannun ta ta zaunar da ita kan kujera snn da kanta taje ta d'ebo mata fura a fridge ta sata a gaba har sai da ta shanye snn ta barta ta tafi,dan haka take fama dasu,tunda akayi  rasuwar nn basa iya cin abinci se idan ta sa su a gaba har umma kuwa se tayi da gaske snn take cin abinci koshi kad'an.
 Bayan zarah ta wuce ta d'auki photon da umma ta ajiye tana kallon photon cike da tausayin umma a ranta karo na biyu knn da ta rasa uban 'ya'yan ta,duk sun tafi sun bar ta da 'ya'ya marayu,ita kuma jarrabawar ta knn.
 "Allah sarki"
Umman kd ta fad'a a fili snn ta share en guntayen hawayen da suka fito mata ta wuce riqe da photon a hannunta dan ta san idan ba 6oye photon aka yi ba,umma bazata daina zowa duk dare tana kallon photon ba,wanda in banda damuwa ba abunda yake qara mata.

 Washe gari da safe zarah ta fito riqe da basket d'in abinci a hannun ta zata kaiwa su saif breakfast d'in su,ta tsaya tana kallon wata irin dakakkiyar mota da aka bud'ewa gate tana kunnowa a hankali cikin gidan,inda motar na fakawa da sauri driver ya fito agurguje yaje ya bud'e gidan baya,se ga wata mata fara tas da ita ta fito cike da qasaita wacce kallo d'aya zakayi mata kasan cewa kud'i sun bala'in zauna mata,ko daga yanayin tsadaddar suturar ta kad'ai in ka kalla zaka ka san hakan.
  Tana fitowa mota idon ta ya sauka akan zarah wacce taji lokaci d'aya duk ta shiga ranta,hakan yasa ta d'anyi murmushi tare da yafuto zarah alamar tazo.
 Ba musu zarah ta ajiye basket d'in da ke hannunta ta qarasa gurinta tare da gaida ta,matar wacce still mumurshi na kan fuskar ta tace"lafiya qalau ya sunan ki en mata?
  Zarah wacce taji ita ma lokaci d'aya taji son matar a ranta,fuskar ta ba yabo ba fallasa tace"suna na zarah"
    Zarah!
Matar ta fad'a tare da zare eyeglass d'inda ke sanye a idon ta,ta mugun d'aure fuska tana yiwa zarah wani irin kallon tsana,da har yasa zarah taji tsoro taja baya tana kallon yanda matar ke masifar kama da saif,da saida ta cire eyeglass d'inta ne snn zarah ta fahimci hakan.
[4/22, 12:44 AM] Paexer: [4/2, 6:27 PM] Billygiro😊: _Monday 02/04/2018_
*«»«»«»SAIFUDDEEN!«»«»«»*





By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«»49/50*
Koda jamil ya qarasa gun saif se jin yayi kuka ya qwace mishi hakan yaje cikin kuka ya kama saif ya rungume shi se rarrashin sa yake yana bashi magana amma saif bai iya daina kukan ba har sai da jamil ya jashi suka fita daga maqabartar.

 *Ci gaban labari*

Mom d'in saif na tsaye agun inda suka faka motocin su,tana kallo jamil ya wuce da saif suka je suka shiga mota,taji duk ranta ba dad'i ganin irin kukan da saif keyi gashi tasan bata da damar da zata je ta rarrashe shi,hakan yasa kawai taje zata shiga mota drivern ta yayi saurin bud'e mata ganbu ta shiga tare da d'aga wayar ta dake ta faman ruri,wacce da alama patient take da a gida unconscious shiyasa duk hankalin ta ya rabu gida biyu,dan tana d'aga waya se cewa tayi ya akayi ne ya sake farfad'owa ne inzo?
 Se tayi shiru tana sauraren amsar da ake bata da ba'a jin mene ne kawai dai yanayin fuskar ta ya nuna ba hakan taso ji ba,can tace"ok naji amma ka tabbatar kayi gaggawar snr dani idan ya sake farfad'owa,bcos i dnt wnt him die ba tare da yasan wanda ya aikata hakan a gare shi ba,nn suna gama waya ta tsinke kiran.
Yayinda jamil shi kuma da shigar su mota ya ciro wayar sa yana tunanin wanda zai kira yazo ya d'auki tashi motar sbd motar saif suka shiga tashi motar na can fake,gashi Alu driver tunda sukayi accident da Abba,unconscious yana asibiti bai ko san inda yake ba,hakan yasa ya kira drivern gidan su,suna gurin har sai da yazo snn ya bashi key suka wuce gabad'ayan su se gidan su saif,har mom d'in shi dake biye dasu a baya.
 Saif da bai ko san da mom d'in tashi tana tare dasu ba sbd yanayin da yake ciki,yana fitowa mota se jin yayi  kansa ya wani irin sara masa da kuma jirin da ya d'ibe shi lokaci d'aya yayi taga taga zai fad'i jamil yayi saurin kama shi,haka ma mom d'in sa tazo da sauri zata kama shi,shaye da toka jamil yayi saurin cewa a'a ta barshi zai iya,hakan ta tsaya bata ce masa komai ba se kallon sa kawai tayi dan ta fahimci haushin ta yake ji,amma be hana tabi bayan shi ba har ya tafi da saif d'akin shi ya kwantar dashi snn ya masa allura da lokaci d'aya ya hau yin bacci.
Yana gama masa allurar ne ya fita daga d'akin,nan mom d'in saif taje ta zauna kan bed kusa da saif tare da d'aura hannunta a hankli kan goshin sa tana shafa goshin nasa har zuwa kanshi cikin sauke ajiyar zuciya sbd wani sanyi da taji a ranta na qaunar d'an nata da ya ratsa ta wacce yau ce rnr farko da ta ta6a shafa kansa tun yana jinjiri bai ta6a samun wnn damar daga gare ta ba se yau.
 Jamil kuwa da fitar sa cikin gida ya tafi ya snr da umma halin da saif yake ciki dan yasan idan kowa zai iya yin fushi da saif ita kam baza ta iya ba ko d'azun ma ya fahimci qarfin hali ne kawai tayi,ae kuwa se gashi sun dawo tare shida umma d'in,mom d'in saif na ganin su  bata ko bar umma ta qarasa cikin d'akin ba ta dakatar da ita tana fad'in"me kuma ya kawo ki a gurin d'ana bayan wulaqanta shi da kukayi kuka saka shi a cikin wnn halin,bai ishe ku ba shine kinzo zaki qarasa shi to kinyi kad'an in ke mayya ce sei dai kici kanki wlh.
  Rai 6ace Jamil ya kalle ta yace"haba dan Allah wae ke kam masifar ki bata qarewa ne duba shi fa tazo yi.
 Kafin mom d'in saif tace komai umma tace"no jamil ba halinka bane wnn ka barta kawai indai saif ne gata nn gashi Allah ya bashi lfy.
 Daga haka umma ta juya ta fita jamil yabi bayan ta suna jin mom d'in saif se masifa take tana fad'in "Allah raka taki gona dukkan ku bana buqatar in sake ganin ku a kusa da d'ana ni kad'ai zan iya kula da abuna matsiyata kawai masu neman rabani da farin ciki na to ta Allah ba taku ba d'ana se ya dawo gare ni da yardar Allah kuwa.
Ba wanda ya kula ta a cikin su dan tuni sun ma daina jiyo me take cewa kasancewar har sun kawo qofar falo,suka tsaya jamil ya kalli umma yace"umma yanzu kina ganin ba matsala bane idan muka barta da saif ni ina tsoro dmn ganin nake matar nn kmr ba tsakani da Allah ne yasa ta dawo gare shi ba da akwai dai.
  Umma ta numfasa tace"bana tunanin haka kuma indai saif ne da kmr wuya ya yarda ya bita shiyasa kaga ban damu ba kawai ina tausayawa halin da yake ciki ne dmn d'azu zarah ta mana bayanin komai ashe duk bayanin da yake da gaske ne,asali ita ma ta nemi sakin da kanta sbd kawai sun sami sa6ani shi kuma zuciya da 6acin rai yasa ya rubuta mata sakin se kuma nn take ya fasa be bata ba ya jefar,ita kuma shine ta tsinci takadar byn har sun haqura sun sasanta kansu,wacce ta ajiye takadar ne a niyyar zata yaga amma abubuwan da suka faru yau taga gwanda kawai ta fidda sbd ta kasa jure cin mutuncin da taji ana mana,wacce har yanzu tana d'aki still abun bai daina damun ta a ranta ba se kuka take shine muka yanke shawarar anjima da yamma idan su yaya zasu koma kd se suje tare da zarah d'in har komai ya lafa snn ko zata dawo.
 Shiru Jamil yayi can yace"amma umma karatun ta fa baza ya shiririce ba?
 Umma tace"to haka ne kam amma shi Alhjn kd cewa ma yayi idan taje baza ta dawo ba ze nema mata wata school a can taci gaba dayin karatun ta har Allah ya kawo mata wani mijin tayi aure.
 Ras jamil yaji gaban sa ya fad'i ya kalli umma da sauri yace"tayi aure umma shi saifudeen d'in fa?
  Umma ta numfasa tace"a gaskiya jamil zarah baza ta komawa saifudeen ba sbd dukkan su ba son junan su suke ba,dan ko Alhjn kd da ya shigo d'azu d'azun nn bada jimawa ba,muka mai bayanin duk da zarah ta mana se duk yaji tausayin saif amma kuma yace rabuwar auren dai shi yafi sbd sake maida auren kmr wani qalubale ne,na d'aya ba son junan su suke ba na biyu kuma shine babban qalubale dan mahaifiyar saif d'in sam baza ta ta6a barinsu su zauna ba tunda har bindiga fa ta nunawa zarah tana ikirarin zata kashe ta idan ta koma ganin ta a kusa da saif wacce ba barazana kad'ai bace zata iya aikata hakan,dmn ba imani ne da ita ba tun daga kan yanda taqi qaunar d'an cikin ta komai zata iyayi akan d'an wani bare mu da ta d'auka en adawar ta ba abun da baza ta iya aikata mana ba,sai dai kawai mu roqi Allah ya ratse mu daga sharrin ta,shi kuma saifudeen Allah ya sasanta tsakanin su shida mahaifiyar tashi indai har da gaske take ba wata manufa ce a tare da ita ba.
"Amin"
Jamil ya fad'a wanda daga haka bai sake cewa umma komai ba,se sallama da ya mata snn yaje yaja motar sa ya bar gidan cike da tunani fal a ransa.

Saif kuwa koda ya farfad'o a mamakin sa se ganin kansa yayi kan wani makeken bed irin tsadaddin gadajen nn an qawata shi awa wani gadon saurata,d'akin na fidda wani irin lafiyayyen sanyi snn kuma an sauya mishi kayan jikin sa da alama wanka aka mai ba haka kawai aka sauya mishi kayan ba dan se wani irin daddad'an qamshin turare ke tashi jikin sa,yana kallon kansa ta mirror har gashin kansa ma duk an taje ya kwanta sosai,snn can ya hango wata qatuwar dardamu  shimfid'e a tsakiyar d'akin an jera masa abinci kala kala har da su fruit duk gasu nn ba wanda babu a gurin kmr wani d'an saurata.
 A hankli ya sauka daga kan gadon ya tafi gun wani  makeken hoton su da ya gani manne a jikin bangon d'akin shida mom d'in tashi da aka had'a ya rungume ta suna dariya tamkar tare suka yishi,wanda ko ba'a fad'a ba ya fahimci inda ta samu photon a instagram ne,kuma yayi hoton ne shida umma a lokacin da suka ta6a kai mishi ziyara England shine tasa aka canza shi izuwa kanta,ae kuwa lokaci d'aya ransa yayi mugun 6aci ya cire photon ya jefar take photon ya rabu gida biyu sbd yanda ya jefar da shi a fusace snn ya nufi gun dardumar da aka jera masa abinci ya hau yin ball da duk wani abun da ke jere akai.
  Nan se ga mom d'in tashi ta shigo d'akin da sauri sanye cikin kayan bacci dan lokacin qarfe tara tayi na dare.
  Taje zata kama shi cike da son ta rarrashe shi yayi saurin ja baya tare da d'aga mata hannu snn cikin wata irin kakkausar murya me cike da 6acin rai yace"ki gaya min ina ne nn kika kawo ni!
  Mom d'in tashi da duk ta marairaice fuska tace"plz calm down my son we are in d town a cikin kano muke ba wani guri na kawo ba,nn gida na ne da na siya kafin na samu na rarrashe ka ka yarda ka bini dmn ko kad'an bana son takura ka my son,but yi haquri zo zauna na kawo ma wani abincin kaci kaji"
 Ta qarashe mgnr ne had'e da kama hannun sa ya qwace hannu da sauri cikin dafe kansa yace"dan Allah ki rabu dani bana sonki ke ba mahaifiya ta bace umma ce kad'ai uwata da haife ni.
  Wani irin ciwo mom d'in sa taji a ranta ta kama hannun sa duka biyu qwallah tap a idon ta tana kallon sa tace"Haba my Son for God sake ka yafe min abunda na ma,nasan a baya na tafka babban kuskure amma yanzu ba kad'an ba nayi nadama wlh bani da burin da ya wuce in dawo da qaunar da ban nuna ma a baya ba,na kasance uwa ta gari a gare ka da zakayi alfahari dani,saif dake kallon ta ya qwace hannayen sa cikin girgiza kansa yace"Never wlh har abadah kin makara wnn qaunar ta riga ta wuce baza ta6a dawowa ba,dmn babu wata qauna mafi soyuwa da tafi ace d'a ya same ta tun yana jinjiri agun uwar sa,ni kuma gashi tun ina cikin ciki na rasa wnn qaunar a gurin ki ta yaya to kike ganin zaki iya dawo da ita how?
  Yana mgnr cikin 6acin rai kmr zai yi kuka dan idanuwan sa cike suke tap da qwallah.
  Yayinda Mom d'in sa tuni nata hawayen suka sauko kan kumatun ta ta share hawayen snn ta kama hannun sa ta tafi dashi kan bed suka zauna tana kallon sa da kulawa snn muryar ta a sanyaye tace"my son haqiqa na tabbata wnn abun duk ya faru ne a dalilin kuskuren da muka aikata nida mahaifin ka na bijirewa iyayen mu da mukayi shine Allah ya nuna mana.
Nida shi mun kasance muna matuqar qaunar junan mu sosai da sosai amma se ya kasance dukkan mu da za6in da iyayen mu suka mana,shi Abban ka umma nn taka itace mahaifin sa yaso tun farko ya aura amma fafur Abbanka yace bazai aure ta ba sai ni,nima kuma da akwai wani d'an uwan mu da ummana taso na aura wanda tun ina yarinya yake sona nima na taso ina son shi sbd yana kula dani sosai yana min duk wani abunda nake so,kowa kaf dangin mu yasan da soyayyar mu dmn tun ina yarinya aka bashi ni jira kawai yake in na girma muyi aure amma tunda na girma muka had'u da Abbanka se naji duk duniya ba wanda nake so kmr shi,a dalilin qaunar shi ne na bijirewa iyayena fafur nace sai shi bazan auri wancan ba,umma na tayi baqin ciki sosai haka har yasa ta kwanta ciwo sbd dama can tanada ciwon zuciya,amma hakan be damen ba mukayi auren mu nida Abbanka,auren da bamu ta6a jin dad'in sa ba knn kullum cikin masifa babu zaman lafiya tamkar ba wa enda sukayi auren so ba haka har muka rabu,yayinda rabuwar bata min zafi ba se bayan na koma gida,na tarar mahaifiyata ta rasu  sbd tun lokacinda ta kwanta ciwo kullum se gaba gaba ciwon yake bata tashi ba har Allah ya kar6i ranta,shiyasa duk dangin mu ba ruwan kowa dani suka fita haraka ta kwata kwata har Abba na kuwa,wanda hatsarin mota ne yayi ajalin sa,a lokacin ne rayuwa ta qara min zafi,amma Abbanka tuni ya shirya da mahaifin sa har ma ya auri ummar ka suna rayuwar su me dad'i ya manta ni gabad'aya,wanda na tabbatar bazai rasa jin labarin rasuwar mahaifyata ba har ma da ta mahaifina amma ko a text be min gaisuwa ba hakan ya qara min ciwo tun daga lokacin se ban sake bincikar rayuwar sa ba dan dama ina bincikawa ne,dmn ni ba er nn kano bace,asalin mu shuwa Arab ne a Maiduguri can muke da zama can ne asalin mu.
 Ina cikin wnn halin ne Allah ya taimake ni nayi auri se na bar zama qasar nn gabad'aya wanda ya aure ni ya tafi dani Thailand yana aikin sa a can ni kuma ya saka ni a school har na zamo cikakkiyar likita na fara aiki nima a can,inda ba wani ne ya aure ni ba face wnn d'in dai na farko da naqi,still shi bai yi aure ba har lokacin kuma abun mamaki abubuwan da suka faru a dalili na baisa ya tsane ni ba hkn ya aure ni muna zaman mu lafiya lau ba wata matsala da kuma ta6a fuskanta a tsakanin mu.
 Amma duk da haka bana jin dad'in rayuwa yanda ya kamata a kullum naga en yara se kawai naji wani qaunar su a raina,se in ta tuna ka har inaji dama ban barka ba kmr inje inzo da kai amma sanin cewa ko nazo mahaifnka bazai ta6a yarda ya bani kai ba yasa kawai na haqura,a tunani na ko zan sami haifuwar wasu yaran da zasu maye min gurbin ka amma shiru har yau ko 6atan wata ban ta6a yi ba,gashi a kullum da qaunar ka nake kwana nake tashi ina tunanin ta yanda za'ayi ka dawo gare ni,kwatsam se naji labarin rasuwar mahaifin ka,a gun wanda nake sa yana bincika min rayuwar ka dama abunda kake ciki,wanda har auren da aka ma baka so duk agun sa naji hakan yasa na bayyana agare ka dmn na qwatar ma haqqin ka na kuma tafi dakai kayi ingatacciyar rayuwa da baka samu kayi ta a baya ba.
  Nan ta kama kumatun sa tace"plz my son ka yarda ka bini kaji,idan kuma kafi son mu zauna a nn i will zan maka duk abunda kake so,amma wad'an can mutane nn ne bana son ka sake kulawa dmn ba masu qaunar ka bane so kawai suke su raba tsakanin mu,wnn matsiyaciyar kuma dan ka sake ta ka daina damuwa,da kaina zan tafi dakai England na nemo maka auren Sophie kaji"
 Saif dake kallon ta fuskar sa a d'aure ya janye hannayen ta daga kan kumatun sa yace"bana buqata"
 Snn ya miqe ya fita daga d'akin yana bin hanyar duk da ya gani,ta bishi se rarrashin sa take amma be saurare ta ba har ya fita daga gidan.
 Ba yanda ta iya se komawa tayi daga ciki ta tura mishi drivern ta acewar yaje ya sauke shi a gida.
  Saif da har yayi nisa da tafiya,yana kallon yanayin anguwar tsit ba alamar zai sami abun hawa nn kusa gashi ko waya babu a tare dashi bare ya kira jamil yazo ya tafi dashi da baisan ya akayi jamil d'in ya bar aka zo dashi nn ba dan se ma yaji haushin jamil d'in sosai.
 Ganin mota tafe yasa ya d'an had'iye 6acin ransa ya tsaya da niyyar zeyi wa motar hannu ta tsaya kawai yaga an faka motar a gaban shi,drivern ya fito da sauri har yana ajiye masa takalmi dan ko takalmi babu a qafar sa haka nn ya fito,wanda ganin haka ya fahimtar dashi aikin mom d'in sa ne kawai yasa takalmin ya kuma shiga motar aka sauke shi se gida.
 Kae tsaye ya wuce 6angaren su umma tunani fal a ransa bai san ta yaya zai fuskanci umma ba,hakan yasa ya kasa zuwa d'akin ta ya tafi d'akin su nusaiba dan sosai yake son yaga zarah,amma koda yayi knocking Nusaiba kawai ya gani da ita ce ta bud'e masa qofar,wacce tana ganin shine kawai ta fad'a jikin sa cikin kuka tana fad'in"yaya ina taje dakai tun d'azun hankalin mu duk ya tashi mun d'auka ko ta tafi da kai knn"
  Ta qarashe mgnr ne tare da d'ago fuskar ta tana kallon shi,saif yasa hannun sa ya share mata hawaye snn a natse yace"gidan ta kawai taje dani dake nn garin amma kar ki damu baza ta sake tafiya dani ba ina nn tare da ku ina zarah ina so zan ganta?
 A sanyaye tace"su Abba sun tafi da ita kd kuma wae shikenan a can zata ci gaba da zama gabad'aya har ma karatun ta duk a can zata ci gaba dayi.
  Komai Saifudeen kasa ce mata yayi se janye ta a hankli yayi daga jikin sa qwalla cike a idon sa ya juya ya bar gurin a ransa yana tunanin dolen sa yaje kd yanzun,ko wane irin hukunci Abba zai mai ya mai amma banda rabashi da zarah.
[4/22, 12:44 AM] Paexer: _Saturday 31/03/2018_
*«»«»«»SAIFUDDEEN!«»«»«»*





By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«»48*
Kafin ya iya yin komai Abban kd yazo ya kar6i takardar ya duba ya kalli saif d'in snn ya kalli zarah yace"yaushe ne ya rubuta miki sakin?
  Kafin tace komai sai da ta kalli saif wanda da saurin sa ya girgiza mata kai cikin yanayin begging baya so ta fad'a.
  Zarah da ba yanda zatayi ta janye idanunta kawai kanta qasa tace da Abban kd yau kwana hud'u knn da ya rubuta min.
   Abban kd dake kallonta yace"kina nufin rnr da Abban sa ya rasu?
  A hankli ta gyad'a masa kai alamar eh.
  Nan Hjy ta hau yin salati,umman kd da su Nusaiba kuwa duk haka suka ji abun ba dad'i,kmr dai
Abban kd wanda cikin wani yanayi ya jinjina kansa yana kallon saif da duk ya marairaice fuska yace"Abb....Abban kd bai barshi ba yayi saurin d'aga mai hannu alamar baya son ji.
  Da saurin sa ya koma kan Zarah yace"Plz zarah ki mai bayani dan Allah jefar da takadar nayi fa ba baki nayi ba kin tsince ta ne kawai ki gaya masa kinji.
  Kallon sa kawai zarah tayi bata iya ce masa komai ba se kuka da taji yana son qwace mata nn kawai ta bar gurin da sauri ta haura zuwa sama.
  Mom d'in saif da sosai taji wani irin dad'i a ranta ta6e da baki tabi zarah da kallo kana ta kalli saif wanda yaje gaban Abban kd jiki sa6ule ya gurfana kan guiyoyin sa snn sosai cikin marairaice wa yana kallon sa yace"wlh Abba tsinta tayi bani na bata ba"
  Abban kd yace"kai dai ka rubuta sakin ko?
  Eh Abba amma....amma me ae tunda har ka rubuta ta gani shikenan bana son jin wata magana ka tashi kawai kabi uwarka ku tafi,dmn baka da wani amfani a gare mu tunda har Abban naka ma baka amfana mishi da komai ba,bayan bijire masa da kayi ka watsa masa qasa a ido,mutumen da duk muka had'u baya da wata magana sai taka ya kasa 6oye farin cikin sa duk a tunanin sa lafiya lau kuke zaune da zarah ashe kana nuna masa ne kawai sbd wata banzar manufar ka.
 Kwallah cike a idon saif muryar sa na rawar kuka yace"wlh kuskure ne Abba bada niyya nayi sakin ba,tuni na janye waccan  manufar yanzu da gaske nake son in faranta mishi shiyasa ma ban bata sakin ba na fasa.....to yanzu da ta gani ya zaunu babu aure tsakanin ka da zarah,kaje ka auri wnn baturiyar da kake so babu wanda zai hanaka tunda dama can bamu isa da kai ba,sha sha sha kawai fitsararre har ni zaka rainawa hankali wae kayi saki a kuskure,bayan qaryar da ka gama shirga mana yanzu har kana rantsuwa wae da gaske ne har cikin ranka ka masa alqawarin baza ka rabu da ita ba har abadah,ashe dan iskanci ka ma rubuta mata takardar sakinta mune kake rainawa hankali,ransa ya qara 6aci ya girgiza kai yace"wlh ka bani mamaki wae ace rnr da Abban naka ya rasu har ka iya rubutawa zarah saki sbd kai a gurin ka burin ka ya cika mai takura makan ya tafi yanzu zakayi rayuwa yanda kake so ko,to kaje kayi tayi indai duniya ce zaka gani.....kul ba bakin ka ba wlh kar ka sake kace zaka yiwa d'ana baki.
 Mom d'in saif ta fad'a cike da masifa.
 Yayinda saif a rikice cikin kuka yace"wlh Abba ba haka bane kafin nasan da rasuwar Abba ne na rubuta wnn takadar wanda 6acin rai ne kawai yasa na rubuta sbd sa6anin da muka samu da zarah amma bada niyya ba.
  Abban kd dake kallon sa cikin girgiza kai yace"sam ni yanzu ba abunda zaka fad'a na yarda da kai,baqin hali ne ka riga ka gado shi a gun uwar ka gata nn,sai ka bita ku tafi can ka d'aura inda ka tsaya tunda haka kake ganin zai fisshe ka.
  Daga haka Abban kd ya fita daga fallon duk ransa a 6ace.
  Yana jin Mom d'in saif se masifa take tayi dashi.
 Saif kuwa ya tafi gun Hjy cikin kuka yana fad'in"Hjy wlh ba haka bane dan Allah ku fahimce ni"
  Hjy da duk haushin sa take ji tace"Allah dai ya shirye ka ni kaga tafiya ta bazan tsaya sauraren shashashan yaro irin ka ba marar tarbiya da baya son bin umarnin iyayen shi se qarya da kasa a gaba kana gaya mana dan kar muga laifin ka a dole ka maida mu shashashai to kaine shashashan in gaya maka.
  Nan ta tashi ta fita daga falon se masifa take tayi dashi,ya bita da kallo d'auke da idanun sa da duk sukayi jajur suna fidda qwallah,hakan ya koma gun umman kd bata ko tsaya ta saurare shi ba ta wuce,haka ma umma wacce a tunanin sa zata tsaya ta saurare shi,amma hkn ta tafi itama ta barshi,gabad'aya ma falon kowa ya watse se mom d'in sa da jamil da duk tausayin sa yake ji,mom d'in sa kam farin ciki take sosai dan ganin take hakan zai sa dolen shi ya haqura ya bita,dan burin ta knn in ta tafi dashi ya zama nata ita kad'ai bata son ya sake kula su umma dama duk wani dangin Abba,hakan yasa a ranta ta tanadar mishi gatar da zata bashi ba er qarama ba wacce zata sa ya manta su gabad'aya,se abunda ta d'aura shi akai.
Nan ta qarasa gurin shi zuciyar ta na mata zafin kukan da yake zata rarrashe shi ya tashi da sauri ya fita se part d'in sa ya rufe kansa a d'aki suka bishi se faman knocking suke mishi da ita har jamil suna bashi magana amma fir yaqi bud'e qofar.

6angaren umma kuwa qarfin hali ne kawai tayi ta tafi ta barshi amma a ranta duk taji ba dad'i,wacce tana barin gurin kai tsaye d'akin su Nusaiba ta nufa taje ta sami zarah kwance kan bed tana kuka,Nadiya da dije sunyi zugum se kallon ta kawai suke sun kasa rarrashin ta Nusaiba kuwa na zaune a kusa da zarah d'in ta had'e kanta da guiwa se kuka take itama,wacce bata ta6a sanin ainihin alaqar su da zarah ba se yau,da can duk a tunanin ta ko en uwan juna ne kawai ashe uwar su d'aya bata sani ba dmn koda kuskure umma bata ta6a gaya musu ba.
 Shigowar umma ne yasa Nadiya da dije suka fita daga d'akin,haka ma Nusaiba a hankli ta tashi ta fita daga d'akin ganin magana umma ke son yi da zarah.
Bayan sun fita ne Umma ta zauna a hankli kan bed tare da janyo zarah jikin ta cikin muryar rarrashi tace"kukan ya isa haka zarah yi shiru kinji gaya min meyasa tun lokacin da saif ya sake ki baki gayawa kowa ba se yau?
  A hankli zarah ta d'ago daga jikin umma kanta qasa hawaye na kan fuskar ta bata share ba se en yatsun ta da ta kama tana wasa dasu kmr me jin nauyin umma cikin muryar ta da tasha kuka tace"tsinta nayi a d'akina ba bani yayi ba"
 Umma dake kallon ta tace"tsinta kikayi amma shine kika san rnr da ya rubuta miki sakin"
  Eh a rnr ne da muka....se tayi shiru ta kasa qarasa zancen,umma tace"rnr ne da kukayi me?
  Muryar ta can qasa kmr baza ta iya fad'a ba tace"sa6ani muka samu a rnr shine nace se ya sake ni,shi kuma yace bazai sake ni ba haushin hakan yasa nace ni kuma idan bai saken ba se na kira Baffa na gaya mai abunda ya min,shine haushin ganin dagaske zan kira Baffa ya kar6i wayata ya jefar duk ta faffashe,a lokacin ne inaga ya rubuta min saki ban sani ba dmn hankalina na gun wayata da ya farfasa min ina kuka,ina cikin kukan ne kawai naga yazo yana bani haquri har yana ce min zai saya min wata waya,hkn yasa na haqura har ma na shirya zamu zo gida sbd Abban kd da ya kirashi yace muzo yana son ganin mu,shine bayan na shirya zan fita daga d'aki naji
na taki abu koda na duba se naga dunqulalliyar takarda ce bansan ta mece ce ba hakan yasa na d'auka na ware na duba,inda ko kad'an banyi mamakin abunda na gani a rubuce ba se ma qoqarin yaga takardar nayi,dmn yanayin yanda na ganta a dunqule kad'ai ya fahimtar dani fasawa yayi ya jefar,amma se ban samu na yaga takardar ba naji ya soma kirana kan na fito muje,shine ina sauri na koma dunqule takardar na saka a jakata.
A lokacin ne koda muka zo gida se muka tarar da ashe baffa ne ya rasu.
  Ta share qwallar da suka zubo mata snn ta ci gaba da cewa"Sam abunda Abban kd yayi tunani ba haka bane,ba bayan rasuwar Baffa ne ya sake ni ba kafin haka ne kuma se ya fasa bai bani ba,ni kuma dana ganta banyi niyyar snr da kowa ba,haka ma sakata da nayi a cikin jakata ba ina nufin in nuna ma wani ba,sai dan idan na samu lokaci in yaga,amma se abubuwan da suka faru yau yasa na kasa jurewa naga gwanda kawai in fitar da takardar dmn ba kad'an ba naji zafin yanda mahaifiyar shi ke zagin ku har tana gaya muku maganganun marassa dad'in ji.
 Ta qarashe mgnr ne sosai cikin muryar kuka.
 Umma dake sauraren ta shiru tayi ta kasa cewa komai duk tausayin saif take ji a ranta.
  Umman kd kuwa wacce tun d'azun ta shigo d'akin tana tsaye a bakin qofa taji komai,hakan yasa jiki sa6ule ta qarasa gurin su ta zauna tana kallon zarah tace"kunyi kuskure dake har shi Zarah sam bai kamata ace da iliminki kin nemi saki a gun mijinki ba a kan wae dan kun samu sa6ani,shi kuma bai kamata ace ya biye maki ba har yabar zuciya ta d'ibe shi yakai ga rubuta miki saki.
 Umma tace"haka ne kam zarah yarinya ce bai kamata ace ya biye mata ba,ita kuma bansan jahilci me ne ya d'ibe ta ba kmr wacce bata je islamiyya ba,wayiwa kawai!
  Umma ta fad'a cikin d'aure fuska tana kallon zarah,wacce da saurin ta ta sadda idanunta qasa qwallah cike a idanun nata har suka shiga silalowa a hankli kan kumatun ta.
 Umma bata damu ba se kallon umman kd tayi tace"yanzu abunda ya kamata yaya kiyiwa Alhjn kd bayani a wanke saif daga gare shi har ma da Hjy da duk suka fita cike da jin haushin sa,amma maganar gaskiya saki kam ya zaunu dmn hakan shine mafi a'ala bazan iya jure cin mutuncin mahaifiyar sa ba.
 umman kd tace"gaskiya kam cin mutunci nata yayiwa harda tozarci,amma ina tausayawa saif sam bazai ji dad'in hakan da zamu yi mishi ba musamman ma yanda har ya kasance zarah na d'auke da cikin sa.
Umma dake kallon ta tace"hm yaya knn zarah fa bata da komai"
  D'auke da mamaki umman kd tace"kmr ya cikin ya zube ne?dmn da jimawa fa Alhj ya gaya min yace Abban saif ya gaya masa har yana murna ze fara ganin en jikokin sa.
  "Allah sarki"
Umma ta fad'a wacce take taji qwalla sun ciko mata a ido.
  Tace"wani zazza6in mura ne fa da zarah ta ta6a yi shine ya d'auka ko ciki ne da ita har nima na d'auka ko haka ne,se gashi saif d'in da kanshi yake gaya min shi ba abunda ma ya ta6a shiga tsakanin sa da zarah,ko da akwai?
  Ta tambayi zarah tana mai kallonta wacce kanta qasa ba tare da ta iya kallon umma ba ta girgiza kanta alamar a'a.
 A sanyaye Umma tace da umman kd"kin gani ko,shiyasa kawai naga rabuwar auren shi yafi tunda dukkan su ba son junan su suke yi ba.
  Umman kd da tayi shiru can ta numfasa snn tace"to Allah sauwaqe yasa hakan shi yafi alkhairi.
 Umma tace"Amin tare da share en guntayen hawayen da suka fito gefen idon ta.
 Zarah kuwa tana jin hukuncin da umma ta yanke bata san meyasa ba se jin tayi ta saki kuka a hankli.
 Umman kd ta tafi da ita jikinta se rarrashin ta take tana fad'in"kar ki damu daina kuka komai ya wuce kinji,a hankli zara ta gyad'a mata kai.
  Umma dai sae kallon su kawai take.

Su jamil kuwa suna can se rarrashin saif suke ya bud'e qofa amma still yaqi bud'ewa suna jinsa se kuka kawai da yake,duk jamil yabi ya damu ga haushin mom d'in saif da yake ji sosai a ranshi har ganin yake kmr a dalilin ta ne saif yaqi bud'e qofa shiyasa kawai yayi tafiyar sa ya barta gurin se ci gaba take da doka qofa tana rarrashin saif cikin lalla6awa dan so take ko yaya ta shawo kansa har ya haqura ya yarda ya bita shiyasa ma sam bata ji ta gaji da rarrashin nasa ba,amma kiran gaggawan da aka mata a waya ne yasa dolen ta ta bar gidan ba dan taso ba.
 Jamil kuwa da yaje gida kasa zama yayi ya koma dawowa amma se ya tarar saif d'in baya nn ya fita,hankalin sa yaji ya tashi kaddai mom d'in tashi ta samu nasarar shawo kanshi ya bita sun tafi.
 Bai ko iya shiga cikin gida ba yaje gun gateman ya tambaye shi ko wnn mtr da tazo tare suka fita da saif?
 Gateman yace masa"a'a ta riga shi fita dmn kafin ma ta fita sai da ta min alheri mai tsoka ta kuma bani numbar wayar ta tace idan naga ya fito na kira ta na snr da ita.
 Jamil dake sauraren shi yace"to ae saif d'in ya fita ban ganshi a d'akin sa ba kuma motar shi bata nn kana nufin baka ga fitar sa bane ko me?
Aa naga fitar sa yanzu yanzu nn nima na bud'e masa gate,kuma har na kira wnn Hjyr na gaya mata,ina gama waya da ita ne ma ka shigo.
  Tsaki kawai jamil yayi ya tafi da sauri yaja motar sa ya bar gidan,yaje duk inda yake tsammanin zai samu saif bai ganshi ba,duk ya rasa me zaiyi ya sake komawa gidan su saif wae ko zai ganshi ya koma,amma bai ganshi ba sai mom d'in saif d'in ya gani wacce tana mishi magana ko kula ta bai yi ba ya shiga motar sa ya wuce,bata ji haushin sa ba sema shiga motar ta tayi itama tasa dirvern ta ya bishi baya,yayinda shi kuma jamil bai zarce koina ba se maqabarta a mamakin sa kuwa se ya samu saif a can gurfane a gaban kabarin Abba yana kuka bana wasa ba duk idanun sa sun kumbura sunyi wani irin jajur da lokaci d'aya jamil ya samu kansa da jin kuka shima,ya tafi sannu a hankali ya qarasa inda saif d'in yake,mom d'in saif kuwa da ke biye dashi kasa qarasawa tayi gurin su se juyawa tayi ta fita daga maqabartar jikin ta duk a sa6ule wacce kallo d'aya zakayi mata ka fahimci cewa tunanin ne fal a ranta da kuma nadamar da ta bayyana qarara a fuskarta.
[4/22, 12:44 AM] Paexer: _Tuesday 03/04/2018_
*«»«»«»SAIFUDDEEN!«»«»«»*





By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»Page«»51*
Yana sauka downstairs yaji muryar umma ta kirashi,tako d'aya bai qara ba ya tsaya had'e da juyawa ya kalle ta sau d'aya ya sadda kansa qasa baya iya kallon ta dan duk kunyar ta yake ji shi kam,umma kuwa da saukowar ta kama hannun sa tayi taje dashi kan doguwar kujera suka zauna,tana kallon sa da kulawa tace"hankalin mu duk ya tashi saif ina taje da kaine koda Nusaiba taje zata duba ka ta samu 6angaren naka ba kowa haka jamil ma ya dawo be same ka ba,gabad'aya duk hankalin sa ya tashi da yaji cewa ta tafi dakai yanzun nn ma na gama waya dashi yana tambayar ko anji labarin inda taje dakai nace masa har yanzu shiru bamu samu wani labari ba,gashi wayar ka idan an kira tana ringing amma ba'a d'agawa da qarshe ma aka kashe wayar.
 Saif da still baya iya kallon umma kansa qasa yace"may be phone d'in tana d'aki ta fad'a wani gurin i dnt know,kawai dai koda na farfad'o se ganin kaina nayi ta kaini gidan ta dake nn garin.
 Umma dake kallon sa tace"dawowa kayi ko ita ce ta maida ka?
 Yace"dowowa nayi umma kuma se na samu banga zarah ba"
 Ya qarashe mgnr ne had'e da kallon ta cikin yanayin nuna rashin jin dad'in faruwar hakan"
 Umma ta numfasa tace"to saif zarah d'in ce se kuka take tayi sbd abunda ya  faru shine Alhjn kd da zasu tafi suka tafi da ita.
 Yace"amma umma  Nusaiba ce min tayi wae zarah ta koma can gabad'aya da zama har za'a nema mata wata school a can.
  Eh haka Alhjn yace.
Idanun sa cike da qwalla yace"Why umma meyasa kuke son ku raba auren mu wlh bada niyya nayi wnn sakin ba 6acin rai ne kuma nn take na fasa ban bata ba"
  Umma dake kallon sa cikin yanayin tausayi tace"ae zarah ta mana bayanin duk yanda abun ya faru kusan duk laifin ta ne ma kuskuren ka d'aya ne biye matan da kayi amma yanzu ae komai ya wuce a idon kowa baka da wani laifi har Alhjn kd da duk yafi d'aukar abun da zafi haka ma Hjy da kaina ma na mata bayani,damuwar mu d'aya ita ce mahaifiyar nn taka dake son zata tafi dakai yanayin ta ya nuna gabad'aya take son ta rabamu dakai kwata kwata,ni kuma zan so ace ko ziyara ce ka riqa d'an kawo mana dmn bana jin zan iya jure tafiyar ka gabad'aya.
   Saif da ko kad'an baya son ana maganar mom d'in shi ya share hawayen da suka zubo mishi snn yace"plz umma ki daina min mgnr wnn matar ni ba inda zanje ina nn tare daku ae ba qaramin yaro bane ni da za'a ce wae anzo za'a tafi dani ta fad'a ne kawai dmn tasan hakan bazai ta6a faruwa ba ma.
  Umma tayi shiru tana kallon shi can ta numfasa tace"Amma saif....yace"plz umma ni ki daina min maganar ta maganar zarah nake son ji.
Nan kawai ya zame qasa gan guiwoyin sa ya hard'e hannayen sa fuskar sa cike da nadama yana kallonta yace"plz forgive me umma nasan nayi kuskure a baya bansan zarah erki bace wlh shiyasa duk nayi wa en nn abubuwan amma dan Allah kiyi haquri ki yafe min rashin sani ne.
   Ya qarashe mgnr hawaye na sauka kan kumatun shi yayi saurin share hawayen,umma  dake kallon sa ta kama kumatun sa tana mai qara share masa hawayen snn a natse tace"ko kad'an ban riqe ka da wnn ba dmn nasan rashin sani ne dan haka kar ka damu kaji komai ya wuce.
  Yanayin fuskar sa kmr qaramin yaro yace"nagode umma amma dan Allah kar ace za'a raba aurena da zarah bana so"
 Da kulawa umma tace"saif meyasa duk kabi ka damu in dan nice dama nasan ba son junan ku kuke yi ba bazan d'auke shi komai ba bare kuma zarahn ce ta nemi sakin da kanta ba laifin ka bane"
 Cikin yanayin damuwa saif yace"plz umma ba haka ba ni ki daina fad'ar haka dmn babu wata macen da nake jin zan iya rayuwar aure da ita face zarah,dan Allah umma ki taimaka min wlh nida ita munyin alqawarin zamu samarwa Abba farin cikin sa,bai kamata ace dan ya mutu muyi fatali da burin sa ba.
  Nan take qwalla suka ciko a idon umma tace"saifudeen haqiqa ina so inga cewa kun cika masa burin sa,amma shi kansan yasan ya bar baya da qura,wanda da alama yaji a jikin sa cewa mutuwa zaiyi  shiyasa da zaiyi tafiya ya maka duk wad'anan maganun da za'a iya kiran su da wasiyya,amma se mahaifiyar ka tazo ta lalata komai dmn kasan maida auren ku kmr wani qalubale ne sam mahaifiyar ka baza ta ta6a barin ku ku zauna lafiya ba komai zai iya faruwa idan aka maida auren,mafi a'ala shine idan zarah ta sami wani mijin tayi aure haka kaima idan ka sami wacce kake so kayi aure.
  Da sauri cikin girgiza kai yace"no umma nifa zarah she is still my wife na gaya muku wancan sakin kuskure ne kuma a take na fasa babu shi dan haka ni wnn matar bata isa ta rabani da zarah ba,kd zan tafi yanzun nn in dawo da ita.
  Aa saif kayi haquri ni bazan iya da rashin mutuncin wnn matar ba,burina kawai inga kun shirya tsakanin ku kaida mahaifiyar taka,bana son wata masifar kuma dmn zancen kace zaka
dawo da zarah kmr wata masifar ce kake son sake tadawa bayan bamu ko fita daga cikin wnn ba.
  Fuskar sa kmr zeyi kuka yace"No umma sai dai idan fushi kikeyi dani ba kya son zarah ta dawo gareni amma ba hujja bace wae ace a kan wnn matar za'a raba aurena da zarah bayan kinsan Abba bayada wani burin da ya wuce ace mun kasance tare nida zarah har abadah.
  Umma da har ranta masifar mom d'insa ce bata iyawa da ita tace"ko kad'an ba haka bane saifudeen bayanin da na maka dai shine"
  Yace"to dan Allah umma ki fita harakar wnn matar ki barni da ita kawai ni nasan me zanyi kuma dan Allah ki barni inje inga zarah.
  Umma tace"shikenan zan barka kaje kaga zarah d'in amma ba yau ba sei gobe"
  Yace"no umma i cnt wait har gobe ina so in ganta yau plz"
  Aa kayi haquri har gobe yanzu dare yayi kuma gashi naji jikin naka da zafi sosai da alama yinin yau baka ci komai ba ko?
 Eh umma amma zan iya....se kuma yayi shiru yana tuna yau gabad'aya in banda sllr asuba ba sllr da yayi.
 Nan kawai ya miqe tsaye da sauri,umma ta kalle shi tace"lafiya?
  Yace"zanje inyi sallalon da ake bina ne umma gabad'aya yau in banda sallar asuba ba sllr da nayi"
  Umma tace"subhanallah bansan kana wasa da sallah ba ya akayi ka manta?
  Saif da bai san mom d'insa ce ta qara yi masa wata allurar ba bayan wacce jamil ya masa yace"Ba mantawa nayi ba umma allurar da jamil ya min ce tasa ni yin bacci sosai shine koda na farka na samu har dare yayi.
 Umma ta miqe tsaye tace"to bari na kawo ma abinci kaci dmn kaji qarfin yin sallolin ko"
 Yace"no umma ni bazan iya cin abinci ba idan ba sallolin nn nayi ba"
Har zai fita se kum ya tsaya yace"plz umma kafin na dawo asa ko Nusaiba ce ta dafa min indomie ita nake jin zan iya ci.
  Umma tace"kar ka damu da kaina ma zan dafa maka amma za'a soya maka qwai ne ko a dafa maka?
  Yace"Aa zarah dafawa take yi nima dafaffen nake so"
 Tace"to shikenan jeka kayi sallolin to.
 Nan saif ya fita umma ta bisa da kallo a ranta tana tunanin kmr son zarah ne fa saif ya farayi nn take kuma se ta basar ta wuce zuwa kitchen dmn dafa mishi indomie d'in.
  Da shigar ta kitchen ruwan Lipton ta fara had'a mishi tasa a mug ta rufe snn ta dafa mishi qwai guda uku,kafin take fara had'a mishi indomie sbd tafi so koda zai dawo indomie d'in bata huce ba da zafin ta dai dai yanda zai fi jin dad'in cinta.
  Ae kuwa da ya dawo sosai yaci indomie d'in dan ba kad'an ba yunwa yake ji dan koda yaje yana yin sallah har wani jiri yake ji,amma hakan ya jure ya samu natsuwar yin su duka.
 Wanda yana gama cin indomie se ga jamil ya shigo sbd kiran sa umma tayi ta gaya masa saif ya dawo shine yazo dmn ya kwana tare da saif d'in dan tsoron yake kar mom d'in saif ta sake dawowa ta bar garin dashi gabad'aya,gashi shi kuma jin saif d'in yake kmr wani d'an uwan sa da baya son ganin ranar da zasu rabu.
Saif na ganin sa ya miqe yana fad'in"yauwa jamil muje ka rakani kd"
 Kafin jamil yace komai umma da dama tana nn zaune a falo tace"saif ba nace kbr tafiyar har gobe ba"
 A d'an shagwa6e ya kalli ta yace"umma am ok now zan iya zuwa kuma kinga ga jamil ko a can ne zamu iya kwana se gobe da safe mu dawo abunda kawai nake so shine inga zarah.
  Jiki sanyaye cikin fad'uwar gaba jamil ya kalle shi,umma tace"A'a just kabar tafiyar nn har gobe hankalina yafi kwanciya"
 Ba yanda ya iya a hnkli ya gyad'a mata kai alamar yaji,kana suka mata se da safe suka wuce part d'in saif.
 Plz Jamil kana da numbar zarah ina so  nayi waya da ita inji ko ta daina kuka,bcos umma tace min kukan da takeyi ne yasa aka wuce da ita kd.
 Saif ya tambayi jamil bayan sun isa 6angaren nashi.
  Jamil ya kalle sa kawai tare da girgiza masa kai alamar bashi da.
  Komai saif bai sake ce masa ba har suka kwanta bacci inda jamil har safe bai iya yin baccin kirki ba se juyi kawai da yake  cike da tunanin zarah a ranshi da kullum qara jin sonta yake a ran shi musamman abubuwan nn da suka faru sei duk ya shiga tausayin rayuwar ta.

Washe gari bayan sunyi wanka har sunyi breakfast suka kama hanyar kd.
Basu jima da wucewa bane umma na d'aki ta soma jin qarar door bell dan rufe qofar tayi sbd wani lokacin se ayi ta sallama basu ji ba suna ciki.
 Koda taje ta bud'e qofa mom d'in saif ta gani wacce kae tsaye ba gaisuwa ba sallama tace"ina d'ana?
  D'anki kin bani ajiyar sa ne?
Umma ta fad'a tana kallonta fuskar ta a d'aure.
Cikin isa da gadara Mom d'in saif tace"ban baki ajiyar sa ba amma inada tabbacin kinsan inda yaje,dan naje 6angaren sa ban same shi ba kuma driver ya tabbatar min jiya har nn gida ya sauke shi.
  Umma tace"ae sai kije ki neme shi tunda shi yaron goye ne da zaki kama faman bibiyar sa duk inda yaje.
  Nan kawai ta rufe qofar ba tare da jira me mom d'in saif d'in zata ce ba.
 Koda ta juya se ganin Nusaiba tayi tsaye a bayan ta wacce jin qarar door bell ne yasa ta fito ta kama hannunta kawai suka wuce zuwa sama.
 Mom d'in saif kuwa tana ganin umma ta rufe mata qofa duk ranta a 6ace ta juya had'e da kiran wanda tasa yana kula mata shiga da fita na saif,suna gama waya dashi taje ta shiga mota tace da driver suje kd.
 Nan driver yaja mota suka hau hanya.
Su saif kuwa a lokacin sun d'anyi  nisa akan hanya yayinda jamil yana jan motar ne kawai amma jin kansa yake kmr wani marar lafiya a hakan har suka isa.
  Abban kd baya nn ya fita se umman kd suka samu,bayan sun gama gaisawa da ita dukkan su sukayi shiru basu sake cewa komai ba kmr wasu baqin kunya.
 Umman kd dake kallon su tace"ya akayi ne saif ko na kira Alhj yazo zakuyi magana ne?
  Saif da kansa ke qasa yace"Eh umma amma ina so dan Allah zanga zarah tukun"
  Shiru umman kd tayi na d'an wani lokaci tana kallon sa can tace"Tana a d'akin su Nadiya zaka iya zuwa ka same ta.
 Wani sanyi saif yaji a ranshi kmr har ya ga zarah d'in ya tashi a natse ya haura sama zuwa d'akin su Nadiya yayi knocking,Nadiya ta bud'e mishi qofa ta gaida shi tare da bashi hanya ya shiga ita kuma ta fita.
 Damuwa ce ta bayyana a fuskar sa ganin Zarah kwance kan bed ana mata qarin ruwa,ya qarasa da saurin sa se kuma ya zauna a hankli kan gadon ganin kmr bacci take,wanda a natse ya d'aura tafin hannun sa a hankali kan goshin ta yaji jikin nata duk zafi bai janye hannun nasa ba kawai yaga ta shiga bud'e idanunta a hankli ta ware su a kan shi se kallon sa kawai take tayi,haka shima ya kafe idanun sa akan ta se kallon ta yake,snn a hankli ya kira sunan ta tare da kama ta ya tafi da ita jikinsa ya kwantar da kanta a kafad'ar shi,yana shafa gadon bayan ta a hankli,zarah wacce ganinsa yasa taji wani sanyi a ranta ta qara lafewa sosai a jikin sa ta sauke ajiyar zuciya a hankali can ciki.
[4/22, 12:44 AM] Paexer: _Saturday 07/04/2018_
*«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»page«» 53*
 Snn cike da mamaki da kuma rud'u ya kalli mom d'in tashi da qyar hannun sa na rawa ya nuna mata Abba,ba tare da ya iya cewa komai ba dan magana ma kasa fito mai tayi se  yanayin fuskar sa da ta nuna alamar  tambayar ta yake shin abunda yake gani gaskiya ne!?
  Da qyar Mom d'in tasa ta iya gyad'a masa kai cikin maida yawun da suka tsinke mata sbd tsoro snn cikin marairaice fuska muryar ta na rawa  tace"but...am..sorry..my...son wlh..i..didn't..mean...to..hurt..u,dole ne tasa nayi hakan dmn na samu ka dawo gare......ae kafin ma ta qarasa zancen ta se jin tayi yayi kukan kura yayi cikinta zai had'a ta da bango,nn kawai se ga jamil ya shigo d'akin ya fizgo shi da qarfi,yana fad'in"haba saif wae me yake faruwa ne  mahaifyar ka ce fa kana hauka ne!
Saif bai saurare shi ba se ture shi yayi da qarfin tsiya har sai da jamil ya tafi taga taga zai fad'a kan Abba wanda se a lokacin ya lura dashi ae kuwa a rud'e yaja baya da qarfi snn ya tsaya cak kmr wani statue komai nasa baya motsi se kallon Abba da yake cikin tsananin mamaki da kuma tsoron da ya bayyana qarara a fuskar sa,ya juya fuskar sa fal tambaya ya kalli saif da ya koma kan mom d'in shi kmr wani zaki,ita kuma se ja baya take a tsorace cikin girgiza kai tana fad'in"No my son plz listen to me wlh ban aikata hakan ba sai dan kai dmn na tabbatar idan mahaifin ka yana raye bazai ta6a barin ka dawo gare ni ba shiyasa kawai nabi wnn hanyar amma.....bata iya qarasawa ba sbd wuqar da taga saif ya d'auko a cikin fruit ya nufe ta gadan gadan zai caka mata ita kafin ta iya yin komai jamil yazo da sauri ya qwace wuqar daga hannu saif ya jefar snn ya rirriqe shi dan ya fahimci gabad'aya baya cikin hayyacin sa da gaske yake son kashe ta.
 Wanda ko kad'an baiji dad'in da jamil ya hana shi ba ransa a mugun 6ace  yace da jamil"i will kill u wlh idan baka sake ni na kashe ta ba!ka sake ni nace!!
 Ya qwace kansa da qarfi tare da ture jamil har sai da ya fad'i,shi kuma cikin hanzari ya tafi zai d'auki wuqa mom d'in sa ta riga sa d'aukar wuqar,ta saita ta akan cikin ta cikin fasa kuka mai ciwo tace"is enough my son! is enough!! ka bar ni da kaina zan kashe kaina indai akan ka ne ba abunda bazan iya yi ba,shiyasa tun tafiyar Abbanka abuja nake bibiyar sa har kan hanyar sa ta dawowa,wanda nice silar accident d'in shi sbd notirin tayar motar sa da nasa aka kunce aka kuma lalata masa birki.
  Bayan sunyi accident d'in ne mukayi sauri nida wa enda nasa muna bibiyar shi na masa allurar da zai yi kwana uku ba tare da an fahimci akwai rai a tare da shi ba,bayan an binne shi da dare nasa aka je maqabarta aka ciro min shi dmn so nake idan ya farfad'o in fayyace masa komai yasan cewa nice na masa wnn aikin snn bayan yasan hakan na sake masa wnn allurar a sake maida shi a kushewar shi can ya qarashi rayuwar shi ya barni inji dad'in d'a nima tunda shi ya gama cin lokacin sa da kai.
 Nan ta saki wuqa cikin marairaicewa tare da had'e tafukan hannayen ta tana kallon saif tace"plz my son i beg u kabar ni in qarasa manufa ta,wlh nayi ma alqawarin babu wani farin cikin da zaka nema ka rasa komai kake so a duniyar nn zan maka i promised u.
 Saif dake kallonta yana ji kmr ya kamata ya mata gunduwa gunduwa sosai cikin qunar rai yace"u are totally mad!!
Se kuma nn kawai ya fashe da wani irin kuka yace"wlh nayi baqin cikin da kika zamo uwata! na tsane ki!! i hate u!!!,bazaki ta6a samuna a matsayin d'anki ba wlh har abadah,kuma yanzu nn zan kira en jarida kafin nasa police su zo su tafi dake sei kowa yasan abunda kika aikata se kowa ya tsine miki muguwa kawai marar imani se Allah ya nuna miki abinki wlh.
  Yana qarashe maganar ya ciro wayar shi,da sauri cikin girgiza kai mom d'in sa tace"no my son idan kayi hakan duniya bani kadai' zata zaga ba har da kai,nifa mahaifiyar ka ce kuma a dalilin ka ne na aikata hakan dmn na samu ka dawo gare ni ta yaya zaka min haka,dan Allah dnt do dis to me kaji my son,kuyi shiru da bakin ku wnn sirri ne ba abune da za'a bayyana shi duniya taji ba,dmn za'a ji abun wani iri bayan a idon kowa mahaifin ka ya rasu is gud a barshi akan hakan,allurar da nake niyyar mishi dmn in samu ko zai farfad'o na fasa,kawai kubar ni nasa a maida shi kushewar sa kunji dan Allah wlh shi kad'ai ne mafita a gurina dmn na tabbatar idan na barshi yaci gaba da rayuwa tamkar na rasa ka ne my son i beg u kar ka ce a'a.
 Komai ma kasa ce mata saif yayi bare shi jamil da duk imani ya cika shi yana kallon mom d'in saif d'in a kwata kwata marar hankali she have mental problem.
 Saif dake kallonta cike da tsana yace"kisa a saki ummana yanzu"
  Da dauri tace"shikenan na amince indai har bazaka bar maganar nn ta fita ba yanzun nn zan sa su maida ta har gida.
 Nan kawai ta d'auko wayar ta dake kan sofa ta kira police cikin basu umarni tace suyi maza su maida wnn matar gidanta....bata jira me zasu ce ba da saurin ta ta tsinke kiran a rud'e tana kallon saif da ya kira police yana gama waya dasu ya kuma kira en jarida se begging d'in sa take har tana gurfunawa amma fir yaqi saurararta har ta koma gun jamil tana fad'in"dan Allah ka fahimtar da my son kar ya min haka nifa uwar sa ce,idan kuma mijina yaji abunda na aikata na tabbatar shikenan ba ruwan sa dani haka shima my son na rasa shi knn,dan Allah ka tayani roqon sa ya kirasu yace musu wasa ne ya fasa ba abunda ya faru a nn gidan kar su zo.
  Jamil dake jin wani irin baqin ciki a ranshi kmr shine abun ya faru dashi ya kauda fuskar sa gefe qwallah cike a idon shi baya ko son ganin ta.
 Saif kuwa yana gama waya dasu kallon ta ya tsaya yana yi yana jin kmr zuciyar sa zata fashe sbd baqin cikin da yake ji sosai a ranshi qwalla cike a idon shi ya juya kawai ya nufi gun Abba inda kai tsaye ya duqa ya d'auki allurar da mom d'in sa ta yar,allura ce mai tsananin had'arin gaske wacce da zarar tayiwa Abba ita koda ya farfad'o tofa bazai wuce minti goma ba allurar zata illata shi ya mutu.
  Nan kawai yaje jikin Abba ya rungume shi a hankali se kuka yake jamil ya qaraso gurin sa cike da tausayi ya kama shi yana ta rarrashin sa,da qyar saif ya samu ya tsayadda kukan snn ya kira Abban kd ya snr dasu abunda ake ciki,yana jin irin yanda hankalin Abban kd ya tashi amma hkn ya tsinke kiran,
nn kawai se ga police da en jarida sun shigo,mom d'in saif da tun d'azu begging d'in su take bata daina ba tana ganin shigowar su hankalin ta gabad'aya ya gama tashi kmr wata zautatta ta rirriqe saif tana wani irin kuka ita ba inda zata je sai tare da shi,da qyar police suka iya fizge ta zasu fita da ita se sambatu take tana fad'in komai yanda ta aikata da kuma dalilin da yasa ta aikata,ae kuwa nn en jarida suka hau rubutawa ana ta d'aukar ta foto bayan an fita da ita snn sukayo kan saif suna son jin qarin bayani daga gareshi amma komai kasa ce musu yayi se faman danne kukan da yake ji yake wanda hakan yasa sukayi ta d'aukar sa photo shima sbd sun fahimci irin yanayin da yake ciki ba d'an qarami bane,haka ma jamil da suka koma kanshi ba abunda ya iya ce musu se kama hannun saif yayi suka fita tare da doctors d'in da suma kiran su saif yayi suka d'auki Abba kan ambulance bed aka tafi dashi aka saka shi a ambulance suka wuce se asibiti har ma da en jarida kuwa.
 Gabad'aya gari take labari ya bazu koina dan Abba mutum ne da aka sanshi sosai a gari,da har wanda bai san shi ba ma yaji mutuwar sa yanzu kuma se gashi anji be mutu ba hakan yasa labari se yad'uwa yake tayi a gari kan yanda tuni aka saka labarin a gidan TV da radio inda kowa yaji se ya tsine wa mom d'in saif dmn abune da ya girgiza mutanen gari sosai.
 Umma kuwa en sanda na maida ta gida labarin yazo kunnen ta sbd kiranda umman kd ta mata ae kuwa sosai cikin tashin hankali da rud'u ta snr da Nusaiba koda suka fito se kici6us sukayi da en jarida sun zo gidan,umma batayi ta kansu ba se fizgar mota tayi suka nufi asibiti dmn ta tabbatar da gaskiyar abunda taji,gaskiya ne shin ko mafarkine take,duk da dai taji a bakinda baya qarya amma ta shiga rud'ani sosai da har sai taga Abba snn ko zata iya tabbatar da abunda taji.
6angaren saif kuwa suna isowa asibiti yana fitowa mota se jin kansa kawai yayi qasa ya zube sbd yanayin da ya tsinci kansa a ciki wanda daga nn bai sake sanin inda yake ba se farfad'owa kawai yayi ya ganshi kwance kan gadon asibiti kowa babu a d'akin sai zarah kad'ai dake can zaune kan sofa tayi tagumi sosai cikin yanayin damuwa wacce tana ganin ya bud'e ido da sauri har tana hard'e qafafu ta qarasa gurin sa ta zauna a hankali kan gadon da yake kwance tana kallon sa snn kmr da tsoro ta kai hannun ta a natse tana shafa gefen fuskar sa qwallah cike a idon ta,se kuma kawai ta saki kuka a hankli ta fad'a kan faffad'an qirjinsa ta rungume shi.
 Da sauri saif ya rufe idanun sa sbd yanda yake jin kukan nata har cikin ranshi,wanda kana ya tashi zaune a hankali rungume da ita a qirjinsa yakai hannun sa a natse cikin yanayin rarrashi yana shafa gadon bayanta ba tare da ya iya ce mata komai ba,amma ganin se kukan take tayi taqi dainawa yasa shi yin magana muryar sa cikin rarrashi yace"ya isa haka mana zarah bana jin dad'i idan kinayin kuka ki daina kinji,gaya min wane condition Abbana yake ciki?
 Ya fad'a tare da d'ago ta daga kan qirjinsa yasa lallausan hannun sa da kulawa ya share mata hawaye,zarah da duk tausayin sa take ji cikin muryar kuka can ciki tace"Baffa yana I.C.U doctors sun hana a ganshi wai a barshi shi kad'ai,amma anbar su umma sun ganshi nida su Nadiya ne ba'a bar mu ba.
  Shiru saif yayi qwallah cike a idon shi dan yanayin da Abba yake ciki ba qaramin yanayi bane da dole yana buqatar kulawa da ko waje aka fita dashi Allah ne kad'ai yasan ko zai rayu.
[4/22, 12:44 AM] Paexer: _Thursday 05/04/2018_
*«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»page«» 52*
Saif dake shafa bayanta muryar sa  a hankali yace"jikin ki yayi zafi sosai zarah,meyasa kikayi tayin kuka har zazza6i ya kama ki haka plz indai akan wnn mtr ne ki cire damuwa a ranki komai zai daidaita kinji"
  Zarah dake manne a jikin sa a hankli ta gyad'a masa kai,yace"kinci abinci?
 Ta girgiza masa kai,ya kalli abincin da aka ajiye mata nn kusa da gefen gado cikin plate an rufe da d'ayan plate fresh milk da cup ajiye a kusa yace"bari to na d'auko maki abincin kici"
Muryar ta can qasa ta marasa lfy tace"um um bana iya ci bakina baya min dad'i,kawai cire min wnn qarin ruwan da ake min ni na gaji dashi.
Tayi maganar ne had'e da miqa masa hannun ta da aka d'aura mata ruwa akai.
Saif ya kama hannun nata a hankali zai cire mata,se ganin sukayi an tizge mata cannula d'in da qarfin tsiya har sai da jini ya fito aguje ba shiri,zarah ta fasa ihu cike da jin zafi wacce kafin ta iya ganin wanda ya tizge mata cannula d'in se jin tayi an kuma fizge ta daga jikin saif had'e da kai mata lafiyayyen mari har sai da ta fad'i kanta ya daki beside drawer,ta fasa ihu tare da dafe gefen kan ta,a rikice saif yaje da sauri ya kamata tuni gefen kanta ya fashe jini na fita nn saif ya d'ago idanun sa da duk sukayi jajur lokaci d'aya,cikin tsananin 6acin rai yake kallon mom d'in sa da duk ita ce tayi aikin,sosai ya jimqe hannun sa jikin sa na wani irin rawa yana jin kmr yaje ya doke ta amma be iya yin hakan ba se qwalla da suka taru a idon shi,ya kalli zarah da sai kuka take zai tafi da ita jikin sa dmn ya rarrashe ta,ta tafi da gudu jikin Umman kd da shigowar ta knn d'akin ita da Nadiya kan jin ihun zarah da yasa su zowa da sauri sbd duk basu san da shigowar mom d'in saif ba dmn saif na barin falon bayan ta kira Abban kd a waya ita ma ta tashi ta nufi kitchen a niyyar zata kawo musu lemu a can Nadiya ta same ta dan koda ta sauka bata ga kowa a falon ba,bcos umman kd na barin falon jamil ya tashi ya fita yaje cikin mota ya zauna sbd kansa dake masa masifar ciwo ya had'e kan nasa da sitarin mota shiyasa har mom d'in saif ta shiga cikin gida baiga wucewar ta ba.
Ae kuwa da mamaki umman kd ke kallon mom d'in saif snn ranta a 6ace tace"masifaffiya masifar taki kuma kika zo zakiyi ta a nn ko kuma kinzo zaki kashe tan ne iye! ta kama hannun zarah ta kai mata ita tace"gata ki kashe ta in san cewa ke cikakkiyar  marar hankali ce me lasisi.
Mom d'in saif dake kallon ta tace"Kome zaki kirani indai akan d'ana ne ni bazan damu ba,amma ina son in gaya miki idan har na sake ganin ta a karo na uku tare da d'ana sai dai ku nemi wata er wlh babu kuma abunda zaku iya yi,idan kuma kinyi gardama mu zuba nida ku shege ka fasa.
 Daga haka ta fita daga d'akin duk ranta a 6ace ta wuce Abban kd da isowar sa knn qofar d'akin zai shiga ya bita da kallo kana ya qarasa daga ciki yana kallon su umma yace"lafiya me kuma ya kawo ta a gidan nn"
  "D'anta ta biyo mana"
 Umman kd ta bashi amsa tare da kama hannun zarah dake ta kuka suka fita daga d'akin har Nadiya.
  Abban kd ya bisu da kallo kana ya juya gun saif yayi tsaye yana kallon saif da ya zauna kan bed tare da dafe kanshi irin cikin damuwa d'in nn,nn ya qarasa kusa dashi ya zauna ya dafa shi a hankali,saif ya d'ago idanun sa da suke jajur kuma cike tap da qwallah muryar sa na rawa sbd 6acin rai da kukan da yake ji yace"Abba ni kam wace irin uwa ce wnn na had'u da ita dan Allah kasa a d'aure ta dmn wlh na fahimci ba hankali ne da ita ba zata iya kashe zarah da gaske.
 Abban kd yace"tabbas kuwa amma kaine kasa hankalin nata ya gushe,kuma kaine zaka iya dawo mata da hankalin nata.
  Da kamar mamaki Saif yace"kmr ya Abba na bita kake nufi ko kuma na rabu da zarah wanne kake nufi ciki?
 Abban kd yace"ae dama ita zarah kun rabu....da sauri yace no Abba zarah she is still my wife wlh a bisa kuskure na rubuta mata saki kuma....is ok basai ka sake maimaita min bayani ba naji komai na kuma fahimci iya inda kake da laifi,but still zarah baza ta koma maka ba sbd a cikin bayanin da aka min da akwai inda na fahimci lallai ba son zarah kakeyi ba wata qil shaquwar zaman da kukayi ne yasa duk kabi ka damu da rabuwar auren ko kuma ince jin ita wace ce a gun umman ka yasa duk kaji idan kuka rabu baka kyauta ba shiyasa kake son a mayarda auren ko?
 A sanyaye saif yace"ba haka bane Abba"
  To yaya ne?
Ina son cikawa Abba burin sa ne.
 Ya fad'a cikin marairaicewa.
 Abban kd yace"ka gaya min gaskiya rasuwar sa ce tasa kake son cika masa burin sa ko tun kafin ya rasu ne kake son ganin ka cika masa burin nasa?
 Saif yace"eh tun kafin ya rasu"
 Abba dake kallon sa yace"meyasa zaka min qarya saif bayan kafin na tambaye ka sai da nace ka gaya min gaskiya"
  Saif yace"Abba gaskiya na gaya maka wlh"
 Abba ya girgiza kansa yace"wnn rayuwar da ka d'aukowa kanka sam bata dace da kai ba saif,idan har gaskiya ka gaya min meyasa to har Abban naka ya rasu ba abunda ya ta6a shiga tsakanin ka da zarah.
 Da sauri saif ya kalli Abban kd se kuma ya sadda kansa qasa yayi shiru bai ce masa komai ba.
 Abban kd yace"ko kuma ba haka bane da akwai?
  A hankli saif ya girgiza kansa yace"babu"
 Abban kd yayi shiru  yana kallon sa can ya jinjina kansa yace"hm saifuddeen knn a hkn ne to kake da burin samarwa Abban ka farin cikin sa har kana fad'in zaka maida auren ka da zarah bayan kulata ma baka iyayi,but shikenan dai yanzu abunda nake so dakai daga yau ka d'auke qafar ka da zowa gurin zarah dmn babu zancen maida auren ka da ita,kabar jamil dake sonta yaci gaba da zowa gurin ta har Allah yasa su sasanta tsakanin su suyi aure.
 A rikice saifudeen ya kalli Abba da yaji zancen nasa kmr saukar guduma,muryar sa na rawa yace"Abba meyasa,dan Allah kayi haquri zaman da mukayi a baya sam ba irin shi zamuyi ba yanzu wlh cike nake da burin samarwa Abba farin cikin sa.
  Abban kd yace"na gama fahimtar ka saifuddeen dan haka ka daina cutuwar kanka kana fad'ar abunda fad'a kawai kake ko an barka baza ka iya aikatawa ba,abunda kawai nake so dakai shine ko kad'an kada kayi wasa da yiwa Abbanka addu'a dmn abunda yafi buqata knn a gurin ka yanzu.
 Mahaifiyar ka kuma ina son kayi haquri ka cire komai a ranka ka mata biyaya dmn sam ban gaya maka halinta dan ka tsane ta ba sai dan ina tsoron kar wata manufa ce yasa tazo zata tafi dakai shiyasa na gaya maka dmn koda ta tafi da kai d'in zaka iya kare kanka daga sharrin ta,amma a yanda na fahimce ta bada nufin cutuwa ta dawo gare ka ba qauna ce,wacce idan ba binta kayi ba hankalinta bazai ta6a kwanciya ba haka muma da kai karan kanka,dan haka kawai kayi haquri ka bita duk lokacinda ka buqaci ganin mu kai namiji ne zaka iya zowa ka kawo mana ziyara akoyaushe amma idan zakayi aure kasan irin macen da zaka aura kar kayi irin kuskuren da Abban ka yayi da farko,da kuskuren ne yazo yana ta bamu matsala a yanzu,Allah de ya kyauta.
   Saifudeen dake jin kuka da qyar ya iya had'iye kukan yace"Abba ni gaskiya bazan iya bin wnn matar ba,burin ta fa taga cewa ta rabani da ku kwata kwata.
 Abba yace"ka ta6a ganin inda aka raba mutum da iyayen shi ae wnn sai dai mutuwa"
  Yace"to ba gashi ba Abba se biye mata kukeyi har kuna cewa zarah baza ta koma min ba"
  Cikin d'aure fuska Abba ya kalle sa yace"we are all educated dan haka kar ka sake yunqurin maida mu shashashai,abunda kawai nake son ji shine gaya min ita mahaifiyar taka a ina take nufin ka bita a can gidan ta na kano da naji ance ta kaika ka ko kuwa Maiduguri?
 Saif dake jin wani qololon baqin ciki ya danne abun yace"Nima ban sani ba kawai dai tace min ko kano d'in nake son inci gaba da zama zata yarda amma kune bata so inci gaba da kulawa wai.
 Abba yace"fad'a kawai take ita kanta tasan bazata ta6a iya rabamu dakai ba,haukar son ganin ka koma gare ta ne kawai ke d'ibar ta,dan haka ka daina tunanin wae zata iya raba mu dakai mutuwa ce kad'ai ta isa tayi hakan,snn ko barin ka da zamuyi ka koma gurin ta dan ita mahaifiyar ka ce da ta haifeka hkn yasa zamu barka ba dan masifar ta ko wani abu ba ka fahimce ni?
  Saif da duk haushi yake ji a ransa ya gyad'a masa kai kawai.
 Nan Abban kd ya tashi ya fita daga d'akin,saif da ya bisa da kallo shima ya tashi ya fita duk ransa a 6ace ya tafi sai d'akin umman kd,se ganin Abban kd yayi a can yaje duba zarah da har an mata dressing kan inda taji ciwo haka ma hannunta a samu jinin ya tsaya.
 Suna had'a ido da Abban kd ya sadda kansa qasa fuskar nn tasa ba annuri yana gudun kar Abban kd d'in yace mai me yazo yi gun zarah kuma,Abban kd kuwa shi a tunanin sa ma ko yazo yiwa umman kd sallama ne zasu wuce,wanda har ya nufi qofa ze fita se kuma ya tsaya yace da saif kafin ku wuce kace da jamil yazo ina son zamuyi magana nida shi.
  Bansan taya ma zan misalta muku abunda saif yaji ba dan ko magana ma kasa yiwa Abban kd yayi,wanda yana gama fad'a ya fita ba tare da ya jira me saif d'in zai ce ba.
  Nan umman kd da Nadiya suma suka fita daga d'akin sbd sun fahimci saif da zarah yake son zai yi magana,wacce tana ganin sun fita ta tashi da sauri itama zata fita,saif ya rigata isa bakin qofar d'akin yasa key ya rufe snn ya kama hannun ta a fusace ya tafi da ita ya manna ta a jikin bango yana kallon ta idanun sa jajur cike da qwallah with deep voice yace"ke wace irin yarinya ce mai fallasa sirrin aure da har zaki bi mutane duk ki gaya musu cewa wai ba abunda ya ta6a shiga tsakani na dake gashi duk kinsa Abba se ganin laifi ne yake akan hakan!
 Zarah da duk ta kame guri d'aya qwallah tap a idonta muryar ta na rawar kuka tace"to ba kai bane ka gaya ma umma"
  A hankli saif ya sassauta riqon da ya mata yana tuna hakane fa se kuma lokaci d'aya ya sake manna ta a jikin bangon yace"ta yaya akayi to suka san cewa har bayan rasuwar Abba ba abunda ya had'a ni da ke idan bake kika gaya musu ba!?
  Tace"to ae duk laifinka ne tun farko,da baka gaya ma umma ba da baza ma su nemi jin qarin bayani daga gare ni ba.....ke kuma wawiya shine se kika gaya musu bayan duk kece kika hana faruwar komai,to wlh bari kiji in gaya miki yanzun nn zan nunawa Abba cewa u are still my wife babu wani d'an iskan da ya isa ya aure ki nine mijinki na har abadah wlh.
  Nan kawai ya hau zare belt d'in wandon sa,a tsorace ta saki  kuka ta kame jikinta sosai tana bashi haquri dmn a tunanin ta ko dukan ta zai yi amma se ganin tayi ya jefar da belt d'in ya kuma zuge zip d'in wandon shi nn ta fahimci abunda yake niyya ai kuwa da sauri ta bud'e ido had'e da girgiza masa kai.
Bai kula ta ba sai jefa ta yayi kan bed ya haye ruwan cikinta tare da had'e bakin sa da nata dan kar tamai ihu su Abba suji bai samu yayi abunda yayi niyya ba,wanda yana had'e bakinsa da nata yakai hannun sa zai raba ta da doguwar rigar da ke jikinta,zarah bata iya zare bakinta ba se kokawa ta shiga yi dashi a hakan duk yabi ya yaga mata riga,snn ya koma kan undies d'inta suma ze yaga,nn ta samu da qyar ta zare bakinta daga nashi cikin kuka ta shiga bashi haquri tana fad'in ya daina kar ya aikata nn fa d'akin umma ne,amma fir yaqi saurararta ganin haka yasa kawai ta shiga yin ihu tana kiran umma.
  Koda su umma suka ji ihun ta suka zo a rikice sai dukan qofar suke baza su iya bud'ewa ba sbd key d'in da saif yasa,dolen su suka zagaya ta d'akin Abban kd da akwai qofa a can da zasu iya shiga d'akin,sukayi sa'a kuwa qofar a bud'e take saif gabad'aya ya manta da qofar bai rufe ba.
  Sai jin yayi sun shigo d'akin,Abban kd ya nufo shi a fusace ya 6an6anre shi daga jikin zarah tare dakai masa lafiyayyen mari yace"d'an iska me kakeyi haka get out ! in daina ganin ka a nn very stupid!!
 Idanun saif ne suka ciko tap da qwallah ya tsaya se huci yake yana kallon zarah da tuni umma ta kamata tasa bedsheet ta rufe mata jikinta,zarah ta rungume ta sosai sai kuka take tana kallon saif ya juya kawai ya fita daga d'akin,a ransa yana fad'in lallai yau kome zata zama sai dai ta zama shi Hjy zai je ya sama idan itama taqi goya mai baya to kuwa sai dai dashi har zarah a neme su a rasa dan kuwa wlh zai d'auke ta ne ya tafi da ita inda ba wanda ya sani bare ace za'a rabashi da ita.

Jamil da still yana nn cikin mota kansa had'e da sitari,duk abunda yake faruwa shi bai ma sani ba haka sam baiji shigowar saif cikin motar ba se jin yayi an rufe ganbun motar da qarfi,ya d'ago kansa da qyar ya kalli saif muryar sa a hankli yace"lafiya ka shigo mota haka ina zarah ba tare zamu koma bane?
  Saif da duk haushin jamil yake ji cikin tsawa yace"da Allah malam ni kaja mota mu bar garin nn!
  jamil ya kalle sa kawai baice masa komai ba ya lalla6a yaja motar suka hau hanyar komawa kano.
 Da shigar su garin kano ne wayar saif dake laqe tana caji ta shiga ringing wacce ya neme ta ne yau da safe shine ya ganta a under pillow.
Ya kalli wayar tashi ransa a mugun 6ace kmr bazai d'aga ba amma ganin Nusaiba ce me kiran yasa ya d'aga kiran.
  Yana d'aga kiran nata yaji sai kuka take sosai tana fad'in"Dan Allah yaya kayi sauri kazo tun d'azun se kiran numbar su Abban kd nake ban samu ba mom d'inka ce tazo da police sun tafi da umma.
 Da sauri saif yace what! a wane police station ne tasa aka je da ita?
 Tace"nima ban sani ba amma ka fara zuwa gidan ta tukun dan bata bisu ba sawa kawai tayi suka wuce da umma wae idan baka bi umarnin ta ba baza ta sa a fidda umma ba.
  Nan kawai ya tsinke kiran ya kalli jamil da ke tambayar sa lafiya wa aka rufe? Yace"bani motar inja dawo nn 6angaren yau sai na nuna mata na fita hauka wlh!.
 Cikin rashin fahimtar abunda yake faruwa jamil yayi kmr yanda saif yace,saif yaja motar a tsiyace inda Allah ne kad'ai yasa suka isa gidan mom d'in tashi lafiya.
  Ya faka motar a bakin gate ya shiga cikin gidan kmr wani zautacce se bud'e duk room d'in da ya gani yake yana neman inda zaiga mom d'in tashi har Allah yakai shi room d'in qarshe da gefen room d'in ya zama kamar wani part na daban kan yanda akayi doguwar hanya ya tafi can daban da sauran d'akuna.
  Yana bud'e d'akin yaga yanayin d'akin kmr clinic room har ma da patient kwance akan bed an sanya masa oxygen amma baya ganin fuskar patien d'in sosai sbd mom d'in sa dake tsaye a gaban patient d'in riqe da allura a hannunta zata yiwa patient d'in,wacce jin an bud'e qofar yasa ta juyo da sauri tana ganin saif ne a tsorace ta saki allurar,nn gaban saif yayi wani irin mugun fad'uwa ya tsaya cak cikin tsananin tashin hankali da tsoro ya bud'e ido yana kallon fuskar Abban sa da shine patient d'in.
[4/22, 12:44 AM] Paexer: _Monday 09/04/2018_ *«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»page«» 54*
Ina su umma suke ne?
Saif ya tambayi zarah tace"en jarida ne fa har yanzu basu barsu ba,saif dake kallon ta kafin yace komai se gasu sun shigo gabad'ayan su,nn zarah ta sauka kan gadon,su umma suka qaraso se sannu suke mishi yayinda kowannen su cike yake da tu'ajjabi,da kallon su kad'ai in kayi zaka fahimci hakan,da akwai kujeru a d'akin can gaba kad'an ta gefen gadon shi aka tsara gurin like small parlor,cos haka asibitin Abba yake duk babban d'aki na musamman haka yake,bayan sun gama mishi sannu suka zazzauna shiru cike da tunani fal a ran kowanen su,musamman Hjy da ke ta faman jinjina kanta dan al'amarin ya girgiza ta matuqa.
 Can Abban kd ya numfasa cikin jinjina kai yace"Haqiqa wannan al'amari da ya faru ba abunda zamu iya cewa sai dai muce Allah ya kyauta,shi kuma Alhj Hussain Allah ya bashi lfy ya kuma qara tsare shi damu baki d'aya,ita kuma Allah ya shirye ta.
   Amin suka fad'a snn yace"Inshaa Allah idan na samu yanda nake so gobe gobe nn zan tafi da Alhj Hussain England domin jikin nashi yana buqatar kulawa sosai duk da ko nn d'in ni mai iya kula dashi ne amma dole a can d'in zai fi samun kulawa sosai da sosai.
A hankli Saifuddeen ya d'ago kansa ya kalle sa yace"zan bika Abba"
 Abban kd yace"Aa kana buqatar ka qara samun lafiya kaima snn ina kabar zancen maida zarah d'akin ta ko kafi so sai an gama jinyar Abban naka?
  Duk da irin yanayin da saifudeen yake ciki amma lokaci d'aya yaji wani dad'i a ranshi har ma ya samu kansa da yin murmushi snn ya sadda kansa qasa cikin sosa bayan kansa irin najin kunya d'in nn yace"duk yanda kace Abba"
 Abban kd dake kallon sa yayi d'an murmushi snn ya maida duban sa gun zarah yace"baza a miki dole ba zarah kina buqatar komawa d'akin mijinki?
  Da sauri saif ya kalle ta haka ma kowa dake d'akin suka kalle ta har jamil dako qyafta idon sa baya son yi a kanta yana jin wani fad'uwar gaba a ranshi duk da yasan dolen shi zai haqura da zarah amma abun ne ya kasa daina mishi,dashi kansa baisan ya zaiyi ba sosai yake son yaga cewa ya haqura ya daina jin komai a ranshi a game da ita amma zuciyar sa ce still taqi bashi wnn damar da yake jin inama kakar sa na raye da kd zai koma can da zama gabad'aya ko zuciyar sa zata haqura idan ta daina ganin zarah.
 Zarah kuwa Abban kd na tambayar ta,ta sadda kanta qasa cikin yanayin jin kunya,ta kasa cewa komai se en yatsun ta da ta kama tana wasa dasu,wacce ko bata fad'a ba dole duk mai kallon ta yasan amsar abunda ke ranta.
D'an murmushi Abban kd yayi snn ya kalli su umma da suma ya fahimci a gurin su ba matsala suna buqatar ta koma d'in yace"to Alhmdlh jibi ranar juma'a se ayi qoqari a maida zarah d'akin ta.
 ko kafi buqatar a maida maka ita ne yau?
 Abban kd ya tambayi saifudeen,saifudeen da still kallon zarah yake ya sadda kansa qasa yace"No Abba yanda kayi d'in nn ma yayi.
 Yace"to shikenan abunda nake son gaya maka dai shine ita rayuwar aure da kake gani dole sai da haquri musamman kai da kake babba duk wani abu kaine zaka riqa haquri kana fahimtar da ita zaman rayuwar auren ba wai ka riqa biye mata ba har ka wani rubuta mata saki dan tace,kan kawai kun samu sa6ani,dan haka bari kaji in gaya maka saki ba abun wasa bane da har zaka ce wae a bisa kuskure kayi,idan har ka sake barin wnn kuskuren ya faru dakai to wlh sai dai ka nemi wata matar ba dai zarah ba dmn bazaka maida mu shashashai ba kana jina!
 Hajiya tace"gaya mishi dai ni nn dakaina zan d'auke zarah in auradda ita ga wanda yasan mutuncin ta ya kuma san darajar aure ka kuma sake wnn kuskuren ka gani.
 Saif da kansa ke qasa muryar sa a hankali yace"inshaa Allah ma hakan bazai sake faruwa ba Hjy.
 Tace"yauwa d'an albarka haka nake son ji Allah yasa ka kiyaye d'in,dan iyayen ka gasu nn dai kana gani lafiya lau suke zaune da matan su ba abunda ya ta6a had'a su amma kai sbd yaran zamani ne ku baku d'auki aure a bakin komai ba da har wae ke zarah zaki nemi saki a gun mijinki ko!
  Hjy ta fad'a cikin turawa zarah idanu.
 ae kuwa da sauri Zarah ta sadda idanun ta qasa.
Hjy da ke kallonta taci gaba da cewa to bari kiji in gaya miki idan baki sani ba ki sani Allah ya la'ani duk matar da ta nemi saki a gun mijinta akan kawai d'an wani sa6anin da bai wuce ku shirya tsakanin ku ba,dan haka ki kiyaye kar ki sake kuskure irin wnn kinji"
  A hankli zarah ta gyad'a mata kai.
  Tace"yauwa er albarka Allah yasa rayuwar auren ku ta d'ore har jannatul firdausi ya kuma sa ina da rai da lafiyar da zan ganin en kamakunne na"
 Amin suka fad'a amma saif ya riga kowa fad'a yana kallon zarah cikin sauke ajiye zuciya,se kuma a hankli ya maida duban sa gun jamil wanda shima ya d'ago idanun sa ya kalle shi,sosai saif yaji tausayin shi har yanayin fuskar sa ya nuna,jamil da ya fahimci hakan yayi murmushi kawai wanda ya qirqiro shi ne da qyar.
Da suka koma gida har washe gari mutane sai shigowa suke tayi suna ta jajanta musu abunda ya faru,sai gidan ya zamo kmr lokacinda aka yi rasuwa duk wanda yazo haka zai zauna cike da jimami da mamakin al'amarin,yayinda ake ta yiwa Abba addu'ar samun sauqi wanda har an wuce dashi England,mom d'in saif kuwa wasu su tsine mata wasu kuma suce Allah ya shirye ta,saif kuwa tausayin sa suke ji sosai har ma wasu suna samun sa a 6angaren sa suna jajanta mishi,dmn mutane da dama se a lokacin suka san cewa ba umma ce ta haife shi ba.
Ranar Friday tun da safe umma ta tura Nadiya da Nusaiba dmn su gyarawa zarah gida.
  Koda suka dawo sun samu ana yiwa zarah lalle se yaba lallen suke tayi yanda yayi kyau,awa inji ne ya zana ba mutun ba dan sosai kam lallen ya tsaru gashi akan farar fata kuma simple ba wani hayaniya har ma an kammala na hannuwa za'a fara na qafa,mai kitso na zaune tana taje mata gashin kanta zasu fara kitso ita kuma,ran zarah baqiqirin kmr zata yi kuka dan ba yanda bata yi ba ita bata son kitso umma tace faffau se anyi.
 Saif ne ya shigo falon ya tsaya yana kallon zarah da se hararar su Nusaiba take dake yaba lallen nata su har abun ma ya basu dariya dan sun fahimci haushin kitson ne yasa take jin haushin kowa.
  Wacce tana ji saif na tambayar ta abunda yake faruwa taqi tace dashi komai dan ko magana ma bata son yi.
  Su Nusaiba dake danne dariyar su suka ce"ae yaya baza ta ma magana ba haushin kowa take ji sbd kawai umma tace se an mata kitso.
  Nan ya kalli zarah kafin yake maida duban sa gun mai kitson ya ciro 5k yace"yi haquri ki tafi kinji tunda bata so"
  Mai kitso kam da murnar ta ta kar6i kud'in tana mishi godiya dan duk a kitse kitsen ta bata ta6a samun kyautar ladan kitson ta irin wnn ba,gashi bata mayi kitson ba amma ta samu har haka ae kuwa har ta miqe sei godiya take ta mishi.
 Nan se ga umma ta fito kitchen da sauri tana fad'in"kmr ya tunda bata so ta tafi se anyi kitson ba zancen fasawa"
  Zarah da har taji dad'i a ranta take ta 6ata fuska kmr zatayi kuka tana kallon umma.
Nan saif ya d'an marairaice fuska yana kallon umma yace"please umma tunda bata so a barta nima ba son kitson nake yi ba wlh nafi so taje saloon a gyara mata gashin.
  umma dake kallon sa cikin rashin damuwa tace"to shikenan mai kitso tafi abunki kawai tunda duk taron zaka zani ne.
Kana ta koma gun su Nusaiba tace"har kun dawo inace kun gyara koina yanda ya kamata?
 Suka ce eh.
 Tace"to sannun ku kuje ku huta anjima sai ku raka zarah saloon.
 Suka ce"to"snn umma ta juya ta koma kitchen.
 Yayinda saif ya gurfana a hankali kusa da zarah ya kama hannuwan ta yana kallon lallen ba tare da ya damu da su Nusaiba dake tsaye ba bare ita mai lallen se ma ciro 10k yayi ya bawa mai lallen yace"na qafa ma kiyi shi sosai yayi kyau kmr yanda kikayi na hannuwan nn"
D'auke da murmushi mai lalle tace "to" har tana mishi godiyar 10k d'in da ya bata sosai cikin nuna jin dad'i.
 Haka ma saif dad'i yake ji sosai a ranshi yau zarah zata koma gidan shi se murmushi yake yana ta kallonta haka itama.
 "Kinga so wai hm wnn ranar ce na jima ina so in gani"
Nusaiba ta fad'a can ciki tana rad'awa nadiya a kunnen ta wacce tayi murmushi kawai.
Saif da baiji me suke cewa ba yadai ji qus qus d'in su ya miqe tsaye cikin tsare su da ido yace"me kuke cewa?
 Uhm ba komai yaya Nusaiba ta fad'a tana mai d'an sosa gefen kanta d'auke  da d'an murmushi a fuskar ta.
  Ta6e bakinsa kawai saif yayi ze fita,se kuma ya juya da sauri gun zarah jin tace"wash ki d'aga min qafa a hankli mana zanji ciwo fa"
 Saif dake kallon ta yayi murmushi dan bako wani d'aga qafar nata aka yi ba asalima abunda aka d'aura qafar nata akai guntu ne ba ya da wani tsayin da har za'a iya ji mata ciwo son jiki ne kawai irin nata,da ta d'auko ko in an d'aga qafar nata za'a iya ji mata ciwo,sbd ba wani sabawa tayi da lalle ba gashi kuma yau haka ta tashi bata son jin abunda ya ta6a jikin nata.
 Saif da still murmushi na kan fuskar sa kallon ta yake a ransa yana tunanin lallai yau da dare da kmr se yayi da gaske ya cire mata duk wani tsoro da son jiki dmn ya samu ya maida ta cikakkiyar mace tare da fatar samarwa Abba farin cikin sa.
 Kana ya maida duban sa gun mai lallai yace"ki mata hankli kinji amarya ce da za'a kaita yau yau d'in nn idan kika ji mata ciwo kuwa angon nata zai sa a d'aure ki.
  Yayi mgnr ne cikin yanayin barkwanci da yasa suyin murmushi.
 Nan kawai suka jiyo sallama,bayan sun amsa sallamar snn mai yin sallamar ya shigo,Zarah na ganin wanda ya shigo d'in ta miqe tsaye da sauri cikin murna ta rungume shi.
   Ba shiri saif ya janye ta daga jikin sa cikin tsawar da bai ko san yayi ba yace"ke meye haka! waye shi da zaki wani rungume shi haka!
  "Yayana ne fa" zarah ta fad'a tana mai kallon yayan nata cike da murna,dan jiya da mutan rimin dako suka zo shine kawai bai samu zowa ba sai yau sbd yana Zariya koda yaji labarin abunda ya faru da shima ya girgiza sosai,shine yazo domin jajantawa.
 Saif ya kalle shi yace Yayanki?
 Kafin zarah tace komai se ga umma ta fito d'auke da murmushi tace"eh shine yayanta da take bima.
  Nan saif ya bashi hannu suka gaisa yana fad'in"am sorry plz ban sani bane yi haquri"
 "Ba komai"
Yayan nata ya fad'a d'auke da d'an murmushi a kan fuskar sa,saif shima ya masa murmushi,snn ya fita.
 Zarah tace"Allah yasa ban 6ata ma  tufafi ba yaya"
 Yayan nata dake sanye da fararen kaya ya kalli tufafin nasa ba inda ya 6aci dan cikin kiyayewa ta rungume shi sbd sanin akwai lalle a hannun ta.
 Yace"A'a indai ke baki 6ata lallen naki ba.
  Ta kalli lallen bai 6aci ba ta girgiza masa kai.
 Yace"to zauna a qarasa lallen ko"
Nan ba musu ta zauna had'e da fad'in"su inna fa suna lafiya?
 Yace"duk suna lafiya,kafin yake maida duban sa gun umma ya gaida ta cike da ladabi ta amsa,snn shima ya amsa gaisuwar su Nusaiba da suka gaida shi.
Daga haka Umma ta wuce dashi sama zuwa qaramin falo.
 Bayan an yiwa zarah lalle har ma sunje saloon sun dawo.
  Umma ta kira zarah a d'ikinta ta bata kazar amare ta haki da aka had'a ta musamman.
A yatsine zarah ta kalli kazar tace"inna wannan kazar fa awa an ciro a kwata.
  Umma tace bana son shashashanci maza cinye ko yanzun na d'ura miki.
  Ba yanda zarah ta iya haka ta fara cin kazar fuskar ta a yatsine har sai da ta cinye snn umma ta bata tsime ta d'aura dashi.
  Bayan ta gama shan tsimen ne umma tace to saura dilka kin ganta gata had'i ne na en Maiduguri,idan kikayi ta sau d'auya tamkar kinyi wata kina gyaran jikin ki ne sbd yanda take da kyau,dan haka tashi yanzu ki shiga bathroom ki shafata  ko'ina a jikin ki se kinyi 30 mnt sannan ko zaki wanke kiyi wanka.
 Zarah tace"wae inna har minti 30 ina bathroom d'in ga magrib ta kusa fa"
 Umma tace"shiyasa nace kiyi kiyi kije kafin magrib d'in tayi dmn ana gama sllr isha saif zai zo ya d'auke ki ne ku tafi,idan kuma kika tsaya shiririta zan zo na same ki har bathroom d'in na miki da kaina.
  A d'an shagaw6a tace"a'a inna bazan ma tsaya shiririta ba dan bana son magrib ta min ina ciki amma to lalle na fa bazai fita ba idan na shafa ta?
  Aa bazai fita ba inda haske ma zaki qara lallen ya qara fitowa maza tashi kije.
  Nan zarah ta d'auki dilkar da akayi ta kmr wani cream ta wuce bathroom.
Koda ta fito ita kanta ta tabbatar lallai dilkar mai kyauce dan kuwa jin jikinta nata take awa an sauya mata fata sbd yanda tayi wani irin laushi da tsantsi har ma wani qamshi na fita a jikin nata da duk ya qara wani haske da sheqi.
  Tana fitowa ne umma ta bata farin miski da wasu turarukkan shafawa a jiki da kowanen su da ga6ar da za'a shafa shi dmn haka ta mata bayani,zarah ta koma bathroom bayan ta shafa kowanne inda umma tace snn ta fito.
  Umma tace"to yanzu se kije kiyi sllr magrib idan kin idar se kici abinci bayan isha'i ki shirya kizo da akwai mgnr da nake son zamuyi,nasa Nusaiba ta fitar miki da kayanda zaki sa kinji.
  Zarah tace"to"snn ta fita daga d'akin.
 Koda bayan isha'i tayi ta kammala tsirinta tsaf,Nusaiba ce ta mata kwalliya se ta fito sak amayar ta se zuba qamshi take tana  zaune kan bed d'akin umma dake zaune kusa da ita tana qara bata shawarwarin yanda zata zauna lafiya da mijinta ba tare da wani yaji kansu ba.
 Zarah dake saurarenta tayi shiru jikin ta duk a sanyaye tana jin fad'uwar gaba a ranta,ta kalli umma muryar ta a sanyaye tace"inna fad'uwar gaba nake ji fa ina tsoron mahaifiyar sa da kmr in na koma akwai matsala"
 Umma,tace"um um ki daina fad'ar haka babu matsala inshaa Allah,kuma ita da ma take can a rufe ki kwantar da hankalin ki kinji babu abunda zai faru sai alheri,amma idan har kina tsoro to ki riqa karanta wnn addu'ar a duk lokacinda kikaji tsoron nata yazo miki.
 Addu'ar ita ce
_Allahumma ikfihim bima shi'ita._
To da yardar Allah,Allah zai kare ki daga gare ta ba abunda zai same ki kinji ko?
  A hankli ta gyad'a mata kai.
Nan se ga saif ya shigo d'akin d'auke da sallama a bakin shi.
  Umma ce ta amsa mishi sallamar yayinda yayi tsaye ba tare da ya iya qarasawa daga ciki ba se kallon zarah da yake tayi har baya son qiftawa,kan yanda ta mishi masifar kyau.
Yayinda ita kuma kanta ke qasa bata ko son su had'a ido,dmn kmr kar ya shigo taji fad'uwar gaban nata ya qaru sbd tasan yau kam ba me qwatar ta a hannun shi se yanda yayi da ita shiyasa ma duk take ta jin tsoron komawa.
  Saif da ke ta faman kallon ta da qyar ya iya janye idon sa cikin sauke mufashi can qasa a hankli,snn ya qarasa ciki yana mai gaida umma,wacce ta amsa tare da kallon zarah tace to tashi kuje ko"
Jiki sa6ule zarah ta miqe suka fita.
 Wacce har suna tafe cikin mota bata yarda sun had'a ido ba se shi dake ta faman kallonta riqe da lallausan hannun ta da ya kama,ya kasa sakin hannun se faman murza shi yake a hankli har suka isa gida.
[4/22, 12:44 AM] Paexer: *«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»page«» 55*
Saif da shine ke jan motar da kanshi,bayan ya faka mota ya kalli zarah wacce duk qamshin ta ya cika motar,har yana ji kmr suyi zaman su a cikin motar dmn yayi ta shaqar qamshin nata.
 Wanda ya kalle ta ne had'e da kai lallausan hannun sa  zai d'ago fuskar ta,bata barshi ba taja gyalen ta a hankali ta rufe fuskar,yayi murmushi yana jin wani irin sonta a ranshi kmr ya had'iye ta kan yanda yake hango fuskar ta a cikin gyalen sai sheqi take cike da sha'awa.
A hankli ya matsa gab da ita bakin sa saitin kunnen ta muryar sa a natse can qasa
Yace"Amarsu ta ango yau ni ake rufewa fuska,to shikenan dai ki zauna yau angon naki da kanshi zai fita ya bud'e miki mota kinji.
 Nan kawai bai jira me zata ce ba ya fita ya zagaya ya bud'e mata ganbu ya kama hannun ta ta fito ya maida ganbun ya rufe suka shiga ciki yayinda take manne a jikin sa har suka isa d'akin shi.
 Numfashi taja a hankli can ciki sbd wani irin sanyi da dadda d'an qamshi da suka tarbe ta a lokaci d'aya,d'akin yasha gyara matuqa dashi kansa yasan dole babbar baquwa ce zata sauka a cikin sa musamman yanda aka shinfid'a qatuwar darduma a nn tsakiyar d'akin kusa da bed,snacks da naman kaji har da drinks jere akai wanda da gani kasan couples ne zasu cin wnn liyafar da akayita iya ta mutum biyu kad'ai,inda ba kowa ne yayi aikin ba face saif da kanshi su Nusaiba d'akin kawai suka gyara amma shi ya jera abinci ta yanda yasan dole zai qayatar da amaryar sa zarah,wacce duk da fuskar ta a rufe take amma tana ganin komai tsarin ya kuma birge ta sosai.
  Nafila suka fara yi raka biyu suka godewa Allah da ya nuna musu wnn ranar snn suka zauna ma cin abinci ya bata ta bashi har saida sukayi kat snn saif ya yarda suka tashi daga kan dardumar.
  Zai kwashe kwanikan abincin dmn ya fitar zarah tazo zata kama mishi cike da so yaja karan hancin ta yace"Aa ki barni inyi komai yau ke amarya ce da angonki baya buqatar ki wahala"
 D'an murmushi kawai Zarah tayi bata ce masa komai ba yaje ya fitar da kayan ya dawo,tana zaune kan bed ya tafi gab da ita ya zauna tare da had'e gefen fuskokin su,hannun sa kan waist d'inta ya zagaya dashi zuwa cikin ta yana shafa cikin ya kalle ta yace"are u ok ba kyada buqatar komai?
  A hankli ta gyad'a masa kai alamar babu.
Nan ya tashi ya ciro musu kayan bacci ya bata nata shi kuma ya ajiye nasa kan bed ya hau cire kayan jikin sa yayinda ita kuma yana bata nata ta wuce bathroom,bayan ta saka kayan baccin ta fito linke da kayan da ta cire riqe dasu a hannun ta, tayi tsaye ba tare da ta iya qarasawa inda yake ba.
 Sai shi ya qarasa gurinta ya tsaya yana kallon farar rigar bancin da ya bata ta saka tayi kyau a jikin ta mai siririn hannu kmr na vest snn tsayin ta iya guiwa gata da tsantsi sosai irin na jan hakali d'in nn.
 "Cutie"
Ya fad'a cikin muryar sa mai dad'i snn cike da murmushi a fuskar sa ya kar6i kayanda ke hannunta yaje ya saka su a wardrobe.
 Ya juyo yana kallon ta still tana tsaye a inda ya barta kanta qasa se wasa take da en yatsun ta,ya qarasa tare da kama en yatsun ya d'aura musu kiss,nn ta d'ago kyawawan idanun ta farare qal ta d'aura su a cikin nashi,cikin d'aga mata gira yace"mene ne?
  Bata d'auke idanun ta akan kallon sa ba se girgiza masa kai tayi alamar ba komai,ya kama hannun ta suka je kan bed suka zauna yana kallonta yace"yau dai na fahimce ki sai wani nonnokewa kk kina tsoro ko,to gwara ma ki sake dan yau bed competition zamuyi nida ke duk wanda yafi zama gwarzo a cikin mu shi keda babbar kyautar da na tanadar,musamman idan aka samarwa Abba farin cikin sa a daren yau.
  Kallon sa kawai zarah tayi ta sadda kanta qasa dan ita ji take kmr On ne yazo mata tana fitowa bathroom taji abu yana fita a jikinta shiyasa ma ta kasa qarasawa inda yake ta tsaya tana sauraren abun.
  Saif da ya fahimci kmr akwai abu a ranta ya d'ago fuskar ta yana kallon ta da kulawa yace"mene ne zarah da akwai abunda yake damunki ne?
   Ta gyad'a masa kai tana kallon sa kafin take sadda idanunta qasa muryar ta a hankali can ciki tace"eh ina ji kmr on ne yazo min"
  "Haba dai!
Saif ya fad'a da sauri yana kallonta.
 Tace"kmr shi d'in ban sani ba dai"
  A sanyaye saif yace"inga"
Zarah tayi saurin kallon sa cikin girgiza masa kai,cikin damuwa yace"to plz jeki bathroom ki duba Allah yasa bashi bane amin.
  Yayi mgnr ne cikin marairaice wa har yana d'aga hannuwan sa sama snn ya shafa addu'ar.
  Hakan ya bawa zarah dariya ta saki murmushi har sai da dimples d'inta suka lotsa,cikin dalla mata harara saif ya kama dimples d'in ya matse yace"kina zolaya ta ne ko"
  Allah ba wasa nake maka ba zarah ta fad'a kmr zata fashe da dariya har tana rufe bakinta.
  Saif ya sake hararar ta yace"no zarah kinga bana son zolaya fa plz gaya min gaskiya ko yanzun na duba da kaina,ba kad'an ba nasa raina a matse nake wlh"
 Sosai yanayin sa ya qara bawa Zarah dariya wacce da saurin ta zata tashi daga kan gadon saif ya kamata yana qoqarin dubawa nn ta qwace kanta tana dariya ta tafi da gudu sai bathroom ta rufe.
  Lokaci d'aya ta natsu ta daina dariya ta duba,ba on bane amma pant d'inta duk ya jiqe kuma abun sai ci gaba yake da fita.
 Nan tayi shiru tana tuna tun lokacinda taci wnn kazar da kuma tsimen da tasha ta fara jin wani yanayi a jikinta kmr tana cikowa wnn abun kam bazata iya gayawa saif shi ba sai dai ta kira umma taji idan ba wata matsala bace kazar ta bata dan itakam bata ta6a ganin haka a jikinta ba.
  Nan ta bud'e  ganbu ta samu saif tsaye a bakin qofar bathroom d'in yanayin sa a sanyaye yace"shine?
 D'auke da murmushi tace"nidai aromin wayar ka na kira inn...umma"
 Tayi saurin canza sunan ne sbd har yanzu bata manta  baya son wnn sunan ba.
 Ba tare da saif yace mata komai ba ya d'auko wayar shi ya kira mata umma ya bata,ta rufe bathroom d'in ta kara wayar a kunnen ta.
 Umma na d'aga kiran tace"ya akayi ne saif?
 Zarah tace"inna nice"
 Ok Zarah ya akayi ne?
Shiru zarah tayi kmr baza ta iya fad'a ba,umma tace"kiyi magana mana zarah ina jinki,
Muryar ta a hankli mai d'auke da nuna jin kunyar maganar da zatayi tace"inna ina ganin wnn kazar ce da kika bani naci ta bani matsala dmn ina gama cinta se na fara jin wani yanayi a jikina gashi abu har yana fitar mun"
 Ta qarashe mgnr ne kmr zatayi kuka,umma tayi murmushi dan ta fahimci zarah irin masu ni'imar nn ce sosai da basa buqatar susha komai se dan ra'ayi kawai cikin kwantar mata da hankli tace"kar ki damu ba komai bane jeki kawai gun mijinki zaifi buqatar ki a haka"
 Nan kawai umma ta tsinke kiran,zarah kuwa se taji kunya sosai dan se yanzu ta fahimci abunda ke fita a jikinta a islamiyya duk an fayyace musu komai a fannin fiqihu.
 Nan ta bud'e bathroom ta fito ta samu saif zaune kan bed bata iya had'a ido dashi ba sai wayar sa ta miqa masa ta rage hasken d'akin ta kwanta,saif da ya bita da kallo jikin sa duk a sa6ule yaje ya kwanta a bayanta had'e da rungume ta a jikin sa muryar sa a hankali yace"zarah gaya min me kk tsoro ne da har ba kya son wani abu ya shiga tsakani na da ke kaddai kan wnn matar ne?
   A hankali ta juyo tana kallon shi tace"A'a ba haka bane"
  Yace"to idan ba haka bane meyasa kika kira umma?
 Tace"abu na manta fa a gida shine nace a ajiye min"
 Yace"to kaddai On d'in ne da gaske naga kin kwanta kawai baki ce min komai ba"
  Zarah dake kallon sa tayi murmushi cikin ware en yatsun ta tace"uheeem nima ban sani ba"
  Nan kawai ta juya,saif da ya fahimci ba wani On da yazo mata ya koma juyota ya lakato hancin ta yana murmushi yace"wato ni kike zolaya ko har ki fad'ar min da gaba lallai ni kuma zan rama da zafi zan miki se kinyi kuka"
  A shagwa6e ta marairaice fuska kafin tace"komai se jin bakinsa tayi a nata ya cafki harshen ta,nn kawai ta lumshe idanun ta a hankali itama ta cafki nasa harshen suka hau kissing d'in juna a hnkli cikin natsuwa,yayinda saif yakai hannun sa a natse ya kama hannun rigar baccinta yana zare mata hannun a hankali har ya sa6ule mata rigar gabadaya,ya shiga shafa jikinta yana shinshinar qamshin jikinta ta koina musamman dukiyar fulanin ta,da yaji qamshin gurin yafi rikitar dashi,jikin sa na 6ari yasa harshen sa akan dukiyar fulanin nata yana mata wani irin salo mai wuyar fassarawa,zarah na jinsa ta kasa hanashi sema narke masa da tayi,idanuwan ta a lumshe tana fidda numfashi a hankali can ciki,wacce tun tana narke mishi har ta fara kama mishi suka hau romancing d'in juna sosai kmr zasu had'iye kan su da gabadayan su sun fita hayyacin su mussaman saif da duk ya rikice a kid'ime jikin sa na 6ari ya nufi hanyar da take rufe bam cikin kasa control d'in kansa yayi yayi ya shiga ya kasa kawai ya shige ta da qarfi,ae kuwa ba shiri zarah ta saki qara ta rirriqe shi tamkar zata shige jikin sa,saif da duk baya hayyacin bai iya dakatawa ba sbd yanda yajita sharkaf da lema se aikin sa ya hau yi baji ba gani,yana faman sambatu da yake jin kukanta kmr sambatu take ita ma,ae kuwa duk yabi ya qara rikicewa ba tare da ya iya barinta ba har saida yaji he is totally satisfied,snn ya dakata tare da rungume ta qam a qirjinsa sai kissing d'inta yake yana zuba mata albarka.
  Cikin kuka sosai zarah ta ture shi,tare da juya mishi baya,nn saif ya tashi zaune da sauri ya janyota ta jikin sa  yana fad'in"me ya faru ne zarah kaddai naji maki ciwo ne?
  Ture shi ta koma yi cikin kuka ta tafi nesa dashi tare da jan blanket ta rufe jikinta,nn saif shima ya samu abu ya rufa jikinsa snn ya kunna wutar d'akin,ya tsaida idanun sa cak yana kallon jinin da ya 6ata farin bedsheets d'inda ke shimfid'e akan gadon,haka ma zarah duk kukan da take haka ta tsaya tana kallon jinin kana ta kalli saif ta fashe masa da wani sabon kuka,cike da son ya rarrashe ta ya matso kusa da ita,da sauri cikin fushi ta miqe a niyyar zata bar d'akin bata san lokacinda ta kai gurfane qasa ba cikin fasa er qara tana yarfi da hannu,da sauri saif ya sauko daga kan gadon yazo gab da ita kmn yanda take a gurfane ya gurfana shima snn ya tafi da ita jikin sa cikin muryar rarrashi yace"am sorry zarah ban san na ji maki ciwo ba wlh yi haquri kinji muje na saki a ruwan zafi....bana so marar tausayi ae da sanin ka kaji min ciwo tunda dama da zafi kace zaka min.
Zarah ta fad'a tare da janye jikinta daga nashi tana kuka.
Cikin damuwa saif yace"haba zarah wnn fa wasa nake miki kema kin sani"
  Tace"ba wani wasa tunda ka aikata min ni bazan d'auki abun a wasa ba.
  Yace"wlh bada niyya na miki ba zarah trust me na kasa control d'in kaina ne"
Tace"ae kam dole tunda dama wnn abun ka damu dashi bani ba duk irin kukan da nake ma ina roqon ka kayi banza dani,na mutu ma oho a gurinka baka damu ba.
  Tayi maganar ne cikin kuka mai cike da shagwa6a.
  Saif ya rungume ta yana fad'in"yi haquri ba haka bane ke d'in ce ta daban da duk na rikice na kasa binki a hankali amma na miki alqawarin gobe idan zamuyi a hankli zan miki.
 Da sauri zarah ta d'ago daga kan jikin sa ta kalle shi cikin bud'e ido tace"gobe cab wlh kayi kai kad'ai bada ni ba ni bazan ma sake yi ba har abadah"
 Saif dake mata wasa sosai ta bashi dariya yanayin yanda tayi magana ya sake maida ta jikinsa yace"ta yaya zanyi ni kad'ai ke d'in dai zanyi dake"
   Tace"naqi ni bazan sake ba"
Yayi murmushi yace"to muje muyi wanka dare nayi"
  Maqale kafad'a tayi tare da qara lafewa a jikinsa alamar bazata ba,yace"yi haquri dai kinsan ba kyau kwana da najasa"
  Ta kalle sa se kuma da saurin ta ta sadda idanun ta qasa dan duk se taji kunyar shi.
  Muryar ta a hankali can qasa tace"ni ina tsoron miqewa kaje kayi naka tukun zanje daga baya"
 Saif yace"kin manta mijin naki qarfi ne dashi muje kawai,ya tallabe ta cak ya wuce da ita bathroom.
  Koda suka gama wanka suka fito da qafafun ta take takawa amma a hankli cikin lalla6awa taje kan sofa ta kwanta.
  Saif da ya bita da kallo duk tausayin ta ne a ranshi,ya yaye white bedsheets d'inda ya lallace yaje ya saka a washing machine snn ya shinfid'a wani ya d'auko zarah da tuni tayi bacci ya d'aura ta akan gadon ya kwanta gab da ita tare da saka ta gabad'aya a cikin faffad'an qirjinsa ya rungume kmr wata er baby yana shafa gadon bayanta a hankali cike da jin qaunar ta a ranshi daga haka har shima yayi bacci.
[4/22, 12:44 AM] Paexer: _Friday 13/04/2018_ *«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»page«» 56*
Washe gari da asuba saif ne ya fara farkawa sbd kiraye kirayen sllr da ake.
  Wanda yana bud'e idanun sa akan zarah ya fara sauke su yana kallonta gashin kanta duk ya rufe mata fuska,yakai hannun sa a hankali ya yaye mata gashin,snn cikin yanayin damuwa ya shiga ta6a jikinta da yaji duk zafi.
Yayi shiru kawai yana ta kallonta can ya tashi ya nufi bathroom ya d'auro arwala.
 Koda ya fito ya samu zarah ta farka tana zaune can qarshen gado ta had'e kanta da guiwa.
  Ya qarasa gurinta ya zauna kan bedside drawer tare da dafa ta,ta d'ago a hankali tana kallon shi,da kulawa yace sannu kinji je kiyi arwala kizo muyi sallah se na baki magani kisha.
 Nan ta tashi a natse cikin tafiyar ta da take d'an lalla6awa ta nufi bathroom.
 Saif da ya bita da kallo a hankli ya sauke numfashi yana tunanin maganin da zai bata jikin nata yayi saurin sakewa.
 Nan ya tashi daga kan bedside drawer d'inda yake zaune ya ciro er wata transparent cute box da yake ajiye magunguna a ciki,ya ajiye ta a nn kan bedside drawer snn ya nufi wardrobe ya ciro white boxer short d'in shi da farar jallabiya ya zare towel d'in jikin sa snn ya saka.
Itama zarah yaje d'akinta ya d'auko mata qaton hijab d'in ta na sallah da kuma doguwar riga marar nauyi da zata saka.
 Bayan sunyi sallah sun idar ya bata magani tasha suka koma bacci.
 Can cikin baccin su da suka jima suna yi saif ya soma jin qarar doorbell,a hankli ya zare jikin sa daga na zarah gudun kar ta tashi.
  Koda ya fito ya bud'e qofa Nusaiba ce da nadiya,suka gaida shi bai amsa ba se ma sha musu toka da yayi yace"me kuka zo yi min a gida tun da sassafe haka?
  "Cab lallai yaya ba makawa ka angon ce sha biyun rana muke fa"
Nusaiba ta fad'a a ranta cikin danne dariyar da take ji a ran nata.
  Kafin a fili take cewa"amma yaya ae sha biyun rana muke yanzu har muna ganin ma munyi lattin kawo muku breakfast d'inku.
 Saif da ya d'auka ko sunzo ne kawai se a lokacin ya lura da basket d'in abinci a hannun ta,snn ya juya ya kalli agogon bangon da ke manne a falon yaga sha biyu tayi kuwa kmr yanda ta fad'a.
  Nan kawai bai ce dasu komai ba ya basu hanya suka shigo suka kai abinci kan dining suka ajiye.
  Saif kuwa yana basu hanya ya wuce sama zuwa d'akin shi.
 Ya samu zarah ta tashi daga bacci har ma ta sauka kan bed tana riqe da qaton hijab d'in ta zata saka.
 Ya qarasa gurin ta ya kar6i hijabin yace"ina zaki je ne?
  Tace"basu nusaiba ne suka zo ba?
  Yace"sune amma bari muyi wanka na qara gasa miki jikin ki ko zaki iya takawa yanda ya kamata,kafin kk zuwa gurin su ko.
 Jikin ta a sanyaye ta sadda kanta qasa cikin wasa da en yatsun ta tace"ni bazan iya sake shiga ruwan zafi ba gurin yana min zafi sosai idan na shiga.
 Saif dake kallon ta ya janyo ta jikin sa cikin kwantar da murya yace"sorry zarah kinsan zafi ke fidda zafi idan kika sake shiga ruwan zafi shi zaisa gurin ya daina miki zafi kinji muje bazan sa miki ruwa masu zafi kmr na jiya ba.
  Nan ya tafi da ita bathroom bayan sun cire tufafi,saif ya had'a musu ruwan zafi a bathtub,ya kama hannun ta suka shiga,cikin shakku zarah ta zauna cikin ruwan da saurin ta zata miqe saif ya riqe ta,wanda duk da bathroom d'in ba wani haske dim light ce,amma har yana ganin yanda idanun ta suka ciko da qwallah,snn cike da jin zafin ruwan ta qanqame shi sosai tare da cusa fuskar ta gabad'aya a cikin qirjinsa ta saki kuka a hankli tana fad'in"ka barni in fita dan Allah ruwan nn sun min zafi"
  Rarrashin ta Saif ya shiga yi yayinda ya qara rungume ta a jikin sa yana mai shafa gadon bayan ta a natse cikin ci gaba da rarrashin ta har ya samu ta d'an saki jikin ta,suka d'an jima a cikin ruwan zaune snn sukayi wanka.
 Suna fitowa zarah ta saka qaton hijab d'inta na sallah sbd towel d'in jikinta guntu ne sosai byn ta saka hijab ta d'auki tufafin ta ta wuce zuwa d'akin ta.
  Ta samu su Nusaiba se fira suke tayi suna ganin ta sukayi shiru suna kallon yanda take takawa a hankli dan still tafiyan taqi bi daidai ta tsaya cikin dalla musu harara tace"kallon fa?
  Cikin gimtse dariyar da suke ji suka ce"a'a ba komai breakfast ne muka kawo muku yana can mun ajiye muku kan dining,bari ma mu tashi mu tafi drivern ki dake kaiki school ne umma ta kira ya kawo mu yana can a waje yana jiran mu.
 Cikin marairaice fuska zarah tace"haba dai ba a nn zaku yini ba?
  Nusaiba ta riqe baki tace"yini fa a gidan ango da amarya hm um rufa mana asiri,ae da qyar ma muka samu umma ta bar mu muka zo a niyyar ta driver kawai zata turo ya kawo muku abincin,shine muko da son ganin qwaf muka dage har ta barmu muka zo mun gani kuma sai anjima Allah ya sauke gajiya yasa an samarwa Abba farin cikin sa a daren jiya amin,suka tofa da sauri suna dariya snn suka kwashi gyaleluwan su suka fita aguje zarah ta d'auki pillows se jifan su take cikin dariya tana fad'in"magulmata kawai se na rama ae auren zakuyi kuma.
  Saif dake d'akin sa yana kallon su a laptop yayi murmushi tare da girgiza kansa dan dama da ganin su yasan cewa gulma ce kawai ta kawo su ba wani breakfast da suka zo kawowa.
  Nan ya rufe laptop d'in shi ya tashi ya shirya cikin qananun kaya se zuba qamshi yake ya nufi d'akin zarah ya samu itama har ta shirya tana tsaye a gaban dressing mirror sanye cikin atamfa d'inkin riga da skirt da sukayi d'as a jikinta haka ma d'aurin d'an kwalin da tayi mai steps da take ganin anayi ta jashi yayi  baya gaban gashin kanta ya kwanta sosai yayi kyau.
 Tana kallon saif a jikin mirror ya qaraso gurin ta ya rungumeta ta baya tare da lumshe idanun sa a hankli yana shaqar qamshin turaren ta,snn a natse ya bud'e idanun sa yana kallonta ta jikin mirror bakin sa saitin kunnen ta cikin lallausar murya yace"kinyi kyau sosai cutie gaya min meye sirrin jiya duk kinbi kin rikitani da qamshin nn naki haka ma yau da nake jin kmr bazan iya haqura har dare yayi ban baki goron wnn kwalliyar da qamshin turaren nn naki mai rikitani ba.
  Zarah dake kallon sa ta jikin mirror ta juyo d'auke da murmushi ta saqalo hannayen ta a bayan wuyan shi tana kallon sa tace"wane irin goro ne da baza a bani ba har sai dare yayi ni ko yanzu ka bani ina so"
  Saif dake riqe da waist d'inta d'auke da murmushi yace"da gaske kina so in baki yanzu?
  Lumshe idanun ta tayi a hankali ta koma ware su a kan shi alamar eh.
 A hankali yaja karan hancin ta yace"to kimin promise baza kimin kuka kmn jiya ba kema zakiyi enjoying kmr yanda nayi ko"
 Fuskar ta a d'an shagwa6e cikin rashin fahimta tace"ban gane ba me kake nufi?
 Sai da yakai bakin sa a kunnen ta cikin rad'a yace"ina nufin wnn abun da mukayi jiya har kika min kuka shine goron"
 Da sauri ta ture shi cike da shagwa6a tace"naqi bana son goron nida ko sauqi ma banji ba"
  Cikin dariya ya rungumo ta yana fad'in amma shine na ganki kinbi su Nusaiba da gudu"
 Zarah wacce hankalin ta bai ko bata ya akayi ya gansu ba,da sauri tace"wlh a'a sune sukayi gudu bani ba ni pillows kawai na d'auka ina jifan su."
  Ta qarashe mgnr cikin turo baki tana wasa da en yatsun ta.
  Saif dake kallon d'an bakin nata cikin sha'awa ya tafi kmn zai had'e bakinta da nashi yana fad'in"to ai tunda kince kina son goron zan baki bazan iya hana miki ba.
 Da saurin ta ta kauce,muryar ta kmr zatayi kuka tana fad'in"uhm ka rabu dani bana so har abadah ni bazan sake wnn abun ba.
 Saif ya tsaya cak yana kallon ta idanun ta kuwa har sun ciko da qwallah,a natse yayi murmushi yace"ni da wasa nake miki wannan ne goron da zan baki"
   Nan kawai ya ciro  abu a aljihun sa d'an qarami kmr gidan zobe yana bud'ewa kuwa zobe ne a ciki diamond ring mai kyau se qyalqyali yake ya kama d'an yatsan ta second to d last one yasa mata.
  D'auke da murmushi zarah ke kallon zoben yayi d'as akan d'an yatsan ta,ta kalli saif cikin nuna jin dad'i ta mishi godiya.
  Baice mata komai ba se en yatsun sa biyu yakai kan dimples d'inta ya lotsa yana murmushi ya kama hannun ta suka tafi cin abinci.
Da dare bayan isha'i saif baya gidan ya tafi dubo jamil da baya jin dad'i dan har anyi admitting d'inshi a asibiti.
  Koda ya dawo kai tsaye d'akin zarah ya wuce riqe da fararen leda biyu a hannun shi,d'ayar gasasshiyar kaza ce d'ayar kuma hollandia yogurt ce me sanyi a ciki.
 Ya sami zarah har tayi shirin bacci tana zaune kan bed tana karatun handouts d'in da tasan ance za'a musu tests a kansu kafin rasuwar Abba.
 Yaje gab da ita ya zauna,ta d'ago kanta a natse tana kallon shi tace"sannu da dawowa ya jikin yaya jamil d'in?
 A sanyaye yace"to Alhmdlh dai za'a ce amma jikin nasa se a hankali"
 Tace"me yake damun sa ne?
 Shiru kawai saif yayi yana kallonta can ya numfasa yace"zazza6i ne"
 Tace"Ayya Allah ya bashi lafiya.
 Saif yace"Amin tashi muje d'akina"
   Kallon sa tayi muryar ta a hnkli tace"um um ka tafi kawai ni karatu nakeyi sbd nasan anyi wasu tests bada ni ba ran Monday idan na tafi dole sai na nemi malaman na musu bayanin uzurina ko zan samu su min.
  Saif dake kallonta yace"to ae ko a d'akina zaki iya ci gaba da karatun ki a can kinga idan ma na fito wanka se na tayaki karatun ina qara fahimtar dake wasu abubuwan koh"
  zarah dake kallon sa tayi shiru ita kam tsoron binsa d'akin sa take dan ganin take kmr abunda ya faru jiya ne zai sake faruwa gashi har  yanzu ita kad'ai tasan me take ji a gurin.
  Saif dake kallon ta take ya fahimci abunda ke ranta ya lakato hancin ta yace"an tsoro to tashi muje ni ba abunda zan miki se kace ni nafi kowa rashin tausayi ko gurin ya daina miki zafi ne?
  Da saurinta ta girgiza masa kai har sai da abun ya bashi dariya.
  Ya kama hannun ta suka tafi d'akin shi.
 Bayan yayi wanka sukaci kazar su da suke korawa da hollandia yoghurt har saida sukayi qat snn suka hau yin karatu,by 12 sukayi bacci.
 Ranar Monday bayan ya kaita school suna cikin mota bata riga ta fita ba ya kalle ta yace"Allah yasa kina tare da wnn wayar taki da na fashe tun gida ina son na tambaye ki na manta"
  Tace"eh nazo da ita a niyyar zan  kunna inga ko zata kawo in samu ta kiran driver idan mun gama lectures.
  Yace"ok to bani wayar"
  Nan zarah ta ciro wayar ba tare da ta tambaye shi abunda zai yi da ita ba ta bashi.
 Ya kar6a ya cire sim card snn ya bud'e drawer motar ya ciro waya sabuwa fil a cikin kwalinta exactly irin tashi da yake aiki da ita komai sak.
  Bayan ya saka mata sim card d'in ta akan wayar snn ya saka numbar shi yayi saving ya bata yace"wnn wayar ki ce da na saya miki,numba ta tana a ciki nayi saving zaki ga sunan,idan kun gama lectures se ki kirani.
  Zarah ta kar6i wayar cike da jin dad'i ta mishi godiya,wacce lokaci d'aya ta fahimci irin wayar sa ce tace"amma wayar nn irin taka ce fa ta min tsada meyasa baka saya min dai dai dani ba.
 D'auke da murmushi saif yaja karan hancinta yace sbd ke d'in tsadaddiya ce shiyasa na saya miki dai dai dake.
  Zarah tayi murmushi tace"nagode"
  Yace"um um ni bana son irin wnn godiyar kimin wacce ta dace dani"
 Zarah da still murmushi na kan fuskar ta tace"wace iri knn gaya min in maka"
  Beyi magana ba se lips d'in sa ya nuna alamar ta mishi kiss.
 A d'an shagwa6e tace"kayi haquri bazan iya ba"
 Cikin shan toka kmr qaramin yaro yace"baki gode ba knn"
  Da saurin tace"haba dai nagode wlh amma bazan iya maka ba kaga fa a cikin makaranta muke za'a iya hango mu"
 Yace"to naji idan munje gida inda ba'a ganin mu se kimin amma ki sani bashi kad'ai nake so ba harda....ya qarashe mgnr a cikin kunnen ta,da saurin ta cikin girgiza kai tace"wlh a'a ni bazan sake wnn abun ba"
 Nan kawai kae tsaye ba shiri yaji saukar kiss gefen kuncen shi tayi mishi cikin sauri da shagwa6a ta d'ago tana fad'in shikenan nama yi maka ba zancen in munje gida wlh.
 Sosai abun ya bawa saif dariya ya hau darawa abun shi sosai kuwa.
  Zarah ta tsaya se kallon sa take tayi cike da sha'awa dmn bata ta6a ganin irin dariyar sa hakaba,ba kad'an ba ya mata kyau.
  Ya tsaigaita dariyar yana kallonta yace"to shikenan is ok yanzu idan kin bincika anyi tests d'in ba kya nn se ki kirani a waya inzo  in sami malaman muyi magana su miki tests d'in koh.
  A hnkli ta gyad'a masa kai snn ta fita daga cikin motar ya bita da kallo d'auke da murmushi a fuskar sa har sai da ta wuce snn yaja motar sa ya tafi.
 Bayan sati biyu,ranar talata guraren qarfe tara zarah na zaune a falo cikin er rigar ta ta bacci wacce da kad'an ta wuce guiwa,tasa handout a gaba se karatu take da kullum aikin knn.
  Saif da ya fito daga d'akin sa sanye cikin kayan bacci shima,yayi tsaye yana kallonta cike da son kasancewa da ita sbd tun first night d'in su bai sake samun ta ba,kullum dare haka zai barta tana ta yin karatu yana kama mata ta hanyar qara fahimtar da ita sbd sosai ya fahimci tana son karatu ga kuma tests d'inda suke tayi da exam d'in da ta gabato musu shiyasa ko kad'an baya son takurata da zancen haqqin shi,da yasan se sunyi rigima kafin yake samu ta barshi.
 A hankali ya sauke numfashi ya qarasa daga cikin falon yaje gab da ita ya zauna.
 Ta d'ago d'auke da murmushi tace"yauwa dear kmr kasan ina son ganin ka wlh har ina batun inje in same ka,wani topic ne nake son ka qara fahimtar dani dan Allah ka ganshi ta bud'e handout d'in tana nuna mishi.
  Saif dake kallonta ya kar6i handout d'in ya ajiye can gefe.
Tace"meye haka dear?
Yace"cutie a matse nake wlh bazan iya nuna miki komai ba.
 Tace"Ayyah to ai da kaje ka sauke in ka kammala sei ka nuna min"
  Yace"No cutie ba wnn ba haqqina fa nake nufi ya kamata ki barni in qara samu haka"
  Ras taji gabanta ya fad'i tasha mishi toka tace"haba dai dear nifa na gaya maka bazan sake wnn abun ba kayi haquri"
  Cikin yanayin damuwa Saif yace"haba cutie kmr ya nayi haquri nifa ba dutse bane da zan iya binki yanda kk so"
 Kauda fuskar ta kawai tayi gefe ya janyo ta cikin rarrashi yace"yi haquri bazan miki da zafi ba a hankali zan miki kinji"
  A shagwa6e cikin doddoka qafafun ta tace"nifa dear banji sauqi ba kuma d'azun na fad'i a bathroom qafafu na duk ciwo suke min ko d'aga su ma bana iya yi yanzu haka.
  Murmushi saif yayi yana kallon en qafafunta da ta gama doddokawa yace"amma shine kk doddoka qafafun?
  Tace"to ae kaine kasa"
  Yace"to naji ni nasa can fa wane irin sauqi ne baki ji ba har yau sati biyu"
  Shaye da toka tace"to zan maka qarya ne bayan kasan....se tayi shiru bata qarasa ba se fuskar ta da ta kauda gefe cikin fushi.
  Saif da ya fahimci me take son qarasawa ya danne dariyar da yake ji ya girgiza kansa d'auke da murmushi yace"cutie cutie ae koni nafi kowa big thing bazai sa kiyi har sati biyu baki ji sauqi ba,nifa mijinki ne bafa rape d'inki nayi ba bare har hakan ta kasance"
  Qwallah cike a idon ta ta kalle shi tace"to naji qarya na ma"
  Nan kawai ta miqe zata bar gurin ya riqo ta da sauri ya maida ta ya zaunar snn ya tafi da ita jikin sa yana kallonta a natse cikin rarrashi yace"am sorry cutie ba ina nufin kimmin qarya bane ae nasan tsoro ne yasa kikace bakiji sauqi ba sbd ganin kk kamar zaki sake jin zafi kamar na farko but ba haka bane,wnn karon bazaki ji zafi kmr farko ba kuma a hankali zan miki kinji plz yi haquri muje"
 A shagwa6e cikin narke mishi tace"uhm ni gaskiya dear um um ina tsoro nasan zanji zafi ko yaya ne gashi fa exam zamu fara ka sani ran monday"
 Yace"amma cutie ae na fiki uzuri nifa gobe goben nn kinsan tafiya zanyi haka kk son in tafi cikin kewar ki"
 Ta kalle sa cikin share qwallar da suka zubo mata tace"ina zaka je?
Wae ban gaya miki ba sorry England zanje duba Abba ance yana samun sauqi amma dai bai farfad'o ba har yanzun tukun.
 Cikin marairaice fuska tace"zan bika dan Allah nima ina so in ganshi.
 Yace"no cutie bazai yiyu ba exam zaku fara gashi kuma baki ta6a fita waje ba dole sai an miki passport da sauran su da baza'a iya yinsu gobe gobe kae tsaye ba,kawai dai idan na dawo bayan kun gama exam dai dai an miki komai se mu tafi koh?
 A hankli ta gyad'a masa kai tana kallon sa muryar ta a sanyaye tace"to in ka je se yaushe zaka dawo?
  Just 3 dayz zanyi bazan jima ba kinga se in maida ki gida gun umma ki riqa zuwa school daga can ko kinfi so ki zauna a nn?
  Da saurin ta ta girgiza masa kai alamar a'a.
 Yace"yauwa to tashi muje d'akina in duba lafiyar abuna ko"
  Yayi mgnr ne cikin murmushi had'e da lakato hancin ta,bata iya kallon shi ba se murmushi tayi itama,cikin yanayin jin kunya ta 6oye fuskar ta a qirjinsa kana ta d'auki handout d'inta ya kama hannun ta bakin sa wasai suka wuce.
[4/22, 12:44 AM] Paexer: _Tuesday 17/04/2018_
*«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»page«» 58*
Nusaiba dake kallonta ta girgiza kanta kawai snn ta tashi taje tayi shirin bacci tazo ta kwanta taci gaba da karatun novel d'in da take karantawa a waya wacce har ta gama karatun bacci ya kwashe ta zarah bata gama waya ba.
 
Washe gari Nusaiba ce da umma zaune kan dining suna jiran fitowar zarah suyi breakfast har umma ta gaji da jiran,ta kalli Nusaiba tace"wae kuwa kin tashe ta wane irin bacci ne ma takeyi haka har qarfe goma sha d'aya.
 Nusaiba tace"hm umma waya sukayi tayi jiya ita da yaya har nayi bacci ni ban san ma sanda suka gama wayar ba,sllr asuba ma da qyar ta iya yi kuma tana idarwa taci gaba da yin bacci,bayan na tashe ta tayi wanka ta shirye ta kuma sake komawa,wata qil ma ko yanzun sake komawa baccin tayi ina ga sai kinje da kan....bata qarasa zancen ba kawai taga zarah tsaye wacce ta dalla mata harara snn taja kujera ta zauna.
 Bayan ta gaida umma ta amsa snn tace"nikam inna wae shekara nawa na bawa Nusaiba?
 Umma ta kalle ta tace"shekara biyu kika bata har ma da en watanni.
Zarah tace"to ama cire watannin inna shekara biyun da na bata ma ya isa ace ba raini tsakanin ni da ita,amma dan ta raina ni shine hadda kawo gulma ta a gurin ki.
  Ta qarashe mgnr ne tana mai kallon Nusaiba da ta hau yin dariya cikin dalla mata harara tace"au dariya ma kk yi zan fad'a fa"
  Take Nusaiba ta daina dariyar da take ta marairaice fuska sosai cikin yanayin begging bata so zarah ta fad'a.
  Umma dake kallon su tace"me ake 6oyewa ne ba'a so a fad'a min kaddai kina kashe kunne ne kina sauraren duk firar da sukeyi ita da mijin nata.
  Da sauri Nusaiba tace"cabd'i wlh ni umma komai ma bana jin me take cewa shi kawai ke jin me take fad'a shida take yin wayar dashi,gamu a gado d'aya kuwa se bakinta kawai da nake ganin yana motsi.....wayyo Nusaiba ta fad'a tare da saurin duqawa ta riqe qafar ta sbd yanda zarah ta daga mata qafar ta akan tata qafar.
  Umma dake kallon su tayi murmushi had'e da girgiza kanta.
 Zarah ta kalle ta cikin yanayin shagwa6a tace"Allah inna kar ki yarda da abunda ta fad'a sheri kawai take min"
 Umma tace"barta ai itama suna gama makaranta auren za'a mata inga sa idon"
  Da sauri cikin zaro ido Nusaiba ta kalli umma tace"haba dai umma dan Allah ki bar wnn zancen ni gaskiya se na qara gaba.
  A d'akin mijin naki ba...zarah ta fad'a had'e da yi mata gwalo.
  Kallonta kawai Nusaiba tayi snn ta kalli umma kmr zata yi kuka tace"amma dai umma da wasa kk ko?
  Umma tace"ina wasa dake ne,tuni muka gama yanke shawara da Abban ki wanda idan Allah ya tashi kafad'ar shi ya samu lafiya kina gama makaranta sai zancen auren ki,dan ma'aruf kam ya tashi,haka mai neman Nadiya jira kawai yake ta gama makarantar itama a had'a ku duka ayi muku auren can kwaci gaba da yin karatu idan mazajen naku sun amince.
   Lokaci d'aya Nusaiba ta fashe da kuka ta tashi tana fad'in"haba umma wane irin abune mutum da gama secondary amai aure wnn ae se en sokoto ni kam gaskiya bana so nama fasa da yaya ma'aruf d'in yaje can ya nemi wata da ta shirya auren nashi bani ba.
  Nan kawai ta bar gurin cikin kuka tana ci gaba da gunguni.
 Kallo kawai suka bita dashi kana zarah ta kalli umma cikin sauke numfashi tace"inna dan Allah da gaske suna gama makaranta aure za'a musu?
  Da gaske ne mana zarah mazanjen gabad'aya sun shirya yaran kawai suke ta jira tuntuni.
  Zarah tayi shiru can tace"amma inna to karatun su fa ya kamata abar su su qara gaba tukun"
  Zarah da akwai abunda yafi aure ne ae duk darajar 'ya mace shine d'akin mijinta.
  A sanyaye zarah tace"hakane inna amma naga kmr Nusaiba tasa ranta sosai akan ta qara gaba wanda ba lallai bane idan anyi auren ko mazajen nasu zasu barsu.
 Umma tace"dukkan su basu da matsala mazajen nasu masu son su ci gaba da yin karatu ne,ae Nusaiba d'in ta duk san yanda ma'aruf keson ta da karatu auren ne dai bata so na rasa meyasa duk aka mata zancen aure se anyi rigima da ita bayan kuwa duk wani girma da ake so a gun 'ya mace Nusaiba ta kammala shi se kace ba 'yar shekara sha biyar ba,shine take ganin anyi mata sauri bayan kuwa kwanciyar hankalin mu shine muga cewa mun auradda ita,idan anyi auren can ta ci gaba da yin karatun ta,mu dai mun sauke nauyin da Allah ya d'aura mana ba ruwan mu da wani banzan shirmen ta ko kukan jini zatayi ita ta sani aure ba fashi ita da ma'aruf da yardar Allah kuwa su kammala jarrabawa kawai.
 Shiru kawai zarah tayi bata sake cewa komai ba,se breakfast da suka soma yi suna kammalawa ta d'ibarwa Nusaiba nata taje mata dashi d'aki.
 Da shigar ta d'akin ta sami Nusaiba ta gama waya knn ta cillar da wayar gefe  da alama ma'aruf ne ta kira ta balbale shi,dan tana cillar da wayar se ga kiran sa yana shigowa nn kawai ta tsinke kiran ta kuma kashe wayar gabad'aya ta bud'e beside drawer ta saka wayar a ciki snn ta maida ta rufe.
 Se a snn zarah ta qarasa gurinta ta zauna tana kallonta cike da niyyar zata rarrashe ta ta bata magana,se ganin tayi Nusaiba ta kar6e breakfast d'inda ke hannun ta da ta kai mata,ta lanqwashe qafafu tare da ajiye plate d'in a gaban ta cikin share qwallah tana fad'in"wlh ni bazan ma sa kaina a damuwa ba ai ba kai kad'ai bane d'a namiji se kaje ka nemi wacce zakuyi auren kaida ita bani ba.
 Zarah dake kallon  ta har zatayi magana...Nusaiba tayi saurin katse ta da cewa"plz dan Allah 6ter yi haquri kar kice min komai na wuce gurin bana so a maida zance baya.
  Nan kawai ta hau cin breakfast d'inta zarah tayi shiru se kallonta ta kawai da take har ta kammala ta tashi taje bathroom ta dawo tana d'an d'ingishi ta kalli zarah cikin yanayin shagwa6a tace"6ter ashe dai sosai kika daka min qafa kinga wae har d'ingishi nake.
  Zarah tayi dariya tace"kad'an kenan daga cikin muguntar da yayanki yake min amma shine har kin manta da muguntar da yake min kina cewa wae son juna muke har ina kira mishi dear idan har a dalilin so nake kira mishi dear ta yaya ma za'ayi na kirashi da haka a gurin umma se kace ni nafi kowa rashin kunya.
Nusaiba tayi murmushi tace"hm 6ter knn idan kina fad'ar haka har ma dariya kike bani wlh,kawai dai kice a farkon auren ku bakwa son juna amma banda yanzu da kike waya dashi can ciki har ma ba'a jin me kk fad'a.
  Zarah tayi murmushi cikin ta6e baki tace"kanki ake ji dai idan kin gaji da sa idon naki ae kya daina"
  Allah 6ter ba wani sa ido se fad'ar gaskiya amma baza ki fahimci abunda nake nufi ba sai nan gaba idan kinsan meye soyayya dan kina buqatar ki sani kam kagi a cikinta tsumbul amma kin kasa ganewa......Dear zarah ta fad'a d'auke da d'an murmushi tana kallon wayar ta da kiran saif ya shigo,kana takai hannun ta a hankali ta d'aga wayar.
  Nusaiba ta zura mata ido se murmushi take tana kallonta amma yanayin fuskar zarah da ta sauya zuwa damuwa yasa murmushin nata take ya 6ace tana ci gaba da kallon zarah har sai da ta gama waya snn tace"6ter lafiya?
  Zarah ta kalle ta d'auke da idanunta da suka ciko da qwallah tace"dear ne baya jin dad'i har ma ana fahimta idan yayi magana"
  Cikin damuwa Nusaiba tace"me yake damun shi?
  Zarah da still qwallah na cike a idon ta tace"nima bai gaya min ba kawai dai yace baya jin dad'i kuma wae kar na gayawa kowa ko nima da ban fahimta ba da bazai gaya min ba,saida na matsa mishi ne snn ya gaya min.
  Nan ta share qwallar da suka zubo mata.
  Nusaiba da ke kallon ta cikin kwantar mata da hankali tace"kinga 6ter canjin yanayi ne fa kawai inaga sbd jimawar da yayi baije ba kar ki damu ki kwantar da hankalin ki kinji.
  Shiru kawai zarah tayi bata ce mata komai ba amma a ranta ji take ita kam ina zancen kwanciyar hankali a tare da ita har dai yanda taji muryar sa daji ciwon ma har ya kaishi kwance.
 Yinin rnr se duk taji jikinta ba dad'i itama,duk tabi tasa damuwa a ranta har washe gari duk ta kasa sakewa karatu ma bata iya yi ba,haka ta d'auko handouts ta ajiye a gabanta se kallon su kawai take cike da tunanin saif a ranta wanda tun jiya take ta faman kiran wayar shi bata samu wayar a kashe,shiyasa duk tabi ta qara shiga damuwa.
  Nusaiba ta shigo d'akin ta same ta riqe da waya a hannun ta se ci gaba da trying d'in numbar sa take,a hankali ta qarasa gurinta ta zauna tana kallonta tace"har yanzu dai jikin ne baiji sauqi ba?
 Sai da Zarah ta share hawayen da suka sauko mata snn muryar ta a sanyaye tace"ina zan sani ya kashe wayar sa tun jiya se faman kiran sa nake bana samu"
  Cikin damuwa Nusaiba tayi shiru can tace"to gaskiya a gayawa umma kawai in yaso ta kira Abban kd tunda yana can se aji ko lafiya"
 Zarah tace"um um ya face karna gayawa kowa abar shi zuwa anjima idan na koma kiran sa ban samu ba snn ko za'a gaya mata.
   Shiru kawai Nusaiba tayi bata ce mata komai ba nn se ga umma ta shigo d'akin.
  Tayi murmushi ganin handouts baje a gaban zarah tace"au wae karatu ake tayi ne shiyasa gabad'aya jiya kika yini a d'aki,to Allah ya taimaka ya kuma bada sa'a amma dai yau kam haquri zakiyi da karatun ki tashi yanzu kuje saloon anjima mai lalle tana nn zowa na kirata a waya na snr da ita.
 A sanyaye Zarah tace"inna se fa gobe ne zai dawo"
 Umma tace"to ae yau ya kamata ace kinyi komai dan nasan halin tafiyar saif da sassafe yake dawowa dan haka tattara handouts d'in ki maida ki ajiye yanzu zan kira drivern ki da je kaiki school yazo ya kaiku saloon.
  Nusaiba tace"yauwa umma dama ina son ince ki bani kud'i kaina yana buqatar gyara in naje se su tsefe min kalabar nn a min stretching d'in shi.
Harara umma ta dalla mata ba tare da tace komai ba ta fita daga d'akin.
 Zarah ta kalle ta tace"me kika yiwa inna ne?
  Nusaiba da tuni har qwallah sun ciko mata ido tace"tun shekaran jiya ne fa akan wnn maganar amma tana fushi dani ne sbd yaya ma'aruf da ya kirata da basan me ya gaya mata ba,kuma ni ina kan bakata wlh indai har yace ina gama makaranta za'a yi auren to sai dai kowa ya kama gaban shi duk son da nake mishi na haqura.
  Zarah dake kallonta tace"Aa Nu...da sauri cikin share qwallah tace"A'a dan Allah 6ter kiyi shiru kawai.
 Nan zarah tayi shiru d'in bata sake yunqurin fad'ar komai ba se kallonta da take.
 Driver na zowa umma tazo ta gaya musu suka shirya suka fita.
Se ga ma'aruf sun had'u dashi da isowar shi knn ya faka motar sa ya fito.
   Shaye da toka Nusaiba ta tsaya suna kallon juna yayinda shi kuma tashi fuskar cike yake da son ya rarrashe ta,ya sakar mata murmushi cikin fara tako zai qaraso inda take,nn kawai da saurin ta ta kama hannun zarah dake shirin su gaisa dashi bata barta ba ta jata kawai suka shiga mota,ma'aruf ya bisu da sauri yana faman kiran Nusaiba yaje ta gefen 6angaren da ta zauna ya duqa yana d'an doka glass d'in cikin rarrashi kan tayi haquri ta tsaya ta saurare shi amma fir taqi saurarrar shi se ma driver da tacewa yayi sauri yaja motar su wuce,nn driver na jan motar ma'aruf ya miqe tsaye riqe da waist d'in sa cikin damuwa yana kallon motar har suka fita.
Se kuma da saurin sa ya juya da alama zai je yaja motar sa ne ya bisu kawai yaga umma,nn ya russuna a natse cikin ladabi ya gaida ta.
 Cikin fara'a umma ta amsa mishi har tana mishi ya hanya,Alhmdlh ya fad'a snn suka shiga daga ciki ya zauna ta kawo mishi ruwa da lemu snn taje a natse ta zauna kan kujerar da ke fuskantar sa tana kallon sa fuskar ta ba yabo ba fallasa tace"yanzu kai ma'aruf biyewa shirmen Nusaiba kayi shine ka taso qafa tun daga Lagos kazo bayan kasan fad'a kawai take ba abunda zai hana auren ku kaida ita sai dai kuma wani ikon Allah.
 Cikin yanayin damuwa yace"wlh umma na da mune sbd sosai take yin fushi dani ta kashe wayar ta gabad'aya ko na kira bana samu shiyasa na biyo jirgi nazo dmn in bata haquri amma kuma tama qi ta saurare ni tayi tafiyar ta.
 Umma tace"kar ka damu kanka indai Nusaiba ce haka take da banzan fushi in ta gaji dan kanta ae ta daina,dan haka bari na kawo ma abinci in kaci ka huta kawai kayi tafiyar ka.
  Yace"wlh umma bazan iya komawa ba idan bana samu ta haqura ba"
  umma tace"amma ma'aruf ae kasan halin Nusaiba ne sai ita bazata saurare ka ba idan ba dan kanta ta huce ba,bare kuma saloon d'in nn da suka je zasu d'auki lokaci kafin su dawo.
  Ma'aruf yayi shiru shi kam duk jimawar da sukayi suna soyayya bai san ma tana da dogon fushi haka ba se yanzu shiyasa duk yabi ya damu.
 Yace"umma koma yaushe ne ni mai iya jiranta ne se a bani makullin part d'in saif naje na jira ta a can.
 Umma tace"to shikenan bari naje na kawo ma abinci kaci tukun.
  Nan taje ta kawo masa abinci yana gamawa ta bashi makullin 6angaren saif yaje zaman jiran dawowar su Nusaiba.

Koda suka dawo anyi sllr azahar suna ida sallah se ga umma ta shigo d'akin riqe da kular abinci a hannun ta da kuma plates da spoons zata ajiye abincin zarah tayi saurin kar6a ta ajiye,umma tace"na kawo muku abincin ne sbd ma'aruf yana a falo sai ki hanzar ta kici abincin dmn na kira mai lalle na gaya mata cewa kun dawo gata nn zowa.
  "To"
Zarah ta fad'a kafin umma ke maida duban ta gun Nusaiba fuskar ta a d'aure tace"ke kuma maza tashi ga ma'aruf can a falo yana jiranki kuma Allah yasa inji kin mai wani iye shegen in zazzane ki a gidan nn wlh,tunda ke ba'a binki ta lalama very stupid tashi ki fice.
  Nusaiba da bata ko tashi daga kan darduma ba kmr zatayi kuka ta miqe ta fita daga d'akin tana faman gunguni ita wlh in yace tana gama makaranta za'a yi auren bashi ba ita.
  Umma da ta bita da kallo ta girgiza kai tace"oh Allah ka shirya mana yaran mu,ga wasu can har neman suke suyi auren basu samu ba amma ke auren na binki kina gudun shi mtsw tayi tsaki snn ta kalli zarah tace"zarah ya akayi ne yau tun safe nake ta kiran wayar saifudeen amma har yanzu wayar tashi a kashe bai kunna ba,ko ya kira ki da wani layin ne?
  A sanyaye zarah ta sadda kanta qasa tace"A'a bai kirani da wani layin ba kuma nima duk na kira haka nake jin wayar tashi a kashe ban san meyasa ba"
  Umma tace"To kar ki damu indai saif ne yanzu haka yana can yana harakokin gaban shi ya cillar da wayar wani gurin,amma dai zuwa anjima idan bai kunna wayar tashi ba se na kira Alhjn Kd muji me yake faruwa da saif d'in kinji.
  A hankali zarah ta gyad'a mata kai snn umma ta fita daga d'akin.
Bayan umma ta fita ne Zarah ta d'ibi abinci tayi shiru se kallon abincin take ta kasa ci har mai lalle tazo,haka ta rufe abincin ta ajiye ba tare da tayi ko spoon d'aya ba sbd damuwar rashin sanin wane hali saif yake ciki kad'ai ya isheta.
 Bayan har sun fara lalle se ga Nusaiba ta dawo d'akin fuskar ta wasai kmr ba ita ce ta fita cikin fushi ba har yaba lallen nasu take tayi tana fad'in itama sai an mata koda za'a zane ta a school kuwa baza ta iya barin wnn lallen ya wuce ta ba dan ganin take kmr ma yafi na farko kyau duk tabi se kod'a lallen take tayi.
  Mai lallen dai godiya ta mata.
 Zarah kuwa bata ce komai ba se tunanin wanda akeyin lallen dmn shi take da har magana bata son yi sbd damuwar da take jin kanta a ciki.
  Nusaiba ta kalle ta zata yi mata magana se taji shigowar umma ta tashi da sauri ta tafi jikin umma cikin murna tana fad'in"umma ki tayani murna yaya ma'aruf yace baza ayi auren ba har sai lokacinda nake so.
 Umma wacce dama ita ta cewa ma'aruf yace mata haka dan kawai a huta da ita ba wai dan za'a fasa yin auren ba,tayi murmushi tace"to congratulation ina ma'aruf d'in yake ya tafi ko yana nn?
  Tace"a'a yana falo ke yake son gani kafin ya wuce shine koda naje na samu kina waya.
  Umma tace"to kawo ma mai lalle ruwa da lemu tasha idan ta gama lallen se ki sa mata abinci taci kafin ta wuce ni zan tafi inga ma'aruf d'in.
  Nan umma ta fita Nusaiba kuwa taje ta kawo ma mai lalle ruwa da lemu snn ta d'ibarwa kanta abinci tayi zaune kusa dasu tana ci tana kallon lallen nasu da ta kasa daina yabawa.
 Ana gama ma zarah ta zauna itama aka fara yi mata.

Da dare bayan isha'i Zarah ce zaune kan stool a gaban dressing mirror ta had'e kanta da jikin dressing mirror d'in,gashin kanta da yasha gyara ya baje sosai kan gadon bayanta sbd a sake yake bata sa ribborn ba asali ma ko tufafi babu a jikinta se towel da take d'aure dashi da alama wanka ta fito amma ko mai ta kasa shafawa dan har yanzu ta kasa jin labarin abunda saif yake ciki still wayar sa a kashe ga umma kuma har yanzu bata ce mata komai ba da tace zata kira Alhj kd suji.
  Ta jima a haka a gurin can ta soma jin daddad'an qamshin turaren saif yana zowa hancinta,ta d'ago kanta sannu a hankali se kuwa taga saif d'in ne ya shigo d'akin,da mamaki ta miqe tsaye tana kallon shi.
  Surprise!
Shine abunda ya fara fad'a snn ya sakar mata murmushi tare da ware hannayen sa alamar tazo,nn ta tafi da sauri ta fad'a jikinsa ta rungume shi sosai had'e da fashe masa da kuka,se kuma da saurin ta ta d'ago ta kai masa duka a qirji cike da shagwa6a tace"meyasa ka min haka"
 Yayi murmushi kawai bai ce mata komai ba se sake maida ta a qirjinsa yayi ya rungume.
[4/22, 12:44 AM] Paexer: _Sunday 15/04/2018_ *«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*


*✨RA'AYIN MU✨*
Group.
Ina miqa  gaisuwa ta a gare ku sbd d'inbin qaunar da kukeyiwa dis novel Allah ya bar min ku akan qaunar da kukeyi yiwa littafin nn da kaf grps d'inda nake ciki kunfi kowa son shi,hakan yasa zarah n saif ke mugun sonku da har ma suke miqa gaisuwar su gare ku.
     Luv u all❤
  And dis page is yours.


*«»page«» 57*
Da isar su d'akin sa ya kar6i handout d'in da ke hannun ta ya ajiye kan bedside drawer,snn ya kama hannun ta suka zauna kan bed ya shafo cikinta yana kallonta da kulawa yace"are u ok ko kina buqatar kici wani abu kafin?
   A hankali ta girgiza masa kai alamar bata buqatar komai,nn ya rage hasken d'akin ya cire kayan baccin da ke jikin sa snn ya kama hannun ta ya d'aura ta kan cinyoyin sa tare da sa6ule mata rigar baccin da ke jikin ta,ya kafe idon sa qyar a kan albarkatattun qirjin ta dake matuqar birge shi da tsokalo mishi sha'awa,nn take ya soma jin wani yar a jikin sa,da har bai san sanda yakai bakin sa zai tsotsa ba,se ganin yayi zarah tasa hannuwan ta duka biyu ta rufe abunta,ya d'ago fuskar sa a kasale cikin had'iyar yawu muryar sa can qasan maqoshi yace"cutie y?
 A shagwa6e zarah ke kallon sa da ko bata fad'a ba ya fahimci me take nufi dan rnr a haukace ya mata kmr zai cinye mata su sbd qamshin turaren ta da duk ya qara haukatar dashi.
  Ae kuwa yana gama tariyo abun yayi murmushi tare da janye hannayen ta yana kallonta cikin shafa nonuwan ta da yake binsu a hankali kmr qwai yace"kar ki damu yau komai a sannu za'ayi shi kinji.
Bata iya cewa komai ba se lumshe idanun ta da tayi sbd saukar lallausan harshen sa da taji a kan na fulanin ta,ya shiga yi mata wani irin salo a hankli cikin natsuwa.
Nan ita ma a natse takai hannuwan ta a bayan wuyan shi tana shafa bayan wuyan nashi sannu a hankali cikin tafiyar tsutsa har zuwa gadon bayan shi.
  Suka jima a haka har zaman ya nemi ya gagaresu suka koma kwance yakai bakin sa a nata ya had'e se can ya iya zare bakin nasa,ya shiga kissing d'in jikinta ta koina da har yakai gabar da yasa zarah duk taji awa zata shid'e da gabad'aya ta wani narke mishi awa ruwa se numfashi da take fitarwa a hankali tana shafa bayan kanshi.
  Koda suka je ga babban aiki saif da har ya fara aikin sa sannu a hankali cike da enjoying,ya tsaya da qyar yana kallon zarah da ta d'an rirriqe shi alamar tana d'an jin zafi.
  Baice mata komai ba se qaramin pillow ya d'aura a under waist d'inta sbd yanda zataji sauqin abun,snn a hankli cikin natsuwa da lalla6ata yaci gaba da aikin shi da yake jin kmr zai zauce  yana sauya musu salon kwanciya daban daban da yasan zarah bazata wahala ba,a hakan har ya samu kanshi yanda yake so cikin sambatun sa da yake ta zubawa zarah albarka.
Ya rungume ta qyam a qirjin sa cikin jin dad'in abun har yana jin kmr ma ya qara dan shi baiqi su kwana suna yi ba ma,amma cutie d'in sa kam yasan baza ma ta yarda ba dan yanda yakejin ta narke akan faffad'an qirjinsa yasan duk a gajiye take se yawo take da hannun ta kan faffad'an qirjin nasa a hankli cikin sauke numfashin gajiya dan duk da a hankali ya bita dole zata gaji sbd saif gwarzon namiji ne kuma abune da bata riga ta saba da shi ba shiyasa har take d'an jin zafi a qasanta.
 Yayinda idanuwan ta suke a lumshe sbd wani irin bacci mai dad'i da take jin yana fizgar ta.
  Amma saif bai bar tayi baccin ba har sai da suka tsalkake jikin su snn.

Washe gari da asuba koda saif ya dawo daga masallaci ya same ta itama ta ida sallah ta gama linke hijab da darduma har ma da zanin da ta d'aura akan rigar baccinta duk ta linke ta saka a wardrobe snn ta juyo tana kallon sa cikin amsa masa sallamar da yayi had'e da mishi ina kwana.
Saif da ya qaraso gurinta cikin shafa gefen fuskar ta yace"Lafiya lau ya naki kwanan gajiyar tabi gado ko?
A d'an shagwa6e cikin turo baki tace"inafa ni har yanzu jikina duk ciwo yake min awa ammin duka"
  D'auke da murmushi me kmr dariya saif yaja karan hancinta yana fad'in"um um fa cutie kiji tsoron Allah duk yanda na biki a sannu"
   Nan zarah tayi saurin shigewa qirjinsa tana murmushi.
 Saif da shima still murmushi na kan fuskar shi yakai hannun sa yana shafa gadon bayanta yace"zaki je school yau?
 Tace"um um ba'ayin komai se Monday ko zan je"
  Yace"ok har in dawo knn baza kije school ba?
  Cikin marairaice fuska tace"eh shiyasa ma naso kaje dani"
  Yace"kar ki damu ae na gaya miki idan na dawo zamu je dai dai kin kammala exam an kuma yi miki komai na tafiya koh"
  Nan ta gyad'a masa kai tare da komawa qirjinsa ta lafe.
Tana ji ya shiga shafa jikinta a hankali yana wasa da hannun rigar baccin ta kmr zai sa6ule mata rigar.
 ta d'ago ta kalle shi se matso fuskar sa yake a hankali zai kai bakin sa a nata.
  Ta kauce da sauri tace"meye haka dear nifa bacci nake ji"
  Bakin sa saitin kunnen ta muryar sa a natse can ciki yace"plz cutie ki d'an barni in d'an qara kinji kinga tafiya zanyi"
  A shagwa6e kmr zatayi kuka ta ture shi tana fad'in"ni gaskiya dear in kana min haka zamu 6ata jiya ka min wayo yau ma shine kake so ka min koh"
 Ta nuna shi ya kama hannun cikin kwantar da murya yace"ba haka bane cutie idan na tafi kewar ki zata min yawa bama kusa da juna,dmn ko ba komai idan ina ganin ki ya fimin akan bana ganin ki,yi haquri kinji in d'an yi"
  Cikin yanayin shagawa6ar da take d'auke dashi tace"uhm ba wani wayo kawai kake so ka min bayan jiya ba kasan jurewa kawai nayi ba amma naji zafi kuma ni gaskiya yanzu bacci nake ji bazan iya ba.
  Sosai ya tafi da ita jikin sa cikin rarrashi yana fad'in"sorry cutie yi haquri kinji tunda kinga ba kya zuwa school idan na kaiki gida sai kiyi baccin ki a can kinji.
 Maqale kafad'a tayi tace"um um ni har yanzu ban daina jin zafin na jiya ba ma"
  Yace"Eyyah to muje in hura miki"
Ya fad'a tare da d'ago fuskar ta,ae kuwa cike da jin kunya ta janye jikinta a nashi da sauri ta tafi kan bed ya bita zata sauka ya cafko ta se cakulkuli yake mata yana dariya yana fad'in"ae tunda kikace baki daina jin zafi ba sai na hura miki.
 Cikin dariya sosai zarah tace"yi haquri wasa nake maka wlh.
  Daga haka wasar tasu ta canja salo har saif ya samu abunda yake so.
  Bayan sunyi wanka sun shirya har ma sunyi breakfast zarah ta d'ebo en kalolin tufafin ta da zata je dasu gida da kuma handouts d'in ta duka ta kwasa suka tafi.
 Da isar su suka sami umma a falo suna gama gaisawa zarah ta haura sama zuwa d'akin su Nusaiba.
  Ta same ta zaune kan bed riqe da waya,bata koji shigowar zarah ba har sai da zarah taje ta zauna gab da ita tare da kar6e wayar snn ta d'ago tace"lah 6ter kece har kun zo?
  Zarah tace"inafa zaki sani kina nn kinsa waya a gaba se charting kk ba kya ko jin sallama"
  Eyyah wlh banji ba kuma bako charting nake yi ba wani novel ne me d'an karan dad'i nake karantawa.
  Zarah tace"hm wae rashin aiki,ni kam ya akayi ma baki je school ba yau?
  Tace"Muna d'an hutun kwana biyu ne kinsan Ss3
 Hakane kam ina nadiya koda yake na manta ta koma kd,yusra dai shikenan ta koma gidan hajiya gabad'aya ba a ko jin d'uriyar ta.
  Nusauba tace"Ae kam yusra yanzu sai dai driver ne ke samun ta a can yana kaita school,amma sun ma kusa yin hutu a nn zata dawo idan hutun ya qare se ta koma kuma.
  Zarah tace"lallai yusra anji dad'in can gida ma ake kawo ma hutu"
 Nusaiba tace"kinsan hajiya komai kake so yi maka take bazata hanaka ba shiyasa tafi jin dad'in can,nn kuwa umma bata yarda da wani banzan iya shege sai dai ma ta kwakkwad'e ta,ko nima da tasan ina karatun Hausa novel d'in da tuni ta kar6e wayar kwata kwata ta hana min.
  Zarah Tace"au shiyasa kike yi a 6oye to lallai kuwa zan gaya mata ne.
  Da sauri Nusaiba tace"ah haba 6ter dan Allah a'a wlh zata hana min riqa waya har sai nayi aure kuma dan tafi so ko zakayi karatun novel d'in to ka bari idan kayi aure indai har dan zaka qaru akan wasu abubuwan rayuwar aure ne ba shirita ke saka karatun ba.
 Zarah tace"ae kuwa   zan gaya mata tasan kin girma aure kike so tunda har kuke zuwa ganin qwaf a gidan mutane magulmata kawai kuma auren zakuyi ae inga ko ku kuna ma iya yin tafiyar.
  Nusaiba tayi dariya tace"inafa ae lokacin kin zama uwa baki da lokacin ganin qwaf se na renon yara kuma dan nasan kam yaya tuni har ya saka miki baby....wayyo Nusaiba ta fad'a sbd pillown da zarah ta d'auka ta doka mata tana fad'in"wlh Allah ya shirye ki kuma yanzun zanje in sami inna in gaya mata kina gama makarantar nn su suyi miki aure dan wnn iya shegen naki km sae aure,nn ta qara doka mata pillow snn ta tafi da sauri tana dariya zata bar d'akin,nan kawai taji ta fad'a kan jikin saif da shigowar sa knn d'akin.
  Cikin dariyar da take d'auke da ita ta kalle sa tace"wae dear baka tafi ba"
  D'auke da murmushi ya lotsa en yatsun sa a dimples d'inta yace "ina zanje ban sallami matata ba..ke bamu guri kin tsaya kina kallon yannanki"
  Yace"da Nusaiba wacce ke kallon zarah cikin marairaice fuska alamar dan Allah kar ta gayawa umma,se kawai kuma yanayin yanda saif ya mata magana ya bata dariya ta gimtse dariyar ta fita da sauri.
 Saif da ya bita da kallo yayi murmushi had'e da girgiza kansa yace"nucy nucy wato dariya ma na bata.
  Zarah tace"ba dole ba kaga yanda ka wani tsare gida.
  Ke bamu guri kin tsaya kina kallon yannanki.
  Ta kwaikwaye shi,cikin dariya ya d'aga hannu kmr zai naushe ta,tace"wayyo tare da cukuikuye shi tana dariya bata son ya doke ta.
 Nan kawai taji ya d'auke cak ya tafi da ita sai kan bed ya fad'a kan jikinta ya mata rumfa tare da kai hannun sa kan qirjin ta da duk ya taso ta saman riga yana shafawa muryar sa a kasale yace"ki bani na sallama kafin in tafi"
 Da sauri Zarah ta zaro ido tace"dan Allah rufan asiri a gida muke fa kuma...kafin ta iya qarasawa se jin bakin sa tayi a nata ya had'e suka jima a haka har yana qoqarin zuge mata zip d'in riga,tayi saurin zare bakinta tana fad'in"plz dear ya isa haka a gidan su umma muke fa ka sani yi haquri har in ka dawo kaji.
  Ta fad'a cikin lalla6a shi kmr wani qaramin yaro sbd tsoron take kar azo a same su haka.
 Saif kuwa da har idanun sa sun sauya kala sbd sauqin da ya fara shiga yace"wasa kawai zanyi cutie"
 Nan kafin ma ta iya cewa komai se jin tayi kai tsaye ya zuge mata zip d'in riga tare da koma kai bakin sa anata cikin wani irin salon da yasa ta kasa hanashi har ma tana ji ya sa6ule mata riga ya shiga wasa da dukiyar fulanin ta cike da qwarewa yana sarrafa su yanda yake so,wanda da alama sam ya manta cewa tafiya zaiyi haka ita ma ta manta inda suke dan se biye masa tayi suka hau romancing d'in juna da har sun shagala sosai....knocking d'inda aka soma yi ya katse su sukayi saurin tashi saif ya taya ta da sauri ta maida rigar ta snn ya iya amsa kiran da umma keta mishi da ita ce ke knocking d'in.
  Bayan ya amsa mata ne tace"kayi sauri lokaci yana tafiya ga driver har yazo yana jiranka.
 Yace"to umma ganin nn zuwa"
  Nan kawai ya ciro 50k ya bawa zarah yace"ga wnn koda kina da buqatar siyen wani abu"
  Snn ya ciro 15k yace"wad'annan kuma idan zan dawo kije saloon a kuma yi miki lalle kinji.
 ya d'aura mata kiss kan goshi snn ya miqe,nn itama ta miqe tana mai yi mishi godiyar kud'in da ya bata,ya girgiza kansa alamar ba wannan godiyar yake so ba ya tara mata kuncen sa,ba musu ta d'aura mishi kiss snn ta d'ago d'auke da murmushi ta mishi Allah ya kiyaye.
  Amin ya fad'a cikin lotsa en yatsun sa akan dimples d'inta snn yana murmushi ya fita yana mata bye baye,haka itama ta bishi da bye bye d'in snn bayan ya fita ta zauna shiru tana kallon kud'in da ya bata.
Can ta tashi riqe da kud'in a hannun ta ta tafi dasu d'akin umma bata same ta a can ba ta sauka downstairs ta same su har sun dawo daga rakiyar saif suna zaune ta qarasa gurin umma ta zauna a natse tare da fara bata 50k snn muryar ta a hankali tace"dear ne ya bani yace wai idan ina buqatar siyen wani abu"
  Snn ta bata 15k tace"wad'annan kuma yace"in zai dawo naje saloon na kuma yi lalle.
  D'auke da murmushi umma ta koma maida mata kud'in tace"kinsha godewa sai ki adana a hannunki,na lalle da na saloon kuma duk suma ki ajiye idan zai dawo d'in se a kira mai lalle ta miki ki kuma je saloon.
 Zarah tace"to amma inna da kin ajiye kud'in a hannun ki inaga yafi se na had'o har da wasu dubu d'ari da ya ta6a bani duk ki ajiye.
  Umma tace"a'a jeki kawai ki adana a wajen ki ba'a zama hakannan Ba kud'i a hannu kinga wata rana kyayi lalurar ki ba tare da kin roqe shi ba.
 Shiru zarah tayi dmn ganin take kud'in sunyi yawa a barsu duka a hannun ta dan dubu d'ari d'in da ke ajiye ma ko sisi bata ta6a ta6awa a cikin su ba,amma dai zatayi kmr yanda umma tace,nn ta tashi ta wuce.
  Nusaiba ta bita da kallo sbd dear d'in da ta kira saif a gaban umma bako jin nauyi awa dama can haka take kiran shi.
 Nan kawai tayi murmushi cike da sha'awar wnn soyayya tasu.
Da dare zarah na kwance kan bed ta gama waya da saif se kallon wayar take cike da jin kewar shi.
 Nusaiba wacce ta fito daga bathroom daga gurin wanka tazo tayi zaune kusa da ita tana kallon ta da kulawa tace"6ter lafiya?
 A hankali zarah ta kalle ta tace"wlh Nusaiba dear ne nake jin kewar sa sosai a raina bansan meyasa ba har ji nake kmr ya kwana biyu baya nn.
  Nusaiba tayi murmushi tace"hm soyayya kenan ae baki ji ma yanda kike birge ni da dear d'in nn da kike kira mishi ba wlh.
  Zarah dake kallon ta ta6e da baki tace"hm wae soyayya ni kam na rasa se yaushe ne zaki fahimci cewa nida yayanki babu wata soyayya a tsakanin mu,muna zama ne kawai sbd biyayyar iyaye da kuma dmn farin cikin Baffa.
 Dariya Nusaiba tayi tace"kae 6ter kina da abun dariya yanzu duk soyayyar nn da kuke zubawa keda shi ba kya gani gashi har kina kira mishi dear kuma har a gaban umma"
  Cikin dalla mata harara zarah tace"ko dai ke d'in ce da abun dariya ba koma ince baki san ainihin meye soyayya ba.
Tayi tsaki snn tace"Dear d'in nn fa da nake kira mishi sunan da yayi saving numbar shi ne a wayata,hakan yasa kawai naga bari na riqa kiran shi a hakan bawai sbd wani banzan tunanin ki da kike yi ba.
  Sosai Nusaiba ta qara fashewa da dariya,cike da takaici zarah ta d'auki pillow zata doka mata...se ta tsaya tana kallon wayar ta da ta hau ringing Dear on call.
 Sai da ta jefawa Nusaiba pillown snn ta d'aga kiran ta kwanta tana magana dashi murya can ciki sosai ba'a ko jin me take cewa sai shi da take wayar dashi.

Sorry typing d'in ne ya goge min gabad'aya sai da na sake muku shiyasa dare ya min.
[4/22, 12:44 AM] Paexer: _Wednesday 18/04/2018_
*«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»page«» 59*
Yana fad'in"sorry yi haquri kinji dole ce tasa na kashe wayata kuma nayi ta kiran ki da wani numba kinqi ki d'aga.
 Fuskar ta cikin fushi ta d'ago tana kallon shi tace"ni ina naga lokacin d'aukar wata numba can bayan baka da lfy kazo kuma ka kashe wayar ka abun kafin ka kashe wayar ko text ne ka turo min amma baka yi ba kasa duk nabi na shiga damuwa.
  Am sorry yi haquri bazan sake ba.
Ya fad'a cikin kama kunnen sa har yana qoqarin ya mata tuman kwad'o tayi saurin d'aga shi tana fad'in"ah haba dear meye haka ae komai ya wuce na haqura ya jikin naka?
 Ta kama kumatun sa tana kallon shi da kulawa,a hnkli ya kama hannayen nata duka biyu da suka sha lalle ya d'aura mata kiss snn yace"ni tuni naji sauqi lokaci d'aya zazza6in ya tafi kmn yanda yazo min lokaci d'aya"
   Tace"ayya to ya jikin Baffa?
Gaskiya sosai yana samun sauqi kuma da yardar Allah zai tashi nn bada jimawa ba"
  Cikin nuna jin dad'in labarin tace"to Allah ya tashi kafad'ar shi ya bashi lafiya"
 Amin my cutie ya fad'a had'e da d'aura mata kiss kan goshi.
 Snn ya sake kamo hannayen ta yana kallon lallen har zuwa na qafarta ya kalle ta yace"gaskiya lallen nn yayi kyau sosai wacce ta miki na farko ne ta miki wnn?
  Eh ita ce
Zarah ta fad'a tana murmushi
Yace"wow gaskiya to daga yau ita zata riqa miki lalle har qarshen rayuwar mu duk lokacin da ya goge a sake wani"
  Murmushi kawai zarah ta koma yi tana kallon shi,ya koma kan gashin kanta da yasha gyara sai shafa gashin yake yana shaqar qamshin gashin nata da yake ta yaba gyaran shima,kana ya d'ago  se ci gaba yake da shafa sumar yana kallon ta yace"amma dai kinsan gobe se an  sake miki wani gyran gashin koh"
  Tace"meyasa?
Ya lakato hancinta yace sbd wnn kam yau zai sha ruwa kema kin sani.
 zarah tayi murmushi tare da shigewa a qirjinsa.
 Nan se ga Nusaiba ta shigo d'akin tana fad'in"6ter congratulation yaya na kan hanyar dawowa wlh yanzu umma ta kira Abban k...se ta tsaya da sauri cikin rufe baki tana kallon su nn ta juya sum sum zata fita,saif yace"ke dakata jeki gayawa umma ina tare da baqo yana a falo ita yake son gani,and u kar ki sake dawowa d'akin nn haka kawai in baso kk kiga abunda ya wuce sanin ki ba.
 Nan Nusaiba ta fita da sauri cikin jin kunya.
  Zarah kuwa a shagwa6e ta d'ago tare da kai masa duka a qirji tace"meye kake fad'a haka"
  Cikin murmushi ya d'auke ta cak ya tafi da ita kan bed ya kwantar had'e da yi mata rumfa yana fad'in"ae gaskiya na fad'a ya zata shigowa mata da miji kai tsaye idan ta isko mu haka fa.....ya had'e bakinsa da nata zarah da taji abun kae tsaye bata iya zare bakin nata ba sbd iya salon gogan nata se ma lumshe idon ta tayi a hankali ta shiga kama mishi,jin yana son zare mata towel yasa tayi saurin zare bakin ta had'e da rirriqe towel d'in tana kallon sa se numfashi suke fitarwa dashi har ita,tana kallo zai sake saka bakin sa a nata ta kauda fuskar ta a hankali gefe tace"No dear ya isa karfa muyi irin na rnr "
  Ya juyo ta yana kallon ta cikin shafa gefen fuskar ta yace"ai rnr ba wanda ya ganmu umma ce baza ta shigo mana haka kawai kai tsaye ba dan haka ni bud'e min abokan wasa na in gan su nayi kewar su sosai.
   Nan kawai kae tsaye taji ya zare mata towel da saurin ta ta rirriqe shi a tsorace cikin zaro ido tace"wayyo dear shi kad'ai ne fa a jikina plz maida min kar azo a same mu haka wlh zanji kunya"
  D'auke da murmushi yaja karan hancinta yace"matsoraciya ba gani a kanki na miki rumfa ba,ba wanda zai zo bare ya ganar min ke sai ni kad'ai da Allah ya bawa wnn ikon.
 Ya qarashe mgnr had'e da kashe wutar d'akin.
 Cikin qara shiga tsoro zarah tace"kae dear meye haka kuma?
Hannun sa kan na fulanin ta yana shafawa yace ba kina tsoron kar a ganmu bane kinga haka se muyi abun mu yanda muke so koh,tace"ni gaskiya a'a nn ta miqa hannun ta ta kamo towel d'inta zata maida jikinta,saif ya kai mata cakulkuli da sauri cikin dariya ta saki towel d'in,saif ya cillar da towel d'in can gefe tare da kai bakin sa a nata ya had'e.
 Sai da ya jagwalgwalata yanda yake so snn yayi lokacin lalubo wayar shi da ke ta faman ringing tun d'azu a cikin aljihun wandon shi,bayan ya ciro wayar yaga mai kiran ya kalli zarah da ta turo baki a shagwa6e cikin fushi tana kallon shi,ya d'aura mata kiss kan d'an bakin ta da ta turo yace"sorry na daina but ina zuwa umma ce ke kirana kinji"
 Nan ya kunna hasken d'akin tasa pillow da sauri ta rufe jikinta ya kalle ta kawai d'auke da murmushi snn ya miqe ya fita daga d'akin.
Yaje downstairs ya sami umma tare da baqon da yazo dashi wato mijin mom d'in shi da yazo basu haquri da kuma jajanta musu abunda ya faru,wanda bayan saif ya same su sosai yayi ta qara bashi haquri yana bashi magana kan yayi haquri da halin mahaifiyar tashi halinta se addu'a.
 Nan yayi sallama dasu ya fita umma ta kalli saif da ya dawo daga rikan shi tace"mutumen nn fa ya nuna damuwar sa sosai inaga belin matar tashi yake son yi ko?
 Da sauri saif ya kalli umma yace"haba umma beli fa ei sosai yaji haushin abunda ta akaita shiyasa ma da isowar mu garin nn ya nemi in kaisa gurin ta,muna zuwa ya miqa mata takardar sakin ta se kuka take tana roqon shi amma fir yaqi saurarrar ta.
Umma tace"to Allah ya kyauta amma kai kuwa ina ka had'u dashi?
 Yaje dubin Abba ne a England da kuma jajantawa Abban kd abunda ya faru shine da zan zo yace yana son kema yazo ya jajanta miki.
 Bawan Allah
Umma ta fad'a snn tace"to ya jikin Abban naka duk da Alhjn kd ya gaya min se qara samun sauqi yake koh.
 Gaskiya kam Alhmdlh umma sai dai muce Allah ya tashi kafad'ar shi ya qara bashi lafiya.
 Umma tace"Amin Amin,amma kai kuma meyasa ka kashe wayar ka ka kuma taso baka snr da mu ba?
  Wlh umma dole ce tasa na kashe wayar sbd Sophie duk inda nake tana sani a wayar ta  haka nima,amma ni sam na manta sai daga baya kawai na lura ta samu ganin ina England har ma tana zowa inda nake tana bin direction shine kawai na kashe phone d'in amma ayi haquri umma"
  Umma tace"ba komai me kake son a dafa ma dan nasan baza ka ci abincin da mukayi ba yau tuwon qullu ne d'an marmari da miyar ku6ewa d'anya ko kana so a kawo ma?
  Yace"no umma ni ruwan Lipton kawai sun ishe ni"
Nan umma ta wuce kitchen dmn had'o mishi ruwan Lipton.
  Saif kuwa ya shiga qwalawa Nusaiba kira wacce tana zowa yace"je ki cewa cutie ta shirya mu wuce gida"
Nusaiba tace"to"
wacce ko ba'a fad'a ba tasan Zarah yake nufi da cutie,tace"kae lallai mutanen nn da gaske suke nuna soyayyar su a fili,dama haka nake so wlh Allah yasa kufi haka qaunar junan ku.
 Tana maganar ne a cikin ranta cike da jin dad'i har tana ji kmr tayi ta tsallen murna.
  Kana taje ta snr da zarah aiken da saif ya mata,koda zarah ta gama shiryawa shima saif ya kammala abunda yake sukayi sallama dasu umma snn suka bar gidan basu zarce ko ina ba sai asibitin Abba.
 zarah ta kalli saif da ya gama faka mota tace"halan har yanzu ba'a sallami yaya jamil bane?
  Saif yace"eh amma se mun fara zuwa duba Alu driver tukun shi zaki kaiwa fruits d'in da muka tsaya kan hanya muka siya"
  Tace"to yaya jamil fah?
 Saif da sam baya da niyyar zuwa da ita gun jamil sbd ganin yake kmr zuwanta qara masa wani ciwon ne da shiga damuwa.
 yace"kar ki damu muje kawai.
 Nan ba musu ta fita sukaje A&E ward,koda suka shiga d'akin da aka kwantar da Alu driver en uwan sa na tare dashi wanda Alhmdlh jikin nasa ya fara sauqi har ma yana cin abinci akasin daa da bai ko san inda yake ba.
  Bayan sun gaisa da en uwan nashi har ma sun musu ya mai jiki suka ce Alhmdlh snn suka koma kan Alu driver bayan sun mai ya jiki saif ya duba jikin nashi har yana mai en tambayoyi sbd dama duk idan yana asibiti shine mai kula dashi.
Nan bayan ya gama duba shi ya rubuta masa wasu magungunan a takarda ya bawa en uwan Alu driver d'in yace gobe da safe a siyo mishi magungunan,suka kar6i takadar had'e da kud'in se godiya suke tayi mishi sbd kudi'n sun fi qarfin na siyan magani,da tun zuwan su asibitin sisin su bai ta6a ciwon kai ba haka ma abinci ko yaushe umma ke aiko musu.
 Fita saif yayi yace da zarah yana zuwa,jim kad'an se gashi ya dawo yace ta taso su tafi nn ta bar fruits d'inda ta kawo musu ta tashi suka fita yayinda en uwan Alu driver da shi Alu drivern suka bisu da godiya.
Zarah dake tunanin gun jamil zasu je se ganin tayi sun tafi gun mota bayan har sun shiga motar ta kalli saif tace"Dear yaya jamil fa banga munje duba shi ba kuma gashi har mun fito zamu tafi?
  Yace"eh naje na samu an sallame shi yanzu gidan su zamu je"
  Tace"yaji sauqi knn?
Eh yaji sauqi ba kmr farko ba dan koda naje England har kirana yayi a waya ya tambaye ni ya jikin Abba.
Tace"Ayya Allah ya qara bashi lafiya saif yace amin.
Daga haka sukayi shiru,basu sake cewa komai ba har suka isa gidan su jamil.
 Saif ya kalle ta yace"kiyi zaman ki a mota zan gaya masa kina masa ya jiki"
  Tace"meyasa bayan gamu har qofar gidan su amma bazanje in gaida shi ba."
  Yace"sbd kitty tana gidan nn kuma duk na shiga a haukace take zowa gurina,shiyasa bana son ta firgita min ke dan haka kiyi zaman ki kawai kinji"
 Ya shafo gefen fuskar ta tare da d'aura mata kiss kan goshi.
  D'auke da murmushi Zarah tace"to ina masa ya jiki"
 Yace"zai ji"
Snn ya fita daga cikin motar.
 Bai wani jima sosai ba ta hango shi ya fito gate rungume da kitty a hannun shi sosai tayi du6ul du6ul ta qara girma yayi tsayin shi bai qaraso ba se Zainab dake tare dashi ta qaraso gurinta suka gaisa snn taje ta kar6i kittyn ta koma daga ciki shi kuma saif yazo yaja motar suka wuce gida.
   Da isar su gida yana gama faka mota ya bud'e boot ya fito ya ciro akwati zarah ta fito itama tana kallon akwatin tace"kaida naga baka je da komai ba a ina kuma ka had'u da akwati"
  D'auke da murmushi ya kalle ta yace"har kya tambaya to tsaraban cutie na ce"
 Cikin yin murmushi  tace"uhm kaima dai da wasa kake kaida kaje duba Baffa me zai had'a ka da tsaraba ina ma kaga wnn lokacin wata qil dai saqon wani ne kawo in kama ma"
 Yace"Aa bud'e bayan motar dai ki d'auko ledar da na ajiye.
  Nan zarah ta d'auko ledar suka shiga daga ciki,da kai tsaye d'akin saif suka wuce.
 Ya ajiye akwatin hannun shi kan bed snn ya kalli zarah yace"ki bud'e akwatin kiga ni zanje nayi wanka"
 Daga haka ya wuce zuwa bathroom.
 Zarah kuwa sai da ta ajiye ledar da ke hannun ta snn ta cire mayafi tare da zama kan bed ta bud'e akwatin da duk qananun kaya ne a cikinta masu kyau da tsada sai d'aukar su take d'ai d'ai tana dubawa.
 Sharp sharp saif ya fito daga wanka d'aure da towel a qugunsa sa ya samu sai ci gaba da duba kayan zarah keyi yaje ta bayan ta ya zauna ya rungume ta tare da had'e gefen fuskokin su yana kallon kayan yace"ya kika ga kayan?
 Tace"gaskiya kayan sunyi kyau na waye halan?
 Cikin qara rungume ta yace"da wa kika ga sunyi kama?
 D'auke da murmushi ta d'an juyo ta kalle shi tace"ina zan sani kawai dai kayan sun min kyau sosai wlh har ma sunfi na cikin kayan lefen da nake sawa"
 Yace"kinsan mijinki ya iya za6en kayan da yasan zasu yiwa matar shi kyau ta fito tana d'aga mishi hankali har ma ya riqa ganin sauran mata a maza ita kad'ai yake gani mace.
  D'auke da er dariya zarah tace haba dai dear da gaske knn kana nufin kaya na ne?
  A hankli ya lumshe idanun sa tare da koma ware su akanta alamar eh.
 Cikin nuna jin dad'i tace"kae amma nagode sosai dear but su Nusaiba da umma banga ka kawo musu komai ba.
  Yace"cutie kinsan ba zuwan da zanje in yi ta kwaso tsraba bane da ke d'in ma kayan ne suka min kyau naga bazan iya barin su ba.
 Tace"to amma duk da haka ka barni in d'ibarwa Nusaiba ko kala uku ne"
  Yace"A'a wad'an nn wa ke kad'ai na siyo su ki bari idan munje duk wanda zakiyi yiwa tsaraba sai ki mai kinji,bare Nusaiba wa zai barta ta sa kayan nn"
Zarah ta kalli kayan taga lallai fa in ba aure Nusaiba tayi ba,ba kayan da zata sa a gida bane is too hot da miji kad'ai za'a sama su.
 Ta kalle sa tace"hakane kam amma wae ni kam har yaushe ka sami lokacin yi min siyayya?
 Yace"wani abokina ne ya gayyace ni inje inga sabon boutique d'insa da ya bud'e shine muna zuwa naga gabad'aya kayan dake suka dace nn kawai bansan lokacin da na shiga d'ibar kayan ba se dariya yake ta min wae in daina haka banyi lokacin sa ba sae da na gama d'ibar kayan yanda nake so snn na bashi kud'in shi.
 Zarah dake kallon sa tayi murmushi tare da qara yi mishi godiya.
 Snn ta d'aura masa kiss gefen kunce kmr yanda ya buqata,haka shima ya d'aura mata kiss d'in yana murmushi ya tashi ya nufi dressing mirror ita kuma ta maida kayan a akwati ta rufe ta kaita inda ta dace.
 Yayinda Saif take duk ya cika d'akin da qamshin kalolin turarukkan da yake ta feshewa jikin sa.
 Zarah dai sai kallon sa kawai take har ya gama ya nemi boxer short n singlet ya saka snn ya kama hannun ta suka zauna ma cin kazar su da suka tsaya kan hanya suka siyo suna korawa da hollandia yoghurt mae sanyi,har sai da sukayi qat snn suka je bathroom sukayi brush.
 Koda zarah ta gama shirin bacci tuni saif na kan bed ita kad'ai yake jira duk ya qagu dan tun d'azun jurewa kawai yake gabad'aya ya riga ya tayar wa kanshi sha'awar abun tun a gidan su umma.
   Ae kuwa zarah na hawa gadon ya tafi da ita jikinsa tare da sanya hannun sa a cikin rigar ta ya kama abunda suka fi rikita shi wato na fulanin ta snn yakai bakin sa a nata ya had'e.
 Kan kace minti goma tuni sunyi fatali da kayan jikin su se qoqarin faranta ran juna da suke musamman saif da yake yin komai cike da qwarewa har yana  qara d'aura zarah akan wasu wasanni da take jin kanta awa jin nice d'in zai shid'ar da ita haka shima ihu ne kawai bai mata ba dan sosai tabi dashi yanda yake so.
  Koda suka je ga babban aiki abun ba'a cewa komai dan zarah da kanta tasan cewa tabbas mijinta gwarzon gaske ne,yayinda shi kuma yake jin kmr kaf cikin maza shi yafi kowa sa'ar mace duk da ana cewa farar mace bata da wata n'ima to shi kam ya qaryata abun dan kuwa yau har second round sai da yayi.
 Ae kuwa washe gari bacci sukayi sosai har sai da ya ishe su snn suka tashi.
 Bayan sunyi wanka sun shirya saif da kanshi ya shiga kitchen kmr yanda ya buqata iyakar zarah ta nuna mishi abunda zai sa da haka har suka kammala breakfast d'in suka zo sukayi zaune kan rug suna ciyadda junan su kmr wasu luv birds.
 Lol.
[4/22, 12:44 AM] Paexer: _Thursday 19/04/2018_
*«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»page«» 60*
Suna kammala cin abincin zarah ta d'auko handouts d'inta tana karatu saif na qara fahimtar da ita.
Haka da dare bayan sunyi wanka sun gama cin grilled meat with soft drink,ta hau yin karatun ta har sai guraren sha biyu bacci yayi awon gaba da ita bata ko sani ba.
 Saif dake can zaune kan bed yana wani aiki a laptop ya gama ya rufe snn ya taso yazo gun zarah dake kwance kan rug,yana d'aga ta a hnkli da niyyar zai maida ta kan bed,kawai ta farka ta tashi zaune a hankali ta tafi jikin shi tana fad'in"wae dear bacci nayi?
  Yace"eh tashi muje kan bed"
 Ta janyo handout d'inta had'e da fad'in"um um karatu zanci gaba da yi"
 Ya kar6e handout d'in yana fad'in"no cutie karatun ya isa haka kinji"
 Tace"um um dear wlh tun tafiyar ka ba abunda na karanta fa gashi gobe ne kad'ai baxa mu fara exam ba"
 Yace"to amma cutie tun yaushe kike ta fmn yin karatun nn yi haquri muje kiyi bacci kinji gobe kyaci gaba.
  Idanun ta rufe bata ko iya bud'e su sosai sbd bacci tace"um um dear ka banni result d'ina nake so yayi kyau in fi kowa"
Murmushi kawai yayi dan yaga abun nata kmr gigin bacci ne,ya kama hannun ta suka je kan bed suka kwanta ta wani shige qirjinsa kmr wata er baby mai shirin shan mamma wacce nn take ta koma yin bacci kafin shima yake biye mata.
  Washe gari da asuba saif na bathroom zarah kuwa na kwance se sharar bacci take bai riga ya tashe ta ba tukun.
 Se wayar sa dake ajiye kan bedside drawer ce ta soma tashin ta sbd qarar da ta shiga yi.
 Da qyar ta iya bud'e idonta cike da jin bacci ta kalli gefen da wayar ke ajiye kafin take maida duban ta gun agogon bangon d'akin taga lokacin asuba yayi hakan yasa ta tashi zaune taja jikinta zuwa qarshen gadon tare da had'e kanta da guiwa tana son baccin ya d'an sake ta kafin saif ya fito daga bathroom dan taji alamun yana bathroom d'in bare kuma baya ko wucewa masallaci ba tare da ya tashe ba.
 Jin kiran da ake mishi ya tsinke an kuma sake kira yasa ta d'ago ta kalli wayar ganin mae kiran yasa taji wani abu a ranta wato Sophie,kafin ta iya yin komai se ga saif ya fito da kai tsaye gun wayar tashi yazo yana ganin mae kiran ya kalli zarah da itama ta kalle shi kawai snn ta sauka kan bed d'in ta wuce zuwa bathroom.
 Shi kuma bai d'aga kiran ba sai wayar ya saka silent ya bud'e bedside drawer ya sakata a ciki snn yayi shirin masallaci ya fita.
  Koda ya dawo daga masallaci ita ma zarah ta ida sallah amma bata riga ta tashi daga kan darduma ba tana karatun qur'ani se bayan ta idar snn ta tashi da kae tsaye ko hijab d'in jikinta bata cire ba taje ta samu saif da ya kwanta kan bed ta kwanta a jikin shi had'e da yi mishi ina kwana.
 A natse ya shafo gadon bayanta had'e da amsa mata gaisuwar snn yace"ina fatar cutie na itama ta tashi lfy?
 Tace"lfy qalau na tashi se bacci da nake ji gashi kuma ina so inyi karatu"
  Yace"cutie brain na son hutu fa ki bari idan kinyi bacci kin tashi snn.
 Tace"Dear amma kasan karatu yafi shiga irin lokacin nn"
 Haka ne amma baccin da kk ji bazai bar ki iya fahimtar komai ba gwanda kawai kiyi baccin.
  Shiru tayi sbd sosai kam take jin bacci ko riqa handout d'in tayi ba lalle ne ta iya karanta abun kirki ba,da gabad'aya bata ganin da akwai wani abun da bata iya ba sai dai ta qara daddaqawa kawai.
Jin shirun yayi yawa yasa ya kira sunan ta snn ya kalli fuskar ta yaga ashe ma har baccin yayi awon gaba da ita,nan ya cire mata hijab d'in jikinta snn a hankali ya miqa hannun sa ya ciro wayar sa da ya saka cikin bedside drawer koda ya duba missed calls d'in Sophie sun fi a qirga yayi d'an guntun tsaki tare da cillar da wayar gefe,snn yayi shiru yana kallon silin kmr mai tunani.
 Ranar Monday wato rnr da su zarah zasu fara exam tun wuri ta kammala komai ta shirya saif ya kaita school zata fita mota ya d'aura mata kiss kan goshi tare da mata fatar nasara,d'auke da murmushi tace masa amin had'e da d'aura masa kiss shima snn ta fita tana mai kiran frnds d'inta a waya taji ko sun shigo.
  Saif da ya bita da kallo bashi yaja motar sa ba har sai da ya daina ganin ta snn ya wuce kmr dai kullum.
 Koda suka gama exams d'in rnr saif sosai aiki ya masa yawa a asibiti be samu yaje d'aukar ta ba se drivern ta da ya tura mata.
 Bayan ta dawo har tayi wanka ta girka musu abunda zasu ci,tana kwance kan bed ruf da ciki,as usual handout a gabanta tana karantawa daga ita sai er half vest a jikinta da d'an bum short na jeans,ta tufke gashin kanta da ribbon kmr wata baby doll yanda fakin d'in yayi sama,se wasa take da en qafafuwan ta a hankali tana ta yawo dasu.
  Saif da ya shigo d'akin nata bata sani ba yayi tsaye se kallonta yake tayi can ya sauke numfashi snn ya qarasa gurinta a hankli ya d'an rankwafa tare da lotsa en yatsun sa kan arse dimples d'in ta.
  Da sauri ta juyo tana ganin shine ta saki murmushi had'e da miqewa tsaye ta rungume shi a hankali tana mishi sannu da zuwa.
  Ya amsa yana mai shafa gefen fuskar ta yace"ya exams?
 Tace"wlh Alhmdlh sosai tayi sauqi ba kad'an ba se murna nake tayi ina roqon  Allah yasa har mu gama exam d'in haka zamuyi ta jin su.
  Amin my cutie Allah yasa,ya fad'a d'auke da murmushi har yana jan karan hancin ta.
 Snn ya zauna cikin sauke numfashi dan duk agajiye yake,nn zarah taje ta kawo mishi ruwa masu sanyi yasha snn ta taya shi ya rage kayan jikinsa.
   Ya kalle ta yace"je kitchen da akwai fruits na ajiye a leda ki gyara mana kisa a fridge suyi sanyi idan nayi wanka mukaci abinci se musha koh.
  Ta gyad'a masa kai d'auke da murmushi snn ta tashi ta fita shi kuma ya tashi ya fad'a bathroom.
 Koda ya fito ya samu har ta kammala wancan aikin ta kawo musu abincin su a n d'akin,snn kuma ta ajiye masa kayan sa da zaisa da ta d'auko masa ad'akin sa.
 Bayan ya shirya suka ci abinci snn ta d'auko musu fruits d'in su da ta ke6e musu kankana daban a cikin bowl ta zube gwangwanin peak milk ta ruwa biyu a ciki snn ta saka qanqara se bayan sun gama shan sauran furit d'in snn suka sha kankanar,ae kuwa saif sosai yaji dad'in had'in har yana santi,wae meye sirrin wa ya koya mata hakan.
 Tayi murmushi kawai bata ce masa komai ba dan abune da baza ta gaya mishi ba,itama a WhatsApp wata frnd d'inta da suke school d'aya ta gaya mata tayi hakan idan sun had'u da mijinta abun ba'a cewa komai da ita har shi sai sun rasa wace duniyar suke.
 Gogan da dama buqace yake da cutien shi bcos an kwana biyu ba'a had'u ba ana gama sllr isha ya lalubo abarshi suka kashe juna da soyayya.
 Har bathroom da suka je wanka ya kasa barinta ita kuwa bata hana shi ba dan had'in kankanar ya sakar mata milk sosai da har bata ji wani zafi ba,shiyasa nn kawai ta sake bada kai bori ya hau.
Se byn sun gama jin nice d'in su snn sukayi wanka suka fito.
Saif ya wuce d'akin shi dmn shirin bacci,Zarah kuwa bedsheets d'in bed d'inta ta cire sbd duk sun 6ata shi yayi staining taje tasa a washing machine snn da ta dawo ta shinfid'a wani,tana gama shirin bacci se ga saif ya dawo d'akin da shima har yayi nasa shirin bacci sai zuba qamshi yake kmr dai zarah wacce ya nufi gurinta cike da so yana murmushi ya d'aura mata kiss snn ya kama hannun ta tare da  d'aukar mata handout d'inta suka tafi d'akin shi.
Koda akayi two weeks har su zarah sun gama exams se zancen zuwa England suke da har saif ya gama shirya musu komai na tafiya a gobe suke shirin zasu tafi,da gabad'aya yinin yau a gidan umma sukayi shi Nusaiba sai jin take kmr suje da ita England d'in taga Abba amma exams d'inda suke bazai barta ba, yusra ko tuni sunyi hutu tazo gida se rigima take ta yiwa umma hadda kuka ita se tabi su zarah gidan su gobe in zasu je England suje da ita taga Abba,cikin rarrashi da wayo umma ta samu ta haqura acewar ae zata je itama ta bari idan zata je se su tafi abinsu tare.

Da dare bayan su zarah sun koma gida,sun gama jin nice d'in su suna kwance suna sauke gajiya,zarah dake kwance kan faffad'an qirjin saif tana yawo da hannunta a kan qirjin nasa a hankali,kmr yanda shima yake shafa gadon bayanta.
 Muryar ta kmr da shagwa6a can ciki tace"wae ni kam dear kuma kuna jin zafi kmr yanda muke ji kuwa?
 Saif yace"A'a bama jin wani zafi d'in nn se in munyi da yawa kema rashin sabo ne da in kika haifu everything will be fine zaki daina jin zafin"
 Muryar ta cikin shagwa6a sosai tace"har sai na haifu fa kace?
 Saif ya tashi zaune tare da ita a jikin sa yana kallon ta da kulawa snn yace"eh ko kina jin zafin ne sosai"
  A hankli ta girgiza masa kai tare da qara lafewa a qirjinsa.
  Saif yayi shiru can yayi er dariya cikin girgiza kae yace"cutie knn meyasa kika min wnn tambayar haka kawai tazo miki?
  D'auke da murmushi ta d'aga fuskar ta ta kalle shi se kuma da saurin ta cikin jin kunya ta maida fuskar ta a qirjinsa ta 6oye.
 Cikin murmushi saif yakai bakin sa a kunnen ta ya mata magana can ciki da ita kadai ta iya jin abunda yace,ba shiri ta sauka kan jikin sa tana dariya ta wuce da gudu zuwa bathroom ya bita,se bayan sun gama soyewar su sukayi wanka snn suka fito.
 Washe gari jirgirin su ya d'aga zuwa England,zarah na rungume jikin saif duk ta wani cumuimuye shi sbd tsoron tashin jirgi sai da jirgin yabi normal snn ta d'an saki jikinta but still tana manne a jikin sa ta kasa sakin shi,shi kuwa tuni an saba se murmushi kawai da yake mata tare da qara rungume ta a jikinsa yana ji ko wani motsin kirki bata son yi har tayi bacci.

Sorry 4 dis one
[4/22, 12:44 AM] Paexer: _Saturday 21/04/2018_
*«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»page«» 61*
Da dare bayan sun isa har ma sunje asibiti gurin Abba sun dawo masaukin su sunyi wanka sun ci abinci suna kwance cikin shirin su na bacci,sun gama waya da su umma knn se ga kiran sophie ya shigo wayar na hannun zarah ta miqa masa wayar cikin nuna ko in kula amma a ranta ita kad'ai tasan me take ji dan yau kusan karo na uku knn bayan rnr amma bata ta6a ce masa komai ba sai dai kawai tayi kmr abun bai dame ta ba,yayinda shi kuma baya ko d'aga kiran sai dai kawai ya saka wayar silent har se ta gaji da kiran ta daina,yanzu kuwa zarah na bashi wayar kashe wayar yayi gabad'aya ya ajiye,yana me kallon zarah da ta wani qara shigewa jikin sa ta hau yin bacci,haka shima take baccin ya kwashe shi,da tun da ya kashe wayar sa ya ajiye bai sake lokacin ta ba asalima washe gari wata er qaramar waya ya fidda da zai ci gaba da aiki da ita har su bar England d'in,dan yasan jiya da Sophie tayi saurin fahimtar ya shigo qasar da sai dai ya ganta kawai kmr yanda ta tashi yi mishi a wancan karon.
  Kwanan su biyar a garin kullum idan sunje asibiti sun duba Abba,saif ya tafi da zarah suyi ta yawatawa koina a cikin garin tana bud'e ido cikin zallar soyayyar su da suke ta zubawa abinsu da duk wanda ya gansu yasan cewa yes they are couples,se fotuna suke tayi a had'ad'd'in gurare daban daban da zarah ke ganin guraren awa aljannar duniya abunda take gani a film se yau gashi a fili tana gani,shiyasa kullum har Allah Allah take su fita.
 Yau wata irin soyayya suke ji a tsakanin su da gabad'aya sun shagala ko asibiti ma basu je ba,se aikin faranta ran juna da suke,can da qyar dai ba dan sun gaji da abunda suke yi ba suka tashi suka je bathroom sukayi wanka suka fito d'aure da towel iri d'aya,zarah na maqale a bayan saif ya goyota da kae tsaye kan bed ya dire ta suka hau shafawa junan su mai,da tuni zarah ta gama shafa mishi amma shi still yana nn guri d'aya kan dukiyar fulanin ta yana ta faman shafar su wae duk mai ne ake ta shafa mata da ya kasa d'auke hannun sa.
 Har zarah taga abun yayi yawa cikin dariya tace"wae ni kam dear wane irin shafa mai ne haka tun d'azu se guri d'aya ake ta fmn murza min...Ah! wayyo! ta fad'a a shagwa6e sbd matsar da ya musu,snn ya kwantar da ita ya mata rumfa cikin dariya yana fad'in"ni da abuna se a hana min yanda naga dama hadda sa min ido.
  Zarah da ita ma dariyar take tace"to Dear asibiti fa zamu je ka sani lokaci yana tafiya"
    yace"ba wani lokaci da ya tafi ni sai na gama wasa da abokanan wasa ta tukun"
   Nan kawai yaje zai kai bakin sa a kansu ta janye jikinta da sauri zata sauka kan gadon tana dariya ya fizgo ta yana mata cakulkuli har ya samu ta bar shi ya shiga wasa dasu son ranshi har ma yana neman wuce guri,se kawai qarar er qaramar wayar sa ta katse shi,ya samu da qyar ya tsaya da abunda yake,ya tashi jikin sa duk a kasale  haka ma idanun sa har sun sauya kala yakai hannu kan bedside drawer ya d'auki wayar.
  Zarah dake kwance se kallon gwarzon mijin nata take da baya gajiya da abun,duk da dai yakan yi kwana biyu koma fiye kafin yake laluba ta amma duk ya lalubo ta to fa rnr ta bani se tayi haquri dashi.
 Nan ta sami kanta da tashi ta matsa gab dashi ta rungume shi tare da kwantar da kanta a gadon bayan shi,snn ta zagaya da hannuwan ta a hankali kan faffad'an qirjinsa tana shafawa.
  Yayinda shi kuma cike da murna ya qarasa wayar da yake ya juya yana gaya mata Abba ya farfad'o,wani irin dad'i zarah taji,yace tayi sauri su shirya su tafi,ae kuwa ba 6ata lokaci cike da murna suka kammala shirin nasu suka tafi se asibiti.
Koda suka je ba a bar sun shiga ba ana duba shi se bayan an gama snn aka barsu.
 Sun sami Abba zaune an d'an tado mishi gadon ta yanda zai jingina bayan shi,wanda duk da yanayin da yake ciki na jin jikin nasa wani iri ba dad'i sbd jimawar da yayi a kwance bai hana ya sakar musu murmushi ba snn cikin muryar sa da bata fara fita sosai ba ya amsa ya jikin da suka mishi,yana kallon yanda duk sukayi wani irin kyau da haske musamman zarah,da yake shirin zai tambaye ta ya lafiyar jikin ta dan har yanzu tunanin tana da ciki ne a tare dashi.
  Bai riga yayi mgnr ba dai Abban kd ya kai masa waya a kunne cike da murna yana fad'in ga hajiya zata yi magana da kai.
  A hankali hannun sa na rawa ya d'an iya kama wayar snn cike da girmawa ya amsa sallamar da ta mishi cikin murna tana fad'in"kae Alhamdulillahi! Alhamdulillahi!!,na gode Allah da ya tada min kai bai bar wnn muguwar matar ta illata min kai ba.
  Abba dake sauraren ta haka yaji zancen wani iri dan shi tun lokacinda sukayi accident bai sake sanin inda yake ba sai farfad'owar da yayi yau.
  Amma sai bai ce mata komai ba se biye mata yake yana ta fad'in Amin kan irin addu'o'in da ta jero tana mishi.
 Yana gama waya da ita ne se ga kiran umma ya shigo a wayar Abban kd d'in wacce kejin awa tayi tsuntsuwa tazo taga Abba shine ta matsu taji ko an gama duba shi taji ko muryar sa ce dan koda Abban kd ya kirasu ya snr da su duk lokacin ana duba shi,se gashi ana d'aga kiran kwatsam taji muryar Abba ae kuwa sosai cikin murna da natsuwa ta shiga yi mishi ya jiki,yayinda shima a natse yake waya da ita da duk yake jin kewar ta sosai a ranshi,duk da baisan iya tsawon lokacinda ya d'auka a kwance ba amma se yaji kmr ya jima bai ganta ba.
  Yana ji ta bawa su Nusaiba wacce cikin kukan murna take wayar dashi tana mishi ya jiki,snn bayan ya gama waya da ita ne aka bawa yusra da tayi ta mishi surutu tayi missing d'in sa yaushe zai dawo ya kawo mata chocolate,Hjy tace wae kayi tafiya kullum in na tambaye ta kai haka take ce min har ma aka bamu hutun makaranta na dawo gida baka dawo ba.
  Ta qarashe mgnr ne kmr zatayi kuka
 Abba dake sauraren ta cikin rarrashi yace"kar ki damu autar Abba ae na kusa dawowa kinji"
 Tace"to Abba ka saya min baby doll mai kyau kmr ni"
 Yayi murmushi yace"to shikenan"
 Nan bayan ya gama waya dasu, umman kd ta kira ta mai ya jiki snn aka barshi yasha tea mai kauri da aka had'o mishi.
  Shan tean yake a hankali har ya gama yana tunanin mgnr hajiya.
  Kana ya kalli Abban kd a natse yace"Naji Hjy tayi wata magana da nake ji kmr akwai abunda ya faru ina cikin rashin lafiyar nn ban sani ba"
Da kulawa Abban kd ke kallon sa yace"wace irin magana knn?
  Yace"Muna waya naji tana cewa ta gode Allah da bai ba wnn muguwar matar damar illata ni ba shine kaina ya d'aure ban fahimci zancen nata ba me take nufi?
 Abban kd da yayi shiru can ya numfasa snn ba tare da ya 6oye masa ba ya shiga zayyano masa duk abunda ya faru,sakin da saif yayiwa zarah ne kawai bai fad'a masa ba dan baya so yasan da wnn.
  Abba da ya gama sauraren shi ya dad'e shiru kmr bazai ce komai ba,can dai ya jinjina kansa yace"Kubra knn Allah ya kyauta duk abunda aka ce tayi ba zanyi mamaki ba dmn komai zata iya aiwatarwa,shiyasa saifuddeen kaga na 6oye maka ban gaya maka ainihin wace ce mahaifiyar ka ba sbd nasan bazaka yi farin ciki da jinta ba,amma kuma ina mai baka haqurin rashin gaya maka da nayi dmn nasan yanzu bayyanar da tayi kayi baqin cikin rashin sani tun farko da kuma baqin cikin jin cewa maman yusra ba mahaifiyar ka bace, ka yafe min saifudeen,ka yafe min haqiqa na aikata kuskuren da nazo ina yin dana sani da hakan ne ya janyo ka samu uwa irin wnn.
   Saif dake zaune kan farar kujerar roba nn kusa da Abba,idon sa tap da qwallah ya kama hannun Abba yace"Abba ni baka min komai ba wlh,kuma ni har yanzu umma ce mahaifiya ta ba wnn mtr ba,da ba abunda zance mata illah Allah ya shirye ta yasa ta gyara halayen ta zuwa na kirki idan tana da niyyar shiruwa,amma bazan ta6a iya d'aukar ta a matsayin uwa ta ba,ta haife ni ne kawai,but still umma ita ce uwata ta har abadah da bazata ta6a yin fatali dani ba.
 Abba dake kallon sa cike da tausayi ya dafa kanshi cikin rarrashi yana bashi magana,snn ya kalli zarah wacce ke kallon saif d'in cikin damuwa ganin yana fidda qwallah,da ita ma take hawaye har sun ciko a idanunta.
 Yace"zarah kema kiyi haquri da abunda ya faru kinji,ina fata dai bata ta6a lafiyar ki da abunda kike tare dashi ba ko?
  A hankali Zarah ta kalli saif da shima ya kalle ta snn ta sadda kanta qasa tare da girgiza kan nata a hankli alamar a'a.
  Abba yace"Alhmdlh Allah na gode maka,Allah kuma ka qara tsare mu daga dukkanin  muguntar d'an adam har ma da aljan da kuma sharrin su gabakid'aya,ka kuma kare mu da aikin dana sani duniya da lafira.
  Amin suka fad'a har suna tofa addu'ar.

Wa enda gabad'aya yinin ranar a cikin farin ciki suka yi shi  har su umma kuwa dake jin kmr su biyo jirgi suzo musamman Hjy da har cewa tayi ita kam tana nn tafe Abban kd yace"a'a duk suyi zaman su ae tunda ya farfad'o baya jin za'a yi sati basu sallame shi ba dan jikin nasa Alhmdlh ya samu kulawa sosai a lokacinda baya farke shiyasa ma bai masa irin nauyin nn ba.

 Da dare bayan su zarah sun koma masaukin su sunyi wanka cikin shirin su na bacci suna kwance shiru da tun lokacinda suka dawo zarah ta lura da yanayin saif kmr wani mara lafiya yake yin abubuwan shi.
 Da kusan kullum in suna kwance zasuyi bacci hannun ta baya rabo da yawo akan faffad'an qirjinsa tana shafashi a hankali,haka shima gadon bayanta zai yi ta faman shafawa a hankali har suyi bacci,amma yau ita kad'ai ke yawo da hannun ta akan qirjinsa,shi sai d'aura hannun sa kawai yayi a gadon bayanta ya kasa moving dashi wanda hakan yasa tasan lallai akwai abunda ke damun shi.
  "Dear"
ta kira sunan shi a natse"
Amma bai amsa ba se saurin kae hannun sa yayi ya share hawayen da suka sauko mishi.
  Nan ta tashi zaune a hankali tana kallon sa tace"Dear kuka kake yi me yake faruwa?
  Saif dake kallonta idanun sa ne suka sake cikowa da qwallah yace"cutie bana so in tuna ba umma ce ta haife ni ba ina jin ciwo a raina ko kad'an banji dad'in da wnn mtr ta kasance uwata ba,da har bana son 'ya'yan da zan haifa suji labarin ta,nn ya miqe zaune tare da had'e tafukan hannayen sa cikin zubda qwallah da gani kasan sosai abun ke masa ciwo a rai,yace"I beg cutie kar ki bar yarana suji labarin ta wlh bana so.
 Zarah da duk kukan take ji itama ta kama hannayen sa tare da kwantar da kanshi a qirjinta tana shafa sumar kanshi a hankali ba tare da ta iya ce masa komai ba se hawaye da suka silalo a hankali kan kumatun ta.

Washe gari koda suka tashi kmr ba su ba se abubuwan su suke tayi cike da nishad'i,musamman saif da duk ya tuna Abba ya farfad'o se yaji kamar ba wani abunda ke damun shi a duniya shiyasa ma se sauri yake su shirya dmn suyi suje asibiti su ganshi.

Koda akayi 3dayz Alhmdlh jikin Abba ya qara sauqi har yana iya tashi da kanshi ba sai an taimaka mishi ba shiyasa ma suke sa ran za'a sallame shi d next day,jibi se su halba zuwa 9ja.
  The next day d'in kuwa aka sallame shi da dare bayan sunyi sllr isha saif yaja zarah suka fita dmn ta siyo en tsaraba ga duk wanda take son yiwa kmr yanda ya mata alqawari.
Sun gama siyayyar  sun fito riqe da ledodi a hannun su,kawai sukayi kicimus da Sophie wacce tana ganin saif ta tsaya cak tana kallon shi,haka shima wanda kafin ya iya yin komai sae jin yayi ta rungume shi da sauri cikin sakar masa kuka.
  Nan ya kalli zarah a hankali cikin kasa janye Sophie daga jikin sa,se ma hannun ta da yake riqe dashi ya sake yana kallonta da kulawa cikin kwantar da murya yace"Dan Allah ina zuwa kinji cutie,ki jirani a nn kar kije ko ina yanzu zan dawo magana kawai zamuyi kinji"
 Komai zarah bata iya ce masa ba tana kallo yaja Sophie se binsu take da kallo idanunta tap da qwallah har suka 6acewa ganin ta,ta kai hannun ta a sanyaye ta share qwallar da suka zuba mata snn taje ta nemi taxi ta wuce masaukin su.
 Da isar ta bedroom ta saki ledar hannunta taje da gudu kan bed ta fad'a cikin fashewa da kuka,sbd abunda take ji a ranta in ba kukan tayi ba bata jin zata ji sauqin abun.
 Sai da tayi mai isar snn ta tashi jikin duk a sanyaye kmr wata mara lafiya,ta rage kayan jikin ta ta fad'a bathroom tayi wanka,tana fitowa tayi shirin bacci cikin wata er farar riga me kmr vest da wandon ta fari d'an guntu iya rabin cinya.
  Sai a snn saif ya dawo har ma tana shirin kwanciya,ya nufe ta da saurin sa  ya rungume ta jikin sa cikin sauke numfashi yake fad'in"kin tsorata ni cutie meyasa kika dawo bayan nace ki jirani"
  Bata ce masa komai ba se janye jikinta tayi a hankali daga nashi ta kwanta cikin juya masa baya taja blanket ta rufe  jikinta.
  Nan saif ya ajiye ledar da ke hannun shi jiki sa6ule ya zauna gefen kan bed d'in kusa da ita tare da kai lallausan hannun sa yana shafa sumar kanta dake tufke da ribbon muryar sa a natse yace"am sorry cutie kiyi haquri nasan ban kyauta ba da na barki kina ta faman jirana wlh ta kasa fahimta ta ne da wuri sai da qyar snn na samu,shine koda nazo ban kangi ba duk hankali na ya tashi se neman ki nake tayi ina kiranki a waya amma baki d'aga ba,dawowar da ma nayi waya ta zan nemo in kunna dmn na samu in duba direction d'in inda kk,but am sorry kinji i didn't mean to hurt u"
 Zarah da ta bashi baya jin maganar tashi take yana qara 6ata mata rai ne kawai,wacce cike da takaici ta share hawayen da suka zubo mata,snn ta tashi taje ta d'auko wayarta ta 6alle ta cire sim card,ta kuma cire zoben diamond d'inda ke hannun ta da ya bata ta had'a da wayar ta ajiye mishi tace"ga kayanka nn bana so kar ka sake sakani a cikin harakar ku kaje can kuci gaba da yin abu iri d'aya kaida ita,idan ma kun iya qauna tasa ku had'iye juna ku kuka sani bai damen ba,dama can ba qaunar junan mu muke yi ba har zuwa yanzu da jikina kawai kake so ba wani abu ba,to wlh ka sani daga yau bazan qara baka jikina ba,kaje can ita taci gaba da baka dama ae kun saba.
 Nan kawai ta kwashi blanket da pillow taje can kan sofa ta kwanta.
 Sosai cikin damuwa Saif ya bita da kallo kafin yake maida duban sa kan wayarta da ta ajiye masa da zobe,yasan of course wayar su iri d'aya ce da Sophie amma zoben kam musamman ya siyawa zarah shi asalima duk soyayyar su da sophie bai ta6a siya mata zobe ba,wanda yasan duk 6acin rai ne kawai yasa ta had'a harda zoben ta jiye masa ba dan ta ga irin shi a yatsar Sophie ba se irin wayar su kawai da ta gani a hannun ta.
[4/23, 10:19 PM] Billy giro😊: _Monday 23/04/2018_
*«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*



*«»page«» 62*
 Nan ya tashi a hankali ya qarasa gurinta cike da son ya rarrashe ta amma fir taqi saurarrar shi,dolen shi ya barta yaje ya shirya musu kayan su sbd sammako zasuyi gobe,yana kammalawa yaje yayi wanka yayi shirin bacci snn ya sake komawa gun zarah wacce tuni tayi bacci ya gurfana a hankali gab da ita yana kallon fuskar ta ya d'aura lallausan hannun sa yana shafa sumar kanta muryar sa a hankali yace"i swear cutie ke nake so ba jikin ki kad'ai ba,kiyi haquri ki daina fushi dani kinji bazan iya jurewa ba.
 Nan ya rankwafa dai dai goshin ta ya d'aura mata kiss snn ya qara gyara mata blanket ya miqe tsaye sai kallonta yake tayi kafin yake barin gurin yaje ya kwanta.
Washe gari tunda ya tashe ta sallah daga can kawai tayi wankan ta tana ida sallah ta hau shiri ba tare da tayi mishi ina kwana ba kmr yanda take mishi kullum idan ta ida sallah,saif da bai riga ya tashi daga kan darduma ba kallonta kawai yake bai ce mata komai ba,ya tashi yaje yayi wanka ya hau shiri shima.
  Yana gama shiri er qaramar wayar sa ta hau ringing ya d'aga kiran yana mai kallon zarah da ta fitar da kayan tsarabar da yasa mata a cikin kayanta da zata bawa mutanen ta duk ta watsar bata so.
  Ya qarasa gurin ta a natse ya kama ta zai tafi da ita jikinsa tayi saurin qwacewa  ya bata waya yace"ungo to ga umma tana son kuyi magana"
  Ba musu ta kar6i wayar ta hau yin magana da ita cikin harshen fulatanci,yayinda saif ya duqa se kwashe kayan yake da ta watsar zai maida a cikin akwatin ta,dai dai ta gama wayar tayi saurin janye akwatin shaye da toka tana kallon shi,yayinda shi kuma ya d'anyi murmushi cikin rarrashi yace"haba my cutie yi haquri kinji,in kin fitar da kayan nn ya kk so nayi dasu kinsan banda inda zan sa miki su.
Tace"ni ina ruwana ai sai ka barsu a nn ni ba abunda zanyi dasu bana son duk wani abu da ya fito daga gare ka,har kai d'in ma ka tafi can gurinta ita da ta damu dakai,har abadah kuwa ni bazan damu dan ba kai ba.
 Kallonta kawai saif yayi da alama mgnr bata masa dad'i ba amma baice mata komai ba se kayan ya zuba a kwatin ta zai rufe,bata barshi ba se qoqarin fidda kayan take.
 Fuskar sa a d'aure yace"cutie bana son raini fa kika fitar da kayan nn wlh ranki zai 6aci"
  Idanun ta tap da qwallah ta kalle shi tace"to nace maka bana so dole ne"
Cikin zaro mata ido yace"eh dole ne sai kin kar6a kin kuma ba duk wanda aka siyo domin shi.
  Nan kawai ya rufe akwatin.
 Ita kuma ta miqe cikin kuka mai kmr na shaga6a tana fad'in"ni wlh bana so kuma ba wanda zan ba ko munje sai dai na zuba su a shara.......wayyo! Tayi ihu sbd qafar ta da ya tad'e zata fad'i ya kama hannun ta ta fad'o kan jikin sa ya kwantar da ita tare da yi mata rumfa yaja karan hancinta cikin murmushi yace"fushi baya miki kyau cutie is enuf ki yafewa mijin naki haka bazai sake ba kinji,ya qarashe mgnr cikin kama kunnen sa snn ya janye tare da d'aura mata kiss yace"kuma ki sani ni ke nake so ba jikin ki ba.
Zarah da ke kallon sa cikin ta6e baki tace"hm wanda yake sona da gaske ae kafi kowa sanin shi yana can rashin samu na har yasa sai faman ciwo yake tayi,dan haka kama daina wahalar da kanka kana fad'ar abunda bashi bane a ranka jikin nawa ne kakeyiwa ba kuma zaka sake samun sa ba na gaya ma.
 Nan kawai ta tashi saif ya bita da kallo d'auke da idanun sa da har sun sauya kala kan mgnr ta da ta masa ciwo yana kuma mamakin a ina taji jamil na sonta shi dai bai gaya mata ba ya kuma san jamil bazai ta6a gaya mata ba bare shi Abban kd da su kad'ai ne suka san da mgnr.
  Bai ce mata komai ba dai se tashi yayi yaje ya bud'e qofa sbd knocking d'in da aka musu,koda ya bud'e d'aya daga cikin ma'aikatan hotel d'in ne ya kawo musu breakfast,da saif d'in ne ya kira a d'azun dmn a kawo musu ya kar6a ya shigo dashi ya ajiye kawai.
 Wanda dashi har zarah ba wanda ya kula breakfast d'in har suka gama shirye shiryen su suka fita,suka had'u da su Abba da duk hotel d'in suke,suna gama gaisawa ba 6ata lokaci suka wuce gabad'ayan su  zuwa airport.

6angaren su umma kuma baki baya rufuwa har umman kd tazo nn garin sai shiryen shiryen tarbon su Abba suke abinci kala kala kmr masu shirin yin kasaitacciyar walima.

Wa enda koda suka gama jera liyafar a kan dining,su Abba har sun kusa isowa,se shiryawa sukayi suka je airport dmn tarbon su,su duka gabad'ayan su har su Nusaiba.
Inda umma ce ta tuqa mota da kanta,sbd drivern da ke kai zarah school da yanzu ya zamo kmr drivern su na gida,shi kuma Hjy zai kai,da itama ke son taje ta tarbo d'an nata da ta matsu tasa shi a ido,haka shima jamil wanda Alhmdlh yanzu jikin sa sosai ya masa sauqi,bai zauna ba sai da yaje tarbon Abba.
 Da gabad'ayan su basu jima da isa ba se ga jirgin su Abba yayi landing,aka tarbi juna cikin murna da farin ciki,yayinda en jarida keta tururuwar ganin Abba sbd tuni sunji labarin cewa ya farfad'o dama rnr da zai dawo shine suka kasa suka tsare kowa yana son yaji wani abu daga gare shi a buga wasu jaridun kuma.
 Police ne suka hana su suka bar su Abba suka wuce,da su kuma dmn kare lafiyar shi kad'ai suka zo gurin.

Bayan sun isa gida ana zaune gabad'aya kowa kan dining se cin abinci suke tayi cike da nishad'i.
Saif da still yana nn a cikin yanayin sa na kafin su baro England,ya kasa cin abincin yanda ya kamata se yi yake yana kallon zarah wacce ke zaune a kusa da gefen shi ta maida hankalin ta se cin abinci take,da take jin kmr bata ci sbd yunwar da take jin na qara taso mata,sbd da ita har saif throughout fushi bai bar sunci komai ba sei yanzu,da har ma ta kusa cinye abincin amma yunwar bata daina ci gaba da azalzalar ta ba,awa ma bata sa komai a cikin nata ba take ji,da lokaci d'aya taji wani irin tashin zuciya har ma amai na qoqarin qwace mata,nn tayi saurin rufe bakinta had'e ta miqewa tsaye cikin hanzari zata kwasa aguje,kawai da miqewar ta wani irin  jiri ya d'ibe ta da lokaci guda ta zube qasa a gurin.
  Ba shiri saif ya ture kujerar da yake zaune akai,ya nufe ta da sauri ya kamata ya tafi da ita jikin sa yana kiran sunanta a rud'e cikin girgiza ta.
  Yayinda tuni kowa yayo kansu se kiran zarah d'in suke tayi suma duk a rud'e,jamil ya d'auko ruwa da sauri ya bawa saif ya shiga yayyafa mata still ba alamar zata farfad'o,nn kawai da saurin sa ya tallabe ta ya haura sama da ita se d'akin su Nusaiba ya kwantar da ita kan bed,su umma da ke biye dashi bai iya ce musu komai ba duk ya rud'e se fita yayi yaje d'akin Abba ya d'auko briefcase d'in Abba ta zuwa asibiti ya hau duba ta.
  Bayan ya gama dube duben sa kawai yaja blanket ya rufa mata jikinta kansa qasa ya kasa kallon su se fita da yake qoqarin yi,hankalin su a tashe suka ce lafiya wae me yake faruwa ne saifudeen ka dubata kuma se qoqarin fita kake baka ce mana komai ba.
  Still bai iya kallon su ba se murmushi yayi cikin sosa bayan kansa irin na jin kunya d'in nn ya kuma fita abun shi ba tare da ya iya ce musu komai ba.
  Hakan yasa dukkan su sukayi murmushi dan yanayin sa kad'ai ya fahimtar da su abunda knn,nn Hjy taje da murnar ta ta gwale idanun zarah a hankali tana dubawa har ma da en yatsun ta duk ta duba,kafin take kallon su baki washe ta d'aga hannayen ta sama tana fad'in"kae Alhmdlh murna kan murna ina en jaridun suke suzo yanzu kam bakina sake zan gaya musu jikana ya kusa haifa min wani mijin,su buga jaridu duniya kowa yaji a tayani farin ciki,abun baqin ciki shine ba dad'in fad'a.
 Nan ta miqe cikin yin rawar su ta tsofaffi idan suna yin murna.
 Su Abba dake kallonta se murmushi suke tayi,a nn Abba ya kalli umma dake kusa dashi wacce bakinta baya ko rufuwa yace"hala dai Hjy ta manta da dama zarah ciki ne da ita inaga kmr na gaya mata fa"
  Umma tace"Alhj kafa san dama can zargi mukeyi bamu tabbatar ba wanda a lokacin da mukeyin zargin babu cikin se yanzun ne aka same shi...."Au haba"
 Abba ya fad'a bakin sa murna fal ya d'aga hannun sa sama yace".
الْحَمْدُ لِلَّهِ الَّذِي بِنَعْمَتِهِ تَتِمُّ   الصَّالِحَات.
_(Godiya ta tabbata ga Allah wanda saboda ni'imar sa ce kyawawan ayukka suke cika)_
        *Wato addu'ar da Annabin mu yake yi idan abun farin ciki ya same shi.*

Bayan Abba ya ida addu'ar snn ya qarasa gurin zarah ya dafa kanta yace"Allah ya baki lafiya zarah,yasa dukkanin mu nn muna raye koda zaki haifo mana abunda kike tare dashi rayayye mai albarka.
 "Amin"
dukkan su suka fad'a.

Saif kuwa yana sauka downstairs jamil yazo da saurin sa yana fad'in"yadai hope ta farfad'o?
  D'auke da murmushi yace"eh a'a is...
  Ya d'an sosa bayan kanshi kmr yana jin kunyar gaya mishi amma kuma farin ciki bazai barshi ya kasa fad'a mishi ba,nn kawai ya rungume shi yana fad'in"congratulation u are going to be a father"
  Jamil da duk ciwon da yayi har ma yana qoqarin manta inda yake ba abunda ya duqufa akai irin addu'ar Allah ya yaye masa son zarah cikin ikon Allah kuwa koda yaji sauqi se yaji kmr an zare masa son nata gabad'aya,se ma qaunar zainab da ta d'arsu a cikin ranshi kan irin hidimar da tayi tayi dashi da baya da lfy.

Ya d'ago saif da sauri yana kallon sa cikin murna yace"kae haba dai!

"Allah kuwa"
Saif ya fad'a d'auke da murnar da yake tare da ita.
 Snn a sanyaye cikin jin tausayin jamil ya kama hannyen sa yace"ina mai qara baka....jamil dake murmushi yayi saurin katse shi cikin dalla mae harara yace"4 what zaka qara bani haquri dan Allah ka daina karma wani yaji mu,yanzu lokaci ne da zamuyi farin cikin qaruwar da zamu samu ba wata magana can da ta riga ta wuce ba,and idan mun natsu ma da akwai labari.
  Cikin murmushi saif yace"to shikenan yanzu muje ka rakani da akwai magungunan da nake son siyowa kafin zarah ta farka.
  Nan suka fita se murna suke tayi musamman saif da farin cikin nasa ma bansan ya zan misalta muku shi ba.

Wanda koda ya dawo ya samu Hjy ta wuce,haka ma su umman kd.
  Nusaiba kawai ya samu a d'akin ita da umma,yusra na can tare da Abba a d'akin shi.
Da shigar sa d'akin kawai yaje yayi tsaye a kusa da zarah d'auke da murmushi yana ta kallon ta da still tana kwance bata farka ba.
  Umma dake kallon sa tayi murmushi tace"ya akayi ne saif magunguna ne ka siyo?
  Sai da ya sadda kansa qasa snn ya d'an sosa bayan kanshi yace"eh umma ina so ne idan ta farka se tasha magungunan"
  Nan ya ajiye ledar magungunan kan bedside drawer yace"ni zanje  masallaci nayi sallah "
 Tace"to shikenan jamil fa ko ya wuce?
  Eh yanzun ya sauke ni ya wuce,suma su Abban kd da Hjy sun wuce ne naga ban gansu ba?
  Tace"eh sun wuce yanzu yanzu nn kasan yaya ba son tafiyar dare take ba duk da dai daren ya riga ya musu.
 Nan saif ya kalli agogon bangon d'akin 9pm yace"haka ne kam to Allah ya kaisu lafiya"
  Amin umma ta fad'a kafin yake fita daga d'akin.

Bai jima da fita ba zarah ta farka wacce ba shiri ta zame daga kan gadon se kwara amai take abun ba sauqi har duk jikinta ya lallace wacce cikin jirin da ke d'ibar ta ta tafi suuu tana qoqarin lemewa a cikin aman kuma,Umma tayi saurin kamata ta wuce da ita bathroom dmn ta wanke mata jikinta.
Nusaiba kuwa fita tayi ta d'auko tsumma ta hau goge d'akin wacce tana jin yanda zarah keta yin wani amman kuma a bathroom se duk gabad'aya taji tausayin ta amma kuma har ranta wani irin dad'i take ji da samuwar cikin.

Koda saif ya dawo ya samu ta gama goge d'akin sai qamshi yake.
  Ganin gadon wayam ba zarah bai kuma ga umma ba ya tambaye ta ina suke?
  Kafin Nusaiba tace komai sai gasu sun fito daga bathroom,Zarah na manne a jikin umma ta riqo ta sbd gabad'aya jikin nata ba qarfi ko tsayuwa ma bata iya yi da kyau.
  Saif ya qarasa gurin su ya kama ma umma ita yana tambayar me kuma ya faru umma naga jikin nata very weak ko tayi amai ne?
  Umma tace"eh amai tayi sosai inaga ma duk ta amayar da d'an abunda taci,Nusaiba je had'o mata tea kinji tasha ko zata d'anji qarfin jikin nata.
 Nan Nusaiba ta fita umma kuwa har zata koma bathroom dmn ta duba kayan zarah da tasa a washing  machine,sei ga yusra ta shigo d'akin acewar Abba na kiran umma,nn umma ta fasa zuwa bathroom d'in ta kama hannun yusra suka fita.
  Yayinda saif ya zauna a hankli kan bed tare da zarah dake manne a jikin shi,se kallonta yake tayi kafin yake kai hannun sa ya gyara mata towel d'inta da yake son zamewa daga kan qirjinta,snn da kulawa ya shafo cikin ta yana kallonta yace"sorry babyna ya baki wahala koh?
 Zarah dake jin jiki da qyar ta d'ago ta kalle shi kmr da mamaki ta d'aura hannun ta akan hannun sa da ya dafa cikinta muryar ta a hankali can ciki tace"baby?
 D'auke da murmushi ya lumshe idanun sa tare da ware su akan ta alamar eh.
  Zarah dake kallon shi samun kanta tayi da yin murmushi cike da jin dad'in samuwar cikin da kuma jin kunya har ma tana 6oye fuskar ta a qirjinsa.
[4/26, 9:37 PM] Billy giro😊:  _Thursday 26/04/2018_
*«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*

_Wannan page in naki ne my lovely besty fa'iza Anfa Allah ya bar min ke akan qaunar da kk min._
    _I heart u irin sosai d'in nn💓_
  _Kici gaba da yi mana muhimmancin budurci yana kawo light👍🏻_


*«»page«» 63*
Saif dake rungume da ita yayi murmushi kawai yana mai shafa gadon bayanta a hankali.
 Jim kad'an se ga Nusaiba ta kawo tean tana bawa saif ta fita.
 "Cutie"
Ya kira sunan ta a hankli ta d'ago yakai mata tean a baki tana sha kawai tayi saurin zamewa daga jikin sa ta tofar da shayin dan sai taji zaqin shayin na kama bakin ta taji wani iri ba dad'i,ga sugar d'in is normal ba yawa tayi ba amma zaqin ne dai taji bai mata dad'i a baki ba,se ma hautsinar mata da zuciya ya qara yi,da har ma taji ko shayin bata son gani ta had'e kanta da guiwa tana cewa saif dake gurfane a kusa da ita ya fitar da shayin bata son ganin shi.
  Ba musu saif ya fitar da shayin,byn ya dawo yasa tissue yana goge wanda ta tofar.
Nan Umma ta shigo d'akin ta kalle sa tace"wani aman kuma ta sake yi ne?
Saif yace"no umma tean ne dai har tasha se kuma ta tofar bata so"
  Umma tace"Ayya shifa laulayi haka yake ba kowa keson abu mai zaqi ba,bari naje to na d'aura miki ko kunu ne ko kinfi buqatar kici abinci na kawo miki?
 Zarah da still kanta na had'e da guiwa a hankli ta girgiza kanta alamar bata son abinci.
  Umma tace"to shikenan bari naje nayi miki kunun se kar asa sugar.
 Ta fita saif shi kuma ya kama zarah a hankali suka koma kan bed sai sannu yake mata yana jin awa ya maida ciwon a jikin shi dan lokaci guda duk jikinta ya saki ba qarfi ta zama kmr wacce tayi sati tana fama da rashin lfy,ga jikin nata da yayi wani irin zafi kuma.
  Yayi shiru se kallon ta yake tayi da duk wani motsi tayi sai ya mata sannu,har umma tayo kunun ta kawo,saif da ya kar6i kunun a natse ya shiga ba zarah wacce bata wani sha sosai ba tace ya isheta,ya 6alla mata magungunan da ya siyo ya bata tasha ta kwanta se bacci daga ita sai d'an towel d'in da take d'aure dashi asalima bata ko samu tayi sllr isha dake kanta ba.
  Se can cikin dare ta farka ta ganta sanye da kayan bacci a jikinta da tasan ba kowa ne zai mata aikin ba face saif.
 Nan ta tashi a hankali cikin lalla6awa ta nufi bathroom ta d'auro arwala tayi sallah,tana idarwa a nn kan darduma taci gaba da yin baccin ta sbd tashin ma wuya yake mata bare har ta iya komawa kan bed.
 Washe gari haka ta yini kwance ba abunda take iya ci sae kunu koshi kad'an se yawan bacci da take tayi,yayinda saif keta faman safa da marwa yana duba ta wanda ji yake kmr ma ya maida ta 6angaren shi,dan ganin yake kmr zaifi jin dad'in bata kulawa yanda ya kamata duk da dai da zarar ya shiga d'akin duk wanda ke ciki fita yake ya bashi guri koda kuwa bacci takeyi ba kuma za'a koma ba har sai ya fita,shiyasa yau da dare ma da kanshi ya taimaka mata tayi wanka dama komai na shirin bacci snn ya lalla6a ta ta d'an sha kunu ya bata magunguna tasha,wacce tana rungume a jikin sa har tayi bacci ya maida ta kan bed tare da rufa mata blanket snn ya fita.

Yana saukowa downstairs ya sami Abba da umma zaune a falo sai fira suke tayi abinsu cike da nishad'i yayinda yusra ke kan qafafun umma tayi bacci,Nusaiba kuwa tana can d'akin umma tana karatun exam.
 Cike da ladabi ya musu sai da safe snn ya fita wanda kafin ya fita sai da Abba ya tambaye sa ya jikin zarah d'in yace"Alhmdlh.

 Bayan 3dayz da faruwar haka ne Abba na d'akin su Nusaiba yaje duba zarah da kullum sai ya shiga duba ta amma yau sai yaga kmr ma tafi jin jiki kan yanda jikin nata ya nuna dan duk ta fad'a tayi wani haske kmr wacce jini ya qare ma,sauqin ta kawai yawan baccin da takeyi da ko yanzu baccin ne take tayi.
 Abba dake kallon ta cikin sauke numfashi ya janye hannun sa akan goshin ta da yaji duk zafi,ya kalli umma cikin damuwa yace"maman yusra a gaskiya ya kamata ki riqa tasa zarah gaba cikin lalla6awa ta d'an riqa cin abinci ko yaya ne kunu fa ba wani riqon ciki ne dashi ba ki dubi yanda duk tabi ta qare cikin en kwanaki,kullum kunu ko kunun ma kince ba wani sha takeyi ba ae dole jiri ya hana mata sukuni tunda kince ko bathroom ma se an taimaka mata take iya zuwa.
 Umma tace"To Alhj ya zanyi abincin ne ko son ganin shi ba tayi ana d'aukowa yanzu zata hau yin amai duk tabi ta amayar da d'an kunun da tasha da wani lokacin ma se an lalla6a ta da qyar snn ake samu tasha,shiyasa nake binta a haka kasan laulayi ba iya mishi ake ba se idan kuma Allah ne ya kawo ma sauqin shi.
  Abba dake kallon ta a sanyaye ya maida duban sa gun zarah da duk yake jin tausayin ta a ranshi.
 Yace"hakane Allah ya sauqaqa miki zarah,kana ya kalli umma yace"ni zan d'an fita in qara dubo jikin Alu driver.
  Umma tace"to a dawo lafiya.
 Ya fita ita kuma taje ta zauna a kusa da zarah ta d'auki ruwa da farin handkerchief d'in da ta ajiye ta hau daddanna mata jikin  ta da kullum take jin kmr ma qara zafi yake.
  Nan se ga saif ya shigo d'akin d'auke da sallama a bakin shi,umma ta amsa tana mai kallon sa har ya qaraso ya zauna kan bedside drawer yana kallon zarah da ake d'an daddana mata jikinta wato ana rage mata zafin jikin nata.
  Kana ya kalli umma yace"sannu da aiki umma bari na qarasa mata naga kmr baqi sun shigo nn gidan basu riga sun shigo falo ba tukun dai.
 Umma dake kallon sa tace"to bari naje inaga mutanen da ke zowa gaida abbanku ne"
 Nan kafin ma ta tashi se ga Nusaiba ta shigo tana snr da ita cewa ga baqi nn sunxo umma ta tashi tana fad'in"to gani zuwa ae yanzun nn yayanki yake gaya min muje ki had'awa baqin ruwa da lemu kafin na kira Abbanku ko zai iya juyowa su gaisa dan yanzun ne fitar sa ba nisa yayi ba.
 Nan suka fita,saif kuwa kafin yaci gaba da daddana ma zarah jikinta sai da ya cire mata rigar jikinta ya barta da half vest snn yaci gaba da daddana mata jikin nata har zuwa d'an lafaffen cikinta da yake ta kallo d'auke da murmushi yana shafa cikin wae babyn sa na a ciki.
  Kana ya kalli fuskar zarah cike da jin qaunar ta a ranshi yakai lips d'insa a hankali kan goshin ta ya d'aura mata kiss,snn ya d'ago yana shafa gefen fuskar ta muryar sa a natse yana roqa mata sauqi a gun ubangiji,kafin yake ci gaba da mata wacce a hankali cikin sauke numfashi take gyara kwanciyar ta sbd yanda taji jikin nata ya d'an mata dad'i zafin jikin ya rage iska mai dad'i na sanyin split na ratsa jikinta.

Da dare koda yazo bai sami kowa a d'akin ba se Zarah kad'ai tana zaune kan bed ta had'e kanta da guiwa,wacce tana jin an bud'e qofa ta d'ago kanta a hankali idanunta cike da qwalla.
  Nan saif ya qarasa gurinta da saurin sa,ya zauna a gaban ta tare da kama kumatun ta da kulawa yana tambayar me aka mata.
  Komai bata ce masa ba se matsowa tayi ta shige jikin shi kmr wata er baby ta sakar masa kuka.
 Ai fa se duk ya qara shiga damuwa ya d'ago ta yana fad'in"plz cutie gaya min kinji wani abu kk so umma ta hana miki ne?
  A hankali ta girgiza masa kai tana kallon sa cikin kukan da takeyi tace"uhm dear ni na gaji bazan iya ba"
  Cikin rashin fahimta yace"Mene ne?
  Nan kawai ta nuna mai cikin ta tace"Dan Allah ka cire min ina jin wahala sosai inaga ma bazan iya haifuwa ba nayi qanqanta.
  Saif ya saki ido tare da saurin rufe mata baki muryar sa can qasa kmr me tsoron wani ya jiyo yace"haba dai cutie kinsan me kk fad'a kuwa"
 A shagwa6e ta janye masa hannu qwallah tap a idon ta cikin marairaice fuska tace"Dan Allah dear ka taimaka min wlh wahala nake ji sosai kana gani fa ko abinci bana iya ci,yanzu haka ma yunwa nake ji kmr zan mutu,kuma ni bazan iya shan  kunu ba na gaji wlh.
  Ta qarashe mgnr cikin kuka.
  saif ya qara rungume ta sosai a jikin sa cikin rarrashi yace"to yi haquri kinji gaya min me kk son ci?
  Ta d'ago fuskar ta sha6e sha6e da hawaye tace"wnn abun nake so d'an wake"
 D'an wake?
 Saif ya tambaya dan shi baisan meye haka ba.
  Zarah kuwa se gyad'a masa kai tayi alamar eh"
Bai tambaye ta meye shi ba se  lallausan hannun sa yakai ya share mata hawaye yana fad'in"to shikenan bari naje na gaya ma umma"
  Nan ya janye jikin sa a hankali daga nata tare da janyo mata pillow ta kwanta dan ya fahimci kwanciyar take son yi.
  Koda yaje ya gaya wa umma akayi d'an waken aka kawo sai kallon d'an waken yake,snn ya kalli umma yace"umma wnn abun kuwa bazai 6ata mata ciki ba"
Tace"A'a baya 6ata ciki ai da kanwa akeyin shi yanda ciki bazai lallace ba.
 Shiru kawai yayi yana kallon d'an waken ya kanyi kyau da haske awa ba kanwa a cikin sa but still yana shakku tunda ba saba ganin sa yayi ba,zarah da itama kallon d'an waken take tayi duk ya biya a ranta,ta kalli saif cikin marairaice fuskar tace"plz dear ka barni inci ina so"
  Da kulawa ya kalle ta yace"ae bazan hana miki ba cutie tunda kina so bari naci dai naji tukun kinji"
 Nan ya d'auki d'aya ya had'o shi tare da abubuwan da ya gani akai wato dafaffen qwai da akayi slicing d'in shi da kusan yawan sa d'aya shida d'an waken da source d'in qoda da aka zuba akai hadda cabbage.
 Had'e da bismillah yasa a bakin shi yaci,ae fa se yaji yawun sa sun tsinke kan dad'i dan umma kam ba dai girki ba sosai ta iya girki ba kad'an ba,musamman d'an wake abu ne da take so shiyasa ko yaushe bata rasa garin shi a ajiye.
  Cikin lumshe ido yake cin d'an waken kafin yake ware idanun sa akan umma yace"wow ummana ashe haka abun yake da dad'i"
  D'auke da murmushi umma tace"ai fa dama kallon ka kawai nake har se kaci tukun.
Yayi murmushi tare da sake kaiwa a bakin sa yana fad'in"gaskiya kam umma wnn abun ae ba cutie kad'ai zata ci ba hadda ni,ina Nusaiba taje ta sake yi mana wani dan ina son cutie taci har sai ta qoshi.
  Umma dake ta fmn yin murmushi tace"da akwai saura ma a kitchen bari na bawa Nusaiba d'in ta kawo muku dan wnn kam bazai ishe ku ba.
  Nan ta fita yayinda saif ya shiga bawa zarah d'an waken sai ci take tana bashi a baki shima,duk suka cinye har wanda Nusaiba ta qaro musu.
  Saif sae dad'i yake taji ganin yanda taci d'an waken sosai bata yi amai ba ya bata magunguna tasha,tana kallo yaje ya sakawa d'akin key dan duk zai taya ta wanka haka yakeyi,duk da cewa d'an waken nn da taci ta d'anji qarfi a jikinta amma haka ta barshi da kanshi ma ya cire mata kaya ya bata towel ta d'aura suka wuce bathroom.
Koda akayi sati Alhmdlh jikin nata yayi sauqi da kullum d'an wake ne ta maida abincin ta da suke cin abinsu tare ita da saif.
 Wanda ganin jikin nata yayi sauqi ya yanke shawarar zasu koma yau har ma yana batun ya gayawa su umma se gashi sun riga shi tunkarar sa da zancen.
  Bayan sllr isha'i ya shirya abun sa tsaf se qamshi yake ta zubawa yaje ya sami zarah a d'akin su Nusaiba ta fito daga wanka knn d'aure da towel a jikinta tana jikin wardrobe zata ciro kayan bacci,se jin tayi an rungume ta wacce kafin ma ta juyo tasan waye sbd qamshin turaren sa da taji.
  Ta juyo d'auke da murmushi tana kallon sa sosai taga ya mata kyau cikin shafo gefen fuskar sa tace"dear ka min kyau sosai ina zuwa haka da wnn dressing awa ango?
  A hankli yaja karan hancinta yana murmushi yace"ae kam ango ne da yazo d'aukar amaryar sa cutie se ki shirya yanzun zamu koma gidan mu kinga se inji dad'in bawa babyna kulawa sosai da sosai koh.
 Ya qarashe mgnr ne yana mai shafar cikinta,da still ya kasa daina murmushin da yake yi,zarah kam na jin zancen sa lokaci guda tasha mishi toka har tana ture hannun sa daga kan cikin ta,tare da juya mishi baya ta ciro kayan baccinta zata je tasa ya riqo ta cikin rarrashi yana tambayar ta me ya faru ko rashin gaya mata da baiyi bane  se yanzun,yaso surprising d'inta ne dama amma tayi haquri.
  Zarah bata saurare shi ba se janye jikinta kawai tayi taje tasa kayan baccinta ta kwanta hadda kashe wutar d'akin,ya bita sai rarrashin ta yake yana ta bata haquri har ma ta gaji da sauraren shi,ta miqe zaune tace"kaga dear dan Allah ka rabu dani,jikina ne kakeyiwa ba kuma zaka sake samun sa ba na gaya ma.
  Cikin marairaice fuska yace"haba cutie meye kuma na dawo da abun da ya riga ya wuce plz i beg u kiyi haquri kinji wlh ni ke nake so ba wai jikin ki kad'ai ba trust me"
Zarah dake jin zancen nasa a yaudara  ta6e da baki ta kalle sa kawai ta koma ta kwanta ba tare da tace da shi komai ba. 
  Saif yayi shiru kawai yana kallonta can ya tashi ya fita daga d'akin ransa ba dad'i.
   Wanda da fitar sa d'akin ne Nusaiba dake bathroom tana wanka ta fito d'aure da towel,wacce da fitowar ta ta tsaya cak ganin ba haske se kawai tayi murmushi tana kallon zarah cikin zolaya tace"Aa 6ter yau kuma da wuri haka aka kashe mana light kaddai duk laulayin ne,da kuwa babyn nn nawa d'an gata ne mai son hutawa.
  Zarah na jinta amma tayi banza da ita dan ko magana ma bata son yi,se kwanciyar ta da ta gyara.
 Nusaiba da tasan tabbas ta jita ta kalle ta cikin murmushi da son sake yin wata magana se kuma ta fasa dan yanayin zarah kad'ai ya nuna bata cikin mood,kasancewar d'akin ba wani duhu ne dashi sosai ba shiyasa har ma ana iya ganin yanayin mutum.
  Inda haka Nusaiba ta bud'e wardobe ta d'auki abunda ya fito da ita wato pad snn ta koma bathroom dmn qarasa yin wankanta

Saif kuwa yana sauka downstairs  ya sami umma da Abba zaune suna kallon labarai ya qarasa gurin su tare da russunawa a hankali cike da tunanin abunda zai ce dasu,nn kafin yace komai Abba ya kalle sa d'auke da murmushi yace"ya akayi ne saifuddeen har zaku tafi knn to ina zarah da ka barta baku fito tare ba bayan kasan jikin nata ba wani qwari yayi sosai ba har yanzu tana fama da jin jiri.
  Saif dake tunanin abun cewa yace"Abba ae ganin ma jikin nata baiyi qwari ba yasa na yanke shawarar da munci gaba da zaman mu a nn kawai har idan jikin nata yayi qwari tukun,kasancewar idan mun koma can ba kowa da zai kula da ita idan bana nn.
  Abba dake kallon sa se da ya d'anyi shiru kafin yake cewa"haka ne kayi magana amma ita zarah d'in ta amince da haka ko kai kad'ai ne ka yanke wnn shawarar?
  Kansa qasa yace"A'a ta amince ai har ma ta kwanta bacci"
  Yace"to shikenan jeka Allah yayi maka albarka ya qara maka tausayin iyalin naka.
  "Amin"
Umma ta fad'a,saif kuwa bai iya cewa komai ba se tashi yayi ya fita.
Wanda har aka share sati gabad'aya a cikin damuwa ya kasance sbd sam zarah taqi ta saurare shi se fushi take tayi dashi,da har idan ya shiga d'akin fita take ta barshi,ga su umma duk basu san abunda ke faruwa ba dan da ita har shi basu bar aka fahimta ba.


Sorry 4 kept u waiting ban zauna bane wlh,and ko yanzu ma ba a nn naso in tsaya ba but inshaa Allah gobe zanyi qoqari inga cewa na turo muku wani page.
   Luv u all❤
[4/28, 8:47 PM] Billy giro😊: _Saturday 28/04/2018_ *«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*

_Am very sorry my Fans nayi muku alqawari kuma se ban samu cikawa ba kuyi haquri dan Allah abubuwan ne se a hankali wlh._
   

*«»page«» 64*
Guraren 9pm saif ya fito daga 6angaren shi zai je 6angaren su umma gun zarah da kullum baya gajiya da zuwa bata haquri.
   Kafin ya qarasa isa 6angaren ne se ga jamil ya kunno motar sa a cikin gidan.
  Nan ya qarasa gun jamil d'in wanda ya faka motar sa ya fito suka gaisa,snn cike da nishad'i yace"kasan tun rnr na ce ma da akwai labari to shine....se yayi shiru yana kallon saif da ya fahimci duk ya fad'a ya rame ga kuma damuwar da ya gani a tattare dashi.
  Kafin ya iya ce masa komai saif d'in yace"what happen ka fara magana kuma kayi shiru?
  Jamil dake kallon sa yace"dole nayi shiru saif sbd yanayin ka ya nuna gabad'aya kana cikin damuwa me yake faruwa ne?
  Shiru Saif yayi kmr bazai ce komai ba can ya numfasa a hankali snn yace"haqiqa jamil bazan iya 6oye maka ba ina cikin damuwa sosai,kaf satin nn da ya wuce zarah fushi take yi dani nayi nayi ta haqura taqi ko saurarata ma bata son yi.
  Jamil da ke kallon sa yace"subhanallah me yayi zafi haka kaddai halinka ne har yanzu baka daina ba saif?
   Saif yace"haba jamil nafa gaya ma duk iskancina ni ba wani abu ne fa nakeyi da mace ba,bare tuni na ajiye wnn yanzu ba wata macen da nake kulawa,a dalilin Sophie ne dai har tazo tana yin fushi dani.
  Sophie?
Jamil ya tambaya yana mai kallon saif.
  Kafin yake cewa kana waya da ita ne?
  Inafa ae duk kiran da na gaya ma tana min ban ta6a yarda na d'aga ba,and ba sau d'aya ba basau biyu ba zarah tasha ganin kiran nata amma bata ta6a ce min komai ba abunda ya mata ciwo shine had'uwar da mukayi da ita Sophie d'in a England.
 Nan ya gaya mishi yanda abun ya faru har ma fushin da zarah tayi dashi a can.
  Snn yaci gaba da cewa shine fa da naga jikin nata yayi sauqi ina mata zancen mu koma gida ta dawo da yin fushin kuma,ba irin rarrashin ta da banyi ba amma taqi ta haqura,ta dake akan ita lallai jikinta ne nake so ba ita ba,bayan kuma ba haka bane jamil ina sonta wlh,wanda na fahimci haka ne sbd irin yanda nake jinta a raina fiye ma da yanda nayi jin Sophie a raina.
  Jamil dake sauraren shi yace"zarah baza ta iya fahimtar hakan ba saif sbd tun farko tasan cewa ba qaunar ta kake yi ba,kuma a ganin ta kunci gaba da yin rayuwar aure ne dmn farin cikin Abba dan haka duk wasu abubuwa da zaka mata dmn nuna qauna a gare ta zata d'auka ko duk dan jikinta ne kawai,tunda ita kanta ta kasa fahimtar cewa tana sonka bare har ta iya gano sonda kake yi mata.
Cikin girgiza kai Saif yace"zarah bata sona jamil amma ni tun kafin a barni na maida ta na fahimci cewa sonta ne nake yi ba wai a dalilin farin cikin Abba kad'ai yasa nake so a barni na maida ta ba,amma ita har yanzu banga alamar ta fara sona ba ma,kawai tana biye min ne akan abubuwan da taga ina mata shine ita ma take min.
  Jamil yayi murmushi yace"hm saif knn kana nufin kaima yanda zarah ta kasa fahimtar kana sonta,itama ka kasa fahimtar sonka take yi,to idan ba sonka take yi ba kan me zata damu dan kun had'u da Sophie har tayi fushi tayi tafiyar ta.
 Saif yace"to ae jamil wnn dole ne taji haushi sbd yanda na barta tana ta jirana,ni kaina nasan ban kyauta ba wanda ba komai ne yasa na tafi da sophie muka ke6ance ba sai dan in kawo qarshen komai mu haqura da junan mu taje tayi auren ta kawai itama tunda tana da wanda yake sonta,shine fa da qyar na rarrashe ta na samu har ta haqura koshi ina ganin ma kmr fushi tayi dan tafiyar ta kawai tayi bata ce min komai ba.
  Amma ita zarah sai ta d'auka ko wani abu ne,wacce ashe har ta lura da wayar hannun Sophie irin tawa ce da na saya mata irin ta itama shine ta cire sim card d'inta,ta bani wayar ta kuma had'a min hadda zoben diamond d'in da na saya mata da bata ko ga irin shi a hannun sophie ba,amma duk ta had'a ta bani bata so wae inje inyi ta kayan iri d'aya nida sophie ita in daina sako ta a cikin mu.
  Jamil yace"to ai nn zaka qara tabbatar da cewa tana sonka dan wnn duk kishi ne.
  No jamil wnn fushi ne kawai,da zarah na sona ya kamata taji ba dad'i a lokacinda take ta ganin shigowar kiran Sophie a wayata amma na lura ko kad'an ban ta6a ganin alamun kishi a fuskar ta ba sai dai ma in muna kwance ta qara gyara kwanciyar ta a jikina ta hau bancinta.
  Jamil yayi shiru can yace"sai dai ko tana 6oye kishin ne a ranta,amma ba makawa zarah na sonka dan wnn fushin duk na sonka ne takeyi,barinta akan hanya tana ta jiranka ba zai sa tayi tayin fushi da kai har haka ba.
  Saif da yayi shiru yace"to yanzu jamil ya kake ganin zan samu in shawo kanta wlh ina cikin damuwa ko kad'an bana jin dad'in wnn fushin da take yi dani.
  Jamil yace"kawai kaje ka qara bata haquri tare da gaya mata dalilin da yasa ka tafi da Sophie kuka ke6ance duk dan kana son ka kawo qarshen komai ne ba wai da wata manufa ba,maybe jin hakan zai sa ta haqura.
  Saif yace"hm jamil ae na gaya mata hakan tun a England amma taqi ta saurare ni,ganin take kmr ina fad'a ne kawai duk dan in shawo kanta wai in samu jikinta haka take gaya min,da tasan yanda kalmar take min ciwo a rai wlh da baza ta gaya min ba,shekaran jiya fa waya na siyo mana nida ita iri d'aya bcos still bata kar6i wancan d'in ba har ma da wani zoben diamond duk na qara siyo mata wani amma da na kai mata ko kallon su taqi tayi,hakan na koma da abuna yanzu haka suna nn d'aki a ajiye,na rasa wane irin fushi ne da zarah.
  Jamil da duk yaji tausayin abokin nashi ya numfasa   yace"kasan bafulatanin mutum zuciya ne dashi sosai,haka kuma wani cikin yana sa baqin rai da fushi,ka mata uzuri ba mamaki sune suka tara mata a lokaci d'aya,amma yanzu jeka d'in dai idan still taqi ta saurare ka se ka dawo da akwai shawarar da zan baka.
  "Ok to"
Saif ya fad'a tare da kama hanya ya nufi ciki.
  Ya sami su umma da Abba zaune a falo suna kallon labarai,yaje ya gaida su cike da ladabi snn ya wuce sama zuwa d'akin su Nusaiba.
Abba da ya bisa da kallo ya kalli umma yace"ya kamata yaran nn su koma gidan su haka tunda dai Alhmdlh jikin zarah se qara sauqi yake.
 Umma tace"maganar da nake so in maka knn Alhj ince ya kamata su koma gidan su haka dmn na fahimci saifudeen duk yabi ya rame kmr wanda yake cikin damuwa,shine nake zargin wai anya tun farko ba yarinyar nn zarah ce tace masa bata tashi komawa ba se taji sauqi,dan nasan halinta zata iya yin hakan.
 Abba dake kallonta yayi shiru can yace"to yanzu dai koma mene ne kije ki gaya mata ta shirya tabi mijinta su koma,idan har ma aikin gidan ne bata iya yi se a samar mata er aikin da zata riqa taya ta.
 Nan umma ta tashi ta haura zuwa sama,wacce da isar ta bakin qofar d'akin kafin tayi knocking kawai ta soma jin muryar zarah cikin fad'a tana cewa saif dake ta lalla6ata.
 "Wai ni kam dear nace bazan koma ba ka rabu dani dan Allah,jiki na ne kake yiwa ba kuma zaka sake samu ba na gaya ma kaje can kuci gaba da yi kaida wnn er iskar baturiyar taka da kuka saba......tas!
 Taji saukar lafiyayen marin da yasa ta saki qara ba shiri,wato har umma ta shigo d'akin basu sani ba,wacce ita ce ta mare ta d'in ta kuma je a fusace ta ciro wayar caji tayo gun zarah cikin tsoratadda ita awa zata duke ta,ae kuwa a tsorace cikin kuka zarah ta tafi da gudu bayan saif ta rirriqe shi tana fad'in"wayyo! Allah inna dan Allah kiyi haquri wlh bazan sake ba"
 Umma bata saurare ta ba sai qoqarin janyo ta take a bayan saif,da duk yabi ya rud'e yana fmn kare zarah cikin bawa umma haquri.
 Nan sai ga Abba ya shigo d'akin da saurin sa yana fad'in"lafiya me yake faruwa?
  Umma ta nuna zarah tace"ka ganta er rainin hankalin nn ashe kuwa duk itace tace bazata koma ba,very stupid! har yana lalla6a ki kina d'aga muryar ki akan tashi ko,oya duqa maza ki bashi haquri ko yanzun nn na zazzane ki wlh!
  Da sauri cikin kuka zarah ta gurfana a gaban saif tana bashi haquri,kafin saif ya iya yin komai Abba ya tashe ta yana kallon gefen kuncen ta da duk yatsun umma sun kwanta akai gurin yayi ja har ma gefen bakinta ya fashe da jini,ransa a 6ace ya kalli umma yace"maman yusra wae marin yarinyar nn kikayi ashe har haka bayan kinsan ba ita kad'ai bace"
  Umma da itama duk ran nata a 6ace yake tace"to Alhj dan tana da yaron ciki se a riqa barin ta tana yin duk iskancin da ta ga dama har tana d'aga muryar ta akan ta mijinta,ta nuna zarah tace"wlh bari kiji in gaya miki kar ki kuskura in dawo d'akin nn in same ki ki d'auki duk wani abu da kika san naki ne kibi mijinki yanzun nn"
 Nan kawai ta fita daga d'akin Abba ya bita da kallo kawai kafin yake maida duban sa gun zarah muryar sa cikin rarrashi yace"ya isa haka kinji daina kuka amma daga yau kar ki sake d'aga muryar ki akan ta mijinki ba kyau duk da nasan laifin sa ne koh?
  Da saurinta ta girgiza masa kai alamar a'a.
  Fuskar sa a d'aure ya kalli saif da yaga yayi saurin kallon zarah,yace"gaya min gaskiya nasan haka kawai zarah baza ta ce baza ta koma ba har tana d'aga muryar ta akan taka,dole kaine babban mai laifin.
  Kafin saif yace komai zarah tace"Aa Baffa ba laifin sa bane fa nawa ne amma kayi haquri bazan sake ba.
 Tana mgnr ne kanta qasa tare da hawayen da ke sauka akan kumatun ta.
Abba dake kallonta yace"to shikenan Allah yayi miki albarka,se ki shirya ku tafi nayi magana da umman ki akan za'a samar miki mai aikinda  zata riqa taya ki aikin gidan kinji"
 A hankali ta gyad'a masa kai tare da yi mishi godiya snn ya fita daga d'akin.
 Nan saif ya qarasa gurinta tare da kai lallausan hannun sa ya share mata jinin da ke gefen bakinta,ta d'ago idanunta ta cike tap da qwallah tana kallon nasa idanun da sukayi ja suka sauya kala sbd marinda umma ta mata sosai yaji abun har ranshi,bare kuma se ya qara jin tausayinta da qaunar ta a ranshi ganin yanda ta maida laifin gabad'aya a kanta,a hankali ya rungume ta yana mai shafa gefen kuncen nata cikin rarrashi da bata haquri,amma se wani sabo kuka yaji ta fashe mishi dashi tare da qara shigewa sosai a jikin shi tana ta bashi haquri itama,dan tasan ita kanta ya cancanci ta bashi haqurin,kan yanda fushi ya d'ibe ta tayi tayi mai rashin mutunci a matsayin sa na mijinta da bai kamata ace tayi mai hakan ba,da ba kowane d'a namiji ne zai yi ta faman haquri yana ci gaba  rarrashin ta har haka ba.
 Ta d'ago cikin kukan da takeyi tace"Dan Allah dear ka rabu da wnn baturiyar wlh bana son huld'ar ka da ita"
 Saif da ya fara yarda tabbas zarah na son shi yaji wani dad'i a ranshi.
 Muryar sa a natse cikin share mata hawaye yace"nayi miki alqawari cutie bazan sake kulata ba dama can dan in kawo qarshen komai nida ita ne yasa har nayi lokacinta amma bazan sake ba kinji 4give me"
 A hankali ta koma kan qirjinsa muryar ta a sanyaye tana fad'in"nima ka yafe min dear bazan sake ba"
   Sosai ya qara rungume ta a jikin shi yana mai shafa gadon bayanta alamar ba komai ya wuce.
  Suka d'an d'auki lokaci a haka snn ya d'ago ta yace"bari mu shirya mu tafi koh"
  Nan ta gyad'a masa kai tare da zamewa daga jikin shi,taje ta bud'e wardrobe ta ciro kayanta ya taya ta suka saka kayan a akwati,ta zira qaton hijab d'inta suka fito,da kai tsaye d'akin umma suka nufa dmn suyi mata sallama kafin su shiga sai gata ta fito daga d'akin Abba,fuskar ta ba yabo ba fallasa ta kalli saif tace"zaku tafin ne?
  Yace"eh umma zamu wuce "
 Tace"to Allah kaiku lafiya,amma bari kaji in gaya maka kar ka sake bari wnn yarinyar tana ma fitsara kayi maganin ta wlh er rainin hankali bansan a ina kika kwaso iye shegen nn ba nikam.
 Tayi mgnr ne tana mai kallon zarah cikin dalla mata harara wacce da saurinta ta sadda kanta qasa qwallah na qoqarin cika mata ido.
 Saifudeen kuwa se cewa yake ayi haquri umma bazata sake ba.
 Nan kafin umma tace komai se ga kiran Abba ya shigo a wayar shi bai d'aga kiran ba sai d'akin Abba da ya nufa.
Umma da ta bishi da kallo ta maida dubanta gun zarah da still kanta yana qasa muryar ta a natse tace"dama ina so in tambaye ki har yanzu bai daina kula wnn baturiyar bane?
 A hankali zarah ta d'ago cikin yanayin shagwa6a tace"Aa ita dai keyi ta fmn kiranshi amma baya d'agawa ban sani ba ko a bayan idona yana d'aga kiran nata,dan da mukaje England har  had'uwa mukayi da ita,yaja ta suka tafi wani gun acewar wai na masa haquri yana son zasuyi magana ne,to shine ni kuma se banji dad'i ba har nakeyin fushi dashi.
 Umma tayi murmushi snn tace"to ae zarah indai wnn ne ae har Alhj ya gayawa had'uwar da sukayi da sophie d'in akan yana son ya yafe mishi kulatan da yayi tunda kinsan ya hanashi har ma yace bai yafe masa ba idan har ya sake kulata to shine yaga ya zama dole ya nemi ya yafiyar shi har ma yayi mai bayanin baiyi hakan ba sai dan yana son ya kawo qarshen komai shida ita sbd ta dame shi da kira,snn ko kwanaki da ya tafi England ae a kanta ne ya kashe waya sbd awayar ta tana iya ganin inda yake,da sam ya manta koda yaje har ma tana qoqarin zuwa inda yake ne se ya ankara ya kashe wayar da bai sake kunna ta ba sai da ya dawo kin kuma sani"
 Tace"eh umma amma bai gaya min dalili ba"
 To ae dan baya son 6acin ranki ne zarah dan haka ki kiyaye harshen ki kar ki sake bari fushi ko 6acin rai yasa ki riqa gayawa mijinki maganganu haka marassa dad'in ji ba kyau kinji na gaya miki.
  A hankali zarah ta gyad'a mata kai.
Nan sai ga saif ya fito daga d'akin Abba da ya d'auka ko fad'a ne ake tayi mata tun d'azu.
 Cikin marairai ce fuska yace"plz umma dan Allah kiyi haquri haka baza ta sake ba.
 Umma tayi murmushi tace"to ae ina ja mata kunne ne dan na fahimci har yanzu yarinta ke cinta bayan gashi har ana qoqarin samar min d'an jika.
  Kunya zarah taji har ma da saurinta ta rufe fuskar ta da tafukan hannayen ta.
Saif kuwa sai kallonta yayi cikin murmushi snn yace da umma"to a daiyi haquri umma mu zamu tafi.
 Nan sukayi sallama da ita suka wuce,yayinda su Nusaiba basu ko san da zasu tafi ba suna can d'akin umma ita da yusra har ma sunyi bacci.
 Su saif kuwa suna fita suka sami jamil still yana nn,bayan sun qarasa gurin shi zarah ta gaisa dashi ta koma can jikin motar saif ta tsaya dan motar ba'a bud'e take ba ko key ma bai d'auko ba.
 Tana jin su se faman dariya suke jamil na tayiwa saif sheri.
Nan dai ba 6ata lokaci sukayi sallama jamil yaja motar shi ya tafi saif kuwa yaje 6angaren shi ya d'auko makullin motar sa suka wuce.

 Bayan sun isa  zarah takai akwatin ta a d'akinta snn suka wuce d'akin saif.
 Sukayi zaune suna cin gasasshiyar kazar su da suka siyo kan hanya suka had'a da fresh milk,bayan sunci sunyi qat snn saif ya tashi ya fad'a wanka.
  Yana fitowa itama zarah taje tayi wankan.
 Da akwai kayan baccinta a d'akin,wacce koda ta gama shirin bacci ta samu saif har yayi bacci.
  Ta hau kan gadon sai kallon sa take jikin ta duk a sanyaye tana shafa gefen fuskar sa a hankali,tasan dole yana buqatar ta amma meyasa zaiyi bacci bayan itama sosai take jin kewar shi a ranta.
  Hakan dai ba yanda ta iya ta kashe wutar d'akin tare da shigewa jikin shi ta hau yin bacci,saif da ba duk bacci yayi ba ya bud'e idanun sa a hankali yana kallonta wanda ba kada'an ba yayi kewar daddad'ar zumar ta,amma kuma baya son taci gaba da mishi kallon jikinta kawai yake so ba ita ba,bare ma yaji jikin nata da d'an zafi zafi zai zama takurawa idan ya neme ta.
 Hakan yasa dolen shi shima ya haqura da abunda yake ji ya hau yin bacci.
  Wanda dashi har ita sun kasa baccin kirki se faman juye juye suke tayi har safe.
[4/30, 8:49 PM] Billy giro😊: _Monday 30/04/2018_
*«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*



By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*

This pages is urs Sumee and Barira ina mugun yinku cos ku na daban ne.
  Luv u so much dearests😍.

*«»page«» 65_66*
Bayan sunyi sllr asuba ya bata magunguna tasha sbd yanda jikin nata duk ya qara yin zafi da ba komai ne ya qara mata hakan ba se rashin samun bacci isasshe.
  Wacce tana gama shan magungunan tayi baccinta rungume a jikin saif da yake ta faman yawo da hannun sa akan cikinta yana ji awa ace cikin yakai wata tara domin ya qagu yaga abunda za'a haifar mishi.
 Koda ta tashi daga bacci se ganin kanta tayi kwance kan bed saif ya fita baya nn,nn ta tashi tayi wanka ta shirya cikin qananun kayanta da ya siyo mata a England da sukayi matuqar yin d'as a jikinta tayi kyau se qamshi take ta zubawa.
 Ta nufi kitchen tayi tsaye tana tunanin abinda zata musu na breakfast dan yanzu har abinci tana iya ci.
 Tana cikin tunanin ne kawai taji an rungume ta a hankli ta baya,ko ba'a fad'a ba dear d'inta ne ta sani dan qamshin turaren sa kad'ai ya shaida mata hakan.
  Ta juyo d'auke da murmushi tana kallon sa da kai tsaye ta sami kanta dakai bakin ta a nashi ta had'e tare da sakar masa lallausan harshen ta a nashi ya cafka sukayi kissing d'in juna snn ta zare bakin nata d'auke da murmushi tana kallon shi had'e da yi mishi ina kwana.
 Cikin murmushi ya amsa snn ya shafo gefen fuskar ta haka ma d'ayan hannun sa akan cikinta yana tambayar ya jikin nata da kuma lafiyar babyn shi.
 Kmr da shagwa6a ta tafi jikin shi tana fad'in"duk lafiya qalau yunwa dai nake ji kuma naga ba komai nayin breakfast a gidan nn"
Nan kawai ya kama hannun ta suka je gun dining ba tare da yace mata komai ba se murmushi yayi kafin yake bud'e warmers d'in da ta gani akai ashe d'an wake ne ya kar6o musu gun umma hadda farfesun  kaji,ae kuwa sosai taji dad'i da ganin d'an waken hadda rungume shi tana mai godiya,kafin suke zama suka ci har sai da suka qoshi.
 Snn bayan sun gama ya jata suka je kan 3seater tana kwance kan laps d'in sa tayi pillow dasu ya ciro wayar sa ya shiga note ya bata acewar ta rubuta duk abunda babu a gidan yaje ya siyo musu.
 Zarah ta kar6i wayar had'e da miqewa zaune ta kalle sa cikin marairaice fuska tace"plz dear zan bika"
 Yace"to ae ba yanzu ne zan tafi ba sai da yamma ko har abunda za'a d'aura da rana babu?
  Tace"da akwai kayan breakfast ne kawai babu se wasu kayan amfani"
  Yace"to shikenan tunda kina zuwa ae ba ma se kin rubuta min ba koh?
 D'auke da murmushin jin dad'i ta gyad'a masa kai tare da miqa masa wayar sa zata koma ta kwanta,bai barta ba yace"sorry zo muje kisa layin ki a waya umma tace tana son zata yi magana da ke.
Nan ba musu ta tashi suka tafi d'akin ta,a tunanin ta ko wayar ta da tayi fushi ta bashi bata so ita ce zai bata ta maida layin ta,amma da shigar su d'akin sai taga wata farar leda kan bed,suka zauna ya bud'e ledar ya fiddo sabuwar waya dal a cikin kwalinta irin ta hannun sa da ya ajiye kan bed da sai lokacin ta lura ashe ba waccan wayar tashi bace irin ta sophie,tuni ya ajiye ta ya fara amfani da wacce ya siyo musu kwanaki har ma taqi ta duba se yanzun da ya fitar take kallon wayar mai kyau tama fi ta farkon tsada da lokaci d'aya taji wayar ta shiga ranta dan ita har ga Allah waccan wayar ta riga ta fita ranta bata ko son sake ganin ta tunda ta ga irinta ce a hannun Sophie.
 Layin ta ta d'auko ta bawa saif kmr yanda ya buqata bayan yasa mata layin ya miqa mata ta kar6a da sauri cikin jin dad'i tare da d'aura masa kiss gefen kunce tana mai godiya snn ta shiga duba wayar,saif se kallonta kawai yake yana murmushi dan ya lura sosai taji dad'in wayar,da har ma yaso ya tambaye ta idan wayar bata mata ba ya sake canzo musu wata yaga ba kad'an ba wayar tayi mata se bai tambaye ta ba ya fasa.
 Ya ciro zoben diamond d'in da ya sake siya mata da shima sosai yafi na farkon kyau,ya kama d'an yatsanta yasa mata,zarah ta ajiye waya da sauri tana kallon zoben har tana yarfi da hannun ta sbd jin dad'i,snn ta mishi godiya cikin d'aura masa kiss ta d'ago fuskar ta d'auke da murmushi ta tsaya kawai tana ta kallon shi da qarara ta hango tsantsar qaunar ta a cikin qwayar idanun sa da ta fahimci tabbas ita d'in dai yake so ba banzan tunanin ta da take yi ba,dan mai sonka ne kad'ai zai riqa yi maka abunda kake so na ganin ya faranta maka.
  Ganin ba alamar zata daina kallon sa ya d'aga mata gira alamar kallon fa,tayi murmushi tare da sadda kanta qasa ta kama d'an yatsan ta tana shafa zoben wacce muryar ta a hankali tace"Dear meyasa ka biye min,bayan ka canza mana waya kuma ka canza min hadda zobe mai tsada haka fushi ne fa kawai banga irin sa a hannun ta ba da ka barni da wancan d'in kar 6arnar kud'in yayi yawa"
  Saif da ke kallon ta d'auke da murmushi yaja karan hancinta yace"sbd ked'in ta daban ce zan iya 6arnatadda koma nawa ne dmn na nisanta ki da duk abunda ba kyaso,kuma abu komai tsadar sa indai zaisa ki farin ciki kina kuma ra'ayin shi to ya gama zama naki muddin baifi qarfina ba,dan haka ki manta da wancan zoben bazan so ki sake ganin sa ba bare ma har ki tuna da wancan fushin.
  Zarah da har ranta taji dad'i bakin ta kawai takai a nashi ta had'e ta hau nuna mishi jin dad'in zantukan nashi da yayi,ya biye mata se kissing d'in juna suke suna ta6e ta6e cike da qwarewa da har ma suka soma fita hayyacin su.
 Can qarar wayar zarah ya katse su suka zare bakin su da qyar,zarah da a tunanin ta ko wayar saif ce cike da kasala ta kwantar da kanta a qirjin sa ta lafe,snn hannun ta cikin rigar sa ta kasa cirewa se faman yawo take dashi tana shafa nipples d'insa a hankali.
 Sai da saif yace mata wayar ta ce fa snn ta d'ago ta kar6i wayar ta kara a kunnen ta cikin  sake komawa a qirjinsa ta lafe tana waya da umma da ita ce ta kirata.
Bayan ta ida wayar ne saif yace"mene ne kike fad'in a barshi kawai zaki iya?
 Zarah da still tana lafe a qirjinsa tace"maganar mai aiki ce umma tace yau baza ta samu ba sai dai gobe,shine nace ni dama an bar zancen er aikin kawai zan iya aikin gidan nn da kaina tunda dai tuni na daina ban ruwan flowers da sharar waje mai gadi duk yaci gaba da yin abinshi ko kuwa ya ka gani?
 Saif da ya samu kansa da rashin jin dad'in tuna wahalar da yayi bata a baya,jikin sa a d'an sanyaye yace"No cutie tunda kinga yanzu ba ke kad'ai bace da akwai babyna,bana son ayukkan nn suzo suna miki wahala,ko a baya ma da na tuna banji dad'in wahalar da nayi baki ba ki yafe min kinji.
  Se a lokacin zarah ta d'ago ta kalle shi d'auke da murmushi tace"dear knn ae ni tuni na yafe maka duk abunda ka min"
  "Thank u"
Ya fad'a cikin nuna jin dad'i ya kai lips d'insa kan goshin ta ya d'aura mata kiss snn ya qara rungume ta a jikin shi yana shafa gadon bayanta a hankali.
 Wacce jin ta daina yawo da hannun ta a qirjinsa yasa ya kalle ta yaga ashe bacci tayi,dmn taji dad'in baccin ya zame daga jinginen da yake ya kwanta tare da ita a jikin sa yana faman shafa cikinta a hankali har  bacci ya kwashe shi shima.
  Se kiran zuhur ne ya tashe shi,bayan yayi arwala snn ya tada zarah ya wuce zuwa masallaci,bai dawo ba se 2:30 dan saif mutum ne mai d'an jimawa yana addu'o'i idan yayi sallah.
Wanda da dawowar sa har yana qoqarin shiga ciki yaji horn kafin yake jin qarar bude gate hakan yasa ya juyo dmn ganin mai shigowa.
Yayi murmushi ganin motar jamil ce tafe.
 jamil ya qaraso ya faka motar sa snn ya fito suka gaisa,har yana tambayar sa ya jikin zarah saif yace Alhmdlh.
 Kafin Jamil ke cewa labarin dai da nake ta ce maka akwai shine kuma ya kawo ni,na kasa zama na kasa tsayi kasan ban iya so ba tunda zainab ta soma kula dani a lokacin da bana da lafiya naji wata irin qaunar ta a raina sbd sosai yarinyar tana da tausayi da kulawa duk da dai nasan sbd qaunar da take min ne,da hakan ne ya qara sa naji lallai itace macen da ya kamata na aura dan ba kad'an ba nasan zan samu kulawa sosai daga gare ta da burina knn in samu mace mai kula dani,but me kace dmn ni na qagu na snr da ita snn ko zan sami Abba na gaya mishi,cos bana so in fara gaya mishi ya kasance da akwai wanda take son zata fitar.
 Saif da yaji wani dad'i da jin zancen jamil yace"Ah haba ai bana tunanin da akwai wani wanda zainab keso bayan kai da har zata iya fitarwa,kowa fa bata iya kulawa a dalilin ka ka kuma sani dan haka kama daina wani zance can,dama na dad'e ina son ince ka aure ta ko dan sonda take ma amma kuma sanin baka son zancen yasa ni yin shiru,but Alhmdlh tunda har da kanka ka kawo zancen,wlh baka ji yanda naji dad'i a raina ba na kuma jiwa zainab,dan haka ka gaggauta snr da ita kawai musha biki na qagu.
  Cikin dariya Jamil yace"ah haba daga ganin sarkin fawa se miya tayi zaqi.
 Saif yace"to meye abun jira dama can kai take jira tayi ta nuna ma so kana nokewa to yanzu da Allah yasa ka fad'a sonta ae sai ayi ayi musha biki wata qil ma zarah na haifuwa next two months or 3 itama zainab d'in ta haifo mana wani babyn.
 Wata irin dariya jamil ya fashe da ita cikin girgiza kai yace"kai saif baka da dama"
  Saif yace"Allah kuwa duka duka fa cikin zarah two months ne bai ko qarasa ba tukun da akwai en kwanaki kaga sai musha bikin mu at this month.
  Jamil yace"wlh kmr kasan haka nake so bare kuma tuni Abba yake matsa min nayi aure,haka ma zainab gabad'aya satin nn duk ta rame sbd tunani da damuwa Abba yace lallai idan bata fitar da mijin aure ba nn da wata d'aya tofa zai had'a ta da duk wanda yaga dama koda bata son shi kuwa,jiya ma da kukan ta tazo tana gaya min na rarrashe ta kawai ban gaya mata abunda ke raina ba sbd nafi son sai nazo na gaya maka tukun inji taka shawarar.
 Saif yace"har wata shawara ce ae kawai yanzun kaje ka snr da ita snn shima Abba ka gaya mai tare da nuna mai da wuri kake son ayi auren.
  Jamil dake jin wani dad'i a ranshi kmr ma yaga har anyi auren.
  Yace"to shikenan yanzun nn kuwa zanje in snr da ita dan koda na fito ma na barta zaune a farfajiyar gidan damuwa ta tara mata se tunani take shiyasa ma duk na qara shiga damuwa dmn sam bana jin dad'in ganin yanayin da take ciki wlh.
 Saif yace"au haba abun har yakai har haka.
  Yace"kasan ban iya so ba jikina har rawa yake banje na gaya mata ba kar Abba ya riga ni kawo wanda yake shirin had'a ta dashi.
 Duk suna mgnr ne cike da nishad'i suna dariya kana sukayi sallama jamil yaja motar sa ya bar gidan.
  Saif dake tsaye har saida yaga fitar sa ya girgiza kansa d'auke da murmushi snn ya shiga daga ciki.
 Da kai tsaye kitchen ya wuce jin alamar zarah na ciki tana had'a musu lunch qamshin abincin nata se tashi yake.
  Da shigar sa ya rungume ta yana kallon aikinda take ta juyo d'auke da murmushi ta kalle shi da kallo d'aya zaka mai ka hango farin ciki a tare dashi tace"wane irin albishir aka ma haka se murna kake?
  Yace"jamil ne wlh....nn ya gaya mata komai,wacce cikin murmushi da nuna jin dad'i tace"Allah sarki Allah ya tabbatar da alkhairi"
  Amin saif ya fad'a, wanda still yana rungume da ita ya kalle ta da kulawa yace"ni kuwa cutie ina so in tambaye ki wae a ina kika ji cewa jamil na sonki?
 Murmushi zarah tayi snn tace"rnr ne kana zaune a falo ni kuma zan sauko naji kana waya dashi kana bashi haquri a game dani,da yasa lokaci d'aya na fahimci komai dan kasan ka ta6a gaya min labarin cewa akwai wacce yake so da yake jiran a saketa ya aura amma se baka cemin ni bace,kawai wayar da naji kana yi dashi ne yasa na fahimta,da kuma nasan baka so in sani shine se nayi shiru abuna.
 Yace"shine rnr se kika nuna min kin sani dan ki 6ata min rai koh?
 Zarah da Still murmushi take cikin shafo gefen fuskar sa tace"yi haquri bazan sake ba 6acin rai ne yasa"
  Ya kama hannun nata cikin d'aura masa kiss yace"no vex komai ya wuce ae me kk dafa mana ne?
 Tace"White Rice ce da stew"
 Ya shafo cikinta yana fad'in"baza kiji yunwa da yawa ba kuwa kafin abincin yayi kinsan fa yanzu jiri ke d'ibar ki idan kikaji yunwa da kinyi abu mai sauqi,am simple komai kika dafa zan iya ci basai kin wahaladda kanki ba.
 Tace"dear to ae wnn ma simple ne kaga shinkafar kad'an ya saura tayi,miyar ma tana kan yi dan ina ida sallah kawai na taso na d'aura.
  Tayi mgnr ne cikin bud'e masa shinkafar ya gani haka miyar ta bud'e masa ya gani mai cike da naman kaji,har yana jan numfashi sbd jin dad'in qamshin miyar yace"wow my cutie abincin zaiyi dad'i daji har na qagu a kammala naci.
Zarah tayi murmushi kawai bata ce masa komai ba,wacce tana kallo ya kama hannun ta ya tafi da ita falo ya tsiyaya mata Fresh milk me sanyi a cup ya bata tasha wae ta rage yunwar kafin abincin ya nina,baya son jiri yazo ya d'ibe ta yana tsoro,cos da jirin yazo mata gabad'aya laulayin dawo mata yake sabo duk se ta wahala yinin rnr.
 Shiyasa ma bata musa masa ba tasha fresh milk d'in duk da ba wata yunwa take ji ba,cos sai yunwar ta mata yawa ne jirin ke d'ibar ta.
 Bayan ta ida abincin ne suka ci sukayi qat snn sukayi wanka suna yin sllr la'asar suka shirya suka fita zuwa shopping.
 Wa enda koda suka fita garin luf luf da hadari kmr za'a yi ruwa har suka dawo.
 Da kae tsaye kitchen suka nufa suka ajiye kayan amfanin kitchen,sauran kuma na d'aki ne da kuma kayan qwalamar da suka siyo duk suka wuce dasu d'akin saif.
 Suna shiga d'akin zarah taji an 6arke da ruwan sama,wacce tun kan hanya take ta roqon Allah yasa ayi ruwa ai kuwa da saurin ta ta ajiye kayan da ke hannunta ta fita tana fad'in dear zanje nayi wanka an fara ruwa.
 Kan yace komai tuni har ta fita da saurin sa ya bita a tunanin sa ko har ta fita waje koda yaje bai ganta ba ya tafi d'akinta,ya samu har ta cire kayan jikinta ta d'auko d'aya daga cikin kayanda Nusaiba ta ta6a kawo mata na shiga swimming pool ta saka.
 Saif dake tsaye riqe da waist d'in sa yana kallonta yace"wai ina zaki je haka?
 Tace"wanka mana zanyi dear ba kaji an fara ruwan sama ba muje in zakayi"
Yayi murmushi had'e da girgiza kansa yace"No ni kam bana yi kuma kema bazaki je ba,u know ba ke kad'ai bace yanzu dole wasu abubuwan se kin kiyaye kin daina yin su cutie.
 Cikin marairaice fuska tace"haba dear bafa tsalle tsalle zanyi ba kawai dai ina son in shiga ruwan ne inyi wanka dan Allah ka barni kasan fa sunna ne shiga ruwan sama.
Ta qarashe mgnr ne cike da shagwa6a kmr zata mishi kuka har da d'an doddoka qafafunta a qasa,shi kuma sai kallonta kawai yake ba kad'an ba kayan sun maida ta kmr wata baby doll skirt d'in ko rabin cinya ma baiyi ba bra d'in kuma duk tsagin mammanta a waje cike da sha'awa.
  A kasale ya qarasa gurin ta tare da kai d'an yatsan sa kan tsagin mammanta yana yawo dashi cikin tafiyar tsutsa,snn yana kallon ta with sexy eyes d'inshi murya qasa qasa yace"to kinsan dai bazan barki ki fita ta qofar falo haka ba a qofar baya zamu fita can gurin swimming pool ryt?
 Cikin nuna jin dad'i zarah ta gyad'a masa kai tana murmushi snn ta hau cire masa kayan jikin sa ta barshi daga shi sai singlet n boxer short suka fita,da kae tsaye swimming pool saif ya shiga da ita ta maqale shi sai tsoro take ji,ya had'e bakin sa da nata sai romancing d'inta yake har ya samu ta sake cike da zallar so suna wasa a cikin swimming pool d'in ana musu ruwan sama da har saida ruwan suka d'auke snn suka iya fitowa yayinda dukkan su se wani irin nishad'i suke ji a ransu,suka je d'akin saif sukayi kwance rairan akan gadon shi ba tare da sun cire kayan da ke jikin su ba sema romancing d'in juna da suka hau yi sosai da se lokacin ne suka iya cire kayan jikin nasu suka jefar snn suka ci gaba da faranta ran juna cike da qwarewa da qarar komai baka ji d'akin sai sautin numfashin su dake fita a hankali.
 Amma saif bai bar sunkai ga babban aiki ba ya miqe hakan nn jikin sa ba komai,ya bar zarah hakan nn itama ya wuce bathroom ya d'auro arwala ya fito,ya shirye cikin farar jallabiya ya fesa turare a jikin shi.
  Snn ya koma gun zarah da still tana kwance ta kasa tashi se jikinta kawai da ta iya rufawa dan gabad'aya ya gama kashe mata ga6o6in jikinta,ta kafe idanunta akanshi se kallon sa kawai take,muryar sa a natse yana mai shafa gefen fuskar ta yace"jekiyi arwala kiyi sallah magrib tayi,ni zanje masallaci sai na dawo kinji.
  Zarah dake kallon sa a hankali ta gyad'a masa kai tana kallo ya tashi ya fita snn ta iya tashi ta d'auke jiqaqqin kayan su ta kuma sauya bedsheets shima snn taje tayi arwala tayi sallah tana jiran dawowar shi dan a tunanin ta ko idan ya dawo zasu d'aura inda suka tsaye ne amma se taga yana  dawowa qwa6e jallabiyar sa kawai yayi ya d'auko ledar da suka dawo da ita ya ware musu kayan qwamulashen su da suka siyo yana ci yana kai mata a baki itama,cos tana nn maqale a jikin shi awa wata er baby,da cin qwamulashen kawai take ba dan tana jin dad'in su ba,dear d'inta kawai take buqata a lokacin ita kam da shima jurewa kawai yake,har dai yanda yake jin hannun ta a jikin shi se wasa take tayi dashi tana tatta6a shi har tayi bacci a gurin,nn saif ya samu a hankali ya zare hannunta dake cikin boxer short d'in shi da har ma ta janyo mishi wanka wacce sam bata ko san bacci ya kwashe ta ba sbd baccin laulayi haka yake zowa mutum kae tsaye ba shiri duk da cikin buqatuwa take kuwa amma ya iya d'aukar ta.
 Se saif ne ya d'auke ta yakai ta kan bed snn yaje yayi wanka.
 Wanda har akayi sllr isha yaje ya dawo baccin take har zuwa 9 yaga ba alamar zata tashi ya tashe ta tayi sallah snn suka ci abincin da yaje ya kar6o musu a gurin umma.
 Bayan sun ida cin abincin ne taje tayi wanka a mamakin ta koda ta fito har yayi bacci.
  Bayanda ta iya haka ta kasance mata kmr jiya dashi har ita.
 Har washe gari kuwa dukkan su abun ba'a cewa komai haka suka yini cike da buqatuwar junan su har dare musamman saif da har wani zazza6i ya taso mishi,yayinda ita kuma zarah da zata je wanka a ranta sai addu'a take Allah yasa yau kar yayi bacci har ma hakan yasa tayi wanka sharp sharp ta fito,wacce tana fitowa ta tsaya cak ganin addu'ar ta bata kar6u ba dan kuwa kmr kullum har yayi baccin,ai nn kawai ta fashe da wani irin kuka ta fita da gudu zuwa d'akinta,saif da likimo ne yake mata ya tashi da saurin shi ya bita zuwa d'akin nata,dai dai ta cire towel d'inta a fusace tayar ta nufi wardrobe se fiddo kayan ciki take tana watsar dasu da ita kanta bata san me take nema ba.
 Saif da ya tsaya yana kallonta da saurin sa ya qarasa gurinta ya janyo ta jikinsa yana fad'in what happen cutie me yake faruwa"
 Ta qwace da sauri cikin kuka tana fad'in ni ka rabu dani ae ka duk sani kullum se kayi bacci ka barni ashe bama baccin kakeyi ba,me na maka da kake min haka?
Cikin rarrashi ya janyo ta jikin sa yana fad'in"ba ki min komai ba cutie kawai bana son na takuraki na neme ki bada ra'ayin ki ba.
 A shagwa6e cikin kuka tace"wane ra'ayi bayan ka riga ka saba min kawai dai na fahimce ka fushi kake dani dan nace ma jikina kake so shine kake hukuntani .
  Nan kawai ta janye jikinta ta tafi kan bed ta had'e kanta da guiwa,ya bita ya zauna gab da ita tare da janyo ta jikin sa,ta d'ago cikin kukan da take tace"plz dear kayi haquri wlh 6acin rai ne yasa na fad'a ma haka bazan sake ba ka janye min wnn hukunci ya min tsauri.
 Saif da har ransa ba yana hukunta ta bane yafi son dai sai da ra'ayin ta snn ko zai neme ta dan baya son taci gaba da yi mishi kallon jikinta kawai yake so.
 Muryar sa a hankali cikin share mata qwallah yace"ba ina hukunta ki bane cutie yanda dai na gaya miki da farko haka ne.
 Tace"amma duk da haka nasan dole maganar ce kema zafi arai kayi haquri ka yafe min bazan sake ba kaji"
 Ta qarashe mgnr ne tare da kama kunnen ta,ya sauke hannuwan nata a hankali snn cikin qara share mata hawaye yace"har ma abunda baki min ba cutie na yafe miki,dan haka yi shiru bana son kukan nn naki tashi muje d'aki na in qarawa babyna kuzari koh?
 Yayi mgnr ne cikin d'aga mata gira har tana yin dariya cikin noke fuskar ta a qirjin shi,wanda da kanshi ya d'aura mata towel snn ya d'auke ta cak suka wuce d'akin shi,da kai tsaye kan bed ya dire ta tare da zare mata towel ya jefar,nn ta lumshe idanun ta da sauri sbd finger d'in shi da taji yayi penetrate a qasanta yana moving nashi cikin wani irin salo mai wuyar fassarawa da yasa taji awa zata shid'e se fidda numfashi take cikin jin nice musamman da taji yakai lallausan harshen sa yana sucking,a lokacin mutuwa ne kawai bata yi ba danji tayi awa tama bar duniyar gabadaya,dan salon akwai nauyi ba ko wace mace ce zata iya d'aukar shi ba,wacce itama da qyar ta iya dawo da hayyacin ta ta hau yi mishi nata salon da itama lokaci guda duk tabi ta rikitar da shi har yana faman yi mata ihu da za'a kirashi sambatu,da ita kanta bata fahimtar me yake cewa se sunan ta kawai da take jin yana ambato cikin qara mata qaimin abunda take yi mishi,a haka har suka je ga babban aiki,yayinda a hankali saif ke bin cutien tashi sbd lafiyar babyn shi.
 Wa enda ko washe gari suna ida sllr asuba saida suka sake lalubo junan su dan jiya haquri kawai sukayi basuyi second round ba dan ba kad'an ba sunyi kewar juna da suka ji awa sun shekara ne basu had'u ba.


*Bamalli*
 zarah n saif na gaida ki irin sosai d'in nn.
  And me
 Luv u so much💔
Kuma nayi missing d'inki two dayz ban ganki a online ba hope  everything is fine.
[5/3, 9:13 PM] Billy giro😊: _Tuesday 01/05/2018_
*«»«»«»SAIFUDEEN!«»«»«»*




By
  *Billy giro😊*




*Dedicated to»»»Zarah gwandu*

*📚UMMIE  NOVEL📚*
*GROUP*
 _NA GAIDA KU AKAN QAUNAR DA KUKE YIWA LITTAFIN NAN_.
  ```AND MASOYAN BOOK D'IN NAN THIS PAGE IS URS
  NIMA INA MUGUN SONKU IRIN SOSAI D'IN NAN❤```


*«»page«» 67*
Bayan sun gama jin nice d'in su ne suna kwance suna sauke gajiya,yayinda zarah se faman yawo take da hannun ta akan faffad'an qirjin saif da take manne akai muryar ta a hankali tace"Dear"
 Saif da idanuwan sa ke lumshe hannun sa akan gadon bayanta yana shafawa a hankali yace"Na'am my cutie ya akayi?
  Tace"kana birge ni ne sosai wlh,akan yanda baka mantuwa da yin addu'a a duk lokacin da zaka shigen ban ta6a jin ka manta ba ko sau d'aya duk irin gid'imin da kake yi kuwa sai ka karanta ta snn.
 Saif yayi murmushi mai sauti snn yace"to my cutie in banda abunki ae ba qaramin illah bane rashin karanta ta shine fa kesa ana haifuwar 'ya'ya gasu nn dai ba tarbiya  duk yanda aka so su kasance masu tarbiya baza su kasance ba,se ma qara fand'arewa da suke suna mugayen d'abiu like zina,sata, caca shaye shayen banza da dai sauran su.
 Shiyasa ko da kuskure bana son in manta da yin addu'ar sbd burina mu samu 'ya'ya masu kyakkwar tarbiyar da dukkanin al'umar musulmi zasuyi alfahari dasu,dan haka ina son kema ki riqa kula a duk lokacinda kika ga kmr zan manta banyi addu'ar ba se kiyi saurin karanto min a fili yanda zanji in tuna kafin na afka tafkin dadda'ar zumar nn taki mai sani in manta kowa da komai.
   Zarah da har ranta taji dad'i sosai ta qara shigewa jikin sa tana murmushi.
  Haka shima murmushin yake kafin yake cewa to karanto min addu'ar inji ko kin iya ta yanda ya kamata.
  Nan ba musu zarah ta karanto mishi.
بِسْمِ اللَّهِ،اللَّهُمَّ جَنِّبْنَــا الشَّيْطَانَ وَجَنِّـبِ الشَّيْطَانَ مَا رَزَقْتَنَا.
Yace"gud gal to fassara min inji.
Tace"Da sunan Allah,Ya Allah! Ka nisantar da shad'ain daga gare mu,kuma ka nisantar da shaid'an daga abunda Ka azurta mu dashi.
 Hakane koh?
Ta tambaya tana mai kallon sa d'auke da murmushi,cike da so yaja karan hancinta yace"of course haka ne my cutie lallai kina maida hankali a islamiyya,Allah ya qara miki basira haqiqa nayi dacen ummul Aulad Allah ya baki ikon tarbiyantar da yarana,tarbiya ta addinin musunci.
 Cikin d'aura masa kiss tace"Amin my Abul aulad Allah ya barmin kai,tashi muje muyi wanka kasan ka gaya min ba kyau zama da janaba.
 Hakane kam dan take mugun aljani yake samun damar shiga jikin mutum,haka ma ko asiri akayiwa mutum a lokacin ne yake saurin kama shi.
 Dan haka hurry up! maza muje mu tsalkake jikin mu bana son wani mugun abu ya illata min ke da babyna.
 Nima ae bazan so wani abu ya illata min kai ba.
 Duk suna mgnr ne cike da zallar so yayinda suka tashi suka wuce zuwa bathroom.

Bayan sunyi wanka sun shirya sunyi breakfast saif ya fita zuwa asibiti kasancewar yau Monday.
  Zarah kuwa da fitar sa dama ta gyara gidan se bacci kawai ta hau yi har saida tayi mai isar ta snn ta tashi ta nemi fresh milk mai sanyi tasha kana taje zuwa girka musu abinda zasu ci da rana.
 Bayan ta kammala ne har ma tayi sllr zuhur tana kwance tana hutawa waya riqe a hannun ta tana chatting da qawayen ta saif ya dawo.
  Da saurin ta ta ajiye wayar taje ta tarbe shi cikin rungume shi tana fad'in"oyoyo dear sannu da dawowa"
  Cikin murmushi ya d'aura mata kiss yace"yauwa my cutie"
 Snn ya shafo cikinta yace"ya babyna?
Ta shafo cikin itama  snn tace"lafiya qalau babynka yake"
 kafin take kar6ar briefcase d'in sa suka haura zuwa sama.
  Wa enda saida suka gama zuba soyayyar su a bathroom gun wanka snn suka fito,byn sun shirya suka ci abinci.
 Sukayi kwance a nn falo kan rug se hutawa kawai suke abinsu yayinda zarah ke manne a jikin saif ta kwantar da kanta a qirjinsa en yatsun ta sarqe a cikin nashi tana wasa dasu.
  Haka shima sai wasa yake da gashin kanta wanda muryar sa a natse yace"ban baki labari ba cutie jamil dai har an sa date next coming month za'ayi auren sa shida zainab.
 D'auke da murmushi zarah ta tashi tana kallon sa tace"kace abun da wuri za'ayi shi"
  Yace"inshaa Allah ae shi jamil a cikin watan nn ma yaso Abban sa ne yace"A'a a barshi zuwa next month dai kar en uwa suji abun girshi sosai wanda ashe dama tuni shi har ya yanke shawarar zai had'a su aure ganin kowannen su yaqi fidda wanda zai aura.
Shiyasa yayi murna sosai a lokacinda jamil yaje masa da zancen wanda duk da jamil ya gaya masa yayi magana da zainab ta kuma amince sai da ya qara kiranta yaji daga bakinta snn manya suka zauna a kasa rana.
 Zarah da still ta kasa daina murmushin da take tace"Allah sarki,Allah ya kaimu lokacin ya kuma sa ayi lafiya"
 Saif yace"Amin ae ko su Nusaiba just two months ne ya rage kinsan"
  Zarah tace"Nadiya dai ko dan Nusaiba kam rigima ta ajiye hadda kuka bata tashi auren ba yaya ma'aruf kuma ya biye mata kan baza ayi auren ba se lokacinda da take so"
 Saif yace"hm ai naji wnn shirmen ba wani auren da aka fasa duk tare za'ayi umma tasa ma'aruf ya gaya mata hakane dan kawai a huta da rigimar ta.
   Cikin dariya Zarah tace"cabd'i ashe kuwa in taji bansan ya abun zai kasance ba zatayi kuka hadda style"
  Sosai kuwa in tayi ta gaji ai ta daina.
 Saif ya fad'a cikin ta6e baki.
 Zarah dake kallon sa ta koma jikin sa ta kwanta tana fad'in"he dear baka ko jin tausayin er qanwar taka she is too young fa"
  Yace"which kind be too young yarinyar da har kwaso qafa take tazo dan kawai ganin qwam ai tun daga lokacin naga ba abunda ya dace dasu sai aure shiyasa ma da naji zancen auren naji is gud duk da sosai naso se sun zurfafa a karatu snn but ko auren sukayi sa yi karatun a can cos yama fi.
 Zarah tace"Gaskiya kam ni da farko ma har banji dad'i ba yanda naga sosai Nusaiba ke son ta qara gaba umma tace min ai duk mazajen nasu masu son suci gaba da yin karatun ne nace to Allah yasa idan anyi auren su barsu dan wasu mazan haka suke nunawa se anyi aure su murje ido su basu san zancen ba.
 Saif yace"ai duk wanda kika ga yayi haka ba mutumin kirki bane,ma'aruf kuwa da Nabil (wato wanda zai auri nadiya da shima  d'an uwan su ne)
  Dukkan su sunyi kad'an baza ma suyi hakan ba,dan ba wanda zai d'aukar musu wnn iye shegen but gogewar su ma bazai bar su iya barin matan su ba karatu ba,dan haka kema ki shirya karatu yanzun kika fara har waje sai mun fita dan da akwai course d'inda nake son zanyi nima.
 Cikin murmushi zarah tace"Au haba ka yarda dani sosai knn"
 Of course ke ta baban ce zarah i really trust u a koina ma nasan zaki kare min mutunci na.
 Murmushi kawai zarah tayi snn tace"ni kuwa dear rimin dako nake son inje dan Allah"
  Yace"sorry cutie duka duka yaushe ne suka zo dawowar mu England fa suka zo duba Abba ki bari zuwa wani lokacin and ina ce dai kin basu en tsarabar su koh?
 A shagwa6e cikin son yin kuka tace"eh duk na ba kowa kawai dai kewar su nake dan Allah ka barni inje zowan su fa ba kmr naje bane.
 Nan saif ya tashi zaune rungume da ita a jikin sa yana kallon ta da kulawa snn cikin rarrashi yace"sorry cutie ba ina son takura ki bane,sabon ciki ne dake yafi son zama guri d'aya ki bari idan cikin ya qara qwari se muje hadda ni koh?
   A hankli ta gyad'a masa kai cikin share en hawayen da suka zubo mata snn muryar ta a sanyaye tace"to amma in muka je bafa rnr zan dawo ba zanyi ko sati d'aya ne"
  Cikin marairaice fuska awa qaramin yaro yace"har one week cutie zanyi kewar ki sosai fa gaskiya i can't.
 Zarah da ke kallon sa tayi shiru tana  jin itama fa baza ta iya sati d'aya ba tare da shi ba sosai zatayi kewar sa ga garin ba wani network ne dashi ba bare su riqa yin waya.
Cikin langwa6war da kai tace"to ko kwana uku ne"
  Saif da yaji ko kwana ukun ma sun mai yawa yace"to shikenan but plz take care of ur self in kinje dan Allah kar kiyi abunda zai jijjiga min jikin ki har yabawa babyna matsala kinji.
 D'auke da murmushi ta gyad'a masa kai dan ta fahimce shi daka ne yake son yace kar tayi,dama kuwa bata yin daka sbd ko kad'an bata so,idan ma dakan ya kama dije keyi ita kuma tayi abinci haka suka raba aikin nasu.
 
Se bayan cikin nata yakai wata biyar snn ya yarda suka je rimin daakon,yasa takai shi koina gurin en uwan ta,ya bud'e bakin aljihun sa se rarraba musu kud'i yake kmr baisan zafin su ba.
 Snn bayan ya bar ta da kwana uku ya koma ya d'auko abar shi,yayinda tuni lokacin jamil yayi aure hadda su Nusaiba wacce koda taji ashe wayo kawai ake mata baza a fasa auren ba,ba irin kukan da bata yi ba se Abba ne ya rarrashe ta har ya samu ta haqura,wacce koda akeyin bikin auren kmr ba ita ba har ma zumud'i take taga ta fara rayuwar auren dan ba kad'an ba yanayin yanda taga su saif na zuba soyayyar su abun na bata sha'awa a gaban kowa ba ruwan su musamman saif dake qara jin qaunar zarah a ranshi a duk lokacinda ya kalli cikinda ke jikinta da duk ya qara mata wani irin kyau da haske ta kuma yi 6ul 6ul abunta cikin ya taso ya mata kyau sosai har ma Abba da umma idan suka kalle ta wani irin farin ciki suke ji a ransu sun kusa ganin jikan su.
Wa enda sam qaunar junan da su saif ke nunawa a gaban kowa basa ganin rashin kunyar su se ma dad'i da suke ji 'ya'yan su na zaman lafiya.

Koda cikin zarah ya tsufa sunyi hutun makaranta shiyasa abun ya qara mata sauqi wacce dama  tun wahalar farko da cikin ya bata,bata sake wahala irin d'in nn ba,cikin se taji awa ma ba'a jikinta yake ba komai lafiya lau takeyi abunta da kullum tunda cikin ya tsufa saif ke janta zuwa d'akin motsa jiki da suke da a nn cikin gidan,safe da yamma duk sai ya tafi da ita ta motsa jiki har shima ya biye mata suyi tayi ta hanyar nuna mata yanda masu ciki zasu motsa jikin su ba tare da sun illata babyn da ke jikin su ba.
Yau monday da safe tunda suka gama motsa jiki ta soma jin marar ta na d'an tsinka mata kad'an kad'an amma bata gayawa saif ba har ya shirya ya fita aiki.
 Wanda gabad'aya yana can hankalin sa a kanta se kallon ta yake ta laptop ta tasa fruits a gaba se sha take awa Allah ya aikota dan aikin knn tunda cikin ya tsufa in bata sha fruits ba ji take awa ma mutuwa zatayi shiyasa sam saif bai ta6a yarda fruits sunyi missing a gidan ba kullum cike suke a fridge.
  Wacce bayan tasha tasha,ta kuma je ta d'ibi wasu ta had'a fresh juice in yayi sanyi tayi zaune kuma tasha.
 Da ko yanzu yana kallonta tana gama sha,taje ta d'ibi wasu ta had'a fresh juice bayan tasa a fridge tazo tayi kwance tana jiran yayi sanyi tasha,waya a hannunta se qyalqyatar dariya take tana chatting dasu Nusaiba da Nadiya,dan ciwon maran beyi wani worst ba shiyasa take ta harakokin gabanta.
 Saif dake kallonta se murmushi yake ganin yanda take ta nishad'i da burin sa knn kullum yaga cutien sa a cikin nishad'i ko kad'an baya son ganin 6acin ranta shiyasa ko fad'a ma basu cika yi ba,koma sunyi to baza su iya kwana basu shirya ba dan dashi har ita bazan iya ce muku ga wanda yafi damuwa idan sukayi fad'a ba kowannen su qoqarin yake yaga ya bawa d'an uwan sa haquri sun shirya.
 Wacce tana nn still kwance tana fmn chatting dasu tana dariya se ga kiran dear d'inta ya shigo wayar ta.
  Tayi murmushi tana kallon kiran kafin ta d'aga dan tasan yana can yana kallonta a laptop cos tuni ya gaya mata da akwai camera a gidan,shine ko  asibiti yaje yana samun kansa free  har sauri yake ya bud'e laptop yaga ya lafiyar ta har dai da cikinta ya tsufa duk yafi damuwa ya ganta sbd yasan ita kad'ai ya bari a gida baya son naquda ya kamata bai sani ba.
 Wanda ko ya ganta a laptop she is doing ok to fa se ya kirata a waya yaji if she is ok d'in.
 Da yau har tambayar ta yayi bata fara jin komai ba tace mishi a'a cos bata so ta tashi hankalin shi ya baro aikinsa akan ciwon da bai kai ya kawo ba,da har dare bai daina mata ba bai kuma qara mata ba.
   Har ma ta iya lalubo dear d'inta suka kashe juna da soyayya,dan tsufan cikin sosai yasa mata buqatuwa.
 Wa enda har ma sunyi wanka sunyi shirin bacci suna kwance rungume da juna,hannun saif akan cikin ta as usual se faman shafa cikin yake,kawai yaga ta sauka da sauri daga kan gadon sbd wasu ruwa da taji suna fita a qasanta sauri sauri.
  koda saif ya sauko daga kan gadon cikin sauri yana tambayar ta mene ne,ina bata iya bashi amsa ba se zubewa qasa tayi da sauri kan guiwoyin ta tana yarfi da hannun ta sbd wani irin azababben ciwo da taji yazo mata lokaci guda,ta rirriqe saif tana fad'in"innalillahi wa inna ilaihi raji'iun! Wayyo Allah dear zan mutu dan Allah ka taimake ni!
 Saif da ya fahimci naquda ce duk yabi ya rud'e sai rarrashinta yake yana son ta sake shi ya d'auko makullin mota su wuce asibiti dan sosai ta rirriqe shi har ma baya iya qwatar kanshi,se ma wani irin nishi da yaji tayi mai qarfin gaske da nn gurin kai tsaye ta fiddo mishi da yaran sa duka biyu maza.
[5/3, 9:49 PM] Billy giro😊: _Thursday 03/05/2018_
*«»«»«»SAIFUDDEEN!«»«»«»*




By
  *Billy giro😊*



*Dedicated to»»»Zarah gwandu*





*«»Page«» 68*
Yayinda zarah ta tafi gabad'aya jikinsa se sauke numfashi take tana kallon yaran d'auke da d'an  murmushi a fuskar ta.
  Haka ma saif kallon yaran yake cikin tsananin farin ciki snn ya kalli zarah tare da qara rungume ta a jikin sa ya d'aura mata kiss yana faman yi mata sannu,duk da cewa d'aya bayan d'aya ta fiddo mishi yaran ba tsaiko amma se tausayin ta yake ji,da kuma wata irin qaunar ta da ta qara d'arsuwa a ranshi.
  Wanda nn ba 6ata lokaci ya kama yaran nasa da se faman canyara ihu suke ya gyara su tas har zarah d'in kuwa,da take ya had'a mata tea mai kauri tasha.
  Wacce tana kallo ya yiwa yaran nashi addu'a en du6ul du6ul dasu jawur kmr ka qwanta jini ya fito,da suka d'auko uban su sak kmr an tsaga kara,wanda yana gama yi musu addu'a yayi shiru yana kallon su qwallah cike a idon shi har ma suna saukowa akan kumatun sa.
  Zarah dake kallon su take ta samu kanta a cikin damuwa ta kama kumatun sa muryar ta a sanyaye tace"dear me yake faruwa ne kana kuka a lokacinda ya kamata ace farin ciki kakeyi?
 Muryar sa a hankali ba tare da ya iya daina kallon yaran ba yace"dole nayi kuka cutie dmn a baya na aikata abunda dashi da zina duk d'aya wanda bazan so 'ya'yana su aikata hakan ba ina tsoro.
 Cikin kwantar da murya tace"Dear inshaa Allah 'ya'yanka ma baza su aikata hakan ba ko dan tubar da kayi a gun ubangiji,kawai dai kaci gaba da yin istigifari kaji"
  A hankali saif ya gyad'a mata kai wanda tun lokacin da ya daina wnn halin yake ta roqon Allah yafiya dan yasan ya aikata babban kuskure.
 Zarah dake share masa hawaye a hankali takai bakinta a nashi ta had'e ko zata d'an rage mishi damuwa ae kuwa koda ta zare bakin nata se murmushi yayi yana kallonta tare da d'aura mata kiss kan goshi,snn yace"to a bawa yarana mamma su sha koh,kinga se tsutsar en yatsun su suke yunwa suke ji.
  Nan ba musu zarah ta d'an yaye towel d'in da ke jikinta mammanta  suka bayyana se kallon su saif keyi kan yanda suka qara wani irin kyau da cikowa da kullum in ya gansu qara ganin kyaun su yake.
 Wanda yana fara bawa d'aya zarah tayi saurin rufe idanunta cikin qanqame jikinta kan zafin da taji.
  "Sannu kinji"
Saif ya fad'a yana kallonta da kulawa.
Zarah ta gyad'a masa kai a hankali tare da bud'e idanunta da har sun ciko da qwallah.
 Yace"ko a cire masa mamman ki huta?
 Tace"um um ka barshi kawai"
 Wacce ta fad'i hakane ganin yanda yaron ya samo shan mamman kmr dama can ya saba.
 Saif kuwa sai sannu yake ta mata har yaran suka gama shan mamman.
 Snn sharp sharp ya shirya mata en kayanta a cikin akwati dan surprise yake son yiwa su Abba shiyasa bai kira su ya gaya musu ba,gashi dare yayi kam har sha biyu da wani abu amma baya iya haqura har safe snn ko zasu je gida,shiyasa ya had'a mata en kayanda zasu buqata kawai zuwa gobe da safe,in yaso gobe d'in daga baya snn ya had'a musu sauran.
 Tafe suke cikin mota yayinda yake rungume da d'ayan a jikin shi,haka ma zarah na d'auke da d'ayan wacce se kallon yaran take tayi an shirya su tsaf sunyi kyau cikin kaya iri d'aya se zuba qamshi suke dasu har ita,tana tunanin irin murnar da su Abba zasuyi idan suka gansu hakan nn by surprise.
  Da ban ma san ya zan fasalta muku murnar tasu ba a lokacin da suka isa,se in cika page nawa ma ban gama fad'ar murnar tasu ba da suka ga abun awa a mafarki,yayinda gidan sai ya zama kmr da rana sam Abba ya kasa haqura se kiran mutane yake tayi yana snr da su,haka ma umma duk a wnn lokacin tayi ta kiran mutanen ta tana snr dasu.
 Hjy kuwa ana snr da ita ai kasa haqura tayi itama saida aka tasa driver yaje ya d'auko ta tazo taga en kamakunnen nata.
 Washe gari gidan se ya zama kmr rnr ne ma akeyin suna,mutan rimin daako su Nusaiba nadiya umman kd duk ba wanda bai zo ba an cika gida tamqal se murna ake en barka nata shigowa da duk wanda yaga zarah se yayi mamaki da kuma jin ta birge shi ganin yanda take koman ta lafiya lau abun sha'awa kmr ba ita ce ta haifi yaran ba,gurin wanka dai ake daaga da ita dan da safe har kuka ta ajiye ma umma ita sai an sirka ruwan sai da umma tayi da gaske snn fa akayi wankan.
  Se gashi koda suka fito wankan se taji jikin nata ya mata dad'i har ma tana jin wani bacci mai dad'i na fizgar ta.
Ta kwanta abunta ta hau baccinta dan tuni ta shirya har ta cika cikinta ta kuma shayar da yaran.
 Yayinda saif ke zaune rungume da 'ya'yan nashi se kallonta yake yana kallon yaran yana mamakin wae 'ya'yan sa ne zarah ce ta haifar masa.
wanda tun da safe yake maqale a d'akin ya kasa fita har sai da jamil yazo shida zainab dake d'auke da d'an cikinta na wata biyar,wacce bayan ta gama ganin yaran suka fita tare ita da saif suka kaiwa jamil dake downstairs zaune a falo,ya kar6i yaran se murna yake awa shi ya haife su,har da kallon zainab ya tambaye ta  wai zata haifar mishi irin su yana so,tayi murmushi kawai cikin yanayin jin kunya ta tashi ta koma sama,wa enda sosai sun jima kafin suke barin gidan dan har sai da zarah ta tashi daga bacci snn.

Ranar suna yara suka ci sunan Abba da Abban kd wato Hassan da Hussain(Daddy &Daddy J)
 Anguwar awa zata tsage dan kuwa walima suka shirya gagaruma abun gwanin sha'awa kowa yaci yasha.

Ana yin arba'in saif ya kwashi cutien sa da yaran sa suka koma gida,nn fa wata irin sabuwar soyayya ta qara taso musu mai cike da tsafta yayinda suke bawa 'ya'yan nasu kulawa sosai.
  Yaran nada wata shida ne mom d'in saif ta rasu sbd ciwon zuciya da  tayi jinya sosai a asibiti bcos tunda aka rufe ta kullum cikin kuka da nadamar abunda ta aikata take.
Wacce bata rasu ba saida ta roqi Abba gafara saif,zarah su umma dama kowa mijinta har en uwanta snn ta tafi cike da qaunar en jikokin ta Daddy & Daddy J.
 Wa enda koda suka cika shekara d'aya da watanni sun girma sunyi wayo awa ba en shekara d'aya da watanni ba da duk wanda ya gansu se yaji awa ace 'ya'yan sa ne kan yanda suke da matuqar shiga rai.
Da tuni Zarah ta yaye su,dear d'inta ya kwashe ta suka tafi qasa mai tsalki dmn sauke farali.

Suna dawawo zarah ta hau ciwo ashe laulayi ne,cikin nata nakai wata tara ta haifo santala santalan kyawawan en matan ta identical masu kyau farare tas dasu kmr wacce ta haifesu.
 Ranar suna suka ci sunan umma da umman kd,aka yi musu laqani da Najwa&Najma.
 Inda a lokacin tuni Zainab ta haifarwa jamil kyakkyawan d'ansa kmr shi har ma ana batun yiwa d'an nasa qani ko qanwa.
 Su Nusaiba da  nadiya kuwa suma duk sun haifu,haka ma yayan zarah yayi aure har an haifar mishi 'ya da ya sakawa sunan zarah wanda ba kowa ya aura ba face dije da suke zaman su a nn kano ta goge awa wacce bata ta6a yin rayuwa a qauye ba dan school ma ya sa ta tana yin karatun ta a nn B U k
Inda Zarah a lokacin ta kammala har ma dear d'inta ya kwashe ta sun tafi UK,da duka 'ya'yan nasu da har ma sun saka Daddy &Daddy J school a can,Najwa&Najma kuma shekarun su biyu a lokacin basu sa su school ba tukun.

Yayinda Sophie tuni ta haqura da saif har ma tayi auren ta.
 Saif kuwa qaunar cutien sa ya mantar masa da ita kwata kwata se rayuwar su suke cike da zallar so shida cutien tashi da yaran su,da gabad'aya UK ta sauya su sunyi wani irin fresh da kyau da kallo d'aya zakayi musu kasan tabbas su en hutu ne da suke cikin qoshin lafiya musamman zarah da kullum qara dawo ma dear d'inta take er shila da ko yaushe baya da aiki se yabon daddad'ar zumar ta mai sashi ya manta kowa da komai.
 Wa enda ko yanzu sun gama jin nice d'in su ne suna kwance rungume da juna,zarah se yawo take da lallausan hannun ta a hankali kan faffad'an qirjinsa,cikin wata irin murya can qasa mai dad'i tace"Dear haqiqa kai na daban ne,da bazan ta6a iya daina qaunar ka a rayuwa ta ba,i really Luv u so much.
 Me too my cutie i  really really luv u so much ko a matan fura'aini ke ta daban ce da bazan ta6a iya had'a ki dasu ba.
 Saif ya fad'a tare da d'aura mata kiss kan goshi yana murmushi snn ya kai bakin sa a nata ya sakar mata lallausan harshen sa ta cafka suka hau kissing d'in juna.
      Pens up!🖊

*ALHAMDULILLAH!*
 A nn na kawo qarshen littafin nn nawa inda nayi kuskure Allah ya yafe min.

*MISS ZOZO*
U are d best among d rest,ke ta da ban ce,i sank u so very much.
 Nagode qwarai Allah ya barmin ke ya nuna min ranar auren ki musha bidiri bired'e.

And u also Zulaihat Abbakar i thank u so very much,Allah ya sauke ki lafiya ya baki rayayye mai albarka.

   *RAZINA'S MUM(Aysha er mama)....HM FAD'AR IRIN QAUNAR KI DA NAKE A RAINA MA YAWA NE,KIN RIGA KIN 6ARE ZUCIYAR💔 KIN SHIGA CAN CAN CIKI IRIN SOSAI D'IN NAN.*
 *ALLAH YA BAR MIN KE AKAN QAUNAR DA KK MIN😍.*


SA'RE ROIBE na gode qwarai.

AND THEN.

*🅱ILLY GIRO NOVELS ROOM*.

*🔥BILLY FANS GROUP🔥.*

*Beelly giro fans*.

*Billy giro &futha Luv Fans1.*

*Billy giro &futha luv Fans2.*

*SAIFUDEEN FANS*

_Kai all grps d'inda suke karatun wnn littafin ina matuqar qaunar ku,Allah ya bar min ku akan qaunar da kuke yiwa littafin nn Amin tanks all._



adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *