Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, June 17, 2020

KAWARTA CE SANADI COMPLETE HAUSA NOVEL

adsense here
KAWARTA CE SANADI COMPLETE HAUSA NOVEL

Compiled by Umar Dalha.








💜💙❤🖤💚💛
KAWARTACE SANADI
💚💛❤🖤💜💙


®zuwairat(ummu Maryam)


1⃣



 *Alhamdulillah*

 *Am back again by the grace of Allah*

 *Please kar Wanda ya chanza min littafi ba tare da izinina ba*

 *_Wannan littafin is nothing but a fiction*


 *Kuma Dan Allah kar Wanda ya hada min photos na stars kuma in mutum yayi har ga Allah ban yafeba* 



Wasu mata ne zaune cikin wani katafaren falo, dukkan su sanye suke da Vail banda daya wance take da alaman cikin gidanta take, duk fuskokinsu looks sad, daya daga cikin Matan mai kama da matangidan tace
"Ni har yanzu ban gane wannan abunba...ya zaayi cikin shekara daya maneman auren yarinyan nan su dinga ja da baya?... Kuma duk sai sun kawo lefe amma daga baya su fasa?..." Bata idaba wata ta katseta dacewa
" kema dai kin fada....wannan abun da gani ba haka nan bane...there is something big behind this... Yarinyan nan ba wani mugun hali gareta balle ace kilan bincike suke kanta....nidai gaskiya Hadiza mu  mike tsaye.... " tafada tana kallon matan gidan, Ahankali Matan ta cire hannun ta daga tagumin datayi ta kallesu Sannan tace
"Yanzu sis me zanyi?...hmmm...nidai nasan kawai lokacin aurenta ne baiyi ba....besides by daughter is just 20 years old.. Name zan dami kaina?..." Tafada cikin sanyin murya,
"Daman abinda zakice kenan...to let me warn you... Wannan abun dake faruwa is not just like that....this is a bad omen,...ya zaayi yarinya son kowa kin Wanda ya rasa ta zama tamkar abun wasa wurin maneman auren ta?...gaskiya dole mu mike tsaye..." Wata babban cikin su ta fada , Dan tsayawa nayi na kurawa dukkan su kallo naga suna dan kama da juna da alaman dukkan su biyar a related ko kuma ince are siblings. Matan gidan kallon wacce tayi magana tayi
"Sisters... Kar muyi staining hannuwanmu da zunubai kan matsalolinmu...yanzu in mukaje wurin malamai..abubuwa daban2 zasu fara fada mana....kawai mu kai kukan mu ga Allah batare da Mun je wani wurin ba...." Mikewa babban cikin su tayi
"Ki zauna nan ...ai kin ga zama...." Tafada tana daukan wani hadadden hand bag tare da Vail da ke kusa daita, kallon ta Matan gidan tayi ta kalli wata mai aiki dake jera abinci kan dinning Sannan tace
"Anty ki zauna ki ci abinci mana..." Matan galla mata harara tayi
"Ke Allah ya sauwake halin ki....wato ta abinci kike?...mtssss" ta fada ta bar sauran nan zaune. Hanyen waje tayi. Matan gidan mikewa tayi jiki ba kwari ta dan raka Matan Sannan ta dawo. Sauran mikewa sukayi Tana karasowa cikin falon ta kalli sauran Matan Sannan tace
"Sisters.. Muje muci abinci..." Tafada cikin sanyin murya, dukkan su mikewa sukayi Sannan daya daga cikin su tace
"Ina ihsan din take?..."
"Tana upstairs..." Matan gidan ta amsa mata. Wacce tayi tambayan ta kama hanyan upstairs sauran suka nufi kan dinning table.

A upstairs kam cikin daya daga cikin dakunan wasu beautiful black beauties biyu ne zaune kan gado, daya bata da Dan kwali tana zaune kan gado don har kafafunta suna kan gadon, da ganinta cikin tunani take, daya kuma zaune bakin gadon hannun ta daya kan cinyan wacce ke zaune kan gadon,
"Babe am so sorry about this... Kiyi hakuri..Allah zai baki Wanda ya fishi..." Inji wacce ke zaune bakin gadon, itadai bata ce komai ba don banda tunanin rayuwan ta babu abinda takeyi,  tacigaba dacewa
"Shahid doesn't deserve you... Ki kwanta da hankalin ki Allah zai kawo Wanda ya fishi..." Tafada tana massaging yatsunta Ahankali,  Ahankali yarinyan dake zaune kan gadon ta daga manyan idanuwanta Sannan tace
"Ni har yanzu abinda ke bani mamaki shine duk basu cewa ga laifina agaresu...ko jiya kwana mukayi da shahid...amma..." Bata idaba ba kuka ya kufce mata
"Sis what have I done wrong?... What is happening to me?...in one year... 3   wedding date amma non is coming through..." Tafada cikin kuka sosai, da sauri dayan budurwan ta haye kan gadon, ta rungume ta tana cewa
"Babe...please don't cry...you know how much I hate to see you cry...please stop it...." Tafada cikin comforting tune, itakam kaman ance ta ta kara volume, rungume kawarta tayi ta cigaba da kuka,
"In kina kuka ni ince me?...remember we are of the same age amma babu namijin da ya taba kawo kudin Neman aurena gidanmu... So kinga yours is better..." Da sauri mai kukan ta fara girgiza kanta tana cewa
"Wallahi naki ya fi....nida sai ansa rana an kawo lefe sai a fasa fah?... Yanzu mutane sai suyita tunanin wani mugun Abu nakeyi yasa ake guduna....Wallahi am tired...." Da sauri kawarta ta rufe mata baki tana cewa
"Shhhh....stop saying that...komai jarabawa ce...Allah ya baki ikon cinye wannan jarabawan...." Bata idaba ba wayanta ya fara ringing, da sauri yarinyan dake kukan ta daga kanta tana kallon wayan kasancewan tasan mai kiranta cos he's ringing tune is different, itama kawarta kallon wayan tayi, ihsan zata dauki wayan kawarta tayi saurin daukan wayan tayi picking tafara cewa
"Munafiki...Allah yaisa tsakanin mu da kai...wallahi yanda ka sa aminiyata hawaye kaima sai kayi Wanda yafi nata.... Shege...." Tana kaiwa nan ta katse wayan, ihsan tsaya kallon ta tayi,
"Haba husna....what did you do that for...." Da sauri ta fara cewa
"Yo ai is better in zage shege....in badan ya rainaki ba ya zaayi  ya fasa auren Sannan ya kiraki Dan uwarshi...."
"Kilan hakuri zai bani..." Tafada ahankali,
"Kam...Allah ya sauwake..." Bata idaba wayan ya dauki ringing kuma da sauri Husna ta dauki wayan ta kashe shi ga baki daya, itakam ihsan bata kara cewa komai ba  tacigaba da kukan bakin cikin abinda ke damunta, itakuma husna sai lallashinta take, kofan dakin aka bude wata ta shigo
"Ambaby Ashe haka aka karayi?..." Matan ta fada, da sauri ihsan ta mike ta fada jikin mata ta kara fashewa da kuka,
"Kai...stop crying... Meye abun kuka?....." Inji Matan,
"Abinda nake fada mata kenan anty Zainab..." Inji husna
"To kinji kawarki ta fiki ahankali... Ki shuru abinki.. Meye cikin auren in badan yana sunnan manzo ba...." Anty Zainab ta fada tana shafa bayanta,
"Amma anty kilan aljanu gareni...."
"Shush...ki bar fadan haka...komai daga Allah ne...ko aljani sai da izinin Allah.... Maza muje ki ci abinci..." Da sauri ihsan ta girgiza kanta
"Anty ban iyacin komai..." Anty Zainab Dan tureta tayi tana cewa
"Ki sauko kici abinci in ba haka ba in kira maki anty Zuwairat..." Da sauri ta kalli Anty Zainab
"Ta zo ne?...."
"Eh..tana downstairs..." Da sauri ta goge hawayenta tare dashiga bathroom ta wanke fuskan ta ta fito amma still idanuwanta ja ba kaman kasan idanuwanta abinda da farar yarinya.
"Babe muje muci abinci..." Ta fadawa husna cikin sanyin murya dukda tasan ko kadan ba abincin zata iyaci ba amma tana tsoron anty Zuwairat don duk cikin yan uwan mom tafi tsoron ta cos she's a no nonsense person. Dukkan su fitowa sukayi.
 Suka zauna kan dinning, mom sai kallon ta take, duk mutane sai cin abinci suke amma banda ihsan dake wasa da spoon dinta,
"Wai baki cin abincin ne?..." Wata mata ta daka mata tsawa da sauri ta fara cin abincin, da gani Matan itace anty Zuwairat, itakam husna ko daga kai bata Iya yi don ba karamin tsoron anty take ba.

Haka ta dinga forcing kanta tana cin abincin har ta dan koshi, gyara kan dinning sukayi itada husna tare da mai aikin su, hanyan upstairs sukayi tare mom ta kirata suka koma falo. Kallon indian movies suke amma hankalin ihsan bai waje duk ta fada duniyan tunani, hannun ta husna ta kama kasancewan zaune suke kusa da junansu , mom kam banda kallon yarta babu abinda takeyi, around 3:30 su yan uwan mom suka zaunar daita suka bata shawara kan ta kwantar da ta dinga adua, jinsu kawai take don tasan she's lazy in the aspect of praying, Sam bata iya daukan good 30 minutes tana gamawa da Allah, ko sallah kullum in tana yi kaman ana jiran ta, mom har tayi mata fada ta gaji kan rashi aduan ta bayan ta  idar da sallah.
Bayan sun gama bata shawara sukayi bankwana da mom Sannan suka tafi. Bayan tafiyan su da yan minutes wani Prada ya shigo gidan, wani babban mutum ne aka budewa kofa ya fito, da kanshi ka ga mahaifi ihsan don har idanuwansu iri daya. Yana shiga falo husna ta ruga da gudu ta fada jikin shi ta fashe da kuka, mutumin rungume ta yayi yana shafa bayanta yana cewa
"Haba momina... Stop wasting your tears...nobody is worth it... Ki bar kuka kinji momin daddy...." Bai idaba wasu yara uku suka shigo ciki da alaman daga school suke don sanye suke da school uniform, suma rungume mutumin Sannan babban cikin su wacce zata kai shekara sha hudu tace
"Yaya ya akayi idanuwanki suka kumbura?... What's wrong with you?..." Ahankali ihsan ta kama hannun yarinyan Sannan tace
"Janna...shahid ya fasa auren...." Tafada wasu hawayen suna zubowa, dan buga kafa janna tayi tana cewa
"But why?...me kika yi mashi?... Wallahi duk na fadawa class mate dina...ohhhhh my Allah..." Duk abinda sukayi mom na zaune tana kallon su haka itama husna, karamin cikin su Wanda bazai wuce 8 years ba yace
"Yeyyyyy...daman banason yaya tayi aure...kullum adua nake kar ta tafi ta barni gidan nan...I always want her around me...." Hannu Janna ta daga zata huge ta ihsan ta rike mata hannu
"Yanzu handsome bakasan inyi aure?...remember am 20..." Yaron daga mata kai yayi alaman eh wato da gaske yake,
"To shikenan... Sai in zauna ka dinga kallona...." Tafada cikin sanyin murya,
"Yeeyyyy daman haka nakeso...after ga bestie dinki batayi aure ba..." Yafada yana nuna husna nake karasowa wurin dad ta durkusa ta gaidashi ya amsa mata cikin jindadi don kowa na gidan suna kaunan husna tamkar yanda suke kaunan ihsan.

Mom ce ta mike ta rike hannun mijinta ta kaishi part dinshi, yan makaranta su ka hau upstairs don cire kayan school.

Around 6:00pm husna ta kalli ihsan Sannan tace
"Babe zan wuce..." Da sauri ihsan ta kama hannun ta Sannan tace
"Pls babe kar ki barni....wallahi I want you around me...banason ki barni..."
"Bari in fadawa mom tunda ba fada mata zan kwana ba...." Ta fada tana dailing number mom dinta
"Ok.." Ihsan ta masa mata, bayan kaman few seconds akayi picking call daga chan bangaren, husna ta fara cewa
"Momcy..zan kwana gidansu ihsan... Gobe zan dawo...." Daga chan bangaren matan tace
"Ok...gobe zanzo gidan sai mu taho tare...ki gaida min su..."
"Ok momcy..." Tafada Sannan ta katse wayan ta
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: ❤💜💚🖤💛💙
KAWARTACE SANADI
💚💛💜🖤💙❤

®zuwairat( ummu Maryam)


2⃣


Gidaje biyar daga gidansu ihsan kam wani babban gida ne Wanda mai gadi ya bude gate adaidai lokacin da wani babban mota Wanda aka rubuta GMC ya yi horn gaban gidan. Mai gadin yana budewa yana  gaida Wanda ke cikin motan, hannu kawai ya daga mashi Sannan ya shiga cikin compound tare da  parking cikin parking lot inda sauran cars suke, bayan ya gama parking yayi relaxing cikin motan for about 5 minutes Sannan ya fito, hmmm am dropping dead cos gayen is beyond handsome, gashi ko kadan ba fari bane, sanye yake da jean da normal t shirt, hannun shi kwance take da gashi don tamkar ayi kitso, a babban yatsanshi silver ring ne mai shegen kyau da tsada, daka ganshi kasan he's tired, bayan ya fito ya zagaya baya ya dauki bag dake dauke da something like system Sannan ya rufe motan ya fara takawa ahankali, gani nayi ya nufi wani part ba mai girma ba don da akwai babban apartment amma Wanda ya nufa is moderate, yanda yake tafiya kama bata lakka ajiki,
"Yaya Ayan!...." Wata yarinya ta kwala mashi kira daga benen babban apartment, daga kai yayi ya  kalle ta,
"Babyna... Ya kike..." Yafada har lokacin yana tsaye, yarinya wacce bazata wuce 15 ba tace
"Am fine...ya aiki?..."
"Alhamdulillah... Hope you took very good care of Umma?..."
"Yes yaya..."
"That's good... Bari in watsa ruwa...."
"Alright yaya..." Ta amsa mashi, ahankali yacigaba da tafiya, bai ida kaiwa bakin kofan ba ya karajin ance
"Yaya Ayan... Welcome..." Daga kai ya karayi ya kalli wasu yanmata biyu da ganinsu kasan yan biyune,
"Yauwa...how was your day?..."
"Fine yaya..." Suka amsa mashi in chorus
"Ya lectures?..." Ya kara tambayan su
"Cool yaya..." Suka kara masa mashi in chorus
"Good.. Let me take a shower...." Yafada masu Sannan ya karasa bakin kofan, ya bude ya shiga. Falon yana da kyau sosai kaman bana saurayiba, one bedroom apartment ne, tun daga falo ya fara cire kayanshi, daga shi sai boxer shorts ya shiga bathroom ya sakar wa kanshi ruwa Sannan ya fito daure da towel. Light kaya ya saka don he don't mind walking naked no dukda kayan daya saka basu da nauyi ji yake kaman da dutsi cikin su. Wayanshi yadauka ya saka cikin aljihunshi Sannan ya fito ya nufi babban apartment din. Yana shiga falo wata babbar mace ta daga kai ta kalleshi, da sauri wani yaro dake zaune gabanta ya taso da gudu
"Yaya...oyoyo..." Yafada yana makale shi. Ayan daukan yaron yayi ya daga shi sama Sannan yace
"Superman...how far..." Yaron Wanda bazai wuce 10 years ba ya amsa da
"Am great yaya..." Karasawa yayi wurin Matan ya zauna
"Umma ina wuni..."
"Alhamdulillah son ya aiki?..."
"Lafiya lau...ina Abba naga motanshi a parking lot..." Yafada yana relaxing kan sofa
"Maza tashi kaci abinci... Don't relax...." Inji Umma, ta fada tana tureshi daga kan kujeran.
"Ohhh Umma am tired ..I want to rest...." Ya fada cikin shagwaba, yaron dake zaune kan kafan Umma saida yayi dariya
"Da akwai patient da yawa a hospital yau ne?.." Umma ta tambayeshi
"Yes Umma..."
"Ko zaka kara doctors ko nurses?..."
"Umma ba karancin doctors ko nurses bane kawai wannan season da koina rashin lafiya ne, baka minti biyar zaune sai an tqdaka...." Yafada yana Kara relaxing

"Eat then you rest...." Inji Umma, yana kokarin nufan kan dinning da aka jera abinci na daidai mutum daya.

Yanbiyu suka sauko,
"Umma zamu he ganin lefen ihsan..." Inji daya daga cikin yanbiyun,
"Ok...nima gobe zan shiga...." Inji Umma,
"Salma!..." Ayan dake zaune kan dinning ya kira daya daga cikin yanmatan
"Yes yaya..."
"Pls serve me before you go..." Yafada mata cikin kasala, da sauri yarinyan daya kira ta je tayi serving dinshi Sannan suka kama hanyan waje
"Ku dawo yanzu..magrub is around..." Umma ta fada masu
"To Umma .." Suka fada Sannan suka fice. Wata yarinya ce ta zauna kusa da Ayan ta fara feeding dinshi yana amsa abinci suna hira, bayan kaman minti talatin da fitan yanbiyu suka dawo.
Yanayin fuskan su said it all
"Lafiya na ganku haka kaman ku dawo daga gidan mutuwa?.." Inji Umma, shikam Ayan juyowa yayi ya kallesu don har lokacin bai tashi daga kan dinning ba dukda ya gama cin abincin. Jiki ba kwari ya yan biyu suka zauna kusa da Umma, Ayan sai kallon su yake don yana tunanin kilan wani ya bata masu rai yayi rashin mutunci
"Wai ba daku akeba?..." Ya daka masu tsawa, ahankali daya daga cikin yan biyu ta fara cewa
"Wai Umma an fasa bikin ihsan...."
"Subhanallahi... Not again..." Inji Umma, Ayan najin abinda suka fada ya juya don baisan inda zancensu ya dosa ba, hira suka cigaba dayi da little sis dinshi mai suna hafsat, Umma kam sai mamakin abinda yan biyu suka fada mata take,
"Har muna murnan da akwai shagali a nan President avenue tunda sati two ke tsakanin nata da namu....amma gashi an fasa kuma..." Inji salma,
"Ni wallahi abinda ke bani mamaki shine ko kadan ihsan bata da halinki....I don't know why this is happening to her...." Inji gudan yan biyu mai suna samera, Umma dai shuru tayi don tunani kawai take
"Ni wallahi kwata2 ihsan bata da wani bad character..ina Iya shaidanta tunda course mate ditace..." Inji salma,
"Samera daukomi gyale daga upstairs..." Inji Umma cikin sanyin murya, da sauri samera ta haye sama  baa dadeba ta dawo da wani expensive Vail ta mikawa Umma, amsa Umma tayi ta yafa, da sauri Dan karamin yaron ta ta mike
"Umma zanje...." Yafada kaman zaiyi kuka
"Lets go..." Tace mashi, Ayan juyowa yayi
"Umma ina zaki?..." Ya tambayeta
"Nan neighbor zan shiga..."
"Ko in rakaki tunda magrub ta gabato?.." Inji Ayan
"No..ka huta...yanzu zan dawo..." Tafada tana kama hanyan waje autanta da biye da ita. Part din Abba sukaje ta fada mashi abinda ke faruwa, shima mamaki ya dingayi don suna mutunci sosai don basu sati basu nemi junansu ba dukda busy schedule dinsu.
 " I think wannan shine kashi na  uku ko?..." Abba ya tambayi Umma
"Eh Wallahi... Wannan abun yayi yawa..." Inji Umma
"Allah ya kawo mafi alkhairi..." Inji Abba
"Ameen... Bari in leka chan..."
"Ok...bari in kira Musa.." Abba ya fada yana daukan wayanshi. Umma fita tayi superman yana biye dashi.

Kanwar Ayan wacce ta bashi abinci yaci my suna Nafisat amma ana kiranta antynmu cos sunan babban kanwar Umma aka mata ta dauko assignment, suna zaune nan kan dinning table yana nuna mata assignment din, yana gamawa ya mike ya nufi part din Abba, cikin respect ta gaidashi as usual Sannan ya fara cewa
"Abba..." Ya kirashi cikin sanyin murya
"Yes son...." Ya amsa mashi
"Daman inason ka bani izini in koma cikin wannan gidan tunda an gama...." Ya fada kanshi kasa, kallon shi  Abba yayi for a moment
"Meye dalilin ka nason barin wannan gidan...."
"Babu wani dalilin... Kawai dan yafi kusa da hospital...." Yafada Ahankali, kai Abba ya girgiza Sannan yace
"Wannan ba dalili bane...anyway ka bari Sai kayi aure..." Da sauri Sadiq ya kalleshi
"Abba yanzu sainayi aure zan koma ?..." Ya tambaya har cikin ranshi bai so hakan ba,
"Eh..ko da akwai wani abu daban da kake na niyyan yi?...." Da sauri ya girgiza mashi kai
"Good... " yafada yana mikewa, Ayan na zaune wurin har Abba ya fito daga bathroom, shima mikewa yayi ya shiga ya dauro alwallah Sannan suka fita zuwa masjid, Suna isa bakin gate Umma da Ismail wanda suke kira da superman suka dawo, da gudu yaron ya tafi bakin tap dake bawa flowers ruwa ya dauro alwallah Sannan suka tafi gabadayan su.



The following day Ayan ya shirya ya ajiye antynmu da ismail a school Sannan yawuce wurin aiki.

A hospital kam yana zuwa wasu guys guda biyu suka nufoshi,
"Fabulous.. How far Abba ya amince?..." Daya daga cikin su ya tambayi Ayan,
"Wallahi guys Abba bai amince ba...wai Sai nayi aure...." Dariyan rainin hankali gayun biyu sukayi Sannan farim yace
"Kambu...kai yaushe zakayi aure?... Ko baby fa baka dashi...." Dariya suka karayi, ba kara kallon suba ya sa mukulli ya bude office dinshi still suka biyo shi,
"Wallahi fab naso muyi rocking wannan gidan kafin kayi aure..,"
"Ka rungumi sorry ..." Inji Ayan dake fiddo laptop dinshi daga cikin bag, duk guys din sunyi mashi tsaye, zama yayi yana kallon su
"Ya akayi ne?..." Ya tambayesu, kallon juna guys din sukayi Sannan daya yace
"Ka nemo mana wata mafitan....we need place to party..." Galla masu harara yayi
"Ku tafi bakin aikinku ko inyi saking dinku yanzu nan...." Yafada in am the boss voice, dariya sukayi tare da tafawa Sannan sukace
"Yes boss..." Suka fada Sannan suka fita


 Abangaren ihsan da following day ta shirya sisters da brother dinta tare da taimakon husna suka rakasu har inda suke hawan school bus Sannan suka dawo gida, har yanzu bata bar tunanin matsalan rayuwan ta ba, suna daf da shiga gida wani mai mota ya dinga horn, bata juya ba sai husna data juya ta kalli saurayin dake cikin motan,
"Baby kizo mu shiga cikin gida...." Inji ihsan, cikin whisper husna tace
"Ke bari inje...kikasani ko nawa mijin ne?.." Tafada Sannan ta juya ta koma wurin mai motan itakuma ihsan ta shige gida. Husna na zuwa wurin saurayin suka gaisa Sannan saurayin yace
"Dan Allah yanmata wancan yar uwarki ce?..." Ya tambayeta , nan take yanayin fuskanta ya chanza.
"Ya akayi?..." Ta tambayeshi fuskan ta kaman bata taba dariya ba
"Tayi min ne...." Dan baki ta tabe Sannan tace
"Ka fada mata...." Tana kaiwa nan ta juya , dasauri saurayin yace
"To Dan Allah ki kiramin ita...." Banza tayi ta shige cikin gidan su ihsan ba tare data amsa mashi ba, cikin kitchen ta tarda ihsan tana jerawa mai aiki abinci kan tray ta kai kan dinning, juyowa tayi ta kalleta
"Har kin gama zancen?..." Ihsan ta tambayeta, lafiya lau tayi dariya kaman ba itaba Sannan tace
"Ke rabu da dan iska..." Dariya ihsan tayi
"Ke kullum wurin ki samari yan iska ne...yanzu me ya fada maki har kika maidashi Dan iska?..." Inji ihsan,
"Babe kawai dan iska ne..." Ta amsa mata atakaice. Breakfast sukayi gabaki dayansu banda sauran yaran dake school da dad dake tafiya da breakfast dinshi office, mom na gani yanda ihsan ta Dan saki jiki ta ci abinci kaman ba ita ba ta kalli husna Sannan tace
"Second daughter ina gode maki....you have always been there for your friend...da bansan yanda zanyi daita ba in babu ke ...na gode Allah yayi maki albarka..." Kanta kasa ta amsa da
"Ameen..." Ihsan kama hannun ta tayi tace
"Thanks for been there for me..." Harara husna ta galla mata Sannan tace
"Nasan ke in ina cikin matsala zaki taimaka min...so.is nothing..." Suna gama breakfast suka gyara gidan kaman yanda suka saba don duk ranar da husna tazo gidansu ihsan da  ita suke aikin gidan haka itama ihsan in taje gidan husna tare suke aikin gidan su. Shakuwansu ta wuce misali, unfortunate twins ake kiransu tunda daga primary school har zuwa yanzu da suke 300 level a buk, amincinsu ya sa iyayensu aminci, amma one thing is that ba halinsu daya ba, ita ihsan is straight forward, bata da fuska biyu while ita husna is a very good pretender

Abinda fuskanta ke fada daban da abinda ke cikin zuciyanta, kuma nobody knows her true colour, ko uwarta batasan real halinta ba, amma kunsan ko wane hali na da inda aka samo shi dukda ba duka halin iyaye yara ke inheriting ba  amma some of children's characters a inherited from their parent. In kana abu to confirm da akwai dan da zaka Haifa ya fika wajen wannan abun. Allah yasa mu dace ameen.


Bayan sallan zuhr Hajiya amina wato mahaifiyar husna ta zo gidan. Lokacin su ihsan da mom na zaune falo, tana sallama ihsan da husna suka mike da gudu suna rige2 isa gareta, rungume ta sukayi har suna neman kadata,
"Mami sannu da zuwa..." Suka fada mata a tare
"Yauwa yan biyun mami..." Tafada tana rungume dasu biyu, mom kam dariya take tana cewa
"Ko yaushe zaku girma?..."
"Ki kyale manisu tunda ni bani dasu da yawa..." Inji mami kasancewan yaranta biyu duk mata, daga husna Sai kanwanta Fiddausi.

Zama mami tayi suka gaisa da mom har lokacin su ihsan na makale da ita,
"Mami ina tsarabanmu?.." Ihsan ta tambayeta,
"Ku duba cikin handbag dina baku rasa abin lasa..." Ta fada tana ajiye masu handbag dinta, da sauri su biyu suka suri bag din suna dubawa, husna ce ta dauko orbit gum da kingtat chocolate, tana daukan su tayi sama da gudu
"Kam.. Ai wallahi kinyi kadan..." Inji ihsan dake biye da ita da gudu, mom da mami ban da dariya babu abinda sukeyi.
Mai aiki mom ta kira ta kawowa mami abin sha. Daga nan hira ta barke tsakanin su
"Oh ni ameenatu...INA mamakin wannan ikon Allah.... Ashe duk Sai su kawo lefe su fasa auren..." Inji mami dake jimamin abinda ke faruwa
"Aikam hajiya" tagumi Hajiya ameenatu tayi for a few minutes Sannan ta mike ta koma kusa da mom, mom dan gyara zamanta tayi don ta samu daman fuskantan Hajiya ameenatu, cikin magana kasa2 Hajiya ameenatu ta fara cewa
"Yanzu Hajiya wace mataki kika dauka?..." Tafada yanda babu mai ji Sai mom, ahankali mom tace
"Hmmm yaruwa adua kawai muke... Komai yayi farko dole zaiyi karshe Sannan duk nisan jifa kasa zai dawo...." Ido mami ta zaro
"Kambu...adua!?..." Ta fada sounding as if mugun abune adua Sannan tacigaba dacewa
"Wa ke tsaya adua yanzu?... Ai Sai a gama da kai kafin aduan taci...." Tafada sounding discourage
"To hajiya in ba adua ba mene abinyi?...Wallahi right now am so confuse...." Yanda tayi maganan ya nuna da gaske she's feed up with her daughter's predicament, hannun ta mami ta rike Sannan ta fara cewa
"Kinsan Hajiya Hadiza tamkar yar uwa na dauke ki...dukda ta sanadin yaranmu Allah ya hada mu..bazan ga abinda zai cutar da ke inyi shuru ba mussanman ihsan cos tamkar husna na dauketa....ina da wani malami a hotoro muje muji actual abinda ke faruwa...." Tunda mami ta ambaci malami mom ta bude baki tana kallon ta, don banda mamaki babu abinda take, Ahankali ta daga mayyan idanuwanta Wanda ihsan ta gada ta kalli mami Sannan tace
"Hajiya na gode da damuwanki kan matsalan mu amma gaskiya I don't want to go astray..." Kallon mamaki mami tayiwa mom don batayi tunanin zatayi gardama with the problem she's having ba
"Amma Hajiya ba going astray bane....kinga wannan yarinyan tana bukatan adua daga manyan malamai don abinda ke faruwa ba haka nan bane....in baki zuwa ki amince Mani in tafi daita wurin malamin ya duba mani ita....pls don't refuse me..." Tafada har lokacin tana rike da hannun mom yanda take magana tamkar itace mahaifiyar ihsan,
"Wannan Matan bata da hankali...yata takeson koyawa bin malamai tun yanzu?...Allah yasa bata koyawa yarta ba din in haka ne to da akwai matsala..." Mom ta fada cikin ranta, azahiri kam murmushi tayi tare da dora hannun ta daya kan hannun mami dake rike da hannun ta Sannan tace
"Hajiya babu Katanga tsakanin mu da Allah... Nasan ba kasafai adua keci da wuri ba amma mahakurci mawadaci....don haka abinda nake bukatan ki yiwa yarki ihsan shine ki taimaka mata adua...with Allah Almighty all things are possible.... Nasan in mijinta yazo babu abinda ya isa ya rabasu...." Mami kallon ta ta tsaya yi, batace kala ba saida ta kai aya Sannan tace
"To shikenan....Allah yasa mu dace...." Tafada batare dataji komai ba,
"Ameen... Uwar ihsan da husna...." Inji mom. Hira suka cigaba dayi har bayan asar Sannan suka shiga mota da husna ta jasu suka bar gidan.
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💙💚💜🖤💛❤
KAWARTA CE SANADI
❤💛💙🖤💜💚


®zuwairat( ummu Maryam)


3⃣


Mami na tuki husna zaune gefen ta tana chatting da wayanta, dan daga kanta tayi taga mami ba hanyan gida tayi ba
"Mami ina zamu?..." Tafada tana kallon hanyan, dukda tasan inda zasu amma still saida ta tambayeta
"Gidan Malam..." Ta amsa mata atakaice,
"Ba last week muje ba?..." Kallon su nayi ina mamakin abinda ke faruwa, wato uwar da dayartatake zuwa gidan Malam,
"Eh...kudi zan kai mashi don naji dadin aikin da yayi min..."
"Ok..." Husna ta fada tana relaxing cikin motan tare da cigaba da chatting.
"Baby...." Mami ta kirata, ahankali ta daga very beautiful and innocent face dinta ta kalleta mami ta cigaba dacewa
"Matsalan kawarki yana damuna... Gashi nayiwa mahaifiyar ta magana kan muje wajen Malam kuma taki..." Dan baki husna ta tabe tare dacewa
"To mami tunda basu so na sai ki kyale su ba...." Kallon ta mami tayi kuma tayi mamakin jin irin wannan maganan a bakinta
"Baby matsalar bai damunki ne?..." Mami ta tambayeta tana karya kwana.
"Mami yana damuna mana..amma tunda basu son taimako sai a kyale su...is not by force..." Tafada in I don't care manner.
"Hmmm...I wish there is something I can do about it..." Inji mami dake parking a kofar wani tsohon gida. Yanda take magana tamkar tana magana da wata kawarta sam kama ba ita ta haifi husna ba nikam mamaki kawai nake.

Dukkan su fitowa sukayi suka shiga wannan karamin gidan, da Sallama suka shiga cikin gidan, da maraba aka amshe su don da gani Matan gidan sun saba da su,
 "Ina Malam?..." Mami ta tambayi Matan gidan, babban cikin su dake shara ta kalli mami da murmushi fuskanta Sannan tace
"Ki shiga ciki...yana nan...." Mami sallama tayi bakin wani karamin kofa wani matured voice ya amsa mata, husna kam, zama tayi kan wani bench dake kofan daki.
"Kema ki shiga mana...sai kace wata bakuwa?...." Inji Matan dake shara, murmushi husna ta saki Sannan tace
"Nan ma yayi..." Ta amsa mata.

Wani babban mutum ne zaune kan katon carpet, gaisawa sukayi da mami da gani mutumin ya ji dadin zuwan mami.
"Hajiya da fatan lafiya?.." Mutumin ya tambayeta,
"Lafiya lau..daman godiya nazo in maka...Wallahi wannan aiki yayi sosai... Ya bani kudin dana bukata...." Tafada tana dariya ,shima mutumin dariya yayi
"AI bai sai kinzo ba...ko waya kikayi ya wadatas...." Inji Malam, itakam husna tana jin duk abinda suke cewa kuma babu alaman surprise tattare da ita cos daita mami ke zuwa wurin malaman ta.

"Ai ya zama dole inzo...." Tafada tana saka hannu cikin handbag dinta. Dubu 50 ta yi counting ta mikawa Malam, mutumin washe baki yayi
"Ga wannan, aikinka yayi kyau...." Inji mami,
"Hahhhh...ai kadan kenan...kudi kam sai an karo maki tunda kin kawo hasafi...." Inji Malam
"In kam alhaji ya karo kaima zakaji ajikin ka.." Inji Hajiya dake dariyan jindadi. Mikewa tayi
"Wucewa zanyi cos daman abinda ya kawoni kenan..." Shima tsohon mikewa yayi
"To nagode..." Mami fitowa tayi tsohon na biye daita,
"Kece kikazo baki shigo kin gaida Malam ba?..." Inji Malam daya gan husna dake zaune kan bench,  murmushi husna tayi tana mikewa tare da gaidashi, shima amsawa yayi yana murmushi.
Har kofar gida ya rakasu suka shige mota suka kama hanyan gida.


Ihsan na kwance tayi ruf da ciki idanuwanta lumshe amma ba bacci take ba, sanye take da doguwa rigan swiss lace, sai karkada kafa ahankali bude kofan da akayi yasa ta bude ido, dan juyawa tayi ta hangi mom, da sauri ta mike zaune don mom bata fiya shiga dakinta ba.
"Habibty..." Mom ta kirata tana zama a bakin gadon ta, kai ihsan ta daga tana kallon ta, Ahankali mom ta sa hannu ta Dan cire mata strand of hair dake fuskan ta,  idanuwanta mom ta kalla tana jin so da kaunar yarta har cikin ranta
"Kiyi hakuri da jarabawan da Allah ya Dora maki...komai yayi farko tabbas zaiyi karshe....kuma dan Allah ki bar wannan 3 minutes prayers... Ki dinga zama kan sallayanki kina rokon Allah...."
 Raurau ihsan tayi da idanuwa,
"Kuma dan Allah in wani abu kike Wanda mu iyayenki bamu saniba to ki bari don na tabbatar ba haka nan maneman auren ki suke ja da baya ba..." Bata idaba ihsan ta fashe da kuka tana cewa
"Yanzu mom zargina kike?..." Da sauri mom ta girgiza mata kai
"Not at all... Kawai am advising you as your mother...." Mom ta fada mata tana kama mata hannu da one hand Sannan tana goge mata tears da dayan hannun ta,
"Mom wallahi ba na mugun abu... Kuma adua am trying hard sai dai bana jure adua sosai...at times I sleep of...."
"To ki kokarta ki dinga yi....sai indai wannan matsalan bai dameki ba...." Mom ta fada in a cool voice
"Ok mom...." Tafada har lokacin bata bar kuka ba, rungume ta mom tayi tana cewa
"And kar ki sake ki biyewa duk Wanda zai nemi ki kauce hanya sanadiyan wannan matsalan.... Do you understand me?..."
"Eh mom..."


After two days ta koma normal kamar babu abinda ya faru don har lectures ta fara zuwa, daman ita ihsan a rayuwar duniya bata da aminiya kaman husna, she can share anything with her, don sau da dama tana fada mata abubuwan da bata fadawa mom.


Bayan wata daya da fasa auren ihsan wani ya fara zuwa wurin ta, family sai cewa suke tana da white blood, itakam husna abun ya fara damunta don ta san ihsan bata fita komai ba amma ko suna tare da anyi horn to ihsan suke so, daman gata good pretender bata nunawa abun yana damunta amma har cikin ranta kaman ta mutu take ji don har cewa take
"Ya zaayi best friend dita tayi aure in dinga zuwa gidansu as budurwa?...AI wallahi saidai muyi tare ko kuma in rigata..." Take fadawa kanta, yanzu kanwarta da suke har maza sun fara neman tabda aure amma ita saidai suzo mata da maganan banza.

Yau ta fito daga wanka daure da towel, gaban mirror ta tsaya tare da cire towel dinta ta tsaya yanda Allah ya halicceta tana kallon kanta, komai nata kaman ita tayiwa kanta, her figure 8 is something else komai normal amma she wonder why nobody is seeking for her hand in marriage. Wayanta ya fara ringing ta duba taga ihsan, saida ta saki tsoki Sannan tayi picking,
"Hello babe how far...." Tayi magana kaman ba ita bace tayi hissing yanzu nan.

Ihsan dake zaune kan gadonta sanye da skirt and blouse na atampa tace
"Babe guest what..."
Daga chan bangaren husna ta gallawa wayan harara tare da Jan inner hiss Sannan tace
"What..." With high tune kaman da gaske
"Could you believe Mahmoud yace zai turo?..." Inji ihsan dake magana sounding extremely happy. Daga chan bangaren idanuwa husna ta zaro, she couldn't believe her ears, jitayi as if her heart will pop her ribcage, nishi ta farayi sama2, amma dayake anamimiyace sai ta sake shewa tare ea guda tana cewa
"Babe are you serious?..." Ta fada kaman da gaske

"Hmmm babe haka yace wai ya samu aiki a American embassy so zai koma chan in the next two months kuma yanason ayi aure kafin lokacin...." Tafada sounding super duper excited, husna rike throat dinta tayi don ji tayi kuka yana Neman kufce mata, kawai saita fara cewa
"Naam... Mami gani nan zuwa...." Tafada kaman ana kiranta Sannan tayi saurin cewa
"Babe...bari in kiraki mami ke kirana...." Bata sauri amsa ihsan ba ta katse wayan ta
[10/16, 5:27 PM] Re@l Zuw@ir@t✍🏼: Dukan kasan tiles tayi kaman ance buga in baki trillions, duk yanda take dukan kasan ko kadan bata jin zafin hannun ta, tana dukan kasa tana kuka, kai kaji kaman komai ba na Allah bane
"Yanzu ina nan a kai kawata abroad kuma zaman aure...no way...." Tafada tana daukan wayanta, wani number tayi dailing after few seconds ta fara cewa
"Kaji aikin ya samu ..."
"Address and details..." Wani katon murya ya fada daga chan bangaren
"I will email you..." Ta fada tana kashe wayan ta. Mikewa tayi ta kara shiga bathroom ta sake wanka,  ta fito ta shirya cikin material lace dinki skirt da riga, bata tsaya kwalliya ba tafito, dakin mami ta shiga
"Mami ki bani kudin tp zanje gidansu ihsan..." Kallon ta mami tayi Sannan tace
"Ba kuna tare ba throughout jiya....kuma dazun kun hadu a lectures... Me zakiyi Chan gidan yanzu...." Ahankali husna tafara cewa
"Mom yanzu nan ta kirani wai wani yace zai turo shine zanje...." Ta fadi maganan tamkar babu abinda ke damunta,
"Wowwww...masha Allah... Har ta samu wani?...kai alhamdulillah..." Ta fada tana kallon eyeball din yarta, ahankali ta fara cewa
"Habibty kar ki damu...kema Allah zai kawo naki when the time is right...." Tafada Ahankali don rashin maneman auren yarta yana daga cikin babban matsalan, kuma yana daga cikin abinda take bawa malaman ta kudi saboda suyi mata aduan samun miji amma har yanzu shuru.
Kai husna ta dan kauda yanda mami yanda bazata ganta ba Sannan ta tabe baki.  Wani pause dake kan mirror maminta umarceta ta dauko mata, dauko mata tayi mami ta dauko 1k ta bata
"Ki dawo kafin magrub..."
"Ok mami..." Ta fada Sannan ta saka kudin cikin handbag dinta.
 A bangaren ihsan kam farin ciki kawai take don tafi son Mahmud kan sauran maneman aurenta, ba karamin kwanta mata yayiba,  tunda ya daukota daga school ya fada mata zai aiko Sannan ya ajiyeta ya wuce, ko mom bata fadawa ba ta shiga dakin ta ta kira husna.

Jiran kiran husna ta tsayayi har lokacin asar kasancewan yau Friday da wuri suke gama lectures, sallah tayi ta sauko,  batafi minti biyar da sauko wa ba sai ga husna, da gudu husna ta rungume ta
"Babe am extra happy..." Husna ta fada cikin farin ciki,  da sauri ihsan tace
"Shhhhhh....kar ki bari mom taji...ban fada mata ba tukunnan...you are the first person I told..." Tafada with excitement all over her. Ko mom husna bata gaida ba suka hau upstairs suka fara labartawa, murna wurin husna kaman gidansu zaa aiko ( people beware of people with two face)..

Har adua ta dingayi mat kan Allah yasa kar a fasa wannan kaman gaske, itakam ihsan sai ameen take, cikin dabara ta fada mata inda Mahmoud ke zama,  around 5:pm husna tace zata tafi, ihsan mikewa tayi don rakata, husna kallon ta tayi
"Babe ina zaki?..." Ta tambayeta kaman batasan abinda zatayi ba
"I want to escort you..." Inji ihsan, hararanta husna tayi Sannan tace
"Da wannan kayan da kika saka tun safe?..." Dariya ihsan tayi  tana cewa
"Wallahi sis tunda na dawo ko ruwa ban shaba saboda murna..." Itama husna dariya tayi tana cewa
"Sarauniyar zumudi...kije da sauri kiyi shower ki fito ki rakani...kuma wallahi in kin Dade tafiyata zanyi...." Bata idaba  ihsan ta shiga cikin bathroom da gudu
"Yanzu nan zan fito...." Husna tabi bayanta da harara Sannan tayi saurin daukan wayanta ta bude ta tura photo da wani guy da nake tunanin shine Mahmud. Komawa wurin ta tayi tana cewa
"Wallahi ki fito ko in tafiyata..." Ta fada da karfi, da sauri ihsan ta fito daure da towel, ko shafa batayi ba ta saka pant da bra Sannan  dauko wata black jallabiya ta saka tare da yafa Vail Sannan suka sauko downstairs, a falo suka tarda mom da sauran family na ihsan, gaidasu husna tayi Sannan ta wuce, fitowa sukayi suka hau kan titin street dinsu.

Adaidai lokacin Ayan ya dawo daga wajen aiki, tun daga nesa ya hango cheeks biyu sun baje kan titi kasancewan motoci basu fiya bin wurin ba saboda residential road ne
"Ji yanda wayan nan yara suka haye kan titi kaman na ubansu...." Inji Ayan dake tuki,
Yana. Zuwa kusa dasu ya fara horning, gani yayi basu da niyyan bashi hanya, kara horn yayi da karfi, gani yayi mai material tayi kokarin matsawa ita kuma mai jallabiya ta rike mata hannu alaman kar ta matsa, sai gani yayi  ta nuna mashi sauran hanyan, alokacin ihsan cewa husna tayi
"Babe rabu da ko waye.. Ba ga titi nan ba?...ko da mota goma zai wuce lokaci daya...."
"Kam...amma those gal sun raina min hankali..." Inji Ayan daya cika yayi fam, daman da frustration ya taho daga wurin aiki don yau sam bai huta ba then ga friends dinshi Wanda yake aiki waje daya dasu sun bashi haushi. Horn ya karayi kaman zai fasa masu kunne, amma hannunsu rike da juna sai tafiya suke cikin kasaita kuma abun haushi ko juyowa basu yi ba balle su kalleshi, da sauri ya tsaida motan ba tare daya rufe ta ba ya fito

Afusace ya nufesu sukam basu San yanayiba, basu ankaraba sukaji an kama
 Masu hannun, dukkan su juyowa sukayi,
"Kam uban nan...." Inji ihsan, itakam husna tsaya kallon wannan handsome face tayi don tunda take bata taba ganin black guy da yayi mata kaman wannan guy ba.
Ayan kam fuskanshi kaman bai taba dariya ba ya jasu gefen titi Sannan ya fara cewa
"Titin na gidanku?..." Yafada yana nuna su one after the other, husna kam kusan sumewa tayi saboda dadin muryan shi, sai kallon cute lips dinshi take, itakam ihsan kaman ta kashe kanta don takaici, don ta sanshi, ban hararanshi babu abinda takeyi
"To ko ba titin gidan mu bane sai akace ka kama mana hannu?..." Inji ihsan tafada afusace
"Hannun banza gareki... Ke har wani hannu gareki?... Mtwwwww stupid..." Yafada yana komawa cikin motanshi,
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: ❤💛💙🖤💚💜
KAWARTA CE SANADI
💜❤💙🖤💚💛


®zuwairat( ummu Maryam)



4⃣


Bin bayan shi tayi da harara,
"We're not stupid wallahi...." Inji ihsan cikin murya kasa2, abinka da mai healthy ears karaf sai a kunnen Ayan, juyowa yayi ya kalleta
"Ke baki da respect ko?...." Ya fada a afusace, ihsan sai kunkuni take, ita kuma husna bakinta bude kaman sakara,
"Be careful... Am not your mate....." Ya kara fada cikin fada, ihsan sai harararan kasan ido take mashi ita wai dole Dan me zai taba masu hannu
"Ba zagin ka nayi ba....cewa nayi we're not stupid...." Bata idaba ba husna ta kama mata hannu,
"Babe let's go..." Tafada muryan ta na cracking ita dole ta ga her crush, Ayan ji yayi kaman ya Zane ihsan don yasanta , at least ya ganta sau daya ko biyu gidansu wajen twins amma shine take ce mashi she's not stupid wato ta rama zagin daya yi mata kenan, kwafa yayi ya shiga motan shi afusace ya bar wajen, bayan gidan biyu yayi horn a kafor gidansu aka bude bashi gate, sai da ya juyo ya kara kallon su especially ihsan ya watsa mata disgusting look Sannan ya shiga gida, itama ihsan hararanshi tayi
"Babe waye wancan?...." Inji husna dake blushing, baki ihsan ta tabe tare dace jan tsoki
"Wansu su salma ne....Dan iska kawai...." Tafada tana hararan gate din. Husna murmushi tayi batare da ta bari ihsan ta gani,
"Wannan guy is mine..." Ta fada cikin ranta. Hiransu suka cigaba dayi har suka kai bakin babban titi amma duk hankalin husna ya tafi ga Ayan. Adaidaita suka tsaida husna ta hau, lokacin har an fara kiran magrub, da sauri take tafiya ta kusa zuwa kofar gidansu Ayan aka bude gidan, shine ya fito sai tare da Abba su da superman, sauri take, still Ayan bai bar hararanta ba , tana zuwa kusa dasu ta gaida Abba ya amsa batare data daga kai ba ta wuce da sauri don sam batason magrub ya tardata waje.


Sai da tayi sallan magrub ta sauko ta shaidawa su dad da mom abinda Mahmoud yace,shuru dukkan su sukayi don suna tsoron a koma gidan jiya,
 Sunfi minti biyar babu Wanda yace kala cikin su, chan daddy ya kalleta
"Momina... Kinsan banason abinda zai bata maki rai...." Kallon dad dinta tayi don batasan inda ya dosa ba,
"Kin tabbatar yana sonki?..." Dad ya tambayeta cikin so da kulawa, Ahankali ta gyada mashi kai alaman eh,
"To shikenan... Zamuyi bincike kanshi ..." Inji dad,murmushi ihsan tayi
"Thank you daddy..." Tafada tana rufe fuskanta, kaman cheeks dinta dad yayi kasancewan zaune take kusa da kafanshi, mom kam murmushi kawai take tana aduan Allah yasa wannan ya zama gaskiya don in har aka samu matsala wannan Karin it will ruin her.
"Go and help your siblings with their assignment..." Mom ta fada mata. Ahankali ta mike ta fita tana tafiya cikin kasaita, one thing about ihsan is she's a good cat walker don tafiyan ta na jan hankalin mai kallon ta, at times course mate dinta suna kiranta da the lady with the most beautiful steps hakan yana daga cikin abinda ke batawa husna rai, so many times zata dinga kokarin tafiya irin na ihsan amma she can never be up to her.
 Ayan kam suna dawowa daga masjid yaci abinci Sannan ya koma part dinshi ya shiga wanka, fitowa yayi daure da towel ya ya kunna kallo Sannan ya haye gado tare da daukan wayanshi, browsing ya shiga yi amma sai ya tsinci kanshi da tuna yarinyan data zageshi dazun, yasan confirm ya taba ganinta gidansu, cos ba zama yake falo ba most of the time yana part dinshi amma ya taba ganinta zata fita daga gidansu tare dasu salma, the last time daya ganta bata kai haka girma ba, ji yake inama zata shigo hannun shi for at least an hour da babu abinda zai hanashi koya mata hankali
"Hmmm she have some nerves.... Me ...stupid.... Lallai yarinya ta girma...." Yafadawa kanshi. Mikewa yayi yacigaba da abubuwan da ya saba kafin ya kwanta still daure da towel don shi ko kadan baya gajiya da daura towel, at times Umma har fada take mashi don sau da dama in zata shigo part dinshi in har batayi sallama ba da towel take tardashi, sai around ten pm ya kwanta still da towel ko boxers babu jikin shi.

The following day was Saturday so bai tafi hospital da wuriba cos bazai ajiye siblings dinshi a school ba, sai around 11am yayi breakfast ya dauki machine dinshi  motobi ya fita daga gida bayan yayi ma su Umma sallama. Yana fitowa kuma yayi daidai da lokacin da sisters dinshi tare da superman sai ihsan da nata siblings din suke dawowa daga islamiyya, don da akwai wani babban islamiyya inda suke zuwa 8am to 10:30am.
Ayan na gani siblings dinshi ya saki murmushi mai kayatar da fuskan shi, Dan rage gudun machine din yayi daya karaso kusa dasu, ihsan da salma tare da sameera suke ke baya kuma itace gefen kusa da titi,tana ganin shi tayi saurin komawa the other side, twins kallon ta sukayi
"Lafiya dai ko?..." Inji salma, kanta kasa ta saki murmushin karfin hali tare dacewa
"Ba komai... " tafada kanta kasa.
 Ayan na kallon abinda tayi don a lokacin ya karaso kusa dasu,da sauri superman yace.
"Yaya me zaka sayomin...." Yafada yana nufanshi, tsayawa yayi tare dacewa
"What do you want...."
"Sneakers..." Inji shi, shima kanin ihsan Wanda ake kira da handsome yace
"Uncle nima ka sayomin sneakers..." Ayan murmushi yayi don kana ganin yaron kasan kanin ihsan ne, siblings ihsan gaidashi sukayi suka wuce Sannan su ihsan suka karaso wurin da yake tsaye, kafin su salma su bude baki suyi magana har ihsan ta zame ta gefen su ta wuce, da sauri sameera tace
"Sis baki gaida yaya ba...." Chak ta tsaya tana niyyan juyowa Ayan ya fixge machine dinshi ya bar wurin, Allah ya taimake su titin ba mai kura bane da ya badesu da dust,twins kallon junansu sukayi Sannan suka kalli ihsan
"Sis wani Abu ya hadaki da yayane?..." Salma ta tambayeta, da sauri ihsan ta nuna kanta tare dacewa
"Ni?..."
"Eh mana...naga baki gaidashi ba kuma kin juyo ya tafi...." Inji sameera, dariya ihsan tayi Sannan tace.
"Ni ina nake ganin yaya balle wani Abu ya hadani dashi?...kawai hankalina ne bai nan...." Tafada sounding very free,
"Hmmm ko ma meye in yayi tsami munji...." Inji salma cikin daria , itama ihsan dariya tayi
"Wallahi ban dariya gareki..." Tafada tana dariya, da sauri ta kara cewa
"Sis na samu wani suitor kuma...." Da sauri salma da sameera suka kalli junansu tare da tafawa
"Wooowwwwww....we're happy for you..." Suka fada in chorus Sannan salma tace
"Allah yasa kar a fasa wannan Karin..," ahankali ihsan ta amsa da
"Ameen..." Cikin zolaya sameera tace
"Sai Mun rigaki sanin meye rayuwar aure...." Tafada tana rufe fuskanta, hararan ta ihsan da salma sukayi Sannan ihsan tace.
"AI ba sai kin rufe fuskanki ba...ki barsu bude ..." Tafada tana dariya,
"Ni zan zo gasaki...." Inji ihsan,dariya suka cigaba dayi.

Hira sukayi sosai kafin su kai kofar gidansu salma sukayi bankwana kan sai 4pm Sannan ihsan da siblings dinta suka wuce masu gidan
 Ayan kam wani irin haushi da takaici ne ya kama shi har adua yake Allah ya hada shi da wannan yarinyan inda babu kowa ya ci ubanta, duk kawayen twins ji suke dashi dukda ba time dinsu gareshi ba amma shine yarinyan da ya tabbatar ya bawa minimum of 8 years take neman raina shi
 Kuma abinda ke kara bashi haushi shine yasan tana yi mashi kallon Dan iska don ya kama mata hannu, har yanzu bai bar ganin idanuwanta a yayin da take hararanshi ba, koda ya isa wurin aiki sai da Yusuf da Mohd suka gane da akwai abinda ke damunshi, kuma koda suka tambayeshi bai boye masu ba, ya kara dacewa
"I wish I can show her some respect..." Yafada yana rolling cikin kujera ahankali, dariya Yusuf da Mohd sukayi
"In banda abinka ai wannan is normal, dan yarinya ta harareka bai kamata ya bata maka rai to such instance ba...." Inji Yusuf, hararanshi Ayan yayi
"Haka nan sai age mate din third sisters dina...." Bai idaba Mohd yace
"Second dai tunda wannan ya rasu...."
"Naji...sai yarinya da na tabbatar na bawa good fucking 8  years sai ta harareni don da kaudasu daga accident?... Da bige shegiya nayi Wallahi..." Dariya suka kara yi mashi
"There is more to this..." Inji Yusuf, hararanshi Ayan yayi
"Kodai kodai..." Inji Mohd dake dariya don ba karamin dariya Ayan yake basu ba, don ya dauki abun very serious
"Kodai kodai uwarka ko?..." Inji Ayan dake kokarin mikewa hannun shi rike da wata files, fuskanshi kaman bai taba dariya ba.
 Daman masu ganin dariyanshi sai family dinshi da friends in kuma ranshi ya baci sai a kwana biyu baa gan sakin fuskan shi ba, wani lokacin Umma ta kance mashi
"Dan Allah ka dan dinga sakin fuska ba komai zaka dinga murtuke fuska ba.


 _Two weeks later_


Ahankali time ke tafiya inda su dad sunyi enough bincike kan Mahmoud da family sa kuma baa gano wani mugun abu game da su ba hakan ya bawa dad daman fadawa ihsan ta sanar dashi ya turo, bayan sati daya ya turo mutanen shi inda suka zo da kudin neman aure.
Atakaice nan aka saka bikin su wata 2, aranan kam duk family suka dinga adua kan Allah ya kauda sharrin shaidan.

Ita dai ihsan ko ruwa ta sha sai ta fadawa KAWARTA don duk zancen da sukayi da Mahmoud sai ta fadawa husna ita kuma already husna ta mutu kan Ayan Wanda hakan yasa ta dinga shige mashi lokacin bikin su twins amma shi Ayan in zaa kashe shi baizai fadi yanda take in short duk yanmatan babu Wanda yake kallo, amma wurin dinner ya ga ihsan, kallon ta ya dingayi don ba Karamin kyau tayi mashi dukda sai yanzu ya nutsu ya kura mata ido, suna hada ido da ita ta kara galla mashi harara tayi da suka hada ido shi kuma yayi mata kallon zaki ci ubanki ne, abinka da munafuka duk husna tana kallon irin kallon da yake yiwa ihsan don ko kadan bata dauke idanuwanta daga kanshi, hakan yasa ta bawa kanta hakuri kan bazata kara bata shirin auren ihsan da Mahmud ba don ta riga ta gano the moment ihsan is around bazata samu Ayan ba.

Ita kuma ihsan ko daidai da minti daya bata taba kwana da Ayan cikin ranta ba cos her Mahmoud was all she want in a man.
While duk lokacin da Ayan ya tuna ihsan sai ranshi ya bace at the same time kuma yayi murmushi kona meye oho.
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💛💚❤🖤💙💜
KAWARTA CE SANADI
💙💜❤🖤💛💚


®zuwairat( Ummu Maryam)


5⃣


 *Friends ina baku hakuri kan yanda kukeson shiga group dina amma contact dina tayi ful* *l Kuyi hakuri kar Ku dauki abun as wulakanci pls* .


 *Masu bina private suna nema daga farko suyi hakuri* *commitment ne Duke yi min yawa* *kar suyi fushi*

 *Thanks* 💋💋

Ihsan ce zaune da Mahmoud a dakin visitors sai labarin su suke,sai lokacin na kalli Mahmoud, mutumin yana da kyau ga maganan shi mai kwantar da hankalin mai sauraro, yanzu bikinsu sauran sati two, ihsan ba karamin son shi take ba don gani take tafi sonshi fiye da sauran suitors dinta.
Hiransu suka cigaba dayi har wajen asar
 Sannan husna ta zo don yanzu kullum sai tazo gidan su ihsan ba don komai ba sai don in zata tafi taga Ayan Kuma dayake tana na zurfin ciki bata taba fadawa ihsan tanason Ayan ba , sallama ihsan tayi da  Mahmoud suka shige ciki, suna shiga falo mom ta kira ihsan ta mika mata cup din magani as usual ta amsa ta sha tana yunkurin amai, dariya kawai husna take mata, sama suka hau suka sha hiransu har lokacin da husna take tunanin Ayan ya kusa dawowa ta mike ihsan ta yafa Vail dinta suka fito.

A bangaren Ayan kam kullum kara cika yake saboda irin kallon rainin hankalin da ihsan take mashi, yanzu ya fara lura daita don yanzu kusan kullum sai ya ganta tare da wata Kuma in har ya kuskura ya hada ido daita sai ta harareshi,  kullum kara jin haushin ta yake don wani lokacin ji yake kaman ya tsaida motan ya ci ubanta,
"Who do she think she is..." Ya fadawa kanshi yana shiga street dinsu,
"Mttsssss...why am I talking about her..." Ya fadawa kanshi again sounding very restless, daga nesa ya hango su biyu as usual
"Talk of the devil...kullum yara cikin yawo cikin unguwa..." Yafadawa kanshi,

Daga nesa suka hango motanshi
"Ga dan iska chan ya taho..." Inji ihsan, hararanta husna tayi batare data barta ta ganta ba, chan kasan ranta wani irin sanyi taji data hangi motan Ayan,
"Wai babe baki mantuwa ne..." Ta fada muryan ta na cracking, kallon ta ihsan tayi
"Meyasa muryan ki yake rawa?..." Ihsan ta tambayeta,
"ba komai", ta amsa mata Sannan tacigaba dacewa
" Abu kasa wata nawa amma baki mantaba?... " inji husna,
"AI abun ne da ban haushi...haka nan ya kama mana hannu..."
"Hmmm sis AI bake kadai ya kama ma hannu ba...remember harda ni...." Baki ihsan ta tabe
"AI naga abun bai bata maki rai ba amma ni ji nake kaman inyita zabga mashi mari wallahi..."
",in your dreams..." Inji husna, ahankali suke tafiya inda shima ya taho yana tukin shi cikin natsuwa, ko kadan ba daga kanshi na don bayason abinda zai bata mashi rai a wannan yamma. Amma as he drives closer to them he became anxious,
"Kilan yau bazata harareni ba..." Yafada cikin ranshi, yana zuwa daidai da inda suke ya Dan daga kanshi ya kallesu aikam kaman tana jira ta galla mashi harara tare dacewa
"Dan iska...." Dukda Ayan baiji abinda tace ba yasan dan iska tafada cos yaga movement din lips dinta
"Kambu..." Yafada zuciyanshi na har bawa da karfi, har ya wuce su ya tsaida motan kan tsakiyan titin kasancewan hanyan ba busy road bane, ihsan na ganin ya tsaida mota ta fara sauri, husna kam juyowa tayi tana kallon shi amma kaman babu kowa wurin yake gani don hankalin shi na kan ihsan
"Ke uban me nayi maki kike zagina!...." Yafada afusace, gaban ihsan mugun faduwa ya farayi amma bata juyoba, kawai kama hannun husna tayi don su kara sauri, da sauri Ayan ya tari gabanta
"Am talking to you..." Yafada yana dungurin goshinta, da sauri ta bige mashi hannu, itakam husna kusan mutuwan tsaye tayi cos ba karamin kwarjini yake mata ba.
"Ina wuni..." Husna ta fada mashi amma ko jinta baiyiba don ya tsaya yana kallon irin courage din ihsan, kokarin wucewa ihsan ta karayi ta gefen shi still hannun ta rike dana husna yakara tare hanyan
"I said uwar me nayi maki kike zagina...." Ya Kara daka mata tsawa, Dan juye2 ihsan tayi don ganin in da maizuwa don ba karamin tsoron shi takeji ba amma street din wayam babu alaman mutane
 Bata amsa mashi ba ta kara kokarin wucewa
"I said why the fuck are you insulting me?..." Ya fada afusace, at the same time yana kara dungurin goshinta, wannan Karin daga manyan idanuwanta tayi ta kara hararanshi tana cewa
"Banso...ka bari...Wallahi in...." Bata idaba ya tsinka ta da mari, da sauri husna taja da baya, wani irin kara ihsan ta saki don tunda uwar data haifeta  bata taba jin irin azaban dataji ba
" I said ubanme nayi maki kike zagina...." Yakara daka mata tsawa,
"Haba Malam...." Husna ta fara fada
"Shut your dirty pit...." Ya dakawa husna tsawa nan take taja bakinta ta tsuke, itakam ihsan kuka ta farayi tana cewa
"Allah yaisa...Kuma sai...." Hannu ya kara dagawa tayi saurin durkusawa don ta lura da gaske yake, tana daga durkushen ta nunata da Dan yatsa ya fara cewa
"Daga yau in kika kara daga stupid eyeballs dinki kika kalleni balle ki harareni...sai na koya maki hankali.. Am not your mate...idiot..." Yana kaiwa nan ya juya, da sauri ihsan ta mike ta koma gidansu da gudu,
"Babe kiyi hakuri... Ni zan tafi tunda magrub ta gabato..." Inji husna ...." Ko sauraron ta ihsan batayi ba ta wuce Ayan da gudu ya bi bayanta da harara ita kuma husna takama hanyan bakin titi.

Kuka ihsan ta dingayi har ta kai bakin kofan gidansu, to Ayan surprise sai taga ta shiga cikin gidansu nan gabanshi ya fara faduwa don a tunanin shi gidansu zata.
 Da sauri ya shiga mota ya juya kan mota ya koma cikin gari.

Ihsan tana kuka tayi sallama kofar falon su, anci saa Umma tana zaune da Ismail, amsa sallama Umma tayi, ihsan shiga falon tayi har lokacin bata bar kuka ba
"Subhanallahi!...." Umma ta fada tana mikewa tsaye tare da nufo ihsan dake shigowa tana kuka
"Lafiya...what happen?... Me yasameki?..." Ta jero mata questions tana riketa, cikin kuka ihsan ta fara cewa.
"Yaya ne ya mareni...Kuma.... banyi mashi.... komai ba...."  Idanuwanta Umma ta zaro
"Mari!..." Tafada afusace, zaunar daita tayi ta fara goge mata hawayenta,
"Kiyi hakuri... Bari zai shigo yanzu nan... Gabanki zan rama maki...." Inji Umma dake goge mata hawaye wasu na biyo baya, sun kai minti biyar babu alaman Ayan har lokacin Umma bata bar rarrashin ihsan ba. Wayanta ta dauka tayi dailing number Ayan, Ayan dake tukin mota yaga kiran Umma ya dauki wayan yayi picking yayi sallama sounding neutral kaman bashi bane yayi laifi, Umma bata amsa sallaman shiba ta fara cewa.
"Dan ubanka kana ina?..." Murmushi Mara fitowa yayi
"Ina office Umma..."
"Kaci ubanka da office... Maza2 yanzu nan ka iso gidan nan kafin ranka ya baci ....Mara hankali kawai..." Tana kaiwa nan ta katse wayan ta, Ayan kallon wayan yayi Sannan ya kara juya kan motan yana cewa
"Kam Allah yasa ba gabanta Umma ta kirani da Mara hankali ba...yarinya ta kara jin dadin raina ni...anyway ta raina ni in gurguri kan ubanta wallahi...." Yafada yana kama hanyan gida don har yayi hanyan gidan su Yusuf.

Hakuri Umma ta dinga bawa ihsan, itakam zama tayi tana jiran zuwanshi Umma ta rama mata marinta amma bai zo ba har aka fara kiran magrub,
"Zan tafi ..." Inji ihsan cikin sanyin murya,
"Ki jira ya zo in rama maki marinki..." Inji Umma,
 Dan girgiza mata kai tayi tana mikewa, itama Umma mikewa tayi
"To Dan Allah kiyi hakuri... Dan Allah kar ki fadawa mom dinki...banason wannan ya kawo matsala tsakanin mu...pls..." Tafada ahankali, kai ihsan ta gyada mata
"To Umma.. Bazan fada mata ba..." Rungume ta Umma tayi
"Nagode kinji... I will make sure bazai kara marin wata ba balle ke..." Kai kawai ta gyada mata tayi hanyan waje, rakota Umma tayi har compound Sannan ta koma ciki, tana bude gate ta fita Ayan na karasowa kallon ta yayi tare dayi mata gwalo,
"Azzalumi..." Tafada mashi, da sauri yayi kaman zai fita daga cikin motan aikam da gudu ta bar wajen ta kama hanyan gidansu.
Dariya yayi
"At least na koya maki respect da tsoro na...idiot... " horn yayi aka bude mashi gate, Umma tsayawa tayi bata ida shiga cikin falon ba. Parking lot ya nufa yayi parking Sannan ya fito ya nufi inda Umma take tsaye,
"Good evening..." Bai idaba ta kama mashi kunne tayi part dinshi dashi, lokacin Abba na fitowa daga nashi part din
"Lafiya dai ko?..." Inji Abba, kara kawai Ayan ke saki
"Laifi yayi..." Inji Umma, dariya Abba yayi yana cewa
"Kun fi kusa...amma kiyi saurin hukuncin don ya samu jam'i ..." Inji Abba.

Tana bude kofan part dinshi ta turashi ciki, kama inda Umma ta rike tayi yana shafa wurin, yana
"Wassshhh...Wallahi zafi Umma..." Umma rufe kofan tayi Sannan ta fara cewa
"Me yar mutane tayi maka ka mareta...." Zaro idanuwa yayi kaman baisan inda Umma ta dosa ba, Umma already ta gane abinda yake niyyan cewa, hannu Umma ta daga mashi
"Don't try me..." Ta fada mashi tana kara daure fuskanta,
"Umma wallahi kusan wata uku kenan kullum in ta ganni sai ta harareni tare da kirana Dan iska just because na rike mata hannu na kaudata daga kan titi...."
"Yo in ba iskanci ba ubanme yasa ka kama mata hannu?... Wallahi ka shiga hankalin ka...tunda nake nan ban taba samun sabani da kowa ba amma shine don rashin hankali zaka mari yarinyan da aurenta sauran sati two?..."
"Kam ashe gara dana ci kaniyanta data gama dani..." Yafada cikin ranshi, Umma tacigaba dacewa
"In ba don na bata hakuri ba iyayenta na iya daukan mataki kanka don rainin hankali ne marin ya mace...wallahi ka shiga hankalin ka..."
"Am sorry...." Inji shi
"Ba wani am sorry.. Kawai kaje kayi salla kadawo kaci abinci kaje gidansu ka bata hakuri..." Idanuwa Ayan ya zaro
"In bata hakuri bayan Wanda kika bata?..." Daguwa Umma tayi mashi
"In baka son ranka ya baci do as I said..."
"Ok Umma.. Amma basan gidansu ba...." Hararanshi Umma tayi
"You are not serious..."
"Wallahi Umma bansan takamemen gidansu ba nadaisan we're neighbors..."
Gida na biyar daga wannan gidan... " Umma ta amsa mashi Sannan ta fita. Da sauri ya daura alwallah ya fita sallah.


Ihsan na shiga falo ta hangi mom da siblings dinta zaune,  itama zama zatayi
"Wai sai yanzu kika dawo daga rakiyan?..."  Inji mom
"Eh sai yanzu tasamu adaidaita..." Tayiwa mom karya
"Ni wallahi na fara gajiya da zariyar wannan aminiyar taki...." Inji  Janna kanwar ihsan, hararanta ihsan tayi
"Kar ki kara samun baki in inayin magana...." Inji ihsan
"La anty me ya samu fuskan ki...." Inji autansu Wanda suke kira da handsome
 Hararan shi tayi batare data amsa mashi ba,
"Ku tashi kuje kuyi salla h..." Inji mom da nake tunanin ba cikin yanayin salla take ba, dukkan su mikewa sukayi tare da haye upstairs, bayan kaman minti biyar sai ga ihsan ta sauko mom dake zaune falo har lokacin kallon ta tayi
"Nace go and pray...." Mom ta fada cikin fada,
"Mom nayi...." Idanuwa mom ta zaro
"Kinyi me?..."
"Sallah mommy...." Kallon haushi mom ta tsaya yi mata
"Wato ihsan har yanzu baki jin magana ta ko?.... Bana hanaki 3 minutes prayer ba?..…ke kullum in few seconds kin idar da sallah despite all the problems surrounding you.... Ke da zaki zama uwa watarana in baki saba da prayers ba me zaki yiwa yaranki...."
"Wallahi... Nayi"
"Keep quite...kinyi din ubanki?...wani irin prayer zakiyi in 3 minutes... Why bazaki nutsu ki fadawa Allah problems dinki ba...."
"AI mom bani da wata matsala...."
"Wannan yarinyan sakara ce...siblings din problems garesu da suke praying?... Look har yanzu basu sauko ba...to wallahi ki shiga hankalin ki..." 1
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💚💙💜🖤❤💛
KAWARTA CE SANADI
💜💛💚🖤❤💙


®zuwairat( ummu Maryam)



6⃣



Haka mom ta tisa ta gaba ta dinga yi mata fada kan rashin maida hankali kan aduoi tunda shine takobin mumini ihsan kam gani take bata da wata babban matsalan da zai bukaci ta kwana kan praying mat, da matsalan ta shine yanda ake fasa aurenta Kuma yanzu alhamdulillah gashi aurenta sauran sati two, batasan neman zabin Allah at all times is very important ba.


Tare Ayan da Abba suka dawo daga masjid, Abba wucewa yayi part dinshi shima ya wuce nashi karamin part, direct bathroom ya shiga yayi wanka ya fito Sannan ya saka light english wears wato black three quarters da white t-shirts.
Main part ya je ya tarda Umma da Ismail tare da Nafisat wato antymu,
"Yaya what keep you long.... Tun dazun nake jiranka kazo in baka abinci..."  Antymu ta fada kaman ita ta haifeshi kasancewan ita ke feeding dinshi, kunnuwanshi ya kama
"Sorry for keeping you waiting..." Yafada Sannan ya gaida Umma ta amsa tana hararanshi, kan dinning ya nufa antymu ta mike ta bi bayanshi, zama yayi itakuma tayi serving dinshi Sannan ta fara feeding dinshi yana ci yana yayi kasa2 da murya Sannan ya fara cewa
"Antymu kisan yarinyan nan da nake baki labarin tana zagina?..." Ya tambayeta yana bude baki tana juye mashi abinci a baki, kai ta daga tare dacewa
"Eh yaya... "
"Yau na mareta...." Bai idaba ta saki murna wai taji dadi da yayanta ya mari wacce take zagin shi
"Yauwa....haka nake so...kaga bazata kara zaginka ba...." Tafada tana mai jindadin abinda yayanta yayi
"Har kuka tayi...." Ya fada Sannan ya fara magana irin na ihsan yana cewa
" _Allah ya isa_ ...INA kara daga hannu tayi saurin durkusawa...." Dariya tayi sosai har Umma ta kallesu, tana mamakin irin shakuwan dake tsakanin abubakar da Nafisat har tunani take yanda zai kasance ranar da yayi aure ya bar gidan
"To uwayen kilibibi...kayi sauri ka tafi inda nace...." Inji Umma, karaf Nafisat tace
"Ai Umma bai koshiba tukunna... Duka spoons shabiyar yaci Kuma akalla yanacin spoon ashirin da biyu zuwa da uku...." Dariya ne ya kufce wa Ayan
"Wato kina counting spoons din abincin da nake ci?..." Da sauri tace
"Eh mana...har tuwo nasan loma nawa kakeci ka koshi..." Umma ma dariya tayi
"Kin yi ki gama...nan da 1 to 2 years aure zaiyi ya bar gidan nan.. Sai inga ta kirga loma ko spoons..." Inji Umma, marairace fuskan antymu tayi da sauri Ayan yace
"Antyna kwantar da hankalin ki...ko nayi aure tare dake zan tafi in su Umma sunki saidai in fasa auren...."
"Kayi sauri ka gama cin wannan abincin kazo ka wuce ko Kuma in fadawa Abbanku abinda kayi...." Tafada afusace
 Kallon shi antymu tayi Sannan tace
"Yaya wai ina zakane?...", Dan kara sauke muryan shi yayi yanda babu Wanda zaiji abinda zaice Sannan yace
" wai gidan yarinyan Umma tace inje in bata hakuri... "
"Cikin wannan Daren?...ko gidansu babu nisa?..." Ta jero mashi questions cikin whisper wai don kar aji hiransu,
"Ba nisa...nan neighborhood ne..." Shima ya amsa mata cikin whisper, idanuwa ta zaro
"Wacece?..." Ta tambayeshi with anxiety
"Baki santaba..."
"Ai nasan yanmatan street dinmu duka..."
"Nidai feed me in tashi ishai prayer na gabatowa..." Dan bata fuska tayi
"To shikenan tunda you are keeping secrets from me amma remember you said no secret..." Tafada kaman wata mate dinshi. Banza yayi daita yacigaba da amsan abinci daga hannun ta har ya koshi ya mike ya koma falo ya zauna kusa da Umma, hararanshi tayi
"Ka tafi mana..kodai sai na fadawa abbanku zakaje?../"
"Wallahi Umma zanje amma bari abincin danaci yayi digesting...sai inyi sallah Sannan inje...,"
"Kai kar ka raina min wayau....maza tashi!" Umma ta daka mashi tsawa ba don yasoba ya mike ya bar falon.
 Waje ya fita ya karewa quite street din ido Sannan ya fara takawa ahankali yana tafiya yana counting numbers na gidaje, a gida na biyar after nasu ya tsaya still hannuwanshi cikin aljihunshi, tsaya kallon gate din yayi yana cewa
"Allah yasa baki da rabon shan wani marin da wannan Daren cos I won't tolerate any act of stupidity..." Yafadawa kanshi, kara kallon gate din yayi har lokacin hands dinshi cikin aljihunshi, kaman ya koma gida yayiwa Umma karya yake ji amma he knows his mother too well, yasan she will definitely ask her, hannun shi na hagu ya fiddo daga cikin aljihunshi ya taka zuwa bakin gate din, ahankali ya saka hannunshi ya danyi knocking , shuru yaji babu alaman zaa bude gate din, kara knocking yayi wannan Karin da karfi, karamin kofan aka bude yaga wani tsohon mutum da gani mai gadinsu ne, dayan hannuwanshi ya fiddo yayi tare dayiwa tsohon sallama gaisawa sukayi Sannan Ayan yace
"Baba Dan Allah yarinyan gidan nan nakeson gani..." Yafada cikin natsuwa,
"To wace daga cikin su?..."Tsohon ya tambayeshi,
" wata fara mai manyan idanuwa..." Yafada yana mamakin yanda akayi ya Iya bada kwatancenta, dariya tsohon yayi
"Hajiya ihsan kenan..." Inji tsohon, Ayan kauda kanshi gefe yayi tare da dan tabe baki, tsohon juyawa yayi batare daya rufe gate din ba, Ayan dan leka cikin compound din yayi, gidan nada kyau da girma amma ko kadan bai kai nasu girma da kyau ba, komawa baya yayi ya maida hannuwanshi cikin aljihunshi.

Alokacin duk su ihsan na zaune a falo banda dad dake abuja, duk ahankalinsu na kan movie da akeyi a zee cinema, baba ne yayi sallama ya shiga falon, dukkan su maida hankalin su
 Sukayi kanshi, gaida Hajiya yayi ta amsa da sakin fuska kaman yanda ta saba, tsohon kallon ihsan yayi Sannan yace
"Hajiya karama kizo kinyi bako...." Ihsan kallon shi tayi Sannan tace
"Ni?..." Ta tambayeshi sounding surprised don tasan Mahmoud bai kara zuwa yau
"Eh...hajiyata..." Inji baba maigadi. Dariya Janna tayi tana cewa
"Ko ma waye baisan aurenki sauran two weeks bako?..." Hararanta ihsan tayi
"Baba ko zaka tambayo waye?..." Ihsan ta fada mashi don ko kadan batason missing movies din.
"Baban zai tambayo maki?...come on kije ki dubo da kanki.." Mom ta daka mata tsawa, da sauri ta mike har lokacin tana sanye da doguwar rigan shadda, kanta ba dankwali, upstairs ta tafi sai turo baki take, da sauri ta dauko Vail kawai ta yafa Sannan ta fito duk haushi ya isheta.

Ayan komawa yayi daga gefe ya maida hannuwanshi cikin aljihunshi ya tsaya batare daya shiga cikin gidan ba, tsohon ne ya dawo ya shaida mashi tana zuwa.

Few min later yaji kafan takalmi, Dan kara lekawa yayi ya gan ta taho, da sauri ya koma ya tsaya fuskan shi dauke da murmushin mugun ta,
Ihsan tsayawa kalle2 tayi taga ba kowa,
"Baba yana ina?..." Ta tambayi baba maigadi
"Yana kofar gida...." Ya amsa mata, Dan bata fuska tayi
"Ka fada mashi ya shigo mana..." Tafada tana gyara tsayuwanta, duk Ayan najin abinda
 Take cewa, kara gyara tsayawan shi yayi, da sauri baba maigadi ya leko da kai
"Dan samari ka shigo ciki...." Yafadawa Ayan, Ayan daga kanshi yayi ya kalleshi Sannan yace
"Tazo sauri nake sako zan bata...." Yafada cikin whisper don kada ihsan data kafa kunne don jin muryan mai magana taji abinda ya fada mashi. Nan ya koma ya fada mata abinda yace, kallon bakin gate din tayi Sannan ta tako ahankali zuwa bakin gate, daidai bakin gate ta tsaya ta Dan leka dakanta karaf sukayi ido hudu dashi, fuskan shi kaman bai taba dariya ba amma sai da ya daga mata gira daya, tana ganin shi ne tayi mashi wani irin dirty and disgusting look tare dacewa
"Mtssssssssss...." Don tafi seconds goma tana Jan tsokin Sannan tajuya da niyyan komawa ciki, da sauri ya fixgota waje tare da rufe mata baki don ba karamin ihu taso yi ba,
"Wa kike yiwa tsoki?..." Ya tambayeta, dukan shi ta farayi don yanda ya rike mata waist har cikin pelvic dinta take jin hannun shi, gashi babu bakin ihu,
 Kara jawota yayi daf dashi yayi saurin rufe gate da dayan hannun shi Sannan ya Kara danne bakinta yakara cewa
"Wa kike yiwa tsoki?..." Ya kara tambayan ta yana zaro mata idanuwa, hawaye tafarayi don ko numfashi da kyar takeyi,
"Kin raina ni ko?..." Ya tambayeta yana kara danne bakinta da karfi, da sauri ta girgiza mashi kai tana hawaye,
"Zan saki bakinki yanzu amma kika sake kikayi min ihu sai na cire maki hakora...nod if you understand..." Da sauri ta yi nodding kaman agama lizard, idanuwanta data gwalalo ya kalla for few seconds Sannan ya cire hannuwanshi daga jikinta, da sauri tayi niyyan komawa ciki ya kara chafko ta, tsayawa tayi har lokacin bata bar hawaye ba
"Dan Allah kayi hakuri... Bazan kara zaginka..." Tafada tana kuka
"Good.. Daman abinda nakeson ji kenan... Yanzu nazo nan ko ban zoba?..." Ya tambayeta sounding very serious
"Kazo..." Tafada tsoro na ratsata, don street dinsu da ba kowa, ihunka banza kuruwanka wofi,
"Dan Allah kayi hakuri zan tafi...."
"Kifi ruwa gudu..." Yafada yana juyawa  da niyyan tafiya, da sauri ta shiga cikin gida Sannan ta tsaya bakin gate ta kalle bayan shi ta fara cewa
"Allah yaisa mugu azzalumi... Ban yafeba...dan iska kawai Kuma ka Sani Wallahi tallahi ba tsoron ka nake...mugu... " tafada tana feeling confident saboda tana tsaye cikin gidansu, juyawa yayi ya kalleta ya saki murmushin takaici yana cewa
"Ki fito mana..." Bai idaba ta katseshi dacewa
"Ban fitowa.. Mugu..." Da matsawa kusa da gate din yayi  ta jabaya da sauri, dariya yayi Sannan yace
"Ko ranar auranki na kamaki sai naci ubanki... That is not a threat but a promise..."
"Har ka isa?... To wallahi ka bar ganin ka mareni dazun na kyale ka...to wallahi ka Kara gigin tabani sai court ta rabamu...." Dariya ya karayi
"To ki fito mana sai court din ta rabamu?..."tsoki kawai taja tare da barin gurin har lokacin gate din na bude, bayan ta Ayan yabi da kallo yayi kwafa Sannan ya tafi.

Ihsan na shiga falo bata tsaya kallon ba ta haye upstairs da gudu don batason karyan alkawarin data dauka da babu abinda zai hanata fadawa mom irin cin  mutuncin da Ayan yake yi mata.

Da sauri ta dauki wayanta tayi dailing number husna, daga chan bangaren saida husna taja wani irin tsokin haushi da tsana don tunda ta dawo take jin haushin abinda ya faru tsakanin Ayan da ihsan, ita ba Marin da Ayan yayiwa ihsan ke damunta ba sai hannun Ayan daya taba fuskan ihsan, wani irin kishi kawai takeji yanzu ji take kaman ta jawo ranar auren Mahmoud da ihsan cos she really want ihsan out of the picture.
"Babe ya kike?..ya fuskan ki hope bai tashi ba...."" Husna ta tambayeta sounding very caring, cikin kuka ihsan tafara cewa
"Babe duk Marin da wannan Mara mutunci yayi min bai isheshi ba sai da yazo har gidanmu..." Bata idaba husna ta mike zaune kasancewan kwance take tare da  katseta dacewa
"What!... Me yazoyi!..." Tafada cike da kishi, ita ihsan was thinking is out of love, cikin kuka ihsan tacigaba dacewa
"Babe har kamamin waist...." Bata idaba husna ta fashe da wani masanacin kuka,
"Allah ka kawo sati two..." Ta fada tana kuka sosai don gani take kilan Ayan son ihsan yake,
"Why did you say that?..." Ihsan ta tambayeta tana mamakin jin irin kukan da husna takeyi wani irin madacine ke fita daga cikin muryan ta
"Don kiyi aure...kafin wani abu ya faru tsakanin ki da shi...." Tafada tana kuka hannun ta daya dafe da kirjinta don ji take kaman heart dinta zai fito waje. Ihsan zata bude baki tayi magana husna tayi saurin cewa
"Babe my battery is about to die...we will see tomorrow..." Bata jira amsanta ba ta kashe wayata.  Bige kanta ta dingayi da kasa don imagining abinda ya faru tsakanin Ayan da ihsan kawai
"Me he have kiss her with his lovely lips... No...no...no...wallahi you are mine...Wallahi duk wacce tayi kokarin rabani da kai sai ya bakunci lahira cos I can't let you go..."
Aranan batayi baccin kirki ba don kuka kawai ta kwanayi.

The following day tazo gidan su ihsan kaman babu abinda ke cikin ranta, nan ihsan ta fada mata duk abinda ya faru tsakanin ta dashi amma abinka da munafuka gani take there is more to the story.

Datazo tafiya bakin gate kawai ihsan ta rakata don ko kadan bata fatan ta kara haduwa da Ayan kafin aurenta.

 Bayan kwana uku da faruwan hakan Ayan bai kara ganin ihsan ba Kuma bai damu ba don yasan har da tsoron shi ya hanata fitowa cos at times yana ganin husna ita kadai that is duk ranar da Allah yasa ya dan kalleta don even for a second bazai Iya bada description dintaba cos he don't care about her.

Kullum husna sai tazo gidan su amma ihsan bata raka waje iyakanta bakin gate.

Ayau datazo tafiya ta hangi motan Ayan
"I have to talk to you today...." Ta fadawa kanta, tana tafiya ahankali, tana zuwa daidai saitin motan shi ta dan daga mashi hannu alaman wait.
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💙💚💜🖤💛❤
KAWARTA CE SANADI
💛❤💚🖤💙💜


®zuwairat( ummu Maryam)


7⃣



Ayan dake tuki ahankali ya ga kaman ta daga mashi hannu ya tsaya amma dayake Dan duniya ne sai yayi kaman bai ganta ba, kara waving dinshi tayi yana kallonta ta wutsiyan ido amma still bai daga kai ba har yazo zai wuce ta yaji tace
"Pls excuse me..." Ta fada da karfi, bai kalleta ba ya Danyi parking gefen titi, husna jikinta sai rawa yake ta tsallaka to the other side, har lokacin Ayan bai daga kai ba saida tazo wurin bakin kofan motan Sannan tace
"Good evening..." Ta fada muryan ta na rawa, daga kai yayi ya kalleta don yaji yanda muryan ta ke cracking,
"Lafiya..." Ya amsa yana kallon gabanshi, ahankali tafara cewa
"Daman inason yi maka magana ne...." Ayan Dan tabe bakin yayi Sannan ya fara juye2
"Are you talking to me?..." Ya tambayeta, ahankali ta gyada mashi kai,
"What?..." Ya tambayeta, husna wani irin dadi takeji cikin ranta wai gata ga Ayan wuri daya, ita batason yanda muryan ta ke rawa amma she couldn't control it, don har jikinta shaking take batasan haka tsayawa kusa da masoyi yake ba.
"Daman its about my friend..." Ta fada mashi still muryan ta na rawa, daga kai yayi ya kalleta
"Wai why is your voice cracking?.." Ya tambayeta babu wasa cikin tune dinshi, murmushin karfin hali tayi don kafafunta sai rawa suke,
"Bakomai..." Ta fada cikin sanyin murya.
"Then why do you stop me...." Ya tambayeta, ta cigaba dacewa
"Daman I want to ask you to pardon my friends lack of manners...." Bata idaba Ayan ya chanza fuska tare dacewa
"Aiko ko tayi?..." Da sauri ta girgiza mata kai
"Aa...I just...."
"Please don't waste my time... Ita ta aikoki ko ke kika aiko kanki?...." Ya fada yana kokarin calming temper dinshi,
"Ba ita ta aikoni....." Bata idaba ya kara katseta dacewa
"Then why do you stop me?..." Ya fada cikin fada,
"Ba komai...."
"Ke dalla rufemin baki...wato kun maidani topic of discussion dinku ko?...in ba don gulma da iyayiba name zaki tsaida ni ?...do I look like your mate?..." Ya daka mata tsawa, husna sunkuyar da kai tayi tare da girgiza mashi kai Kuma abinda ke bata mamaki shine ko hannu zai daga ya bigeta bazata ji haushin shi ko kadan ba har in short she loves the way he nags.
"Kayi hakuri da rashin respect din kawata...."
"Keep quite... Ai da gani both of you a birds of the same feathers so you flug together...." Murmushi tayi
"Ba halin mu da..." Bata idaba ya kara katseta dacewa
"I don't bloody care...both of you can go to hell of all eternity...." Yafada cikin fada sosai
"To ka yafe mata..."
"You people should stay far away from me...Kuma ki fadawa wannan yarinyan ban fidda ran zan kamataba...if she likes she should run to China sai ranar da aka daura auranta ta tsira daga hannu na...and you don't ever stop me again...." Yana kaiwa nan ya tada motanshi,
"We're sorry..."  Tafada mashi amma bai saurareta ba yayi gaba abun shi,
 Ayan dai irin mutanen nan ne marasa daukan rainin hankali, ya iya wasa da dariya amma even he's friends knows better, ko are  hospital da kyar ayi patients da basu San halin shi ba, that is Mr fabulous kaman yanda friends dinshi suke kiranshi Sannan wasu na kiranshi da black diamond amma Sam bayason wannan sunan cos most of the time suna amfani da wannan sunan don bata mashi rai especially Yusuf da mohd.

Yanzu sauran sati daya bikin ihsan, duk hankalin family dinsu kwance tunda duk cikin ranakun aurenta babu Wanda yake kaiwa haka kafin abun ya tarwatse, husna kam yau ta dawo gidan su ihsan da zama wai har sai an gama biki zata koma gidansu, son Ayan kam kaman zai kasheta Kuma ko da wasa ba taba fadawa ihsan ba don cikin ta yafi rijiya zurfi, saidai yau natazo ihsan taga ramanta sosai sabanin jiya Kuma ba komai ya haddasa hakan ba sai rashin bacci don yau kwana tayi zaune saboda mafarkin datayi wai ihsan ta kwace mata flowern da take mutu kar so, dukda batasan maanar mafarkin ba amma tasan is not something good, aduan ta kawai Allah yasa ayi bikin ihsan lafiya Sannan tasan abinyi kan Ayan.
"Babe wai meke damunki ne kika koma haka?..." Ihsan ra tambayeta,
"Ya na koma?..." Itama ta tambayeta
"Wallahi babe naga kaman idanuwanki sun koma ciki...ko da abinda ke damunki?...ko dayake hardly kiyi sharing problem dinki dani amma ni komai nawa kin sani...." Bata idaba husna ta balla mata harara
"Yanzu kina nufin bani sharing problems dina dake?..."
"Yo eh mana...."
"Kam amma kin Iya batawa mutane rai wallahi...to ba komai yasani raman nan ba sai missing dinki...wallahi kullum dake nake kwana nake tashi,...yanzu in kun tafi abroad saidai a waya..." Raurau ihsan tayi da man idanuwa cos yanda husna tayi maganan babu mai cewa she's lying
"But babe ai ba mutuwa bace...nima wallahi Allah kadai yasan yanda nakeji muna tare for the past 18 years amma aure zai rabamu...." Ihsan tafada tana fashewa da kuka, husna tabe baki tayi Sannan ta taso ta rungume ta suka fara kuka kaman wayanda akayiwa mutuwa, ita ihsan tana kukan rabuwa da family da kawarta ita kuma husna tana kukan son Ayan da take da baisan da zamanta ba, haka suka sha kukansu su kadai cikin bedroom din ihsan Sannan suka sauko  don taya mai aiki hada kayan dinner, mom na zaune falo su Kuma suka wuce kitchen, wayan ihsan ne ya fara ringing murmushi tayi kasancewan tasan mai kiranta, picking tayi suka fara soyewansu,
"Babyna zan tafi Kaduna yanzu..." Inji Mahmoud, da sauri ihsan tace
"Da yamman nan zaka kd?...Dan Allah ka bari sai gobe...." Tafada kaman zatayi mashi
 Kuka,
"Don't worry insha Allah gobe da wuri zan dawo..."
"Yanzu fa after four...dare zaiyi kafin ka isa..." Tafada mashi cikin shagwaba, husna sai kallon ta take tana fere doyan sakwara,
"Kiyi hakuri in tafi...is important...is urgent..." Yafada mata ahankali,
"To shikenan.. Drive carefully..." Tafada cikin sanyin murya. Hira suka danyi Sannan sukayi sallama.

Around 6:00 sun gama komai suka j
 Jera abinci kan dinning,
"Babe wallahi jikina ba dadi...am feeling feverish..." Ta fada tana ajiye ruwan wanke hannu kan dinning,
"Kin ma raina mana wayau....salon kice baki cin abinci ko?...wallahi baki isaba...." Inji husna,
"No babe...kawai jikinna has suddenly becomes cool...Kuma wallahi tundazun lafiya ta lau...sanyine ya dan kamani yanzu..." Inji ihsan da duk jikinta yayi sanyi for no reason,
"Sorry... Muje muyi wanka kilan gajiyan daka sakwara ne...let's go and shower kafin su mom su sauko...." Inji husna. Daidai stairs suka ci karo da mom dake sauko tare da handsome sai mai bima Janna maisuna Aisha,
"Ina zaku Kuma?..." Ta tambayesu,
"Wanka zamuyi..." Ihsan ta amsata,
"Kuyi sauri kufito kuci abinci kafin magrub..." Inji mom. Mom na saukowa anty Zuwairat tare da wata sister mom   suka shigo, sai baba mai gadi daya fara shigowa da wasu foreign bedsheets cikin kwalin su. Mom rungume yarta tayi tana cewa
"Ai anty wannan hidiman is too much..." Anty Zuwairat banza tayi daita ta zauna kan daya daga cikin kujeran falon, baba maigadi kara komawa yayi ya shigo da wasu kayan, atakaice saida yayi kusan taki biyar yana shigo da kaya kala2, mom kam baki ta bude, don kayan are far beyond her expectations,
"Wannan shine kayan da aka saya da kudin da family suka tara..." Inji anty Zuwairat,
"Nagode..." Kawai mom ta dinga maimaitawa,
"Ina sauran yaran?..." Ta sake tambayan ta
"Suna upstairs...." Mom ta amsa mata.  Hira suka dan yi kafin dad ya shigo falon, gaisawa sukayi dasu anty Zuwairat Sannan suka hau kan dinning. Tare ihsan da Husna abinci suka ci, suna gamawa ana kiran magrub, dad da handsome suka tafi masjid, dukkan su watsewa sukayi donyi salla, bayan kowacce tayi suka dawo falo,  banda mom da su anty da suke dakinta suna magana.

Suna saukowa wayan ihsan ya fara ringing, jin mai kira yasata sakin murmushi tare dacewa
"The person I need..." Tafada kasan makoshinta Sannan tayi picking tare dayi sallama, daga chan bangaren aka amsa, muryan datajine yasata kara daga wayan daga kunnenta don tabbatar in da Mahmoud take magana, confirm number dinshi ne amma ba muryan shi ba
"Pls waye... Pls give the phone to the owner..." Tafada cikin sanyin murya, daga chan bangaren akace
"Dan Allah kece matar mai wannan number?.." Mutumin ya tambayeta,
"Tofah..." Ihsan ta fada Wanda hakan yasa dukkan su suka maida hankalin su kanta including husna,
"Eh nice waye Dan Allah?...." Tafada gabanta na faduwa Wanda ita kanta batasan dalilin hakan ba.
Daga chan bangaren aka ce
"Daman mai wannan number ne suka samu accident... Kuma Allah yayi masa cikawa...." Da sauri ihsan ta daga wayan daga kunnenta, tare da sakin murmushi, Kara maidawa tayi kunnenta Sannan tace
"Pls haram ne tsorata Muslim... Pls this is not funny...."
"No...daman number dayayi saving da mom is not going through dats why muka kira da number dayayi saving da my queen...so pls in har kin san mai number pls ki shaidawa family..." Bai idaba ta wurgar da wayan tare dacewa
"Inna lillahi waina ilaihi rajuun.!!!!.." Tafada da karfi, Sannan ta yanke, daman tunda su husna na Janna sukaji irin wayanda takeyi suka maida hankalin su kanta, tana wurgar da wayan sukayi kanta amma kafin sukai har ta sume, da gudu husna, Janna da Zainab suka karaso wajenta suna kiranta da karfi tare ihu Wanda yasa mom sa su anty Zuwairat saukowa da gudu, husna sai girgiza ihsan take amma ko motsawa batayi,
"Me ya faru!..." Mom ta tambayesu cikin tashin hankali,
"Wani ne ya kirata da number yaya Mahmoud shine...." Kuka ne yaci karfin Janna tayi shuru, da gudu anty Zuwairat ta amsheta daga hannun husna tafara girgiza ta tana kiranta amma shuru, mom cikin tashin hankali ta amshi wayan ihsan daga hannun Janna tayi dailing number Mahmoud nan aka shaida mata abinda ke faruwa, kuka tafarayi tana salati,
"Wai meke faruwa ne!..." Anty zuwairat ta tambayi mom
"Anty mahmoud ya rasu...." Nan falon gabaki daya aka fara kuka, da  sauri mom tayi dailing number dad.

Alokacin dad da Abba su Ayan tare da Ayan da handsome sai superman suna dawowa daga masjid cos most of the time tare suke dawowa, dad da Abba na gaba sai Ayan da sauran yara na bayan su, wayan dad dake cikin aljihunshi ne yafara vibrating, fiddowa yayi ya duba yaga ihsan, da bazai dauka ba amma sai ya tuna bata taba kiranshi haka na so picking yayi, cikin kuka  mom tafara cewa
"Alh dan Allah ka taho a tafi da ihsan hospital.. Mahmoud ne ya rasu..gata nan ko motsawa batayi..." Tafadi magana kaman batasan abinda take fadaba don kawai hakan maganan suka dinga fitowa daga bakinta
 "Inna lillahi waina ilaihi rajuun!..." Da dad ya fada ya maida hankalin su Abba kanshi,
"Lafiya dai ko?..." Abba ya tambayeshi,
"Suitor din yarinyan nan ne Allah yayiwa rasuwa...yanzu ance she's in a bad shape..." Dad ya amsa mashi yana sauri sosai, Ayan kallon dad yayi amma baice kala ba,
"Subhanallahi!..." Inji Abba
"Bari in yi sauri in kaita hospital..." Inji dad, da sauri Abba ya kalli Ayan Sannan yace
"Son kabi shi..if her condition is critical call ambulance..."
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💙❤💚🖤💜💛
KAWARTA CE SANADI
♥💜💛🖤💚💙


®zuwairat( ummu Maryam)


9⃣



Da sauri ya dinga cin abincin dukda baisan inda abinci ke tafiyaba. Ko rabi baiciba ya mike, ya koma falo, Umma kallon shi tayi surprisingly Sannan tace
"Son har ka koshi?...ko dan yau antymu batayi feeding dinka ba?..." Ta tambayeshi
"Umma na koshi...inason in je in duba drip din kar ruwan ya kare..."
"Ok...ya condition dinta hope is not bad..." Kai ya girgiza mata
"Kawai shock ne..she will come around..." Yafada mata.
"Ok...sai gobe ni zanshiga...."
"To Umma... Bari in tafi chan..." Tafada yana barin falon.
Part dinshi ya tafi yayi shower sai sauri yake kaman ance be early or be dead, fitowa yayi daure da towel, da sauri ya bude wardrobe ya dauko Jordan baki da blue polo, turare ya fesa Dan tsayawa yayi yana cewa
"What am I doing this for?..." Ya tambayi kanshi, sakin murmushi yayi Sannan yace
"Am always use to looking good... So is not because of anybody...." Daure fuska yayi
"Who say it is because of somebody?..." Ya tambayi kanshi, dariya yayi ya fita tare da jawo kofan.

Bakin gate yaje ya kira security dinsu
" zan fita yanzu Kuma kika sai dare sosai zan dawo...so pls kar Ku barni inyita knocking... " ya fada mashi
"To shikenan..." Mutumin ya amsa mashi Sannan yafita, da sauri ya isa gidansu ihsan yayi knocking baba maigadi ya bude mashi ya shiga, sallama yayi dad da mom suka amsa mashi, shiga yayi ahankali amma ya rasa courage din hawan sama,
"Har ka dawo?..." Dad ya tambayeshi,
"Eh..daman don Karin ruwan ya kare ..." Ya amsa mashi kanshi kasa.
"Ok...ka hau saman mana...." Dad ya fada mashi. Bai Kara cewa kalaba ya hau sama.

Da sallama ya shiga  har lokacin hannun ta cikin na anty, husna na zaune kan kujeran dressing mirror sai handsome da Janna na zauna kan gado kusa da ihsan, yana shiga husna ta mike,
"Ka zauna nan..." Banza yayi daita ya kalli ruwan da ko rabi bai kaiba, hannun ta ya kama don ganin in ruwa na zubowa normal, sai da ya gama inspecting hannun Sannan ya koma gefe yana kallon swollen lips dinta, kallon ta ya tsaya yi kaman madubi,
"Wannan guy da ya rasu ya mutu da bakin cikin rashin samunki  amatsayin matarshi..." Yafada cikin ranshi.
"Ka zauna mana...." Anty ta fada mashi tana nuna inda husna ta tashi. Zama yayi ya fiddo wayanshi ya fara lase2, husna kam kallon shi kawai take amma ko side dinta bai kallaba balle yaga irin kallon da takeyi mashi, Janna dai ta gani Kuma tana mamakin irin kallon da take yi mashi.
 Around 9:30 anty ta kori Janna da handsome suje su kwanta sai lokacin mom ta shigo tare da dad,
"Ko zaka nuna mana yanda zamu cire ya n drip din ya kare tunda time is going Kuma gobe zaka aiki..." Dad ya fadawa Ayan,
"No problem.. Zan zauna ya kare sai in tafi..." Ya amsa mashi cikin natsuwa.
Suma zama sukayi for almost an hour Sannan dad ya tafi ya kwanta har lokacin drip bai kareba, anty ce ta umarci mom ta je ta kwanta dukda bataso amma batason tayiwa yarta gardama,mikewa tayi tare dayiwa Ayan godiya tafita,
"Anty kije ki kwanta zan kula daita...." Inji husna dake son dakin ya rage daga ita sai Ayan,
"Don't worry..." Kawai anty tace mata.
Motsi ihsan tayi Wanda yasa Ayan mikewa ya dawo kusa daita, bude ido tayi, bata gani sosai don komai double take gani,
"Zan shiga....bathroom...." Ta fada,
"Ta yaya zaki shiga bathroom ga drip hannun ki?..." Anty ta fada, fuska tayi kaman zatayi kuka,
"Bari in cire mata in ta dawo sai in maida mata tunda ya kusa karewa..." Inji Ayan, ihsan Kara bude idanuwanta data lumshe tayi ta galla mashi harara, hannun ta ya kama ya cire drip. Mikewa tayi kokarin yi juwa ya dauketa da sauri Ayan ya riketa kafin anty da husna su kai gareta, kwace kanta tayi husna jitake kaman kirjinta zai fito don ba karamin haushin abinda ke faruwa takeyi ba amma she don't have a say.

Tana dawowa ta kwanta tana cewa
"Yaya Mahmoud...." Tafada tana rufe idanuwanta nan bacci ya dauketa.

Sai wajen 11:30 drip din ya kare Ayan ya cire mata yayi masu  sai dasafe ya tafi.

The following day gidan su ihsan ya cika da yn jaje wasu sai gulma suke suna cewa da gani wannan yarinyan miyagun aljanu gareta Wanda basuson tayi aure.

Tare da Abba da dad da wasu family akayi janaizan Mahmoud cos an maidoshi Kano.

Kukan ihsan kam ba kadan ba don duk yanda su anty da sauran dangi ke kokarin hanata abun cin tura yayi.

Ayan bai tashi da wuri ba koda ya tashi da gudu ya shiga wanka ya shirya cikin manyan kaya, ya tafi office bayan yayiwa Umma sallama.

Yanayin shi ya nuna yana cikin jin dadi don fuskan shi fayau kallon shi Mohd da Yusuf sukayi Sannan Mohd yace
"Fab yadai?..." Kallon shi Ayan yayi
"Ban gane yadai ba?...." Shima ya tambayeshi
"Ai munga you look happy... Ko yar mutane ka kara Mari?..." Yusuf yafada. Dariya Ayan yayi
"Not at all... Wannan yafi mari...wannan yarinyan suitor din ya rasu jiya...."
"Ayya...." Su Mohd da Yusuf suka fada in chorus, kallon haushi yayi masu tare da tabe baki Sannan yacigaba dacewa
"So she was having a little bit of nervous breakdown... So unluckily for her sai Abba yasa in je in dubata..." Dariya mugun ta yayi Sannan yacigaba dacewa
"Yanzu allura 20 zanyi mata 2 everyday for ten days..." Idanuwa suka zaro
"Allura 20 for nervous breakdown?..." Yusuf ya tambayeshi, dariya yayi
"No...na zagina ne...." Ya amsa mashi with I don't care tune
"Amma gaskiya you are wicked..." Inji Yusuf
"Ashe wicked... Ai da farko danaje I want to pity her amma sai na lura conditions din data shiga bai sa tayi taushi ba...so zan da koya mata hankali ne..."
"What if something happens to her in the process?...." Mohd ta tambayeshi
"Nothing will happen... Kawai paracetamol ne da gentamacin...."
" amma kasan too much of paracetamol is dangerous to the liver ko?..." Inji Yusuf, hararanshi Ayan yayi
"To the professional doctor ka koya min tunda kafini experience..."
"Wallahi babu wani zancen experience.. Kawai mugun ta zakayi...banza black dai..." Bai idaba Ayan ya wulla mashi wani decor dake kan table din gaban shi, da sauri Yusuf ya kauce, su biyu mikewa sukayi shima Ayan ya mike, da sauri suka kai bakin kofa
"Banza wande coal..." Inji Yusuf daya fita da gudu yana dariya, shima Mohd cewa yayi
"Sai shegen gardama kaman arnan farko...idiot black diamond... Ga bakin fuska ga bakin halin...." Kafin Ayan ya karaso inda yake har ya bar wurin da gudu, curridor Ayan ya biyosu yana cewa
"In banyi suspending dinku ba Ku kirani da shege...." Bai idaba Yusuf daya kusa fita daga curridor yace
"Daman AI shegen ne kai...black diamond kawai...." Ayan tsayawa yayi ya rike kugunshi yana jin inama yarane su Mohd da babu abinda zai hanashi dukansu, kwafa kawai yayi ya koma cikin office
 Sai daf da magrub ya dawo gida, wanka yayi ya shiga falo antymu tayi feeding dinshi as usual Sannan ya koma falo kusa da Umma dake zaune,
"Zan tafi masjid daga nan zan wuce Chan gidan inyi mata injections..." Inji Ayan
"Ok son...amma gaskiya ina tausayawa yarinyan nan...dazun danaje ta koma kaman ba ita ba..." Ayan kauda kanshi yayi gefe ya tabe baki Sannan yace
"Kyaleta Umma.. Rashin danganane...." Yafada yana mikewa, fita yayi yana rike da hannun Ismail, bakin gate suka tadda Abba suka wuce masjid bayan shi sa Ismail sun daura alwallah nan waje.

Tare da dad suka dawo gidansu ihsan lokacin few women ne zaune falo, izini dad yayi mashi ya tafi upstairs.

Ihsan na zaune kan praying mat sanye take da long hijab, idanuwanta sunyi mugun kunburi, wasu yanmata su biyar ne zaune cikin dakin Cikin su har aminiyarta husna da ganin sauran yanmatan cousins dinta ne. Ihsan ta kurawa selfie dasukayi da Mahmoud ido, dukkan su dariya suke ya sanda ya daukesu. Wasu sabon tears ne suka kara gangaro mata, sallama Ayan yayi ya shiga dakin, ahankali ta daga kanta ta kalleshi da swollen eyes dinta, kuka ta farayi tana cewa
"Banason allura,... Dan Allah kar kayimin allura..." Duk yanmatan dake dakin dariya sukayi farayi banda husna datayi mutuwan zaune don ganin heart desire dinta,, daya cewa tayi
"Wallahi sis da abun dariya kike...allura kikewa wannan kukan kaman yanka ki zaayi?..." Cikin kuka tace
"Nidai banso..." Ayan murtuke fuska yayi yaje wajen drawer  da ya ajiye drugs dinta ya dauko ya fara mixing Maganin, yana hadawa kukan ihsan da kara volume, yanmatan mikewa sukayi banda husna, tsayawa yayi kanta
"Stand up..." Ya umarceta, daga kanta tayi ta harareshi tana hawaye,
"Pls kiyi sauri ya tafi kalan baici abinci ba yazo don taimaka...." Husna bata idaba ya katseta dacewa
"Tashi mana!..." Ya fada cikin fada, ahankali ta mike tana kokarin mika mashi hannun ta, girgiza kai yayi
"Wannan bana jijiya bane...na bombom ne..." Yafada babu wasa fuskan shi, kallon shi tayi
"Gaskiya Aa...in dai bazaka yimin a hannu ba ka barshi kawai..." Tafada sounding serious, baki ya tabe
"Ok...bari in fadawa dad dinki..after all shi ya kawoni nan..." Ya fada
"Ka bari in kirawo anty Zuwairat...." Husna ta fada
"Wallahi ki bari..." Inji ihsan dake kuka  Husna bata saurareta ba ta yi hanyan kofa,da sauri ihsan tace
"Dan Allah ki dawo....zan bari..." Ta fada cikin kuka, Ayan tsaye yayi yana kallon ta haka nan sai yayi tunanin ina ma matarshi ce
"Stop it..." Yafada cikin zuciyanshi, husna dawo dakin tayi ihsan ta rungume husna ta bashi baya still tana sanye da hijab,
"Ke dalla cire hijab dinki ko so kike ni in cire maki...." Ya daka mata tsawa,  ahankali ta daga bayan hijab dinta tana kuka,  nan ya hango well shaped hips dinta sanye da skirt na less, baisan sanda yayi biting lower lip dinshi ba, dukawa yayi ya dan yi kasa da skirt  dinta white skin dinta ya bayyana, ihsan sai kuka take Ahankali ya soka mata injection ta saki ihu sai dariya ta kufce mashi
"Ke wallahi kin fiya son jikinki..."
"Ba wa wani son jiki...zalunta ta kawai kake..." Tafada cikin kuka, husna tureta tayi daga jikinta saboda haushi da kishi.

Atakaice kullum sai yazo yayi mata allura Kuma yace dole sai a bombom, Kuma kullum inyazo sai tayi mashi tsiwa Kuma one thing shine the more yana ganinta the more yana zama attached to her, ko kadan yasan bazata bashi chance ba, amma confirm he has fallen for her amma hakan bai hanashi yi mata injection na mugun ta ba. Bayan kwana 3 da rasuwan Mahmoud mami ta umarci husna data koma gida don zata aiketa Maiduguri, ba haka husna taso ba amma dole ta koma gida.

A week later around 5:30pm ihsan ta rako wata cousin sis dinta datayi visiting dinta,  suna cikin tafiya ta hango motan Ayan, da sauri ta kauda kanta gefe don ba karamin kunyan shi take jiba, horn yayi masu amma bata daga kanta ba, murmushi yayi Sannan yace
"My patient where are you going?.." Ya fada da karfi yanda zataji shi daga inda take, banza tayi dashi yakara cewa
"Patient ki koma gida ko anjuma in nazo maki injection inyi maki mai zafi..." Tana kin haka ta daga kanta ta harareshi tacigaba da tafiya shi Kuma ya wuce yana dariya
"Waye wancan?.." Inji cousin dinta,
"Rabu dashi...mugune..." Ta fada mashi, dariya cousin dinta tayi Sannan tace
"Mai white blood da alaman wancan yanason ki..." Da sauri ihsan ta kalleta ta tabe baki
"Allah ya sauwake.. Wancan azzalumi?.."
"Ai is written all over him...Allah dai ya zaba maki Wanda yafi alkhairi..."
"Ameen sis...amma banda wancan..." Dariya cousin dinta tayi tana cewa
"Nidai gani da 5 months pregnancy dina Kuma am so excited... I can't wait kiji yanda mukeji..."

Hiransu suka cigaba dayi har sis dinta ta hau adaidaita ta tafi gidanta.
 
Bayan sallan magrub yaje gidansu don bata injection sai kuka take as usual ta dafe bango tare da bashi bayanta, duk bombom dinta yayi ja saboda yanda yake tsira mata allura for the past one week, ja yayi gaskiya he can't bear hearing her cry for his wickedness anymore, juyar daita yayi tare da ajiye injection dake hannun shi,
"Yanzu let's negotiate..." Ya fada mata ahankali, Dan hararanshi tayi Sannan tace
"Wane irin negotiation?..." Ta tambayeshi tana goge hawayenta,
"Na farko kar ki kara hararata... Na biyu zan baki number ta ki kirani...if you don't zan zo gobe for more injection... Accepted?.." Ya tambayeta, shuru tayi for a moment Sannan tace
"Ni gaskiya bazan kirakaba....." Bata idaba yace
"Ok...bani ass dinki...." Da sauri tace
"Zan kiraka..." Murmushi yayi
"Dats good... Yanzu kawo phone dinki..." Ya umarceta,
"Ban fito dashiba..." Ta fada mashi kasancewan yanzu a dakin baki yake yi mata injection,
"Kije ki dauko mana...." Ba musu ta fita ta dauko wayanta tana ta tunanin manufan shi
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💙💜❤🖤💛💚
KAWARTA CE SANADI
❤💛💚🖤💙💜


®zuwairat( ummu Maryam)



8⃣

 *Fans ina godiya da sonku agareni Kuma ina baku hakuri kan yanda bana samun reply messages dinku especially my  Facebook fan, Allah ya barni tare daku, you guys are really awesome, I heart you all, thanks* 💋♥


Ayan kallon Abba yayi Sannan yayi saurin dauke kanshi, dukda haushin ihsan yakeji at that moment sai da ya tausaya mata. Dad kam sauri kawai yake Ayan da handsome da biye dashi.

Har sanda suka shiga falon ihsan bata tashi ba, babu irin jijjigan da baayi mataba amma shuru, da ka shigo falon sai kayi tunanin ta mutu don banda kuka babu abinda ke tashi ba kaman husna Wanda kukanta ya bambamta dana kowa don abinda ke ranta daban Dana sauran, da gudu dad yashigo handsome na biye dashi, da sauri ya amshe ta daga hannun anty ya fara girgiza ta yana
",momina...mommy pls don do this to me...." Sallama
 Ayan yayi ya shiga falon, da sauri husna ta daga kanta ta kalleshi, shima da sauri ya karaso ya durkusa gaban dad dake zaune kasan carpet kan ihsan kan kafanshi, hannun ta ya rike don jin vita sign nan ya samu palse,
"Pls someone should get me a cup of water..." Bai idaba husna ta mike da gudu ta dauko cup cike da ruwa ta mika mashi in the process hannun su ya hadu which husna tayi intensionally, Ayan kam bai maida hankalikanta ba so bai San abinda tayi ba, ruwa ya diba cikin tafin hannun shi ya watsa mata a fuska, ajiyan zuciya ta sauke,da sauri Ayan ya koma baya ya tsaya, ahankali ta bude idanuwanta, dad ta gani,da sauri tace
"Dad...Ku bani wayata in kira yaya Mahmoud...." Nan su Janna da mom suka kara fashewa da kuka, kallon su tayi daya bayan daya amma Allah bai bata daman ganin Ayan dake tsaye gefe ba.
"Dad why are they crying?...nasan karya suke lafiyan Mahmoud lau...kawai mom Ku bani wayata in kirashi Ku gani...." Tafada fuskan ta babu hawaye ko dai su Janna kam sai share hawaye take, wayan dad ne ya fara vibrating da sauri ihsan tace
" dad waye?.." Dad duba wayan yayi yaga uncle din Mahmoud, picking dad yayi uncle Mahmoud ya sanar dashi abinda ke faruwa
"Eh an sanar da mu..." Inji dad,
"Da gaske ne ya rasu?.." Ihsan ta tambayi dad,
"Momina kiyi hakuri...." Girgiza kanta tayi tafara murza kafafunta kasa tana kuka tare dacewa
"Wayyo yaya Mahmud ka dawo..." Tafada cikin kuka mai ratsa zuciyan mai saurare, Ayan tsaya kallon ikon Allah yayi
"If you love him so much why don't you follow him..." Yafada cikin zuciyanshi.
Kuka ta dingayi tana dirje kafafunta akasa
"Ke dalla rufewa mutane baki...an fada maki kuka akeyiwa mamaci?...." Anty ta daka mata tsawa, da sauri ta kama bakinta amma kirjinta sai up and down yake saboda yanda take kukan zuciya,
"Kaina...wayyo kaina ne ke yimin ciwo...." Tafada cikin matsanacin kuka, dad daga kai yayi ya kalli Ayan alaman pls help, husna kam kuka take amma duk hankalin ta yana kan Ayan shi Kuma baisan Allah ya ajiyeta wajenba, sai kallon gashin kan ihsan yake kasancewan kanta babu dankwali, sai kallon yanda kirjinta ke tashi yake kawai sai ya tsinci kanshi da jin haushin kukanta, husna kam sai kukan bakin ciki da haushi take
 Ahankali ya kara takawa zuwa inda take, daga idanuwa tayi ta ganshi, ita dake kuka sai ta daure fuskanta tare da watsa mashi kallon haushi batasan ya akayi ya zo gidansu ba amma ko ma meye batason shi cikin gidansu, durkusawa yayi zai taba kanta nan take tayi baya da kanta tana cewa
"Dad ni wannan ya tafi a kiramin anty sakinat,..." Bata idaba anty Zuwairat ta daka mata tsawa da
"Kar ki rainawa mutane hankali mana....kai duba and pls give her the necessary help..." Tafada Ayan, cikin jin haushin kallon da tayi mashi yasa yace
"Ku kaita dakinta...zan rubuta injections da drip a sayo sai in sa mata...." Ihsan najin injections ta kwalla ihu
"Wallahi ban so...wannan mugune....wayyo kaina Ku kiramin yaya Mahmud... Wayyo Allah na shiga uku..." Tafada cikin kuka,
"Wai bazaki rufe mana baki ba?..." Anty ta kara daka mata tsawa, shuru tsyi amma bata bar hawaye ba.
"Pls give me a paper and a pen..." Yayi directing maganan shi to Janna Wanda daya ganta yasan kanwar ihsan ce, da sauri husna ta mike itama Janna ta mike tana goge hawayen fuskan ta, school bag dinta ta dauko daga mini library dake gefen falo ta bude ta dauko pen da paper ta mika mashi. Amsa yayi ya rubuta prescription har dana zalunci, don yasan abinda ke damunta will be heal with time,
"Gashi...zaa yi mata injections 2 everyday for 10 days...." Ihun ihsan ya hanashi kara magana don sauran kadan dariya ta kufce mashi
"Wallahi mugune....karya yake...wallahi zaluntata zaiyi...."  Afusace mom ta taso ta bige mata baki sai ta kara fashewa da kuka tana kallon Ayan, irin kallon ka tausaya min amma sai ya fakaici idanuwan mutane ya kashe mata ido daya tare da sakin murmushi for just 1 second Sannan ya daure kaman bashi yayi dariya ba
"Kuma zaayi mata Karin ruwa biyu...." Ya karasa maganan shi
"Wallahi ban so...." Tafada cikin tsiwa at the same time tana kuka, dad mikewa yayi zai amshi prescription din
"In babu Wanda zai sayo bari in sayo..." Ayan ya fadawa dad ,
"Ok...bari in dauko maka kudi...." Dad ya fada yana kokarin mikewa,
"Don't worry sir..." Ayan ya fada yana fita daga falon, da sauri husna ta bishi sai da ya fita waje ta ce
"Ka kawo in sayo...ko I should follow you... In case.. Zaa bukaci wani Maganin..." Juyowa yayi ya kalleta sannan ya tabe baki ba tare dayace kala ba ya tafi,
"This girl don't know how very annoying she is...." Ya fadawa kanshi yana fita daga gidan. Gidansu ya koma ya dauki kudi da machine ya fita bayan ya shaidawa Abba da Umma, yana tuki yana dariya
"Daman na sai ranar da kikayi aure zan fidda ran cin ubanki...." Yafadawa kanshi yana dariya sosai.
Dad part dinshi ya koma ya fara shaidawa yan uwa da abokan arziki abinda ke faruwa, anty ta mikar da ihsan suka tafi dakinta tare da husna, itama Janna na biye dasu Anty ta koreta ya mom kam zamatayi nan falo tana kuka.
 Husna sai kuka take kaman ita akayiwa mutuwa,
"Ke dalla rufe mana baki muji magana..." Anty ta daka mata tsawa, itama rufe bakinta tayi amma kaman ihsan hawaye basu bar zubowa ba, ihsan sai shessheka take, gani take her world has come to an end cos har yanzu bata yarda Mahmoud is gone ba
"Somebody wake me up...from... This.. Bad dream...ya Allah kasa mafarki nake..." Tafada cikin hawaye,
"Haba daughter... Dukkan mu nan lokaci muje jira...kiyi hakuri... Allah zai kawo maki Wanda yafi alkhairi... Adua kawai zaki dinga yi mashi...kinji habibty..." Anty ta fada mata tana jawota jikinta, fashewa tayi da kuka sosai tana tuna irin hiran da sukayi dashi jiya,
"Anty my heart hurts badly... Ciwo yake min..." Tafada tana dafa kirjinta
"Sorry kinji...bari wannan doc ya dawo..." Sai lokacin ihsan ta tuna dashi, sabon kuka ta fara
"Anty banason shi...."
"Ai ba soyayya akace kiyi dashiba...checking dinki zaiyi kawai..."
"To anty lafiya ta lau ...Dan Allah..."
"Shsssss..." Anty ta fada mata, shuru tayi hawaye yacigaba da kwararowa.

Bayan dad ya gama kiran family da waya ya dawo falo ba Dade ba  Ayan yayi sallama ya shigo da ledan kayan da ya sayo.
Dad dake dafe da kanshi ya daga kai ya kalleshi Sannan ya umarci janna data kaishi dakin ihsan, bene ta hau ya bi bayan ta yana Dan Satan kallon yanda gidan take, wani kofa ra bude, ihsan daga kanta tayi daga janna da Ayan aikam sai ta fashe da kuka don ita da allura wara duka don ko kadan batason allura, yana shiga dakin ya ajiye ledan bakin gado ya dauko allura tare da wani roba na daure hannu,
"Your hand..." Ya fada mata, volume ta karawa kukanta tana kankame  Anty, hannun ta anty ta mika mashi sai ihu take, hannun ta ya rike kawai sai ya tsinci kanshi da jin wani irin abu da bai tabaji ba, daure hannu ta yayi sosai sai ihu take,
"Kai ka bi ahankali mana...." Anty ta fada mashi, banza yayi daita yacigaba da abinda yake, saida ya daure tamau Sannan ya fara neman jijiya, husna kam tamkar ta hadiye zuciya ta mutu don ko takalmin ihsan batason Ayan ya taba amma ga hannun shi cikin nata,
"Da na Sani da ban raba aurenta da previous suitors din ta ba...da yanzu tana  gidan mijinta... Never the less you are mine..." Tafada cikin ranta tana kallon keyan Ayan dake sheki saboda yanayin gyaran gashin kanshi. Cannula ya dauko,  runtse idanuwanta tayi tana kuka, tafin hannun ta ya saka cikin nashi Sannan ya tura alluran cikin vein dinta, ihu ta saki sosai kaman an figi maganan daga bakinshi sai cewa yayi
"Sorry..."
"Don't tell me sorry... Kawai ka ciremin wannan abun ..." Tafada cikin tsiwa, baisan lokacin da ya saki wani kasaitaccen murmushi ba, kallon dakin yayi yana Neman inda zai rataya drip, bag hanger ya hango ya cire dukkan bags da sauri husna ta taso tana amsa bags din daga hannun shi bag hanger din ya dauka ya kawo bakin gado yayi fixing drip Sannan ya umarceta ta kwanta, tana hawaye amma fuskan ta daure don Allah kadai yasan irin haushin shi da takeji , drip ya sa mata yayi alluran bacci cikinta. Ko minti ashirin batayiba bacci yayi gaba daita. Yana tsaye gefe yana kallon beautiful face dinta with adoration har tayi bacci, yana kallon ta husna na kallon shi, shi baisan husna tanayi ba itama ihsan batasan yanayi ba,
"Hajiya zan koma gida.. Zuwa anjuma zan dawo in cire mata...." Yafadawa anty
"Daman nan kusa kake ne?.." ta tambayeshi
"Eh..." Ya amsa mata yana ajiye sauran Maganin ta kan bedside drawer.

Fita yayi husna ta bishi,
"Ka tsaya in baka ko ruwane kasha..." Ta fada mashi tana bin bayanshi
"Tofah..." Ya fada yana juyawa don kallon ta,
"Ai you have tried.. You deserve a treat..." Ta fada mashi cikin sanyin murya kanta kasa
" thanks for the treat.. Am OK..." Ya fada yana barin wurin komawa tayi cikin dakin ihsan dake bacci Anty tana rike da hannun ta da aka sawa drip.

Direct masjid ya wuce yayi sallah Sannan ya dawo gida, yau bai tarda antymu falon Umma ba dole yayi serving kanshi yaci abinci amma to his surprise sai yaji he wants to go back and watch the drip drop to the end
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: ❤💚💛🖤💜💙
KAWARTA CE SANADI
💜💛💚🖤💙❤



®zuwairat( ummu Maryam)


1⃣0⃣




Ahankali ta karaso inda yake ya ta mika mashi wayan ya amsa ya saka mata number dinshi tare dacewa
"Yanzu gashi na saka maki...ki kirani by 9:30..." Kallon shi tayi tare da hararanshi as usual
"Oh you forgot what I told you ko?...nace ki bar hararata.." Ya fada cikin Dan bacin rai, Dan turo baki tayi tare dacewa
"Mancewa nayi..."
"Wallahi ki cigaba da mantawa ni Kuma bazan manta dayi maki injection ba..." Yafada knowing shi ne abinda zai iya scaring dinta dashi at all times,
"Now karfe nawa nace ki kirani?..." Ya tambayeta
"9:30.." Ta amsa mashi atakaice Kuma under her breath
"Banji ba..."
"9:30..."
"Good...na tafi..." Batace kala ba tabi bayanshi da harara y fito itama ta fito ta shiga falo. Direct upstairs ta nufa don tunda akayi wannan rasuwan bata zama falo always tana dakinta thinking about how short life is, har yanzu bata bar kuka ba amma ba kaman wancan lokacin ba, wayanta ta dauka tayi dailing number husna.

Husna na ce kwance kasan carpet kanta kafan wata tsohuwar mata wacce daga ganinta kasan an sha duniya, Matan fara ce da akwai wani abu kaman H a gaban goshinta daga ganinta kasan grandma dinta ce, Matan sai shafa kanta take, wayanta ne ya fara ringing ta dauka ta duba, tana ganin ihsan taja wani irin irritating tsoki ta ajiye wayan gefenta, tsohuwar kallon ta tayi
"Bazaki dauki wayan ba?..ko na sariki na ne?.." Ta tambayeta, tsoki husna ta karaja Sannan tace
"Wata yar iska ce Wallahi.. Ai kinsan ni har yanzu bani da saurayi... Duk wayanda ke zuwa are not serious..." Tafada tana sauraron wayanta dake faman ringing,
"Ki kwantar da hankalin ki..dudu shekarunki nawa?..." Husna daga kanta tayi ta kalli Matan
"20 fa...ai na isa aure Wallahi...Kuma yanzu wani nakeso amma Sam baisan da zamana ba..." Inji husna, tsohuwar kallon ta tayi Sannan tace
"Hala shiyasa kika kanjame kamar kudin guzuri?...ki kwantar da hankalin ki...don wannan ba wani abu bane..." Wayanta ne ya fara ringing Kuma ta Kara dubawa taga still ihsan ce, kaman bataso tayi picking
"Kawas ya kike?..." Daga Chan bangaren ihsan dake zaune kan gado ta amsa mata dacewa
"Ina kika ajiye wayanki na kiraki baki daga ba?..."
"Ina bathroom ne..." Tafada tana hararan wayan kaman mutum
"Ok..ya Maiduguri ya grandma?..."
"All is fine..ya injections.. Har yanzu bai bar baki ba?..." Ta tambayeta seeking for information,
"Hmm dats why na kiraki....kinsan abinda ya faru?..." Ihsan ta tambayeta, da sauri husna ta gyara zama tana cewa
"Bani insha kawas ban San abinda ya faruba..." Nan ihsan ta kwace yanda sukayi da Ayan ta fada mata without hiding anything, dafa kirjinta tayi har grandma nacewa lafiya, da sauri ta mike ta bar wurin
"Yanzu kiranshi zakiyi!...." Ta tambayeta muryan ta na rawa kaman zatayi kuka,
"Do I have a choice?..." Kuka husna ta farayi don jitayi she can't control her emotions
"Sis what happened?...." Ihsan ta tambayeta cikin tension,
"Wallahi Mahmoud na tuna...yau ne ya kamata kuyi aure amma Allah bai amince gashi har zakiyi wani saurayin... Har kin mance da Mahmoud...."
 Tafada cikin kuka sosai kaman thats the real reason, Da sauri ihsan tace
"Why are saying such?... Waye sabon saurayin...?" Tafada tana shirin kuka
"Wannan Ayan mana..."
Kuka ihsan ta farayi
"Yanzu abinda zakice kenan?... Kinsan ko zan so mutum banda wannan Dan iskan.... You don't know what I have pass through tun ranar da ya fara bani allura cikin visitors room...." Da sauri husna tace
"Wani abu yake yi maki?..." Ta tambayeta cikin tashin hankali
"Ba wani abu yake yimin ba...amma sai yace in cire hijab dina...ya dinga kallon kirjina..." Kuka sosai husna ta dingayi tana cewa
"Anya ba sonki yake?..." Bata idaba ihsan ta katse shi dacewa
"Allah ya sauwake..."
"In kika kirashi yace yanason ki fa?...what will you say?.." Da sauri ihsan tace
"Kam I will spit on him...not after the many holes he have put on my ass..." Dan sanyi husna taji cikin ranta, one thing she knows about ihsan very well is that bata karya, komai na cikin ranta fada mata take Kuma exactly the way it is,
"Ok...Dan Allah ko yace yanason ki karki amince... Mutane zasuyi tunanin bakison Mahmoud..." Dan dariya ihsan tayi tana cewa
"Kodai kina ciki ne....." Bata idaba husna ta katseta dacewa
"Cikin ina?..."
"Cikin Ayan..." Tsoki husna taja tare dacewa
"Amma kin raina min hankali...sam baiyi min ba....he don't have the quality of my ideal man..." Tafada tana shafa heart dinta don tasan confirm no Ayan no life for her,,
"Ok...anyway bari in kashe don yace 9:30 dot zan kirashi kar inyi exusting credit dina..."
"Ok.." Kawai husna tace tana katse wayanta, kwantawa tayi tana karajin Ayan cikin system dinta.

Ayan wanka yayi ya zauna daure da towel as usual ya tisa wayanshi a gaba yana jiran kiran ihsan, bai taba budurwa ba sai lokacin dayake ABU Zaria Kuma suna gamawa school suka mance da juna, amma yanzu he's realizing what true love is tunda gashi ya sa wayanshi gaba yana jiran call din mace, sai haushin kanshi yakeji da bai amshi number ta ba,    counting time ya dingayi har lokacin yayi..
Ihsan kam ba don son ranta ba ta yi dailing number dinshi, Ayan na ganin wayanshi ya kawo wuta yayi saurin daukan waya amma baiyi picking ba saida ta kusa tsinkewa Sannan yayi picking tare  dacewa
"Hello..who is this?." Yafada kaman baisan wace ba, wani irin gululu ne ya taunuke zuciyan  ihsan, batace kala ba ta katse wayanta
 Yana ganin an kashe wayan ya saki dariya tare da sake dailing number ta, ringing ya dinga yi ihsan na kallon wayan har ta tsinke bata dauka ba
"Da rabon zakisha injection gobe kenan..." Ya fadawa kanshi yana kara dailing numberta, saida ta kusa tsinke wa Sannan tayi picking Kuma batace komai ba, kaman baisan wace ba yafara cewa
"Babyna na yayi kike..." Yafada cikin sweet voice... " da sauri ihsan ta kalli wayan ta ajiye shi kan gado tare da maidawa hands free, Ayan yacigaba dacewa
"Habibty ko laifin danayi maki dazun da rana Dana zo ne kike fushi har yanzu?... Am sorry... Yanzu who is the owner of this new number?..." Yafada yana murmushi, ihsan tsoki taja tare dacewa
"Malam kace in kira Kuma da kira so sai anjuma..." Da sauri Ayan yace
"Wai kece?...to haka mukayi dake?...ai yanzu ni na kiraki...so yanzu zan kashe wayata sai ki kirani ..in Kuma ba kudi cikin wayanki I understand...." Tsoki ta kara bugawa tana cewa
"Nifa zan kashe wayata tunda na kira...."
"Kika kara yimin tsoki wallahi gobe sai nayi maki injection... Kuma kika kara cewa zaki kashe wayanki kinsan sauran..." Turo baki tayi tana hararan wayan kaman shine zaune gabanta tana son yi tsoki amma bata iyawa,
"To yanzu gani say what you want to say..bacci nakeji..." Dariya Mara sauti yayi
"Ya ajikin ki?..." Ya tambayeta cikin whisper, tabe baki tayi
"Wane jikin?...."
"Jikin ki mana? Wanda kika sha allurai sha hudu saboda shi..." Yafada yana dariyan mugun ta,
"Kai kanka kasan lafiyata lau ka zalunce ni...Kuma Allah sai ya sakamin..."
"Daga taimako sai ki fara tsinemin?...to yanzu a bar wannan maganan...kiyi hakuri in kina jin haushina kan injections din nayi maki...." Bai idaba tace
"Marin dakayimin fah?..."
"To shima kiyi hakuri..." Yayi magana kaman bashi ba, itama ihsan tsaya kallon wayan tayi cos bata taba jin muryan shi kwance haka ba,
"Kinji kiyi hakuri.. Bazan Kara ba..kinji sister...." Shuru dai tayi batace kala ba
"Say something mana...." Ahankali tace
"Na yafe injections din amma Marin sai na rama zan yafe...." Bata idaba dariya ya kufcewa Ayan
"Yanzu ihsan in ma baki fuskata sai ki mareni?....." Ya fada sounding surprised
"Ka bani ka kagani mana...ni da nake mace baka ji nauyin marina ba sai ni zanji nauyin marinka?.... Aa wallahi..." Tafada cikin fada
"Amma kin fiya fada..."
"Kai Kuma ka fiya zalunci..."
"Nidake munyi match kenan..." Baisan sanda maganan ta kufce mashi ba, da sauri ya kama bakin shi yana sauraron reply dinta,ihsan kurawa wayan ido tayi tana tunanin abinda yace amma sai tayi pretending kaman batasan abinda yace ba
"Ni zan kwanta...sai da safe...."
"Nifa na kiraki Kuma sai kice min saida safe?....gaskiya ban yarda ba...bari mu Dan kara hira kadan"
"Ni bacci nakeji..." Tafada atakaice,
"Ni bani jin bacci... Yanzu kin yafemin?...."
"No..."
"Yanzu meye mafuta?..." 
"In rama kawai..." Shuru Ayan yayi yana tunanin yanda yake da pride da ego mace ta mareshi? Amma Kuma bakinshi cewa yayi
" yanzu ki fito nima zan fito saiki rama marinki...." Yafada yana mikewa Kuma fuskan shi dauke da murmushi,
"Ka bari sai gobe yanzu bacci zanyi..."
 "Aa ki fito yanzu ko Kuma ki yafe...am on my way..." Yafada yana katse wayan. Da sauri ya saka boxer tare da jean ya dauki riga ya saka ya fito rike da wayan.

Yana kashe wayanshi ihsan ta mike zaune daga kan gado tana zaro idanuwa tare da dariya
" he's kidding right?... " ta tambayi kanta,
"Hmmm if he thinks am joking then he's wrong..." Ta fadawa kanta tana dailing number husna.

Daman tun 9:30 da ihsan ta fadawa husna zata kira Ayan taketa trying number ihsan sai taji shi busy, hankalin ta ba karamin tashi yayiba don gani take soyewa kawai suke, kuka ta farayi dataga har kusan ten minutes number ihsan busy
"Ya Allah why is his love killing me?... Is it the punishment for my offence?... Wallahi in har wannan ne sakayyar abinda nayi mata to tayi tsanani..." Tafada tana kuka Kuma hannun ta dafe da chest dinta, kara trying number ta tayi taji still busy ta kara rushewa da sabon kuka, kwantawa tayi tacigaba da trying number ta gaji don kanta ta ajiye wayan, tana ajiyewa  ya fara ringing da sauri ta dauki wayan tana ganin ihsan ta gallawa wayan harara tare dacewa tare dacewa
"Banza..." Sannan tayi picking tana cewa
"Babe har na fara bacci.. Ya dai?...." Tafada tana gyara muryan ta don kar ihsan ta gane abinda ke faruwa.
Nan ihsan ta fada mata duk hiran da sukayi dashi
"Wai har dacewa munyi matching saboda yanayin characters dinmu..." Husna sai goge hawaye kawai take amma kukan bai fitowa, ihsan ta cigaba dacewa
"Yanzu yana kan hanya zaizo in rama marina Kuma wallahi ramawa zanyi..." Ta fada tana dariya, husna hararan wayan tayi Sannan ta ce
"Kawai ki fada mashi karyazo...ki yafe mashi...ga Mahmoud is no more.. Duniya is  nothing..." Tafada kaman wata aminiyar kwarai.
" to shikenan yaci darajanki...bari in kirashi in fada mashi kar yazo..." Tafada husna bata saurareta ba ta kashe wayanta tana cigaba da kuka.

Ihsan dailing number Ayan tayi yana fara ringing yayi picking tare dacewa
"Ki fito na karaso..." Ya fada muryan shi babu wasa idanuwa ta zaro
"Ka barshi na yafe maka..." Bata idaba ya katseta dacewa
"Ke kar ki raina min wayau...ki fito wallahi gani ina jiranki..." Yafada yana katse wayan shi tare da jingina da gate don daman yana niyyan kiranta ta kirashi.

Ihsan tafi minti biyar zaune bayan ta shaidawa husna abinda yace, ji tayi kaman ta mutu ta katse wayanta kawai with out saying a word.

Mikewa tayi ta dauki praying hijab dinta ta fito lokacin falo ba kowa ta fito gidan wayam saida ta tada maigadi ya bude mata ta leka waje ta ganshi jingine da gate, fuskan shi murtuke yace
"Kifito ki rama..." Yafada babu, bata fitoba ya tace ka barshi kawai na yafe maka... " bata idaba ya fixgota waje
"Ki rama nace..."  Idanuwa ta zaro
"I said na yafe..." Tafada cikin tsiwa, tsaya kallon glowing face dinta yayi Sannan ya kama hannun ta ya dora bisa face dinshi
"Ki rama..." Yafada yana kallon eyeball dinta,
 Kokarin zare hannun ta tayi amma yaki sakin hannun ta
"Revenge..." Yafada wannan Karin muryan shi bai fitowa sosai don ba karamin effect hannun ta ke dashi kan skin dinshi ba,
"Ihsan my heart is beating ...very fast...and I think it is because of you...." Yafada kaman an fixgi maganan daga bakinshi, da sauri ta zare hannun ta daga cikin nashi dake manne kan fuskan shi ta shige gida da sauri.


❤💜♥💚💙

Masoya kuyi min hakuri zakujini shuru for at least two days insha Allah, pls don be offended.. Thanks
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💙💚❤🖤💛💜
KAWARTA CE SANADI
💚❤💙🖤💛💜


®zuwairat( ummu Maryam)




1⃣1⃣


Tana shiga ya tsaya nan yana leka ta, gani yayi da gudu ta shiga falo kaman ya bi bayanta yaji, da sauri ya dauki wayan ya fara dailing number dinta, ringing ya dingayi har karshe bata daga ba, kara calling dinta yayi still no answer. Gida ya koma yana
 Amma for the first time ya kasa bacci juye2 ya dingayi yana kara dailing number dinta amma daga baya yajita not reachable mikewa yayi ya dauro alwallah.

Ihsan na shiga ta zauna falo ta fara kuka ba komai ke sata kuka na illa da Mahmoud bai rasuba da yau tana gidanta amma shine yanzu har wicked and mean Ayan zaice he's heart is beating faster because of her, mikewa tayi ta hau sama tana kuka, tana shiga daki taji wayan ta na fama ringing da sauri ta karasa wajen taga number shi bata dauka ba har ta tsinke tana tsinkewa ta saka number dinshi a blacklist ta fara trying number husna.

Husna kam kashe wayan ta tayi don kar ihsan ta gane ta saboda ba karamin kuka ta dingayi ba har kakarta na tambayanta matsalan amma bata yarda ta fada mata gaskiyan matsalan ba.

Duk basuyi bacci ba don kowa da abinda ke damunsa, ita ihsan kukan rabuwa da Mahmoud ta dingayi don kaman yau ya rasu, ita husna kukan kishi da son Ayan Sannan da haushin ihsan shi Kuma Ayan ji yake kaman in har ihsan bata saurareshiba yana iya rasa ranshi cos ji yake she belongs to him and him alone
 Sallan nafila ya dingayi har 1am Sannan ya kwanta still dai bacci bai dauke shi ba sai around 3am.
The following day saida Umma ta zo ta ta dashi ya tafi aiki amma cewa yayi bai jin dadi so bai zuwa, kiran su Mohd yayi ya sanar da su su kula da hospital ba zaizo ba
"Lafiya dai ko?..." Mohd ya tambayeshi,
"Haka nan... Bazan zo aikiba sai yarinyan da nakeso ta amince Mani..." Ya fada in a sleepy tone, dariya Mohd yayi
"Who is the lucky gal..."
"The lady I gave 14 injections.." Yafada mashi
"You must be out of your sick mine...ka gama zaluntan yarinya Sannan ka dawo kace kana sonta?...in nice bazan amince ba..."
"To tunda you are not the one you should just zip up...kawai Kula da patients..." Yafada yana katse wayan shi. Kallon agogo yayi yaga to 11 am, mikewa yayi cikin kasala ya dauki wayan shi yayi dailing number ihsan still not reachable shuru yayi for a while Sannan ya dauki wata wayar ya saka number dinta yayi dailing sai yaji tana ringing relaxing yayi kan kujera yana jiran tayi picking
"Wato she add me to blacklist..." Yafada wayan na kunnenshi.

Itama ihsan tunda tayi sallan subhi ta koma bacci mom bata tadata ta shirya yara su tafi school ba saboda halin da take ciki, kaman a dream taji phone dinta na ringing, bata bude ido ba ta lalubi wayan da hannun ta Sannan tayi sliding yanda take receiving call ta ta kanga ga ear dinta still idanuwanta ta rufe,
"Hello..."  ta fada, Ayan najin muryan ta yasan daga bacci ta tashi shuru yayi yana sauraron yanda take numfashi
"Hello..." Ta kara fada yana bude idanuwa ahankali,
"Hello..." Shima ya fada ahankali, da sauri ihsan tayi widening idanuwanta tare da kallon fuskan wayan
"Waye?..." Tafada tana komawa zaune,
"If you switch off the phone you will be in trouble..." Yafada sounding very commanding, already ihsan ta gane shine, yacigaba dacewa
"Yanzu don na fada maki my heart is beating for you shine kika shige gida with out answering me ko?...Kuma to make matter worst kikayi adding number ta a blacklist... Kin kyauta kenan?... Laifi nayi don na fada maki am developing feelings for you?...." Yanda yake magana kasan he's angry amma daji he's trying to control his temper, ihsan shuru tayi tana sauraron ikon Allah, yacigaba dacewa
"Yanzu laifi nayi?... In laifi nayi then tell me I will apologize... Amma pls ko bani ba don't shun somebody just because they say they love you... Sam hakan is not wise...so again tell me laifi nayi?..." Ya kara tambayan ta, ihsan mamakin wannan bawan Allah take don duk cikin mazan da suke yi mata magana he seems different Sannan ta lura he is a straight forward person bashi da boye2 irin na samarin zamani he always hit the nail at the head
"I nasan you are joking..." Ta fada, hakan nan sai ta tsinci muryan ta na rawa Sannan she was looking for a saliva to swallow don faratdaya yawun bakinta ya kace which she don't know why
"Ni abokin wasan kine?..." Ya tambayeta fuskan shi daure kaman tana zaune gabanshi, itama kaman yana tsaye gaban ta sai cewa tayi
"Aa..."
"Then why zakice kinsan wasa nake...." Ya tambayeta, shuru tayi batace kala ba, shima shuru yayi for a while Sannan ya kwantar da muryan kaman bashi bane yayi nagging yanzu ya fara cewa
"Ihsan am not joking... Besides ban taba jin irin abinda nakeji ji game dakeba....am totally in love with you.... But if you don't want I will understand cos ni bazan kasance cikin masu son wacce bata son su ba...." Shuru yayi, ihsan kam mutuwan zaune tayi gani take kaman he's still joking cos shekaranjiya  dayazo yi mata injection babu irin rokon da batayi ba amma fuskan shi kaman bai taba dariya balle ya tausaya mata amma yanzu wai yana sonta this guy must be a joker ta fadawa kanta
"Pls say something don't give the silent  mode..."
"Ni me zan fada?..." Ta fada muryan ta na rawa kaman wacce bata taba magana da matured guy ba
"Tambaya ta kike?...this gal is insane...." Bai idaba ba tace
"" you should stop insulting me....gaskiya I don't like the way you talk to me... Sai kace kai ka haifeni...am not interested in the relationship... " tafada cikin tsiwa, bata idaba yace
"Ni kikewa ihu cikin kunne?....kawai don nace ina sonki sai ki  kama yimin fada?...".
" ni banyi maka fada ba...kawai I said am not interested.... " mikewa tsaye yayi .
"To shikenan... No problem... The negotiations is of so ki shirya zanzo inyi maki injection..." Yafada babu alaman wasa cikin muryan shi, Idanuwa ta zaro
 "Ikon Allah... Shikenan don kace kana sona nace banyi sai kayi min injection?... To Wallahi kazo sai na fadawa dad da mom Kuma wallahi har Umma zanzo jar gidanku in fadawa..." Yanda tayi maganan yasa Ayan dariya
"What will you tell them?..."
"Zan fada masu everything.. Zan fada masu don kace kanasona nace banyi shine kake punishing dina da allura..." Dariya Ayan ya karayi
"Your word against mine..." Yafada yana katse wayan shi, da sauri ihsan ta kara dailing number don tasan bazata iya fadawa su mom gaskiya ba kuma tasan in har yazo babu abinda zai hanashi yi mata injection, Ayan ajiye wayan yayi don da gaske yake zaije gidan amma bazaiyi mata injection ba kawai he wants to see her and confess in love to her in person, jin karan wayanshi yasa ya dawo ya duba wayan yaga number dinta murmushi yayi tare da picking
"What?..." Ya tambayeta sounding serious
"Yanzu da gaske zuwa zakayi?..."
"Wait and see mana...." Da sauri tace
"To let me think about what you said... Pls" yanda take magana ya tabbatar mashi karya take kawai she wants him off her back
"Ki bar wannan maganan kawai...sai nazo...."
"Wait..wait... Wait..." Tafada da sauri Sannan tacigaba dacewa
"Yanzu me zanyi?..." Ya gane inda ta dosa amma sai ya nuna baisani ba
"Kaman ta?.."
"I mean what should I do?... Can we renegotiate?..." Murmushi yayi amma yace
"I don't think so..."
"Pls let's renegotiate..." Tafada tana turo baki..."
"Ki bari inzo mana...then we shall see if the renegotiation is possible or not..."
"Basai kazo ba... Kawai tell me what to do..." Dariya Ayan yayi yana cewa
"AI har na kusa gama sa kaya so am in my way....and don't let me wait for you..." Yafada yana katse wayan shi.
 Daman yayi wanka so kaya kawai ya saka tare da wanka da perfumes kala2 ya fito.

Ihsan komawa tayi ta kwanta Kuma the next second ta mike ta shiga bathroom, da sauri ta sakarwa kanta shower tana tunanin maganan Ayan, tasan Ayan is among the most handsome black guys, don duk inda mai kyau yake shima zai iya shiga amma one thing she don't like about him is he is the type that always want to be in control, always commanding ,
"Hmmm ni bazaa mulkani ba Wallahi..." Tafada tana fitowa daga bathroom, mai ta shafa wayanta na ringing tana dubawa taga shine sai ta tsinci kanta tana murmushi, barin shafa man tayi ta saka doguwar Riga tare da long hijab ta dauko wayanta ta fito, a falo ta tada mom sai mai aiki dake busy da her daily activities, gaida mom tayi mom ta amsa tana kallon ta
"Inazuwa?.... " mom ta tambayeta
"Yaya Ayan ne zai bani sako..." Tafada kanta kasa, mom bata yarda da maganan ta ba
"Wane sako?..." Mom ta kara tambayan ta, kanta kasa bata amsa ba, wayan hannun tane ya fara ringing ta kalli wayan taga still shine mom tsaya kallon tayi
"Ki tafi..." Mom ta fada mata, ahankali ta taka ta bar falon, daga chan bangaren ta hango shi tsaye hannuwanshi cikin aljihunshi
"Always looking like the boss..." Tafada cikin ranta, shima kafa ta yayi da ido yana kallon her natural beauty don ko kwalli babu a fuskan ta amma she looks adorable, karasowa tayi wurin shi ta gaidashi tana da daure fuskanta,
"In baki son gaida ni ki bari mana..." Yafada yana kara kurawa lips dinta ido
"Ina injections din?...maza dauko shi in hada inyi maki zan tafi ..." Yafada kaman da gaske
 Kallon shi tayi Sannan ta sauke kanta don sai taga bata iya hada ido dashi,
"Muyi renegotiating pls... Banason injection..." Tafada kaman zatayi kuka...." Tsaya kallon ta yayi for about ten to 15 seconds Sannan yace
"Amma AI kince baki sona...so ni bazan ta kura maki ba...sai indai kin amince dani...." Daga kai tayi ta kalleshi suka hada ido da sauri ta dauke kanta,
"Ni ba haka nace ba..."
"To ya kikace?...you said you don't like me..."
"I did not say that...."
"Then what did you say?.... " shuru ta danyi Sannan tace
"Kayi hakuri... Let's just be friends... Kasan just last week suitor dina ya rasu so banyi adalci ba in har na fara soyayya..." Tafada muryan ta na rawa, Ayan kallon yanda lips dinta ke motsi kaman ba ita tayi magana ba yayi ya saki dariya
"Amma you are very funny... Kin taba ganin inda mace dana miji sukayi friendship?.... Kuma ai shi wancan daya rasu is gone and will never come so you can't because of him refuse to give other a chance... So nidai gaskiya I don't want to be your friend...I want to be a lover...a companion...somebody you can rely  one... Somebody you can share all your problems with....I want to be your life partner..." Da sauri ihsan ta kalleshi, shima kallon ta yayi yacigaba dacewa
"Yes...I mean everything I said...nasan you have pass through a lot in the hands of your suitors...from one disappointment to another amma I think all that happens because you are mine..." Kara kallon shi tayi wannan karin idanuwanta sun shiko da kwalla, shima kallon eyeball dinta yayi yacigaba dacewa
"I know you are mine....and I don't mind being married to you today.... In har kin amince..." Hawaye ne suka gangaro fuskan tayi saurin gogewa, Ayan kallon ta yake with out blinking ya cigaba dacewa
"All you have to say is yes and I will take away your sorrow..." Yafada yana kallon  idanuwanta da suka chanja launi,
"We don't know each other much... I can't accept with out knowing you..." Tafada kanta kasa, ahankali yace
"I know you... Even though my attention have not been on you for a while I know you are the kind of wife for me...and as for me...yabon kai jahilci amma am not a bad person... But still zanso ki bani dama don ki sanni...am not as bad as I look..." Yanda ya furta maganan yasa ihsan dariya
"Wai bad..." Ta fada cikin ranta,
"And why are you laughing?...." Ya tambayeta
"Nothing... Kawai I want you to give me sometime to think about it..." Marairace fuska yayi tare dacewa
"Ni wallahi sai kin fadamin yanzu...hakan nan ki hanani sukuni?..." Yafada kaman Dan karamin yaro, itadai ihsan banda dariya babu abinda takeyi
"Allah sai kin bani amsata yanzu ko in zauna nan gidan in fadawa su Abba you are holding me hostage..." Cikin dariya tace
"Right now am out of words...." Tafada tana rufe face dinta,
"Ki kalato kawai ki fadamin... Plsssssss..." Shuru tayi for a moment Sannan tace
"Na amin.....ce...." Idanuwa ya zaro
"You mean you will marry me!..." Da sauri ta girgiza kai
"Not yet...I want to know you better...."
"So we should have a relationship?..." Ahankali ta gyada mashi kai
"For how long?..." Ya Kara tambayan ta,
"For few months to come..." Da sauri ya girgiza kai yana cewa
"Aa wallahi... For at least a month..."
"A month?... Gaskiya is small..."
"Small?... Not at all.. Kinsan shekara nawa anacewa in fiddo mata?...sai yanzu na samu wacce nakeso Kuma in tsaya wasa?....not at all....yanzu zanje in breakfast... Zan dawo da yamma..." Ya fada yana dagawa daga jikin bango,
"Ok..." Sallama sukayi Ayan ya tafi, yana komawa gida ya dauki mukullin motanshi yayi wa Umma sallama data tambayeshi inda zashi cewa yayi hospital, yanda yake cikin jin dadi yasa Umma ta gane something good has happened to him.
"Pls son share  what is making you happy with me...."  Dariya Ayan yayi yana cewa
"I will Umma amma ba yanzu ba...." Yafada hankalin shi kwance.
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💛💚💙🖤💚❤
KAWARTA CE SANADI
❤💙💚🖤💜💛


®zuwairat(ummu Maryam)




1⃣2⃣



 *

 *Masoya ban gajiya da gode maku I wish I can name you one after the other amma gaskiya that is* *impossible but I want all of you to know that I love you guys so much.*


 *Dedicated to my fans* ♥♥♥
 " _Allah ya Allah... Guide me all the way to your_ _janna...ya Allah oh Allah don't let me go astray cos I need you by side I_ _wish to be close...close to you through out my life ya Allah.. Oh Allah... Be with me all the way..._" wakan Maher zain da Ayan ya dingayi kenan lokacin da yake tuki zuwa hospital, yanda yake wakan tamkar shi ya yi wakan Kuma duk Wanda ya ganshi yasan cikin farin ciki yake, wurin parking dinshi ya nufa ya yayi parking ya fito har lokacin bai bar waka ba, bai je office dinshi ba ya nufi office din Mohd lokacin ya chanja wakan zuwa
"Rabhitu billahi rabba...." Still na Maher zain, ya shiga office din yana waka sai lumshe idanuwa yake alaman yana jin dadin wakan dayake, Mohd dake rubuta wani abu cikin prescription slip ya daga kai yana kallon Ayan dake waka kaman sabon shiga mahaukaci, kallon shi Mohd ya tsaya yi for almost 40 seconds, murmushi ya saki baice kala ba ya dauki wayan shi yayi dailing number Yusuf   shikuma sai waka kawai yake hankalin shi kwance,
"Helo guy ka taho we have a case....and its serious..." Mohd ya fadawa Yusuf Sannan ya katse wayan, Ayan bai bar wakan jindadi ba har Yusuf ya shigo shikuma Mohd bai ce mashi kala ba,
"Guy lafiya?..." Yusuf daya shigo thinking is something serious ya tambayi Mohd, Mohd nuna mashi Ayan dake waka yayi sai lokacin ya lura dashi
 "Lafiya kai Kuma?..." Yusuf ya tambayi Ayan,
"Ko rashin lafiya ne ya taba maka brain..." Ya Kara tambayan shi,
"She accepted..." Shine abinda Ayan ya fada masu
"Who accepted?.." Su biyu suka dawo tambayeshi tare,
"Ihsan...ta amince min...I will soon be married..." Yafada cikin jindadi,
"Kambu...ta amince bayan duk rashin imanin da ka nuna mata?..." Yusuf ya tambayeshi, hararanshi Ayan yayi
"To Dan bakin ciki ta amince..."
"Ka bar murna wallahi don sai naje har gidansu na zugata...." Inji Mohd
"Ka dai zagowa kanka wallahi don ko chanjin fuska na gani wurin ta you will be dismissed..."inji Ayan
" kace zamu sha shagali kenan..." Inji Yusuf,
"Insha Allah... It won't take much time... Kawai all I want is for her to say yes..." Surprise look ne kwance kan fuskan su
"Kana nufin bata amince ba kake wannan iskanci?..."
"Iskanci Kuma?...ai ta amince da friendship..." Wani tsokin rainin hankali Yusuf yaja yana barin office din
"Wallahi kai banza ne...I have better things to do" yafada yana barin office din, shima Mohd mikewa yayi da prescription slip hannun shi, harara ya gallawa Ayan ya barshi nan zaune shi kadai.
 Wani irin jindadi kawai yake gani yake he can't be happy, relaxing yayi kan kujeran office din Mohd ya cigaba da wakar Maher zain.
 Ihsan na shiga tayi hanyan kitchen kiranta mom dake zaune inda ta barta tayi,ahankali ta taka ta dawo wajen mom
"Sakon me yabaki?.." Mom ta tambayeta, ihsan bata ce kala ba ta sadda kanta kasa,
"Ina sakon?.." Mom ta kara tambayan ta, ihsan shuru tayi tana tunanin ta fadawa mom? Amma sai ta yanke hukuncin ta fara fadawa aminiyarta tukunna. Ganin bata da niyyan fada mata yasa tacewa
"Kije kitchen ki hado breakfast dinki..." Mom ta umarceta, direct ta shiga kitchen tana trying number husna amma har lokacin switch off, kwai biyu ta soya Sannan ta hada tea, sliced bread ta dauko ta hada sandwich da kwan Sannan ta fito rike da plate da cup of tea, bata zauna kan dinning ba falo ta zauna tana cin abincin tana trying number husna mom dake zaune kura mata ido tayi tana kallon ta ihsan kam bata saniba ajiye wayan tayi tacigaba da breakfast amma time to time sai ta saki murmushi mom kallon ta take Kuma tasan da akwai wata a kasa cos is written all over her
"Habibty is there anything you will tell me?..." Ta tambayeta in a caring tune, ihsan daga kai tayi ta kalleta, ta Dan girgiza mata kai,
"Kinsan am your mother.. You should share all your problems and joys with me...am the only one you should confide in..." Tafada ahankali don babu abinda take so kaman ihsan ta dinga fada mata ita Kuma abinda bata saniba shine ihsan are the type that prefer sharing ideas with friend than parent.
"You can tell me anything dear..." Mom ta kara fada mata, kallon mom tayi Sannan tace
"Mom babu komai..." Tafada kanta kasa,
"To shikenan..." Mom ta fada ba don ta yarda da abinda ta ce ba.

Tana gama breakfast dauki plate da cup zata mike wayanta ya fara ringing, tana dubawa taga Ayan ne murmushi ta saki tayi hanyan kitchen rike da plate, da sauri ta shiga tayi picking, hira ya dingayi mata Kuma hiran yanda rayuwansu zai kasance tare Kuma ihsan is loving every part of the conversation, daga karshe yace
"Sugar Dan Allah ki cire number ta daga blacklist..."
"To yanzu nan zan cire..." Daga karshe sukayi sallama. Nan take ta cire shi daga blacklist tayi saving number shi da yaya Ayan.  Kara kiran number husna tayi don ji take kaman tayi flying taje Maiduguri ta labarta mata abinda ke faruwa, daga karshe text ta rubuta mata kaman haka
 _"Babe pls kina kunna wayanki pls call me...I have hot gist for you... I think am falling in love_ " ta rubuta ta tura mata.


Abangaren husna kam yanda ta ga rana haka ta ga dare inda taci kuka ta koshi Kuma ta dau aniyan ko blood sister dinta Ayan yace yanaso sai tayi Maganin ta balle wata kawar banza, sai bayan sallan subhi bacci ya dauketa Kuma ba karamin ciwon kai ta kwana dashiba.


Har 12 bata fitoba haka yasa grandma dinta ta shiga dakin da take ganinta kwance yasa ta Dan taba kafanta cikin kulawa, ahankali ta bude idonta
"Subhanallahi..." Grandma ta fada ganin yanda idanuwanta suka kumbura
"Meyasameki?..." Ta tambayeta, Dan turo baki Husna tayi Sannan tace
"Me akayi?..."
"Naga fuskan ki tayi kumburi...meke damunki..."
"Ba komai..." Ta fada mata tana kokarin mikewa
 "Ki fadamin mana...ko Kuma ki shirya ki koma tunda zuwa anjuma zaa kawowa mamanki sakon..." Ta fada, banza husna tayi daita ta mike ta dauko brush dinta tayi ta wanke bakinta ta dawo dakin
"Ga abincin ki grandma ta dawo dakin da plate of delicious traditional food. Husna bude abincin tayi ta dauko wayanta ta bude tana cin abinci, wayanta na gama budewa message din ihsan ya shigo wayanta, da sauri tabude nan taga abinda ihsan ta fada
" kam uban nan!... It should not be what am thinking... " tafada tana dailing number ihsan, ihsan na ganin kiranta tayi saurin picking
"Babe what happened to your phone... I have been trying your number all morning..." Tafada with exaggeration feeling eager to tell her everything, baki ihsan ta tabe Sannan tace
"Battery dina ne ya mutu yanzu ma babu chargi sosai... So meke faruwa?..."  Ahankali tace
"Ayan said he loves me!..." Dan take husna ta dafe kirjinta, wasu zafafan hawaye ne suka fara gangaro mata, ture abincin gabanta tayi gefe
"Kuma I think I love him too...." Ihsan ta fada mata, nan take husna ta kashe wayan ta ta fara ihu tana dafe da kirjinta, da gudu grandma ta taho dakin, husna ta gani kwance kasa tana ihu tana buga kafafunta kasa hannuwanta biyu kan chest dinta
"Wayyo Allah nashiga uku..." Ta dinga fada kaman sabon shigan mahaukaciya
"Lafiya?.." Grandma ta tambayeta,
"Wallahi ta amshe min Wanda nakeso...wallahi grandma do something before I die...Wallahi ban taba son kowa kaman yanda nake sonshi ba shine zata kwace min shi..." Tafada cikin ihu, wayanta ne ya fara ringing tayi saurin daukan wayan ta kashe ta gabaki daya.
"Ke ki nutsu ki fada min abinda ke faruwa..." Inji grandma, cikin kuka husna ta fada mata komai game da yanda take jin in babun ayan babu rayuwa.
"Kin kwantar da hankalin ki..." Inji grandma, husna kuka ta cigaba dayi
"Maza ki gama cin abincin muje wurin Wanda zai hadawa mamanki sako..." Inji grandma, da sauri husna tace
"Granny na koshi...Dan Allah muje yanzu..." Tafadawa grandma, mikewa su biyu sukayi, ko wanka husna batayiba ta dauko wata doguwar gown ta saka ta dauko Vail ta yafa.
Itama grandma kaya jikinta ta sake ta dauko hijab ta saka suka fita.
 Cikin gari suka shiga, hanyan wani kauye suka kama dake shatan taxi sukayi, wani karami kauye suka shiga husna sai kalle2 take don bata taba ganin such a small rural area irin wannan ba, grandma tayiwa mai taxi umarni daya tsaya, fitowa sukayi grandma tana baya ita na biye daita, gaban wani hut ta tsaya ta fara kwala sallama, muryan wani katon ne ya yayi masu izinin shigowa. Shiga sukayi babu komai wurin sai tabarma da kayan aiki.
"Lafiya na ganku?...bana fada maki sai gobe zan aiko da abunba?..." Inji wannan mutumin,
"AI ba wannan tafiyan bane...wani abune daban ya kawoni....wannan yarinyan..." Ta nuna husna Sannan tacigaba dacewa
"Jika tace...to wani take so shi baisonta...asalima baisan da zamanta ba...Kuma wani abun haushin aminiyarta ta kutdakut zata kwace mata Wanda take so...Kuma kai kasani duk abinda mukeso muddin da akwai ka bani da case...don haka ka fada mana abinyi.. " saida tayi shuru Sannan mutumin ya daga kai ya kalli husna data kame waje daya don tunda take raka maminta wajen malamai bata taba ganin irin wannan ba don shi kanshi tsoro yake bata,
"Ke yarinya me kikeso ayi maki?..." Ya tambayeta, haka nan sai husna ta rasa bakin magana
"Kinason a kashe wannan aminiyarki?..." Da sauri husna ta girgiza kai
"To me kikeso?..." Yafada yana zaro idanuwa, muryan ta narawa don bata taba bata auren ihsan da asiri ba kawai makirci take hadawa Wanda kesa menamimin aurenta su fasa
"Kawai... Inason....ya...soni....ni kadai...." Yafada jikinta na karma, dariya mutumin yayi, chanting ya farayi for a while Sannan ya saka hannu cikin wani tulu dake hayaki ya dauki kullin Magani ya mikawa husna
"Gashi....ki tabbatar ki saka mashi cikin abinci ko abunsha kafin nan da sati daya...in har hakan ya yuwu to babu shi ba wata saike koda kuwa bayan ranki ne bai kara ganin kowa sai ke" Idanuwa husna ta zaro
"Ni ina zan ganshi har in bashi abinci?..." Tafada gabanta na dukan uku2 ( hmmm bad things always make us restless... Gwanda ka rike Allah ka samu kwanciyan hankali)
"Wannan matsalarki..." Inji mutumin,
"In ya wuce sati daya me zai faru?..." Grandma ta tambayeshi
"Maganin zai lalace..." Ya amsa mata a takaice, hannu grandma ta da ta dauko kudi daga cikin bag dinta ta mika mashi, itadai husna tasan is a lost course saboda ko kadan tasan babu inda zasu hadu da Ayan balle ta bashi abinci ko abinsha,
"Kina Iya komawa gidansu ihsan da zama har ki samu b abinda kike so...never the less I will not give up until Ayan becomes mine...." Tafada cikin ranta, hanyan gida suka kama husna na lafe jikin grandma ta daga kanta ta kalleta
"Granny.. Pls kar ki fadawa mami munzo nan...."
"Wannan ba matsala bane..." Ta amsa mata tana shafa kanta.


Itakam sakarar ihsan koda husna ta kashe wayan ta bata dauki wani abuba kawai tunanin ta tunda ta fada mata bata da battery kilan wayan ta ne ya kara mutuwa kunsan abinka da masu positive mind.
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💚❤💙🖤💜💛
KAWARTA CE SANADI
💙💛❤🖤💜💚


®zuwairat( ummu Maryam)


1⃣3⃣




Tun ranan husna ta kimsa kayanta tana jiran akawo sakon maminta ta dawo Kano saida ta kimsa kanta ta gama plan din komai Sannan ta bude wayanta takira ihsan alokacin taji wayanta busy da alaman waya take tasan confirm da Ayan take waya don tafi hour tana trying amma busy
"All this will soon stop... Is a matter of time...." Tafada with confidence don tasan abinda aka bata zaiyi aiki cos takanji mami da bawa aminanta labarin mai kankat Maiduguri, zama tayi tana imagining yanda koma zai kasance bayan ta samu Ayan.

Ayan kam through out ranar banda shiririta babu abinda yake, sunan yaje aiki ne kawai amma babu abinda  ya sinana, su Mohd da Yusuf da sauran nurses din sukayi aiki Kuma duk Wanda ya ganshi yasan yana cikin jindadi da farin ciki.

Da wuri ya dawo gida yayi wanka ya saka shadda fari tas ya je wurin Umma antymu tayi feeding dinshi as usual Sannan ya tafi masjid tare da Ismail kasancewan Abba yayi tafiya.

Yana dawowa ya zauna wajen Umma, Umma kallon shi tayi
"Son wannan kamshin haka inazuwa?..." Ta tambayeshi, murmushi yayi Sannan yace
"Umma zance zani...." Dariya Umma tayi don ba karamin dadi tajiba, da sauri antymu dake zaune Dan nesa dashi tace
"Yaya wurin wa zakaje zancen?...."
"Wurin budurwa ta..." Ya amsa mata,
"Kai rabu daita...tell me is she someone I know?..." Inji Umma, dariya yayi kawai tare da daga mata gira, da matsawa tayi da kanta kusa dashi Sannan tace
"Wacece?...." Lumshe idanuwa kawai yayi batare dayace kala ba. Su nan zaune ya mike ya
"Umma zan tafi masjid... Daga nan zan wuce inda na fada maki..." Ya fada, murmushin jindadi Umma tayi
"Allah yab tsare min kai..." Inji Umma
"Ameen.... Momcy" ya fada  Sannan ya fita. Yan fitowa daga masjid ya kama hanyan gida sai sauri yake kaman ance be early or be square,yana dab da zuwa gidan ya kirata.


Tunda tayi sallan magrub tayi wanka tafito daure da alwallah, mai ta shafa ta yi kwalliya ta shirya Sannan tayi sallan ishai ta sauko falo, kallon ta mom da siblings dinta sukayi,
"Sis wannan kwalliyan haka?... Ko kina expecting wani ne?..." Janna ta fada cikin zolaya, wani irin harara ta bita dashi tana cewa
"Kinga am not your mate...kifita ido na in rufe..." Tafada cikin fada
"To sarauniyar son girma..." Inji Janna, bata dade da zama ba wayanta ya fara ringing daman ta San da zuwanshi,
"Mom zanje wajen yaya Ayan in amso sako..." Tafada mom, kai kawai mom ta daga mata alaman OK Sannan ta fita.
 Janna kallon mamaki ta zauna yiwa yayarta don ta san confirm husna na son shi cos kallon dataga tana yi mashi last time ba kallon haka nan bane,
"May is not something personal..." Ta fada cikin ranta.

Ayan da ihsan hira sukasha inda the more minutes they spend with each other the more they feel attached to one another, ihsan tayi mamakin yanda akayi ya shiga ranta farat daya, she can believe she has fallen for the mugu azzalumi Ayan.

Har ten bai tafiba hamma tayi
"Feeling sleepy already?..." Ya tambayeta yana kallon yanda take lumshe idanuwa,
"Eh..."
"What are your plans for tomorrow in Allah ya kaimu?..." Shuru tayi kaman mai tunani Sannan tace
"Nothing much... Kawai zanje lectures by 10 to 3pm..."
"I will drop you... Kuma I will bring you back..." Dariya tayi
"Aikin fa?..."
"Don't worry about that, yanzu  I will be your driver... Duk inda zaki I will take you... Call me at anytime.. Am all yours..." Ihsan lumshe idanuwa tayi tana murmushi cikin ranta tana aduan Allah yasa he belongs to her don she can be without him, mikewa yayi itama ta mike yana gaba tana biyedashi, har bakin gate,
"Sai da safe..." Ta fada mashi don bata da niyyan binshi waje, juyowa yayi
"Gaskiya sai kin rakani waje...ni wallahi tsoro nakeji..." Dariya tayi shima dariya yayi fita yayi waje itama ta Dan biyoshi waje amma bata bar bakin gate dinba, kaman yana jira ya jawota jikin shi, idanuwa ta zaro, kugunta ya rike da two hands dinshi kaman yana measuring fadin waist dinta,
"I don't know what I will do with you when you are completely mine...but am sure is going to be fun..." Da sauri ta Dan janye hannun shi daga jikinta
"Gaskiya banso...kar ka kara..." Tafada babu wasa muryan ta, murmushi yayi
"Bazan karaba...daman I want to know if your waist can carry..." Bai idaba yayi shuru, bata kalleshi ba ta shige cikin gida shima ya tafi yana waigota, hannuwanshi ya bude kan titi da ba kowa babu motsin komai, tafiya yake amma hannuwanshi bude idanuwanshi lumshe,
"Alhamdulillah..." Kawai yake maimaitawa har ya kai gida.

Ihsan na shiga falo taga ba kowa sai Janna dake kallo, tana shigowa tayi saurin kallon ta,
"Sis pls I want to ask you something..." Tafada in a serious tune, Dan bata rai ihsan tayi
"What?.." Ta fada a takaice,
"Sis Dan Allah ki zauna muyi wata magana?..." Janna ta kara fada mata,
 Kallon ta ihsan tayi from head to toe irin kallon ke wacece da zaki ce in zauna muyi magana ta dingayi mata
"Sis Wallahi serious talk zamuyi..." Janna ta kara fada, ahankali ihsan ta zauna ba don taso ba, Janna zama tayi kusa daita Sannan tace
"Sis Dan Allah nasan kina da temper amma karkiji haushin tambayan da zanyi maki..." Tsaya kallon ta ihsan tayi tacigaba dacewa
"Pls meye tsakanin ki da yayansu anty salma?..." Tambayan Janna yasa sakin baki tana kallon ta, tasan Janna is no more a child amma da akwai good four years between them
"Wane irin tambaya ne wannan?..." Ihsan ta fada sounding upsetting,
"Sis dan Allah kiyi hakuri ki bani amsa...I have my reasons..."
"Sona yake...hankalin ki ya kwanta?..." Ta fada tana kokarin mikewa, da sauri itama janna ta mike
"Sis ba saurayin yaya husna bane?..." Ta tambayi ihsan, wani irin kallo tayi mata
"Kin taba ganin inda kawaye sukayi sharing saurayi?... Amma baki da hankali Wallahi..." Inji ihsan da ta kama hanya upstairs, bin bayan ta Janna tayi
"Wallahi sis in har ba saurayin yaya husna bace am sure tana sonshi..." Da sauri ihsan ta juyo tana kallon Janna,
"Look at this silly gal...what do you know about love?... Besides why did you say that?.." Ta tambayeta cikin daga murya,
"Sis kar ki so kiga irin kallon da takeyi mashi ranar da yazo yi maki Karin ruwa..." Bata idaba ihsan ta daga mata hannu tare dacewa
"Come on shut up... Stop mingling in my affairs... Nasan baki son husna but don't you ever tell me bad about her..." Janna shuru tayi ihsan tacigaba da balbaleta da fada Kuma cikin harsh voice Wanda yasa mom dake sanye da rigan bacci saukowa kasa,
"Lafiya kuke yiwa mutane ihu cikin Daren nan?.." Mom ta fada cikin fada,
"Mommy don na fadawa anty cewa husna tana son yayansu anty salma shine take yimin fada..." Mom kallon mamaki tayi wa Janna,
"What are your reasons for saying such?..." Mom ta tambayeta, Janna zata bude baki tayi magana ihsan ta fara cewa
"Mommy ki fada mata ta fita harkata....Wallahi in bata bariba ranta zaiyi mugun bacci..."
"Yimin shuru..." Mom ta daka mata tsawa, Sannan tacigaba dacewa
"She's your sis...what ever she say or do is for your interest..." Mom ta fada wa ihsan,
"Nidai banso...ta fita harkata..." Inji ihsan Sannan ta hau upstairs ta barsu nan tsaye, mom da Janna bin bayan ta sukayi da kallo,
"Wallahi mommy I know husna tanason..."
"Keep quite... what do you know about love..." Mom ta daka mata tsawa,
"Maza ki kashe electronic ki hau upstairs..." Mom tafada tana komawa sama.

Ihsan cire kayanta tayi ta kwanta kan gado daga ita sai bra da pant, sai tunanin maganan kanwar ta take
"What if Janna is right?..." Ta tambayi kanta, da sauri ta girgiza kanta
"I know husna won't hide it from me...zata fadamin in har tana son Ayan..." Firgita tayi da karan wayanta cos she was lost in thought, tana ganin husna ce tayi saurin picking
"Haba babe.. Meke faruwa ne?.. Dazun bamu gama wayaba kika kashe sin then I have been trying your number..." Daga Chan bangaren husna tace
"Kiyi hakuri sis...wallahi wannan shegen infinix din is giving me tough time...kashe kanta take Kuma yanzu the battery is no more strong bai rike charji sosai..." Tayi mata karya,
"Daman I thought so..."
"Dazun kina bani labari mai dadi ..."
"Kedai bari...wallahi sis nayi heart desire...Ayan is my everything.
." nan ta fara bata labari abinda ke faruwa tsakanin ta da Ayan, yanda husna ta dinga fada yasa ta kauda
 Tunanin ko tanason Ayan, she gave her hundred percent support, Wanda in ba Wanda Allah yasa ba bazaka taba sanin she's a green snake under a green grass,
"Kice zamu sha shagali kwanan nan...kinsan babe kar kiyi wasting time.. Kawai ki aminiyan bakin ciki suji kunya..." Tafada mata amma cikin ranta tana cewa
"Not while am a life...." Hira sukayi har wajen 11 inda husna ta shaida mata zata dawo gobe Kuma zatazo gidansu the next day.


Kaman yanda Ayan ya fada wace gari shi ya kai ihsan school Kuma lokacin tashi ya maidota gida su Mohd sai fada suke don har cewa suke sai sun hadashi da Abba tunda yanzu bai aiki sai shiririta kaman kanshi farau soyayya. Ko kallo basu isheshi ba balle ya tamka masu. Mom dai yanzu tasan Ayan yanason ihsan don yanzu in yazo sai ya shigo har falon su ya gaida ta Sannan su koma dakin baki da ihsan su sha hiransu.

Abangaren husna wace gari data dawo tace zata gidansu ihsan mami ta hanata, kuka husna ta farayi don gani take mami da nema bata mata plan, ko kallon ta mami batayi ba balle ta tausaya mata kan kukan da take,
 Har wace gari bata bar kuka ba, ba karamin kumburi idanuwanta sukayi ba, dakinta mami ta shiga
"Wai dan uwarki ubanme kikeyi gidansu ihsan?..." Mami ta tambayeta,
"Ba komai..." Tafada muryanta bai fita sosai
"To kukan me kike don na hanaki zuwa gidansu...wallahi ki shiga hankalin ki...ina noticing this days  baki kwana biyu sai kinje presidential avenue,.. Baki ganin ita ihsan tafi wata biyu bata zo gidan nan ba amma kullum kece zarya kan titi salon kijamin zagi gurin mutanen gari...to wallahi baki isaba..."  Husna sai kuka take kaman ranta zai fita,  mami fita tayi daga dakin ta barta nan tana kuka kaman wacce akayiwa albishir da wuta.

Sai kiranta ihsan. Take wai bazata zoba? Ita ihsan batasan rashin zuwanta shine alkhairi agareta ba amma duk ta damu wai tazo tana missing dinta.
Ganin har karfe biyu bata zo ba yasa ta shirya tare da izinin mom tafi, tana daf da fita bakin titi Ayan ya kirata don jin yanda take nan ta sanar dashi zata wajen KAWARTA
"Wait for me...zanzo in kaiki..."  ya fada mata, nan ta tsaya har yazo ya dinga fada wai don me zata fita bazata kirashi ya kaita ba.

Kofar gidansu husna yayi parking yace zai jirata har ta fito ya maidota gida.

Ihsan na shiga cikin falon su husna ta tarda mami hannuwa mami ta bude mata ta fada jikinta ta rungume ta tamkar yanda take rungume husna
"My second baby...ya kike ya Karin hakuri?..." Mami ta tambayeta cikin kulawa
"Lafiya lau mami....ina husna?..."
"Tana chan dakinta.. Tun jiya take kuka don na hanata zuwa wajenki..." Dan marairace fuska ihsan tayi
"Why mami...banifa da lafiya dats y takeson zuwa..." Tafada cikin shagwaba daman mostly tafi yiwa mami shagwaba don mami ta na ji dasu tunda ba yara gareta da yawa ba.
"Mami Dan Allah ki yarda mu tafi tare ..." Tafada kaman zatayi kuka,
"Ok...amma kar ta wuce three days..." Da gudu ihsan ta mike ta tafi dakin husna dake kwance tana kuka Mara hawaye, fadawa ihsan tayi kanta, a firgice husna ta mike zaune, baki ihsan ta bude ganin yanda husna ta koma ga rama ga duhu datayi Sannan ga idanuwanta da suka rine saboda kuka,
"Babe meke damunki?..." Ta tambayeta cikin tashin hankali, murmushin karfin hali ta saki tare dacewa
"Babe mestral pain ne Wallahi Kuma gashi na roki mami ta barni inzo wurin Ku ta hanani...." Da sauri ihsan tace
"Ta amince!..." Idanuwa husna ta zaro
"Da gaske?..."
"Eh...yi sauri ki shirya tare nake da yaya Ayan sai ya maidamu tare..." Da moment ta furta Ayan taga wani abu a idanuwanta for just a second kuma the next second she was smiling and saying
"Da gaske?... Bari inyi shower ..." Tafada tana shiga bathroom dinta.

After 30 minutes su biyu suka fito, Ayan na ganin su ya fito ya budewa ihsan gidan gaba yana cewa
"My baby kin fito?..." Yafada kaman babu kowa wurin
"Ina wuni..." Husna ta gaidashi,
"Lafiya..." Yafada bai daga kai ya kalleta ba, husna murmushin mugun ta tayi
"We shall see..." Ta fada cikin ranta.

Bayan ya yi parking kofar gidansu ihsan, husna ta fito ihsan tayi niyyan fita ya rike mata hannu alaman ta tsaya, kallon husna datayi cikin gida yayi Sannan yace
"Habibty wai ya kuke da wancan?...." Hararan shi ihsan tayi
"Wancan fa kace...."
"Sorry love..."
"She's my one and only friend..." Ta fada mashi, shuru yayi for a moment before saying
"I don't like her..." Ya fada a takaice
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: : 💚💜❤🖤♥💛
KAWARTA CE SANADI
💚💜🖤❤💛💙


®zuwairat (ummu Maryam)



1⃣4⃣



Hararanshi tayi tana turo baki tace
"Me bestie dita tayi maka zakace bakason ta?..." Kallon yanda take turo baki yayi ya saki murmushi at the same time yana tunanin abubuwa da yawa cikin ranshi don ji yake kaman ya dauketa kawai,
"Bata yimin komai ba...kawai I don't like her..." Wannan Karin hararan gaske tayi mashi, biting lower lip dinshi yayi
"In kina hararata sai na cire maki idanuwa......you know am not your mate" Bai idaba ta sa hannun ta zata bude motan tana cewa
"Bari in tafi tunda you are not my mate..." Da sauri Ayan ya riko hannun ta yana cewa
"Sorry... You are my mate...." Bai saki hannun ta ba yacigaba dacewa
"Baby am serious I don't like her...kawai jini na bai hadu da nata ba..."
"Pls stop it...she's the only friend I have... She is the only person I can confide in... Ban jindadi in kana cewa bakason ta..." Shuru Ayan yayi yana kallon yanda bakinta ke motsi, Sam bai jin abinda take cewa
"Baby did you know you are extra ordinarily beautiful?..." Yafada yana massaging hannun ta ahankali, ahankali tace
"Thanks..."
"Komai naki is beautiful... You voice is something else... I can't wait to have you as mine ...baby pls ki amince in turo...." Kallon shi tayi Kuma tana jin yanda yake magana kaman mai jin bacci
"Ka Dan kara hakuri mana...we started dating few days back... Ka bari muyi at least one month kaman yanda ka fada..." Da sauri ya girgiza mata kai
"No...I can't...I want to be with you... I love you" yafada cikin whisper, kwantar da kanta tayi kan seat din motan tana lumshe idanuwa
"You are...hand...some..." Tafada tana saurin rufe fuskanta da free hand dinta. Dariya Ayan yayi yana dauko wayanshi kara matsawa yayi kusa daita ya dauke su selfie,
"Baby dan Allah in turo?...plsssss" yafada babu alaman wasa.
"Bari in yi tunani..." Tafada tana kokarin zare hannun ta daga nashi..." Da sauri ya daga hannun ta yayi mata kiss Sannan yace
"Sai nazo later..."
"Ok..." Tafada tana fita daga cikin motan. Kiss ya dinga blowing har ta shiga cikin gida.
Tunda husna ta shiga cikin gidan ta haye upstairs tana kallon su nan waje, tamkar zuciya ta ta fito don bakin ciki amma data tuna Maganin da aka bata sai hankalin ta ya kwanta don ta Riga ta gama plan yanda komai zai kasance.


Bayan sallan magrib Ayan ne zaune kusa da Umma da Abba a part din Abba daman shi ya ce masu he wants to talk to them,
"Son we are listening..." Inji Abba, Ayan Dan shafa kanshi yayi alaman jin kunya dukda hakan bai nuna a idanuwanshi ba,
"Kai ni zan tashi in babu abinda zaka fadamana..." Inji Umma, daga kanshi yayi ya kalleta Sannan ya fara cewa
"Da ...samu wacce nakeso..." Ya fada kaman mai jin kunya..
"Alhamdulillah... Alhamdulillah.... Am so happy...." Inji Abba, Umma is not that surprised saboda tasan he's in love amma batasan ki wacece ba
"Masha Allah..." Inji Umma,
"Who is she?..." Abba ya tambayeshi, shuru yayi har saida Abba yakara tambayn shi Sannan yace
"Halima...." Da sauri Umma tace
"Wacece Halima...."
"Ihsan..." Idanuwa Umma da Abba suka zaro
"Daman so ne yasa ka shekawa yar mutane mari kwanaki baya?..."
 Inji Umma, murmushi yayi still kanshi kasa
"Mari Kuma?.." Abba da baisan abinda ya faruba ya tambayi Umma,
"Eh mana...har da kukanta ta shigo gidan nan.... Kai alhamdulillah... Ashe Kaine mai rabo... Maybe rabon ka ne ya Kore sauran suitors dinta..." Umma ta fada cikin excitement, Abba kam kasa boye murnan shi yayi don farin cikin har fuskan shi,
"Amma naji dadi...yanzu zanyiwa babanta magana...." Inji Abba, wani sanyi Ayan yaji cikin ranshi,
"Abba yaushe?..." Ayan ya tambayi Abba, dakuwa Abba yayi mashi
"Ina ruwanka...kaidai ka fadamin so that's all..." Mikewa Ayan yayi Umma sai hamdala take don ba karamin son ihsan take ba ta dauketa tamkar yar da ta haifa ta dauki ihsan
"Naji dadi wallahi.. I can't believe ihsan will be part of my family..." Inji Umma,
"Nima ba karamin dadi nake ji ba ...dukda nasan halin yarinyan nan ba na yaba da nutsuwan ta....ga gaida manya.....kai alhamdulillah..." Shima Abba ya fada.

Ayan shower yayi ya shirya cikin nice and lovely dress don daga masjid zai wuce gidansu ihsan.

Itama ihsan wanka tayi alwallah ta fito, husna na zaune kan gado sai latsa waya take amma hankalin ta duk kan ihsan amma babu Wanda zai gane hakan don duk Wanda zai ganta zaiyi tunanin wani abu take, ihsan bude wardrobe dinta tayi ta dauko wani Arabian gown blue
"Babe ya kika ga wannan kayan?..." Ta tambayi husna, da sauri husna ta daga kanta kaman batasan abinda ke faruwa ba
"Kai is beautiful.. Kaman Wanda mom ta sayo mana ko?..."
"Yes..."
"Me zakiyi dashi?.." Ta tambayeta, murmushi ta saki
"Sawa zanyi..kinsan my Ayan is coming..."
"Hehehe devil laughs....wai my Ayan.. Hmmm we shall see who owns him...stupid fool..." Husna ta fada cikin tanta amma a zahiri tace
"Wow ba karamin haduwa zakiyi ba.." Mikewa tayi
"Bari in baki turaren da grandma ta bani....ki shafa...it will make him go gaga..." Tafada tana daukan handbag dinta, ihsan dariya kawai tayi ta cire towel dinta ya rage daga ita sai pant and bra don sun saba su tsaya gaban junansu haka ba tare da wata ta ji kunyar yaruwanta ba doguwar gown ta zurmuka husna ta dauko turaren ta  shafa mata a jikinta,
"Woww...wannan kamshin is different... Shine baki fadawa grandma ta bani nawa ba?..." Tafada idanuwanta lumshe don ba karamin kamshin turaren takeji ba Kuma wani irin seduction scent gareshi.
"You can have it...in na koma sai in amso wata..." Inji husna dake ajiyewa ihsan turaren kan mirror,  bayan ta gama sa kayan ta kalli husna
"Babe muje downstairs..." Da sauri husna ta girgiza mata kai
"No...mu zauna nan...tunda nasan bada dadewa ba zaizo..." Tafada don tasan in sunje downstairs plan dinta zai watse, husna dauki system dinta tayi ta bude wani sabon american movies datayi downloading. Wayan ihsan ne ya fara ringing, da sauri ta mike ta dauko wayan
"By heart desire is here..." Ta fada tana rungume wayanta, hararan kasan ido husna tayi mata Sannan tace
"Love bird..Allah yasa mu a danshinku..." Tafada kaman da gaske
"Don't worry dear...naki sai yafi namu... Naki is special dats why baiso da wuriba...."
"Banza...." Tafada cikin ranta,
"Badai haka zaki fitaba..." Ta tambayi ihsan, ihsan kallon kanta tayi
" nayi kyau bane?..."
"Kina da kyau mana...amma ance in kina da kyau ki kara da wanka...so ki zauna ki tsara kwalliya ni Kuma zan sauka downstairs in hada maki ruwan da zaki kai mashi..." Tafada tana kashe system dinta
 Kallon mamaki ihsan tayi mata,
"Ruwan sha kaman Wanda ya taho daga wani wuri mai nisa?..." Kallon ta husna tayi
"Badai baki bashi ruwan sha ba?..." Ta tambayeta surprisingly,
"Ban taba bashi wani ruwa ba..."
"Amma ke baki yiba Wallahi... Ki gyara fuskan ki...kafin ki sauko na shirya maki ruwan..." Tafada tana ajiye system dinta kusa da handbag dinta in the process ta dauki Maganin daman she kept it handy, da sauri ta fita daga dakin itakuma poor ihsan ta dauko makeup kit dinta ta shafa foundation da lipstick Wanda haka yasa fuskan ta ya dinga wani irin glowing kaman wata amarya. Tana gamawa ta yafa Vail ta fito.

Husna kam tana sauka downstairs ko falo bata shiga na ta wuce kitchen, kalle2 tayi ta tabbatar babu mai kallon ta Sannan ta dauko juice daga cikin fridge ta saida ta kara waige2 Sannan ta bude ta zuba Maganin da aka bata, mom da Janna da sauran siblings din ihsan na zaune falo amma babu Wanda yabi ta kanta cos she's family, tana zubawa ta girgiza shi sosai Sannan ta ajiye kan tray ta dauko tumbler guda daya ta ajiye gefen juice din ta fito rike da da tray, mom kallon ta tayi.
"Sannu da kokari..." Mom ta fada mata, murmushi kawai tayi ta zauna tana jiran  isowan ihsan, few minutes later ihsan ta sauko, kowa na falon bude baki yayi
 "Ina zuwa?..." Mom ta tambayeta don gani take kwalliyan bana zance bane kawai
"Yaya Ayan ke kiranta..." Husna ta fada, mika mata tray din tayi ihsan tayi waje ita Kuma tayi upstairs tana jiran result
 Mom mamakin ihsan take har yau bata taba fada mata abinda ke tsakanin ta da Ayan ba data tambayeta sai tace babu komai, ita kam Janna gani take kaman tayiwa husna kazafi don yanzu ta San batason Ayan cos babu alaman wani abu a fuskan ta da zai nuna tanason Ayan.

Ihsan fita tayi ta hangi Ayan tsaye inda ya saba tsayawa in dare ya zo in Kuma da rana ne sai su zauna dakin baki, baki ya bude yana kallon ta don tunda yake zuwa wurin ta da natural face dinta take zuwa amma yau she extra ordinarily beautiful, tana karasowa ya saki murmushi Kuma abun mamaki sai ya tsinci kamshin turarenta very pleasing at the same he was very unease
"My princess.. You look lovely ko mu tafi yawone?..." Dariya kawai tayi ta ajiye drink din inda suke zama tare
"You look cool too..." Ta fada mashi, shima murmushi yayi yana kallon kanshi Sannan yace
"Not as you..." Yafada yana zama, ko kadan bai lura da abinda ta ajiye mashi, sai kallon ta yake kaman yau ya fara ganinta. Hira suka dingayi a
 Kaman yau suka fara magana Sam bai ga drink data kawo mashi ba balle yace zai sha, duk abinda suke a idon husna data labe a jikin window tana kallon su,har hawaye take babu haske dakin so babu Wanda ya ganta. Itadai kawai taga Ayan ya sha drink din.

"Babyna ji nake kaman in tafi dake kawai...you are rising the man in me..." Yafada cikin whisper, kauda kanta tayi kaman bataji abinda yace ba
"Aww...na mance ga drink na kawo maka..." Sai lokacin ya ga tray dake zaune gefen shi, baki yadan tabe Sannan yace
"Kin raina min hankali... Tunda nake zuwa baki taba bani drink ba sai yau?...to ban sha..." Yafada yana harde hannayenshi cikin hammatanshi, dariya ihsan tayi
"Ayya sorry baby ...kasame?..." Ta tambayeshi kai ya girgiza mata
"Wacce kace bakason itace ta bani shawaran in baka ruwa...ni I was thinking tunda muna kusa no need..." Bata rai yayi
"Wato bani da darajan da zaki bani ruwa sai an fada maki...to wallahi bansha..." Yafada in a serious tune,
"Sorry baby na..."
"Stop calling me your baby..."  Yafada irin bai so dinnan,
"Bari in zuba maka....." Tafada kaman tana lallashin shi, hararan ta yayi
"Bansha..."
"Plssssss.." Tafada kaman zatayi kuka, hannu yasa ya daga chivita drink din ya kalleta sosai Sannan yace "bansha.." Kara marairace wa tayi
"Why..."
"Bana shan sweet drink..." Idanuwa ta zaro
"Adalili?..." Ta kara tambayan shi surprisingly,
"Saboda sweet things make men weak...tana rage mana karfi..."
"Karfin me?..." Ta kara tambayan shi
"Karfin fada daku..." Yafada sounding naughty, hararanshi kawai tayi
"Yanzu bazaka sha ruwan gidan mu ba...."
" ni ba kishin ruwa nake ji ba...."
"Then what do you want?.." Matsar da kanshi yayi kusa daita Sannan yace
"Am hungry for you..." Bai idaba ta galla mashi harara,
"Wallahi zamu bata da kai...ga ruwa na kawo baka shaba Sannan ga anyhow talk..." Nuna kanshi yayi
"Ni ke anyhow talk?.. Kin rainani wallahi... Amma no case...zan rama"
"Ko Kuma ka rame ba..."
"We shall see..."


Husna dake labe jikin window har legs dinta sunyi sanyi saboda tsayuwa kawai taga Ayan yasha drink din shine farin cikin ta amma har ya daga Kuma ya ajiye bai shaba nan hankalin ta ya tashi ..tana kallon su taga ya mike ihsan na biye dashi, wasu zafafan tears ne suka fara zubo mata.

💜🖤❤💛💙💚


Kuyi hakuri kunsan yanda weekend yake game iyali. Thanks for your understanding
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: ❤💛💚🖤💜💙
KAWARTA CE SANADI
💛💜💙🖤💚❤


®zuwairat( ummu Maryam)



1⃣5⃣




Dukan bango ta farayi tana kuka kaman ranta zai fita
"Wallahi this will never stop until you are mine...wallahi you are mine... Ko baka sha wannan ba...I will not stop... Nothing.. No one will stand in my way...not even your stupid love..." Ta fada cikin wani irin kukan bakin ciki, komawa tayi ta kwanta tare da goge hawayenta, tasan ko mutun zata kada ta yanka she will do it for the love of Ayan, rufe kanta tayi da bkanket kaman mai bacci amma idanuwanta biyu sai hawaye ke bulbulowa.


Har kofar gida ihsan ta raka Ayan sai kumbure2 take wai yaki shan ruwan gidansu
"Kasan bazan sha ruwa gidanku ba duk ranar dana shiga..." Dariya yayi yana kallon yanda take turo baki
"Kinsan Wallahi banshan can or packed juice... I prefer homemade juice... Kinsan am a doctor and am telling you duk wayan nan kayan kwali da sauran su are not good for your health..." Hararanshi tayi
"Bawani inda bashi da kyau da tuni na mutu cos ba kwana daya bansha can or bottled drink ba..." Bakinta ya rike
"Wato kinsaba chan zaki ko....to when we are married no more sweet drinks..." Yafada itadai shuru tayi
"Na fadawa su Umma about us...hope su mom basu kini ba?..." Ya tambayeta thinking ta Riga ta fada masu,  ahankali tafara cewa
"I haven't told anyone of them... Husna kawai na fadawa..."  Kallon mamaki yayi mata
"What the hell do you mean by that?..." Yafada cikin fada,daga kanta tayi ta kalleshi zatayi magana yayi saurin cewa
"Ya zaki maidani  Dan iska?.. Wato duk zuwan da nake gidanku iyayenki basu saniba?...salon ace wani Abu ke kawoni wurin ki?...gaskiya baki kyauta min ba...in Kuma baki sona tell me...pls don't let me waste my precious time..." Ihsan shuru tayi tana sauraron shi,
"Kuma ai at least you should have told your mother.. Yanzu ni abinda ke bani haushi shine Abba zaiyiwa dad dinki magana alhalin ke baki fada mashi komai ba...nidai pls tell me if you are not into me..." Ya cigaba da nagging, daga kai tayi
"Amma ka fiya fada wallahi..." Tafada cikin tsiwa,
"Daga fadin gaskiya sai kice na fiya fada?... Ai ko babu Wanda yasan abinda ke tsakanina da ke mom ta Sani amma wani abun haushi wai husna take kowa? Wai ita kadai ta Sani...ke gaki mai bestie ko?...nima ina da bestie in short besties amma still I told my parents balle ke mace?..to nidai bazan kara zuwa na saidai in kin kirani kin sanar dani in turo amma ban kara zuwa ana yimin kallon Mara aikin yi..." Yana kaiwa nan ya fara takawa zai fita tafi, ihsan bin bayanshi da harara tayi tana
"Ayya zan Iya zama da wannan bawan Allah?... Mutum sai fada?... He's talking to me as if he's my father..." Ta fada cikin ranta azahiri tace
"Kada Allah yasa ka dawo.." Tafada da Dan karfi yanda zaiji   , juyowa yayi ta kalleta
"Haka dai kikace ko?...no problem...daman ba sona kike ba haka nan kikasa nayi wasting time dina..." Zai kara wata magana ta shigewarta gida tare da daukan juice din data ajiye mashi ta kai cikin kitchen ta maida cikin fridge Sannan ta hau upstairs.
 Tana shiga wutan dakin ta kunna taga husna kudundune cikin blanket kaman mai bacci Kuma idonta biyu, ihsan cire kayanta tayi ta dauko kayan bacci ta saka ta zauna bakin gado tadan taba kafan husna ahankali, banza tayi daita kaman batajinta, kara taba ta tayi husna tadan yi motsi kaman wacce aka tada daga bacci,
"Babe pls tashi ki bani shawara..." Tafada ahankali, husna mikewa zaune tayi tana murza idanuwa don kar ihsan ta gane tayi kuka, idanuwanta sunyi ja saboda kuka amma ihsan was thinking saboda baccin data tadata ne,
"Sorry na katse maki bacci.." Tafada tana haye kan gado
"No p.." Inji husna
"Meye zaki fadamin?.." Ta tambayeta, ahankali ihsan datayi balance kan gado ta fara cewa
"Ayan yanason turowa!..." Husna ji tayi kaman an soka mata arrow a heart dinta, amma dayake shaidaniya ce sai ta saki murmushi Wanda ko throat dinta bai kai ba balle cikinta,
"So soon?..."
"Nima abinda na fada mashi kenan amma yau har fushi yayi dani wai in ban fadawa su dad ba bai kara zuwa nan..." Da sauri husna tace
"To what are you waiting for?.. Kina da komai... Ga kayan furniture da other home item dinki intact... Kawai ki fada mu sha shagali...." Tafada tana girgiza boobs dinta kaman gaske,
"Wallahi sai mun tada garin Kano da jazz..." Ta cigaba dacewa,
"Amma ni it's too urgent... Duka yaushe muka San juna...ina tsoro kar ace wani abu nawa yakeso..." Husna kallon ta tayi
"Hmmm you are dreaming too far..." Tafada cikin ranta,
"I don't take so...yanason ki da gaskiya...kawai just give him chance..."  Shuru ihsan tayi Sannan ta fara cewa."har cewa yake bazai kara zuwa ba sai na kirashi nace ya turo...kawai don ya lura na damu dashi...don yasan I have grown use to him. ..mtswww"..tafada tana kwantawa, kallon bayan husna tayi ta wulla mata harara
"Kuma a haka zaki rabu dashi ko Kuma ahaka zai rabu dake...I will make sure he hate you as hell..." Ta fada cikin ranta tana kwantawa tare da juyawa ihsan baya wasu hawayen na zubowa, da sauri ta goge su tana tunanin
"Stop wasting your tears...he is definitely yours..."evil heart dinta yayi reassuring dinta
 Ayan yana tafiya yana surutu shi kadai Allah ya taimaka darene da ance he's insane, yasha ganin salma da sameera suna sharing love life dinsu da Umma wani lokacin har bedroom din Umma yake tardasu suna bawa Umma labarin wayanda suke so da kauna amma wai duk yawon nan dayake iyayenta basu sani bani
"salon a dauke ni Dan iska.." Ya furta a zahiri yana bude gate dinsu, haka ya shiga part dinshi ranshi bace.
Wanka yayi am still bai samu saukin bacin rai ba shi gani yake sonshi ke batayi shiyasa bata fada gida ba sam baisan bata sharing wani abu nata da family dinta sai aminiyarta. Da kyar bacci barawo yayi gaba dashi.

Wacegari bayan sallan fajr ta sami mom dakinta, sallama tayi mom ta amsa mata tana yi mata kallo mamaki
"What's wrong?.." Mom ta tambayeta don tasan bata fiya shiga wurin ta haka da wuriba,
"Good morning...Mommy" tafada tana zama bakin gado mom
"Morning... Meke damunki?..." Mom ta kara tambayan ta,
"Bakomai... Wata magana ce zan fada maki..." Tafada kanta kasa, da sauri mom ta gyara zamanta kan praying mat Sannan tace
"Am listening..." Shuru tayi for a while Sannan tace
"Its about Ayan..."
"What about him?.." Ta tambayeta kaman batasan abinda ke faruwa ba,
"Yace zai turo..." Tafada cikin sanyin murya,
"Daman kuna soyayya dashi ne?..." Ta tambayeta, shuru ihsan tayi bata ce kala ba,
"I said were you seeing each other?.." Ta kara tambayan ta, ahankali ta gyada mata kai, shuru mom tayi, Sannan ta fara cewa
"Yanzu soyayya kike dashi amma kullum ya zo na tambayeki sai kice sako ya kawo maki...yanzu kin kyauta kenan?... Yanzu do you have any adviser apart of me?..." Da sauri ihsan ta girgiza mata kai
"Then why are you hiding your secret from me?...am your mother..." Cikin sanyin murya tace
"Mommy am not hiding anything from you.."
"To ke kika Sani..yanzu kinason abubakar din?..." Mom ta tambayeta ahankali ta gyada mata kai
"To shikenan.. Kisanar da dad dinki..." Mom ta fada mata, hira suka danyi ta mike ta koma dakinta tare da sanar da husna yanda sukayi da mom.

Part din dad ta je ta sanar dashi the same abinda ta fadawa mom,dad ba karamin dadi yaji ba don har cewa yayi ba sai anyi bincike ba kawai ya turo don babu abinda basu Sani game dashiba.

Dadi taji har cikin ranta ta koma ta fadawa husna, husna kam har rawa tayi gaban ihsan tana cewa
"Ayiiiiiirrrrrrr....I can't wait for the day..." Tafada.
"Amma bazan fada mashiba sai na yi mashi yanga tukunna.." Ta fada tana catwalk, bayanta husna tabi da harara.
"Muyi mu shirya tunda muna da lectures by 9am.." Inji husna.
 Agidan su ihsan da akwai abinda ke faruwa Wanda babu Wanda ya Sani sai Allah, my aikin su tana da Dan hali, to ba gidan take kwana ba , takanzo da har bag dinta in zata tafi ta Dan lalubi Dan wani Abu kaman indomie, maggi , mai, da kayan sha, to yau tana zuwa kasancewan da wuri take shigowa at times kafin su mom su sauko har tayi wanke2 da some other things, kamar kullum ta zo, kalle2 tayi ta dauki indomie biyu ta saka cikin dan hand bag dinta, unluckily for her ta bude fridge ta dauki juice da aka husna ta zuba magani ta saka kasan bag din ta rufe da hijab dinta ta ajiye cikin locker Sannan ta cigaba da her daily activities.

Ihsan na shiga bathroom husna tayi saurin sauka downstairs, direct kitchen ta shiga ta bude fridge, to lokacin data saka magani chivita biyu ne cikin fridge din sai sauran drinks irin su hollandia da sauran su, saurin da take wurin zuba Maganin baisan ta lura da su biyu bane, hakan yasa ta dauki dayan chivita a tunanin ta Wanda ta saka magani ne, alokacin mai aiki na gyara falo so bata cikin kitchen, da sauri ta bulbule juice din cikin sink Sannan ta yarda kwalin kasan dustbin ta koma sama.

Around 8:30 kowa na gidan hallara wurin dinning, ihsan da husna sun shirya don daga nan zasu wuce school.

Shima Ayan tunda ya tashi sallan fajr bai koma ba, wani irin ciwon kai take sakamakon dashi baccin da baiyi ba jiya zama yayi yana tunanin rayuwan duniya shidai aduan shi Allah yasa kar ihsan ta ki shi don baisan yanda rayuwan zata kasance mashi ba, drawer ya bude ya dauko wata takarda ya duba da alaman timetable din ihsan ne, mikewa yayi ya shirya, around 8: ya fito ya wuce wurin Umma yayi breakfast a tsatsaye Sannan ya wuce, kofar gidansu ihàopisan yayi parking ya dauki wayan dauki wayanshi yayi dailing number ta
 Su ihsan na fitowa compound wayanta ya fara ringing tana picking yace
"Kifito in ajiyeki..." Bai inji amsanta ba ya kashe wayanshi. Ihsan kallon husna tayi
"Babe anya zan Iya da halin wannan mutumin kuwa?..." Tafada tana bude gate, nan suka hango motanshi tsaye, fuskan shi tamkar anyi forcing dinshi ya dauketa , kara daure fuska yayi dayaga su biyu
"Wato ni zata maida driver..." Ya fada cikin ranshi, suna karasowa husna ta shiga baya ita Kuma ihsan ta shiga gaba,
"Ina kwana?..." Ta  gaidashi, kallon in resistable face dinta yayi ya galla mata harara ya kauda kanshi ya tada mota, 
"Good morning.." Itama husna ta gaidashi muryan ta narawa, banza yayi daita kaman baiji abinda tace ba. Suna cikin tafiya ta kalleshi Sannan tace
"Ka turo...." Ts fada mashi atakaice, wani irin haushi ne ya kamashi yanda tayi maganan kaman anyi forcing dinta, parking yayi gefen titi, kallon bayan yayi
"Excuse us..." Ya fadawa husna babu wasa cikin muryan shi, ihsan tsaya kallon ikon Allah, cikin jin haushi da bakin kishi husna ta fita ta tsaya daga gefen titi, kallon ta yayi yafara cewa
"Repeat what you said..." Yafada ahankali tace
"I said ka turo..."
"Kuma dayake baki da mutunci shine zaki fada min a gaban wancan?...see in baki sona you should tell me..."
"Ikon Allah... Me nayi Kuma?..." Tafada tana ware hannuwanta
"In ba don kin raina min hankali ba gaban wancan zaki fadamin in turo?...gabanta nace maki in turo? Wallahi you are annoying"
"Wai ba kawata bace?.... Ni wallahi banson yanda kake tisani gaba ka dingayi min fada kaman kai ka...."
"Keep shut!.." Ya daka mata tsawa, idanuwa ihsan ta zaro
"Ko ban haifekiba na girmeki...kawai don INA sonki bazan fada maki gaskiya ba?..." Motan ihsan ta bude
"Gaskiya bazan iyaba...I can't cope with your temper...ban iya auren Wanda zai maidani kamar yarda... Kawai forget nace ka turo..." Tafada tana kokarin fita daga cikin motan
"Get out!... To hell with you..." Yafada da karfi cikin high tune.
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💚❤💙🖤💜💛
KAWARTA CE SANADI
💛💜❤🖤💙💚



®zuwairat( ummu Maryam)



1⃣6⃣



 _Faty afree naga program dinku Kuma ya burgeni sosai, salma da badiya I love you too, nima ina gaidaku, ya rabbi ya bar zumunci_ 👏🙏🤝👍

Fuhhh ta fita daga cikin motan shima figa motan yayi ya bar wajen,
"Wai me ya farune?.." Husna da ranta kwal da farin ciki ta tambayi ihsan
"Rabu dashi...gaskiya na fasa  auren shi... Ya fiya nagging..." Kauda kai husna tayi ta saki murmushi
"Ashe kudina bazai sha wahala ba kenan..." Tafada cikin ranta, ihsan sai kumbure2 take wai yace mata to hell with you ita kam husna tamkar ta zuba ruwa kasa tasha don jindadi. Nan suka tsaya suna neman a daidaita.

Ko nisa Ayan baiyiba yayi packing motanshi gefen titi tare da hada kanshi da staring motan, sai nishi yake sama2 saboda too much temper, yasan he don't have right to shout at her, she's not salma, sameera, antymu or Ismail she's the woman he loves amma ya gane she don't take corrections and that's one thing he hates, kaman ance run for your life ya juya kan motan, daga nesa ya hangeta tsaye suna jiran abun hawa don ko kadan bai ganin husna,
"Sai taurin kai kaman arnan farko..." Yafada yana parking gabansu, Dan dukar da kanshi yayi
"Angel ki shigo mu tafi..." Yafada kaman bashi bane yafe fada few minutes ago, ihsan kauda kanta gefe tayi don har lokacin bata bar fushi dashi ba, husna kam kaman da ita yake ta bude baya tayi zamanta , hakan ba karamin haushi ya baiwa Ayan ba, ihsan kam hararan ta tayi
"Babe ki shigo mutafi pls...kinga lokacin lectures na wucewa..." Tafada amma cikin ranta bata ki trailer tabi ta kanta nan take ba, sunfi minti biyar na tsaye bata shiga ba, Ayan fitowa yayi daga cikin motan
"Baby kiyi hakuri... Kinsan kin fini laifi cikin abinda ya faruwa...bai kamata ki fadamin such personal matter gaban wata ba..you know it is a serious matter..." Hararanshi tayi Sannan tace
"Watace?...is she not my friend?.. Amma shine har dacewa I should go to hell..."
"To kiyi hakuri... Bazan kara ba..." Yafada cikin tattausan lafazi, kara hararanshi tayi Sannan tace
"Kuma gaskiya in har haka zaka cigaba dayi min fada to bazan iyaba,..."
"Am sorry.. Kinsan I have siblings kaman ki..Kuma ina fada masu Abu suji...so anytime na fada maki magana kika nuna min ba haka ba sai raina ya baci ...amma kiyi hakuri bazan karaba..." Dan turo baki tayi
"Promise?...yatsanshi  daya ya daga sama
" cross my my heart... Swear to die..." Dariya tayi shima ya saki dariya, inda at that moment zasu kalli fuskan husna da sun gano true colour dinta don wani irin kallon haushi takeyi masu especially ihsan,

"Yanzu kin yafe min?..." Ya tambayeta, ahankali ta daga mashi
"Thank you my angel.. One more thing.. Pls kar ki kara bari wancan ta cikin motan ta kara shiga motata..." Hararanshi tayi
"Zaka farako?..." Da sauri yace
"Sorry tunda baki kishina...wasu yanmatan basu yarda friends dinsu su san sanadin masu amma ke ko ajikin ki..."
"Wayanda suke wannan tsoron basu aminta da friends dinsu ba ni Kuma I know she will die for me..."
"Naji...yanzu tunda kinyi hakuri hope ina Iya turowa ko?..." Murmushi kawai tayi, wurin motan ya koma ya bude mata ta shiga shima ya shiga, husna fara latsa wayanta tayi kaman batasan dasu ba, juyowa ihsan tayi
"Babe sorry Mun barki zaune..." Da sauri ta daga kanta ta sakar mata murmushi Sannan ta maida kanta kan wayan Wanda ko haskenta bata kunna ba
 Shi kam Ayan yana mamakin abinda yasa ko kadan baison yarinyan, tunda yake bai taba jin mutum bai kwanta mashi ba kaman wannan yarinyan Kuma daman ance follow your instinct cos it may be for the best. Haka sukayi driving in silence don ko kadan baisan magana gaban husna, suna isa husna ta fita ita Kuma ihsan ta zauna nan cikin motan sukasha hiransu cos lokaci ya kure masu already so basuyi attending lecture din ba.


Sai around 12 ya bar buk ya koma office, itakuma husna na zaune daga nesa tana tunanin yanda zatayi ta raba Ayan da ihsan cos ta lura their love is very deep first tayi deciding she will make Ayan hate ihsan,
"Zanyi abinda na sabayi..." Tafada cikin ranta, wayanta ta dauka ta kira wani
"Ina fa da aiki...ya zaayi?..." Ta fada atakaice, dajin abinda tace kasan she have been doing it,
"Haka kikace kwanakin baya amma kika watsar dani..." Wani ya fada daga chan bangaren
"Kar ka damu...wannan yafi sauran... Cos wannan case din nawa ne..." Tafada daga chan ta hangi ihsan ta taho da sauri tace
"Zan kiraka later..." Tafada tana katse wayanta.


Bayan karfe biyar ya maidosu gida, alokacin mai aiki ta kusa gama aikinta, tana ganin su ihsan sun dawo ta samu mom a falo ta sanar daita zata tafi, as usual mom tasa ta debi abinci, mom ta bata kudin abun hawa Sannan ta tafi. Bakin titi ta nufa ta tsaida abin hawa ta hau ta kama hanyan sabuwar gandu, wurin da nisa sosai don ana kiran sallan magrib ta iso gidansu, a kofar gidan data tsaya wani saurayi ne zaune sai zukan taba yake, da ka ganshi kaga irin samarin nan masu zaman banza, gayen baki ne amma bakinshi tafi fuskanshi baki saboda shaye2, mai aikin na ganin shi ta daure fuskan,
"Wato ana kiran sallah kai kana nan sai zuke2 zuke kakeko?..." Saurayin mikewa yayi,
"Ina sannu da dawowa... Me zan samu?.." Yafada cikin muryan Wanda yasha yayi tatul, Matan dan to she hancinta tayi
"Yanzu giyan ka kara sha?...Matan ta fada kaman zatayi kuka..."
"Ni inna ki bani abinda kika kawo inci...yunwa nake ji...Wallahi kaman an yayemin yan hanji nakeji..." Yafada yana tangal2, tsoki inna taja zata wuce saurayin yayi saurin taran hanyan
"Wallahi baki wucewa sai kin bani wani abu..." Saurayin ya fada yana tare hanya,
"Wallahi ka bar wajen nan kafin in Tara maka mutane... Banza shasha..." Dariya saurayin yayi Sannan yace
"Ke kika haife shasha...ki bani wannan abincin inci ko Kuma in amshe duka abinda kika kawo...kinsan karamin aikina kenan..." Yafada kaman mai maye,
"Wallahi ban baka wannan abincin,..." Tafada tana bude bag dinta , indomie daya ta dauko zata mikawa saurayin wuf ya amshe bag dinta
"Dan uwar ka ka bani jakata..." Bai saurareta ba ya bude ya fiddo sauran indomie da lemon asirin husna,
"Bazaka bani ba!..." Inna ta fada a afusace , wulla mata bag din yayi ya kara gaba yana balle murfin lemon, nan take ya kafa kai ya shanye bako bisimillah, bai daga kaiba saida yaji nothing is dropping out.
 Ayan na dawowa gida ya sanar da Abba da Umma yanda sukayi da ihsan,
"Shikenan ma...babu wani bincike da zaa tsayayi...zuwa jibi zamuje kawai..ka sanar daita..." Inji Abba, Ayan Dan bata fuska yayi don shi he was thinking gobe Abba zaije
"Sai jibi?..." Ya tambayi Abba, kallon shi Abba yayi
"Eh...ko da matsala ne?..." Dan turo baki yayi Sannan ya girgiza kai
"Bakomai..." Yafada yana mikewa daga dakin
 Ranar ya koma gidansu ihsan ya sanar daita cewa iyayenshi zasu zo jibi yana maganan farin ciki na fita ta koina jikinshi, bayan ya tafi itama ta sanarwa su mom da Abba cewa zasuzo jibi, Sannan ta fadawa husna, murna wurin ta baa magana don babu Wanda zai gane da akwai wata a kasa, the following day tace zata koma gida, daman abinda ya kawo shine don ta samu ta sakawa Ayan maganin Kuma hakan bai faruba Kuma tasan zamanta nan bashi da wani amfani dole ta koma gida ta zage damtse, da kyar ihsan ta shawo kanta ta zauna don su hada kayan da zaa tari su abban Ayan dashi.

Ranar da zasuzo tare suka hada kayan abinci kala2 da drinks kala2 don tare baki, around 4pm su Abba da families dinshi su six suka zo nan sukaci sukasha Sannan akayi magana inda nan take dad ya bawa Ayan ihsan yace duk sanda suka gandama akawo sadaki su dauketa, ba karamin dadi Abba da yanuwansa sukaji ba nan aka saka biki sati six. Daga nan gidan sukayi sallan magrib Sannan Abba suka wuce gidanshi, daman sarkin zumudin baije aiki ba wai yau zaa je nemar mashi mata don haka ya bawa kanshi Hutu.

Yana ganin shigowansu ya fito daga apartment dinshi, bai Iya tambayan Abba yanda suka kaya,daman da akwai  wani kanin Abba da Ayan ya mugun raina, mutumin ba babba bane don shekara goma yabawa Ayan, da sauri Ayan ya gaida sauran Sannan ya kama hannun Wanda ya raina, tambayan shi yarayi kan yanda akace nan mutumin ya fada mai komai,baki ya washe yana cewa
"You mean nan da sati shida zanyi aure?..." Ya fada yana zaro idanuwa,
"Eh sarkin zumudi..." Ihu Ayan ya saki Wanda yasa Abba da sauran family juyowa, wani irin harara Abba ya gallawa Ayan Wanda yasa yayi saurin kaman bakinshi
 Suna shigowa shima ya shiga nashi part ya fara kiran Muhammed, yana picking yace
"Am getting married in the next six weeks..." Muhammad zai bude baki yayi magana kat ya katse wayanshi ya kira Yusuf, shima still the same thing ya fada mashi ya katse wayanshi, haka ya dinga kiran friends ya fada masu
"Am getting married in the next six weeks.."  Ba tare daya ya bari sunyi magana ba sai ya katse wayan, Kuma suyi ta kiranshi yana rejecting.

A bangaren ihsan kam dad ya sanar dasu yanda komai ya kasance ihsan dai kanta kasa haka nan sai ta tsinci gaban ta na faduwa ba kaman in ta tuna zafin ran Ayan, husna kam zufa ta farayi bayan ihsan ta sanar daita komai, amma still she was still wearing a wonderful smile kaman nothing is going on. Wayanta ne ya fara ringing tayi picking ganin Ayan ne, hands free ta saka wayan,
"Baby am getting married in the next six weeks..." Yafada yana lumshe idanuwa tare da biting lips dinshi, ihsan kallon husna dake murmushin karfin hali tayi Sannan ta kalli wayan dake hannunta tace
"To who..." Ta tambayeshi muryanta na shaking ahankali, dariya yayi
"To the most lovely...beautiful... Stubborn... Brilliant... Lucky... Charming... Adorable... Ravishing lady.. Mai suna ihsan....do you by any chance know her?..." Ya tambayeta cikin sanyin murya, ihsan lumshe idanuwa tayi, husna kam ji tayi she can't listen anymore, mikewa tayi ta shiga bathroom,
"No...I don't know her..." Ta amsa mashi cikin wani irin murya,
"Then kinyi missing... Duk Wanda baisan ihsan ba baisan mutum ba...halimatu mai hali dubu....ranar auren mu zanyi mata wani special kyauta cos nasan zan amshi wani babban abu wurin ta...." Ahankali ihsan ta dan Dora hannun ta kan chest dinta don ba karamin bugawa take ba, amma she's enjoying every part of the conversation
"Me ne zaka amsa?..." Ta tambayeshi cikin whisper, dariyan kasan makoshi yayi
"Something that belongs to me and me alone....something that I thank Allah for not letting anyone having except me...halima I love you so much... I can't wait for us to be together so that I will shower my love and blessings on you...." Ihsan dai shuru tayi don tunda suke magana muryan shi na yau ya sha banban Dana sauran kwanakin, he was talking as if he was force to, sun fi hour suna waya inda through out husna tana cikin bathtub tana kuka .


The following day tunda da wuri husna tace zata gida, shiryawa ihsan tayi ta rakata suna wuce kofar gidansu Ayan aka bude gate, Ayan ne ya fito kan machine robaroba,  kallonta yayi ya saki murmushi Sannan yace
"Pls go back home..." Ya umarceta, hararanshi tayi
"Rikiya zanyi ..ko zaka ajiyeta?..." Ta tambayeshi,
"Ba hanyan nayiba...amma go home..." Turo baki tayi
"I said go back home... Banson yawo....Sam ban kaunar gantali..." Yafada Sannan ya Kara cewa
"Zo ki hau in ajiyeki gida sai in dawo in ajiyeta..." Yafada kaman da gaske, sakaran hawa tayi bayan sunyi bankwana da husna, yana ajiyeta ta shige gida ya dawo ya wuce husna da gudu kaman ba kowa wuri, husna cire wayanta tayi ta kira wani tare dacewa
"Kajirani kofar gidanmu..."
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💚❤💜🖤💛💙
KAWARTA CE SANADI
💜💙💛🖤❤💚



®zuwairat(ummu Maryam)


1⃣7⃣



 *Masoyan KAWARTA CE SANADI zan baku hakuri saboda daga wannan bazan kara posting ba sai na gama, pls I want* *you fans to understand, kar kuyi fushi Kuma in na gama zan fada maku inda zaku sameshi complete batare da kun ts* *aya jiran one page kullum ba, thanks for your cooperation, Allah ya barmu tare.*


Tana cikin adaidaita tana tunanin halin Ayan ,daman haka yake ko ita kadai yakewa haka don kiri2 tana ganin tsanan ta a idanuwanshi amma ko kadan bai bata mata rai, kullum kara hura mata sonshi ake ita kawai matsalar ihsan, gani take son dayakewa ihsan ne ke sashi wannan behaviour, gurinta kawai ta kauda ihsan daga cikin rayuwan Ayan. Tana isowa kofar gidansu ta hangi wani saurayi jingine da bangon gidansu, biyan mai a daidaita tayi ta sauka ta nufi saurayin yayin da shima ya nufota,
"Yaya dai?..." Saurayin ya tambayeta, da sauri ta fara cewa
"Wani zaka kara yiwa yanda ka saba..." Ta fada mashi,
"Ina yake?..." Ya tambayeta, nan ta bawa saurayin address din office din Ayan, saurayin cewa yayi
"To wannan karin dubu hamsin zaki bani..." Bai idabao idaba ta wangalo idanuwa
"Yo ya akayi?...ai kinsan dole inyi hayan kaya Sannan zanyi hayan mota...Kuma da akwai balance din 5k da zaki bani...ko kin manta..." Dirty look tayi mashi
"Amma baka da kirki...yanzu dubu hamsin for such little job?... Duka nawa ake hayan kaya da mota?... Gaskiya 40k zan baka  harda balance dinka..." Girgiza kai saurayin yayi
"Gaskiya Aa...ko ki bani 50k ko Kuma ki bani balance dina kawai sai ki samu wani...." Hararanshi ta karayi
"Ashe daman haka kake?... Duk contract din da nake baka amma zaka fadamin haka?..."
"Contract ko watsa farin cikin wani?... Ai ya kamata ki dinga biyana fiye da haka wallahi..." Saurayin ya fada sounding very tensed,
"Naji...karkayi min ihu...I will give you..." Murmushi gayen yayi yana shafa sajenshi
"Yanzu yaushe zaki bani kudin..."
"Ka saurareni zuwa gobe..." Ta fada Sannan ta shiga gidansu
 Direct part din babanta ta wuce, a falon shi ta tardasuda mami, mami na rungume dashi kaman wasu yara, Dan dagowa mami tayi ta kalli husna data shigo da sallama, amsawa sukayi Sannan babanta yace
"My baby kin dawo?..."
"Eh ABU..." Mami kurawa husna ido tayi tana mamakin ramarta, mikewa tayi zaune Sannan tace
"Wai meye matsalarki?...duk kin rame kin koma kaman ba keba...." Mami ta tambayeta, marairace fuska tayi Sannan tace
"Babu komai... Kawai wani lecturer mu ne yace ayi mashi kyauta ko Kuma ayi repeating course dinshi...to abune ke damuna..." Tafada kaman da gaske.
"Wane irin Dan iskan lecturer ne wannan?...." Bai idaba mami tace
"Ka bata ko 50k ne ta bashi..kasan haka wasu suke da Neman kudi..." Daman kunsan he don't have a say, mikewa yayi ya shiga bedroom dinshi, husna kallon mami tayi tare dacewa
"Nagode mami..." Bata amsa mata ba cos a tunanin ta da gaske take, itakam hankalin ta kwance cos tasan kudi ba matsalan su bane, kome zata bukata mami zaisa dad dinta yayi koda kuwa bayason yi. Few minutes later ya fito rike da wrapper din 500 naira guda daya ya mika mata , godiya tayi ta mike tare da wulla kudin cikin bag dinta, tana fita daga part din ta kira mai yi mata aiki ta sanar dashi yazo yanzu ya amshi kudin ba sai gobe ba.
 Ihsan kiranta tayi don jin sun iso lafiya ?
"Lafiya ..."kawai ta fada mata batare data fada mata rashin m da Ayan yayi mata ba.

Aranar ma Ayan yaje gidansu ihsan sun sha hiransu, the following day da wuri ya tafi office saboda da akwai patient da zasu yiwa surgery.

Around ten suka fito daga surgery ya koma office yayi relaxing yana tunanin yanda rayuwar auren su zai kasance kawai sai wani ya banko kofa ya shigo Wanda hakan yasa Ayan saurin mikewa tare da zaro idanuwa
" kai lafiya ka shigo min office haka babu sallama?..." Yafada cikin daga murya, saurayin Wanda shine husna ta bawa kudi naga ya chanza don fuskan shi ya sha gyara, ga kamshi dayake Sannan ga expensive dress daya saka sai ka rantse wani dan hamshaki ne ko Kuma mai aikin kirki, karewa Ayan kallon yayi ya tabbatar shine Wanda husna tayi describing
"Ina Neman doctor abubakar..." Yafada atakaice, Ayan kare mashi kallo yayi Sannan yace
" am doctor abubakar... May I help you?.. " shima ya tambayeshi fuskanshi babu faraa cos shima saurayin fuskan shi daure take, nuna Ayan yayi da yatsa Sannan yace
"Am the one that is here to help you... Ina son in ja maka kunne kan babyna...stay away from my sex partner... Bani da lokaci much talk amma in kunne yaji to jiki ya tsira,...in Kuma bakaji ba you will join those that are underground...." Ayan bude baki yayi yana kallon ikon Allah Kuma abu daya kawai yake mashi yawo a kunne
"Sex partner...", saida saurayin ya kai aya Sannan Ayan yayi mashi wani kallon rainin hankali Sannan yace
" pls excuse me...who exactly are talking about?... " ta tambaya don shi he is sure the guy is not talking about his ihsan,
"Oh tambayata kake?... To am talking about my sweet halima..." Jin yakira ihsan da sweet yasa Ayan kumbura,
"You have got some nerves...how dare you step in to my office and tell me such rubbish?... You I could just slaughter you and nothing will happen..." Inji Ayan dake magana cikin bacin rai, dariya saurayin yayi Sannan ya kara nuna shi da dan yatsa,
"You want to prove stubborn?... Ba matsala... Mahmoud daya nuna he's stubborn yana inna?...I will deal with you if you don't stay away from my sugar...." Afusace Ayan ya nufoshi, saurayin na ganin haka ya fara ja da baya
"Yau sai na koya maka hankali... And you have to tell me who sent you... " saurayin naji statement dinshi ya kama hanyan waje yana cewa
"We shall see..." Inji saurayin dake fita da gudu , Ayan binshi yayi shima da gudu in the process suka cikaro da Yusuf, da sauri Yusuf ya kama shi,
"Guy lafiya?..." Donshi baiga Wanda Ayan yabi ba, sai saurayin Wanda ya kusa fita daga cikin hospital compound din yace
"Ka rabu da ihsan ko Kuma insa a kasheka..." Ayan ture Yusuf yayi da karfi Yusuf ya fadi kasa Ayan  ya bi bayan gayen da gudu kaman mahaukaci, aikam da sauri saurayin ya shiga cikin rented car dinshi ya bar wajen yana waigawa, don tunda yake zuwa wurin suitor din ihsan bai taba cunkaro da irin Ayan ba.
 Da gudu Ayan ya dawo ya haye Yusuf da naushi, tureshi Yusuf yake amma ina bugunshi yake yana cewa
"Ubanwa ya saka rike ni...yanzu gashi ya tafi ban kama shiba..." Da gudu Muhammad da wasu doctors biyu sukazo suna kama Ayan, ana kamashi yana kufcewa har kayan jikin shi kecewa yayi, da kyar aka rikeshi suka shiga office dinshi dashi , sai huci yake kaman Wanda yayi fada da zaki,
"Somebody have to die..." Ya dinga fada
"Lafiya?.." Muhammad ya tambayeshi, bai bashi amsa ba yacigaba da nishi, afusace ya mike ya dauki makullin motanshi ya fita daga office din ba tare daya kalli ko daya daga cikin doctors dake office din ba, bayan shi Muhammad yabi yana cewa
" guy meke faruwa ne?... " Muhammad ya tambayeshi, ko side din dayake bai kallaba balle ya amsa mashi
 Cikin motanshi ya shiga har lokacin bai bar huciba, figan motan tafiya bar hospital premises, yana tuki yana waige2 ko Allah yasa yaga motan saurayin amma bai ganta ba
"Hmmm my ihsan someone's sugar...no!...its not possible... Ihsan is mine... Mine alone...." Ya dinga fada yana tuki. Har ya iso gida bai bar magana ba, wani mahaukacin horn yayi a bakin gate, mai fadi ya bude gate sauran kadan daya bi ta kan shi.
Mai gadi staya kallon ikon Allah yayi, Ayan fitowa yayi maigadi ya bude baki ganin yanda kayan jikinshi ke yage,Umma dake bacci ta farka lokacin dayake horn, ta leko ta upstairs tana kallon shi,
"Son lafiya?..." Ta tambayeshi tana tsaye cikin balcony din upstairs, da sauri ya shige part dinshi ya fada kan kujera kawai sai ya fashe da kuka, ba komai ke sashi kukaba illah yanda bai kama wannan saurayin ba, ji yake kaman ya fiddo heart dinshi ya yar saboda bakin ciki. Umma ce ta shigo ta hangeshi kwance yana kuka,
"Subhanallahi!..." Umma ta fada cikin tashi hankali, karasowa tayi wajen shi
"Son what happened??.." Ta tambayeshi, cikin kuka ya daga kanshi
Ya kalleta da idanuwanshi da suka chanza kala Sannan fuskanshi jike da hawaye,
"Wai meye?..." Umma ta Kara tambayanshi cikin tashin hankali, kura mata ido yayi yana hawaye, shidai yasan bazai Iya fada mata gaskiyan abinda ke sashi kuka ba don shi kanshi bai amince da maganan wannan saurayin ba amma deep down in his heart his very angry,angry because the guy looks real.
"Umma wasune suka tareni..." Idanuwa Umma ta zaro
"Me suka yi maka ?.." Ta tambayeshi tana duba jikin shi don ba kadan hankalin ta ya tashi ba mussanman yanda kayan jikin shi ya kece da Kuma yanda yake kuka
"Son tell me me sukayi maka!.." Tafada kaman zatayi kuka,
"Ba komai..." Yafada yana kokarin maintaining kanshi,
"Karya kake...tell me abinda sukayi maka?..." Tafada still frightened, itadai tasan Ayan da taurin zuciya so ganin sha yana kuka haka makes her think the worst,
"Babu komai... Am just angry because of the way they humiliated me..." Kallon kanshi yayi Sannan yace
"Umma kalli kayan jikina..." Yana kara fashewa da kukan takaici, goge mashi hawaye Umma tayi tana cewa
"Ka bar wannan kukan haka nan..." Inji Umma.
"Zaa gano su...ko ka san su?.." Umma ta tambayeshi, girgiza kai yayi.

Da kyar Umma ta shawo kanshi ya chanza kayan ya koma ya kwanta yana tunanin maganganun da sukayi da wannan saurayin,
"Ihsan can't be somebody's sex partner... I know he's lying..." Yayi reassuring kanshi, wayanshi ne ya fara ringing yana ganin ihsan  yayi saurin picking yana sauke ajiyan zuciya
"Mine yakike?..." "Lafiya lau..ya surgery dakace zakuyi hope it was success?...".
" yes alhamdulillah... " hira sukayi for a moment amma Ayan was a little bit down koda ta tambayeshi cewa yayi he's ok.
 💜💚❤💙🖤💛

Ina barar aduan Ku mai house bai da lafiya an kwantar damu hospital, thanks
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: ❤💙💛🖤💜💚
KAWARTA CE SANADI
💛💙❤🖤💜💚


®zuwairat( ummu Maryam)




1⃣8⃣




Da gudu gayen ya iso gidansu husna cikin rented car, daman already ya kira Husna kan ta jirashi waje,yana fitowa daga cikin mota ya Dan waiga don tabbatar Ayan bai biyoshi ba don shi gani yake kaman yana biye dashi cos tunda yake wa husna aiki bai taba cikaro da irin Ayan ba, husna da tsaye bakin gate tana jiran karasowa shi, da sauri ya karasa inda take
"Ya na ganka kaman Wanda aka biyo ta 360?.." Ta tambayeshi, Dan kara waigawa yayi Sannan yace
"Kinsan yau Allah ya taimake mu..." Ya fada sounding scary, Dan tabe baki husna tayi Sannan tace
"kaman ya Allah ne ya taimakemu?..." Da sauri gayen ya fara cewa
"Wallahi gayen gwaska ne...inda ya kamani yau da asirin mu ya tonu...." Bata fuska tayi
"Pls spare me all this... Anci nasara ko yaya?..." Ta tambayeshi atakaice,
"Nasara!...ina?... Ai bai gamajin abinda ke tafe daniba ya biyoni a guje..." Hararanshi husna tayi
"Kambu...kana nufin babu nasara?..."
"Gaskiya banga alaman hakan ba..." Yafada mata gaskiya, ashariya ta saki Sannan tace
"AI Wallahi saika koma..." Bata idaba saurayin ya katse ta dacewa
"Inkoma ina?...Ai ko a lahira bana fatan haduwa da wannan gayen....ni yanzu tsoro nakeji kar ya ganni cikin gari ya ganeni..." Yafada yana share zufa kuma at the same time yana regretting zuwa shi office din Ayan,
" ai wallahi baka isaba... You think haka nan zan baka 50k?...dole ka koma kayi winning dinshi kaman yanda kake winning sauran mutanen... " girgiza kai saurayin yayi
"Kinsan maganan gaskiya ki hakura da wannan kawai in badai so kike asairinki ya tonuba...." Wani irin disgusting look ta watsa mashi Sannan tace
"Sannu mai hankali... Tunda na rabata wayanda banaso... To wallahi babu abinda zai hanani rabata da Wanda nakeso da kuma kauna...." Kai saurayin ya kada yana cewa
"Kina da aiki..." Kicin2 tayi da rai Sannan tace
"Dole ka koma...ko kuma ka samu Wanda zaka biya yaje...don Allah na gani bazanyi asaran 50k a banza ba...tunda kasan that is what we bargained for... Kace in biyaka 50k kayimin aiki sai yanzu kazomin da wata magana?...wallahi bazan yarda ba..." Tafada tana cika tana batsewa,yanda taje magana ya tabbatar wa gayen she's damn serious, shuru gayen yayi for a while Sannan yace
"Yanzu ki karo dubu goma..." Bai idaba ta daga mashi hannu alaman
"Shuushh..." Sannan tace
"That will be over my dead body...kawai kasan abinyi amma kosisi bazan kara maka ba.." Ta fada atakaice, shima saurayin katseta yayi dacewa
"Bakison aiki kenan... Nidai kin gan tafiyata,...daman wai ki karo dubu goma in bawa wani yaje don ni Allah na gani ban komawa...kinga tafiyata..." Yafada yana juyawa da alaman zai tafi, tsaya kallonshi tayi ta san the moment gayen ya tafi bazata Kara samun Wanda zaiyi mata aiki kaman shi ba kuma tasan wannan harkan secret ne don ba kowa zaka fadawaba,
"Dalla tsaya!..." Tafada tana gallawa bayanshi harara, tsayawa yayi, saida ta harareshison ranta Sannan ta shiga gida, cikin monthly allowance dinta ta dauko 10k ta bashi duk ranta babu dadi
 Abangaren gidan mai aikin gidansu ihsan kam tunda danta rabe ya shanye juice rayuwan shi ta chanza, don yanzu kusan kwana biyu kenan duk inda yake zuwa tare da kwalin yake zuwa, sai dai kaji yana cewa
"Sonta kawai nake..." Daya fadi haka sai ya rungume kwalin juice din, inna su bata dauki zancen serious ba, amma yanzu abokanshi masu shaye2 irin shi kiranshi suke da sonta nake, yau bayan inna ta dawo daga gidansu ihsan ta ganshi zaune bakin kofan dakin rungume da kwalin juice din, kallon shi tayi ta tabe baki Sannan ta shiga dakinta, few minutes later ta fito rike da kettle, kallon yanda yake rungume da kwalin tayi, itadai bata taba lura cewa kwalin juice din data dauko kusan kwana biyu da suka wuce yake rungume daita ba,
"Wai kai ina ka samu wannan kwalin... Da kake rungume wa kaman jariri?..." Bude red but Sexy eyes dinshi yayi ya kalleta,
"Inna sonta nake..." Ya fada a atakaice Sannan ya maida idanuwanshi ya rufe, ajiye butan inna tayi Sannan tace
"Wa kakeso?.." Ta tambayeshi surprisingly, kwalin kawai ya nuna batare daya bude idanuwanshi ba, afusace inna ta doso inda yake tayi kokarin kwace kwalin, aikam nan take ya Bude ido ya tureta ta kusa faduwa, ihu inna ta saki Wanda yasa neighbors dinsu biyu fitowa daga dakinsu,
"Dan wannan kwalin zaka tureni?.." Ta fada afusace Sannan ta mika mashi hannu
"Bani kwalin yanzu..." Tafada da karfi, neighbors din tsaya kallon su sukayi irin already sun saba da ganin rigiman su babu wacce ta sa baki sai kallonsu kawai suke,
"Wallahi ban badawa sonta nake..." Ya fada yana maida kwalin cikin hammatanshi, baki inna ta bude,
"Wai INA ka samo wannan kwalin tukunna?..."
"Wanda kika kawo daga wajen aiki ne..." Ya amsa mata yana kara tura kwalin a hammatanshi, idanuwa Inna ta zaro
"Wato wannan kwalin ne hannun ka har yanzu don rashin aikin yi?...to maza he ka yardata yanzu nan...." Tafada , wani yaro ne Wanda bazai wuce shekara bakwai bane yace
"Nima inna jiya nace ya bani in zuba ruwa inyi wasa yace min sonta yake..." Kallon rabe inna tayi don tabbatar da magana Dan autanta, shikuma banda kokarin protecting kwalin babu abinda yake yi.

Atakaice duk yanda inna taso ta amshi kwalin kin bata yayi har ta bishi da gudu ya fita rungume da kwalin yana cewa
"Wallahi babu mai rabani dake don sonki nake..." Itakam inna ko kadan ranta bai bata wani abu serious kawai tana tunanin shakiyancin danta ne.


Duk ranar kam Ayan baici abinci ba,duk yanda yake son fidda abun cikin ranshi hakan ya faskara, wata zuciya na fada mashi it can't be while wata na fada mashi it might be true, around 5:pm Yusuf da Muhammad sukazo gidan, part din Umma sukaje suka gaidashi Sannan suka shiga wurin Ayan, daman yana tsaye bakin window yana kallon shigowansu, sanye yake da boxes sai pure white singlet, suna shigowa ya koma ya zauna jikin shi ba kwari, Yusuf zama yayi while shi Muhammad ya nufi mini fridge dake dakin ya budeta ya dauko bottle water daya Sannan ya zauna ,su biyu kurawa Ayan ido sukayi Sannan Muhammad daya Dan sha chill water yace
"Wai guy me ya faru ne dazun a hospital?..." Ya tambayeshi yana kara shan ruwa, Ayan kallon shi yayi Sannan ya kalli Yusuf da gefen fuskan shi ya danyi ja saboda naushin da yayi mashi yace
"Guy am sorry for my irrational behavior earlier..." Yayi directing maganan shi zuwaga Yusuf, murmushi Yusuf yayi Sannan yace
"Ai da ina fushi da bazan zo nan ba...wannan ya wuce...all we need to hear is the reasons behind that action..." Inji Yusuf,
 Dan hararanshi Ayan yayi Sannan yace
"Baku ji abinda wannan saurayin da nakebi yace ba?..." Yusuf girgiza mashi kai yayi alaman baiji ba shikuma Muhammad ya fara cewa
"I had him say something like... Ka rabu da ihsan ko..." Sai Kuma yayi shuru saboda yanda idanuwan Ayan suka chanza kala, afusace Ayan ya fara cewa
"That guy meet me in my office and warn me to stay away from ihsan...."
"What!!!..." Su biyu suka fada sounding unbelievably, cikin dacin murya Ayan yacigaba dacewa
"He said ihsan is his...." Sai kuma ya kasa karasa maganan da gayen ya fada mashi,
"Kambu amma Allah yazo gayen...na yau na lahira sai ya fishi sukuni Wallahi..." Yafada cikin bacin rai,
"Amma that guy most have been stupid... Baisan an saka maku rana ba?..." Inji Muhammad, Ayan dake karkada kafa saboda bakin ciki yace
"The stupid guy was threatening me to stay away from his sex partner..." Maganan ta kufce mashi, da sauri Yusuf da Muhammad sukace
"Sex partner!!!..." Hakan ba karamin bawa Ayan haushi yayi ba, shuru sukayi suna kallon junansu, ahankali Yusuf yace
"Hmm this is serious... Yanzu do you think the guy is right?..." Yusuf ya tambayeshi, wani irin dirty look Ayan ya watsa mashi
"What do you mean by that?..." Ya tambayeshi afusace, da sauri Yusuf yace
"Don't be offended... Kawai maganance is some how..." Gyara zama Muhammad yayi Sannan yace
"Guy ka kwantar da hankalin ka...dukda basan yarinyan ba I know she is not somebody of such character.. Kilan gayen yanason ta shine yake son ruguje wedding plans dinta... Remember wasu daga cikin suitors dinta sun ja baya kuma am suspecting irin wannan threat ne yasa suke guduwa...so guy duk yanda zasuyi ihsan is yours Sannan kai zakayi removing abinka cikin Leda..." Yafada yana kashewa Ayan ido daya, maganan shi ba karamin farantawa Ayan yayi ba don sai gashi ya saki murmushi
 " thanks bro..you know the right thing to say at the right time... " ya fadawa Muhammad Sannan ya juya ya wullawa Yusuf harara, dariya Yusuf yayi yana cewa
"Kaidai kawai kana jin haushi na this days... Dazun you hit me for nothing yanzu kuma you are eyeing me..." Ya fada sounding funny, kara hararanshi Ayan yayi, relaxing Muhammad yayi Sannan yace
"Guy me zai hana tunda Allah ya shigo damu area dinku yau ka kaimu mu gaisa da ihsan..."
"Yes...exactly what we should do..." Yusuf yayi adding, shuru Ayan yay for a while Sannan yace
"I don't know if I can see her today..." Da sauri Muhammad yace
"Why?..."
"Because of what that guy told me..." Ayan ya amsa mashi idanuwanshi lumshe, Yusuf dai shuru yayi don yasan halin Ayan in har ya fara jin haushin ka to what ever you will say will sound like mockery to him,
"Hope you are not doubting her?..." Muhammad ya tambayeshi cikin nutsuwa, Ayan shafa kanshi yayi Sannan yace
"I don't really know... Kawai dai abinda wannan gayen ya fada gets to me..." Yafada cikin sanyin murya, ahankali Muhammad ya mike shi kam Yusuf sai kallon su kawai yake, zama Muhammad yayi kusa dashi ya dafa kafardanshi Sannan ya fara cewa
"Guy don't let devils ruin your happiness... Kawai ka manta da abinda wannan ya fada maka...let's start having our preparations for the big day ahead..." Shuru Ayan yayi  for a while Sannan ya mike, kallon shi Yusuf yayi ya saki murmushi
"Na meye?.." Ayan ya tambayeshi
"Ba komai...kawai ka shirya muje mu gano princess dinka..."
 Hararanshi Ayan ya karayi ya dauki wayanshi, dailing number ihsan dayayi saving da queen of my heart yayi, daga chan bangaren ihsan dake cikin kitchen tana hadawa kanta assorted indomie saboda tuwo da miyan egusi akayi kuma she's not a fan, ringing wayanta yasa ta ajiye onions din da take slicing ta dauki wayan, ganin mai kiranta yasa ta saki murmushi tare da jinginawa da locker din kitchen Sannan tayi picking tare dacewa
"Allo babyna...." Cikin wani kasaitaccen murya, Ayan najin wannan muryan ya fara mika yana shigewa bedroom dinshi, bayan shi Muhammad da Yusuf suka bi da kallon tare da sakin dariya. Yana shiga bedroom ya kwanta kan gado tare da yin rubda ciki saboda yanda muryanta ya tafi da imaninshi,
"My angel... Ya kike?.." Ya tambayeta cikin whisper,
"Alhamdulillah..." Ta amsa mashi tana rage gas,
"What are you doing?.." Ya tambayeta, cikin nutsuwa ta fara cewa
"Amma cooking for myself..." Lumshe idanuwa Ayan yayi yana imagining lokacin da zata yi mashi abinci kuma tayi serving dinshi Sannan tayi feeding dinshi,
"Hmmm I which tare zamuci..." Dan dariya tayi Sannan tace
"Kazo muci mana..." Shima dan dariya yayi yana dan cizon lebenshi na kasa Sannan yace
"Zakiyi feeding dina?..." Idanuwa ta zaro kaman suna waje daya Sannan tace
"Feeding dinka kaman wani karamin yaro?..."
"Ni karamin yaro ne mana...har yanzu banacin abinci da kaina...kuma da munyi aure dole kiyi feeding dina..." Dariya tayi
"Yanzu sai ka zauna  ka bude baki In baka abinci kaci?..." Ta fada sounding surprised,
"Hmmm..ni feeding dina akeyi...kuma In the next five weeks five days zaki gani ...." Dariya kawai tayi batace kala ba,  Ayan dake kwance kan gado yana mika at the same time yana viewing dinta kwance next to him, yace
"Baby inason in kawo wasu friends dina Ku gaisa...amma zan bari sai next time tunda you are busy..." Da sauri tace
"No...not at all.. Kuzo... Daman I want to see you... " dariya jin dadi Ayan yayi
"Me zaki bani?..."
"Nothing... I just miss your handsome face..."
"Just the way I miss your beautiful and innocent looking face..." Dariya itama tayi don ba karamin jindadi muryan shi ke sataba, jitake duk tafi sonshi kan sauran wayanda sukazo suka tafi, she's feeling as if without him her world would be over.
"To bari in saka kaya muzo..." Yafada Sannan ya katse wayan shi. Itama kashe gas din tayi ta fito falo da sauri Wanda yasa mom ta kalleta
"Har kin gama?.." Ta tambayeta, da sauri ihsan data fara hawan upstairs ta juyo tace
"Ban idaba...yaya Ayan ne zaizo da friends dinshi mu gaisa..." Tafada tana hawan upstairs da gudu, kallon ta mom ta dingayi har ta bace mata, tana mamakin irin son data tayiwa abubakar cos babu Wanda take zumudin gani kaman shi kuma kullum sai yazo amma duk sanda  zaizo fuskan ta zai nuna she's eager to see him.
 Da sauri tahau sama ta yi shower Sannan ta fito ta shafa mai da sauri ta dauki wani swiss lace mai peach da ratsin brown dinki Riga da skirt, batayi kwalliya ba amma her face was flawlessly beautiful. Tana gamawa su Ayan na zuwa, waya ya daga ya kirata ya sanar daita isowansu, da sauri ta fito yafe da Vail Dan karami mai stones, Janna dake zaune kusa da mom ta kalla Sannan tace
"Janna ki shigarmin da su yaya Ayan visitors room.." Tafada tana shigan  kitchen, drinks ta hada ta fito, sai sauri take kaman zata tashi sama mom kam baki ta bude tana kallon ikon Allah.
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💙💚❤🖤💛💜
KAWARTA CE SANADI
❤💚💙🖤💛💜



®zuwairat( ummu Maryam)



1⃣9⃣


Saida ta fita waje Sannan ta daidaita tafiyanta izuwa ta kasaita Wanda ke sa Ayan going secretly insane, dukansu na zaune kan kujeran alfarma dake wurin, Yusuf ne ya saki baki don gani yake kaman wata aljanace cos kyawunta is beyond words, Ayan kam relaxing yayi da jikin kujeran yana shafa well groomed beard dinshi fuskan shi dauke da murmushi yana tunanin mai raba shi da wannan angel sai mutuwa, shi kam Muhammad tunda yaga Janna ya mance da inda yake zaune, gabaki daya ta tafi da imaninshi, sallama tayi ta shiga Wanda haka ya maido Muhammad cikin hayyacinshi, amsa mata sukayi amma banda Ayan da ke wata duniyar don shigarta na yau is quite different, one side of his mine he is jealous, gaida su tayi cikin faraa suka amsa mata cikin jindadi, Yusuf sai murmushi yake ya kasa rufe baki,  bayan sun gama gaisawa ta mike don zuba masu drink, Ayan yayi saurin rike mata hannu kasancewan kusa dashi take zaune, kallon Yusuf yayi Sannan ya wulla mashi harara saboda haushin yanda yake wa ihsan murmushi
"Ga drink mana...ko bazaku shaba?..." Ya fada masu, Dan kallon shi tayi
"Bari in zuba masu, kara hararanta yayi, dariya Muhammad yayi Sannan yace
" kai irin wannan hararan kaman mace...komai harara...to in bakaso mu gaisa da amarya to be ka fada mana mu tafi mana..." Yafada cikin dariya,
"Ku tafi...I don't mind being alone with my baby..." Atakaice cikin zolaya suka dinga hiransu, ihsan kam bata cewa komai saidai tayi murmushi, ko minti talatin basuyi ba lokacin sallan magrib ta gabato, alwallah sukayi daga gidansu ihsan Sannan suka wuce, suna kan hanya Muhammad ya kalli Ayan Sannan yace
"Guy amma baka da hankali..ai da ganin wannan yarinyan she's an angel... So karka bari wani abu ya bata wannan lovely union..."
"Thanks..." Ayan ya fada mashi,Muhammad yacigaba dacewa
"Kuma ni wallahi wannan yarinyan data kaimu wannan wurin tayi min...ka shige min gaba ka gabarta dani...." Bai idaba Yusuf ya saki dariyan rainin hankali yana cewa
"Kaji wani iskanci banza...wai ya gabatar dashi kaman wani ubanshi...kar kaje ka gabatar da kanka ...kilan sai na rigaka...lunatics kawai...." Dariya Ayan yayi shi kam Muhammad banda hararan Yusuf babu abinda yakeyi, shima Yusuf dago big eyes dinshi yayi
"Kai Mr potato head ka bar kallo na..." Yanda yayi magana yasa dukkan su darawa.
 Ihsan na komawa gida tayi sallah Sannan tayi dailing number husna, husna kam bata daga ba amma kaman dole sai da ta jera mata 5 miss call Sannan ta daga kuma ba wai bata kusa da wayanba, asalima wayan na gabanta amma sam batason jin muryan ihsan, kuma tasan da zaran ta kirata bata da wata magana sai na Ayan ita kuma hakan na CI mata tuwo a kwarya, yanzu ji take inama ana yi cire son mutum daga cikin zuciyan ka da da gudu ta cire son Ayan daga cikin ranta cos ba karamin wahalal daita yake ba, kullum kara karewa take kaman kudin guzuri, and the most annoying part he hates her and he's not hiding how much he dispise her and shows how much he loves her best friend, wayanta ne daya fara ringing for the fifth time ta kalla tare da sakin wani hissing kaman snake Sannan tayi picking, one thing about husna is that she's good at what ever she does,
"Amarsu to be..." Ta fada sounding very sweet like honey, bazaka taba cewa hatred and bitterness is consuming her ba.
Daga Chan bangaren ihsan tayi saurin cewa
"Babe naso ace kina gidan nan yau..." Itama da sauri tace
"Ya akayi ne?...ko samuwa ce?..."
"Wallahi yanzu nan wasu gayu suka bar nan wajen..." Gyara zama,
"Which gayu?..." Ta ta tambayeta
"Su Ayan da two close friends dinshi..." Hararan wayan tayi, ihsan ta cigaba dacewa
"Naso ace kinan...gayun sun hadu fiye da zatonki...nasan da babu abinda zai hana daya daga cikin su toasting dinki inda you are around..." Wani murmushin haushi da takaici husna tayi,
"Hmmm....kedai ki kwantar da hankalin ki....na kusa samun Wanda nakeso....babu abinda zai hanani samun shi...." Idanuwa ihsan ta zaro
"Babe Kina da Wanda kikeso ne?..." Ta tambayeta sounding very surprised, dariya husna tayi
"Wanda nakeso kuma?...that's is not what am talking about...I mean Wanda ya zan so...kin gane?...." Shuru ihsan tayi don sam that's is not what she heard
"Kar ki maidani sakara mana...cewa fa kikayi kin kusa samun Wanda kikeso, and you said babu abinda zai hanaki samun shi....pls tell me the truth...kinsan komai fada maki nake...."
"Ke dai kawai you want to misinterpret what I said...." Bata idaba ihsan ta katseta dacewa
"Kedai ki fadi gaskiya...daman this days your attitude have changed..in da akwai Wanda kikeso  ki fada ba sai mu dinga adua ko Allah zaisa ya zama alkhairi?..." Tabe baki husna tayi
"Da gaske babu Wanda nakeso...ai if am in love you will be the first to know...."
"Ai shikenan... Amma ki Sani...I know something is definitely wrong with you... Amma tunda bazaki fadamin ba do problem... Nima sai in daina sharing problem dina dake...." Dariya husna tayi kaman gaske Sannan tace
"Kefa da gaske kike ko?..."
"Am serious... I feel you are not telling me something..."
"Something like what?..."
"You don't want to tell me the person you are in love with..." Shuru ihsan tayi at that moment sai maganan Janna ta dawo mata, what if she's right, ta fada cikin ranta, ahankali ihsan tace
"Ko Ayan kike so!!!!..." Nan take husna ta dafe kirjinta,
"Ayan ne Wanda kike cewa kin kusa samu kuma babu abinda zai hanaki samun?..." Cikin karfin hali husna ta saki wani irin dariya Wanda yasa ihsan cire wayan daga kunnenta for as long as the laughter last,
"Amma ke bakiyiba Wallahi... Waye Ayan?... To for your information babu ma mijin dana tsana kamanshi...." Da sauri ihsan tace

 "tsana kuma?...pls tell me the truth..."
"Yes tsana...you know why I hate him?..."
"No..." Ihsan ta amsa mata atakaice, husna ta cigaba dacewa
"Saboda Marin daya yi maki...I will never forget that...kuma ni bazan iyason namijin da yake daga hannu ya doki mace ba balle mari..."
 Maganan ta ba karamin batawa ihsan rai yayi ba,
"Kinsan maganan gaskiya I don't know you anymore... Kin nuna Ayan is the best and now you are telling me you hate him...kwanki har ruwa kika bani in bashi...anyway you are entitled to your opinion..." Inji ihsan
"Ya kikeson inyi?...you loved him...kuma babu kyau shiga tsakanin masoya...amma har yau ba bar jin karan marin da yayi maki ba...kuma always ina aduan Allah yasa kar ki kara laifin da zai daga hannu ya doki cos naga he's high at times... Kalli last time da fada maki you should go to hell...Allah na gani dukda bani da serious suitor bazan taba son mutum irin Ayan ba...so ki Sani ni bani da Wanda nakeso..." Shuru ne ya biyo baya, ihsan bata rai tayi don haka nan sai taji marin Ayan na kara sauka kunnenta, ita kuma husna tana aduan Allah yasa wannan yayi contributing to their separation,, ahankali ihsan ta cire wayan daga kunnenta ta kashe, tare da kwantawa, ita kuma husna cewa tayi
"Yesssss.." Don tasan maganan ta yayi tasiri.

Ihsan tunani ta farayi, kawai sai ta tsinci kanta da jin haushin Ayan,
"How could I fall for somebody that rise his hand on me...hmmm...he have to promise me never to touch me again..." Tafada cikin bacin rai.

Bayan sallan magrib wasu mata uku suka zo gidansu Ayan, cikin babban mota daya sukazo, alokacin su Ayan sun dawo daga masjid, suna  zaune falo suna dinner dasu Yusuf Matan sukayi sallama suka shigo, daga kai su Ayan sukayi, umma dake zaune mikewa tayi don da ganin Matan sun girmeta kuma da ganin daya mahaifiyarta ce
 Shima Ayan mikewa yayi tare dasu Yusuf sukazo gabansu suka durkusa tare da gaidasu, amsawa sukayi Sannan daya daga cikin matan ta kalli Ayan
"Dada dai zakayi aure...ka gama ruwan idon ko?..." Tafada cikin raa, dariya kawai Ayan yayi baice kala ba, Umma ma gaida Matan tayi Sannan ta wuce dasu saman bene.

Zaune suke a wani katafaren bedroom da gani na Umma ne,  zancen auren Ayan suka fara tattaunawa sai daya daga cikin su tace
"Amma da gaske ne maneman auren yarinyan uku suna fasawa Sannan da karshen nan rasuwa yayi?.." Matar ta tambayi Umma, dan murmushi Umma tayi Sannan tace
"Ikon Allah... Har kunji labarin hakan kenan?..."
"Da gaske ne?.." Tsohuwar ta tambayeta
"Eh haka ne..."
"Tofah...amma kunsan dalilin faruwan hakan?... Ko kawai hakan bai damekuba?.." Tsohuwar ta kara tambayan Umma, shuru Umma tayi
"Tambayan ki take..." Inji wacce ta tada maganan, ahankali Umma tace
"Gaskiya bamu san dalilin ba..amma gaskiya matsalan ba daga yarinyan bane don kowa na unguwan nan sunyi mana murnan da sadeeq zai aureta...."
"Ai gaskiya zanyiwa Yunusa magana akarayin bincike don kar a samu matsala..." Inji tsohuwar. (Yunusa shine baba Ayan, Baban Abba da maman Umma uwa daya uba daya suke..so bayan rasuwan Baban Abba sai Maman Umma ta rikeshi, so ko wanne hukuncin ta yanka is final.).. Ahankali Umma tace
"To shikenan... Daman anyi bincike saidai a kara..."
"Dole kam a kara don ba haka nan maneman aurenta suke ja baya ba...." Tsohuwa bata idaba ba Matan wacce ta tado magana ta fara cewa
"Daya ma mutuwa yayi... Da akwai dalili babba..." Daga cikin su wacce batafiya magana ba tace
"Haba Anty uwa AI don wannan ba wani abu bane...komai ai daga Allah ne..." Daga mata hannu anty uwa tayi
"Nafisat ba dake nakeba..." Tsawa Hajiya babba ta daka masu sukayi shuru Sannan ta mike
"Ina zaki Hajiya?..." Umma ta tambayeta itama tana mikewa
"Yi zamanki..ina zuwa..." Ta fadawa Umma Sannan ta fita. Alokacin Ayan ya dawo daga rakiyan su Yusuf, yana ganin tsohuwar ya saki murmushi tare dacewa
"Old woman ina zuwa ke kadai?..." Ahankali ta karaso inda yake Sannan tace
"Daman bangaren ka zani..." Dariya yayi ya kama mata hannu sukayi part dinshi yana cewa
"Dafatan dai ban yi laifi ba...don ba haka nan kike zuwa nan gidan ba..." Dariya tayi tana tafiyan ta irin da old people tace
"Bakayi laifin komai ba...."
"To shikenan amma kiyi sauri zani zance..."
"To Mara kunya" ta amsa mashi suna shiga part dinshi
 Zama tayi tana karewa dakin da yayi kaca2 da paper Hajiya tayi Sannan tace
"Wayan nan tarkacen fa?.."
"Na aikine..." Ya amsa mata yana  zama kusa daita, kallon shi tayi tace
"Kayi mata zaka manta da tsohuwa ko?..." Dan murmushi yayi tare da shafa kanshi, Hajiya ta cigaba dacewa
"Sai dai abinda ke damuna yanzu shine naji ance duk maneman aurenta fasawa suke Sannan na karshen da bai fasaba mutuwa yayi...ka San da wannan maganan?..." Ta tambayeshi cikin nutsuwa, shuru yayi for a moment Sannan yace
"Nasani..."
"Kuma kayi bincike kan dalilin su nayin hakan?.." Ta sake tambayan shi, Dan bata rai yayi
"Yo ni ina ruwana da wannan... Kawai Allah bai kaddara zaayi dasu ba...nidai grandma nasan koma meye reasons dinsu ba laifinta bane...so wannan ya zama matsalan su..." Ya fada mata in I don't care manner, Dan girgiza kai Hajiya tayi
"Dan nan ba haka ...nasan yarinta ke damunka..."
"Ai grandma nayi bincike... Sam bata da matsala..." Yafada kaman ya kosa da maganan,
"To shikenan.. Amma mudin aka gano wani abu zaa fasa auren don..." Bata idaba ya katseta dacewa
"Hajiya babu abinda zaa binciko sai alkhairi... Kawai I love ihsan...so duk abinda mutane zasu ce is their business..." Tsaya kallon shi tayi for a moment, daman tasan shi da shegen gardama, mikewa tayi tace
"Allah yasa hakan shi yafi alkhairi..." Da sauri yace
"Ameen..." Shima yafada yana mikewa, ko fita baiyiba ya fara kiran ihsan kan ta shirya gashi nan zuwa, amma surprisingly taki daga wayan, don har lokacin tana kwance tana tunanin maganan husna, Ayan kara kira yayi  ta daga amma batayi magana ba,
"Hey baby...am on my way..." Yafada mata cikin sanyin murya,
"Ba sai kazo na yau...ai Baku dade da barin nan ba..." Ta fada mashi atakaice, Ayan daga wayan yayi daga kunnenshi don tabbatar number ihsan ya kira,
"Hello baby is that you?../" tsoki taja Sannan tace
"Bakasan number wacce ka kira bane?..."
"What's wrong?.." Ya tambayeta don yasan something is definitely wrong,
"Hmmm ba komai.. Saidai kawai marin dakayi min ne ya dawo sabo..." Ahankali Ayan ya koma kan kujeran daya tashi
"But you said you have forgiven me... Why are you saying this now..."
"I know I said that amma you have to promise me never to touch me again..." Dariya Ayan yayi
"Touching you is under must.. But hurting you I will not do..." Yafada cikin wani irin murya, shuru ihsan tayi  yacigaba dacewa
"Yanzu can I come and promise what I will and what I wouldn't in person?..." Yafada yana shafa beard dinshi, lumshe idanuwa tayi, kawai sai tace
"This guy is driving me insane...." Da sauri ta kama bakinta don Sam ta mance she's on the phone with him.
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: ❤💜💛🖤💙💚
KAWARTA CE SANADI
💙💚❤🖤💜💛



®zuwairat( ummu Maryam)



2⃣0⃣





Aranar ma sai da Ayan yaje gidansu ihsan ya kara bata hakuri kan babu abinda zaisa shi kara taba lafiyanta ita kuma tayi mashi alkawarin bazata kara fada mashi mganar da zata bata mashi raiba, sai 10 ya koma gida, aranar sai da ihsan ta kira husna kan ta barjin haushin Ayan cos yayi mata alkawarin nothing will ever stand in the way of their love. Wannan maganan data fadawa husna yasa kara yi alkawarin saita raba Ayan da ihsan koda kuwa bazai so taba, balle she already have everything planned according to her wish.

 _2 days later_

Life was now moving smoothly for both Ayan and ihsan cos Ayan ya mance maganan da wannan gayen yayi mashi, bangaren su mom kam dama basu da wata more preparation saboda komai an siyawa ihsan, komai nata is intact.

Side din su Umma kam yan gulma basu bar surutu ba wai Ayan zai auri yarinyan da maneman aurenta ke guduwa wasu kuma suce Ayan zai auri yarinyan da maneman aurenta ke mutuwa, daman Umma da Abba have made up their mind, cos they have been wishing to have a daughter in-law like ihsan,. Kuma kunsan duk yanda unguwake na yangayu baa rasa magulmata da mahassada din har yan cikin Presidential avenue ke zuwa wurin Umma suna yimata gulma kan kar ta bari Ayan ya auri ihsan saidai ta amsa masu da to kawai, kuma wayanda suke wannan maganan sune wayanda suke da yara yanmatan da suke expecting Ayan zai so daya daga cikin yaransu amma sai aka samu akasin hakan.

Ayau alhamis Abba ya bawa Umma check na 1m kan ta sayi kayan lefen auren Ayan,
"Ahhh.. Thanks.." Tafada tana kallon mijinta cikin so da kauna, murmushi yayi kawai ya dauki wayanshi ya kira Ayan, yana fitowa daga wanka ya dauki wayanshi dake ringing ganin Abba ya hanashi
 Picking, da sauri ya saka jallabiya dukda yayi niyyan shirin aiki amma he don't want to keep his father waiting, yana saka kayan wayan ya sake dau Kara still Abba ne, daukan wayan yayi ya fita ya nufi falon Abba, sallama yayi ya shiga falon inda ya tarda Umma zaune da check a hannun ta, kallon Abba yayi Sannan yace
"Abba gani..." Yafada yana zama kasan carpet don yasan muddin Abba yana gida ya kirashi a waya ta wata magana ce zai fada mashi, kallon shi Abba yayi tare da dan gyara zama Sannan yace
"Daman ba komai yasa na kiraka face maganar auranka..." Gaban Ayan ne ya fadi
"This old woman have succeed..." Yafada cikin ranshi tana gyara zama don a tunanin wani abu Abba ya binciko, Abba yacigaba da cewa
"Inason kasan aure ya fi karfin inda kake tunani, wallahi duk yanda zakaji labarin aure bazaka gane ba har sai kayita...so inason kazama mai hakuri in all your situation... Daman it is what I have been telling you... Patience opens doors to anything..." Dan ajiyan zuciya Ayan yayi dayaji inda maganan Abba ya dosa, nasiha Abba ya dinga yi wa Ayan kaman gobe zaiyi auren,
"Ina kara fada maka marriage is not a bed of roses..it has ups and down....so patience is the only way forward.. Don in har baka yin  hakuri bazaka Iya zama da mace for a whole month without breakup ba..." Yafada yana kallon Umma, hararan shi Umma tayi tana murmushi, shima kashe mata ido daya yayi, kan Ayan na kasa don haka baisan abinda suke yiba, makkulin Abba ya dauko daga gefen inda yake zaune,
"Kuma ga keys din gidan...nasa yan zumunta furniture sun zuba maka kaya part dinka...din haka kaje ka gani in case da akwai wasu abubuwa da zaka bukata,..." Ya karasa maganan yana mikawa Ayan keys din, murmushin jindadi Ayan yayi ya taso ya amshi keys din tare dacewa
"Abba nagode...." Hannu Abba ya daga mashi
"Banason godiya you know that... Kawai abinda nakeso gareka shine ka rike yar mutane da daraja..."
"Insha Allah Abba..."
"Good..." Abba ya fada Sannan ya kara dauko wata check,
"Ga wannan... Is 500k...ka chanza wardrobe dinka...kasan you are about to be an ango..." Yafada yana dariya, Umma ma dariya tayi, Ayan kam murmushi kawai yake don gani yake kaman babu uba irin nashi,
"Abba is too much... I ina da enough clothing..." Ya fada cikin sanyin murya, Kai Abba ya girgiza mashi,
"No... Ka amsa..." Yafada yana mika mashi check din, hannu Ayan yasa ya amshi check din tare da karayiwa Abba godiya, Umma kallon shi tayi Sannan tace
"Habibi...Abba ya bada 1m ayi lefen matarka...." Ayan sunkuyar da kai yayi ya karayiwa Abba godiya, tare dacewa
"Abba kayi komai...is too much... Ina da 1.8m a account dina...ka rage saini in Kara .." Yafada cikin nutsuwa, dariya Abba yayi
"Kai that is about to start a family me 1.8 zaiyi maka?...besides it is your right inyi maka auren farko...so is nothing.. Kuma sai ka zabi inda kakeso ayi amfani dashi for the wedding events sai insa a kama wurin in time..." Inji Abba,
"Ok Abba.." Ayan ya amsa mashi, zama yayi bai mikeba, har saida Abba ya sallameshi Sannan ya mike hannun shi rike da keys da check, itama Umma mikewa tayi ta tafi part dinta
 Juyowa Ayan yayi yafaga Umma , d sauri ya dawo gurin ta Sannan yace
"Umma ga check din nan ki Kara Dana lefen...tunda nasan yanzu ban bukatan sutura ko kadan..." Umma bata musaba ta amsa Sannan tace
" ka hada duka check din ka amso kudin don inason in fara siyayya..." Tafada tana Kara mika mashi dukkan check din amsa yayi ya nufi part dinshi, ita kuma Umma ta shiga nata part,
 Umma na shiga part dinta ta kira Hajiya Hauwa dake Malaysia ta fada mata ta turo mata pics din the best shoes, bags, materials, Vail, set da perfumes zata zabawa daughter in-law, daman wurin mata take yiwa su salma da sauran yaranta shopping kuma within one week kayan suke isowa Kano.

Ayan na shiga part dinshi tsale ya daka ya haye kan kujera don farin ciki, waka ya fara yana dailing number ihsan, rawa ya dingayi har tayi picking, da sauri yace
"Yace baby an bani makullin gidanmu..." Yafada mata yana rawa, ihsan dake daure da towel tana drying kanta da hand dryer ta saki murmushi,
"Congrats..." Kawai tace, murmushi yayi Sannan yace
"Yaushe zaki shirya in kaiki ki gano gidanki?..." Ya tambayeta,Dan bata fuskan ta tayi
"What did you say?.."  tafada kaman bataji abinda ya fadaba,
"I said when are we visiting the house together?... Kinsan ya kamata kije..." Yafada yana shafa bayan kanshi Sannan fuskan shi dauke da shuumin murmushi duk da da wasa yake he sounds serious,
"In na amince sai ka dauke ni ka kaini?.." Ta fada tana jiran amsan shi, dariya yayi
"Eh mana..or don't you trust me?..." Kallon wayan tayi amma batace kala ba,
"Well you should trust me.. Cos you are my first and you will be my last..." Murmushi tayi
"Allah yasa..." Tafada cikin sanyin murya,
"My precious I have to go...zan kiraki later..." Yafada
"Ok..."
"I love you..."
"Love you too..." Ta amsa mashi feeling on top of the world for having such person as a lover,  katse wayan yayi ya cire jallabiya ya dauko wasu beautiful jean trousers da wata Riga Wanda jikinta ke kaman jean shima blue sakawa yayi ya gyara fuskan shi, fita yayi daga dakin bayan ya dauki car keys dinshi, fadin haduwanshi is a waste of time amma just imagine a black guy with a very handsome face and well build body
 Sai around 11:30am ya iso bank, Allah ya taimaka babu queue sosai, da wuri ya bar bank bayan ya amshi kudin, gida ya koma ya mikawa Umma kudin Sannan ya nufi hanyan gidanshi.

Bakin wani katon gate ya tsaya ya fito yasa key ya bude Sannan ya shiga mota ya tuka cikin gidan. Gidan ya hadu beyond words duk sakar gidan interlock ne, fadin gidan zaici akalla cars goma, gidan ba bene bane amma is well decorated with flowers daga waje, kofa daya gareta, da ganin gidan kasan babu Wanda ya taba zama cikin ta don komai looks new daga waje, key ya sa ya bude kofan Wanda is double, kofan kanta abin kallo ne, bakin kofan ya tsaya yana kallon wagegen falon Wanda ba komai cikinta sai wasu manyan electric bulb masu kyau da tsada, kasan falon yasha wasu irin manyan tiles farare masu blue flowers, Ayan tsayawa yayi yana imagining yanda rayuwarshi da ihsan zata kasance cikin wannan gidan, kawai jiyake inama she's at home already so that she will welcome him with kisses and hug, ahankali ya taka matakala uku ya takaya  shiga cikin falon, kofofi uku ne one from left and the other from right, then the other one in the middle, na daman ya bude yaga ba komai shima dakin katone sosai sai doors uku, suma, kowanne dakin baccin dauke yake da bathroom dinshi, daga falon farko har na inda yake duka tiles farine sai paint purple and pink, sai pop daga tsakiya,
"My precious part..." Yafada yana komawa baya tare da Jan kofan, na middle ya bude, kitchen ne babba sai store daga nan ciki, kitchen din yasha beautiful kitchen cabinets, shima rufeta yayi ya koma na hagun, yana budewa ya hangi wasu beautiful royalty leather cushion complete set, kayan dakin fari ne tas, dariya Ayan yayi yana cewa
"Sai kace nine amarya?... Wannan kayan sunyi yawa..karfa nawa yafi na precious,.." Ya fadawa kanshi yana dariya, kofa daya ya bude na cikin dakin ya hangi wasu pure white mbf furniture, da katon wardrobe mai six doors, dariya ya karayi yana cewa
"Dole kake bani kudin kaya...wannan wardrobe kaman na unguwa guda?.." Yafada yana bude wardrobe din Wanda ke wayam babu komai sai bedsheets guda biyu,, rufewa yayi ya bude kofan bathroom nauran wanka ne sai washing machine daga gefe.

Komawa falo yayi ya wulla kanshi kan gado tare da lumshe idanuwa. Yafi minti talatin a haka Sannan ya fita daga gidan tare da rufe kofar gidan.

Sai bayan sallan zuhr ya je office, yana isa office din Muhammad ya wuce, Muhammad na zaune yana rubuce2 ya shiga sai kada keys din gidan yake, daga kai Muhammad yayi ya kalli keys din hannun shi
"Guy wannan keys din fah?"
 Cikin yanga kaman mace Ayan yace
"Na gidana..." Tsale Muhammad yayi
"At last...at least zamu kwashi azonto wurin kafin kayi aure..." Baki Ayan ya tabe tare dacewa
"Ashe..." Yafada yana barin office din, da sauri ya Muhammad yabi bayanshi, office din Yusuf yashiga still yana karkada keys, same question Yusuf yayi mashi kuma same answer ya bashi ya bar wajen Yusuf na biye dashi, bai ankaraba Muhammad ya yi kokarin kwace key din, wani irin wawan naushi ya kai mashi, da sauri Yusuf ya rikeshi daga baya, dukkan su kakorin kwace key din suke shi kuma yana rike dashi gam, basu ankaraba aka bude kofa, wata nurse ce, da sauri suka sakeshi, gyara kayan jikin shi yayi ya bar wurin yana bin kowannensu da hara,
"Kar ki kara shigo min office bakiyi knocking ba..." Inji Yusuf,
"Yes sir..." Tafada tana ajiye mashi wata file gabanshi.

Around 3pm Ayan na zaune yana duba scan din wata patient aka bude kofa tare da sallama, daga kai yayi yaga wani babban mutum cikin shiga ta alfarma, hannu ya mikawa Ayan suka gaisa  har lokacin yana tsaye,
"Pls sit..." Inji Ayan yana nuna mashi kujera, mutumin zama yayi ya Dan gyara babban riganshi Sannan ya fara cewa
"Nasan baka San ni ba...ni suna Bello.. Nazo ne da wata magana amma bansan ko hakan zaiyi maka dadi ba..." Ayan gyara zama yayi don jin abinda mutumin yazo dashi, don sam hankalin shi bai kai inda mutumin ya dosa ba, mutumin shuru yayi for a while Sannan yacigaba dacewa
"Dan Allah Dan annabi abinda zan fada maka in har zai bata maka rai kayi hakuri...kasan musulmi dan uwan musulmi ne..."
"Go on am listening..." Inji Ayan that is eager to hear what his visit was all about. Malam Bello Wanda rake yake saidawa amma aka bashi dubu goma kacal don ya fadi abinda zai fada ya ce
" daman maganar yarinya da zaka aurane..." Nan take Ayan ya hade gabas da yamma,
"Ina jinka..." Yafada, yanda ya hade rai yasa gaban Malam bello faduwa, Amma yana tuna dubu goma ya kara gyara zama ya cigaba dacewa
" maganan gaskiya wannan yarinyan bata dace da kaiba... Ba komai yasa na fadi haka ba sai saboda yanda maza ke kawota wani gida kusa da gidana...na samu labarin kai zaka aureta kuma mahaifinka mutumin kirki ne...shiyasa nace in fada maka don in fita don bai kamata in bar Dan da zan iya Haifa yayi zabin da bai kamata ba...amma kayi hakuri in maganar Dana fadamaka ta bata maka rai..." Yafada yana gyara babban rigan jikinshi, Ayan shuru yayi kaman wanda ruwa ya cinye, idanuwanshi sun yi ja Sannan sun ciciko, daga idanuwanshi yayi ya kalli mutumin dake zaune gabanshi Sannan yafara cewa
"Me nayi maku?...menayi maku kukeson rugujemin farin cikina...Ku tuna duk Wanda ya sa wani cikin bakin ciki Allah ba zai barshi haka nan ba...." Ya fada hawaye na gangaro mashi, Malam bello ji yayi jikinshi yayi sanyi amma 10k bai barin shi ya fadi gaskiya, Ayan goge hawayen fuskan shi yayi amma wasu suna biyo bayan wannan, tamkar ya fada mashi gaskiya yaji amma rabonshi daya ya rike 10k har ya mance,
"Dan Allah..." Bai idaba Ayan dake hawaye ya nuna mashi kofa, jiki ba kwari mutumin ya mike ya bar dakin, kuka Ayan ya cigaba dayi bayan ya Dora kanshi kan desk yasan ko a lahira bazaiyi fatan ya auri fasika ba tunda shi ba fasiki bane
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: ❤💛💚🖤💜💙
KAWARTA CE SANADI
💜💛❤🖤💙💚



®zuwairat( ummu Maryam)



2⃣1⃣



Bubbuga kafa ya farayi kasa saboda yanda zuciyanshi ke zafi saboda bakin ciki, at that moment baiki ya cire heart dinshi ya yar ba,
"What if is true?...oh Allah... Ihsan...pls let's this not be true..." Ya dinga fada yana hawaye, daga kanshi yayi ya dauko hanki ya goge hawaye, amma still wasu basu bar zubowaba,
"Ya zanyi da raina?...I need to know the truth.." Ya kara fadawa kanshi, kara maida kanshi yayi kan desk har lokacin hawaye basu bar zubowa ba. Yana zaune bai ankaraba yaji an dauke makullin gidan dake kan table din gabanshi, ahankali ya daga kanshi ya kalli Muhammad da Yusuf da wet face dinshi, da sauri Yusuf ya saki keys din ya dawo kusa dashi likewise Muhammad, Ayan kara fashewa yayi da kuka kaman Dan karamin yaro,
"Subhanallahi!!!." Suka fada tare Sannan Yusuf yayi saurin cewa
"What's the problem?..." Ya tambayeshi sounding very tensed, Ayan shuru yayi bai bashi amsa ba amma bai bar hawaye ba, dafa shoulder shi Muhammad yayi cikin tashin hankali yace
"Wai meye!..." Shima ya tambayeshi cikin dagin murya at the same time yana girgiza shi, ahankali Ayan ya fara cewa
"An ce my ihsan is...a ...whore...." Yafada muryan shi na rawa, da sauri Muhammad ya buga kafa kasa yace
"Oh Allah not again..."
"An kara threatening dinka ne?..." Yusuf ya tambayeshi, girgiza kai Ayan yayi
"No...wani ne yazo ya fada min ana kaita kusa da gidanshi.....I think he's saying the truth..." Yafada yana hawaye, da sauri Yusuf ya girgiza mashi kai,
"Pls don't conclude..." Yafada yana dafa shoulder Ayan, shima Ayan girgiza kai yayi
"Two people can never ba wrong... What if gaskiya suke fadi...guys you know me too well... Bazan...." Bai idaba Muhammad ya katseshi dacewa
"Guy ka bar wannan maganan... That gal is too gentle to be a halort...something is wrong somewhere..."
"Ku fadamin ya zanyi da raina in ihsan karuwa ce...I loved her more than diamond and gold...every beat of my heart is for her...sonta a jinina yake...Dan Allah Ku fadamin ina zan saka kaina inji dadi?..." Yafada yana kara fashewa da matsinacin kuka, Yusuf dafe kai yayi don bai taba ganin Ayan cikin irin wannan yanayin ba,
"Pls stop crying... Let's think... Wallahi kilan karyace..." Inji Muhammad dake magana cikin tension,
"Allah yasa karyace...ban Iya auren yarinyan da wani namiji yayi kissing balle yarinyan da wasu suka devouring..screwed....bleebed...I need a good mother for my children... Inason macen da zata bawa yarana tarbiya mai kyau...pls someone should wake me from this dream ..." Hannu Yusuf ya fallawa shoulder shi bugu Sannan yace
"Look at the way you are crying like you caught her having sex with another man?...kawai wannan maganan is not true...kawai in kanason ta ka to she kunnenka ka aureta..." Ayan daga kanshi yayi ya kalli Yusuf da red eyes dinshi Sannan yace
"Koda da gaske karuwace?..."
"In Allah ya yarda ba karuwa bace..." Inji  Muhammad,
"Yo ko karuwace saime..." Yusuf Yafada in I don't care tune,hararanshi Ayan yayi  amma ko kallon shi Yusuf baiyiba yacigaba dacewa
"Maza nawa suka aurimacen da ba virgin ba?...kuma suna zaune lafiya...kai ka dame mu da wata magana...kuma abun haushi baka San gaskiyan maganan ba amma you are busy wasting your tears... Kawai ko ma meye marry her...zaka samu lada...that is if you truly love her like you always said..." Ya karasa maganar shi batare daya kalli either Ayan ko Muhammad ba, shi kawai abinda ke cikin ranshi ya fada kuma he means it. Ayan nuna kanshi yayi Sannan yace
"Yanzu Yusuf zaka bani shawaran in auri another's man's leftover?..." Ayan Yafada sounding very angry and disappointed, baki Yusuf ya tabe Sannan yace
"Inma da gaske karuwar ce in har ka aureta zaka samu sakayya babba...kuma in ba don kana senseless ba ai da sai ka sa mutumin ya kaika gidan da ake kaita inyaso sai ga zahiri...amma kana zaune anzo an fadamaka magana bakayi bincike ba kazauna kana hawaye... Well in ka gandama ka shika wancan drum da tears... Is your business..." Yafada fuskan daure,baki Muhammad ya bude yana kallon Yusuf, Ayan kam yasan halin Yusuf don haka ko kadan bai bashi haushi, dama Mr straight forward suke kiranshi, hannu Yusuf yasa cikin aljihunshi ya fara takawazai bar office din, amma yana kaiwa bakin kofa ya kara juyowa ya cire hannun shi daya daga cikin aljihunshi ya rike kunnenshi Sannan yace
" am repeating myself... In har you love her...just play deaf and marry for love..afterall har zawarawa da suka haifi yara biyar ana aure balle yarinyan da in tayi gudun tsiya ta haure 20years...a word is enough for the wise...."
"Why are so stupid..." Muhammad ya fada mashi amma hannu Yusuf ya daga mashi
"Pls kayimin shuru Mr potato Head... You know am saying the fact... Lunatic fringe kawai..." Yana kaiwa nan ya barsu ya fice abinshi, kuma ko second biyar baiyiba ya dawo ya dauki keys din gida daya yarda yana cewa
"Babu abinda zamu fasa.. Ko ?...Mr potato head?.." Yayi directing maganan shi to Muhammad
 Wani irin harara Muhammad ya watsa mashi har lokacin hannun shi kan kafadan Ayan dake hawaye har lokacin, Yusuf fasa fita yayi ya tsaya daga nesa da su yana kallon su, Muhammad sai rarrashin Ayan yake shi kam Yusuf tabe baki yayi yana cewa
"Wallahi both of you are so super duper annoying...anyway in kasan bazaka aureta ba pls kar ka fadawa kowa wannan maganan... Ni sai in aureta so that I will find out if she's truly a whore or a virgin....inyaso sai in baku labarin yanda take..." Wannan maganan ba karamin batawa Ayan rai yayi ba, a afusace ya mike ya nufeshi, dariya Yusuf ya kama yana barin office din, juyowa yayi ya kalli Ayan dake bakin office din Sannan yace
"Wallahi am serious..." Yafada yana shigewa office dinshi, Ayan komawa ciki yayi ya tsaya ya rasa abinda ke yi mashi dadi,
 Ahankali Muhammad ya nufoshi ya kara dafa shoulder dinshi Sannan yace
"Guy ka kwantar da hankalin ka...am sure wannan gayen daya yi threatening dinka is behind this... Just keep calm...that gal loves you and you loves her too..." Yafada mashi cikin natsuwa, kallon Muhammad yayi with red eyes dinshi Sannan yace
"Har yanzu Baku gane inda na dosa ba...what if what they are saying is the truth?... What if she's what they say she is?...pls advise me...." Muhammad dawowa yayi gabanshi ya Dora two hands dinshi kan shoulders dinshi Sannan yace
"Pls forget all they said...tunda kana son ta..am sure karya suke...ka bari ka aureta..." Ya fada mashi suna kallon eyeball din juna, Ayan shuru yayi baice kalaba,
"Muje muyi sallah..." Inji Muhammad, hannuwan Muhammad yadan ture daga shoulder dinshi ya shiga bathroom din office, wanke fuskan shi yayi amma duk Wanda zai ganshi sai yasan something is definitely wrong, alwallah ya dauro ya fito, shima Muhammad office dinshi ya koma yayi alwallah.



Mal bello na fita daga office din Ayan ya karya corner, wata adaidaita ce tsaye daga ciki gayen da husna ta taba turo wane sai kuma husna ne zaune suna ji ranshi,   ahankali ya karaso kusa dasu jikin shi ba kwari,
"Kai ya ?...anyi nasara?..." Gayen ya tambayeshi, mal bello kallon su yayi one after the other Sannan yace
"Gaskiya bakuyi min adalci ba...yau kunsa na shiga hakkin wani...kunsani nasa wani kuka...." Yafada kaman zaiyi kuka wani irin disgusting look husna tayi mashi Sannan tace
"Dalla Malam ka fadamana...anyi nasara?..." Kai kawai ya daga masu Sannan yace
"Naga kaman ya yarda...yana kuka na baro wurin...", nan take tayi relaxing jikin kujera adaidaita  tana murmushi at the same time idanuwanta lumshe,
" finally.. Finally.. Finally... " tafada sounding very excited, gayen dake zaune kusa da husna ya sa hannu cikin aljihunshi ya dauko dubu goma ya bawa mal bello Sannan yace
"Yanzu ka zagaya chan ka Ciro min kayan jikinka..." Yafada yana wulla mashi wasu kazaman kaya cikin Leda, mal bello amsa yayi ya dan shiga wani wuri ya chan kayan shi, husna kam batasan abinda sukeyi ba, kawai kiran ihsan take jira as usual.
"Pls call... I want to hear that your excitement vanish...I want to hear you cry while saying babe Ayan have change his mind about our marriage.." Ta fadawa kanta, mal bello dawowa yayi da kayan da aka bashi ya saka ya mikawa gayen Sannan suka tafi.

Ihsan kam yau bata da lectures so tana gida sai dirka mata kayan gyaran jiki da niima mom take, tana zaune falo da cup din magani da mom ta bata sai sha take amma tana kokarin amai, tana sha tana kallon agogon dakin, tana tunanin yanzu kusa hours biyar kema basuyi waya da Ayan ba, which is on like him, sai kuma ta tuna yace mata anbashi keys din gida so anata tunanin yana busy ne, har 4:30 basuyi waya ba, ajiye effizzy tayi ta dauki wayan ta ta hau upstairs tana dailing number dinshi, alokacin Ayan yana driving jin ringing din wayanshi yasa ya dauki yana kallon sunan dake yawo kan screen din wayan, precious, ajiye wayan yayi bai yi picking ba, don at that moment he don't want to talk to her, kawai he wants to be left alone, ihsan najin baiyi picking up ba ta ajiye wayan tare da Dan kwantawa tana tunanin kilan yau aikin is too much.
 Ayan gida ya shiga tare da shiga part dinshi, kwantawa yayi yana tunanin  abinda ke faruwa, sai juye2 kawai yake ko kadan babu sukuni tare dashi, har 6:30  bai je main house ba, Umma ce ta kirashi a waya kan ya shigo ciki, mikewa yayi yana takawa a hankali kaman Wanda bayason taka kasa yashiga falon Umma, Umma na ganin shi ta gane something is wrong
"Son lafiya?.." Ta tambayeshi tana kallon shi, murmushin karfin hali yayi
"Ba komai..." Yafada yana zama gefen Umma, Umma kara kallon swollen red eye dinshi tayi
"Don't tell me ba komai... Meke damunka?..." Ta tambayeshi,
"Wai Umma me nayi?..."
"You eyes shows you have cried..." Dariya yayi kaman gaske
"Kuka kuma?...ni banyi kuka ba...kawai dazun wani abu ya shige min ido..."
"To shikenan... Kaje kaci abinci.. Zai kazo muyi selecting kayan da kake ganin zai dace  da ihsan..." Shuru yayi baice kalaba,
"Kaji.." Umma takara fada mashi, ahankali yace
"Umma duk abinda kika zaba is ok..." Yafada yana kokarin mikewa, yanda yayi maganan ya kara jaddawa Umma da akwai matsala, da sauri Umma ta ja hannun shi
"Sit down.." Ta umarceshi, babu musu ya zauna
 "What's wrong?.." Ta sake tambayan shi,
"Umma da gaske am ok... Kawai am a little bit exhausted... That's all..." Kura mashi ido Umma tayi din she wants to know if he's saying the truth
"To then go and eat before we select your brides clothing..." Tafada mashi atakaice, bai ce komai ba ya mike ya nufi dinning kaman Kazan da kwai ta fashewa a ciki, daman already antymu tana zaune kan dinning tana jiranshi, kallon ta yayi ya matsa kusa da kunnenta Sannan yace
"Little sis...banjin yunwa...pls kar ki bari Umma ta gane banci abinci ba..." Ya fada mata cikin kunnenta, itama cewa tayi
"Why?.." Tafada the same way shima ya fada
"Na ci abinci gidan su Muhammad..." Yayi mata karya,
"Ok.." Tafada, daman dinning area bai kallon inda Umma take zaune don haka Umma batasan baici abinci ba.

Bayan  minti talatin ya koma falon
"Umma zanje masjid..." Ya fada mata yana tsaye,
"To in ka dawo kazo muyi selecting ...."
"Umma pls do it.. Ko kuma ki kira su salma da sameera daga gidansu su taimaka maki ...ni basan abinda zaiyi mata kyau ba..." Baki Umma ta bude tana sauraron shi
"Sadeeq..kai dakewasu salma online shopping shine kake yimin karya?..."
"Ai Umma su salma kikace...wannan kam I don't know what will suit her..." Umma bata kara cewa komai ba
"Umma na tafi..." Yace mata Sannan ya fita.

Ihsan kam jiran zuwan Ayan kawai take don tunda suke bai taba tsallake rana ba, hakan yasa tana gama sallan magrib ta shiga bathroom ta yi wanka ta fito ta mulka jikin ta da perfumes da wata sister mom ta kawo mata dazun,  Sannan ta shirya cikin wani hadadden black Arabian gown. Kwalliya ta zauna ta tsara kaman wacce zata outing.

Abangaren husna kam jiran kiran ihsan kawai take as usual kaman yanda ihsan ke kiranta ta sanar daita matsalan ta amma shuru, har 6 bata kirataba, ta zauna ta ajiye wayan ta a gabanta tana jiran ringing har  bayan sallan magrib ganin bata kirataba yasa ta yi dailing number ta
 💙❤💜❤🖤💛💚
Kuyi hakuri, aikin is three much for me, love you all
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💛💙💜🖤❤💚
KAWARTA CE SANADI
💛💚❤🖤💜💙




®zuwairat( ummu Maryam)



2⃣2⃣




Ihsan dake zaune gaban mirror tana kwalliya taji wayanta na ringing, da sauri ta mike don a tunanin ta Ayan ne, tana daukan wayanta taga husna ce, haka nan sai jikinta yayi sanyi cos she wasn't expecting her, jiki ba kwari tayi picking tare dacewa
"Babe how far?.." Daga chan bangaren husna saurarawa tayi ko zataji tension cikin muryan ta amma sai tajita normal
"Wallahi fine...ya kike?.."
"Am great... Meye labari?..." Ihsan ta tambayeta tana komawa kan mirror,
"Lau...ya ango to be?..." Ta tambayeta don jin amsarta
"Yana lafiya...yanzu ma makeup nake...he's on his way..." Ta fada mata tana kallon beautiful face dinta cikin mirror, baki husna ta tabe,
"Allah ya samu a danshinku..." Tafada tana dariyan da baikai makoshinta ba,
"Ameen... Bari in gama makeup.. Kar yazo ban idaba...you know I always wants to look gorgeous before him..." Tafada cikin zolaya,
"Su looking gorgeous manya... Mu dabamu da wayanda zamuyiwa kwalliya sai mu ce me?.." Dariya ihsan tayi
"Bawai baki da su ba...kawai kice baki basu dama ba...remember wannan course mate dinmu...." Tafada cikin zolaya again, hararan wayan husna tayi tare da tabe baki
"Ai wannan ba ajina bane...when I see my class I know... Kuma naga wani dazun..." Da sauri ihsan ta daka tsalle tana cewa
"Da gaske?.."
"Eh..he's cute.. Handsome... Amma fa baisan inason shi ba...." Da sauri ihsan tace
"I knew it....shine baki fadamin ba sai yanzu... In nice you will be the first I would told..."
"Ai ina jin kunyan in fada maki...inason Wanda bai San da zamana ba..." Ahankali ihsan tace
"Haba babe...meye abun kunya....kawai muyi ta adua Allah yasa ya zama alkhairi..."
"Hmmm...to ki tayi ni da adua wallahi in ban sameshi ba mutuwa zanyi..." Idanuwa ihsan ta zaro
"In Allah ya yarda zai soki... Kawai keep praying... Kin fadawa mami?..."
"Aa...ke kadai na fadawa...kema saboda amincin dake tsakanin mu..." Dadi ihsan taji don a ganin ta her friend is telling her what she felt is a secret,
"Allah ya zaba mana...abinda yafi alkhairi..." Inji ihsan,
"Ameen...." Husna ta fada tana kashe wayanta, kumbura tayi don na karamin tashin hankali tashiga ba, ita she was expecting ihsan zata fada mata wata magana kan sun samu matsala da Ayan amma sai taji wai kwalliya take tana jiran zuwan shi,
"Wallahi I won't give up...Ayan is mine..." Yafadawa kanta wasu zafafan tears na gangarowa daga idanuwanta.

Ihsan na gama kwalliya ta yi sallan ishai cos tana da alwallah, tana idar da sallah ta dan kwanta tare da rike wayanta a hannun ta, kallon agogon dakin tayi taga quarter to 8, hakan nan sai gabanta yafara faduwa saboda tunda suke basu taba kaiwa kaman haka basu yi wasu sau uku hudu ba amma gashi bai kirata ba Sannan ta kirashi bai dauka ba Sannan he didn't callback, kawai  sai ta fara cewa
"Allah yasa lafiya...."
 Juya kwanciyar ta tayi tana lumshe idanuwanta.

Ayan kam tunda ya tafi masjid yayi sallan magrib bai dawo gida ba, gefe daya ya zauna ya hada kai da gwaiwa yana fadawa Allah damuwanshi, yana nan har akayi sallan ishai Sannan ya nufo gida, tafiya kawai yake amma Sam hankalin shi baya jikin shi, yana zuwa kofar gidansu ya tsaya yana kallon gidansu ihsan daga inda yake, hannun shi ya maida cikin aljihunshi ya tsaya nan yana kallo gidan, he's feeling as if he should see her, kawai gida ya shiga.

Few minutes later ya kwanta amma sai yaji he can't sleep with out seeing her, wayanshi ya dauka ya kalli time yaga after 8, dailing number ta yayi ko yaji muryan ta ya samu sauki, ihsan dake kwance rike da wayanta naji first vibration before ringing tayi saurin picking tana cewa
"Baby..." Kaman zatayi kuka, Ayan lumshe idanuwa yayi tare da cewa
"Yes precious..." Da sauri tace
"What did I do?..." Ta tambayeshi kaman  tasan da akwai matsala sai ta fashe da kuka,
"Precious me akayi?..." Ya tambayeta cikin tashin hankali don yana jin muryan ta ya mance da abinda ke faruwa, cikin kuka ta fara cewa
"Tunda da safe...sau daya kawai ka kirani....kuma na kiraka...baka dauka ba...and I have been waiting for you... Baka...zoba..." Tafada tana kara fashewa da wani sabon kuka, da sauri Ayan ya mike zaune yana dafa kirjinshi
"Am so...sorry precious... Am sorry...." Yafada muryan shi na rawa kaman zaiyi kuka, cikin kuka tace
"Sorry for what?..."
"Sorry for making you cry...I don't want to hear or see you cry...precious pls stop crying..." Yafada hawaye na gangaro mashi,
"Zakazo?.." Ta tambayeshi tana murmushi at the same time tana share hawayen fuskan ta,
"Precious... Bazan taba yafewa duk Wanda ke son...." Sai kuma yayi shuru, da sauri ihsan ta zauna tana cewa
Wanda ke son me?..."
"Nothing..." Yafada yana daidaita muryan shi, kara fashewa tayi da wani sabon kuka tana cewa
"Wallahi sai ka fadamin..." Kawai Sai ya fara dariya,
"Nothing... Kawai ki fito waje ni ma zan fito...yau kar mu hadu gida...let's meet on the street..." Yafada mata cikin wani irin muryan da bata sanshi dashi ba,
"Bazan iya fitaba...kawai kazo..." Tafada cikin shagwaba, murmushi yayi yana tunanin bazai iya rabuwa daita for any reason in the world, the love he have for her is geniu and pure,
"No precious just come out... Yau banjin dadi...I just need to see your face...." Ya umarceta, shuru tayi kaman mai tunanin wani abu Sannan tace
"Ok..baby..anything for you..." Tafada tana murmushi, shima murmushin yayi
"Are sure anything for me?.." Ya fada yana tuna maganan da aka fada mashi, shuru tayi bata ce komai ba
"Ki fito am coming now..." Yafada yana katse wayan. Bai bata lokaci ba ya saka palm sandal ya fito.

Itama ajiye wayan tayi ta kara gyara fuskan ta tare da kara fesa turare Sannan ta yafa Vail din rigan data saka ta fito, duk Wanda ya ganta sai yayi tunanin ganin sarki zata, sai walkiya take, falo ta sauka ta tarda mom da su Janna,
"Mommy zanje wajen yaya Ayan..." Ta fadawa mom, kallon tayi Sannan taji irin kamshin da take,
"Habibty kin fara shafa wannan perfumes ne?..." Kai ta daga mata tare dacewa
"Eh mommy..."
"Pls don't use it when you are going out..."
"Ok..." Kawai ta fada ba tare data San dalilin dayasa ta fadi hakan ba,  da sauri ta fita ta bude karamin kofan gate ta fita, tana fitowa kaman yana jira ya rike mata waist, ba karamin firgita tayi ba, da sauri ta dauke hannun shi tana cewa
"Stop it..."
 Ta fada tana waige2, tsaya kallon yanda ta hade rai yayi yana tunanin ayya ba sharri ake jawa precious dinsa ba?, marairace fuska yayi tare dacewa
"You said anything for me..." Turo baki tayi Sannan tace
"Yau me nayi maka ka kyalleni?..."
"Nothing precious... Kawai I was exhausted..." Lumshe idanuwa yayi yana shakan kamshin perfumes dinta daya bade inda take tsaye,
"You are looking more beautiful... Meye sirrin..." Murmushi tayi tare da  dan hararanshi,
"Babu komai...dazun you were saying something...." Da sauri yace
"Something like what?.." Yafada yana kallon glowing face dinta, at that moment she was driving him to insanity, ji yake kaman ya dauketa kawai ya tafi daita, for that moment he forget all he worries about.. Farat daya ta yaye mashi damu,
"You are magical..." Yafada mata, Dan bubbuga kafa tayi tace
"Pls ka fada min abinda kaso fadamin dazun kan waya?..." Ta kara fada kaman zatayi kuka, dariya yayi yace
"Babu komai..."
"Nidai nasan you are not saying the truth..."
"Na mance "yafada don ko kadan bayason tuna wani abu, he just want to enjoy the moment,
" you were saying something like..bazaka yafewa duk Wanda ke son..." Kura mata ido yayi, kuma for that moment he wants to ask her if she have someone else apart from him amma sai wata zuciya ta hanashi
"Cewa nayi bazan yafewa duk Wanda ya kalleki ba..." Ya yi mata karya, kura mashi ido tayi shima ya kalleta, at that moment ji take nothing matters except him, sunfi minti biyu suna kallon junansu, kawai sai maganar wannan gayen da Bello suka fara yawo cikin kunnenshi, da sauri ya dauke kanshi daga ya fara kallon gefen street, kara daga kanshi yayi ya kalleta Sannan yace
"Precious can I ask you a question?..." Yafada yana kurawa lips dinta ido acikin ranshi yana Allah yasa kar wani ya taba shan wannan bakin, ahankali ta gyada kai,
"Kina iya aure na in ina Neman mata?...." Bai idaba ta zaro idanuwa,
"Kaman ya Neman mata?..." Ta fada kaman an fixgi maganan daga bakinta,
"Kaman in dauki matar banza in biya bukatata daita..." Ya Kara fada,  ihsan sauke kanta kasa tayi don haka nan sai taji maganar babu dadin ji, girgiza mashi kai tayi,
"Bazaki iya aurena a hakan ba?.." Ya sake tambayan ta, wannan Karin maganar ta Sosa mata rai, ahankali ta daga idanuwanta ta kalleshi,
"Pls ka fadamin gaskiya... Kana Neman mata ne?..." Dariya ne ya kufcewa Ayan, nun kanshi yayi
"Me?..." Turo baki tayi
"Ai you are making me worry...kawai muna cikin hirarmu mai dadi ka kawo maganar neman mata...ai dole in damu..." Dariya ya karayi
"To ki kwantar da hankalin ki...ki zaki cireni a Leda...." Bata fuska tayi tare da juya mashi baya, da sauri ya dawo gabanta bayan ya gaba karewa bayanta kallo,
"Me nayi?.." Ya tambayeta,
"Ni ka bar fadamin irin wannan maganan... Banaso..." Kura mata ido yayi yana son gano if she's saying the truth,
"Yanzu precious don na fadi wannan maganan sai ranki ya bace bayan nan da sati biyar b this time you will be lying next to me...naked..." Bai karasa ba ta nufi gate dinsu, da sauri ya kama hannun ta, ta fixge ya kara kamawa wannan Karin da karfi ya jawota baya ta tsaya daf dashi har suna shakan numfashin juna, ja da baya tayi, shi kanshi baisan dalilin dayasa yake behaving hakan ba amma kuma he has to be sure,
"Yanzu precious ni zakiyi abandoning?..."  Yafada yana kallon yanda ta kumbura tana Neman fashewa,
"To kiyi hakuri bazan kara fadan irin wannan kalaman ba...yanzu back to business.. Baki bani amsar tambayan danayi makiba..." Ya tambayeta sounding formal
"AI na baka amsar..."
"No banjiba..."
"To..bazan iya auren mazinaci ba..." Tafada a takaice, wani irin ajiyan zuciya ya saki Wanda yasa ihsan kallon shi,
"To I have another question?..."
"Inajinka.." Tafada tana harde hannuwanta kan kirjinta, yacigaba dacewa
"Yanzu ace nine ihsan...kece Ayan... Zaki iya aurena...in ni yar iska ce???." Wannan tambayan yasa ihsan daga kai ta kurawa Ayan ido
"Wane irin tambaya ne wannan?.." Ta tambayeshi tana kallon shi ko kiftawa batayi, kallon idanuwanta yayi yaga annoyance kwance kan fuskan ta, da sauri yace
"Don't be offended... Dazun mukayi gardama da friends dina kan irin wannan maganan shine muka bawa kanmu assignment...  pls tell me..." Dan kallon shi tayi Sannan tace
"Bazan iya aurenta ba..." Tafada mashi atakaice sounding firm and sure,
"To in baki Sani ba...ko kuma anata fadamiki yar iska ce sai kika ki yarda Kika aureta only to find out she's not a virgin ...me zakiyi?..." Kara kallon shi tayi tana cewa
"Pls where is this coming from?..." Ta fada sounding tensed, da sauri ya kama shoulders dinta biyu tayi saurin buge mashi hannu ya saukesu tare da dariya Sannan yace
" pls just tell me.."
"Well gaskiya in ban yarda da itaba bazan aureta ba...so in any situation na sameta ina iya hakuri in zauna daita..." Ayan kura mata ido yayi for a moment Sannan yace
"Kina nufin kina iya zama daita bayan kin gano she's another man's trash?...well ni bazan Iya ba...duk wacce na aura...in har she's not a virgin.. On our first night zan saketa!!" Yanda yayi maganan cikin daci yasa ihsan kura mashi ido, kawai sai ta fashe da kuka tana cewa
"What are you saying?..."
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💙💚💜🖤💛❤
KAWARTA CE SANADI
💜💛❤🖤💚💙



®zuwairat(ummu Maryam)




2⃣3⃣



 *Zan fara lissafo masoyana, guest who am starting with* ... *My sweet, lovely,understanding, educated, nice, caring,* *all loving, wise, civilise* _ANTY ZAINAB_
 *(ANTY SIS)*

This page is all yours, love you wujiga wujiga♥♥💋

Ayan kura mata ido yayi yana kallon ta with adoration kuma at the same time yana mamakin abinda ke sata kuka, ihsan sai kuka take kaman wacce akayiwa albishir da mutuwa, gyara tsayuwan shi yayi Sannan yace
"Precious... Why are you crying..." Ya tambayeta yana cire hannun ta data rufe fuskanta dashi,  fixge hannun ta tayi tacigaba da kuka,
"Kodai da gaske ne?..." Ya fada cikin ranshi,
"Pls precious tell me why you are crying....banason kukanki..." Hararan shi tayi tana cewa
" haka nan sai kace zaka saki mace saboda kasameta ba budurwa ba?... " idanuwa ya zaro
"Gaskiya bazan iya zama da sauran wani ba..." Kara hararan tayi
"Kasan dalilin faruwan haka gareta?..."
"Tofah...so you are serious... Kina nufin in zauna da macen da ta gama yawon duniya?...Wallahi bazan iyaba..." Ihsan goge fuskan ta tayi tana tuna wata cousin dinsu da akayi wa fyade sai kuma wasu sabbin hawayen suka kara zubowa,  Ayan Dan bata fuska yayi Sannan yace
"Is there something I should know?..." Kallon shi tayi da wet face dinta Sannan tace
"Su wayanda basu da budurcin ba zasuyi zaman aure ba kenan?..." Ta tambayeshi tana hawaye,
"Zasuyi zaman aure amma ba a gida na ba..." Shuru tayi bata kara cewa komai ba amma data goge fuskan ta sai wasu hawayen su zubo, Ayan kallon ta kawai yake
"Precious..." Ya kira ta cikin wata irin murya, daga kanta tayi ta kalleshi Sannan yace
"Ke ba budurwa bace?..." Ya tambayeta cikin wani irin murya mai dauke da wata maana, ihsan zaro idanuwa tayi zata bude baki tayi magana amma sai ta kasa,  kara matsawa kusa daita yayi ya kara cewa
"Pls is it true?..."   Kallon mamaki tayi mashi don ta lura da gaske yake,
"Wane irin tambaya ne wannan?... Na lura da akwai abinda you are not telling me....fada maka akayi ni yariskace?..." Da sauri Ayan yace
"No...kawai naga your attitude change kawai don nace bazan zauna da wacce ba budurwa ba...."
"Kuma is that enough reason ka yi min wannan tambayan?..." Dan daure fuska yayi
"Laifi nayi don na tambayeki?...ni bana fada maki am a virgin ba?..ni dai kawai ki fadamin.." Itama bata rai tayi
"Basani ba!..." Ta fada cikin tsiwa, juyawa tayi zata tafi ya kara riko hannun ta,
"Precious don't take it too harsh...to kiyi hakuri... Kawai yanda kike kukan nan ne ya tadamin hankali,..." Fixge hannun ta tayi daga nashi ta kalleshi Sannan tace
"Ni wata nake tunawa...." Da sauri Ayan yace
"What happened to her?.." Hararan shi tayi tare dacewa
"Ban saniba....pls let's talk something more important..." Dariya yayi yana cewa
"Ai wannan is more important to me than you think..." Dan buga kafanta tayi Sannan tace
"Ni zan shiga gida cos my legs are getting weak...banason tsayuwa..." Kura mata ido yayi yana kallon ta yana lumshe idanuwa Sannan yace
"Wannan turaren nan naki is something else... I love it...hope zaki rage Wanda zaki dinga shafa min a gida..."yafada sounding naughty, Kauda kanta gefe tayi tana murmushi cikin ranta tana cewa
" ai don kai din aka hado turaren..."
"Precious... I love you... I wish we are married already...." Murmushi ta karayi Sannan tace
"Why?..." Tafada tana lumshe idanuwa, matsawa kusa daita yayi Sannan yace
"So that I will explore every inch of you body..
" turo baki tayi tana cewa
"Ni ka bar fadamin irin wannan maganan..."
"Na bari..." Ya fada yana yana murmushi.
 Haka suka dinga hararsu ta masoya kaman ba Ayan dake kuka saboda abinda aka fada mashi ba, sunfi hour uku tsaye Sannan daga baya sukayi sallamada juna ba don Ayan ya so ba. Yana kan hanyan komawa gida ya fara tunanin bai kara bari waniya shiga tsakanin shi da ihsan, yasan with out her his life is meaningless,
"Duk shegen daya kara yimin maganar ta shi ya jawa kanshi matsala..." Ya fadawa kanshi.

Ihsan kwantawa tayi bayan ta cire kayan jikinta, one thing about her is that bata fiya bacci da kaya ba, tunanin hirarsu da Ayan ta farayi, tana tunanin shikenan duk macen da bata da budurci mijinta bazai so ta ba? Koda kuwa ba yar iska bace,
"Hmmm...nasan duka maza ba kaman Ayan sukeba...am sure da akwai wayanda zasu yarda da kaddara. Haka ta dinga tunani har bacci yayi gaba daita.


Husna kam yanda ta ga rana haka taga dare, tana tunanin Ayan wane irin mutum ne, tasan duk sauran samarin ihsan da anje an fada masu karya suke hakura da da ita amma shi Ayan is different, daman ko sauran ba sonta suke ba?, kokuma basu Isar da sako yanda ya kamata ba? Juya kwanciyan ta tayi tana kallon ceiling, kallon agogon bangonta tayi taga 2:30am,
" wallahi sai ka soni... Wallahi sai na tabbatar ka tsani wannan shegiyar...wallahi you must love me...you are my man..I don't mind killing that idiot to have you... Ayan you are the one for me... " Tafada tana kuka sosai, rungume pillow dinta tayi kaman ta rungume Ayan, sai kissing pillow take tana kuka tana cewa
"Pls ka soni..kar in aikata abinda yafi na da muni..Ron Wallahi bazan iya rayuwa in ganka da ihsan ba...it will be over my dead body..." Ta fada da karfi tana wurgar da pillow data rungume, kasa ta dawo ta kwanta nan kasa tana kuka kaman ranta zai fita,
"Allah why are you punishing me?...nasan am an asshole amma wannan hukuncin is too much.... Ka cire min sonshi ya Allah ko kuma wallahi in kashe ihsan...wallahi Allah ka cire shi daga raina and I promise to let them marry in peace ko kuma wallahi sai na hallaka duk macen dayace yanaso..ko da kuwa uwatace..." Tafada da karfin not minding the time. Ji tayi an bude kofanta, da sauri ta daga kai ta kalli mami dake sanye da kayan bacci amma daure da zani, gani yanayin da yarta ke ciki yasa tayi sauri karasowa cikin dakin tana t
"Baby..what is the problem?..." Ta tambayeta tana zama nan kasa tare da tallabo wet face dinta, husna bata amsa mata ba sai hawaye take tana rike hannun mami dake gefen kunnuwanta,
"Baby pls talk to me...am your mother... Meke damunki?..."
 Ta tambayeta cikin tashin hankali cis bata taba ganin ta haka ba,
"Pls talk to me..." Ta kara tambayan ta, ahankali husna ta dauki hannun mami ta dora kan heart dinta dake beating extra fast, idanuwa mami ta zaro dataji yanda heart din yarta ke harbawa kaman zai fito waje,
"Inna lillahi... Baby what is wrong?... Why is your heart beating very fast?...pls talk to me..." Tafada tana kurawa yarta ido, husna babu bakin magana cos ko a mafaraki bazata taba fadawa mami Ayan Wanda ihsan zata aura take so ba, tasan mami tafi ji da ihsan fiye daita,  kuka ta dingayi tana dafa kirjinta, cikin tashin hankali mami ta fita don kiran Baban ta, husna kwantawa tayi nan kasa tana kuka tana shure2 da kafafunta kuma hannuwanta biyu kan kirjinta, few minutes later Baban ta yashigo tare da mami, dagata yayi zaune yana tambayan ta abinda ke damunta amma bata cewa komai sai kuka, nan mami ta fashe da kuka tana cewa
"Alh...ka kira doctor... Kar zuciyar yata ta fashe...something is wrong.." Tafada tana amshe husna dake kan cinyar babanta, mikewa yayi ya kira number family doc amma switch off. Dawowa yayi dakin yana cewa
"Number shi bai zuwa...kawai tashi ki chanza kaya munkaita hospital..." Inji Baban husna, da sauri mami ta mike ya shiga dakinta ta sanya long hijab Sannan ta shiga dakin kanwar  husna dake sharara baccin ta batare datasan abinda ke faruwa ba ta shaida mata zasu kai husna hospital, itama dakin tazo ta ga yayarta sai kuka take tana
"Wayyo.. Xuciyata....wayyo.. Ku cire shi in huta..."  Durkusawa tayi gabanta tana
"Anty lafiya?...meke damunki?..." Husna banza tayi daita ta cigaba da kukanta, ciki wardrobe dinta mami ta shiga ta dauko gown ta saka mata tare da hijab Sannan ta rike mata hannu suka fita har lokacin bata bar kuka ba.

Sai wajen karfe 3am suka iso hospital kasancewan it is a little bit far from their home, suna zuwa aka amsheta.

Bayan an gwaje2 doc dake duty ya gano tana Neman samun heart attack nan mami ta Dora hannu bisa kai ta fara kuka tana cewa m"na shiga uku...ban cikin masu yara da yawa...why me?...." Ta fada cikin kuka . Baban husna rarrashin ta ya dinga yi.

Karin ruwa akayi mata tare da alluran bacci nan take yayi gaba daita.
 Wannan ranar husna tayi bacci sosai don bata farka ba har karfe goman Safiya, mami gida ta koma ta shirya tare dasa masu aiki su dafawa husna abinci Sannan ta kira mom da sauran mutane ta sanar dasu husna na hospital.

Alokacin da aka kira mom tana zaune falo itakuma ihsan tana zaune kan dinning table tana breakfast don in har bata zuwa school to sai ta kai 11 na safe bataci abinci ba. Tana jin mom tace
"Subhanallahi.." Ta maida hankalin ta kanta tana sauraron wayan da take, aikam tanajin abinda ke faruwa ta fashe da kuka tana cewa zata tafi hospital din, da kyar mom ta shawo kanta ta yarda ta jira mom  ta shirya Sannan suka tafi tare , suna cikin tafiya kasancewan mom ke tukin, wayanta dake ringing ta fiddo tayi picking, Ayan ne
"Precious.. Na iso office.. How are you?...kinyi breakfast?.." Ya tambayeta, kuka ta fara yi Wanda yasa mom kallon ta, cikin kuka ta fara cewa
"Hospital zamu...an kwantar da husna..." Jin kuka ihsan yasa hankalin shi ya tashi.
"Who is husna?..." Ya tambayeta, dukda tana cikin tashin hankali sai data ta harari wayan Sannan tace
"My bestie..."
"Oh sorry... Na mance...is that why kike kuka?..." Maganan shi batawa ihsan rai yayi kawai sai ta kashe wayanta ta cigaba da kuka.
[11/22, 8:08 PM] Re@l Zuw@ir@t✍🏼: 💛💜💚❤♥💙
My angels kuyi hakuri, am so super duper busy ,am ai kunsan inason Ku ko?, naga wata tayi murmushi, keep smiling, thanks for the love
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: 💛💜💚🖤💙❤
KAWARTA CE SANADI
💙💚💜🖤💛❤



®zuwairat( ummu Maryam)



2⃣4⃣



 _This page is dedicated to my sweet_ *Sadnaf* , _Allah ya karemin ke daga sharri masu sharri, Allah ya bar zumunci._




Ajiye wayan tayi gefe ta cigaba da kuka, mom dake tuki kallon ta tayi Sannan tace
"Wannan kukan nan is enough...sai kuka kike kaman wacce akayiwa mutuwa,..." Ta daka mata tsawa, shuru tayi amma hawaye basu bar zubowa ba, ita kawai tunanin ta kar ace son mutumin data fada mata shine silan rashin lafiyanta.

Ayan naganin ta kashe wayan ya saki murmushi cos intensional ya fadi abinda ya fadi, tsoki yaja yana cewa
" I wonder why that girl is special to her..." Yafada yana zama kan seat dinshi na office, shuru yayi for a while yana tuna maganar da husna ta fada mashi game da ihsan ranar data tsaida shi,
" _Ba halin mu daya ba...I want to ask for your forgiveness about my friend disrespect.._" ya tuna
"I think she said that..." Ya fadawa kanshi Sannan fuskan shi look surprised,
"Why haven't I remember that statement?..." Ya tambayi kanshi, kara gyara zamanshi yayi yana cewa
"Precious is not special to her the way she's special to my precious...."ya kara fadawa kanshi,
" anyway is a matter of time... Mutane da banaso bazasu ziyarci gidana ba..."  Wannan Karin ya fada cikin ranshi.

Kofa aka bude Yusuf ya shigo ciki, kallon Ayan yayi ya tabbatar he's in a good mood amma dayake Dan rainin hankali ne sai cewa yayi
"Dude ya maganan mu ta jiya?..." Daure fuska Ayan yayi yana cewa
"Wace magana?..." Dariya Yusuf yayi
"If you like frown your face babu ruwana... Ka barmin ihsan din?..." Hararan shi Ayan yayi batare daya ce mashi kala ba,
"Kayi shuru..."
"Pls get out of my office... Am busy...." Ayan ya fada mashi atakaice,
"Oh have changed your mind kenan...well Allah ya taimakeka...rubbish.." Yafada yana mikewa, Ayan bayanshi yabi da harara tare da Jan tsoki..
 Wayanshi ya dauka ya kara dailing number ihsan.

Wayan na fara ringing bata dauka ba don tasan Ayan ne kallon ta mom tayi
"Bakiji wayanki is ringing?..." Mom ta fada mata, bata ce komai ba ta dauki wayan tayi picking ta dora kunnenta batare datace kala ba, daga chan bangaren Ayan ya fara lallashinta yana bata sweet words, bata magana sai dai murmushi saboda mom dake zaune kusa daita, kafin ta su kai hospital har ta kwantar da hankalin ta kasancewan Ayan knows the right words to say. Sallama sukayi Sannan ta fito daga cikin motan.

Room 6 inda aka kwantar da husna suka shiga a lokacin mami zaune tana bawa husna tea tana sha, husna na daga kai ta kai ihsan
"Here comes the bitch that is blocking my happiness..." Ta fada cikin ranta, amma a zahiri ta saki murmushi, da sauri ihsan ta karasa ta zauna bakin gadon tana kallon husna data kara ramewa saboda rikicin data sawa ranta, ita kam ihsan hawaye ne suka ciko mata don ana tunanin wannan Wanda take so data fada mata is the cause of her predicament, batasan her Ayan is the one she's dying for ba. Hannun ta ihsan ta kama itama husna ta kama hannun tana
"I will surely deal with you..." Husna Tafada cikin ranta, mom ce ta karaso bakin gadon suka gaisa da mami Sannan mom ta fara cewa
"Daughter.. Me ke damunki?..." Mom ta tambayeta, husna murmushi kawai tayi amma cikin ranta tace
"Ke fadawa shegiyar yarki ta barmin Ayan..." Tafada cikin ranta amma fuskanta dauke da murmushi,
"Wai ciwon zuciya ke neman kamata..." Inji mami, idanuwa mom da ihsan suka zaro, ihsan kara rike hannun husna tayi
"Daughter me ya jawo maki ciwon zuciya?..." Mom ta tambayeta, itakam ihsan gani take she knows the actual reason,
"Ku tambyar min ita...babu irin tambayan da ban yi mata ba amma cewa take babu komai..." Inji mami dake magana kaman zatayi kuka, mom kama mata dayan hannun ta tayi tana cewa
"Haba daughter... Ki fada mana abinda ke damunki..." Murmushi husna tayi
"Wallahi... Mom nima ban saniba...haka nan kawai zuciyata ta fara yimin zafi..." Tayi masu karya, ihsan goge hawayen dake gangaro mata tayi, husna kallon ta tayi
"Da kinsan abinda na shirya maki da kin bar yimin kuka kin yiwa kanki kuka...filthy bitch..." Husna ta fada cikin ranta amma azahiri tace
"Babe ki bar kuka..I will be alright... " tayi assuring dinta,
"Baby pls tell me abinda ke damunki... Wallahi zan baki ko meye..." Mami ta fada mata,
"Pls daughter tell us..." Mom ta kara fada, husna kam fuskanta dauke da murmushi tana cewa
"Wallahi babu komai..." Ihsan kam shuru tayi.

Haka mami da mom suka dinga rarrashin husna ko zata fada masu abinda ke damunta amma kememe ta ki fadi daga baya data ga sun addabeta sai cewa tayi
" gidansu ihsan nake son zama har ayi aurensu..." Tafada don tasan haka zai fi mata sauki don next plan dinta.
"Wannan ba matsala bane..." Inji mom,
"In aka sallameki sai kije chan direct... If that's what you want..." Inji mami, ba karamin dadi ihsan tajiba don ita ko kadan bata gajiya da husna, cos in reality halinta na so ne.


Abangaren gidan inna mai aikin gidansu ihsan kam matsala is getting worse don yanzu rabe danta bai zuwa koina sai gida kuma kullum rungume yake da wannan kwalin juice yana cewa
"Sonta nake...Ku nemomin ita kar in mutu..." Yanzu hankalin inna ya fara tashi cos ko abincin kirki baici sai dainya dinga maimaita magana guda. Inna kam sai tsoro ke kamata amma still batayi figuring out cewa magani ke da akwai cikin drink din daya shaba.
 Da akwai wurin da yake gadin karanta yanzu ko zuwa baiyi in kuma anci SAA yaje makale yake da wannan kwalin yana maimaita magana daya.


Yau da wuri Ayan ya dawo daga office, direct pary dinshi ya nufa ya sakar wa kanshi shower Sannan ya fito daure da alwallah, mai ya shafa Sannan ya dauko wasu sky blue shadda ya saka Wanda ya yi mashi shegen kyau, masjid ya wuce yayi sallan asar, yana dawowa ya shiga part din Umma, salma da sameera ya hanga zaune sai Umma zaune tsakiyan su dauke da laptop da gani aiki suke, karasowa yayi wajensu ya gaida Umma su kuma suka gaida shi, kallon twins yayi one after the other Sannan yace
"Lafiya Ku biyu kuka zo?..." Yafada yana neman wurin zama,
"Kayan amaryarka Umma ta kiramu zaba..." Bata fuska yayi
"Ku zaku zabi kayan matata?...gaskiya Ku tashi Ku koma gidajenku ni da Umma zamuyi selecting..." Yafada babu wasa, hararanshi Umma tayi
"You are not serious... Jiya magiya na dingayi maka kace in kirasu...yanzu saida na kirasu?...kawai kaje kaci abincinka ka wuce ka bamu wuri...." Tafada tana nuna mashi dinning,  mikewa yayi yana bubbuga kafa da kasa yana cewa
"Gaskiya ni ki fada masu su tafi ni dake muyi selecting..." Yafada kaman karamin yaro, dariya salma ta farayi ya watsa mata harara tayi shuru, Umma banza tayi dashi ta nuna monitor laptop din Sannan tace
"I think wannan colour will be okay ko?..." Ta fadawa su salma, kai kawai suka gyada mata, da sauri Ayan ya koma bayan kujeran da suke zaune yanda zaiga screen din laptop din da kyau,
"Gaskiya Umma wannan red colour is too loud for her tunda ita farace...why not something cool..." Bai idaba Umma ta jefeshi da troy pillow dake kan kujeran, barin wajen tayi ya koma gabansu
"Baku tashi!..." Ya daka masu salma tsawa da sauri suka mike su ka bar wajen, tsaya kallon shi Umma tayi tana cewa
"Naga ta yanda zakazo ka zauna..." Dariya kawai yayi ya koma bayan kujeran. A haka suka cigaba da selecting kaya daga baya yayi dabara ya dawo ya zauna kusa daita, ba karamin kaya suka zaba mata ba don fadin kyau da tsadan su is a waste of time, saida suka zo wajen selecting inner wears Umma ta koreshi amma kememe ya ki tashi, sai rashin kunya yake zubawa don da Umma ta zabi bra sai yace ba size dinta bane ko kuma is not sexy, sai dukan shi take da Troy pillow amma yaki tashi. Sai wajen 6:00pm suka gama Sannan yaci abinci ya koma side dinshi, kwantawa yayi ya kira number ihsan don jin in ta dawo,
"Precious kun dawo?.." Ya tambayeta, ihsan dake zaune kusa da husna tace
"Aa...ina nan sai an sallameta..." Bata rai Ayan yayi kaman tana zaune gabanshi
"Kamanya sai an sallameta?...kina nufin bazaki dawo ba yau in baa sallameta ba?..."
"Eh.." Kawai ta amsa mashi atakaice,
"What about me...kinsan in ban ganki ba I can't sleep..." Dariya ihsan tayi
"To kayi hakuri yau..."
"Kaman ya inyi hakuri?..gaskiya ki jirani zanzo daukan ki...gobe da safe sai in maidaki hospital..." Girgiza kai ihsan tayi tana cewa
"Aa...kawai saidai kazo ganin Mara lafiya..." Bata rai yayi,
"Kin ma raina min hankali... Kawai ki fadamin inda kike zanzo....ai bake ya kamata kiyi jinya ba...ko so kike doc on duty su dinga kallemin ke?..." Husna na sauraron duk hiran da suke  kuma ta tabbatar babu fushi ko wani abu a tsakanin su
"Kaima haka kake kallon wasu kenan.." Dariya yayi
"Ai babu wata mace  sai ke...yanzu inzo?..." Murmushi tayi tana lumshe idanuwa
"Eh...amma ban zuwa gida sai an sallameta ...kawai kazo cos nayi missing handsome face dinka..." Wani irin harara husna ta buga mata amma bata ganiba,
"To zanzo...kilan mu kwana hospital din tare..." Dariya tayi
"Aa..ka daizo mu gaisa Sannan kaga Mara lafiya sai ka koma..."
"Ni ba ganin Mara lafiya zanzoba...ganinki zanzo...", dariya kawai tayi don batason husna tasan abinda yake cewa, amma duk a kunnenta cos ta kasa kunne don taji muryan Wanda tafi kauna a duniya
"To me zan kawo maki cos nasan kilan bakici abinda kike so ba..." Dariya tayi Sannan tace
"Gaskiya ba sai ka kawo komai ba...kawai gazo in ganka.."
"Don't worry zan kawomaki shawarma, juice, fruits... Zan kawo kayan dadi sai kiyi feeding dina..." Dariya tayi tana cewa
"Sai dai ka kawowa Mara lafiya..."
"Pls bani address kawai.." Address din hospital ta bashi Sannan ta katse wayan, husna dake lumshe idanuwa kaman mai jin bacci kallon ihsan tayi tana cewa
"Waye?..."  Ta tambayeta kaman batasan wayeba
"My prince charming..." Ta amsa mata tana wani irin murmushin jindadi,
"Ok..." Kawai Tafada tana juya kwanciyan ta
"Yace zaizo nan..." T fadawa husna,
"Ok..don Allah ki kira mami ta tahomin da cheeps and salad...nasan sun kusa isowa..." Inji husna, Tafada don taji abinda ihsan zatace,
"Bari kawai in fadawa Ayan tunda shima yana hanya..." Tafada tana daukan wayanta, husna da ta bata baya lumshe idanuwa tayi tana tunanin zata CI abinda Ayan ya sayo.
"Ki barshi....kar ki sashi dawainiya..." Tafada kaman gaske, banza ihsan tayi daita tayi dailing number Ayan, alokacin ya daura alwallah ya fito yana daukan wani dark blue cap, dorawa yayi kanshi fuskan shi yayi more handsome, kiran ihsan yasa shi dauka wayan.
"Precious.."
"Naam...daman cheeps and salad zaka sayomin..." Dariya yayi
"I know you are lying...somebody ask you to say that..." Yafada yana dariya tare da kashe wayan. Fita yayi yana rike da car keys dinshi, part Umma ya shiga ya fada mata kawar ihsan bata da lafiya don haka ba zai dawo da wuri ba.

Yana fita ya dauki motanshi ya tsaya gaba masjid yayi sallan magrib Sannan ya wuce hospital da ihsan tayi mashi kwatance kan hanya ya tsaya ya sayi kayanci kala2 kaman Wanda zaije dakin amarya amma abun mamaki bai sayi abinda ihsan ta kirashi ya saya ba, yana zuwa hospital din ya fito tare da daukan kayan daya sayo, amma kuma sai yayi tunanin kilan da mutane wurin sai ya maida kayan cikin motan ya kulleta yana shuumin murmushi.

Room six da ihsan ta fada  mashi ya tsaya tare da sallama ya shiga, ihsan najin muryan shi ta sadda kanta kasa tana murmushi saboda su mami da wasu mata biyu da basu Dade da isowa ba, durkusawa yayi ya gaidasu tare dacewa
"Ya mai jiki?.."
"Mai jiki da sauki..." Mami ta amsa mashi da faraa fuskan ta don ta San shine Wanda ihsan zata aura,  husna kam kura mashi ido tayi tana kallon shi kawai ya daga kai sai suka hada ido daita
"Hattara dai..." Yafada cikin ranshi,


💙💚❤💛💜


Kuyi hakuri wayata ta kwafsa nayi typing duk yayi deleting, Wallahi kaman inyi Kuka. Sorry for waiting.
[25/11, 22:41] Yar Niger Frd Husaini: ❤💜💛🖤💚💙
KAWARTA CE SANADI
💜💚💙🖤💛❤


®zuwairat(ummu Maryam)



2⃣5⃣




 _Ina kike *Surbajo* is your turn, I want you to know you have a special place in my heart, ina yinki fiye ya da yanda kike tunani, I love you so much, Allah ya barmu tare da masoyan mu, ameen_ _love you_


Ayan kauda kanshi yayi amma husna bata bar kallon shi ba cos at the moment ji take kaman.she can take it anymore, she feels as if tayi screaming on top of her voice ta fadawa duniya she loves him, Ayan zama yayi kan wata kujera dake empty ya  kara daga kai ya ya kalleta, surprisingly har lokacin bata bar kallon shi ba, shima kura mata ido yayi yafara intimidating dinta da manyan idanuwanshi, kallon ihsan dake wasa da yatsunta yayi yaga bata daga kai ba amma fuskan dauke da murmushin jindadi saboda zuwan masoyinta, Ayan kara kallon husna yayi yaga still tana kallon shi with out blinking, su mami sai hira suke da Matan da ke dakin don haka basu lura da abinda ke faruwa ba, daure fuska yayi ya zaro mata idanuwa kaman yanda ake tsorata yara da idanuwa nan take ta dauke kanta hawaye na gangarowa, shidai bazai Iya interpreting irin kallon da take yi mashi ba dukda ya saba ganin irin wannan kallon wurin yanmata,
"Not possible..." Ya fadawa kanshi cikin ranshi, ahankali ya Dan sa kafanshi ya taba kafan ihsan dake wasa da yatsunta har lokacin, daga kanta tayi ta fara kallon su mami don tabbatar basu ganshiba Sannan ta kalleshi, wani irin kasaitaccen murmushi ya sakar mata itama ta mayar mashi da martani, yayi mata alaman su tafi waje, idanuwa kawai ta zaro tare da Dan girgiza mashi Kai tayi, ido daya ya kashe mata tare dacewa
"Plsss..." Yanda babu Wanda yaji sai ita da kuma husna dake kallon duk movement dinsu, kai ta kara girgiza mashi tana kallon empty hands dinshi, kallon ina abinda nace ka sayomin yake tayi mashi, shi kuma yayi mata kallon na mance, bata fuska tayi ta kauda kanta gefe daya, husna kam tunani take anya wayanda ta aika suje wurin Ayan sunje kuwa? Don  ko kadan babu alaman haushi ko zargin ihsan tattare dashi,
"I will see how much you loves her..." Tafada cikin ranta.

Suna nan zaune har 9pm, duk yanda yayi ea ihsan alama da ido kan ta tashi su tafi waje ki tayi wai tana fushi don bai kawo komai ba, kuma ya dau niyyan saidai su kwana nan tare muddin bata bishi waje ba.

 kawayen mami ne suka mike itama mami ta mike tana dora Vail dinta kan shoulder dinta, wurin gadon sukaje suka kara yiwa ihsan Allah bada lafiya Sannan suka fita mami na bayansu, Ayan na gani daga shi sai ihsan don sam mantawa yake da husna dake kwance,  da sauri ya mike ya kama mata hannu yana cewa
"Haba precious... Muje waje mana..." Da sauri ta fixge hannun ta tana cewa
"Ina chips danace ka sayomin?..."
"Yana cikin mota... Muje in baki..." Yafada yana kashe mata ido daya, hararan shi tayi tana kauda kanta gefe
"Precious pls ki taso...da akwai abinda zan nuna maki..." Yafada yana kara kama hannun ta Kara fixge hannun ta tayi tana cewa
"Ban zuwa..." Tafada tana harde hannuwanta kan kirjinta, husna dake kallon su cikin annoyance ta saki murmushi kaman gaske tana cewa
"Babe haba...bakonka annabinka...pls kije... I will be alright..." Tafada ihsan, juyawa sukayi da sukaji kafa mutum da alaman mami ce ta dawo, da sauri Ayan ya koma ya zauna, bude kofan tayi tashigo da sallama duka amsa mata, kallon ihsan tayi Sannan tace
"Habibty... Ki tashi ki shirya ya maidaki gida..." Tafadawa ihsan, wani irin sanyi Ayan yaji, Dan turo baki tayi
"Mami ni nan zan kwana...." Bata idaba mami ta girgiza mata kai
"Aa...maza ki tashi ya kaiki gida...gobe ma doc yace zaa sallameta..." Kaman zatayi kuka tafara bubbuga kafanta kasa tana cewa
"Wayyo ni nan zan kwana..." Ayan zama yayi yana kallon ta with adoration fuskan shi dauke da murmushin so da kauna,
"Daughter banason gardama... Iya tashi...gobe first thing in the morning zan sa driver yazo daukan ki inyaso in an sallameta sai Ku koma gida tare...oya ...Iya...stand dare na karayi..." Tafada mata not giving her chance to complain
 Tana turo baki kaman zatayi kuka ta mike ta saka vine flat shoe dinta dake kasan kafanta Sannan ta warwate karamin Vail data maida dankwali ta yafa shi Sannan ta duka tayiwa husna kiss a goshi tare dacewa
"See you in the morning insha Allah..." Itama husna tallabo face dinta tayi da two hands dinta tana cewa
"Allah ya kaimu..." Ayan kaman yana jira ya mike ya yana cewa
"Mami Allah ya kara sauki..."
"Ameen.. Mun gode kwarai..." Mami ta amsa mashi, fittt ya fita daga dakin, ihsan dauka handbag dinta tayi tabi bayanshi bayan tayiwa mami sai da safe,
 Waje ya tafi ya tsaya gefen motanshi yana jiran fitowanta, sai murmushin keta yake, few minutes later sai gata ta fito rike da handbag dinta fuskanta Sam babu walwala, bakin motan ta karaso yayi saurin bude mata kofa, shiga tayi still fuskan ta daure,tana shiga tafara jin kamshin kayan ciye2,
"Kambu..." Tafada a daidai lokacin daya shigo cikin motan, kallon ta yayi
"Precious... Ya akayi ne?..." Ya tambayeta kaman baisan fushi da take ba, hararan shi tayi Sannan tafara cewa
"Pls why are you doing this to me..."
"Menayi kuma?.."
"Na fada maka ka tahomin da chips amma ka ki...why..." Dan dariya yayi
"Because nasan bake zakiciba..."
"Does it matter who zai ci?... At least tunda na bukata sai ka sayomin..."
"Inda wani wuri kike da zan sayo maki.,...amma nasan kilan friend dinki zaki bawa... That's is why naki sayowa..." Yafada sounding frank, kallon mamaki tayi mashi
"Wai pls meke tsakanin ka da ita?..."
"I don't like her...kuma kaman yanda bazan gaji da fada maki I love you ba...bazan gaji da fada maki I hate her ba..." Afusace itama tace
"She don't like you either...." Sai da tafadi hakan sai ta kama bakinta cos sam bata so ta fada mashi ba, wata bazawaran dariya ya saki
"Hehehe....you see... That makes us even... I don't like her...she don't like me...which I totally disagree..." Da sauri ihsan tace
"Why do you disagree... She personally told me so..." Dariya ya karayi tare da tabe baki Sannan yace
"Precious.. Plsssss can we forget others and talk about us?..." Yafada cikin natsuwa, da sauri tace
"No!...you people should tell me what is happening between you two...I know something is wrong..." Da sauri shima yace
"Ba dai daga bangare na ba...may her..." Yafada yana tada motan,
"I don't like him....I don't like her...kar wannan abun yayi turning to something else...nasha kallon movies inda hatred ke komawa so..." Tafada kaman zatayi kuka, wata irin dariya Ayan yayi at the same time yana daure fuskan shi
"Hmmm don't be offended.. But you are thinking with your ass..." Da sauri ta luka mashi duka ya kece da dariya  yana cewa
"What ?...ai banyi karya ba...ko.mata sun kare bazan iya son wannan yarinyan ba...I hate her with passion... Allah kadai yasan dalilin dayasa banason ta....ewwww she is disgusting...." Tsaya kallon fuskan shi ihsan tayi tana kallon yanda he's saying every word with bitterness, bata ankara ba taji yayi parking gefen lonely street of the hospital, kalle2 quite street din tayi ta kalleshi dake fita daga mota, shuru tayi tana tunanin kilan he wants to ease himself, amma sai ya zagayo  ya bude inda take , bai jira reactions dintaba ya fiddota tare da rike mata waist, idanuwa ta bude tana kokarin magana amma bakinta bai buduwa, bayan motan ya bude ya sata ciki kallon kayan ciye2 dake tsakiyan seat din motan tayi kaman Humpty Dumpty, shima shigowa yayi ya kalli surprised face dinta ya saki murmushi Sannan yace
"Let's eat...." Kallon haushi tayi mashi
"Banci..." Ta fada atakaice,
"To mu kwana nan..." Idanuwa ta zaro ta fara nuna shi da yatsa tana cewa
"Daman am suspecting your attitude..." Bata ankara ba ya shafke mata yasa cikin bakinshi,da sauri ta zare tana kallon yastan
"Ohhh...baki yarda daniba kenan... To shikenan... Bari kawai in gwada maki halina...." Yafada yana shuumin murmushi, kokarin fita tayi daga cikin motan ya rike mata hannu yana dariya
"Am joking... Pls...muci abinci..." Kara girgiza mashi kai tayi
"Nakoshi..."
"To feed me then...."
"Gaskiya  I can't..."
"Pls precious... Start practicing..."
"No..."
"Pls..."
"No I can't..."
"Plsssssssss..." Sunfi minti goma suna wa juna magiya, gani tayi time is going,
 Yasa ya amince zata yi feeding dinshi, har da
"Yeeeeyyyy..." Yafada don dadi Sannan ya warware kayan, hararanshi tayi tafara feeding dinshi babu kunya ya wangale mata baki har abun yana bata dariya, cikin dubara ya bata tun bata amsa ta fara amsa, sunfi hour suna abi guda, suna gamawa Ayan yayi relaxing bai da niyyan tafiya,
"Pls mu tafi ...the night is not getting young..." Tafada mashi, lumshe idanuwa yayi yana cewa
"Ban driving immediately after eating..."

Sai bayan minti talatin suka kama hanya , driving ya dingayi ahankali suna hira har suka iso kofar gidansu ihsan, sallama sukayi ta  fito ta kwankwansa gate aka bude mata ta shiga.


Fitan ihsan da Ayan ke da wuya husna ta kara dafe heart dinta tana hawaye, mami tasowa tayi ta tsaya kanta tana tambayan ta gaskiyan abinda ke damunta, amma sam taki fadi, kawai cewa tayi
She's missing ihsan. Sai da alluran bacci tayi bacci, the following day tun da wuri Ayan ya kai ihsan hospital, ganin ihsan da Ayan tare yasa zuciyanta kusan bugawa, Wanda hakan yasa ko da doc yazo yace bazaa sallameta ranar ba cos nothing have changed, haka suka yini nan da dare Ayan ya kara zuwa daukan ihsan. Atakaice saida tayi kwana uku hospital Wanda yayi daidai da 4weeks to Ayan and ihsans wedding,  shima ba don jikinta yayi sauki ba amma sai don tasan zaman ta hospital is meaningless kuma time is passing her by, ranar da suka iso gidan su ihsan  ta riga ta gama plan din komai kuma tasan babu abinda zai hana Ayan rabuwa da ihsan muddin plans dinta yayi scaling through.

Wajen karfe goman dare bayan ihsan ta dawo daga wurin Ayan ta shigo dakin kallon husna na ke kudundune cikin blanket kaman mai bacci tayi tabi ahankali don kar ta tada ta ta cire kayan jikinta as usual ya rage daga ita sai pant,  wata sleeping gown mai kama da after dress ta dauko ta saka shima don husna na gidan amma on a normal ground tafison kwana ba kaya, tana dora wannan ta kwanta tare da rufe kafanta zuwa waist dinta da blanket, daga waist dinta zuwa samanta bude.

Bayan hour biyu idanuwan husna bude, sai da ta tabbatar shine ihsan tayi bacci Sannan ta mike zaune tare da kallon ihsan da Dan kayan bacci ta ya bar chest dinta bare, ahankali ta dauko wayanta, ta seta kan fuskanta tare da boobs dinta dake naked ta dauketa pic, cikin bacci ihsan taji kaman ana flashing fuskanta, da mikewa zaune tayi taga husna kwance kaman tana bacci, gyara kayan baccin ta tayi Sannan ta koma ta kwanta.

[12/2, 7:45 PM] ‪+234 706 582 0685‬: 💙💜💚🖤💛❤
KAWARTA CE SANADI
💙💜💚🖤💛❤



®zuwairat(ummu Maryam)



2⃣6⃣




 _This one is for you my habibty, har kin gane da ke nake cos I see you smile for seeing habibty, inason ki my one and only *sawwama* , Allah ya karemin ke, I am saying this from the bottom of my heart not my stomach_ .


Tana kwanciya bacci yayi gaba daita, husna dake rike da wayanta gam tana murmushi keta.

The following day kowaccensu ta mike kaman nothing happened, ihsan is free cos she have nothing to hide while husna is happy don gani take ta kusa cimma burinta. Downstairs suka saukasuka taya mai aiki hada breakfast as usual. Their life go on smoothly har suka gama breakfast ihsan tafara hawa sama don yin wanka, tana hawa husna ta bi bayanta, dama tasan ihsan bata rufe kofar bathroom in tana wanka, sadaf2 ta shiga bedroom din ihsan, one more habit na ihsan is that ta saba waka in tana shower, in kana dakinta da zaran ta fara wanka zakaji waka kala2 bakinta kaman tana party, tana waka tana rawa,  yau ma is the same thing, tana ciki wanka sai wakan awww na dija take,
" _Boy you the one I want... Cos you got what I need...Tell me boy do you see...happiness in me...I love my life anytime am with you Ahhh as long as you love me...there is nothing I won't do to make you smile... There is nothing I won't do to make you happy...._" ta dingayi on top of her voice, shuumin murmushi husna tayi tana cewa
"The right song.." Tafada cikin ranta Sannan ta nufi bathroom din da wayanta a hannun ta, ahankali ta leka Dan hole din dake wurin key taganta tsaye cikin shower kanta duk kunfa da alaman kanta take fara wankewa kafin ta wanke jikinta, ahankali ta bude kofan kasancewan bai da kara kuma ko yana da kara wakan da take bai barinta jin an bude kofan. Yanda ta bude kofan ya bata daman ganinta da kyau ahankali ta daga wayanta ta saka video tayi saurin fara videoing dinta,ita kuma sai waka take tana rawa at the same time hannuwanta biyu cikin gashinta dake cike da kunfa, tafi minti biyu tana daukanta amma ihsan bata gama wanke kanta ba balle ta bude idanuwanta, sai dataga ta fara murza face dinta tayi sauki dauke wayan tare da jawo kofan, da sauri tayi saving video tana ajiyan zuciya, bata zauna dakinba, ta bude kofa ta saukan downstairs, kan stairs ta hadu da mom ta nufo dakin da cup a hannun ta da gani magani ne ciki, gaida mom tayi  ta masa mata cikin faraa da jin dadi ta hau saman itakuma ta saukan zaman
"Aiyi dai mugani..." Tafada cikin ranta tana kallon bayan mom. Tun a bakin kofan mom ke jin wakan ihsan daga bathroom, tsoki tayi tana cewa
"Ban San abinda yasa wannan shegiyar yarinyan batajin magana ba...." Tafadawa kanta Sannan ta fara cewa
"Yanzu halima cikin kewayen kike wannan iskanci kaman a gidan biki?....Wato zuwa islislamiyya bai yi maki amfani bako?.....to Wallahi kika bari na bude wannan kofan nashigo na lahira sai yafiki jindadi..." Mom ta fada mata cikin fada
 Sosai, nan take ta rufe bakinta amma dayake is her habit bata bar humming ba, mom ta cigaba dacewa
"Haka zakije gidan miji ki jamana zagi...mijinki ya dinga ganin. Kaman wajen mu kika koya...to wallahi ki shiga hankalin ki...kuma kiyi maza ki fito ga magani nan ki shanye... Sauran ki zybda kice kinsha..." Mom ta fada mata sannan ta ajiye abinda ta zo dashi ta fita daga dakin, hmm one awful thing about ihsan is that she is extra stubborn, tanajin mom ta fita tacigaba da wakanta don already ya zame mata habit, sai bayan minti ashirin ta fito daure da towel a kirjinta sai daya kuma a kanta,  zama tayi kan mirror tana kallon cup da mom ta ajiye mata, daukan cup din tayi tana cewa
"Ni har na gaji da shan Sannan drugs din...tun lokacin Mahmoud.. Har yau ban huta ba....." Tafada tana bude cup din, Dan dangwala harshen ta tayi ciki taji da bauri, Dan bata fuska tayi  Sannan tace
"Anything for you.. My prince charming..."  Tafada tana kafa kai, bata dauke ba sai da ta shanye shi tas ta ajiye cup din ta shiga bathroom da gudu ta dauraye bakinta, tana fitowa wayanta na ringing, murmushi tayi tana cewa
"Talk of the devil..." Tafada don tasan Ayan ne, picking tayi ta zauna kan mirror tana kallon kanta suna wayan so da kauna, kurawa beautiful skin dinta ido tayi tana murmushi don ita kanta tasan Allah yayi mata abubuwan da ba kowacce mace Allah yayi wa ba, sunfi minti talatin suna waya Sannan sukayi sallama ta shafa mai, batayi kwalliya ba amma ko government house tana iya zuwa a hakan, skirt da riga ta dauko ta saka ta tsaya gaban mirror tana kallon kanta from head to toe,
"Alhamdulillah..." Tafada  Sannan ta fita.

A ranar basu je school ba kasancewan Sunday, duna gida through out suna labari amma ko da wasa husna bata ajiye wayanta ba kuma Allah baisa ihsan ta kai hankalin ta wajen ba, ita kawai jiran kiran Ayan especially da bayan sallan ishai tayi, kuma sai gashi ya zo as usual sunsha love.

Alokacin da suna compound suna hiran yanda rayuwan su zai kasance ita kuma husna tana zaune bakin gadon tana tunanin yanda zata dauki next plan dinta which tasan babu abinda zaisa Ayan yacigaba maganar auren muddin ta gama Plan dinta.

Kawai tunanin next action dinta kawai take, kaman wacce ta tuna wani abu sai tace
"Yesssss..." Tafada tana mikewa , ahankali ta Kara komawa zaune tana cewa
"zaiyi yawa...kar wani yaga nakedness dinta...so dole ni zan aikata da kaina...Allah I need is a new simcard....and komai zai tafi as planned..." Tafada tana relaxing kan gado. Da sauri ta dauko wayanta ta fara kallon nude pic din ihsan Sannan video, murmushin jindadi tayi yana cewa
"Bari inga in son gaske kake yi mata...precious..." Tafada tana dariya, kara kallon pic din tayi Sannan tayi rubuta
" _My baby cooling off after hot round of sex...na fada maka ka bar ta amma ka ki...anyway tayi assuring dina yau aurenka bazai hamu komai ba ..so go on and marry my sweet potatoes... She is really sweeeet in bed...can't stop swimming in her..._ " tayi rubuta kasan pic din tayi saving tana murmushin keta, amma the little good side of her is thinking abinda takeyi is not good amma the bad side have dominate the good side,
"Mtwww..." Tafada tana kara bude video, shima editing dinshi tayi ta rubuta
" _Just want to show you how romantic this afternoon was for us....yau ba karamin dadi ta shayar daniba....pls kalli how beautiful she is...daman Don in fada maka ba haka nan nake fada kanta ba...she's so adorable..."_ ta Kara rubutawa kasan video tayi saving tare da kashe wayan gabaki daya since shes not expecting any call.

Sai wajen karfe goma ihsan ta shigo Cikin daki, husna ta hanga zaune tayi tagumi hawaye na Zubowa daga idanuwanta
Da sauri ihsan ta karaso dakin ta zauna gefen ta tare da dafa shoulder dinta tana cewa
"Babe lafiya?..." Idanuwa husna ta daga ta kalleta Sannan tace
"Ba komai..." Tafada wasu new tears na rolling, cikin tashin hankali ihsan tace
"Ya za kice ba komai...you are crying.. Ko jikin...ne?..." Ta tambayeta muryan ta na cracking kaman zatayi kuka don tausayin aminiyarta,
"Wanda nakeso na tuna..." Tafada cikin kuka sosai, da sauri ihsan ta rungume ta tana cewa
"Sorry dear...yanzu meye abinyi?..." Ta tambayeta sounding very caring,
"Nayi missing dinshi ...I want to see him...k na minti biyu ne..." Tafada cikin kuka kaman gaske,
"Wane unguwa yake..."   Cikin kuka husna ta fada mata sunan unguwan,
"Yanzu ya zamuyi?...ko muje gobe Monday... Tunda lectures din mu bai dadewa?..." Shuru husna tayi for a while sai kuma ta tuna hakan bazaiyi favouring plan dinta ba sai cewa tayi
"Ai lokacin yana wurin aiki...in da ba Ayan zai kaimu school ba gobe da sai ince ki rakani in gashi ko daga nesa ne sai mu tafi school..." Shuru ihsan tayi tana tunanin ayya Ayan zai barta ta tafi school ita kadai, sai kuma ta tuna ita ba matar shi bace tukunna
"Ko ki tafi school ni zanje in gano shi sai in wuto school...tunda banason yasan abinda ke faruwa..." Taji husna na cewa cikin kuka, da sauri ihsan tace
"No need...gobe zan fada mashi da akwai inda zani...basai yazoba..." Wani irin sanyi husna taji cikin ranta don that is exactly the way she wants it to be,
"To shikenan..." Tafada tana goge hawayen ta, ihsan baya ta bata tana cewa
"Jawomin zip din Riga ta kasa..." Tafada Sannan tace
"I can't wait inga Wanda ya sacewa aminiyata zuciya..." Tafada cikin zolaya, dariya husna tayi
"Wallahi he's cuter than you expect.. Kawai Allah ya kaimu gobe muyi window shopping..." Tafada hankalin ta kwance, at that moment ji take kaman ta jawo goben. Haka suka sha hiransu Sannan bacci yayi gaba da ihsan itakuma husna bakin halinta da bad thinking sun hanata good night rest.


Wace gari tun 8 ihsan ta fara kiran Ayan don lectures din su na 9 ne, kiranta ya tasheshi daga bacci, daukan wayan yayi yana magana ta mai jin bacci, muryan shi sa ihsan dariya yayi
"Lafiya kika tadani daga bacci?.." Ya tambayeta cikin sleepy voice, dariya ihsan ta karayi Sannan tace
"Bakomai.. Daman inason in fada maka tau kar ka kaini school... Zan je wani wuri kafin in tafi school..." Idanuwa Ayan ya bude yana cewa
"Ina zaki Wanda ni bazan kaiki ba kafin in wuce daki school?..."
"Wurin wata friend ditace...kawai na hutar dakai yau..."
"Gaskiya ni ban yardaba....ni sai na kaiki...." Ya fada kaman Wanda zaiyi kuka,
"Ka kwantar da hankalin ka...mu shirya kazo daukata..." Ta fada mashi,bai Kara yi mata gardama ba  suka sha hiransu sharp2 Sannan sukayi sallama.
 Yana ajiye wayan ya koma ya kwanta tare da rufe kanshi da blanket.
Itama ajiye wayan tayi ta ida karasa shafe2 ta Sannan ta sauka downstairs, daman husna ta shirya tana dinning table tana shan tea da bread, itama ihsan zama tayi ta sha, data daga kai suka hada ido da husna sai taga ta saki murmushi, har ta gaji ta tambayeta wannan murmushin na meye? Sai cewa tayi kawai farin cikin zata ga fuskan masoyinta ne.
 Haka suka gama breakfast fuskan husna dauke da murmushi. Da sauri suka fita bayan sun amshi kudin abun hawa gurin mom.

Bakin titi sukaje suka tsaida abun hawa, ihsan sai missing Ayan take don rabon da  ta hau public fair har ta mance.

Adaidaita suka tsaida suka hau zuwa unguwan da husna ta fada masu, dama unguwan wata kawar mami ce so ta san wurin da kyau Sannan da akwai wani da take targeting ta nunawa ihsan  amatsayin Wanda take so.
Suna zuwa unguwan tasa mai adaidaita ya tsaya, kallon ta ihsan tayi
"Babe nan ne inda yake?..."
"Eh..." Tafada cikin sanyin murya Sannan ta nuna wani gida
"Wancan gidan yake...Allah yasa bai tafi aiki ba..." Tafada kaman da gaske.

Sunfi minti ashirin nan Sannan aka bude gate, wani saurayine, ya fito kan machine roba2, baki ihsan ta bude don saurayin ya hadu babu karya amma he's nothing compared to her Ayan.
"Wow babe ya hadu babu karya..." Inji ihsan, husna kam sai lumshe idanuwa take tana kallon saurayin da baisan wainar da suke toyawaba, ta inda suke ya wuce da machine dinshi ko kallon side din bai yiba, suma barin wurin suka husna sai lumshe idanuwa take wai dadi take ji taga habibi dinta.

Aranar haka suka je school, daga nan husna ta koma waje ta sayi simcard ta cire layinta ta saka Wanda ta sayo Sannan ta turawa Ayan pic da video din ihsan via WhatsApp bayan ta chanza WhatsApp number dinta daman already ta Dade da daukan number din shi daga cikin wayan ihsan.


Bayan Ayan ya gama komai around ten ya shiga office that is bayan yayiwa Umma sallama.

Har 2pm bai bude data ba balle yaga sakon da aka bar mashi, yana ta aiki har 3 bai bude data ba sai bayan sun fito daga surgery tare dasu Muhammad ya kalli time yaga three, hissing yayi yana cewa
"Yau ban samu daukan precious ba..." Yafada yana cire surgical cote dake jikinshi, ratayata yayi Sannan ya dauki wayan shi yayi dailing number ihsan, hakuri ya bata kan baizo daukanta ba ita kuma ta nuna mashi ba komai cos sun hau adaidaita lokacin zasu dawo gida. Ajiye wayan yayi cos daman he's not a social media person amma zaman dayayi bai da abinyi yasa ya kara daukan wayan ya bude data, nan messages suka dinga shigowa, hra dana husna. WhatsApp dinshi ya bude ya fara duba messages, farat daya idanuwanshi suka kai kan Wanda bai da suna cos mostly yana da number dukkan sauran. Ahankali ya bude wannan message din, dukda bai buda pic da video din ba yasan is not something good don da gani kasan is something nude, rubutun dake kasan message din ne ya kara Jan hankalin shi, tun bai karanta ba hankalin shi yafara tashi gashi gabanshi na mugun faduwa, hannu yasa ya bude pic din few seconds later ta bude, idanuwa ya zaro ganin ihsan kwance with her boobs bare. Kirjinshi ya dafa kuma jikin shi na rawa hannun yasa ya kara bude video, nan yaga his ihsan dancing nake in the bathroom, da sauri ya saki wayan yana cewa
"Inna lillahi waina ilaihi rajuun!!!!..." Yafada da karfi Wanda yasa Yusuf dake daf da office din tahowa da gudu, Ayan kokarin mikewa yayi amma sai ya kasa, tari ya farayi da karfi hannun shi daya kan kirjinshi daya kuma kan makogaronshi, irin tarin dayake yasa Yusuf zuwa inda yake zaune, kokarin kara mikewa yayi wannan Karin ya yanke jiki ya fadi kasa sai shaking yake kaman mai convulsing.
 💛❤💚💜💙🖤

Tun baa kai koina ba kun fara complaining, kuma da husna ta fara shan wahala still nasan zakuyi complain, haka kukayi lokacin ZAKISAN KONI WAYE, har wasu suka fara cewa raayin wasu nabi, inason Ku Sani kafin in fara novel inda complete story cikin kaina, so pls just keep reading kawai inason nuna muku length din da makiyinka zai Iya zuwa just to destroy you. So pls stay put and enjoy the ride as more is yet to come
[12/2, 7:55 PM] ‪+234 706 582 0685‬: 💛💚❤🖤💜💙
KAWARTA CE SANADI
❤💜💙🖤💛❤



®zuwairat(ummu Maryam)



2⃣7⃣


 _My *Habeeba* , wannan page is yours,thanks for the love and affection, Zuwairat na kaunar ki tamkar yanda take kaunar blood sisters dita, I love you._





Cikin tashin hankali Yusuf ya fara girgiza Ayan yana kiran
"Inna lillahi waina ilaihi rajuun!... Ayan... Ayan..." Ina baiji sai shure2 yake da legs dinshi har lokacin hannun shi daya kan kirjinshi dayan kan throat dinshi, idanuwanshi kafewa sukayi kaman Wanda ake zarewa rai, da gudu Yusuf ya fita waje yana kiran doctors, nan take doctors sunfi uku suka fito daga cikin office dinsu cikin su har da Muhammad,
"Lafiya?..." Ya tambayi Yusuf,
"Dan Allah Ku biyoni...something bad is happening to Dr Ayan..." Yafada yana komawa cikin office din da gudu, suma bayanshi sukabi suna shiga suka ga Ayan kwance ko motsi ya baryi,
"Inna lillahi..." Dukkan su suka dinga maimaitawa suna daukan shi, tambayan Yusuf suka dingayi kan abinda ke damunshi amma shi kanshi ba San amsar da zai basu ba kawai cewa yayi
"I was passing by sai naji shi yana inna lillahi waina ilaihi rajuun... Ina shigowa na ganshi yana tari and the next thing he was convulsing..." Yafada cikin tashin hankali, wani doctor ya fita da gudu ta dauko abinda ake dauka Mara lafiya dashi aka dirashi sama, hannu Muhammad ya dora kan kirjinshi yaji heart beat dinshi is beyond normal,
"What could be the cause of this?..." Muhammad ya fada
"I don't know..." Yusuf ya amsa mashi kaman zaiyi kuka. Emergency room suka shiga dashi suka fara kokarin ceto ranshi don at that moment gani suke kaman zai rasa ranshi. Da kyar suka samu ya saki ajiyan zuciya amma bai bude idanuwa ba, kawai sai suka ga hawaye da fita idanuwanshi suna shiga cikin kunnenshi saboda yanayin kwanciyan shi. Zuciyanshi sai up and down yake saboda yanda yake numfashi da kyar,
"I think we should give him oxygen..." Inji Yusuf, babu musu suka jona mashi oxygen, da sauri Muhammad ya fita yana cewa
"Bari in kira Abba in sanar dasu halin da ake ciki..."

Ayan kam baisan duniyar da yake ba, haka nan yana ji yana gani ya kasa controlling breath dinshi. Kawai adua yake Allah yasa ba ihsan dinshi ya yagani ba,
"I know am dreaming..." Yafada cikin zuciyanshi, ahankali ya daga hannun shi ya Dora kan heart dinshi dake yi mashi ciwo, da sauri Yusuf ya zo daf dashi ya rike mashi hannu, ahankali ya bude idanuwanshi, har lokacin hawaye basu bar rushing ba
"Guy What is the problem?..." Yusuf ya tambayeshi yana rike da hannun shi, Ayan daga idanuwanshi da sukayi mashi nauyi yayi ya kalli Yusuf, amma Sam bai da bakin magana, how can he tell his friend that his fiancee is a whore, he can't say it,
"Pls what's the problem..." Yusuf ya sake tambayan shi, kara kallon Yusuf yayi hawaye shar kaman tap, bakinshi sai kyarma yake kaman mai jin sanyi, hannu Yusuf yasa cikin aljihunshi ya dauki hanki ya goge hawayen amma wasu na zubowa, abun oxygen dake hancin shi ya ture gefe yana kokarin mikewa, kara rike shi Yusuf yayi
"Ina zaka?..." Ya tambayeshi,
"My....phone..., did you.... See...what's on...my ....phone?..." Ya tambayeshi kaman mai koyan magana, kai Yusuf ya girgiza mashi, Ayan lumshe idanuwa yayi hawaye na zubowa
"What is on your phone?..." Yusuf ya tambayeshi, ahankali ya koma ya kwanta batare daya mashi amsa ba.
Har Muhammad ya je ya sanar dasu  Abba ya dawo Ayan bai bar hawaye ba, shima Muhammad questions ya dingayi mashi amma bai magana sai kuka duk yanda sukayi su rarrashe shi abun ya shi tura, Yusuf fita yayi ya je office din Ayan, wayanshi dake kasa ya dauka ya bude Allah ya taimaka da akwai pattern da shima haka zaiga nakedness din ihsan, ganin bai Iya budewa yasa ya dauko wayan yashiga inda Ayan ke kwance, hannu ya mika mashi shi kuma ya mika mashi wayan, riketa yayi gam yacigaba da kuka, bayan kaman minti talatin lokacin su Yusuf sun gaji da tambayan shi kallon su yayi Sannan yace
"My heart....hurts...."  Muhammad dayayi tagumi yace
"Ka fadi abinda ke damunka ko munsan Maganin daya dace abaka...amma sai hawaye kake..." Yusuf kam bai ce komai ba ya zo daf dashi ya dora hannun shi kan kirjinshi, after few seconds ya kalli Muhammad Sannan yace
"I think muyi mashi alluran bacci cos the rate of the heartbeat is high...kuma kasan hakan is dangerous..." Muhammad baice komai ba ya nufi wata closet ya bude ya dauko injection ya hada ya dawo wajen Ayan, Ayan kallon shi yayi Sannan ya sauke idanuwanshi da suka koma kaman garwashi, hannun shi ya dauka ya dauke Sannan yayi mashi alluran. Bai dadeba bacci yayi gaba dashi.

Sai bayan sallan zuhr Abba da Umma tare da antymu da Ismail suka shigo hospital, har lokacin Yusuf da Muhammad na tsaye kanshi suna auna rate na heartbeat dinshi. Cikin tashin hankali Umma ta farq tambayan su Yusuf abinda ya sameshi exactly abinda suka saninsuka fada masu. Antymu sai kuka take don dukda Ayan na bacci eye lashes dinshi jike suke da hawaye
 Umma zama tayi bakin gadon tana kallon danta cikin tashin hankali tana wondering abinda ya sameshi, Abba kam kan wata kujera ya zauna sam babu alaman tsoro ko karaya tattare dashi amma shima deep down yana wondering abinda ke faruwa.



Husna kam bata cire wannan simcard ba sai da ta tabbatar an bude message din Sannan ta bude wayanta ta fidda simcard din ta kakkarya shi ta zuba cikin dustbin.

Around 4 bayan sun yi salla suci sunsha ihsan mikewa tayi haka nan sai ta tsinci jikinta babu kwari, saman bene ta hau tana tafiya ahankali, tana zuwa dakin ta kwanta tare da rufe kanta da blanket kaman mai jin bacci itama husna hawa tayi ta zauna bakin gadon tana kallon ihsan
"Babe ya dai?..." Ta tambayeta
"Nothing... Kawai dai banjin dadi ne...."
"Kilan is stress..."
"I don't think so...haka jikina yayi Mun lokacin da yaya Mahmoud zai rasu...yan zu ma am feeling down..." Da tabe baki husna tayi
"Ki huta ko zuwa anjuma kin ji daidai..." Ihsan bata kara cewa komai ba ta lumshe idanuwa.


Bayan sallan magrib Umma ta kira mom ta sanar daita Ayan na hospital bai da lafiya, Allah ya taimaka ba a gaban ihsan aka kirata ba, amma haka nan itama gabanta ya dinga faduwa, zaune take kan praying mat lokacin da sukayi wayan, hannuwanta ta daga sama ta fara cewa
"Ya Allah... Ya rabbi...ka bashi lafiya....in har wani ya samu wannan yaron shikenan halima tayi kaurin suna...ya Allah pls...have mercy..." Haka ta zauna ta dinga adua Sannan takira dad ta sanar dashi halin da ake ciki kasancewan bai gari nan dad ya fada mata ta tafi ta ganoshi amma kar ta fadawa ihsan. Haka akayi ta fito ta shiga dakin ihsan, zaune ta tardata kan mirror sai shafe2 take
"Zan fita yanzu zan dawo..." Mom dake tsaye bakin kofan Tafada mata, kallon ta ihsan da husna sukayi husna tayi saurin cewa
"Mom ina zaki?..."
"Nan neighborhood akayi haihuwa... Zanje barka yanzu zan dawo...." Ta fada masu Sannan ta jawo masu kofan ta tafi.

Har taje Ayan bai tashi daga bacci ba,  sai around 8 ta komo gida. Ihsan tana zaune falo taci kwalliya, husna kam sai jira take taji abinda zai biyo baya.

Har 8: 30 bai zo ba wayanta dake gefen ta ta dauka tayi dailing number shi.
 

Alokacin bai tashi daga bacci ba, wayanshi dake rike cikin hannun shi ya fara ringing, Umma dake zaune kusa dashi ta amshi wayan taga precious ke kira, ajiyewa tayi bata dauka ba.  Kara kira ihsan tayi wannan Karin Yusuf ne ya dauki wayan yayi picking, bai jira maganar ta bayace
"Bai farka ba har yanzu..." Yafada don a tunanin shi ta Sani tunda mamanta tazo, nan ihsan ta zaro idanuwa tace
"Tashi daga ina?..." Husna dake zaune kusa daita kasa kunne tayi don taji abinda zasuce
"Daga baccin... Alluran bacci akayi mashi..."
"Alluran bacci kaman ya?...." Da sauri ta daga wayan ta kalli screen din Sannan ta mai dashi kunnenta bayan ta tabbatar number Ayan ne ta kira,
"Wai waye ke magana?..." Tafada cikin tsiwa,
"Nine Yusuf... Har yanzu bai farka ba...zan fada mashi...." Da sauri ta katseshi dacewa
 "Kuma inane?.…."
"Hospital...." Aikam bai idaba ta katse wayan, da gudu ta tashi ta hausama husna na biye daita cikin ranta sai cewa take
"Anzo wurin..." Azahiri tace
"Babe lafiya?..." Ihsan da tuni ta fara zubda hawaye tafara cewa
"Wai Ayan ne bashi da lafiya....yana kwance hospital...." Tafada cikin kuka adaidai lokacin da tashiga dakin mom, mom dake zaune ta rafka uban tagumi ta kalleta da kuma yanda ta shigo bako sallama har zata fara yi mata fada taga fuskanta jike sharkaf da hawaye
"Lafiya ..." Mom ta tambayeta tana Allah yasa ba ganewa tayiba don tana tsoron rikicin ihsan. Kwantawa tayi kasa tana cewa "mom an kwantar da Ayan...."
"Wa ya fadamiki hakan..."
"Wallahi abokinshi ya fadamin... Zuwa zanyi..." Tafada cikin kuka sosai
"Ki bari gobe kinje.." Mom ta fada tana shafa kanta
 Da sauri ta fara girgiza kai tana cewa
"Ni wallahi mom sai naje...."
"Ke!..." Mom ta daka mata tsawa Sannan ta fara cewa
"Zaki farako...nace gobe kinje..." Fada cikin fada, sabon kuka ta fara tana cewa
"Mom dan Allah ki bari inje..." Bata idaba husna ta ce
"Mom zan rakata..." Kai mom ta girgiza
"Ku bari sai gobe...don ko kunje yana bacci..." Da sauri ihsan ta kalli mom
"Daman mom chan kikaje dazun?..." Tafada cikin kuka
"Nasan wannan haukan zakiyi that's why ban fada maki ba...tashi ki koma dakinki gobe sai kije da wuri..." Da kyar ihsan ta yarda ta bar dakin mom don babu irin magiyan da bata yi mata ba kan ta barta taje amma kememe mom taki, haka tana kuka kaman wacce akayi wa mutuwa ta bar dakin. Sai ihu take tana buga kanta da kasa tana cewa
"Nasan in da dad yana nan zai barni in je..." Aranar haka ta kwana kuka sai trying number Ayan take amma switch off, itama husna hankalin ta ba karamin tashi yayi ba don taji Wanda tafi so a duniya kwance hospital, ji take kaman ta jawo goben don har adua take Allah yasa ba wannan message din yayi sanadiyan kwantawanshi hospital ba don ko kadan batason abinda zai taba her Ayan.


Ayan bai farkaba sai wajen 12 na dare alokacin su Umma da Abba sun tafi bayan Yusuf da Muhammad sun shaida masu su tafi they will keep them posted, ahankali ya bude idanuwanshi da sukayi masa nauyi,  kallon Yusuf da Muhammad dake bacci, da sauri ya kalli agogon yaga after 12 da sauri ya sauka yayi alwallah ya dawo ya rama sallan duk da ake binshi har lokacin su Yusuf basu tashi ba, ahankali ya koma kan gado yana aduan Allah yasa duk abubuwan da suka faru su zama mafarki, ahankali ya dauki wayan shi ya kunna. Zama yayi yakara shiga WhatsApp dinshi wannan Karin nutsuwa yayi ya kalli video da kyau, yana kallo hawaye na digha kan screen din wayan,
"Why me..." Shine abinda ya dinga maimaitawa, kara playing yayi, still yana hawaye,
"Ihsan why....halima  kin cuceni...kin yaudareni....kinsa da aminta dake....kin CI amanata....bazan yafe makiba...I surely teach you a lesson of a life time..." Yafada yana hawaye, maganan shi ya tada Yusuf da Muhammad, da sauri ya kashe wayan ya ajiye yana goge hawayen shi yayi, wurin shi suka zo suka zuba mashi idanu suna mamakin abinda ke faruwa, shidai bai fada masu kala ba, hawaye kawai yacigaba dayi yana tunanin abinda zaiyiwa ihsan ya huce,
"Zan yaudareki the way kika yaudare ni...zanyi maki abinda guys dinki basu taba  yi maki ba...is not my way of life but am starting with you..." Yafada cikin ranshi, magiya Yusuf da Muhammad suka dinga yi mashi kan ya fada masu abinda ke damunshi amma bai fada masu komai ba daga karshe daya ga zasu rakurashi kawai cewa yayi
"Its just a nervous breakdown..."  Yafada fuskan shi daure ba don sun yarda ba suka kyaleshi.

The following day tun asuba ihsan da husna suka shirya, idanuwan ihsan sunyi mugun kumburi, abinka da farar mace duk kasan idonta sunyi ja. Da kyar mom ta shawo kanta ta sha tea Sannan suka fito tare da motan mom mai gadi ya tukasu, shigowansu hospital yayi daidai da fitowan Ayan dake shirin komawa gida don ya kwanta, da sauri ihsan ta fito   ta nufo shi, kaman ance ya juya sai sukayi ido hudu, idanuwanshi kumbure nata kumbure, husna zaune take cikin mota tana kallon abinda zai faru. Ayan ida juyawa yayi ya fuskan ce ta kawai sai yaga he's seeing her naked, tamkar babu kaya jikinta ya dinga kallon, kawai sai ya sakar mata wani irin shuumin murmushi Wanda yasa hancin husna dake kallon su tsinkewa.
[12/2, 7:55 PM] ‪+234 706 582 0685‬: ❤💛💚🖤💙💜
KAWARTA CE SANADI
💜❤💙🖤💚💛


®zuwairat( ummu Maryam)




2⃣8⃣



 _You are among my first friends, kina tare dani tun lokacin sune SANADI, ZAKISAN KONI WAYE, kuma nasan yanzu ma kina tare dani my dearest *Fiddausi sodangi* , ina jinki har cikin jinina, I meant what I said. Love you, Allah ya bar so da kauna ya rabamu da sharri makiya da mahasada._

Itama murmushin karfin hali ta sakar mashi tana karasawa inda yake, kura mata ido yayi yana kallon each step dinta
"I wish you were decent... Da muyi rayuwa mai dadi dake....amma now am after doing to you what you are use to..." Yafada cikin ranshi yana kallon eyeball dinta ba tare dayayi blinking ba, irin kallon da yake yi mata ne yasa tayi saurin dauke kanta, kurawa dan shoulder ta da ya Dan fito yayi kasancewan gyalen ta bai rufe mata dukan wuyan ta ba cos ba babba bane, wasu new tears ne suka fara taruwa idanuwanshi amma yayi saurin maidawa, kallon shi ta karayi tana mamakin dalilin dayasa idanuwanshi suka kumbura haka, shima tunanin da yake kenan,
"Precious... Meya samu idanuwanki?..." Ya tambayeta cikin husky voice, kawai sai ta fashe da kuka tana cewa
"Ba kai bane baka da lafiya ..amma you don't care to call me...sai yanzu nasan baka damu dani ba..." Tafada cikin kuka, husna sai kallon su kawai take gaban ta na mugun faduwa don ko kadan Ayan bai nuna yana jin haushin ihsan ba, heart dinta ta dafe tana son ganin any bad reactions da zai shaida mata her plan has worked, tana ganin ihsan ta fashe da kuka ta danyi ajiyan zuciya tana tunanin kika he's breaking up with her as she wanted cos ko kadan batajin abinda suke cewa,
"Munafuka..." Yafada cikin ranshi, azahiri yace
"Am so sorry... Kinsan banason tada maki hankali.... Is that why idanuwanki suka kumbura haka?..." Hararan shi tayi Sannan tace
"AI kaima naka are swollen... Why?..." Ta tambayeshi cikin sanyin murya, murmushin karfin hali yayi Sannan yace
"Jiya naga abinda ya chanza min rayuwa ne...." Da sauri ta daga idanuwanta ta kalleshi
"What could that be?..."
"Kar ki damu....dake  zai fara....now tell me..did you miss me?...cos jiya dake na kwana cikin raina...." Yafada kaman he means it, murmushi tayi tana wasa da yatsunta tace
"Wallahi I miss you like hell...." Tafada cikin sanyin murya, daure fuska yayi cos ba kallon shi take ba, amma tana daga kai ya sakar mata wani irin murmushi,
 Yanzu muje in ajiyeki gida ni kuma sai in dan kwanta , kallon shi tayi
"Ba fadamin abinda ya sameka ba...what happened?..."
"Is nothing bad...just a reality about life..."
"Pls ban gane ba...what actually happened?..."
"I just have a nervous breakdown..." Ya fada mata, bata ankaraba ya kama mata hannu,
"Muje,..." Da sauri ta yi kokarin fixgewa tana kalle2 amma abun mamaki ba da wasa ya rike hannun ta ba,
"Pls ka sakar min hannu... Kasan banaso kana rike min hannu..." Dan baki ya tabe,
"Kaman da gaske..." Yafada cikin ranshi
"Yanzu precious rike hannu wani abune a wajenki?..." Yafada har lokacin yana rike da hannun ta, wurin motanshi suka nufa hannun su cikin juna dukda sam ihsan bataso hakan ba, husna was gasping for air cos kawai her world was turning black, ji tayi zafi na keto mata ta koina, she can't believe what she's seeing
"Yanzu after everything... After all my effort... Har yanzu bai wulakanta taba?...oh my God... What do I have to do?..." Tafada cikin ranta azahiri ta doki kujeran motan da karfi har driver ya juyo ya kalleta tare dacewa
"Lafiya dai ko?..." Harara ta watsa mashi batare data amsa mashi ba
"Wallahi billahi I will not give up...Ayan you are meant for me and me alone..." Tafada cikin ranta, kawai sai ta fashe da kukan zuciya muryanta bai fitowa sai dai hawaye.

Tafiya suke amma kaman janta yake,
"Pls ka sakar min hannu... Zafi yanda ka rike ni..." Tafada don har Dan murda hannun ta yake kuma he us doing it on purpose, jiyake kaman ya karya hannun don yanda zuciyanshi ke bugawa saboda haushi da kishi amma sai ya daure, kawai tunanin ta taba romancing wani da wannan hannun yake
"Kaji...pls hannun ciwo...." Tafada mashi adaidai lokacin da suka karaso bakin motan,
"Oh sorry precious... Or should I call you sweet potatoes...." Yafada yana tunani abinda aka fada mashi, rike wrist dinta tayi don tana jin zafin hannun sosai, mota ya bude mata bai jira ta ba ya turata ciki still cikin zalunci daman gashi sarkin keta, yana kallon bata dauke  hannun ta daga bakin kofan ba da gangan ya maida kofa ya rufe, wani irin razanannen ihu ta saki da sauri ya bude kofan kaman bai san abinda ya faru ba
"We are just getting started... This is just genesis..." Yafada cikin ranshi, da sauri ya durkusa nan kasa ya kama hannun ta data rike tana hawaye cikin bakinshi ya saka yatsan ya fara sha kaman wani lollipop,  Yusuf da Muhammad ne suka fito, daidai parking lot sukaga Ayan durkushe yatsun ihsan cikin bakinshi ita kuma ihsan sai kuka take,
"Lafiya?..." Yusuf ya tambayeshi,
" datse mata hannu nayi mistakingly... " Yafada masu amma bai cire yatsunta daga bakinshi ba, sannu sukayi mata suka wuce Muhammad sai mamakin yanda Ayan ke licking yatsanta yake,
"Sorry precious...." Yafada yana lumshe idanuwa, kai kawai ta gyada mashi,
"Ya bar zafi?..." Kai ta kara gyada mashi badon ta bar jin zafin ba sai don yanda tsigan jikinta ke tashi saboda yanda yakewa fingers dinta, amma still bai bar shan yatsanta ba, idanuwa ya daga ya kalleta yaga ta lumshe idanuwa
"Ka bari ...I don't like this..." Tafada mashi, ahankali ya zare hannun ta ya ajiye mata kan cinyanta which in the process ya taba mata laps..." Zagayowa yayi itakuma ta tsinci gaban ta na faduwa saboda behavior dinshi na yau ya banbanta Dana sauran rana, bude motan yayi ya shiga ya zauna yana kallon ta.
"Kawai ka tafi tunda bani kadai bace...."
"Hmmm..keda waye?..."
"Husna..." Ta amsa mashi kanta kasa don kasa kallonshi tayi
"Mtwwwwwss...ta taho mana..." Yafada yana tada motaan
 "To bari in fada mata..." Ta fada tana kokarin fita daga motan wani irin fixga yayi mata yana cewa
"I said let her find her way..." Ya daga mata tsawa cikin irin muryan da bata sanshi daita ba, zama tayi tafara kallon shi wasu new tears na forming idonta, bai kalleta ba ya figi motan,
"Me nayi maka?..." Shine tambayan data yi mashi, murmushin karfin hali yayi
"Precious baki yimin komai ba...kawai banason kina ketara magana ta saboda wancan yarinyan da bata zama gidansu sai yawon gidan kawaye...." Yafada cikin nutsuwa amma inda zaa bude heart din shi wulik take saboda bakin ciki.


Husna zama tayi tana kallon su suka tafi, kuka tayi ta godewa Allah Sannan ta umarci driver da ya tafi. Tunanin next plan din ta tayi,
"Wallahi ko bazaka aureni ba...bazaka auri wancan shegiyar ba...I can't bear seeing you with her..." Tafada cikin ranta. 

Ba karamin tashin hankali ihsan ta shiga kafin su iso gida ba cos yanda yake tukin motan kaman zai tashi sama. Parking yayi bakin gate dinsu Sannan ya kalleta da red eyes dinshi tare sa sakin murmushi
"Precious.... Zan tafi sai da maraice...in ban zoba hope zakizo ganina..." Idanuwa ta zaro tana cewa
"Kambu ...saidai muyi waya..." Murmushin gefen baki yayi Sannan yace
" why bazaki zo ganina ba?...haba is not fair...kullum shikenan ni zan dinga zuwa?...nidai gaskiya tunda ba lafiya gareni ba kizo ganina... " Yafada babu zancen wasa,
"Yo haka nan sai in kama hanyan zuwa gidan saurayi?...gaskiya I can't..." Tafada atakaice, hararanta yayi Sannan yace
"Ni ai na wuce saurayin ki...wayanda basu kaini matsayi ba sun samu abinda suke so balle ni?..." Da sauri ta kalleshi
"I Don't understand your last statement..."
"Zaki gane ne...filthy slut..." Yafada cikin ranshi Sannan yace
"Ai yanmata na zuwa wajen samarin da ko gidansu basu Sani ba balle ni da bikin mu sauran few weeks?..."
"Ni bana cikin wayannan yanmatan... Ka bar hadani dasu..." Tafada cikin tsiwa
"Pretender always do the worst .." Yafada cikin ranshi,
"Ai shikenan., nasan zama na dake....amma ki Sani in har bazaki iya takawa nan da few blocks ki zo ganina ba then ni ma bazan zo ba...." Yafada fuskanshi daure,
"Yanzu don bazan zo gidan Ku ba...kai bazaka zo ba?..." Ta tambayeshi kaman zatayi kuka
"Eh..." Ya amsa mata atakaice, tsaya kallon face dinshi tayi tana tunanin ko kwana biyu bazata iyaba sai dashi
"Gaskiya inajin kunyan Umma ko Abba su ganni nazo wurin ka..." Dan tabe baki yayi
"Yo ya zaayi su sani...ai ba ganinki zasuyi ba..."
"Ban gane ba?.."
"Ai ba main house zaki shigaba...part dina zakizo..." Idanuwa ta zaro
"Lallai..." Yafada tana bude kofan motan, waist dinta ya tsaya kallo, kawai sai ya fara imagining ga wani yana shafa kugunta, kauda kanshi yayi wasu hawayen na Neman zubowa. Tana rufe mashi kofan ya fixgi motan sai gidansu, yana shiga yaga Umma tsaye bakin mota mai aiki na ajiye wasu beautiful food warmer cikin motan, Umma na ganin shi ta taho da murmushi fuskanta. Da sauri yayi parking ya fito, rungume shi Umma tayi,
"Yajikin?..." Ta tambayeshi bayan ta amsa gaisuwan shi,
"Da sauki Umma..."
"Ai yanzu wurinka zanzo...da Mun sha banban..." Tafada tana kallon shi, tsaya kallon yanda idanuwanshi suka chanza tayi
"Habibi...what happened to you?..." Karyan da yakewa mutane yayi mata,
 Girgiza kai Umma tayi
"Son I don't believe you... Haka nan mutum bai samun nervous breakdown... Remember kafin ka zama doctor ni na fara .,..pls son tell me what the problem is..." Ta tambayeshi hannun ta cikin nashi, murmushin karfin hali yayi
"Bakomai Umma... Kawai haka nan naji heartbeat din yana rising.. The next thing I was gasping for air...that is the only thing I know..." Kallo mamaki Umma tayi mashi tana cewa
"To that is a sign of heart attack...me ke damunka ?..."
"Babu komai Umma..." Da sauri yace
"Umma zan je inyi wanka in kwanta..." Yafada yana son barin wurin cos yasan Umma is very inquisitive, da haka tana iya binciko gaskiyan abinda ke damunshi,
"A shigo maka da abincin chan ko.a barshi part dina?..."
"A shigo min dasu don kwantawa zanyi bayan na gama wanka in na tashi sai inci..." Ya amsa mata dukda yasan ko a mafarki bazai iya shan koda ruwa ba balle abinci... Abinda ya dameshi ya isheshi, nan take Umma ta umarci mai aiki ta kai abincin part dinshi itakuma ta koma nata bangaren.

Ayan na shiga ya kwanta kan gado tare da lumshe idanuwa, wayanshi ya kara fiddowa ya fara kallon pic da video din ihsan, wannan Karin bai yi kuka ba, kawai sai ya fara lusting for her, chanza kwanciyan shi yayi zuwa rub da ciki, ya dinga maimaita video yana kallon each and every part of her body,
"Devil in disguise..." Yafada cikin ranshi. Mood din daya shiga yasa jikinshi daukan zafi rau, da kyar ya samu yayi wanka ya kwanta ko kaya babu jikinshi, ruf kanshi yayi da blanket yana aduan Allah yasa ihsan tayi gigin zuwa gidan nan
 Ihsan bata Dade da shiga gidaba husna ta shigo fuskanta daure, bedroom ta shiga ta tarda ihsan kwance wani irin wulakancen kallo tayi mata Sannan tace
"Wato halima ni zaki disga?...din kin gan ni bani da saurayi?... Kawai sai ki shanyani...kawai sai gani nayi  kun tafi...." Tafada  cikin fushi, da sauri ihsan dake kwance bacci na Neman dauketa ta tashi zaune
"Kiyi hakuri... Wallahi Ayan wani irin burkekken mutum ne...." Husna fashewa tayi da kuka tana cewa
"Wallahi ba karamin kunya kikasa naji ba....gaskiya gida zani..." Ta fadi abinda tayi niyyan yi,
"Dan Allah kiyi hakuri... Kinsan wannan wedding is around the corner, pls don't go..." Ihsan ta fada mata tana dafa shoulder dinta,
"Ayidai mu gani...." Husna ta fada cikin ranta.  Da kyar ihsan ta shawo husna ta yarda ta zauna amma cikin ran husna kam bata dau niyyan zama ba cos bata ganshi ba.



Sai bayan sallan zuhr Ayan ya tashi daga bacci, masjid yaje yayi salla ya dawo ya zauna yana tunanin rayuwan duniya da yanda abubuwa suka chanza mashi, ajiyan zuciya ya saki yana kara daukan wayan shi, duk sanda zai dauka sai yayi aduan Allah yasa ba ihsan bace ciki amma ina, ita din dai ce.

Karfe biyar su Muhammad sukazo gidan, hira suka shiga yi bayan sun gaido Umma a part dinta, Muhammad kallon Ayan yayi yace
"Ango kace a t and j concept aka bawa event planning ko?..." Kallon shi Ayan yayi ya kauda kanshi bai bashi amsa ba
"Kai dalla da kai ake...munason muyi masu magana su fidda mana ankon da zai dace ne..." Yusuf ya fada mashi, wani irin disgusting look Ayan ya watsa mashi Sannan yace
"Na fasa auren!!!!..…"
"What?..." Suka fada in chorus,
"What are you talking about?...." Yusuf ya tambayeshi cikin tashin hankali
"Are you guys deaf?...nace the wedding plans is no more...amma Ku kadai na fadawa tukunna..." Mikewa tsaye Muhammad yayi
"Wai uban me kake fada ne haka?...what is happening?..." Banza yayi dashi,
"Kambu ...you must be insane...anata preparation sai kace ka fasa kuma kace kar Wanda yasani?...pls guy what is the problem... Share with us...we are friends..."
"Pls nace kar Ku fadawa kowa...zuwa next week my plans will be over...lokacin sai in sanar da kowa na fasa..." Ayan ya fada in I don't care manners, da sauri Yusuf yace
"Wane irin plan ne?..."
"Ban saniba....when is over I will tell you...." Yafada yana relaxing
"Don't do something you will regret..." Muhammad ya fada mashi , daga manyan idanuwanshi yayi ya kalli Muhammad Sannan yace
"Ashe regret..."
[12/2, 7:56 PM] ‪+234 706 582 0685‬: 💙❤💛🖤💚💜
KAWARTA CE SANADI
💛💚💜🖤❤💙



®zuwairat(ummu Maryam)


2⃣9⃣


 *Asmy b Aliyu* _wannan shafin naki ne, Zuwairat naji dake har cikin ranta, I love you much, Allah ya bar mu da masoyan mu makiyan mu can hug a transformer, love you._

Yana cewa hakan yayi kokarin mikewa, aikam tureshi Yusuf yayi ya koma ya zauna yana huci yana kallon shi
"Who do you think you are.... Uban me tayi maka zakace ka fasa aureta?... What are those hideous plan you are talking about..." Yusuf ya fada cikin dagin murya, daga zaune Ayan ya nuna Yusuf da Dan yatsa Sannan ya fara cewa
"Wallahi ka kara gigin tabani sai na zubda maka hakora...." Yafada afusace Sannan ya mike, Yusuf kara tunkaranshi yayi Muhammad yayi saurin rikeshi, Sannan ya kalli Ayan yace
"Guy kasan we're one, ...we don't hide anything from each other... Ko me ke dalilin ka pls tell us...zamu baka shawaran da ya kamata...."
"Wai dole ne?...nace babu komai... Na nace ina sonta kuma ni nace na FASA... Why are you taking panadol for my headache... Na fada maku I have my plans in na gama the wedding in off...officially..." Yafada masu, ajiyan zuciya Yusuf ya saki Sannan ya dafa shoulder Ayan amma dayake he's high sai ya buge mashi hannu yana cewa
"Remove you filthy hand..." Yafada cikin fada, maganan shi ba batawa Yusuf rai ba cos he heard more indai wurin Ayan ne, cikin natsuwa Yusuf ya fara cewa
"Ba sai ka fada mana abinda ya hadaka da ihsan ba..amma pls don't do anything stupid... That gal is innocent... Don't hurt her..." Yanda yayi maganan yasa Ayan kallon shi don har zargin ya ga video din yayi, Ayan rike kugun shi yayi ya tsaya daf da Yusuf Sannan yace
"What makes you think she's innocent?..."
"Nidai shawara na baka...in har bazaka aureta ba ka sanar da su Abba da wuri and forget about any plans..." Baki ya tabe yana kallon Yusuf from head to toe
"Sannu Abba...kasan before ka bani shawara go and check your HIV status..." Yafada atakaice, bata rai Yusuf yayi
"What do you mean by that?.." Ya tambayeshi afusace,
"Exactly what you heard..." Yafada yana tafiya kaman dawatsu don yasan ya bakantawa Yusuf, afusace Yusuf ya bar falon yana huci da sauri Muhammad yace
"You shouldn't have say that..." Yafada yana bin bayan Yusuf, dariya Ayan yayi yana cewa
"To hell with you all..." Yafada yana shigewa bedroom dinshi. Bai damu ko su Yusuf da Muhammad sun tafi ba, kwantawa yayi ya fara kiran number ihsan, adaidai lokacin tana zaune falon tare da sauran yan gidansu har da aminiyarta, tana gani kiran Ayan ta mike ta dau hanyar upstairs tana picking, hira suka farayi kaman babu abinda ke faruwa, after few minutes of talking yace
"Sweet potatoes.. Zaki zo?..." Ya tambayeta cikin whisper,
"Ina?.." Tafada don ta manta maganar daya fada mata
"Oh..kin ma manta...that means you don't care about me...sai anjuma...." Ya fada mata ya fara kokarin katse wayan shi, da sauri tace
"Pls baby wait...wai kana nufin bazaka zo ba?..."
"Eh...bani da lafiya...ki zo dubiya tunda sai na bukata..." Yafada fuskan shi murtuke,
" ka jirani kofar gidanku bayan sallan ishai, Dan bazawaran dariya ya saki kaman mace sanna yace
"Hope you are not serious?... Wai meyasa kuke wannan maganan?... Don't you trust me...." Yafada mata cikin natsuwa,
"Ba haka bane...I trust you..kawai ina jin kunyan haduwa dasu Umma ne...besides ka samu sauki..." Baki ya tabe Sannan yace
"Tunda ba da rana bane... Nobody will see you..in jiraki?.." Ya tambayeta with eagerness, shuru tayi for a while tana tunanin taya zaayi taje har chan gidan su mom basu saniba
"Kilan..."
"No don't keep me waiting.. In zaizo ki fadamin kawai..."
"What are you up to?...ai kama ji sauki..." Da sauri yace.
"For where?...ko yanzu kaina ciwo yakemin...kilan in koma hospital...amma ko kadan banason inje nesa dake that's why na dawo gida so zaki zo..."
"To ..."
"Thanks precious... Oh sorry sweetie..."
"Ni Gaskiya nafison precious..." Tafada cikin shagwaba, dariyan da bai kai kasan cikin shi ba yayi Sannan
"Ok precious...." Yafada ya katse wayan shi
 Ajiye wayan yayi ya zauna ya har hannuwanshi biyu kan kirjinshi yana tunani fuskan daure tamau daman in ace ana bada kyautan daure fuska da shan kamshi to tabbas shi zaa baiwa. Sai karkada kafa yake ko meke yawo cikin ranshi oho.

Wajen sallan magrib yayi wanka ya dauro alwallah ya fito mai ya shafa Sannan ya sanya jallabiya fari tas ya fita rike da wayanshi. Part din Umma yaje ya sa mai aiki ta hada mashi cool tea ya sha ya kurkura bakinshi Sannan yayiwa Umma dasu antymu sai da safe
"Da wuri haka?..." Umma ta tambayeshi
"Eh...sai bayan sallan ishai zan dawo kuma I want to sleep early..." Ya fada mata Sannan ya fita ya tafi masjid, sai bayan sallan ishai ya fito yana kan hanya ya dauki wayan shi yafara dailing number ihsan. Daga chan bangaren ihsan tayi wanka ta shirya cikin doguwar gown ta gyara fuskanta jikinta sai kamshi yake, husna kwance tana kallon ta ranta wulik sai tunanin next solutions take,  wayanta na fara ringing ta dauki wayan ta mike ta shiga bathroom, bayan ta husna tabi da kallo tana mamakin what is happening, tana dagawa bai bata lokaci ba yace
"Ina jiranki..." Yafada kaman wani ubanta, kallon wayan tayi gabanta na faduwa,
"To..." Tafada muryanta na rawa, bai Kara cewa komai ba ya katse wayan, jiki ba kwari ta fito, batason zuwa kuma batason batawa masoyinta rai,
"I trust him kawai..." Tafada cikin ranta Sannan ta kalli husna
"Babe bari in je...Ayan is waiting for me..." Tafada batare data fada mata gidansu Ayan zataba don tana tsoron kar tayi mata fassaran yar iska, kai kawai husna ta gyada mata. Dan karamin Vail ta dauko ta yafa ta fita rike da wayanta a hannun ta.

Ayan komawa ciki yayi ya zauna kan kujera ya Dora kafanshi daya kan daya yana girgiza su a hankali. Ihsan na fitowa falo taci saa mom bata nan sai Janna kawai,
"Sis ki fadawa mom in ta sauko ina wajen Ayan..." Tafada Janna bata jira amsarta ba ta fice abinta, karamin gate ta bude ta fita, tana tafiya tana waige saboda bakajin motsin komai, gabanta na faduwa amma kaman dole haka ta dinga ta kawa har ta kai bakin gate dinsu Ayan, Dan taba gate din tayi taji da tauri alaman kulle take daga ciki, wayanta ta dauka tayi dailing number Ayan kaman yana jira yayi picking baice komai ba,
"The gate is locked..." Yafada muryan ta na rawa, baice uffan ba ya kashe wayan yayi dailing number maigadi, bayan yayi picking ya shaida mashi da akwai bakuwa waje, ya bude mata gate Sannan ya kawo ta falon shi. To kawai mai gadi ya fada da sauri ya mike ya dauko keys ya fito ya bude kofan, ihsan na tsaye sai walkiya take saboda yanda fuskan ta ke glowing, ana bude kofan ta shigo ciki jikinta sai rawa yake cos tunda uwar data haifeta bata taba zuwa gidan saurayi ba amma gata gidansu Ayan kuma bawai wajen ummanshi zataba no wajen shi,
"I trust him..." Ta kara assuring kanta,
"Muje .." taji maigadi ya fada mata, gaba ya shiga tabi bayanshi, bakin kofan Ayan yaje ya kwankwasa Sannan ya koma, mai gadi kam sai mamaki yake abinda ke faruwa amma who is he to say a word,
"Allah ya shirya...." Yafada yana komawa bakin gate.

"Come in the door is open...." Ya fada mata, hannun ta na shaking ta bude kofan, hangoshi tayi zaune ya daura kafa daya kan daya
 Yana ganinta ya saki murmushi tare da mikewa, ahankali ta shigo daki ya maida kofan ya rufe,
"Ga precious.. Ga precious... Precious sannu da zuwa..." Yafada yana kama hannun ta, kan wata doguwar kujera ya zauna daita, yanda gabanta ke faduwa yasa ta kasa magana sai dai murmushin karfin hali, zama yayi kusa daita ya dira hannun shi kan shoulder dinta Sannan yace
"What can I offer my precious..." Ya tambayeta cikin sanyin murya, ahankali ta dan ture hannun shi Sannan tace
"Bakomai.. Ya ..jikin?..." Ta tambayeshi muryan ta na cracking, kara maida hannun shi yayi yace
"Am doing great... Yanzu you have to drink atleast water..." Yafada yana mikewa, ita kawai girgiza kai tayi Sannan tace
"Nagode...am ...OK..." Tafada wannan Karin muryan ta na rawa sosai, Ayan daya nufi bedroom fridge ya tabe baki,
"Why is she shaking..." Yafada cikin ranshi, ruwa ya dauko don bai shan juice ya dawo rike cup da bottle water.

Zama yayi ya bude ruwan ya zuba mata cikin cup Sannan ya mika mata, amsa tayi amma bata shaba,
"Precious... Kisha mana..."
"No....nagode..." Tafada tana ajiye cup din gefe daya, ahankali ta mike, kallon Ayan yayi shima ya mike ya tsaya daf daita yana shakan kamshin turaren ta, da matsawa baya tayi tace
"Zan tafi..." Tafada tana kokarin juyawa, ahankali ya riketa tare dacewa
"Yanzu fa kika zo...AI ko minti biyu bakiyi ba..." Ahankali ta zare hannun ta Sannan tace
"Ai kai...nazo..gani...kuma kasamu...sauki..." Yanda take magana yasa Ayan ganewa a tsorace take, tsaya kallon kirjinta yayi, dukda da akwai kaya naked yake ganinsu,
"Will you at least give me a good by hug..." Yafada cikin sanyin murya, kallon shi tayi batace kala ba,
"Plssss..." Yafada mata Sannan ya bude mata hannuwanshi yana tsaye yana kallon ta,tsaye tayi bata je wajen shi ba,
"Yanzu precious har hug wata tsiyace?... Pls give your hubby to be a hug..." Yafada mata kaman zaiyi kuka har lokacin hannuwanshi bude, tafi minti biyu tsaye Sannan ta taka a hankali ta fada jikinshi, wani irin runguma yayi mata nan take yaji he wants her, kokarin matsawa baya tayi amma ya rungume ta gagam, bakinshi ya kai saitin kunnenta yace
"I love you..." He wants to believe he is playing, don't mean what he said amma yasan har cikin ranshi he truely love her,
"Precious why..." Yafada cikin wata irin murya, itadai kokarin ta ta kwace kanta daga jikin shi don muryan shi har cikin brain dinta, yanda ya rungume ta yasa ko kadan bata iya motsi, lumshe idanuwa yayi yafara kissing wuyanta, jikinta ne ya fara rawa sosai,
"Pls...stop.... It..." Tafada da kyar, bai saurareta ba yacigaba da abinda yake, hana kissing wuyanta ya daga face dinta, rumtse idanuwa tayi bakinta sai rawa yake, bakinshi ya dora kan nata, nan take ta bude ido
"What...are..you...." Bata idaba ya hada bakinshi da nata, aikam nan ta fara tureshi, amma ko kadan her power is nothing compared to his, yanda ya rike bayan wuyanta cikin zalunci yana kissing dinta full of hatred yasa ta fara bugunshi da two hands dinta, da kyar ta kwace  bakintawani irin zafi taji bakinta nayi, kallon yanda idanuwanshi suka chanza kaman ba Ayan ba yasa ta fara hawaye, hannun ta rike ya turata bedroom dinshi,idanuwa ta zaro ta fara cewa
"Me...me...me zakayi min?..." Ta fada cikin tashin hankali, rakugbewa tayi jikin bango, tana kallon shi from head zuwa manhood dinshi that is erected, hannuwanta ta fara yarfawa tana cewa.
"Ka rufamin asiri yanda ..." Bata idaba ya karaso ya tureta kan gado, da sauri ta mike data tashi ya kara tureta, tsaya kallon ta yayi yana imagining dinta kan gadon wani, yasan abinda zaiyi mata, yasan irin plan da ya dauka kanta and this is not the right place, kawai sai ya tuntsure da dariya yana zama bakin gadon, da sauri ta ja baya, Dan juyowa yayi har lokacin bai bar dariyaba,
"Precious Ashe haka kike da tsoro?...haba...don't you trust me any more?..." Yafada don ya kauda tunanin ta cos yasan muddin baiyi hakan ba he will not succeed, hararanshi tayi da tana gyara riganta
"Wane irin wasa ne wannan..." Tafada tana yi mashi wani hararan,
"AI kinsan I will never do something to hurt you... Za ki tafi...am just joking..." Yafada yana dariya kaman da gaske, da sauri ta bi ta dayan gefen ta sauka daga kan gadon ta dauki Vail dinta ko kallon shi batayi ba zama yayi ya kasa mikewa  yayi ya zauna nan bakin gadon
"Precious... Sai gobe..." Aikam ko kallon shi batayiba ta fice kaman walkiya saboda sauri har lokacin bata bar hawaye ba
 Bayanta Ayan yabi da harara, shi duk tsoron da take ji gani yake kaman munarfuci ne, kwantawa yayi yana tabe baki,
"I know babes like you, ayi iskanci waje ayi pretending to be decent,... I will deal with you..." Yafada babu wasa.


Umma dake tsaye upstairs baki ta bude datagan ihsan ta fito daga part din Ayan tana goge hawaye,
"Inna lillahi waina ilaihi rajuun!..." Ta dinga maimaitawa, what am I seeing? Murza idanuwanta tayi don tabbatar da ganinta amma she's not dreaming
"Subhanallahi... No wonder ya nuna ya san size dinta...Allah wadaran..." Tafada tana komawa cikin, ihsan na fita ta ta gyara Vail dinta, Abba dake dawowa yaga kaman mace ta fita daga gidanshi, karasowa yayi cikin mota yayi horn mai gadi ya bude
"Kai waur wancan data fita yanzu?..." Ya tambayi mai gadi, saida maigadi ya kalli kofan Ayan ya tabbatar rufe yake Sannan yace
"Ranka shi Dade...wannan yarinyan da karamin alh...zai aurane..."
"Wajen wa tazo?..."
"Wajen shi...."
[12/2, 7:56 PM] ‪+234 706 582 0685‬: 💜❤💙🖤💛💚
KAWARTA CE SANADI
💙💛💚🖤❤💜



®zuwairat(ummu Maryam)


3⃣0⃣



 My *amnoor* Allah ya kareki ya baki duk abinda kike so duniya da lahira, I love you so much, wannan page nakine kiyi duk abinda kikeso dashi💝



 _Pls masoya na fara gajiya da rashin hakurinku, indai baku daina wannan korafe2 ba zan daina turawa har sai na gama, ni ke rubutawa kuma ni nasan yanda na_ _ _tsara labari na, kun manta 99 days for a thief but only 1 day is for the owner, pls stay tuned cos_ _we're just getting started._




Abba na parking yaga an bude kofan part din Umma, Umma ya gani ta fito sam fuskan ta babu walwala, inda Abba yake ta nufo shima ya fito daga cikin mota, gaidashi tayi kaman yanda ta saba tana kumbure2
"Hajiya lafiya dai?.." Ya tambayeta,
"Wajen Ayan zani..." Tafada mashi, yanda tayi maganan yasa Abba ganewa da akwai matsala,
"Yayi laifi hala?... " ya tambayeta, kai kawai ta girgiza don Umma na daga cikin iyayen nan wayanda basu son fallasa laifina yaransu ga mutane koda kuwa ubansu ne,
"Kedai ki bar rufa mashi asiri ki fadamin laifin da yayi..." Inji Abba dake pretending kaman baisan abinda ta gano ba
"Nace ba komai..." Ta fada mashi kawai ita gurin ta taje ta ci burouban shi, murmushi Abba yayi Sannan yace
"Is it about yarinyan data bar nan yanzu nan?..." Da sauri Umma ta kalleshi
"I saw her too..." Ya kara fada, aikam sai Umma ta fashe da kuka tana cewa
"Yanzu alh...Ayan ya lalata rayuwar yar mutane under my roof?....Wallahi she was crying.. Dukda nasan tana da nata laifin..amma wallahi mai rabani da abubakar gidan nan sai...." Bata idaba Abba ya kama mata hannu,
" taho kiji..." Ya fada mata, binshi tayi part dinshi, zaunar daita yayi shima ya zauna gefen ta hannu yasa ya goge mata hawaye Sannan ya fara cewa
"Haj..kiyi hakuri.. Yaran zamani sai adua...AI dukan aurensu sauran kwana nawa?... Kawai ki kyaleshi...kiji ki dinga yi mashi adua don duk su biyu suna da laifi...Allah kawai ya shirya...." Inji Abba, Umma share wasu new tears tayi Sannan tace
"Yanzu alh you want me to pretend as if nothing happens?..." Kai Abba ya gyada mata alaman eh,
"Amma alh da ban haushi...Allah kadai yasan sau nawa yana kawota nan gidan..." Murmushi Abba yayi
"Ai baka rantsewa yaran zamani...rashin hakurin su is beyond your expectations... Abinda sukewa kwakwa watarana zai ishesu...dadin abun aure zasuyi...su je chan sun gane..." Umma kallon shi tayi ta galla mashi harara,
"Kai matsalan ka kenan...kullum baka daukan abu serious..." Dariya yayi
"Ai in ka biyewa yaran zamani sai hawan jini ta kamaka...kuma kilan babu abinda ya shiga tsakanin su..maybe dubiya tazo..." Kara hararan shi tayi
"Tazo dubiya kuma sai ta koma da kuka?...kai dai kawai..a bar maganan amma sai nayi Maganin Ayan..." Tafada cikin bacin rai
"Kiyi hakuri my love.. Mun dai kawai Mun haifesu amma sam bamu haifi halayensu ba.." Bata kara cewa komai ba ta mike ta hada mashi ruwan wanka.


Ayan kam baisan wainar da suke toyawa ba kawai kwanciya yayi yana tunanin yanda zai lallaba ihsan ta amince dashi ta bishi sabon gida. Yafi minti arbin kwance yana planning kawai sai ya saki murmushin keta ya dauki wayan shi.

Ihsan kam duk yanda taso controlling kanta ta kasa kuka ta dingayi har ta iso gida kawai sai taji ta tsaneshi, don tunda aka haifeta bata taba ganin yanayin namiji ahakan ba sai yau wani irin haushin shi ta dingaji, ganin hawayen ta yaki tsayawa yasa ta kasa shiga falo don tana tsoron kar su mom ko husna agane abinda ke faruwa, dakin baki ta bude ta shiga ta zauna
Ta bude sabon babin kuka, Dade zaune tana kuka Sannan daga baya ta shiga bathroom dake wurin ta wanke fuskan ta tare da gyara fuskan ta da gashin kanta daya dan barbaje, Sannan ta fito ta tarda wayanta na ringing, jin ringing din yasa ta ta gane Ayan ne, wani irin tsoki taja ta dauki wayan tayi rejecting wayan. Daga chan bangaren Ayan kallon wayan yayi ya daure fuska yana cewa
"This little bitch is rejecting my call..." Yafada yana kara dailing number.

Ihsan na daf da shiga falo wayanta ya dau kara, tsayawa tayi ta jingina da bango tana lumshe idanuwa, picking tayi Sannan tace
"What?.." Tafada cikin tsiwa, dariya ya farayi yana cewa
"Badai har yanzu kina fushi da ni ba?..." Bata amsa mashi ba ta ja tsoki, dariya ya karayi amma deep down he's boiling
"Haba precious.. Nace am sorry.. I don't know what came over me...pls in kinason ganin manzon tsira ki yafemin..." Yafada kaman zaiyi kuka, ihsan hararan wayan tayi bata ce kala ba kuma bata kashe wayan ba
"Babyna pls ki yafemin... Kinsan I love you.. Wallahi sharri shaidan ne...I problem ko fingernail din ki bazan kara tabawa ko munyi aure sai kin amince... Pls pardon me..."
"Kai dai Allah ne yasa ka nunamin halinka...you are cruel...mean and wicked..." Ayan tabe baki yayi ya daga wayan daga kunnenshi ya kalleta yana cewa
"You will soon know the real meaning of cruelty..." Tafada under his breath,Sannan yace
"My love am sorry... Ki gafarta min...I have never touch any woman..." Kuma wannan gaskiya ce, yacigaba dacewa
"Am sorry.. Ki fadamin abinda kikeso..." Baki ta tabe
"Ni babu abinda nake so illa ka bar kirana har in huce..." Dariya Ayan yayi
"Kina dai son in mutu ne...pls baby am on my kneels..forgive me..." Ya dinga yi mata magiya, amma dayake ihsan is somebody with a simply mind sai ta yafe mashi,
"Gobe zanzo kaiki school..."
"No..banso...."
"Hmmm zakije karuwancin kenan..." Yafada cikin ranshi azahiri yace
"Baby why?...are you still mad with me?..." Dan rolling manyan idanuwanta tayi Sannan tace
"Nop...ai ya wuce...amma tunda ba lafiya garekaba kawai ka huta..." Baki ya tabe
"Ke dai fadi gaskiya... Kawai bakison in daukeki cos you are still mad at me..."
"Not at all... Kawai I want you to rest..." Ta fada cikin sanyin murya.
"Ok..love you with all my heart..." Yafada yana shafa kanshi
"Love you too..." Ta amsa mashi Sannan sukayi sallama. Falo ta shiga taga ba kowa, direct upstairs ta hau ta tarda husna zaune da laptop gabanta da gani film take kallo amma she absent minded don har ihsan ta shigo bata Sani ba har saida ta tabata ta firgita, daga kai tayi ta kalli ihsan ta sakar mata murmushi, Dan kura mata ido tayi for a moment Sannan tace
"Babe your eyes are swollen..." Tafada, tana Neman jin good news, ihsan kallon ta tayi
"Ahhrr..." Kaman zatayi magana sai kuma tayi shuru, da sauri husna ta mine ta dafa shoulder dinta
"Babe is anything the problem?.." Ta tambayeta sounding very caring, murmushi ihsan tayi
"Nothing... Kadai bacci nakeji..." Tayi mata karya for the very first time, husna kura mata ido tayi for a moment Sannan ta fara sniffing jikin ihsan
"Lahhh...babe..kamshin turaren Ayan kike?..." Da sauri ihsan ta kalleta
"Ya akayi kika San kamshin turaren Ayan..." Ihsan ta tambayeta sounding suspicious, dariyan karfin hali tayi
"Wallahi you are funny.. Kinsan I have a very good sense of smelling... Am joke aside.. Why are you smelling like him...kodai??..."
"Kodai me?..." Ihsan ta fada tana hade rai, Dan bugun shoulder dinta Hus.a tayi tana cewa
"Ke kiyi hakuri naga kaman you are tensed..." Ihsan bata ce komai ba ta fara cire kayan jikinta sai taji da gaske kamshin ayan take
 Husna sai binta take da kallo ko Allah yasa ta fada mata abinda ke damunta amma shuru bata ce mata komai ba, wayanta ta dauko tana cewa
"Baby dazun nayi browsing best ashobi pics of the year., inason muyi selecting Wanda muke so..." Tafada mata don taji amsarta
"Ok..amma mu bari sai gobe mu duba cos yanzu kai cewa yakemin,.." Tafada lokacin daga ita sai pant da bra, bayan wuyanta ta dan shafa don har lokacin bata bar jin zafi ba, sai lasan bakinta take tana zubda saliva don har lokacin tana jin bakinshi cikin nata, husna sai binta take da kallo saboda yanda take zarya cikin toilet saboda zubda saliva, do kawai tasa mata ko zata fada mata abinda ke damunta cos she couldn't figure it out, daga baya kan gado ta hau har lokacin babu komai jikinta sai pant and bra, matsawa husna tayi kusa daita Sannan tace
"Haba babe...da ganin ki kina cikin damuwa amma you are not sharing it with me...kinsan saboda mu dinga sharing problem din mu yasa na dawo nan mussanman now that your wedding is around the corner.. Pls tell me...hankali ma tashi yake in na ganki haka..." Tafada kaman zatayi kuka, ihsan kallon ta tayi for a moment sai taji bata kyauta mata ba for not being truthful,
"Gidan su Ayan naje...." Nan ta fada mata duk abinda ya faru tsakanin ta da Ayan, husna rushewa tayi ea kuka saboda kishi don ita gani take his hands belongs to her,
"Yanzu babe abinda wannan azzalumi yayi maki kenan?... Gaskiya ki fadawa mom da dad...mugu ne shi...he don't deserve you..." Tafada cikin kuka kaman gaske, ihsan dafa shoulder ta tayi ta fara cewa
"Stop crying.."
"Ki tashi kije ki fadawa mom...." Da sauri ihsan tace
"I can't share such thing with her...ni dai kunya nake ji..." Hararan kasan ido husna tayi mata
"Saboda me?...badai zaki yafe irin wannan taadancin ba..." Dan tabe baki ihsan tayi
"Ai har na yafe mashi...I love him...." Wani irin gululu husna taji
"Wai she loves him...she's loves my man...we shall see..." Ta fada cikin ranta, azahiri tace
"Ni kam sai na fadawa su mom..." Da sauri ihsan ta daga mata hannu
"No...don't try it...ke kadai da fadawa ..." Tafada tana kwantawa, wani irin disgusting look husna tayiwa bayan ihsan Sannan ta kwanta tana cewa
"What ever..."



The following day Ayan ya yi shirin aiki ya tafi part din Umma suna hada ido ta watsa mashi wani irin kallon haushi da takaici, gaidata yayi ta amsa kaman bataso, zama yayi gefen ta tare dacewa
"Umma nayi wata laifi ne..."
"Kaci burouban ka...tashi ka bani wuri..." Ta daka mashi tsawa, jiki ba kwari ya mike ko breakfast baiyiba ko kadan baiyi tunanin Umma taga ihsan ba cos a nashi tunanin in har taga ihsan kashinshi ya buce.
Da wuri su ihsan
 suka tafi school suka dawo da dare Ayan yazo suka sha hira na so da kauna baka taba cewa da akwai wani Abu cikin ranshi, don har snacks da chocolate ya kawo mata ta bawa siblings dinta.

Wace gari ma the same thing har ihsan ta mane abinda ya faru tsakanin su, suna zaune suna hira ya kalleta yace
"Precious wata antyna ta haihu...inason ki rakani kasuwa in sayo kayan babies...."
"Gaskiya ba sai na raka ba...kawai in ka  shiga inda ake saida kayan yara ka fada masu su baka mai kyau tunda nima basanin kayan yara nayi ba..." Ta amsa mashi atakaice, marairace fuska yayi Sannan yace
"I wanted us to go and see the baby together... Tunda jibi suna gobe sai muje kasuwa  mu sayi kayan mukai..." Yafada mata kaman gaske,
"AI ina da lectures gobe...."
"Karfe nawa kuke gamawa?..."
"Karfe 2..."
"In naje daukan ki sai muje kasuwa daga nan so mu wuce gidan..." Shuru tayi bata ce komai ba
"Kinji..." Ya kara fada mata, kai kawai ta guda mashi. Haka suka sha hira Sannan sukayi sallama ran Ayan kwal da farinciki.

Ihsan  na komawa  ta sanar da mom zata shiga kasuwa gobe don haka bazata dawo da wuri ba, tana haura sama ta fadawa husna gaskiya kan inda zata taka Ayan, itama murmushi tayi tana cewa
"Daman jiranki nake kizo in fada maki...grandma tace inzo Maiduguri in amso maki sako tunda bazata samu samun zuwa ba......" Tsale ihsan ta daka tana fadawa jikin husna
[12/2, 7:57 PM] ‪+234 706 582 0685‬: 💙❤💜🖤💚💛
KAWARTA CE SANADI
💙💚🖤💛💜❤



®zuwairat( ummu Maryam)



3⃣1⃣




 _Ban manta dake ba my dear *queen mermur* ban bance dake ba, ummu Maryam tace I love you_💋



Husna ma rungume ta tayi cikin ranta tana tunanin Sam bata ga zamaba tunda har yanzu bata ga matsala tsakanin Ayan da ihsan ba.

Wacegari ihsan ta shirya cikin India dress mai wando da riga, kalan orange and green, gyara kanta tayi ta shafe dukkan jikinta da perfumes as usual ta sauko ita kuma husna shiryawa tayi ta dauki bag dinta, around 9: 00am Ayan ya zo gidan daukan ihsan don ya kaita school, sanye yake da English wear sai kamshi yake fuskan nan sam babu walwala
 Kiran ihsan yayi ya sanar daita yana jiranta,
"Ok.." Kawai  Tafada ta kalli ihsan
"Babe muje...yazo..." Dan bata rai husna tayi tana cewa
"Babe da ya kaiki kawai tunda ni ban zuwa school yau..."
"Aa...tashi mu tafi sai ya ajiyeki..." Ta fada tana kama mata hannu. Mikewa sukayi ihsan ta tayata daukan bag dinta da tazo gidansu ihsan dashi, wurin mom sukaje tayiwa mom ta bata 5k kyauta ta mikawa ihsan 5k itama don a tunanin ta wani abu zata saya don ta fada mata zata market yau. Godiya sukayi kowacce ta zuba kudinta cikin bag.

Suna bude gate Ayan dake zaune yayi relaxing  cikin motan, da dagawa yayi ya kalli gate din, cire glasses dake fuskanshi tare dacewa
"Kan uban nan!!.." Yafada cikin ranshi dayaga ihsan rike da traveling bag, suna karasowa ya fito ya tsaya yana kallon adorable face dinta gaidashi tayi tana murmushi ya amsa, itama husna gaidashi tayi ya basar yana cewa
"Wannan bag din fa?... " ya tambayeta
"Na husna ne..." Ta amsa mashi, daure fuska yayi ya bude mata gidan gaba yayi tashiga shima ya shiga, husna bude baya tayi ta shiga ranta wulik don bakin ciki, kallon ta yayi ta mirror yaga ta wani hade rai, tabe baki yayi ya ja motan, suna zuwa bakin titi ya tsaya gefe daya yace
"Precious ki bata bag din ta tsaida abun haka ko?..." Ya fada mata babu wasa, Dan marairace fuska tayi
"Haba baby...mu ajiyeta mana kafin mu wuce..." Wani irin kallo yayi mata
"Pls stop wasting my time... Ina da abubuwan ya kafin inzo daukanki muje kasuwa...I don't have time..." Yafada cikin fada, da sauri husna ta fita ta kwace bag dinta daga hannun ihsan ta bar su nan, tada motan yayi ihsan ta bude marfin motan
"Kawai ka barshi....I will go to school myself..." Tafada tana kokarin fita, da sauri ya kamo hannun ta yana cewa
"Haba precious... Yanzu wancan zata shiga tsakanin mu?..." Kallon hannun shi dake kan hannun ta tayi yayi sauri zare hannun shi tare dacewa
"Sorry.. Na mance.." Yafada yana ajiye hannun shi kan laps dinshi,
"Zaki ci uwarki ne..." Ya fada cikin ranshi.
"Ni gaskiya banason yanda kake wulakanta friend dita...." Tafada kaman zatayi kuka
"Am sorry... Bazan karaba...yau shine first and last..." Ya fada mata, shuru tayi ta maida murfin motan ta rufe, ya figi motan kaman zai buge husna nake tsaye tana jiran abun hawa, wani irin gululu taji, kawai sai hawaye,
"His love is becoming unbearable..." Tafada cikin kuka.
"Hmmm....wallahi you will beg for my love..." Ta fada cikin ranta.


Suna zuwa school ya ajiyeta tare da fada mata sai ya dawo daukanta.


Yana barin wurin ya nufi unguwan da gidan shi yake, budewa yayi ya  shiga, direct part dinshi ya shiga ya chanza bedsheets dake kan gadon Sannan ya fita, wani unguwan yaje yayi horn kofar wani karamin gida, baa Dade ba wani saurayi ya fito, keys ya mika mashi
"Gashi...ka tabbatar kana gidan kafin karfe biyu..." Ya umarceshi, da sauri saurayin yace
"To yallabai..." Motanshi ya shiga ya bar wajen, gaban wani gida ya tsaya ya dauki wayan shi ya kira wata number, ana picking yace
"Safeena gani nan kofar gidanku ...ki fito I need your assistance..." Yafada atakaice Sannan ya kashe wayanshi.
 Relaxing yayi tare da dora legs dinshi gaban mirror tare da kafa glasses dinshi sai karkada kafa yake. Few minutes later wata budurwa wacce bazata wuce shekara ashirin zuwa da biyu ba ta fito sanye da black gown looking very excited, murmushi ne dauke kan face dinta, karasowa tayi kusa da motanshi Sannan tace
"Doctor ina kwana?..." Tafada sounding excited,
"Lafiya lau..." Yafada yana gyara zaman shi,
"Lafiya dai naga doc da kanshi gidan mu?..."
"Eh lafiya ...ki shigo mana..." Ya fada mata, ahankali ta sa hannun ta tabude motan ta shiga, Ayan fuskan ta ta yayi Sannan yace
"Sister safeena pls wane duty kike yau?...."
"Afternoon..." Ta amsa mashi
"Ok..pls wata alfarma nake son kiyi min..."
"To meye...anything for you..." Ta amsa mashi thinking what exactly he wants from her, nan Ayan ya fada mata exactly abinda yake so tayi mashi, shuru tayi tana sauraron shi har ya kai aya Sannan tace
"Yaushe zanyi hakan?..."
"Yau...in kin amince zan zo daukan ki by 1: daga nan sai ki wuce hospital tunda is not far..." Shuru dai tayi for a while Sannan tace
"Babu matsala... Allah ya kaimu ..." Ta amsa mashi feeling comfortable don tasan Ayan will not do anything stupid,
"Nagode sosai...sai nazo daukanki..." Ya fada mata, murmushi kawai tayi ta fita daga ciki motan. Shi Kuma ya bar wajen ya koma office, a corridor suka cikaro da Yusuf amma ko inda yake Yusuf bai kalla ba shima bai kalli Yusuf ba kowa ya wuce sai kumbure2 yake.





Husna kam tsaida mai adaidaita tayi ta fada mashi ya kaita hotoro.
Akofar gidan malamin mami ta tsaya ta biya mai adaidaita ta shiga gidan da bag hannun ta ta kasa hakuri taje gida ta ajiye shi, tana shiga gidan yan gidan sukayi mata maraba kasancewan sun san ta sosai saboda yanda mami ke yawan aikota, turakan Malam ta shiga suka gaisa Sannan Malam yace
"Yata... Hajiya ta aikoki?..." Kai ta girgiza tare dacewa
"Aa..wata matsala ce ya kawoni..." Mutum gyara zama yayi yana kallon ta
"Ina jinki yata..." Kuka ta farayi Sannan ta fara cewa
"Malam.. Wani ne nakeso...Sam baisan da zamana ba....kawata yakeso...Kuma kullum in muka kahadu da shi banda wulakanci babu abinda yakeyi....Dan Allah Malam ka taimaka min... Wallahi in ban sameshi ba mutuwa zanyi..." Tafada tana kaman kafan Malam, hannun ta mutumin ya rike Sannan ya saka hannu cikin aljihunshi ya dauko hanki ya bata
"Goge hawayen ki......" Amsa tayi ta goge fuskan ta amma still tears sai Flowing yake,
"Yata..." Ya kirata,
"Naam baba..." Ta amsa mashi tana kuka
"Hajiya tasan zaki zo nan?..." Ya tambayeta, ki ta girgiza mashi tare dacewa
"Aa...bata Sani ba.." Ta amsa mashi, kallon yatsaya yau for a while Sannan yace,
"Me kikeso ayi maki..." Da sauri husna ta fara cewa
"Inason arabasu...inason ya wulakanta ta fiye da yanda yake Mani...inason ya soni kaman ranshi...Dan Allah baba ka taimaki raina..."
"Wannan ba wani abu bane..." Murmushin jin dadi tayi yacigaba dacewa
"Amma bazaki samu dukkan su lokaci daya ba...dole sai dai a kafara da daya.." Da sauri ta bata rai
"Baba me zai hana a yi su lokaci daya?...yanzu auransu sauran kwana ashirin da hudu..." Da sauri mutumin yace
"Ansa masu rana ne?.."
"Eh..." Ta amsa mashi, kai ya fara girgizawa
"Yata indai haka ne to INA baki shawaran mu kyalesu...kinsan da akwai rabo.. Kuma ni gaskiya bana irin wannan aikin...ko.ba gaskiya ba?...." Fuhhh husna ta mike
"Baba kawai ka fadamin bazaka iyaba amma wane rabo?... An raba mata da miji... Uwa da da...balle saurayi da budurwa?..."
"Eh ko da irin aikin da yakeyi ni gaskiya bani aiki da bakaken aljinu..." Bata kara sauraron shi ba ta fita
 Ko kallon yan cikin gidan bata yiba ta fita. Wajen wani malamin mami ta kara, shi wannan cewa yayi ta kawo dubu Dari cash taga aiki, rokanshi tayi kan zata kawo  dubu hamsin daga baya ya kawo sauran yaki. Atakaice har daya na rana bata koma gida ba tana yawon gidan malaman mami amma duk inda taje sai an samu matsala amma ko kadan batayi giving up ba, wurin wani data je har cewa yayi zai yi mata aiki amma sai ya fadawa mami nan ma barin wurin tayi, tana tafiya tana hawaye kaman wata zautatta. Gindin wata bushiya ta tsaya ta ajiye bag dinta Sannan ta dauko wayanta ta kira grandma dinta, matar da picking ta fashe da kuka
"Wallahi grandma mutuwa zanyi...sonshi zai kashe ni..." Tafada cikin kuka sosai,
"Ki taho...." Matar ta fada mata atakaice, da sauri tace
"Mami bata barina...."
"Ki kwantar da hankalin ki...zan kirata yanzu...." Inji grandma,
"To shikenan..." Tafada tana kashe wayanta, wani yaro dake yawo da pure water ta kira ta sayi daya tasha sai zufa take kaman wacce aka sa dole 5k da mom ta bata ta kashe abanza wurin transport zuwa gidan malamai.


Ayan na zaune sai kallon agogo kawai yake. 10 minutes to 1 yayi alwallah. Yanajin kiran salla ya fita yabi jami Sannan ya dauki motanshi ya fita. Yusuf da Muhammad sai kallon shi kawai suke suna mamakin irin zaryan da yake haka.
Kofar gidansu wannan budurwan ya tsaya ya kira ta ta fito sanye da after dress amma daga cikin kayan aikin nurse ne. Gaisawa sukayi ya kalleta tare dacewa
"You look gorgeous..." Yafada yana kashe mata ido daya. Murmushin jindadi tayi batace kala ba.
Driving yake amma hankalin shi na kan agogon don he don't want to keep ihsan waiting. Yana zuwa kofar gidanshi yayi horn wannan saurayin dayaje gidansu ne ya bude mashi gate bai shiga da mota ba suka fito da yarinyan, general parlour ya kaita ya kara fada mata exactly abinda yake son tayi, kai kawai ta gyada mashi tana mamakin abinda ke faruwa. Dasauri ya fita ya kama hanyan buk.

Kan hanya ya tsaya ya sayi take away guda biyu da abinsha mara sugar.

Ihsan ta gama lectures tana tsaye tana jiran zuwan shi sai hamma take saboda gajiya, ji take inda batayi wa Ayan alkawarin zata rakashi ba da gida zata straight taci abinci ta kwanta cos she's exhausted. Daga nesa ta hangoshi ta taho, ahankali ta fara takawa cikin kasaita kaman yanda ta saba, Ayan tuki yake ahankali amma hankalin shi na kanta cos she walks like a queen, kawai sai ya tuna video dinta dake cikin wayanshi sai ya hade rai. Kusa daita yayi parking ya fita ya bude mata, gaidashi tayi tana murmushi shima ya amsa yana kallon eyeball dinta at that moment inda ihsan zata nutsu she would have seen something amma Sam bata luraba, shiga tayi ya maida ya rufe ya zagayo ya shiga ya kalli yanda take lumshe idanuwa yace
"Sannu..."
"Yauwa..." Tafada tana ajiye bag dinta gefe tare da gyara Vail dinta dake Neman barin kanta. Ayan kallon gashin kanta dake sheki yayi ya kauda kai cos tunanin wani ya taba ganin wannan kai naked kawai yake. Dan kallon shi tayi Sannan tace
"Baby...why not mu bari next time muje?...wallahi am so tired..." Tafada tana relaxing.
"Ayya.. Sorry.. Amma na Riga na fada mata we're coming.. But tunda you are tired kawai ba sai muje kasuwa ba..kawai Zan bata kudi...ko ya kikace?..."
"Ok then...ina tsoron kar bacci ya dauke ni ne..." Tafada tana hamma,
"Sorry... Relax kafin mu isa..." Y fada mata. Yanda tayi relaxing yasa kirjinta Dan  bankarawo, kallon ta yayi ya kauda kanshi ya cigaba da driving abubuwa da dama suna yi mashi yawo cikin kai.

Quarter to 3 suka iso gidan, horn yayi aka bude mashi,
Ya shiga, ihsan dake zaune kallon compound din tayi taga kaman babu mutane cikin gidan, kalle2 ta zauna yi har yayi parking,
"Baby gidan looks new..." Ta fada, murmushi yayi mata
"Eh is new..." Kallon shi tayi gabanta na faduwa
"How...ba gidan antyn ka bace?.." Yanda tayi maganan yasan she afraid
"Gidanta ne...basu Dade da dawowa ba.." Yafada yana bude motan. Fitowa yayi ya bude mata, ahankali t fido pure white leg dinta dake sanye da toms lemon green kalan kayan ta. Rufewa Ayan yayi ya yi gaba tabi bayan shi, ihsan dai kallon gidan take don ita har yanzu she couldn't believe an taba rayuwa cikin gidan, Kuma tasan gidan haihuwa baa rasa mutane amma nan wayam, Dan ajiyan zuciya ta saki don anata tunanin Ayan will not go this far to do something bad, bakin kofa Ayan ya fara knocking as planned. Few seconds later wata budurwa ta bude da murmushi fuskan ta, tana ganin ihsan ta dan chanza fuska for one to two seconds cis she wasn't expecting to see him with a woman, shi dai kawai fada mata zai zo da mutum Kuma tayi pretending nan gidan ta ne.

Ihsan dadi taji data ga mace yaruwarta dukda she wasn't expecting to see such a young gal tunda Ayan Yafada mata antyshi ce.
"Sannu Ku da zuwa..." Safeena tayi karfin halin cewa, cos tana ganin innocent ihsan jikin ta yayi sanyi, Ayan bata rai yayi daya lura da mood dinta. Hakan yasa tayi saurin sakin jikinta cos he's the boss.
"Ku shigo mana..." Ta fada masu, ahankali suka shiga cikin wagegen falon da ba komai, hanyan part din Ayan safeenat ta nufa as planned tana cewa
"Bisimillan Ku...." Tafada tana bude kofan, ihsan dai murmushi ne kwance kan fuskan ta amma batace kala ba, zama tayi kan wani hadadden sofa shima Ayan ya zauna. Gaisawa suka farayi da ihsan har lokacin kanta kasa bata daga kaiba balle ta kalli face dinta,
"Bari in dauko muku ruwa..." Safeena ta fada tana mikewa, barin dakin tayi after 10 seconds shima Ayan ya mike yana cewa
"Precious... Bari in dauko wayata na mance ta a mota..." Yafada mata,
"Ok..." Ta fada cikin sanyin murya.

Da sauri ya fita ya tarda safeena ta dauko handbag dinta jikinta babu kwari,
"Thanks so much..." Yafada mata, bata iya cewa komai ba cos she believed she has betray her fellow woman, har bakin gate ya rakata ya dauko kudi yan dubu daya2 ya bata ta ki amsa ta tafi. Shi dai maigadi kudi ya bashi ya amsa yayi godiya ya tafi, kulle gate din yayi ya bude motanshi ya dauko takeaways daya saya tare da drinks ya dawo cikin . general falo.
[12/2, 7:58 PM] ‪+234 706 582 0685‬: 💙❤💜🖤💚💛
KAWARTA CE SANADI
💜💙❤🖤💚💛




®zuwairat( ummu Maryam)




3⃣2⃣



 _Wannan shafin naki ne *ummey zeey* , I want you to know that you are unforgettable, I love you wella._




Rufe kofan general parlour yayi batare da ya kulleba cos yasan nobody is coming, hanyan part dinshi yayi rike da takeaway, hannu yasa ya bude kofan, ihsan dake zaune inda ya barta ta daga kai ta kalleshi tare da sakar mashi murmushi amma ko kallon ta baiyiba ya maida kofa ya rufe ya nufi inda dinning take, binshi tayi da kallo ya zauna, sai lokacin ya kalleta
"Zo muci abinci..." Ya fada mata atakaice fuskan shi babu faraa, kai kawai ta girgiza mashi ya tabe baki tare da fara bude abincin, ihsan ganin 2,3,4to 8 minutes antyn Ayan bai dawoba yasa tace
"Baby ina antynka?..." Ayan dake kai abinci bakinshi kallon ta yayi yace
"Ta tafi...." Ya fada mata atakaice, da sauri ihsan tace
"Ban gane ta tafi ba...."
"We are alone... Is just you and me.... Precious..." Yafada yana cin abinci hankalin shi kwance. Bata rai ihsan tayi tana dan dafa kirjinta dake bugawa da karfi tace
"Pls if it is a joke stop it...pls tana ina?..." Ta kara tambayan shi not believing what he said, kara tabe baki yayi Sannan yace
"Who is joking with you?... Nan gidana ne...is all a plan... Wannan shine gidan da da zaa kawoki before I find out you don't worth it..." Yafada yana cin abincin shi, tsoki ihsan taja ta dauki bag dinta ta mike, da sauri Ayan ya kalleta da wani irin kallon da bata San shi dashi ba Sannan yace
"Wallahi if you as much as move an inch...Wanda ke cikin jahannama sai yafi ki jin dadi...." Yafada sounding extra serious amma dayake ihsan is stubborn banza tayi dashi ta fara heading for the door, da sauri ya mike cikin taki biyu ya kamata, wani irin wawan mari ya dauketa dashi tare da tureta kasa. Idanuwa ihsan ta zaro cos komai nata tsayawa yayi cos Marin ya mugun gigitata, nunata yayi da yatsa
"Try moving again and more than this awaits you..." Yafada, har lokacin ihsan bata dawo hayyacinta ba, kan dinning ya koma.
Ahankali ta daga hannun ta ta Dora inda ya mareta ko kadan babu hawaye idanuwanta amma inda zasu zubo mata da zatafi samun sauki, wani kara kunnenta ya dingayi har few seconds Sannan jinta ya dawo, ahankali ta juya ta kalleshi sai lokacin hawaye suka fara gangarowa idonta, ko kallon ta baiyi ba, ahankali fara cewa
"Pls...meye laifina?..." Tafada muryan ta na rawa, murmushin yake yayi ya rufe abincin ya fuskan ce Sannan ya fara cewa
"Bakisan laifi kiba?..." Da sauri ta daga mashi kai, tana hawaye har lokacin hannun ta inda ya mareta,
"Ok..then...when am done with you..... Zakiyi confessing laifinki da bakinki......" Yafada yana mikewa, kuka ta farayi tana komawa baya, da sauri ta fara cewa
"Pls ...ko me nayi maka ka yafemin....pls don't hurt me..." Ta fada tana ja da baya shi Kuma yana nufota,
"Ba hurting dinki zanyiba....kawai I want to swim in you the way those guys are swimming in you...." Yafada yana daga ta tsaye, ihu ta saki ya sa hannun shi ya bige mata baki,
"I don't want to hear a word from you... Stop this pretending...." Da sauri ta sa hannun ta ta kama bakinta
 Tashin hankali bai barta ta gane inda maganar shi ta dosa  ba, kuka ta farayi sosai tana cewa
"I beg you... Pls don't ruin me..." Bata idaba Ayan ya kwace da dariya yana cewa
"Did I hear you say ruin?...well ni kika yi ruining, cos I loved you fiye da yanda nake son kaina...I was ready to give all I have just to make you happy... Ihsan kin cuceni....kin yaudareni....I don't know you could be a slut...." Sai lokacin ihsan ta gane zargin da yake yi mata, idanuwa ta lumshe wasu zafafan tears suka zubo, ahankali tayi kneeling gabanshi,
"Pls....pls....am not a slut....kill me if you want... Amma pls dont...call me a slut...." Tafada cikin kuka sosai,  Ayan kura mata ido yayi sai ya fara hawaye, he wish she saying the truth amma yana da enough evidence to show that she's a slut, murmushi yayi ya goge hawayen shi yana cewa
"I will make sure you never longs for any man...zanyi maki abinda babu Wanda ya taba yi maki...." Jikin ta ne ya fara rawa, tana yarfe hannuwanta tana cewa
"Daman this is what you have always wanted from me....daman abinda kakeso kenan...pls ka tausayawa rayuwata....", dariya yayi yana cewa
" drama queen..., ban taba zinaba...sai yau zan fara so kisan duk halin dana shiga daga yau is as a result of you deciet..." Yafada sannan ya Daga ta tsaye
"Kizo in nuna maki what you missed..." Yafada yana Jan hannun ta da karfi
 Kara ta saki saboda zafin hannun ta daya rike, janta ya farayi har zuwa main falo ihsan sai ihu take tana
"Dan Allah kar kyaleni...Wallahi am not a slut..." Ayan dake hawaye saboda bakin ciki don ji yake kaman yanzu ya fara ganin wannan video, main falo ya jata Sannan ya fara cewa
"Look... I was planning to be happy with you..." Yafada itadai batace kala ba sai kuka, hanyan daya part din yayi har lokacin yana janta, sakin jikinta tayi ta fadi kasa amma bai saki hannun ta ba yacigaba da janta, yana bude kofan ya wullata cikin falon dake kaman nashi saidai babu kaya ciki, yana wullata ta fadi kasa ta kife kasa
"This would have been your apartment..." Yafada yana kallon yanda take kuka kaman ana zare mata rai,
"Kuma the wedding is off...amma abun mamaki har yanzu I love you..." Yafada yana goge hawayen fuskan shi, nufota yayi
"Why did you play with my heart... Why do you toy with me?..." Ihsan ja take da baya tana cewa
"Pls kayi hakuri.... "
"Ihsan I was threatened... Amma ban fasa ba...I was warned still ban fasa ba...that's is to tell you I deeply love you... Amma..." Yayi shuru yana hada ta da bango da karfi, wani razanannen kara ta saki saboda yanda bayanta ya bugu, Dan ne ta yayi ya daga riganta ya kama boobs dinta da karfi, ihu ta dingayi
"Are you enjoying it?..." Ya daga mata tsawa, da sauri ta girgiza mashi kai tana haki hawaye na sharara,
"Pls stop...you ...are hurting... Me..." Tafada cikin kuka mai tsanani, kara chakumo su yayi cikin zalunci ta kara kwala ihu, cikin tsiwa tace
"Koni karuwa ce...ka rabu dani...." Dagata yayi ya kara dauke ta da mari, ahankali tayi baya numfashin ta na neman daukewa,
"Bazan rabu dake ba...I will deal with you more than you do to me...." Ihsan kwantawa tayi kasa saboda yanda kanta ke zafi da ciwo, binta yayi kasa yasa hannu ya fara kokarin cire mata Riga, dukda bata da karfi rike riganta tayi gam,
"Bazaki sakiba sai na shake ki?..." Yafada da karfi, Ahankali ta gyada mashi kai tana kallon eyeball dinshi,
"Just kill me....pls ka kasheni...amma in dai ina raye...I will not have what you want...." Tafada cikin dakekken murya.
"Ok..then..." Yafada ya mikewa, buttons din riganshi yafara balle wa, ihsan tana nan kwance tana duk aduan dayazo zuciyanta, kura mashi ido tayi tana kallon yanda idanuwanshi suka sauya kaman ba Ayan dake zuwa gidan su looking nice and cool ba, yana gama ya wurgar da riga ya cire three quarter dake  jikinshi, da sauri ihsan ta runtse idanuwanta, daga shi sai singlet da boxer, duka wa yayi ya dauke nan ta fara yaginshi da fingernails dinta dama tana ajiye su, nan take ya saketa kasa ji kake timm, wani kara ihsan ta saki tana kama kanta da hannuwanta biyu saboda azaba,
"Wayyo Allah...nashiga uku....I cursed the day I meet you..." Ta fada tana nishi, Ayan kallon chest dinshi data yaga yayi yaga ta ji mashi ciwo, hannun ta ya kama ya fara janta nan kasa.
"Nima I cursed the day I meet you bitch Yafada yana janta, sakin jikinta kawai tayi ya dinga janta har general falo, sakinta yayi ya zauna koma ya zauna gabanta yana kallon ta, itama daga idanuwanta tayi ta kura mashi ido hawaye na zauna,
" ihsan...who is the guy?..." Ya tambayeta, bakinta sai kyarma yake amma ta kasa magana, ahankali ta daga hannuwanta ta rike kanta gam, jiri kawai take gani,
"Ihsan who is the person you are sharing your beautiful body with?...." Ya sake tambayan ta, kura mashi ido tayi ko kiftawa bata yi, wani irin kallon tsana da kiyayya take mashi,
"I loved you....ina kaunan ki ihsan....I adore you..." Yafada yana kara mikewa, daukanta yayi ahankali tace
"In har ka taba jin kwayan zarran sona cikin ranka....pls...let me...go...." Ta rokeshi, banza yayi daita yacigaba da tafiya, kofan part dinshi ya bude ya shiga falon ya kara shiga daya daga cikin dakin kan gadon ya wullata, da sauri ta mike zaune tare da sauka daga kan gado
"Halima...hau kan gadon nan da kanki..." Ya umarceta, makalewa tayi cikin bango tana kuka
 Inda take tsaya ya nufa ya manna ta jikin bango ya fara rough play daita sai kuka take tana bashi hakuri amma a banza, kara daga riganta yayi ya sa bakinshi kan boobs dinta ya fara bad play daita Kuma not in a romantic way but in a wicked way, ihu kawai take, kara daukanta yayi ya kaita kan gado wannan Karin ko karfin daga kanta bata dashi, kwantawa kawai tayi tana kallon yanda yake kokarin rabata da kayan jikinta, daga idanuwanta da sukayi mata nauyi tayi ta kalleshi, ahankali ta daga hannun ta ta tabashi, tsayawa yayi yana kallon ta, da kyar ta bude bakinta ta fara cewa
"Pls...in ka ....samu...abinda ...kake...nema...just.. Kill...me..." Ayan daya fita hayyacinshi tabe baki yayi
"Wasu basu kasheki ba sai ni?...sai dai in na ajiyeki kofar gidanku ki kashe kanki saboda Dan unguwan Ku yayi screwing dinki...pretender..." Yafada babu alaman tausayinta tattare dashi.




Safeena kam tana tafiya tana tuntube cos duk hankalin ta na kan halin da su Ayan ke shiki, bata hau abun hawa ba cos gidan is not far from the hospital, tana shiga cikin hospital ta kusa pumping into Muhammad dake fitowa daga dakin wani patient, ko daga kai batayi ba ta wuce shi cos ko kadan bata cikin mind dinta,
"Safeena... Lafiya dai..yau ba magana Kuma you came late...." Ya tambayeta cos yasan she a nice lady, ahankali ta daga kanta
"Lafiya lau..." Yafada cikin sanyin murya Sannan ta wuce shi, shima juyawa yayi ya tafi office dinshi ita Kuma ta tafi inda  wurin signing, kasa rubuta sunan ta tayi ta dawo office din Muhammad da sauri, shima da sauri ya daga kai  don yanda ta shigo ya nuna da akwai matsala,
"Lafiya safeena?.. Nasan da akwai matsala... Pls share it with me..."Kaman tana jira sai ta fashe da kuka tafara fadawa Muhammad abinda ya faru tsakanin ta da Ayan yau, da sauri Muhammad ya mike yana cewa
" ya yarinyan take?...." Description din ihsan ta bashi,
"Inna lillahi waina ilaihi rajuun...." Muhammad ya dinga maimaitawa yana fita daga office din. Da gudu2 ya shiga office din Yusuf, nan ya fadawa Yusuf abinda safeena ta fada mashi,
"To ya zamuyi?...is his life..he should live it the way he like..." Yusuf dake fushi da Ayan ya fadawa Muhammad atakaice, da sauri Muhammad yace
"Don't say that... He's our friend...something is wrong somewhere... And remember poor ihsan...kasan yanda Ayan yake when he's mad...pls muje kafin something bad happens... Pls ... Lets not allow him do something that will ruin our good name don kasan cewa ake abokin barawo barawone..." Yafada mashi, Ahankali ya dauki car keys din shi ya mike, da sauri suka shiga mota dukda sun San ko a kafa suna Iya zuwa amma da gudu suka toho, daman tsakanin gidan zuwa hospital baifi gidaje 35 zuwa 40 ba ko minti 7 basuyi ba suka isa gidan, da sauri suka fito suka taba gate din amma a rufe, motan suka kawo daf da gidan Muhammad ya hau kan motan Sannan ya hau bangon Allah ya bashi saa ya dire cikin gidan, da sauri ya budewa Yusuf kofa, nan waje suka bar motan su shiga falon cos kofan bude take, tun falo suka fara jin ihun ihsan cikin wahala da galabaita, Yusuf ji yayi legs dinshi basu daukan shi, nan ya sulale ya zauna ya fara kuka
💚💛💛💙💜


Yau Ayan zakaci ubanka hannu masoyan ihsan nidai babu ruwana 🏃🏾‍♀🏃🏾‍♀🏃🏾‍♀🏃🏾‍♀
[12/2, 7:58 PM] ‪+234 706 582 0685‬: ❤💛💜🖤💙💚
KAWARTA CE SANADI
💜💙💚🖤💛❤



®zuwairat(ummu Maryam)





3⃣3⃣



 _My dear *Khaleesat hydar* wannan shafin naki ne, I want you to know in jinki har cikin raina, I love from the bottom of my heart._




Muhammad tsayawa yayi yana fargaban bude kofan cis baisan abinda zai tarda ba,
"Wayyo Allah na....kayi hakuri... Pls..." Yaji ihsan na cewa Kuma yanda take magana ya tabbatar masu in baa kawo dauki ba tana iya mutuwa cos maganan ta kaman ba nata ba, Yusuf dake zaune ne ya mike afusace ya bude kofan, falo suka shiga inda ihun ihsan na kara karfi da gudu ya bude kofan da yake jin muryan ihsan daga cikin,
"Subhanallahi!!!...." Ya fada da karfi ganin ihsan dungule waje daya kan gado shi Kuma Ayan yana kokarin cire mata kayanta Kuma yayi nasaran cire mata hannun ta daya daga cikin rigan, Allah ya taimaketa kayan datasa suna da manyan stones a wuya da jikin shi da tuni ya yage kayan, afusace Ayan ya juyo jin muryan Yusuf, ahankali shima ya shigo ya kalli ihsan dake dukunkune kaman mai jin sanyi sai kyarma take,
"Ubanwa ya ce Ku shigo min gida!..." Ya fada cikin irin muryan da basu sanshi dashi ba, mikewa yayi daga kan gadon ya sauka kasa ya nufo su afusace, Yusuf da Muhammad kallon juna sukayi don tamkar ba Ayan ba, idanuwanshi sun chanza kala. Yana zuwa wurin Yusuf ya daga hannu aikam bai ankaraba yaji Muhammad ya sakar mashi wani irin wawayan naushi a hanci, nan take yayi baya2 yana daf nose dinshi kafa Yusuf yasa mashi ya fadi nan suka tarar mashi da naushi, kokarin mikewa yake amma ance karfin yawa yafi sarki power. Ihsan kam da sauran karfin da ya rage mata ta maida hannun riganta daya cire, kokarin tashi tayi sai taji bata iyawa saboda duk joint dinta ciwo yake mata mussanman boobs dinta da takeji kaman zasu tsinke saboda yanda Ayan ya dinga yi masu full of wickedness, duk abinda su Muhammad kewa Ayan bai dame shi sai dayaga ihsan tana kokarin tashi ya mike, kamashi su Yusuf sukayi amma kokarin kwacewa yake don ya tafi wurin ihsan, bakinshi sai jini yake amma ya rufe ido dole shi zashi wurin ihsan
"Shame on you!..." Yusuf ya fada cikin kuka,
"Wallahi wallahi wallahi kuka bari wannan yarinyan ta bar gidan nan....I will reap all of you apart..." Yafada cikin gurnani kaman wani lion, ihsan najin abinda yace tayi kokari ta mike, kallon ta sukayi Yusuf yakara fashewa da kuka cos shi mutum ne mai tausayi dukda he's stubborn, duk ta koma kama ba itaba dukkan face dinta yayi ja, sai haki take,
"Go back to the bed!..." Ya daka mata tsawa, ihsan ko kallon inda yake batayiba ta sauka kasa
"We're so sorry..." Muhammad Yafada,
"Sorry my ass...." Ayan da suka rike ya fada  da karfi,
"Where is the love you always claim you have for her?....we are disappointed in you..." Yusuf ya fada mashi,
"I don't care....she's a whore....Kuma wallahi ban aurenki...and sai na samu abinda nakeso ki ba yauba....." Yafada yana kokarin kwacewa daga rikon da sukayi mashi,
"Ubanwa yace dole sai ka aureta?...if you can't marry her you let her be...." Muhammad ya fada mashi,
 "No!...she played with my heart... She toy with me...zan nunamata  ba kowanne namiji akaewa wasa da zuciya ba...Ku sakeni...." Ya fada cikin ihu Kuma yana hawaye,
"Pls stop this..." Muhammad ya fada yana kara rikeshi sosai don kokarin kwacewa yake, ihsan dai ahankali ta fara takawa tana tafiya kaman mai jin sanyi, tana dafa bayanta dake mata ciwo, Ayan gani yayi da gaske fita zatayi yayi kukan kura ya kwace daga rikonsu, kafin su kama shi ya kama ihsan, wani kara ta karayi, rungume tayi yayi ta baya ya matse mata ciki sosai, Yusuf da Muhammad rikeshi sukayi suna kokarin kwace hannun shi daga jikinta amma ina
"Kai kasheta zakayi?..." Muhammad ya tambayeshi cikin tashin hankali, ihsan kam daura hannun ta tayi kan nashi, numfashi ta na Neman daukewa, Sakin jikin ta tayi, da kyar suka cire hannun shi daga nashi, yake jiki tayi ta fadi kasa tana
"Pls...Ku bari ..kawai ya karasani.....Ku tafi ya ida nufin shi kaina...." Tafada tana haki,  cikin kuka ya fara cewa
"Wallahi sai nayi ruining dinki....you destroy my life and I must destroy you... Ke kin yi kadan ki kashe min zuciya in kyale ki,..." Yafada yana kuka, har lokacin bakinshi da Muhammad ya nausa bai bar jini ba, ihsan kwantawa tayi nan kasa bata tashi ba cos at that moment she has given up on life, kawai she prefer to die,
"Pls...come and kill me...." Tafada cikin kuka,
"Don't worry... Bazan kasheki ba... Amma I will make sure you never cheat on any man again..." Yafada yana kuka shima,
"Pls Ku bar wannan maganan hakan nan...kiyi hakuri.. Duk abinda ya faru sharrin shaidan ne..." Inji Muhammad,
"No... Ba sharri shaidan bane...she caused it...wallahi ina nan ina sonta don Allah... Ita stupid.. Filthy.... Slut tana chan ta fucking wani..." Ihsan kara fashewa tayi da kuka tana imagining why is Ayan telling her  such horrible words
"And so what?...dole akayi ma?...if you can't you quit..." Yusuf ya fada cikin fada, shima Ayan cikin ihu yace
"I won't until am done with her..."
"To bisimillah..." Yusuf Yafada mashi, ahankali ihsan ta kara mikewa tayi juyo ta kalli Ayan da suka rike gam tace
"Why are ...you spoiling ...my name...why?..." Tafada cikin kuka sosai, baki Ayan tabe tare dacewa
"Ki tambayi saurayin ki ya fada maki abinda ya turo mani...ask him cos he's the one that betrays you not me..." Yafada cikin kuka
"Allah yaisa tsakanina dake...you have hurt me beyond words... Wallahi I will not marry you..." Inji Ayan cikin kuka, ihsan dan girgiza kai tayi
"Daman ko Kaine autan maza.....gara inbi duniya da in aueeka...." Itama ta fada ciki kuka
"Daman ke yar duniyar ce...Kuma ki bar ganin wayan nan wawayen sun rike ni...ko ba yauba sai nayi maki abinda bazaki kara shaawan namiji ba...." Yafada
"Haba Ayan... In rai ya baci ai hankali bai gucewa...ina iliminka....ina addinin ka?...ina trabiyan ka?...Wallahi ba haka kake ba...." Inji Muhammad, bai idaba Ayan ya ce
"She made me the way you see me...her love is destroying me...wallahi wannan yarinyan ta cuceni...she deceived me...." Yafada cikin kuka sosai, har lokacin bai bar kokarin kwacewa daga rikon da akayi mashi ba, ahankali ihsan ta mike ta fita daga dakin, Yusuf nason zuwa ya dauke ta amma yasan muddin suka saki Ayan babu abinda zai hanashi kamata, "wallahi Ku sakeni kar ta tafi...." Yafada yana kallon ihsan data kusa fita daga dakin
Kara rikeshi sukayi har singlet dake jikin shi yayi tearing amma bai bar kokarin kwacewa ba, saliva din bakin dake hade da jini ya zubda ya kalli Yusuf yace
"Wallahi muddin wancan yarinyan ta tafi ban ciwa burina ba...sai na ragargaza rayuwa tasnem..." Ya fadawa Yusuf Sannan ya kalli Muhammad dake shake dashi yace
"In har baku sakeni ba...if she leaves this house unscrewed by me...wallahi babu abinda zai hana dalla dalla da rukayya..." Yafada yana kuka,
"Don Allah calm down... You are better than this..." Muhammad ya fada mashi cikin kwantar da murya,
"No...baku San abinda tayi ba....that bitch allows her bastard boyfriend send me her nude pic with her video in shower...can you believe that?..." Yafada cikin kuka kaman ranshi zai fita, Yusuf da Muhammad kallon juna sukayi, ahankali Yusuf yace
"An auri karuwa dake zaune a hotel balle wacce ka zaune a gidan iyayenta?... Kawai that does not justify your action... You are nothing better than her now..." Inji Yusuf, kafa Ayan yasa ya harbeshi,
"Wallahi kilan sharri akayi mata....you should have investigate...." Muhammad ya fada, kai ya daga ya watsa mashi harara yana cewa
"You guys are dump ass...wane investigation zanyi ga zahiri?..what haven't I done?...kunsha ganina ina kuka saboda ita...I loved her so much but she betrayed me..." Kuka ne yaci karfin shi yayi shuru Sannan yacigaba dacewa
"Her love and charm have ruin my perfect life... Na tsani kaina...I hate life...ta gama dani...Wallahi bazan yafe mata..." Yafada cikin ihu yana hawaye.


Ihsan zama tayi kan daya daga cikin kujeran tana kuka tana hawaye, gani taje bazata kara tsanan mutum kaman yanda ta tsani Ayan ba, tana zaune tana sauraron abinda yake fadawa su Muhammad, ko kadan bata yarda da gaske yake ba kawai ta dauka yana yi mata sharri ne kawai, ahankali ta gama saka toms dinta ta tashi da kyar ta dauki gyalenta tare da bag, ko yafa shi batayi na ta fara tafiya har lokacin tana jin Ayan nacewa
"Ta cuceni!!!!..." Fita tayi daga wanna falon ta shiga babban falo tana tafiya ahankali tana hawaye, tunani take daman haka namiji suke, ita ba Ayan kawai ta tsana ba, she hates all men, sai shessheka take.

Ayan kwantawa yayi kasa yacigaba da kuka kaman zai mutu zuciyanshi sai bugawa yake da karfi, sakin shi sukayi yacigaba da kuka, Muhammad shafa bayanshi ya dingayi. Ganin bai mikebayasa Yusuf barin dakin da sauri, bakin gate ya hangi ihsan tana tafiya ahankali tana yafa Vail dinta, da sauri ya karaso gurin ta
"Kiyi hakuri.. Duk abinda zaiyi kyau sai ya fara samun matsala...pls kiyi yafe mashi kar ki fadawa kowa wannan maganan cos abun kunya ne..." Yafada mata, ihsan dai kuka kawai take bata daga kanta ba, da sauri ya wuceta ya bude mata mota, bata shiga ba ta cigaba da tafiya ahankali
"Pls ki shiga in kaiki hospital..in baki drugs you must be feeling sore..." Ya fada mata. Bata daga kanta ba ta girgiza mashi kai kawai,
"Pls...in kinawa Allah ki shiga..."  Yafa yana rokanta, amma bata kara cewa komai ba tacigaba da tafiya amma hawayen ta basu tsaya ba
 Da kyar Yusuf ya shawo kanta ta shiga mota ya tafi hospital daita, tambayan ta yayi ko taci abinci amma bata amsaba sai hawaye take da gani Kuma hankalin ta bai jikinta.parking yayi ya barta nan cikin mota ya shiga office dinshi ya hada cool tea tare da drugs ya kawo mata, Maganin ta amsa tasha da tea Sannan ta maida mashi sauran tea din. Maidawa yayi office dinshi Sannan ya fito yaci karo da safeena, da sauri yace
"Safeena.. Mun gode...Allah saka da alkhairi, .." Sannan ya fita ya shiga mota, hanyan gidansu amma ta fada mashi ba gida zata ba, tambayan ta sunan unguwan da zata yayi ta bashi sunan unguwan su husna, ahankali ta bude bag dinta ta dauko wayanta, ganin tayi 10 minutes after 5 Sannan ga miss call din mom guda uku, hanki ta dauko ta goge hawayen ta tayi dailing number mom, ringing biyu mom ta amsa
"Wai ina kika ajiye wayanki ne?.." Mom ta fada cikin fada, daidaita muryan ta tayi Sannan tace
"Cikin bag dina..."
"Ya akayi baki dawo gida ba har yanzu?.. Ko baki baro kasuwan ba?.." Mom ta tambayeta, shuru tayi for a while Sannan tace
"Yanzu ina kan hanya amma gidansu husna zani tukunna..."
"Baki gani dare na gabatowa?...ki yi sauri ki dawo gida..." Mom ta umarceta,
"Ok..." Ta fada har zata katse wayan mom tace
"Ya akayi muryan ki ya shake kaman kinyi kuka?.." Da sauri ta ce
"Mom mura ne ya kamani yanzu nan..."
"To kiyi sauri...zansa inna ta dafa maki pepper soup kafin ta tafi..."
"Ok mom..." Ta fada Sannan ta kashe wayanta, wasu new tears na rolling idanuwanta.


Ayan mikewa yayi ya cire singlet dinshi da su Muhammad suka yaga ya wurgar Sannan ya fita daga dakin, Muhammad sai binshi yake a baya bangaren daya cire kayanshi ya shiga ya dauko three quarters dinshi tare da rigan ya saka ya koma part dinshi ya dauko car keys daga kan dinning ya fito da sauri Muhammad ma binshi yayi yana cewa
"Kayi relaxing nan..duk Wanda ya ganka yanzu yasan da akwai problem.. You face is swollen.." Ya fada mashi, ko kallon shi baiyi ba ya shiga cikin mota ya figeta ya bar wurin, ko kulle doors din baiyi ba. Direct hospital ya nufa yana shiga cikin ya fara kiran safeena da karfi, da sauri ta taho gabanta na faduwa,
"You are fired..get out of my hospital before I do something stupid..." Ya daka mata tsawa, baki kawai ta tabe ta bar wajen.


❤💜💛🖤💚💙
KAWARTA CE SANADI
💜💚💙🖤💛❤


®zuwairat(ummu Maryam)



2⃣5⃣




 _Ina kike *Surbajo* is your turn, I want you to know you have a special place in my heart, ina yinki fiye ya da yanda kike tunani, I love you so much, Allah ya barmu tare da masoyan mu, ameen_ _love you_


Ayan kauda kanshi yayi amma husna bata bar kallon shi ba cos at the moment ji take kaman.she can take it anymore, she feels as if tayi screaming on top of her voice ta fadawa duniya she loves him, Ayan zama yayi kan wata kujera dake empty ya  kara daga kai ya ya kalleta, surprisingly har lokacin bata bar kallon shi ba, shima kura mata ido yayi yafara intimidating dinta da manyan idanuwanshi, kallon ihsan dake wasa da yatsunta yayi yaga bata daga kai ba amma fuskan dauke da murmushin jindadi saboda zuwan masoyinta, Ayan kara kallon husna yayi yaga still tana kallon shi with out blinking, su mami sai hira suke da Matan da ke dakin don haka basu lura da abinda ke faruwa ba, daure fuska yayi ya zaro mata idanuwa kaman yanda ake tsorata yara da idanuwa nan take ta dauke kanta hawaye na gangarowa, shidai bazai Iya interpreting irin kallon da take yi mashi ba dukda ya saba ganin irin wannan kallon wurin yanmata,
"Not possible..." Ya fadawa kanshi cikin ranshi, ahankali ya Dan sa kafanshi ya taba kafan ihsan dake wasa da yatsunta har lokacin, daga kanta tayi ta fara kallon su mami don tabbatar basu ganshiba Sannan ta kalleshi, wani irin kasaitaccen murmushi ya sakar mata itama ta mayar mashi da martani, yayi mata alaman su tafi waje, idanuwa kawai ta zaro tare da Dan girgiza mashi Kai tayi, ido daya ya kashe mata tare dacewa
"Plsss..." Yanda babu Wanda yaji sai ita da kuma husna dake kallon duk movement dinsu, kai ta kara girgiza mashi tana kallon empty hands dinshi, kallon ina abinda nace ka sayomin yake tayi mashi, shi kuma yayi mata kallon na mance, bata fuska tayi ta kauda kanta gefe daya, husna kam tunani take anya wayanda ta aika suje wurin Ayan sunje kuwa? Don  ko kadan babu alaman haushi ko zargin ihsan tattare dashi,
"I will see how much you loves her..." Tafada cikin ranta.

Suna nan zaune har 9pm, duk yanda yayi ea ihsan alama da ido kan ta tashi su tafi waje ki tayi wai tana fushi don bai kawo komai ba, kuma ya dau niyyan saidai su kwana nan tare muddin bata bishi waje ba.

 kawayen mami ne suka mike itama mami ta mike tana dora Vail dinta kan shoulder dinta, wurin gadon sukaje suka kara yiwa ihsan Allah bada lafiya Sannan suka fita mami na bayansu, Ayan na gani daga shi sai ihsan don sam mantawa yake da husna dake kwance,  da sauri ya mike ya kama mata hannu yana cewa
"Haba precious... Muje waje mana..." Da sauri ta fixge hannun ta tana cewa
"Ina chips danace ka sayomin?..."
"Yana cikin mota... Muje in baki..." Yafada yana kashe mata ido daya, hararan shi tayi tana kauda kanta gefe
"Precious pls ki taso...da akwai abinda zan nuna maki..." Yafada yana kara kama hannun ta Kara fixge hannun ta tayi tana cewa
"Ban zuwa..." Tafada tana harde hannuwanta kan kirjinta, husna dake kallon su cikin annoyance ta saki murmushi kaman gaske tana cewa
"Babe haba...bakonka annabinka...pls kije... I will be alright..." Tafada ihsan, juyawa sukayi da sukaji kafa mutum da alaman mami ce ta dawo, da sauri Ayan ya koma ya zauna, bude kofan tayi tashigo da sallama duka amsa mata, kallon ihsan tayi Sannan tace
"Habibty... Ki tashi ki shirya ya maidaki gida..." Tafadawa ihsan, wani irin sanyi Ayan yaji, Dan turo baki tayi
"Mami ni nan zan kwana...." Bata idaba mami ta girgiza mata kai
"Aa...maza ki tashi ya kaiki gida...gobe ma doc yace zaa sallameta..." Kaman zatayi kuka tafara bubbuga kafanta kasa tana cewa
"Wayyo ni nan zan kwana..." Ayan zama yayi yana kallon ta with adoration fuskan shi dauke da murmushin so da kauna,
"Daughter banason gardama... Iya tashi...gobe first thing in the morning zan sa driver yazo daukan ki inyaso in an sallameta sai Ku koma gida tare...oya ...Iya...stand dare na karayi..." Tafada mata not giving her chance to complain
 Tana turo baki kaman zatayi kuka ta mike ta saka vine flat shoe dinta dake kasan kafanta Sannan ta warwate karamin Vail data maida dankwali ta yafa shi Sannan ta duka tayiwa husna kiss a goshi tare dacewa
"See you in the morning insha Allah..." Itama husna tallabo face dinta tayi da two hands dinta tana cewa
"Allah ya kaimu..." Ayan kaman yana jira ya mike ya yana cewa
"Mami Allah ya kara sauki..."
"Ameen.. Mun gode kwarai..." Mami ta amsa mashi, fittt ya fita daga dakin, ihsan dauka handbag dinta tayi tabi bayanshi bayan tayiwa mami sai da safe,
 Waje ya tafi ya tsaya gefen motanshi yana jiran fitowanta, sai murmushin keta yake, few minutes later sai gata ta fito rike da handbag dinta fuskanta Sam babu walwala, bakin motan ta karaso yayi saurin bude mata kofa, shiga tayi still fuskan ta daure,tana shiga tafara jin kamshin kayan ciye2,
"Kambu..." Tafada a daidai lokacin daya shigo cikin motan, kallon ta yayi
"Precious... Ya akayi ne?..." Ya tambayeta kaman baisan fushi da take ba, hararan shi tayi Sannan tafara cewa
"Pls why are you doing this to me..."
"Menayi kuma?.."
"Na fada maka ka tahomin da chips amma ka ki...why..." Dan dariya yayi
"Because nasan bake zakiciba..."
"Does it matter who zai ci?... At least tunda na bukata sai ka sayomin..."
"Inda wani wuri kike da zan sayo maki.,...amma nasan kilan friend dinki zaki bawa... That's is why naki sayowa..." Yafada sounding frank, kallon mamaki tayi mashi
"Wai pls meke tsakanin ka da ita?..."
"I don't like her...kuma kaman yanda bazan gaji da fada maki I love you ba...bazan gaji da fada maki I hate her ba..." Afusace itama tace
"She don't like you either...." Sai da tafadi hakan sai ta kama bakinta cos sam bata so ta fada mashi ba, wata bazawaran dariya ya saki
"Hehehe....you see... That makes us even... I don't like her...she don't like me...which I totally disagree..." Da sauri ihsan tace
"Why do you disagree... She personally told me so..." Dariya ya karayi tare da tabe baki Sannan yace
"Precious.. Plsssss can we forget others and talk about us?..." Yafada cikin natsuwa, da sauri tace
"No!...you people should tell me what is happening between you two...I know something is wrong..." Da sauri shima yace
"Ba dai daga bangare na ba...may her..." Yafada yana tada motan,
"I don't like him....I don't like her...kar wannan abun yayi turning to something else...nasha kallon movies inda hatred ke komawa so..." Tafada kaman zatayi kuka, wata irin dariya Ayan yayi at the same time yana daure fuskan shi
"Hmmm don't be offended.. But you are thinking with your ass..." Da sauri ta luka mashi duka ya kece da dariya  yana cewa
"What ?...ai banyi karya ba...ko.mata sun kare bazan iya son wannan yarinyan ba...I hate her with passion... Allah kadai yasan dalilin dayasa banason ta....ewwww she is disgusting...." Tsaya kallon fuskan shi ihsan tayi tana kallon yanda he's saying every word with bitterness, bata ankara ba taji yayi parking gefen lonely street of the hospital, kalle2 quite street din tayi ta kalleshi dake fita daga mota, shuru tayi tana tunanin kilan he wants to ease himself, amma sai ya zagayo  ya bude inda take , bai jira reactions dintaba ya fiddota tare da rike mata waist, idanuwa ta bude tana kokarin magana amma bakinta bai buduwa, bayan motan ya bude ya sata ciki kallon kayan ciye2 dake tsakiyan seat din motan tayi kaman Humpty Dumpty, shima shigowa yayi ya kalli surprised face dinta ya saki murmushi Sannan yace
"Let's eat...." Kallon haushi tayi mashi
"Banci..." Ta fada atakaice,
"To mu kwana nan..." Idanuwa ta zaro ta fara nuna shi da yatsa tana cewa
"Daman am suspecting your attitude..." Bata ankara ba ya shafke mata yasa cikin bakinshi,da sauri ta zare tana kallon yastan
"Ohhh...baki yarda daniba kenan... To shikenan... Bari kawai in gwada maki halina...." Yafada yana shuumin murmushi, kokarin fita tayi daga cikin motan ya rike mata hannu yana dariya
"Am joking... Pls...muci abinci..." Kara girgiza mashi kai tayi
"Nakoshi..."
"To feed me then...."
"Gaskiya  I can't..."
"Pls precious... Start practicing..."
"No..."
"Pls..."
"No I can't..."
"Plsssssssss..." Sunfi minti goma suna wa juna magiya, gani tayi time is going,
 Yasa ya amince zata yi feeding dinshi, har da
"Yeeeeyyyy..." Yafada don dadi Sannan ya warware kayan, hararanshi tayi tafara feeding dinshi babu kunya ya wangale mata baki har abun yana bata dariya, cikin dubara ya bata tun bata amsa ta fara amsa, sunfi hour suna abi guda, suna gamawa Ayan yayi relaxing bai da niyyan tafiya,
"Pls mu tafi ...the night is not getting young..." Tafada mashi, lumshe idanuwa yayi yana cewa
"Ban driving immediately after eating..."

Sai bayan minti talatin suka kama hanya , driving ya dingayi ahankali suna hira har suka iso kofar gidansu ihsan, sallama sukayi ta  fito ta kwankwansa gate aka bude mata ta shiga.


Fitan ihsan da Ayan ke da wuya husna ta kara dafe heart dinta tana hawaye, mami tasowa tayi ta tsaya kanta tana tambayan ta gaskiyan abinda ke damunta, amma sam taki fadi, kawai cewa tayi
She's missing ihsan. Sai da alluran bacci tayi bacci, the following day tun da wuri Ayan ya kai ihsan hospital, ganin ihsan da Ayan tare yasa zuciyanta kusan bugawa, Wanda hakan yasa ko da doc yazo yace bazaa sallameta ranar ba cos nothing have changed, haka suka yini nan da dare Ayan ya kara zuwa daukan ihsan. Atakaice saida tayi kwana uku hospital Wanda yayi daidai da 4weeks to Ayan and ihsans wedding,  shima ba don jikinta yayi sauki ba amma sai don tasan zaman ta hospital is meaningless kuma time is passing her by, ranar da suka iso gidan su ihsan  ta riga ta gama plan din komai kuma tasan babu abinda zai hana Ayan rabuwa da ihsan muddin plans dinta yayi scaling through.

Wajen karfe goman dare bayan ihsan ta dawo daga wurin Ayan ta shigo dakin kallon husna na ke kudundune cikin blanket kaman mai bacci tayi tabi ahankali don kar ta tada ta ta cire kayan jikinta as usual ya rage daga ita sai pant,  wata sleeping gown mai kama da after dress ta dauko ta saka shima don husna na gidan amma on a normal ground tafison kwana ba kaya, tana dora wannan ta kwanta tare da rufe kafanta zuwa waist dinta da blanket, daga waist dinta zuwa samanta bude.

Bayan hour biyu idanuwan husna bude, sai da ta tabbatar shine ihsan tayi bacci Sannan ta mike zaune tare da kallon ihsan da Dan kayan bacci ta ya bar chest dinta bare, ahankali ta dauko wayanta, ta seta kan fuskanta tare da boobs dinta dake naked ta dauketa pic, cikin bacci ihsan taji kaman ana flashing fuskanta, da mikewa zaune tayi taga husna kwance kaman tana bacci, gyara kayan baccin ta tayi Sannan ta koma ta kwanta.

[12/2, 8:19 PM] ‪+234 703 821 5964‬: 💙💜💚🖤💛❤
KAWARTA CE SANADI
💙💜💚🖤💛❤



®zuwairat(ummu Maryam)



2⃣6⃣




 _This one is for you my habibty, har kin gane da ke nake cos I see you smile for seeing habibty, inason ki my one and only *sawwama* , Allah ya karemin ke, I am saying this from the bottom of my heart not my stomach_ .


Tana kwanciya bacci yayi gaba daita, husna dake rike da wayanta gam tana murmushi keta.

The following day kowaccensu ta mike kaman nothing happened, ihsan is free cos she have nothing to hide while husna is happy don gani take ta kusa cimma burinta. Downstairs suka saukasuka taya mai aiki hada breakfast as usual. Their life go on smoothly har suka gama breakfast ihsan tafara hawa sama don yin wanka, tana hawa husna ta bi bayanta, dama tasan ihsan bata rufe kofar bathroom in tana wanka, sadaf2 ta shiga bedroom din ihsan, one more habit na ihsan is that ta saba waka in tana shower, in kana dakinta da zaran ta fara wanka zakaji waka kala2 bakinta kaman tana party, tana waka tana rawa,  yau ma is the same thing, tana ciki wanka sai wakan awww na dija take,
" _Boy you the one I want... Cos you got what I need...Tell me boy do you see...happiness in me...I love my life anytime am with you Ahhh as long as you love me...there is nothing I won't do to make you smile... There is nothing I won't do to make you happy...._" ta dingayi on top of her voice, shuumin murmushi husna tayi tana cewa
"The right song.." Tafada cikin ranta Sannan ta nufi bathroom din da wayanta a hannun ta, ahankali ta leka Dan hole din dake wurin key taganta tsaye cikin shower kanta duk kunfa da alaman kanta take fara wankewa kafin ta wanke jikinta, ahankali ta bude kofan kasancewan bai da kara kuma ko yana da kara wakan da take bai barinta jin an bude kofan. Yanda ta bude kofan ya bata daman ganinta da kyau ahankali ta daga wayanta ta saka video tayi saurin fara videoing dinta,ita kuma sai waka take tana rawa at the same time hannuwanta biyu cikin gashinta dake cike da kunfa, tafi minti biyu tana daukanta amma ihsan bata gama wanke kanta ba balle ta bude idanuwanta, sai dataga ta fara murza face dinta tayi sauki dauke wayan tare da jawo kofan, da sauri tayi saving video tana ajiyan zuciya, bata zauna dakinba, ta bude kofa ta saukan downstairs, kan stairs ta hadu da mom ta nufo dakin da cup a hannun ta da gani magani ne ciki, gaida mom tayi  ta masa mata cikin faraa da jin dadi ta hau saman itakuma ta saukan zaman
"Aiyi dai mugani..." Tafada cikin ranta tana kallon bayan mom. Tun a bakin kofan mom ke jin wakan ihsan daga bathroom, tsoki tayi tana cewa
"Ban San abinda yasa wannan shegiyar yarinyan batajin magana ba...." Tafadawa kanta Sannan ta fara cewa
"Yanzu halima cikin kewayen kike wannan iskanci kaman a gidan biki?....Wato zuwa islislamiyya bai yi maki amfani bako?.....to Wallahi kika bari na bude wannan kofan nashigo na lahira sai yafiki jindadi..." Mom ta fada mata cikin fada
 Sosai, nan take ta rufe bakinta amma dayake is her habit bata bar humming ba, mom ta cigaba dacewa
"Haka zakije gidan miji ki jamana zagi...mijinki ya dinga ganin. Kaman wajen mu kika koya...to wallahi ki shiga hankalin ki...kuma kiyi maza ki fito ga magani nan ki shanye... Sauran ki zybda kice kinsha..." Mom ta fada mata sannan ta ajiye abinda ta zo dashi ta fita daga dakin, hmm one awful thing about ihsan is that she is extra stubborn, tanajin mom ta fita tacigaba da wakanta don already ya zame mata habit, sai bayan minti ashirin ta fito daure da towel a kirjinta sai daya kuma a kanta,  zama tayi kan mirror tana kallon cup da mom ta ajiye mata, daukan cup din tayi tana cewa
"Ni har na gaji da shan Sannan drugs din...tun lokacin Mahmoud.. Har yau ban huta ba....." Tafada tana bude cup din, Dan dangwala harshen ta tayi ciki taji da bauri, Dan bata fuska tayi  Sannan tace
"Anything for you.. My prince charming..."  Tafada tana kafa kai, bata dauke ba sai da ta shanye shi tas ta ajiye cup din ta shiga bathroom da gudu ta dauraye bakinta, tana fitowa wayanta na ringing, murmushi tayi tana cewa
"Talk of the devil..." Tafada don tasan Ayan ne, picking tayi ta zauna kan mirror tana kallon kanta suna wayan so da kauna, kurawa beautiful skin dinta ido tayi tana murmushi don ita kanta tasan Allah yayi mata abubuwan da ba kowacce mace Allah yayi wa ba, sunfi minti talatin suna waya Sannan sukayi sallama ta shafa mai, batayi kwalliya ba amma ko government house tana iya zuwa a hakan, skirt da riga ta dauko ta saka ta tsaya gaban mirror tana kallon kanta from head to toe,
"Alhamdulillah..." Tafada  Sannan ta fita.

A ranar basu je school ba kasancewan Sunday, duna gida through out suna labari amma ko da wasa husna bata ajiye wayanta ba kuma Allah baisa ihsan ta kai hankalin ta wajen ba, ita kawai jiran kiran Ayan especially da bayan sallan ishai tayi, kuma sai gashi ya zo as usual sunsha love.

Alokacin da suna compound suna hiran yanda rayuwan su zai kasance ita kuma husna tana zaune bakin gadon tana tunanin yanda zata dauki next plan dinta which tasan babu abinda zaisa Ayan yacigaba maganar auren muddin ta gama Plan dinta.

Kawai tunanin next action dinta kawai take, kaman wacce ta tuna wani abu sai tace
"Yesssss..." Tafada tana mikewa , ahankali ta Kara komawa zaune tana cewa
"zaiyi yawa...kar wani yaga nakedness dinta...so dole ni zan aikata da kaina...Allah I need is a new simcard....and komai zai tafi as planned..." Tafada tana relaxing kan gado. Da sauri ta dauko wayanta ta fara kallon nude pic din ihsan Sannan video, murmushin jindadi tayi yana cewa
"Bari inga in son gaske kake yi mata...precious..." Tafada tana dariya, kara kallon pic din tayi Sannan tayi rubuta
" _My baby cooling off after hot round of sex...na fada maka ka bar ta amma ka ki...anyway tayi assuring dina yau aurenka bazai hamu komai ba ..so go on and marry my sweet potatoes... She is really sweeeet in bed...can't stop swimming in her..._ " tayi rubuta kasan pic din tayi saving tana murmushin keta, amma the little good side of her is thinking abinda takeyi is not good amma the bad side have dominate the good side,
"Mtwww..." Tafada tana kara bude video, shima editing dinshi tayi ta rubuta
" _Just want to show you how romantic this afternoon was for us....yau ba karamin dadi ta shayar daniba....pls kalli how beautiful she is...daman Don in fada maka ba haka nan nake fada kanta ba...she's so adorable..."_ ta Kara rubutawa kasan video tayi saving tare da kashe wayan gabaki daya since shes not expecting any call.

Sai wajen karfe goma ihsan ta shigo Cikin daki, husna ta hanga zaune tayi tagumi hawaye na Zubowa daga idanuwanta
Da sauri ihsan ta karaso dakin ta zauna gefen ta tare da dafa shoulder dinta tana cewa
"Babe lafiya?..." Idanuwa husna ta daga ta kalleta Sannan tace
"Ba komai..." Tafada wasu new tears na rolling, cikin tashin hankali ihsan tace
"Ya za kice ba komai...you are crying.. Ko jikin...ne?..." Ta tambayeta muryan ta na cracking kaman zatayi kuka don tausayin aminiyarta,
"Wanda nakeso na tuna..." Tafada cikin kuka sosai, da sauri ihsan ta rungume ta tana cewa
"Sorry dear...yanzu meye abinyi?..." Ta tambayeta sounding very caring,
"Nayi missing dinshi ...I want to see him...k na minti biyu ne..." Tafada cikin kuka kaman gaske,
"Wane unguwa yake..."   Cikin kuka husna ta fada mata sunan unguwan,
"Yanzu ya zamuyi?...ko muje gobe Monday... Tunda lectures din mu bai dadewa?..." Shuru husna tayi for a while sai kuma ta tuna hakan bazaiyi favouring plan dinta ba sai cewa tayi
"Ai lokacin yana wurin aiki...in da ba Ayan zai kaimu school ba gobe da sai ince ki rakani in gashi ko daga nesa ne sai mu tafi school..." Shuru ihsan tayi tana tunanin ayya Ayan zai barta ta tafi school ita kadai, sai kuma ta tuna ita ba matar shi bace tukunna
"Ko ki tafi school ni zanje in gano shi sai in wuto school...tunda banason yasan abinda ke faruwa..." Taji husna na cewa cikin kuka, da sauri ihsan tace
"No need...gobe zan fada mashi da akwai inda zani...basai yazoba..." Wani irin sanyi husna taji cikin ranta don that is exactly the way she wants it to be,
"To shikenan..." Tafada tana goge hawayen ta, ihsan baya ta bata tana cewa
"Jawomin zip din Riga ta kasa..." Tafada Sannan tace
"I can't wait inga Wanda ya sacewa aminiyata zuciya..." Tafada cikin zolaya, dariya husna tayi
"Wallahi he's cuter than you expect.. Kawai Allah ya kaimu gobe muyi window shopping..." Tafada hankalin ta kwance, at that moment ji take kaman ta jawo goben. Haka suka sha hiransu Sannan bacci yayi gaba da ihsan itakuma husna bakin halinta da bad thinking sun hanata good night rest.


Wace gari tun 8 ihsan ta fara kiran Ayan don lectures din su na 9 ne, kiranta ya tasheshi daga bacci, daukan wayan yayi yana magana ta mai jin bacci, muryan shi sa ihsan dariya yayi
"Lafiya kika tadani daga bacci?.." Ya tambayeta cikin sleepy voice, dariya ihsan ta karayi Sannan tace
"Bakomai.. Daman inason in fada maka tau kar ka kaini school... Zan je wani wuri kafin in tafi school..." Idanuwa Ayan ya bude yana cewa
"Ina zaki Wanda ni bazan kaiki ba kafin in wuce daki school?..."
"Wurin wata friend ditace...kawai na hutar dakai yau..."
"Gaskiya ni ban yardaba....ni sai na kaiki...." Ya fada kaman Wanda zaiyi kuka,
"Ka kwantar da hankalin ka...mu shirya kazo daukata..." Ta fada mashi,bai Kara yi mata gardama ba  suka sha hiransu sharp2 Sannan sukayi sallama.
 Yana ajiye wayan ya koma ya kwanta tare da rufe kanshi da blanket.
Itama ajiye wayan tayi ta ida karasa shafe2 ta Sannan ta sauka downstairs, daman husna ta shirya tana dinning table tana shan tea da bread, itama ihsan zama tayi ta sha, data daga kai suka hada ido da husna sai taga ta saki murmushi, har ta gaji ta tambayeta wannan murmushin na meye? Sai cewa tayi kawai farin cikin zata ga fuskan masoyinta ne.
 Haka suka gama breakfast fuskan husna dauke da murmushi. Da sauri suka fita bayan sun amshi kudin abun hawa gurin mom.

Bakin titi sukaje suka tsaida abun hawa, ihsan sai missing Ayan take don rabon da  ta hau public fair har ta mance.

Adaidaita suka tsaida suka hau zuwa unguwan da husna ta fada masu, dama unguwan wata kawar mami ce so ta san wurin da kyau Sannan da akwai wani da take targeting ta nunawa ihsan  amatsayin Wanda take so.
Suna zuwa unguwan tasa mai adaidaita ya tsaya, kallon ta ihsan tayi
"Babe nan ne inda yake?..."
"Eh..." Tafada cikin sanyin murya Sannan ta nuna wani gida
"Wancan gidan yake...Allah yasa bai tafi aiki ba..." Tafada kaman da gaske.

Sunfi minti ashirin nan Sannan aka bude gate, wani saurayine, ya fito kan machine roba2, baki ihsan ta bude don saurayin ya hadu babu karya amma he's nothing compared to her Ayan.
"Wow babe ya hadu babu karya..." Inji ihsan, husna kam sai lumshe idanuwa take tana kallon saurayin da baisan wainar da suke toyawaba, ta inda suke ya wuce da machine dinshi ko kallon side din bai yiba, suma barin wurin suka husna sai lumshe idanuwa take wai dadi take ji taga habibi dinta.

Aranar haka suka je school, daga nan husna ta koma waje ta sayi simcard ta cire layinta ta saka Wanda ta sayo Sannan ta turawa Ayan pic da video din ihsan via WhatsApp bayan ta chanza WhatsApp number dinta daman already ta Dade da daukan number din shi daga cikin wayan ihsan.


Bayan Ayan ya gama komai around ten ya shiga office that is bayan yayiwa Umma sallama.

Har 2pm bai bude data ba balle yaga sakon da aka bar mashi, yana ta aiki har 3 bai bude data ba sai bayan sun fito daga surgery tare dasu Muhammad ya kalli time yaga three, hissing yayi yana cewa
"Yau ban samu daukan precious ba..." Yafada yana cire surgical cote dake jikinshi, ratayata yayi Sannan ya dauki wayan shi yayi dailing number ihsan, hakuri ya bata kan baizo daukanta ba ita kuma ta nuna mashi ba komai cos sun hau adaidaita lokacin zasu dawo gida. Ajiye wayan yayi cos daman he's not a social media person amma zaman dayayi bai da abinyi yasa ya kara daukan wayan ya bude data, nan messages suka dinga shigowa, hra dana husna. WhatsApp dinshi ya bude ya fara duba messages, farat daya idanuwanshi suka kai kan Wanda bai da suna cos mostly yana da number dukkan sauran. Ahankali ya bude wannan message din, dukda bai buda pic da video din ba yasan is not something good don da gani kasan is something nude, rubutun dake kasan message din ne ya kara Jan hankalin shi, tun bai karanta ba hankalin shi yafara tashi gashi gabanshi na mugun faduwa, hannu yasa ya bude pic din few seconds later ta bude, idanuwa ya zaro ganin ihsan kwance with her boobs bare. Kirjinshi ya dafa kuma jikin shi na rawa hannun yasa ya kara bude video, nan yaga his ihsan dancing nake in the bathroom, da sauri ya saki wayan yana cewa
"Inna lillahi waina ilaihi rajuun!!!!..." Yafada da karfi Wanda yasa Yusuf dake daf da office din tahowa da gudu, Ayan kokarin mikewa yayi amma sai ya kasa, tari ya farayi da karfi hannun shi daya kan kirjinshi daya kuma kan makogaronshi, irin tarin dayake yasa Yusuf zuwa inda yake zaune, kokarin kara mikewa yayi wannan Karin ya yanke jiki ya fadi kasa sai shaking yake kaman mai convulsing.
 💛❤💚💜💙🖤

Tun baa kai koina ba kun fara complaining, kuma da husna ta fara shan wahala still nasan zakuyi complain, haka kukayi lokacin ZAKISAN KONI WAYE, har wasu suka fara cewa raayin wasu nabi, inason Ku Sani kafin in fara novel inda complete story cikin kaina, so pls just keep reading kawai inason nuna muku length din da makiyinka zai Iya zuwa just to destroy you. So pls stay put and enjoy the ride as more is yet to come
[12/2, 8:21 PM] ‪+234 703 821 5964‬: 💛💚❤🖤💜💙
KAWARTA CE SANADI
❤💜💙🖤💛❤



®zuwairat(ummu Maryam)



2⃣7⃣


 _My *Habeeba* , wannan page is yours,thanks for the love and affection, Zuwairat na kaunar ki tamkar yanda take kaunar blood sisters dita, I love you._





Cikin tashin hankali Yusuf ya fara girgiza Ayan yana kiran
"Inna lillahi waina ilaihi rajuun!... Ayan... Ayan..." Ina baiji sai shure2 yake da legs dinshi har lokacin hannun shi daya kan kirjinshi dayan kan throat dinshi, idanuwanshi kafewa sukayi kaman Wanda ake zarewa rai, da gudu Yusuf ya fita waje yana kiran doctors, nan take doctors sunfi uku suka fito daga cikin office dinsu cikin su har da Muhammad,
"Lafiya?..." Ya tambayi Yusuf,
"Dan Allah Ku biyoni...something bad is happening to Dr Ayan..." Yafada yana komawa cikin office din da gudu, suma bayanshi sukabi suna shiga suka ga Ayan kwance ko motsi ya baryi,
"Inna lillahi..." Dukkan su suka dinga maimaitawa suna daukan shi, tambayan Yusuf suka dingayi kan abinda ke damunshi amma shi kanshi ba San amsar da zai basu ba kawai cewa yayi
"I was passing by sai naji shi yana inna lillahi waina ilaihi rajuun... Ina shigowa na ganshi yana tari and the next thing he was convulsing..." Yafada cikin tashin hankali, wani doctor ya fita da gudu ta dauko abinda ake dauka Mara lafiya dashi aka dirashi sama, hannu Muhammad ya dora kan kirjinshi yaji heart beat dinshi is beyond normal,
"What could be the cause of this?..." Muhammad ya fada
"I don't know..." Yusuf ya amsa mashi kaman zaiyi kuka. Emergency room suka shiga dashi suka fara kokarin ceto ranshi don at that moment gani suke kaman zai rasa ranshi. Da kyar suka samu ya saki ajiyan zuciya amma bai bude idanuwa ba, kawai sai suka ga hawaye da fita idanuwanshi suna shiga cikin kunnenshi saboda yanayin kwanciyan shi. Zuciyanshi sai up and down yake saboda yanda yake numfashi da kyar,
"I think we should give him oxygen..." Inji Yusuf, babu musu suka jona mashi oxygen, da sauri Muhammad ya fita yana cewa
"Bari in kira Abba in sanar dasu halin da ake ciki..."

Ayan kam baisan duniyar da yake ba, haka nan yana ji yana gani ya kasa controlling breath dinshi. Kawai adua yake Allah yasa ba ihsan dinshi ya yagani ba,
"I know am dreaming..." Yafada cikin zuciyanshi, ahankali ya daga hannun shi ya Dora kan heart dinshi dake yi mashi ciwo, da sauri Yusuf ya zo daf dashi ya rike mashi hannu, ahankali ya bude idanuwanshi, har lokacin hawaye basu bar rushing ba
"Guy What is the problem?..." Yusuf ya tambayeshi yana rike da hannun shi, Ayan daga idanuwanshi da sukayi mashi nauyi yayi ya kalli Yusuf, amma Sam bai da bakin magana, how can he tell his friend that his fiancee is a whore, he can't say it,
"Pls what's the problem..." Yusuf ya sake tambayan shi, kara kallon Yusuf yayi hawaye shar kaman tap, bakinshi sai kyarma yake kaman mai jin sanyi, hannu Yusuf yasa cikin aljihunshi ya dauki hanki ya goge hawayen amma wasu na zubowa, abun oxygen dake hancin shi ya ture gefe yana kokarin mikewa, kara rike shi Yusuf yayi
"Ina zaka?..." Ya tambayeshi,
"My....phone..., did you.... See...what's on...my ....phone?..." Ya tambayeshi kaman mai koyan magana, kai Yusuf ya girgiza mashi, Ayan lumshe idanuwa yayi hawaye na zubowa
"What is on your phone?..." Yusuf ya tambayeshi, ahankali ya koma ya kwanta batare daya mashi amsa ba.
Har Muhammad ya je ya sanar dasu  Abba ya dawo Ayan bai bar hawaye ba, shima Muhammad questions ya dingayi mashi amma bai magana sai kuka duk yanda sukayi su rarrashe shi abun ya shi tura, Yusuf fita yayi ya je office din Ayan, wayanshi dake kasa ya dauka ya bude Allah ya taimaka da akwai pattern da shima haka zaiga nakedness din ihsan, ganin bai Iya budewa yasa ya dauko wayan yashiga inda Ayan ke kwance, hannu ya mika mashi shi kuma ya mika mashi wayan, riketa yayi gam yacigaba da kuka, bayan kaman minti talatin lokacin su Yusuf sun gaji da tambayan shi kallon su yayi Sannan yace
"My heart....hurts...."  Muhammad dayayi tagumi yace
"Ka fadi abinda ke damunka ko munsan Maganin daya dace abaka...amma sai hawaye kake..." Yusuf kam bai ce komai ba ya zo daf dashi ya dora hannun shi kan kirjinshi, after few seconds ya kalli Muhammad Sannan yace
"I think muyi mashi alluran bacci cos the rate of the heartbeat is high...kuma kasan hakan is dangerous..." Muhammad baice komai ba ya nufi wata closet ya bude ya dauko injection ya hada ya dawo wajen Ayan, Ayan kallon shi yayi Sannan ya sauke idanuwanshi da suka koma kaman garwashi, hannun shi ya dauka ya dauke Sannan yayi mashi alluran. Bai dadeba bacci yayi gaba dashi.

Sai bayan sallan zuhr Abba da Umma tare da antymu da Ismail suka shigo hospital, har lokacin Yusuf da Muhammad na tsaye kanshi suna auna rate na heartbeat dinshi. Cikin tashin hankali Umma ta farq tambayan su Yusuf abinda ya sameshi exactly abinda suka saninsuka fada masu. Antymu sai kuka take don dukda Ayan na bacci eye lashes dinshi jike suke da hawaye
 Umma zama tayi bakin gadon tana kallon danta cikin tashin hankali tana wondering abinda ya sameshi, Abba kam kan wata kujera ya zauna sam babu alaman tsoro ko karaya tattare dashi amma shima deep down yana wondering abinda ke faruwa.



Husna kam bata cire wannan simcard ba sai da ta tabbatar an bude message din Sannan ta bude wayanta ta fidda simcard din ta kakkarya shi ta zuba cikin dustbin.

Around 4 bayan sun yi salla suci sunsha ihsan mikewa tayi haka nan sai ta tsinci jikinta babu kwari, saman bene ta hau tana tafiya ahankali, tana zuwa dakin ta kwanta tare da rufe kanta da blanket kaman mai jin bacci itama husna hawa tayi ta zauna bakin gadon tana kallon ihsan
"Babe ya dai?..." Ta tambayeta
"Nothing... Kawai dai banjin dadi ne...."
"Kilan is stress..."
"I don't think so...haka jikina yayi Mun lokacin da yaya Mahmoud zai rasu...yan zu ma am feeling down..." Da tabe baki husna tayi
"Ki huta ko zuwa anjuma kin ji daidai..." Ihsan bata kara cewa komai ba ta lumshe idanuwa.


Bayan sallan magrib Umma ta kira mom ta sanar daita Ayan na hospital bai da lafiya, Allah ya taimaka ba a gaban ihsan aka kirata ba, amma haka nan itama gabanta ya dinga faduwa, zaune take kan praying mat lokacin da sukayi wayan, hannuwanta ta daga sama ta fara cewa
"Ya Allah... Ya rabbi...ka bashi lafiya....in har wani ya samu wannan yaron shikenan halima tayi kaurin suna...ya Allah pls...have mercy..." Haka ta zauna ta dinga adua Sannan takira dad ta sanar dashi halin da ake ciki kasancewan bai gari nan dad ya fada mata ta tafi ta ganoshi amma kar ta fadawa ihsan. Haka akayi ta fito ta shiga dakin ihsan, zaune ta tardata kan mirror sai shafe2 take
"Zan fita yanzu zan dawo..." Mom dake tsaye bakin kofan Tafada mata, kallon ta ihsan da husna sukayi husna tayi saurin cewa
"Mom ina zaki?..."
"Nan neighborhood akayi haihuwa... Zanje barka yanzu zan dawo...." Ta fada masu Sannan ta jawo masu kofan ta tafi.

Har taje Ayan bai tashi daga bacci ba,  sai around 8 ta komo gida. Ihsan tana zaune falo taci kwalliya, husna kam sai jira take taji abinda zai biyo baya.

Har 8: 30 bai zo ba wayanta dake gefen ta ta dauka tayi dailing number shi.
 

Alokacin bai tashi daga bacci ba, wayanshi dake rike cikin hannun shi ya fara ringing, Umma dake zaune kusa dashi ta amshi wayan taga precious ke kira, ajiyewa tayi bata dauka ba.  Kara kira ihsan tayi wannan Karin Yusuf ne ya dauki wayan yayi picking, bai jira maganar ta bayace
"Bai farka ba har yanzu..." Yafada don a tunanin shi ta Sani tunda mamanta tazo, nan ihsan ta zaro idanuwa tace
"Tashi daga ina?..." Husna dake zaune kusa daita kasa kunne tayi don taji abinda zasuce
"Daga baccin... Alluran bacci akayi mashi..."
"Alluran bacci kaman ya?...." Da sauri ta daga wayan ta kalli screen din Sannan ta mai dashi kunnenta bayan ta tabbatar number Ayan ne ta kira,
"Wai waye ke magana?..." Tafada cikin tsiwa,
"Nine Yusuf... Har yanzu bai farka ba...zan fada mashi...." Da sauri ta katseshi dacewa
 "Kuma inane?.…."
"Hospital...." Aikam bai idaba ta katse wayan, da gudu ta tashi ta hausama husna na biye daita cikin ranta sai cewa take
"Anzo wurin..." Azahiri tace
"Babe lafiya?..." Ihsan da tuni ta fara zubda hawaye tafara cewa
"Wai Ayan ne bashi da lafiya....yana kwance hospital...." Tafada cikin kuka adaidai lokacin da tashiga dakin mom, mom dake zaune ta rafka uban tagumi ta kalleta da kuma yanda ta shigo bako sallama har zata fara yi mata fada taga fuskanta jike sharkaf da hawaye
"Lafiya ..." Mom ta tambayeta tana Allah yasa ba ganewa tayiba don tana tsoron rikicin ihsan. Kwantawa tayi kasa tana cewa "mom an kwantar da Ayan...."
"Wa ya fadamiki hakan..."
"Wallahi abokinshi ya fadamin... Zuwa zanyi..." Tafada cikin kuka sosai
"Ki bari gobe kinje.." Mom ta fada tana shafa kanta
 Da sauri ta fara girgiza kai tana cewa
"Ni wallahi mom sai naje...."
"Ke!..." Mom ta daka mata tsawa Sannan ta fara cewa
"Zaki farako...nace gobe kinje..." Fada cikin fada, sabon kuka ta fara tana cewa
"Mom dan Allah ki bari inje..." Bata idaba husna ta ce
"Mom zan rakata..." Kai mom ta girgiza
"Ku bari sai gobe...don ko kunje yana bacci..." Da sauri ihsan ta kalli mom
"Daman mom chan kikaje dazun?..." Tafada cikin kuka
"Nasan wannan haukan zakiyi that's why ban fada maki ba...tashi ki koma dakinki gobe sai kije da wuri..." Da kyar ihsan ta yarda ta bar dakin mom don babu irin magiyan da bata yi mata ba kan ta barta taje amma kememe mom taki, haka tana kuka kaman wacce akayi wa mutuwa ta bar dakin. Sai ihu take tana buga kanta da kasa tana cewa
"Nasan in da dad yana nan zai barni in je..." Aranar haka ta kwana kuka sai trying number Ayan take amma switch off, itama husna hankalin ta ba karamin tashi yayi ba don taji Wanda tafi so a duniya kwance hospital, ji take kaman ta jawo goben don har adua take Allah yasa ba wannan message din yayi sanadiyan kwantawanshi hospital ba don ko kadan batason abinda zai taba her Ayan.


Ayan bai farkaba sai wajen 12 na dare alokacin su Umma da Abba sun tafi bayan Yusuf da Muhammad sun shaida masu su tafi they will keep them posted, ahankali ya bude idanuwanshi da sukayi masa nauyi,  kallon Yusuf da Muhammad dake bacci, da sauri ya kalli agogon yaga after 12 da sauri ya sauka yayi alwallah ya dawo ya rama sallan duk da ake binshi har lokacin su Yusuf basu tashi ba, ahankali ya koma kan gado yana aduan Allah yasa duk abubuwan da suka faru su zama mafarki, ahankali ya dauki wayan shi ya kunna. Zama yayi yakara shiga WhatsApp dinshi wannan Karin nutsuwa yayi ya kalli video da kyau, yana kallo hawaye na digha kan screen din wayan,
"Why me..." Shine abinda ya dinga maimaitawa, kara playing yayi, still yana hawaye,
"Ihsan why....halima  kin cuceni...kin yaudareni....kinsa da aminta dake....kin CI amanata....bazan yafe makiba...I surely teach you a lesson of a life time..." Yafada yana hawaye, maganan shi ya tada Yusuf da Muhammad, da sauri ya kashe wayan ya ajiye yana goge hawayen shi yayi, wurin shi suka zo suka zuba mashi idanu suna mamakin abinda ke faruwa, shidai bai fada masu kala ba, hawaye kawai yacigaba dayi yana tunanin abinda zaiyiwa ihsan ya huce,
"Zan yaudareki the way kika yaudare ni...zanyi maki abinda guys dinki basu taba  yi maki ba...is not my way of life but am starting with you..." Yafada cikin ranshi, magiya Yusuf da Muhammad suka dinga yi mashi kan ya fada masu abinda ke damunshi amma bai fada masu komai ba daga karshe daya ga zasu rakurashi kawai cewa yayi
"Its just a nervous breakdown..."  Yafada fuskan shi daure ba don sun yarda ba suka kyaleshi.

The following day tun asuba ihsan da husna suka shirya, idanuwan ihsan sunyi mugun kumburi, abinka da farar mace duk kasan idonta sunyi ja. Da kyar mom ta shawo kanta ta sha tea Sannan suka fito tare da motan mom mai gadi ya tukasu, shigowansu hospital yayi daidai da fitowan Ayan dake shirin komawa gida don ya kwanta, da sauri ihsan ta fito   ta nufo shi, kaman ance ya juya sai sukayi ido hudu, idanuwanshi kumbure nata kumbure, husna zaune take cikin mota tana kallon abinda zai faru. Ayan ida juyawa yayi ya fuskan ce ta kawai sai yaga he's seeing her naked, tamkar babu kaya jikinta ya dinga kallon, kawai sai ya sakar mata wani irin shuumin murmushi Wanda yasa hancin husna dake kallon su tsinkewa.
[12/2, 8:22 PM] ‪+234 703 821 5964‬: ❤💛💚🖤💙💜
KAWARTA CE SANADI
💜❤💙🖤💚💛


®zuwairat( ummu Maryam)




2⃣8⃣



 _You are among my first friends, kina tare dani tun lokacin sune SANADI, ZAKISAN KONI WAYE, kuma nasan yanzu ma kina tare dani my dearest *Fiddausi sodangi* , ina jinki har cikin jinina, I meant what I said. Love you, Allah ya bar so da kauna ya rabamu da sharri makiya da mahasada._

Itama murmushin karfin hali ta sakar mashi tana karasawa inda yake, kura mata ido yayi yana kallon each step dinta
"I wish you were decent... Da muyi rayuwa mai dadi dake....amma now am after doing to you what you are use to..." Yafada cikin ranshi yana kallon eyeball dinta ba tare dayayi blinking ba, irin kallon da yake yi mata ne yasa tayi saurin dauke kanta, kurawa dan shoulder ta da ya Dan fito yayi kasancewan gyalen ta bai rufe mata dukan wuyan ta ba cos ba babba bane, wasu new tears ne suka fara taruwa idanuwanshi amma yayi saurin maidawa, kallon shi ta karayi tana mamakin dalilin dayasa idanuwanshi suka kumbura haka, shima tunanin da yake kenan,
"Precious... Meya samu idanuwanki?..." Ya tambayeta cikin husky voice, kawai sai ta fashe da kuka tana cewa
"Ba kai bane baka da lafiya ..amma you don't care to call me...sai yanzu nasan baka damu dani ba..." Tafada cikin kuka, husna sai kallon su kawai take gaban ta na mugun faduwa don ko kadan Ayan bai nuna yana jin haushin ihsan ba, heart dinta ta dafe tana son ganin any bad reactions da zai shaida mata her plan has worked, tana ganin ihsan ta fashe da kuka ta danyi ajiyan zuciya tana tunanin kika he's breaking up with her as she wanted cos ko kadan batajin abinda suke cewa,
"Munafuka..." Yafada cikin ranshi, azahiri yace
"Am so sorry... Kinsan banason tada maki hankali.... Is that why idanuwanki suka kumbura haka?..." Hararan shi tayi Sannan tace
"AI kaima naka are swollen... Why?..." Ta tambayeshi cikin sanyin murya, murmushin karfin hali yayi Sannan yace
"Jiya naga abinda ya chanza min rayuwa ne...." Da sauri ta daga idanuwanta ta kalleshi
"What could that be?..."
"Kar ki damu....dake  zai fara....now tell me..did you miss me?...cos jiya dake na kwana cikin raina...." Yafada kaman he means it, murmushi tayi tana wasa da yatsunta tace
"Wallahi I miss you like hell...." Tafada cikin sanyin murya, daure fuska yayi cos ba kallon shi take ba, amma tana daga kai ya sakar mata wani irin murmushi,
 Yanzu muje in ajiyeki gida ni kuma sai in dan kwanta , kallon shi tayi
"Ba fadamin abinda ya sameka ba...what happened?..."
"Is nothing bad...just a reality about life..."
"Pls ban gane ba...what actually happened?..."
"I just have a nervous breakdown..." Ya fada mata, bata ankaraba ya kama mata hannu,
"Muje,..." Da sauri ta yi kokarin fixgewa tana kalle2 amma abun mamaki ba da wasa ya rike hannun ta ba,
"Pls ka sakar min hannu... Kasan banaso kana rike min hannu..." Dan baki ya tabe,
"Kaman da gaske..." Yafada cikin ranshi
"Yanzu precious rike hannu wani abune a wajenki?..." Yafada har lokacin yana rike da hannun ta, wurin motanshi suka nufa hannun su cikin juna dukda sam ihsan bataso hakan ba, husna was gasping for air cos kawai her world was turning black, ji tayi zafi na keto mata ta koina, she can't believe what she's seeing
"Yanzu after everything... After all my effort... Har yanzu bai wulakanta taba?...oh my God... What do I have to do?..." Tafada cikin ranta azahiri ta doki kujeran motan da karfi har driver ya juyo ya kalleta tare dacewa
"Lafiya dai ko?..." Harara ta watsa mashi batare data amsa mashi ba
"Wallahi billahi I will not give up...Ayan you are meant for me and me alone..." Tafada cikin ranta, kawai sai ta fashe da kukan zuciya muryanta bai fitowa sai dai hawaye.

Tafiya suke amma kaman janta yake,
"Pls ka sakar min hannu... Zafi yanda ka rike ni..." Tafada don har Dan murda hannun ta yake kuma he us doing it on purpose, jiyake kaman ya karya hannun don yanda zuciyanshi ke bugawa saboda haushi da kishi amma sai ya daure, kawai tunanin ta taba romancing wani da wannan hannun yake
"Kaji...pls hannun ciwo...." Tafada mashi adaidai lokacin da suka karaso bakin motan,
"Oh sorry precious... Or should I call you sweet potatoes...." Yafada yana tunani abinda aka fada mashi, rike wrist dinta tayi don tana jin zafin hannun sosai, mota ya bude mata bai jira ta ba ya turata ciki still cikin zalunci daman gashi sarkin keta, yana kallon bata dauke  hannun ta daga bakin kofan ba da gangan ya maida kofa ya rufe, wani irin razanannen ihu ta saki da sauri ya bude kofan kaman bai san abinda ya faru ba
"We are just getting started... This is just genesis..." Yafada cikin ranshi, da sauri ya durkusa nan kasa ya kama hannun ta data rike tana hawaye cikin bakinshi ya saka yatsan ya fara sha kaman wani lollipop,  Yusuf da Muhammad ne suka fito, daidai parking lot sukaga Ayan durkushe yatsun ihsan cikin bakinshi ita kuma ihsan sai kuka take,
"Lafiya?..." Yusuf ya tambayeshi,
" datse mata hannu nayi mistakingly... " Yafada masu amma bai cire yatsunta daga bakinshi ba, sannu sukayi mata suka wuce Muhammad sai mamakin yanda Ayan ke licking yatsanta yake,
"Sorry precious...." Yafada yana lumshe idanuwa, kai kawai ta gyada mashi,
"Ya bar zafi?..." Kai ta kara gyada mashi badon ta bar jin zafin ba sai don yanda tsigan jikinta ke tashi saboda yanda yakewa fingers dinta, amma still bai bar shan yatsanta ba, idanuwa ya daga ya kalleta yaga ta lumshe idanuwa
"Ka bari ...I don't like this..." Tafada mashi, ahankali ya zare hannun ta ya ajiye mata kan cinyanta which in the process ya taba mata laps..." Zagayowa yayi itakuma ta tsinci gaban ta na faduwa saboda behavior dinshi na yau ya banbanta Dana sauran rana, bude motan yayi ya shiga ya zauna yana kallon ta.
"Kawai ka tafi tunda bani kadai bace...."
"Hmmm..keda waye?..."
"Husna..." Ta amsa mashi kanta kasa don kasa kallonshi tayi
"Mtwwwwwss...ta taho mana..." Yafada yana tada motaan
 "To bari in fada mata..." Ta fada tana kokarin fita daga motan wani irin fixga yayi mata yana cewa
"I said let her find her way..." Ya daga mata tsawa cikin irin muryan da bata sanshi daita ba, zama tayi tafara kallon shi wasu new tears na forming idonta, bai kalleta ba ya figi motan,
"Me nayi maka?..." Shine tambayan data yi mashi, murmushin karfin hali yayi
"Precious baki yimin komai ba...kawai banason kina ketara magana ta saboda wancan yarinyan da bata zama gidansu sai yawon gidan kawaye...." Yafada cikin nutsuwa amma inda zaa bude heart din shi wulik take saboda bakin ciki.


Husna zama tayi tana kallon su suka tafi, kuka tayi ta godewa Allah Sannan ta umarci driver da ya tafi. Tunanin next plan din ta tayi,
"Wallahi ko bazaka aureni ba...bazaka auri wancan shegiyar ba...I can't bear seeing you with her..." Tafada cikin ranta. 

Ba karamin tashin hankali ihsan ta shiga kafin su iso gida ba cos yanda yake tukin motan kaman zai tashi sama. Parking yayi bakin gate dinsu Sannan ya kalleta da red eyes dinshi tare sa sakin murmushi
"Precious.... Zan tafi sai da maraice...in ban zoba hope zakizo ganina..." Idanuwa ta zaro tana cewa
"Kambu ...saidai muyi waya..." Murmushin gefen baki yayi Sannan yace
" why bazaki zo ganina ba?...haba is not fair...kullum shikenan ni zan dinga zuwa?...nidai gaskiya tunda ba lafiya gareni ba kizo ganina... " Yafada babu zancen wasa,
"Yo haka nan sai in kama hanyan zuwa gidan saurayi?...gaskiya I can't..." Tafada atakaice, hararanta yayi Sannan yace
"Ni ai na wuce saurayin ki...wayanda basu kaini matsayi ba sun samu abinda suke so balle ni?..." Da sauri ta kalleshi
"I Don't understand your last statement..."
"Zaki gane ne...filthy slut..." Yafada cikin ranshi Sannan yace
"Ai yanmata na zuwa wajen samarin da ko gidansu basu Sani ba balle ni da bikin mu sauran few weeks?..."
"Ni bana cikin wayannan yanmatan... Ka bar hadani dasu..." Tafada cikin tsiwa
"Pretender always do the worst .." Yafada cikin ranshi,
"Ai shikenan., nasan zama na dake....amma ki Sani in har bazaki iya takawa nan da few blocks ki zo ganina ba then ni ma bazan zo ba...." Yafada fuskanshi daure,
"Yanzu don bazan zo gidan Ku ba...kai bazaka zo ba?..." Ta tambayeshi kaman zatayi kuka
"Eh..." Ya amsa mata atakaice, tsaya kallon face dinshi tayi tana tunanin ko kwana biyu bazata iyaba sai dashi
"Gaskiya inajin kunyan Umma ko Abba su ganni nazo wurin ka..." Dan tabe baki yayi
"Yo ya zaayi su sani...ai ba ganinki zasuyi ba..."
"Ban gane ba?.."
"Ai ba main house zaki shigaba...part dina zakizo..." Idanuwa ta zaro
"Lallai..." Yafada tana bude kofan motan, waist dinta ya tsaya kallo, kawai sai ya fara imagining ga wani yana shafa kugunta, kauda kanshi yayi wasu hawayen na Neman zubowa. Tana rufe mashi kofan ya fixgi motan sai gidansu, yana shiga yaga Umma tsaye bakin mota mai aiki na ajiye wasu beautiful food warmer cikin motan, Umma na ganin shi ta taho da murmushi fuskanta. Da sauri yayi parking ya fito, rungume shi Umma tayi,
"Yajikin?..." Ta tambayeshi bayan ta amsa gaisuwan shi,
"Da sauki Umma..."
"Ai yanzu wurinka zanzo...da Mun sha banban..." Tafada tana kallon shi, tsaya kallon yanda idanuwanshi suka chanza tayi
"Habibi...what happened to you?..." Karyan da yakewa mutane yayi mata,
 Girgiza kai Umma tayi
"Son I don't believe you... Haka nan mutum bai samun nervous breakdown... Remember kafin ka zama doctor ni na fara .,..pls son tell me what the problem is..." Ta tambayeshi hannun ta cikin nashi, murmushin karfin hali yayi
"Bakomai Umma... Kawai haka nan naji heartbeat din yana rising.. The next thing I was gasping for air...that is the only thing I know..." Kallo mamaki Umma tayi mashi tana cewa
"To that is a sign of heart attack...me ke damunka ?..."
"Babu komai Umma..." Da sauri yace
"Umma zan je inyi wanka in kwanta..." Yafada yana son barin wurin cos yasan Umma is very inquisitive, da haka tana iya binciko gaskiyan abinda ke damunshi,
"A shigo maka da abincin chan ko.a barshi part dina?..."
"A shigo min dasu don kwantawa zanyi bayan na gama wanka in na tashi sai inci..." Ya amsa mata dukda yasan ko a mafarki bazai iya shan koda ruwa ba balle abinci... Abinda ya dameshi ya isheshi, nan take Umma ta umarci mai aiki ta kai abincin part dinshi itakuma ta koma nata bangaren.

Ayan na shiga ya kwanta kan gado tare da lumshe idanuwa, wayanshi ya kara fiddowa ya fara kallon pic da video din ihsan, wannan Karin bai yi kuka ba, kawai sai ya fara lusting for her, chanza kwanciyan shi yayi zuwa rub da ciki, ya dinga maimaita video yana kallon each and every part of her body,
"Devil in disguise..." Yafada cikin ranshi. Mood din daya shiga yasa jikinshi daukan zafi rau, da kyar ya samu yayi wanka ya kwanta ko kaya babu jikinshi, ruf kanshi yayi da blanket yana aduan Allah yasa ihsan tayi gigin zuwa gidan nan
 Ihsan bata Dade da shiga gidaba husna ta shigo fuskanta daure, bedroom ta shiga ta tarda ihsan kwance wani irin wulakancen kallo tayi mata Sannan tace
"Wato halima ni zaki disga?...din kin gan ni bani da saurayi?... Kawai sai ki shanyani...kawai sai gani nayi  kun tafi...." Tafada  cikin fushi, da sauri ihsan dake kwance bacci na Neman dauketa ta tashi zaune
"Kiyi hakuri... Wallahi Ayan wani irin burkekken mutum ne...." Husna fashewa tayi da kuka tana cewa
"Wallahi ba karamin kunya kikasa naji ba....gaskiya gida zani..." Ta fadi abinda tayi niyyan yi,
"Dan Allah kiyi hakuri... Kinsan wannan wedding is around the corner, pls don't go..." Ihsan ta fada mata tana dafa shoulder dinta,
"Ayidai mu gani...." Husna ta fada cikin ranta.  Da kyar ihsan ta shawo husna ta yarda ta zauna amma cikin ran husna kam bata dau niyyan zama ba cos bata ganshi ba.



Sai bayan sallan zuhr Ayan ya tashi daga bacci, masjid yaje yayi salla ya dawo ya zauna yana tunanin rayuwan duniya da yanda abubuwa suka chanza mashi, ajiyan zuciya ya saki yana kara daukan wayan shi, duk sanda zai dauka sai yayi aduan Allah yasa ba ihsan bace ciki amma ina, ita din dai ce.

Karfe biyar su Muhammad sukazo gidan, hira suka shiga yi bayan sun gaido Umma a part dinta, Muhammad kallon Ayan yayi yace
"Ango kace a t and j concept aka bawa event planning ko?..." Kallon shi Ayan yayi ya kauda kanshi bai bashi amsa ba
"Kai dalla da kai ake...munason muyi masu magana su fidda mana ankon da zai dace ne..." Yusuf ya fada mashi, wani irin disgusting look Ayan ya watsa mashi Sannan yace
"Na fasa auren!!!!..…"
"What?..." Suka fada in chorus,
"What are you talking about?...." Yusuf ya tambayeshi cikin tashin hankali
"Are you guys deaf?...nace the wedding plans is no more...amma Ku kadai na fadawa tukunna..." Mikewa tsaye Muhammad yayi
"Wai uban me kake fada ne haka?...what is happening?..." Banza yayi dashi,
"Kambu ...you must be insane...anata preparation sai kace ka fasa kuma kace kar Wanda yasani?...pls guy what is the problem... Share with us...we are friends..."
"Pls nace kar Ku fadawa kowa...zuwa next week my plans will be over...lokacin sai in sanar da kowa na fasa..." Ayan ya fada in I don't care manners, da sauri Yusuf yace
"Wane irin plan ne?..."
"Ban saniba....when is over I will tell you...." Yafada yana relaxing
"Don't do something you will regret..." Muhammad ya fada mashi , daga manyan idanuwanshi yayi ya kalli Muhammad Sannan yace
"Ashe regret..."
[12/2, 8:23 PM] ‪+234 703 821 5964‬: 💙❤💛🖤💚💜
KAWARTA CE SANADI
💛💚💜🖤❤💙



®zuwairat(ummu Maryam)


2⃣9⃣


 *Asmy b Aliyu* _wannan shafin naki ne, Zuwairat naji dake har cikin ranta, I love you much, Allah ya bar mu da masoyan mu makiyan mu can hug a transformer, love you._

Yana cewa hakan yayi kokarin mikewa, aikam tureshi Yusuf yayi ya koma ya zauna yana huci yana kallon shi
"Who do you think you are.... Uban me tayi maka zakace ka fasa aureta?... What are those hideous plan you are talking about..." Yusuf ya fada cikin dagin murya, daga zaune Ayan ya nuna Yusuf da Dan yatsa Sannan ya fara cewa
"Wallahi ka kara gigin tabani sai na zubda maka hakora...." Yafada afusace Sannan ya mike, Yusuf kara tunkaranshi yayi Muhammad yayi saurin rikeshi, Sannan ya kalli Ayan yace
"Guy kasan we're one, ...we don't hide anything from each other... Ko me ke dalilin ka pls tell us...zamu baka shawaran da ya kamata...."
"Wai dole ne?...nace babu komai... Na nace ina sonta kuma ni nace na FASA... Why are you taking panadol for my headache... Na fada maku I have my plans in na gama the wedding in off...officially..." Yafada masu, ajiyan zuciya Yusuf ya saki Sannan ya dafa shoulder Ayan amma dayake he's high sai ya buge mashi hannu yana cewa
"Remove you filthy hand..." Yafada cikin fada, maganan shi ba batawa Yusuf rai ba cos he heard more indai wurin Ayan ne, cikin natsuwa Yusuf ya fara cewa
"Ba sai ka fada mana abinda ya hadaka da ihsan ba..amma pls don't do anything stupid... That gal is innocent... Don't hurt her..." Yanda yayi maganan yasa Ayan kallon shi don har zargin ya ga video din yayi, Ayan rike kugun shi yayi ya tsaya daf da Yusuf Sannan yace
"What makes you think she's innocent?..."
"Nidai shawara na baka...in har bazaka aureta ba ka sanar da su Abba da wuri and forget about any plans..." Baki ya tabe yana kallon Yusuf from head to toe
"Sannu Abba...kasan before ka bani shawara go and check your HIV status..." Yafada atakaice, bata rai Yusuf yayi
"What do you mean by that?.." Ya tambayeshi afusace,
"Exactly what you heard..." Yafada yana tafiya kaman dawatsu don yasan ya bakantawa Yusuf, afusace Yusuf ya bar falon yana huci da sauri Muhammad yace
"You shouldn't have say that..." Yafada yana bin bayan Yusuf, dariya Ayan yayi yana cewa
"To hell with you all..." Yafada yana shigewa bedroom dinshi. Bai damu ko su Yusuf da Muhammad sun tafi ba, kwantawa yayi ya fara kiran number ihsan, adaidai lokacin tana zaune falon tare da sauran yan gidansu har da aminiyarta, tana gani kiran Ayan ta mike ta dau hanyar upstairs tana picking, hira suka farayi kaman babu abinda ke faruwa, after few minutes of talking yace
"Sweet potatoes.. Zaki zo?..." Ya tambayeta cikin whisper,
"Ina?.." Tafada don ta manta maganar daya fada mata
"Oh..kin ma manta...that means you don't care about me...sai anjuma...." Ya fada mata ya fara kokarin katse wayan shi, da sauri tace
"Pls baby wait...wai kana nufin bazaka zo ba?..."
"Eh...bani da lafiya...ki zo dubiya tunda sai na bukata..." Yafada fuskan shi murtuke,
" ka jirani kofar gidanku bayan sallan ishai, Dan bazawaran dariya ya saki kaman mace sanna yace
"Hope you are not serious?... Wai meyasa kuke wannan maganan?... Don't you trust me...." Yafada mata cikin natsuwa,
"Ba haka bane...I trust you..kawai ina jin kunyan haduwa dasu Umma ne...besides ka samu sauki..." Baki ya tabe Sannan yace
"Tunda ba da rana bane... Nobody will see you..in jiraki?.." Ya tambayeta with eagerness, shuru tayi for a while tana tunanin taya zaayi taje har chan gidan su mom basu saniba
"Kilan..."
"No don't keep me waiting.. In zaizo ki fadamin kawai..."
"What are you up to?...ai kama ji sauki..." Da sauri yace.
"For where?...ko yanzu kaina ciwo yakemin...kilan in koma hospital...amma ko kadan banason inje nesa dake that's why na dawo gida so zaki zo..."
"To ..."
"Thanks precious... Oh sorry sweetie..."
"Ni Gaskiya nafison precious..." Tafada cikin shagwaba, dariyan da bai kai kasan cikin shi ba yayi Sannan
"Ok precious...." Yafada ya katse wayan shi
 Ajiye wayan yayi ya zauna ya har hannuwanshi biyu kan kirjinshi yana tunani fuskan daure tamau daman in ace ana bada kyautan daure fuska da shan kamshi to tabbas shi zaa baiwa. Sai karkada kafa yake ko meke yawo cikin ranshi oho.

Wajen sallan magrib yayi wanka ya dauro alwallah ya fito mai ya shafa Sannan ya sanya jallabiya fari tas ya fita rike da wayanshi. Part din Umma yaje ya sa mai aiki ta hada mashi cool tea ya sha ya kurkura bakinshi Sannan yayiwa Umma dasu antymu sai da safe
"Da wuri haka?..." Umma ta tambayeshi
"Eh...sai bayan sallan ishai zan dawo kuma I want to sleep early..." Ya fada mata Sannan ya fita ya tafi masjid, sai bayan sallan ishai ya fito yana kan hanya ya dauki wayan shi yafara dailing number ihsan. Daga chan bangaren ihsan tayi wanka ta shirya cikin doguwar gown ta gyara fuskanta jikinta sai kamshi yake, husna kwance tana kallon ta ranta wulik sai tunanin next solutions take,  wayanta na fara ringing ta dauki wayan ta mike ta shiga bathroom, bayan ta husna tabi da kallo tana mamakin what is happening, tana dagawa bai bata lokaci ba yace
"Ina jiranki..." Yafada kaman wani ubanta, kallon wayan tayi gabanta na faduwa,
"To..." Tafada muryanta na rawa, bai Kara cewa komai ba ya katse wayan, jiki ba kwari ta fito, batason zuwa kuma batason batawa masoyinta rai,
"I trust him kawai..." Tafada cikin ranta Sannan ta kalli husna
"Babe bari in je...Ayan is waiting for me..." Tafada batare data fada mata gidansu Ayan zataba don tana tsoron kar tayi mata fassaran yar iska, kai kawai husna ta gyada mata. Dan karamin Vail ta dauko ta yafa ta fita rike da wayanta a hannun ta.

Ayan komawa ciki yayi ya zauna kan kujera ya Dora kafanshi daya kan daya yana girgiza su a hankali. Ihsan na fitowa falo taci saa mom bata nan sai Janna kawai,
"Sis ki fadawa mom in ta sauko ina wajen Ayan..." Tafada Janna bata jira amsarta ba ta fice abinta, karamin gate ta bude ta fita, tana tafiya tana waige saboda bakajin motsin komai, gabanta na faduwa amma kaman dole haka ta dinga ta kawa har ta kai bakin gate dinsu Ayan, Dan taba gate din tayi taji da tauri alaman kulle take daga ciki, wayanta ta dauka tayi dailing number Ayan kaman yana jira yayi picking baice komai ba,
"The gate is locked..." Yafada muryan ta na rawa, baice uffan ba ya kashe wayan yayi dailing number maigadi, bayan yayi picking ya shaida mashi da akwai bakuwa waje, ya bude mata gate Sannan ya kawo ta falon shi. To kawai mai gadi ya fada da sauri ya mike ya dauko keys ya fito ya bude kofan, ihsan na tsaye sai walkiya take saboda yanda fuskan ta ke glowing, ana bude kofan ta shigo ciki jikinta sai rawa yake cos tunda uwar data haifeta bata taba zuwa gidan saurayi ba amma gata gidansu Ayan kuma bawai wajen ummanshi zataba no wajen shi,
"I trust him..." Ta kara assuring kanta,
"Muje .." taji maigadi ya fada mata, gaba ya shiga tabi bayanshi, bakin kofan Ayan yaje ya kwankwasa Sannan ya koma, mai gadi kam sai mamaki yake abinda ke faruwa amma who is he to say a word,
"Allah ya shirya...." Yafada yana komawa bakin gate.

"Come in the door is open...." Ya fada mata, hannun ta na shaking ta bude kofan, hangoshi tayi zaune ya daura kafa daya kan daya
 Yana ganinta ya saki murmushi tare da mikewa, ahankali ta shigo daki ya maida kofan ya rufe,
"Ga precious.. Ga precious... Precious sannu da zuwa..." Yafada yana kama hannun ta, kan wata doguwar kujera ya zauna daita, yanda gabanta ke faduwa yasa ta kasa magana sai dai murmushin karfin hali, zama yayi kusa daita ya dira hannun shi kan shoulder dinta Sannan yace
"What can I offer my precious..." Ya tambayeta cikin sanyin murya, ahankali ta dan ture hannun shi Sannan tace
"Bakomai.. Ya ..jikin?..." Ta tambayeshi muryan ta na cracking, kara maida hannun shi yayi yace
"Am doing great... Yanzu you have to drink atleast water..." Yafada yana mikewa, ita kawai girgiza kai tayi Sannan tace
"Nagode...am ...OK..." Tafada wannan Karin muryan ta na rawa sosai, Ayan daya nufi bedroom fridge ya tabe baki,
"Why is she shaking..." Yafada cikin ranshi, ruwa ya dauko don bai shan juice ya dawo rike cup da bottle water.

Zama yayi ya bude ruwan ya zuba mata cikin cup Sannan ya mika mata, amsa tayi amma bata shaba,
"Precious... Kisha mana..."
"No....nagode..." Tafada tana ajiye cup din gefe daya, ahankali ta mike, kallon Ayan yayi shima ya mike ya tsaya daf daita yana shakan kamshin turaren ta, da matsawa baya tayi tace
"Zan tafi..." Tafada tana kokarin juyawa, ahankali ya riketa tare dacewa
"Yanzu fa kika zo...AI ko minti biyu bakiyi ba..." Ahankali ta zare hannun ta Sannan tace
"Ai kai...nazo..gani...kuma kasamu...sauki..." Yanda take magana yasa Ayan ganewa a tsorace take, tsaya kallon kirjinta yayi, dukda da akwai kaya naked yake ganinsu,
"Will you at least give me a good by hug..." Yafada cikin sanyin murya, kallon shi tayi batace kala ba,
"Plssss..." Yafada mata Sannan ya bude mata hannuwanshi yana tsaye yana kallon ta,tsaye tayi bata je wajen shi ba,
"Yanzu precious har hug wata tsiyace?... Pls give your hubby to be a hug..." Yafada mata kaman zaiyi kuka har lokacin hannuwanshi bude, tafi minti biyu tsaye Sannan ta taka a hankali ta fada jikinshi, wani irin runguma yayi mata nan take yaji he wants her, kokarin matsawa baya tayi amma ya rungume ta gagam, bakinshi ya kai saitin kunnenta yace
"I love you..." He wants to believe he is playing, don't mean what he said amma yasan har cikin ranshi he truely love her,
"Precious why..." Yafada cikin wata irin murya, itadai kokarin ta ta kwace kanta daga jikin shi don muryan shi har cikin brain dinta, yanda ya rungume ta yasa ko kadan bata iya motsi, lumshe idanuwa yayi yafara kissing wuyanta, jikinta ne ya fara rawa sosai,
"Pls...stop.... It..." Tafada da kyar, bai saurareta ba yacigaba da abinda yake, hana kissing wuyanta ya daga face dinta, rumtse idanuwa tayi bakinta sai rawa yake, bakinshi ya dora kan nata, nan take ta bude ido
"What...are..you...." Bata idaba ya hada bakinshi da nata, aikam nan ta fara tureshi, amma ko kadan her power is nothing compared to his, yanda ya rike bayan wuyanta cikin zalunci yana kissing dinta full of hatred yasa ta fara bugunshi da two hands dinta, da kyar ta kwace  bakintawani irin zafi taji bakinta nayi, kallon yanda idanuwanshi suka chanza kaman ba Ayan ba yasa ta fara hawaye, hannun ta rike ya turata bedroom dinshi,idanuwa ta zaro ta fara cewa
"Me...me...me zakayi min?..." Ta fada cikin tashin hankali, rakugbewa tayi jikin bango, tana kallon shi from head zuwa manhood dinshi that is erected, hannuwanta ta fara yarfawa tana cewa.
"Ka rufamin asiri yanda ..." Bata idaba ya karaso ya tureta kan gado, da sauri ta mike data tashi ya kara tureta, tsaya kallon ta yayi yana imagining dinta kan gadon wani, yasan abinda zaiyi mata, yasan irin plan da ya dauka kanta and this is not the right place, kawai sai ya tuntsure da dariya yana zama bakin gadon, da sauri ta ja baya, Dan juyowa yayi har lokacin bai bar dariyaba,
"Precious Ashe haka kike da tsoro?...haba...don't you trust me any more?..." Yafada don ya kauda tunanin ta cos yasan muddin baiyi hakan ba he will not succeed, hararanshi tayi da tana gyara riganta
"Wane irin wasa ne wannan..." Tafada tana yi mashi wani hararan,
"AI kinsan I will never do something to hurt you... Za ki tafi...am just joking..." Yafada yana dariya kaman da gaske, da sauri ta bi ta dayan gefen ta sauka daga kan gadon ta dauki Vail dinta ko kallon shi batayi ba zama yayi ya kasa mikewa  yayi ya zauna nan bakin gadon
"Precious... Sai gobe..." Aikam ko kallon shi batayiba ta fice kaman walkiya saboda sauri har lokacin bata bar hawaye ba
 Bayanta Ayan yabi da harara, shi duk tsoron da take ji gani yake kaman munarfuci ne, kwantawa yayi yana tabe baki,
"I know babes like you, ayi iskanci waje ayi pretending to be decent,... I will deal with you..." Yafada babu wasa.


Umma dake tsaye upstairs baki ta bude datagan ihsan ta fito daga part din Ayan tana goge hawaye,
"Inna lillahi waina ilaihi rajuun!..." Ta dinga maimaitawa, what am I seeing? Murza idanuwanta tayi don tabbatar da ganinta amma she's not dreaming
"Subhanallahi... No wonder ya nuna ya san size dinta...Allah wadaran..." Tafada tana komawa cikin, ihsan na fita ta ta gyara Vail dinta, Abba dake dawowa yaga kaman mace ta fita daga gidanshi, karasowa yayi cikin mota yayi horn mai gadi ya bude
"Kai waur wancan data fita yanzu?..." Ya tambayi mai gadi, saida maigadi ya kalli kofan Ayan ya tabbatar rufe yake Sannan yace
"Ranka shi Dade...wannan yarinyan da karamin alh...zai aurane..."
"Wajen wa tazo?..."
"Wajen shi...."

[12/2, 8:23 PM] ‪+234 703 821 5964‬: 💜❤💙🖤💛💚
KAWARTA CE SANADI
💙💛💚🖤❤💜



®zuwairat(ummu Maryam)


3⃣0⃣



 My *amnoor* Allah ya kareki ya baki duk abinda kike so duniya da lahira, I love you so much, wannan page nakine kiyi duk abinda kikeso dashi💝



 _Pls masoya na fara gajiya da rashin hakurinku, indai baku daina wannan korafe2 ba zan daina turawa har sai na gama, ni ke rubutawa kuma ni nasan yanda na_ _ _tsara labari na, kun manta 99 days for a thief but only 1 day is for the owner, pls stay tuned cos_ _we're just getting started._




Abba na parking yaga an bude kofan part din Umma, Umma ya gani ta fito sam fuskan ta babu walwala, inda Abba yake ta nufo shima ya fito daga cikin mota, gaidashi tayi kaman yanda ta saba tana kumbure2
"Hajiya lafiya dai?.." Ya tambayeta,
"Wajen Ayan zani..." Tafada mashi, yanda tayi maganan yasa Abba ganewa da akwai matsala,
"Yayi laifi hala?... " ya tambayeta, kai kawai ta girgiza don Umma na daga cikin iyayen nan wayanda basu son fallasa laifina yaransu ga mutane koda kuwa ubansu ne,
"Kedai ki bar rufa mashi asiri ki fadamin laifin da yayi..." Inji Abba dake pretending kaman baisan abinda ta gano ba
"Nace ba komai..." Ta fada mashi kawai ita gurin ta taje ta ci burouban shi, murmushi Abba yayi Sannan yace
"Is it about yarinyan data bar nan yanzu nan?..." Da sauri Umma ta kalleshi
"I saw her too..." Ya kara fada, aikam sai Umma ta fashe da kuka tana cewa
"Yanzu alh...Ayan ya lalata rayuwar yar mutane under my roof?....Wallahi she was crying.. Dukda nasan tana da nata laifin..amma wallahi mai rabani da abubakar gidan nan sai...." Bata idaba Abba ya kama mata hannu,
" taho kiji..." Ya fada mata, binshi tayi part dinshi, zaunar daita yayi shima ya zauna gefen ta hannu yasa ya goge mata hawaye Sannan ya fara cewa
"Haj..kiyi hakuri.. Yaran zamani sai adua...AI dukan aurensu sauran kwana nawa?... Kawai ki kyaleshi...kiji ki dinga yi mashi adua don duk su biyu suna da laifi...Allah kawai ya shirya...." Inji Abba, Umma share wasu new tears tayi Sannan tace
"Yanzu alh you want me to pretend as if nothing happens?..." Kai Abba ya gyada mata alaman eh,
"Amma alh da ban haushi...Allah kadai yasan sau nawa yana kawota nan gidan..." Murmushi Abba yayi
"Ai baka rantsewa yaran zamani...rashin hakurin su is beyond your expectations... Abinda sukewa kwakwa watarana zai ishesu...dadin abun aure zasuyi...su je chan sun gane..." Umma kallon shi tayi ta galla mashi harara,
"Kai matsalan ka kenan...kullum baka daukan abu serious..." Dariya yayi
"Ai in ka biyewa yaran zamani sai hawan jini ta kamaka...kuma kilan babu abinda ya shiga tsakanin su..maybe dubiya tazo..." Kara hararan shi tayi
"Tazo dubiya kuma sai ta koma da kuka?...kai dai kawai..a bar maganan amma sai nayi Maganin Ayan..." Tafada cikin bacin rai
"Kiyi hakuri my love.. Mun dai kawai Mun haifesu amma sam bamu haifi halayensu ba.." Bata kara cewa komai ba ta mike ta hada mashi ruwan wanka.


Ayan kam baisan wainar da suke toyawa ba kawai kwanciya yayi yana tunanin yanda zai lallaba ihsan ta amince dashi ta bishi sabon gida. Yafi minti arbin kwance yana planning kawai sai ya saki murmushin keta ya dauki wayan shi.

Ihsan kam duk yanda taso controlling kanta ta kasa kuka ta dingayi har ta iso gida kawai sai taji ta tsaneshi, don tunda aka haifeta bata taba ganin yanayin namiji ahakan ba sai yau wani irin haushin shi ta dingaji, ganin hawayen ta yaki tsayawa yasa ta kasa shiga falo don tana tsoron kar su mom ko husna agane abinda ke faruwa, dakin baki ta bude ta shiga ta zauna
Ta bude sabon babin kuka, Dade zaune tana kuka Sannan daga baya ta shiga bathroom dake wurin ta wanke fuskan ta tare da gyara fuskan ta da gashin kanta daya dan barbaje, Sannan ta fito ta tarda wayanta na ringing, jin ringing din yasa ta ta gane Ayan ne, wani irin tsoki taja ta dauki wayan tayi rejecting wayan. Daga chan bangaren Ayan kallon wayan yayi ya daure fuska yana cewa
"This little bitch is rejecting my call..." Yafada yana kara dailing number.

Ihsan na daf da shiga falo wayanta ya dau kara, tsayawa tayi ta jingina da bango tana lumshe idanuwa, picking tayi Sannan tace
"What?.." Tafada cikin tsiwa, dariya ya farayi yana cewa
"Badai har yanzu kina fushi da ni ba?..." Bata amsa mashi ba ta ja tsoki, dariya ya karayi amma deep down he's boiling
"Haba precious.. Nace am sorry.. I don't know what came over me...pls in kinason ganin manzon tsira ki yafemin..." Yafada kaman zaiyi kuka, ihsan hararan wayan tayi bata ce kala ba kuma bata kashe wayan ba
"Babyna pls ki yafemin... Kinsan I love you.. Wallahi sharri shaidan ne...I problem ko fingernail din ki bazan kara tabawa ko munyi aure sai kin amince... Pls pardon me..."
"Kai dai Allah ne yasa ka nunamin halinka...you are cruel...mean and wicked..." Ayan tabe baki yayi ya daga wayan daga kunnenshi ya kalleta yana cewa
"You will soon know the real meaning of cruelty..." Tafada under his breath,Sannan yace
"My love am sorry... Ki gafarta min...I have never touch any woman..." Kuma wannan gaskiya ce, yacigaba dacewa
"Am sorry.. Ki fadamin abinda kikeso..." Baki ta tabe
"Ni babu abinda nake so illa ka bar kirana har in huce..." Dariya Ayan yayi
"Kina dai son in mutu ne...pls baby am on my kneels..forgive me..." Ya dinga yi mata magiya, amma dayake ihsan is somebody with a simply mind sai ta yafe mashi,
"Gobe zanzo kaiki school..."
"No..banso...."
"Hmmm zakije karuwancin kenan..." Yafada cikin ranshi azahiri yace
"Baby why?...are you still mad with me?..." Dan rolling manyan idanuwanta tayi Sannan tace
"Nop...ai ya wuce...amma tunda ba lafiya garekaba kawai ka huta..." Baki ya tabe
"Ke dai fadi gaskiya... Kawai bakison in daukeki cos you are still mad at me..."
"Not at all... Kawai I want you to rest..." Ta fada cikin sanyin murya.
"Ok..love you with all my heart..." Yafada yana shafa kanshi
"Love you too..." Ta amsa mashi Sannan sukayi sallama. Falo ta shiga taga ba kowa, direct upstairs ta hau ta tarda husna zaune da laptop gabanta da gani film take kallo amma she absent minded don har ihsan ta shigo bata Sani ba har saida ta tabata ta firgita, daga kai tayi ta kalli ihsan ta sakar mata murmushi, Dan kura mata ido tayi for a moment Sannan tace
"Babe your eyes are swollen..." Tafada, tana Neman jin good news, ihsan kallon ta tayi
"Ahhrr..." Kaman zatayi magana sai kuma tayi shuru, da sauri husna ta mine ta dafa shoulder dinta
"Babe is anything the problem?.." Ta tambayeta sounding very caring, murmushi ihsan tayi
"Nothing... Kadai bacci nakeji..." Tayi mata karya for the very first time, husna kura mata ido tayi for a moment Sannan ta fara sniffing jikin ihsan
"Lahhh...babe..kamshin turaren Ayan kike?..." Da sauri ihsan ta kalleta
"Ya akayi kika San kamshin turaren Ayan..." Ihsan ta tambayeta sounding suspicious, dariyan karfin hali tayi
"Wallahi you are funny.. Kinsan I have a very good sense of smelling... Am joke aside.. Why are you smelling like him...kodai??..."
"Kodai me?..." Ihsan ta fada tana hade rai, Dan bugun shoulder dinta Hus.a tayi tana cewa
"Ke kiyi hakuri naga kaman you are tensed..." Ihsan bata ce komai ba ta fara cire kayan jikinta sai taji da gaske kamshin ayan take
 Husna sai binta take da kallo ko Allah yasa ta fada mata abinda ke damunta amma shuru bata ce mata komai ba, wayanta ta dauko tana cewa
"Baby dazun nayi browsing best ashobi pics of the year., inason muyi selecting Wanda muke so..." Tafada mata don taji amsarta
"Ok..amma mu bari sai gobe mu duba cos yanzu kai cewa yakemin,.." Tafada lokacin daga ita sai pant da bra, bayan wuyanta ta dan shafa don har lokacin bata bar jin zafi ba, sai lasan bakinta take tana zubda saliva don har lokacin tana jin bakinshi cikin nata, husna sai binta take da kallo saboda yanda take zarya cikin toilet saboda zubda saliva, do kawai tasa mata ko zata fada mata abinda ke damunta cos she couldn't figure it out, daga baya kan gado ta hau har lokacin babu komai jikinta sai pant and bra, matsawa husna tayi kusa daita Sannan tace
"Haba babe...da ganin ki kina cikin damuwa amma you are not sharing it with me...kinsan saboda mu dinga sharing problem din mu yasa na dawo nan mussanman now that your wedding is around the corner.. Pls tell me...hankali ma tashi yake in na ganki haka..." Tafada kaman zatayi kuka, ihsan kallon ta tayi for a moment sai taji bata kyauta mata ba for not being truthful,
"Gidan su Ayan naje...." Nan ta fada mata duk abinda ya faru tsakanin ta da Ayan, husna rushewa tayi ea kuka saboda kishi don ita gani take his hands belongs to her,
"Yanzu babe abinda wannan azzalumi yayi maki kenan?... Gaskiya ki fadawa mom da dad...mugu ne shi...he don't deserve you..." Tafada cikin kuka kaman gaske, ihsan dafa shoulder ta tayi ta fara cewa
"Stop crying.."
"Ki tashi kije ki fadawa mom...." Da sauri ihsan tace
"I can't share such thing with her...ni dai kunya nake ji..." Hararan kasan ido husna tayi mata
"Saboda me?...badai zaki yafe irin wannan taadancin ba..." Dan tabe baki ihsan tayi
"Ai har na yafe mashi...I love him...." Wani irin gululu husna taji
"Wai she loves him...she's loves my man...we shall see..." Ta fada cikin ranta, azahiri tace
"Ni kam sai na fadawa su mom..." Da sauri ihsan ta daga mata hannu
"No...don't try it...ke kadai da fadawa ..." Tafada tana kwantawa, wani irin disgusting look husna tayiwa bayan ihsan Sannan ta kwanta tana cewa
"What ever..."



The following day Ayan ya yi shirin aiki ya tafi part din Umma suna hada ido ta watsa mashi wani irin kallon haushi da takaici, gaidata yayi ta amsa kaman bataso, zama yayi gefen ta tare dacewa
"Umma nayi wata laifi ne..."
"Kaci burouban ka...tashi ka bani wuri..." Ta daka mashi tsawa, jiki ba kwari ya mike ko breakfast baiyiba ko kadan baiyi tunanin Umma taga ihsan ba cos a nashi tunanin in har taga ihsan kashinshi ya buce.
Da wuri su ihsan
 suka tafi school suka dawo da dare Ayan yazo suka sha hira na so da kauna baka taba cewa da akwai wani Abu cikin ranshi, don har snacks da chocolate ya kawo mata ta bawa siblings dinta.

Wace gari ma the same thing har ihsan ta mane abinda ya faru tsakanin su, suna zaune suna hira ya kalleta yace
"Precious wata antyna ta haihu...inason ki rakani kasuwa in sayo kayan babies...."
"Gaskiya ba sai na raka ba...kawai in ka  shiga inda ake saida kayan yara ka fada masu su baka mai kyau tunda nima basanin kayan yara nayi ba..." Ta amsa mashi atakaice, marairace fuska yayi Sannan yace
"I wanted us to go and see the baby together... Tunda jibi suna gobe sai muje kasuwa  mu sayi kayan mukai..." Yafada mata kaman gaske,
"AI ina da lectures gobe...."
"Karfe nawa kuke gamawa?..."
"Karfe 2..."
"In naje daukan ki sai muje kasuwa daga nan so mu wuce gidan..." Shuru tayi bata ce komai ba
"Kinji..." Ya kara fada mata, kai kawai ta guda mashi. Haka suka sha hira Sannan sukayi sallama ran Ayan kwal da farinciki.

Ihsan  na komawa  ta sanar da mom zata shiga kasuwa gobe don haka bazata dawo da wuri ba, tana haura sama ta fadawa husna gaskiya kan inda zata taka Ayan, itama murmushi tayi tana cewa
"Daman jiranki nake kizo in fada maki...grandma tace inzo Maiduguri in amso maki sako tunda bazata samu samun zuwa ba......" Tsale ihsan ta daka tana fadawa jikin husna
[12/2, 8:24 PM] ‪+234 703 821 5964‬: 💙❤💜🖤💚💛
KAWARTA CE SANADI
💙💚🖤💛💜❤



®zuwairat( ummu Maryam)



3⃣1⃣




 _Ban manta dake ba my dear *queen mermur* ban bance dake ba, ummu Maryam tace I love you_💋



Husna ma rungume ta tayi cikin ranta tana tunanin Sam bata ga zamaba tunda har yanzu bata ga matsala tsakanin Ayan da ihsan ba.

Wacegari ihsan ta shirya cikin India dress mai wando da riga, kalan orange and green, gyara kanta tayi ta shafe dukkan jikinta da perfumes as usual ta sauko ita kuma husna shiryawa tayi ta dauki bag dinta, around 9: 00am Ayan ya zo gidan daukan ihsan don ya kaita school, sanye yake da English wear sai kamshi yake fuskan nan sam babu walwala
 Kiran ihsan yayi ya sanar daita yana jiranta,
"Ok.." Kawai  Tafada ta kalli ihsan
"Babe muje...yazo..." Dan bata rai husna tayi tana cewa
"Babe da ya kaiki kawai tunda ni ban zuwa school yau..."
"Aa...tashi mu tafi sai ya ajiyeki..." Ta fada tana kama mata hannu. Mikewa sukayi ihsan ta tayata daukan bag dinta da tazo gidansu ihsan dashi, wurin mom sukaje tayiwa mom ta bata 5k kyauta ta mikawa ihsan 5k itama don a tunanin ta wani abu zata saya don ta fada mata zata market yau. Godiya sukayi kowacce ta zuba kudinta cikin bag.

Suna bude gate Ayan dake zaune yayi relaxing  cikin motan, da dagawa yayi ya kalli gate din, cire glasses dake fuskanshi tare dacewa
"Kan uban nan!!.." Yafada cikin ranshi dayaga ihsan rike da traveling bag, suna karasowa ya fito ya tsaya yana kallon adorable face dinta gaidashi tayi tana murmushi ya amsa, itama husna gaidashi tayi ya basar yana cewa
"Wannan bag din fa?... " ya tambayeta
"Na husna ne..." Ta amsa mashi, daure fuska yayi ya bude mata gidan gaba yayi tashiga shima ya shiga, husna bude baya tayi ta shiga ranta wulik don bakin ciki, kallon ta yayi ta mirror yaga ta wani hade rai, tabe baki yayi ya ja motan, suna zuwa bakin titi ya tsaya gefe daya yace
"Precious ki bata bag din ta tsaida abun haka ko?..." Ya fada mata babu wasa, Dan marairace fuska tayi
"Haba baby...mu ajiyeta mana kafin mu wuce..." Wani irin kallo yayi mata
"Pls stop wasting my time... Ina da abubuwan ya kafin inzo daukanki muje kasuwa...I don't have time..." Yafada cikin fada, da sauri husna ta fita ta kwace bag dinta daga hannun ihsan ta bar su nan, tada motan yayi ihsan ta bude marfin motan
"Kawai ka barshi....I will go to school myself..." Tafada tana kokarin fita, da sauri ya kamo hannun ta yana cewa
"Haba precious... Yanzu wancan zata shiga tsakanin mu?..." Kallon hannun shi dake kan hannun ta tayi yayi sauri zare hannun shi tare dacewa
"Sorry.. Na mance.." Yafada yana ajiye hannun shi kan laps dinshi,
"Zaki ci uwarki ne..." Ya fada cikin ranshi.
"Ni gaskiya banason yanda kake wulakanta friend dita...." Tafada kaman zatayi kuka
"Am sorry... Bazan karaba...yau shine first and last..." Ya fada mata, shuru tayi ta maida murfin motan ta rufe, ya figi motan kaman zai buge husna nake tsaye tana jiran abun hawa, wani irin gululu taji, kawai sai hawaye,
"His love is becoming unbearable..." Tafada cikin kuka.
"Hmmm....wallahi you will beg for my love..." Ta fada cikin ranta.


Suna zuwa school ya ajiyeta tare da fada mata sai ya dawo daukanta.


Yana barin wurin ya nufi unguwan da gidan shi yake, budewa yayi ya  shiga, direct part dinshi ya shiga ya chanza bedsheets dake kan gadon Sannan ya fita, wani unguwan yaje yayi horn kofar wani karamin gida, baa Dade ba wani saurayi ya fito, keys ya mika mashi
"Gashi...ka tabbatar kana gidan kafin karfe biyu..." Ya umarceshi, da sauri saurayin yace
"To yallabai..." Motanshi ya shiga ya bar wajen, gaban wani gida ya tsaya ya dauki wayan shi ya kira wata number, ana picking yace
"Safeena gani nan kofar gidanku ...ki fito I need your assistance..." Yafada atakaice Sannan ya kashe wayanshi.
 Relaxing yayi tare da dora legs dinshi gaban mirror tare da kafa glasses dinshi sai karkada kafa yake. Few minutes later wata budurwa wacce bazata wuce shekara ashirin zuwa da biyu ba ta fito sanye da black gown looking very excited, murmushi ne dauke kan face dinta, karasowa tayi kusa da motanshi Sannan tace
"Doctor ina kwana?..." Tafada sounding excited,
"Lafiya lau..." Yafada yana gyara zaman shi,
"Lafiya dai naga doc da kanshi gidan mu?..."
"Eh lafiya ...ki shigo mana..." Ya fada mata, ahankali ta sa hannun ta tabude motan ta shiga, Ayan fuskan ta ta yayi Sannan yace
"Sister safeena pls wane duty kike yau?...."
"Afternoon..." Ta amsa mashi
"Ok..pls wata alfarma nake son kiyi min..."
"To meye...anything for you..." Ta amsa mashi thinking what exactly he wants from her, nan Ayan ya fada mata exactly abinda yake so tayi mashi, shuru tayi tana sauraron shi har ya kai aya Sannan tace
"Yaushe zanyi hakan?..."
"Yau...in kin amince zan zo daukan ki by 1: daga nan sai ki wuce hospital tunda is not far..." Shuru dai tayi for a while Sannan tace
"Babu matsala... Allah ya kaimu ..." Ta amsa mashi feeling comfortable don tasan Ayan will not do anything stupid,
"Nagode sosai...sai nazo daukanki..." Ya fada mata, murmushi kawai tayi ta fita daga ciki motan. Shi Kuma ya bar wajen ya koma office, a corridor suka cikaro da Yusuf amma ko inda yake Yusuf bai kalla ba shima bai kalli Yusuf ba kowa ya wuce sai kumbure2 yake.





Husna kam tsaida mai adaidaita tayi ta fada mashi ya kaita hotoro.
Akofar gidan malamin mami ta tsaya ta biya mai adaidaita ta shiga gidan da bag hannun ta ta kasa hakuri taje gida ta ajiye shi, tana shiga gidan yan gidan sukayi mata maraba kasancewan sun san ta sosai saboda yanda mami ke yawan aikota, turakan Malam ta shiga suka gaisa Sannan Malam yace
"Yata... Hajiya ta aikoki?..." Kai ta girgiza tare dacewa
"Aa..wata matsala ce ya kawoni..." Mutum gyara zama yayi yana kallon ta
"Ina jinki yata..." Kuka ta farayi Sannan ta fara cewa
"Malam.. Wani ne nakeso...Sam baisan da zamana ba....kawata yakeso...Kuma kullum in muka kahadu da shi banda wulakanci babu abinda yakeyi....Dan Allah Malam ka taimaka min... Wallahi in ban sameshi ba mutuwa zanyi..." Tafada tana kaman kafan Malam, hannun ta mutumin ya rike Sannan ya saka hannu cikin aljihunshi ya dauko hanki ya bata
"Goge hawayen ki......" Amsa tayi ta goge fuskan ta amma still tears sai Flowing yake,
"Yata..." Ya kirata,
"Naam baba..." Ta amsa mashi tana kuka
"Hajiya tasan zaki zo nan?..." Ya tambayeta, ki ta girgiza mashi tare dacewa
"Aa...bata Sani ba.." Ta amsa mashi, kallon yatsaya yau for a while Sannan yace,
"Me kikeso ayi maki..." Da sauri husna ta fara cewa
"Inason arabasu...inason ya wulakanta ta fiye da yanda yake Mani...inason ya soni kaman ranshi...Dan Allah baba ka taimaki raina..."
"Wannan ba wani abu bane..." Murmushin jin dadi tayi yacigaba dacewa
"Amma bazaki samu dukkan su lokaci daya ba...dole sai dai a kafara da daya.." Da sauri ta bata rai
"Baba me zai hana a yi su lokaci daya?...yanzu auransu sauran kwana ashirin da hudu..." Da sauri mutumin yace
"Ansa masu rana ne?.."
"Eh..." Ta amsa mashi, kai ya fara girgizawa
"Yata indai haka ne to INA baki shawaran mu kyalesu...kinsan da akwai rabo.. Kuma ni gaskiya bana irin wannan aikin...ko.ba gaskiya ba?...." Fuhhh husna ta mike
"Baba kawai ka fadamin bazaka iyaba amma wane rabo?... An raba mata da miji... Uwa da da...balle saurayi da budurwa?..."
"Eh ko da irin aikin da yakeyi ni gaskiya bani aiki da bakaken aljinu..." Bata kara sauraron shi ba ta fita
 Ko kallon yan cikin gidan bata yiba ta fita. Wajen wani malamin mami ta kara, shi wannan cewa yayi ta kawo dubu Dari cash taga aiki, rokanshi tayi kan zata kawo  dubu hamsin daga baya ya kawo sauran yaki. Atakaice har daya na rana bata koma gida ba tana yawon gidan malaman mami amma duk inda taje sai an samu matsala amma ko kadan batayi giving up ba, wurin wani data je har cewa yayi zai yi mata aiki amma sai ya fadawa mami nan ma barin wurin tayi, tana tafiya tana hawaye kaman wata zautatta. Gindin wata bushiya ta tsaya ta ajiye bag dinta Sannan ta dauko wayanta ta kira grandma dinta, matar da picking ta fashe da kuka
"Wallahi grandma mutuwa zanyi...sonshi zai kashe ni..." Tafada cikin kuka sosai,
"Ki taho...." Matar ta fada mata atakaice, da sauri tace
"Mami bata barina...."
"Ki kwantar da hankalin ki...zan kirata yanzu...." Inji grandma,
"To shikenan..." Tafada tana kashe wayanta, wani yaro dake yawo da pure water ta kira ta sayi daya tasha sai zufa take kaman wacce aka sa dole 5k da mom ta bata ta kashe abanza wurin transport zuwa gidan malamai.


Ayan na zaune sai kallon agogo kawai yake. 10 minutes to 1 yayi alwallah. Yanajin kiran salla ya fita yabi jami Sannan ya dauki motanshi ya fita. Yusuf da Muhammad sai kallon shi kawai suke suna mamakin irin zaryan da yake haka.
Kofar gidansu wannan budurwan ya tsaya ya kira ta ta fito sanye da after dress amma daga cikin kayan aikin nurse ne. Gaisawa sukayi ya kalleta tare dacewa
"You look gorgeous..." Yafada yana kashe mata ido daya. Murmushin jindadi tayi batace kala ba.
Driving yake amma hankalin shi na kan agogon don he don't want to keep ihsan waiting. Yana zuwa kofar gidanshi yayi horn wannan saurayin dayaje gidansu ne ya bude mashi gate bai shiga da mota ba suka fito da yarinyan, general parlour ya kaita ya kara fada mata exactly abinda yake son tayi, kai kawai ta gyada mashi tana mamakin abinda ke faruwa. Dasauri ya fita ya kama hanyan buk.

Kan hanya ya tsaya ya sayi take away guda biyu da abinsha mara sugar.

Ihsan ta gama lectures tana tsaye tana jiran zuwan shi sai hamma take saboda gajiya, ji take inda batayi wa Ayan alkawarin zata rakashi ba da gida zata straight taci abinci ta kwanta cos she's exhausted. Daga nesa ta hangoshi ta taho, ahankali ta fara takawa cikin kasaita kaman yanda ta saba, Ayan tuki yake ahankali amma hankalin shi na kanta cos she walks like a queen, kawai sai ya tuna video dinta dake cikin wayanshi sai ya hade rai. Kusa daita yayi parking ya fita ya bude mata, gaidashi tayi tana murmushi shima ya amsa yana kallon eyeball dinta at that moment inda ihsan zata nutsu she would have seen something amma Sam bata luraba, shiga tayi ya maida ya rufe ya zagayo ya shiga ya kalli yanda take lumshe idanuwa yace
"Sannu..."
"Yauwa..." Tafada tana ajiye bag dinta gefe tare da gyara Vail dinta dake Neman barin kanta. Ayan kallon gashin kanta dake sheki yayi ya kauda kai cos tunanin wani ya taba ganin wannan kai naked kawai yake. Dan kallon shi tayi Sannan tace
"Baby...why not mu bari next time muje?...wallahi am so tired..." Tafada tana relaxing.
"Ayya.. Sorry.. Amma na Riga na fada mata we're coming.. But tunda you are tired kawai ba sai muje kasuwa ba..kawai Zan bata kudi...ko ya kikace?..."
"Ok then...ina tsoron kar bacci ya dauke ni ne..." Tafada tana hamma,
"Sorry... Relax kafin mu isa..." Y fada mata. Yanda tayi relaxing yasa kirjinta Dan  bankarawo, kallon ta yayi ya kauda kanshi ya cigaba da driving abubuwa da dama suna yi mashi yawo cikin kai.

Quarter to 3 suka iso gidan, horn yayi aka bude mashi,
Ya shiga, ihsan dake zaune kallon compound din tayi taga kaman babu mutane cikin gidan, kalle2 ta zauna yi har yayi parking,
"Baby gidan looks new..." Ta fada, murmushi yayi mata
"Eh is new..." Kallon shi tayi gabanta na faduwa
"How...ba gidan antyn ka bace?.." Yanda tayi maganan yasan she afraid
"Gidanta ne...basu Dade da dawowa ba.." Yafada yana bude motan. Fitowa yayi ya bude mata, ahankali t fido pure white leg dinta dake sanye da toms lemon green kalan kayan ta. Rufewa Ayan yayi ya yi gaba tabi bayan shi, ihsan dai kallon gidan take don ita har yanzu she couldn't believe an taba rayuwa cikin gidan, Kuma tasan gidan haihuwa baa rasa mutane amma nan wayam, Dan ajiyan zuciya ta saki don anata tunanin Ayan will not go this far to do something bad, bakin kofa Ayan ya fara knocking as planned. Few seconds later wata budurwa ta bude da murmushi fuskan ta, tana ganin ihsan ta dan chanza fuska for one to two seconds cis she wasn't expecting to see him with a woman, shi dai kawai fada mata zai zo da mutum Kuma tayi pretending nan gidan ta ne.

Ihsan dadi taji data ga mace yaruwarta dukda she wasn't expecting to see such a young gal tunda Ayan Yafada mata antyshi ce.
"Sannu Ku da zuwa..." Safeena tayi karfin halin cewa, cos tana ganin innocent ihsan jikin ta yayi sanyi, Ayan bata rai yayi daya lura da mood dinta. Hakan yasa tayi saurin sakin jikinta cos he's the boss.
"Ku shigo mana..." Ta fada masu, ahankali suka shiga cikin wagegen falon da ba komai, hanyan part din Ayan safeenat ta nufa as planned tana cewa
"Bisimillan Ku...." Tafada tana bude kofan, ihsan dai murmushi ne kwance kan fuskan ta amma batace kala ba, zama tayi kan wani hadadden sofa shima Ayan ya zauna. Gaisawa suka farayi da ihsan har lokacin kanta kasa bata daga kaiba balle ta kalli face dinta,
"Bari in dauko muku ruwa..." Safeena ta fada tana mikewa, barin dakin tayi after 10 seconds shima Ayan ya mike yana cewa
"Precious... Bari in dauko wayata na mance ta a mota..." Yafada mata,
"Ok..." Ta fada cikin sanyin murya.

Da sauri ya fita ya tarda safeena ta dauko handbag dinta jikinta babu kwari,
"Thanks so much..." Yafada mata, bata iya cewa komai ba cos she believed she has betray her fellow woman, har bakin gate ya rakata ya dauko kudi yan dubu daya2 ya bata ta ki amsa ta tafi. Shi dai maigadi kudi ya bashi ya amsa yayi godiya ya tafi, kulle gate din yayi ya bude motanshi ya dauko takeaways daya saya tare da drinks ya dawo cikin . general falo.
[12/2, 8:25 PM] ‪+234 703 821 5964‬: 💙❤💜🖤💚💛
KAWARTA CE SANADI
💜💙❤🖤💚💛




®zuwairat( ummu Maryam)




3⃣2⃣



 _Wannan shafin naki ne *ummey zeey* , I want you to know that you are unforgettable, I love you wella._




Rufe kofan general parlour yayi batare da ya kulleba cos yasan nobody is coming, hanyan part dinshi yayi rike da takeaway, hannu yasa ya bude kofan, ihsan dake zaune inda ya barta ta daga kai ta kalleshi tare da sakar mashi murmushi amma ko kallon ta baiyiba ya maida kofa ya rufe ya nufi inda dinning take, binshi tayi da kallo ya zauna, sai lokacin ya kalleta
"Zo muci abinci..." Ya fada mata atakaice fuskan shi babu faraa, kai kawai ta girgiza mashi ya tabe baki tare da fara bude abincin, ihsan ganin 2,3,4to 8 minutes antyn Ayan bai dawoba yasa tace
"Baby ina antynka?..." Ayan dake kai abinci bakinshi kallon ta yayi yace
"Ta tafi...." Ya fada mata atakaice, da sauri ihsan tace
"Ban gane ta tafi ba...."
"We are alone... Is just you and me.... Precious..." Yafada yana cin abinci hankalin shi kwance. Bata rai ihsan tayi tana dan dafa kirjinta dake bugawa da karfi tace
"Pls if it is a joke stop it...pls tana ina?..." Ta kara tambayan shi not believing what he said, kara tabe baki yayi Sannan yace
"Who is joking with you?... Nan gidana ne...is all a plan... Wannan shine gidan da da zaa kawoki before I find out you don't worth it..." Yafada yana cin abincin shi, tsoki ihsan taja ta dauki bag dinta ta mike, da sauri Ayan ya kalleta da wani irin kallon da bata San shi dashi ba Sannan yace
"Wallahi if you as much as move an inch...Wanda ke cikin jahannama sai yafi ki jin dadi...." Yafada sounding extra serious amma dayake ihsan is stubborn banza tayi dashi ta fara heading for the door, da sauri ya mike cikin taki biyu ya kamata, wani irin wawan mari ya dauketa dashi tare da tureta kasa. Idanuwa ihsan ta zaro cos komai nata tsayawa yayi cos Marin ya mugun gigitata, nunata yayi da yatsa
"Try moving again and more than this awaits you..." Yafada, har lokacin ihsan bata dawo hayyacinta ba, kan dinning ya koma.
Ahankali ta daga hannun ta ta Dora inda ya mareta ko kadan babu hawaye idanuwanta amma inda zasu zubo mata da zatafi samun sauki, wani kara kunnenta ya dingayi har few seconds Sannan jinta ya dawo, ahankali ta juya ta kalleshi sai lokacin hawaye suka fara gangarowa idonta, ko kallon ta baiyi ba, ahankali fara cewa
"Pls...meye laifina?..." Tafada muryan ta na rawa, murmushin yake yayi ya rufe abincin ya fuskan ce Sannan ya fara cewa
"Bakisan laifi kiba?..." Da sauri ta daga mashi kai, tana hawaye har lokacin hannun ta inda ya mareta,
"Ok..then...when am done with you..... Zakiyi confessing laifinki da bakinki......" Yafada yana mikewa, kuka ta farayi tana komawa baya, da sauri ta fara cewa
"Pls ...ko me nayi maka ka yafemin....pls don't hurt me..." Ta fada tana ja da baya shi Kuma yana nufota,
"Ba hurting dinki zanyiba....kawai I want to swim in you the way those guys are swimming in you...." Yafada yana daga ta tsaye, ihu ta saki ya sa hannun shi ya bige mata baki,
"I don't want to hear a word from you... Stop this pretending...." Da sauri ta sa hannun ta ta kama bakinta
 Tashin hankali bai barta ta gane inda maganar shi ta dosa  ba, kuka ta farayi sosai tana cewa
"I beg you... Pls don't ruin me..." Bata idaba Ayan ya kwace da dariya yana cewa
"Did I hear you say ruin?...well ni kika yi ruining, cos I loved you fiye da yanda nake son kaina...I was ready to give all I have just to make you happy... Ihsan kin cuceni....kin yaudareni....I don't know you could be a slut...." Sai lokacin ihsan ta gane zargin da yake yi mata, idanuwa ta lumshe wasu zafafan tears suka zubo, ahankali tayi kneeling gabanshi,
"Pls....pls....am not a slut....kill me if you want... Amma pls dont...call me a slut...." Tafada cikin kuka sosai,  Ayan kura mata ido yayi sai ya fara hawaye, he wish she saying the truth amma yana da enough evidence to show that she's a slut, murmushi yayi ya goge hawayen shi yana cewa
"I will make sure you never longs for any man...zanyi maki abinda babu Wanda ya taba yi maki...." Jikin ta ne ya fara rawa, tana yarfe hannuwanta tana cewa
"Daman this is what you have always wanted from me....daman abinda kakeso kenan...pls ka tausayawa rayuwata....", dariya yayi yana cewa
" drama queen..., ban taba zinaba...sai yau zan fara so kisan duk halin dana shiga daga yau is as a result of you deciet..." Yafada sannan ya Daga ta tsaye
"Kizo in nuna maki what you missed..." Yafada yana Jan hannun ta da karfi
 Kara ta saki saboda zafin hannun ta daya rike, janta ya farayi har zuwa main falo ihsan sai ihu take tana
"Dan Allah kar kyaleni...Wallahi am not a slut..." Ayan dake hawaye saboda bakin ciki don ji yake kaman yanzu ya fara ganin wannan video, main falo ya jata Sannan ya fara cewa
"Look... I was planning to be happy with you..." Yafada itadai batace kala ba sai kuka, hanyan daya part din yayi har lokacin yana janta, sakin jikinta tayi ta fadi kasa amma bai saki hannun ta ba yacigaba da janta, yana bude kofan ya wullata cikin falon dake kaman nashi saidai babu kaya ciki, yana wullata ta fadi kasa ta kife kasa
"This would have been your apartment..." Yafada yana kallon yanda take kuka kaman ana zare mata rai,
"Kuma the wedding is off...amma abun mamaki har yanzu I love you..." Yafada yana goge hawayen fuskan shi, nufota yayi
"Why did you play with my heart... Why do you toy with me?..." Ihsan ja take da baya tana cewa
"Pls kayi hakuri.... "
"Ihsan I was threatened... Amma ban fasa ba...I was warned still ban fasa ba...that's is to tell you I deeply love you... Amma..." Yayi shuru yana hada ta da bango da karfi, wani razanannen kara ta saki saboda yanda bayanta ya bugu, Dan ne ta yayi ya daga riganta ya kama boobs dinta da karfi, ihu ta dingayi
"Are you enjoying it?..." Ya daga mata tsawa, da sauri ta girgiza mashi kai tana haki hawaye na sharara,
"Pls stop...you ...are hurting... Me..." Tafada cikin kuka mai tsanani, kara chakumo su yayi cikin zalunci ta kara kwala ihu, cikin tsiwa tace
"Koni karuwa ce...ka rabu dani...." Dagata yayi ya kara dauke ta da mari, ahankali tayi baya numfashin ta na neman daukewa,
"Bazan rabu dake ba...I will deal with you more than you do to me...." Ihsan kwantawa tayi kasa saboda yanda kanta ke zafi da ciwo, binta yayi kasa yasa hannu ya fara kokarin cire mata Riga, dukda bata da karfi rike riganta tayi gam,
"Bazaki sakiba sai na shake ki?..." Yafada da karfi, Ahankali ta gyada mashi kai tana kallon eyeball dinshi,
"Just kill me....pls ka kasheni...amma in dai ina raye...I will not have what you want...." Tafada cikin dakekken murya.
"Ok..then..." Yafada ya mikewa, buttons din riganshi yafara balle wa, ihsan tana nan kwance tana duk aduan dayazo zuciyanta, kura mashi ido tayi tana kallon yanda idanuwanshi suka sauya kaman ba Ayan dake zuwa gidan su looking nice and cool ba, yana gama ya wurgar da riga ya cire three quarter dake  jikinshi, da sauri ihsan ta runtse idanuwanta, daga shi sai singlet da boxer, duka wa yayi ya dauke nan ta fara yaginshi da fingernails dinta dama tana ajiye su, nan take ya saketa kasa ji kake timm, wani kara ihsan ta saki tana kama kanta da hannuwanta biyu saboda azaba,
"Wayyo Allah...nashiga uku....I cursed the day I meet you..." Ta fada tana nishi, Ayan kallon chest dinshi data yaga yayi yaga ta ji mashi ciwo, hannun ta ya kama ya fara janta nan kasa.
"Nima I cursed the day I meet you bitch Yafada yana janta, sakin jikinta kawai tayi ya dinga janta har general falo, sakinta yayi ya zauna koma ya zauna gabanta yana kallon ta, itama daga idanuwanta tayi ta kura mashi ido hawaye na zauna,
" ihsan...who is the guy?..." Ya tambayeta, bakinta sai kyarma yake amma ta kasa magana, ahankali ta daga hannuwanta ta rike kanta gam, jiri kawai take gani,
"Ihsan who is the person you are sharing your beautiful body with?...." Ya sake tambayan ta, kura mashi ido tayi ko kiftawa bata yi, wani irin kallon tsana da kiyayya take mashi,
"I loved you....ina kaunan ki ihsan....I adore you..." Yafada yana kara mikewa, daukanta yayi ahankali tace
"In har ka taba jin kwayan zarran sona cikin ranka....pls...let me...go...." Ta rokeshi, banza yayi daita yacigaba da tafiya, kofan part dinshi ya bude ya shiga falon ya kara shiga daya daga cikin dakin kan gadon ya wullata, da sauri ta mike zaune tare da sauka daga kan gado
"Halima...hau kan gadon nan da kanki..." Ya umarceta, makalewa tayi cikin bango tana kuka
 Inda take tsaya ya nufa ya manna ta jikin bango ya fara rough play daita sai kuka take tana bashi hakuri amma a banza, kara daga riganta yayi ya sa bakinshi kan boobs dinta ya fara bad play daita Kuma not in a romantic way but in a wicked way, ihu kawai take, kara daukanta yayi ya kaita kan gado wannan Karin ko karfin daga kanta bata dashi, kwantawa kawai tayi tana kallon yanda yake kokarin rabata da kayan jikinta, daga idanuwanta da sukayi mata nauyi tayi ta kalleshi, ahankali ta daga hannun ta ta tabashi, tsayawa yayi yana kallon ta, da kyar ta bude bakinta ta fara cewa
"Pls...in ka ....samu...abinda ...kake...nema...just.. Kill...me..." Ayan daya fita hayyacinshi tabe baki yayi
"Wasu basu kasheki ba sai ni?...sai dai in na ajiyeki kofar gidanku ki kashe kanki saboda Dan unguwan Ku yayi screwing dinki...pretender..." Yafada babu alaman tausayinta tattare dashi.




Safeena kam tana tafiya tana tuntube cos duk hankalin ta na kan halin da su Ayan ke shiki, bata hau abun hawa ba cos gidan is not far from the hospital, tana shiga cikin hospital ta kusa pumping into Muhammad dake fitowa daga dakin wani patient, ko daga kai batayi ba ta wuce shi cos ko kadan bata cikin mind dinta,
"Safeena... Lafiya dai..yau ba magana Kuma you came late...." Ya tambayeta cos yasan she a nice lady, ahankali ta daga kanta
"Lafiya lau..." Yafada cikin sanyin murya Sannan ta wuce shi, shima juyawa yayi ya tafi office dinshi ita Kuma ta tafi inda  wurin signing, kasa rubuta sunan ta tayi ta dawo office din Muhammad da sauri, shima da sauri ya daga kai  don yanda ta shigo ya nuna da akwai matsala,
"Lafiya safeena?.. Nasan da akwai matsala... Pls share it with me..."Kaman tana jira sai ta fashe da kuka tafara fadawa Muhammad abinda ya faru tsakanin ta da Ayan yau, da sauri Muhammad ya mike yana cewa
" ya yarinyan take?...." Description din ihsan ta bashi,
"Inna lillahi waina ilaihi rajuun...." Muhammad ya dinga maimaitawa yana fita daga office din. Da gudu2 ya shiga office din Yusuf, nan ya fadawa Yusuf abinda safeena ta fada mashi,
"To ya zamuyi?...is his life..he should live it the way he like..." Yusuf dake fushi da Ayan ya fadawa Muhammad atakaice, da sauri Muhammad yace
"Don't say that... He's our friend...something is wrong somewhere... And remember poor ihsan...kasan yanda Ayan yake when he's mad...pls muje kafin something bad happens... Pls ... Lets not allow him do something that will ruin our good name don kasan cewa ake abokin barawo barawone..." Yafada mashi, Ahankali ya dauki car keys din shi ya mike, da sauri suka shiga mota dukda sun San ko a kafa suna Iya zuwa amma da gudu suka toho, daman tsakanin gidan zuwa hospital baifi gidaje 35 zuwa 40 ba ko minti 7 basuyi ba suka isa gidan, da sauri suka fito suka taba gate din amma a rufe, motan suka kawo daf da gidan Muhammad ya hau kan motan Sannan ya hau bangon Allah ya bashi saa ya dire cikin gidan, da sauri ya budewa Yusuf kofa, nan waje suka bar motan su shiga falon cos kofan bude take, tun falo suka fara jin ihun ihsan cikin wahala da galabaita, Yusuf ji yayi legs dinshi basu daukan shi, nan ya sulale ya zauna ya fara kuka
💚💛💛💙💜


Yau Ayan zakaci ubanka hannu masoyan ihsan nidai babu ruwana 🏃🏾‍♀🏃🏾‍♀🏃🏾‍♀🏃🏾‍♀
[12/2, 8:25 PM] ‪+234 703 821 5964‬: ❤💛💜🖤💙💚
KAWARTA CE SANADI
💜💙💚🖤💛❤



®zuwairat(ummu Maryam)





3⃣3⃣



 _My dear *Khaleesat hydar* wannan shafin naki ne, I want you to know in jinki har cikin raina, I love from the bottom of my heart._




Muhammad tsayawa yayi yana fargaban bude kofan cis baisan abinda zai tarda ba,
"Wayyo Allah na....kayi hakuri... Pls..." Yaji ihsan na cewa Kuma yanda take magana ya tabbatar masu in baa kawo dauki ba tana iya mutuwa cos maganan ta kaman ba nata ba, Yusuf dake zaune ne ya mike afusace ya bude kofan, falo suka shiga inda ihun ihsan na kara karfi da gudu ya bude kofan da yake jin muryan ihsan daga cikin,
"Subhanallahi!!!...." Ya fada da karfi ganin ihsan dungule waje daya kan gado shi Kuma Ayan yana kokarin cire mata kayanta Kuma yayi nasaran cire mata hannun ta daya daga cikin rigan, Allah ya taimaketa kayan datasa suna da manyan stones a wuya da jikin shi da tuni ya yage kayan, afusace Ayan ya juyo jin muryan Yusuf, ahankali shima ya shigo ya kalli ihsan dake dukunkune kaman mai jin sanyi sai kyarma take,
"Ubanwa ya ce Ku shigo min gida!..." Ya fada cikin irin muryan da basu sanshi dashi ba, mikewa yayi daga kan gadon ya sauka kasa ya nufo su afusace, Yusuf da Muhammad kallon juna sukayi don tamkar ba Ayan ba, idanuwanshi sun chanza kala. Yana zuwa wurin Yusuf ya daga hannu aikam bai ankaraba yaji Muhammad ya sakar mashi wani irin wawayan naushi a hanci, nan take yayi baya2 yana daf nose dinshi kafa Yusuf yasa mashi ya fadi nan suka tarar mashi da naushi, kokarin mikewa yake amma ance karfin yawa yafi sarki power. Ihsan kam da sauran karfin da ya rage mata ta maida hannun riganta daya cire, kokarin tashi tayi sai taji bata iyawa saboda duk joint dinta ciwo yake mata mussanman boobs dinta da takeji kaman zasu tsinke saboda yanda Ayan ya dinga yi masu full of wickedness, duk abinda su Muhammad kewa Ayan bai dame shi sai dayaga ihsan tana kokarin tashi ya mike, kamashi su Yusuf sukayi amma kokarin kwacewa yake don ya tafi wurin ihsan, bakinshi sai jini yake amma ya rufe ido dole shi zashi wurin ihsan
"Shame on you!..." Yusuf ya fada cikin kuka,
"Wallahi wallahi wallahi kuka bari wannan yarinyan ta bar gidan nan....I will reap all of you apart..." Yafada cikin gurnani kaman wani lion, ihsan najin abinda yace tayi kokari ta mike, kallon ta sukayi Yusuf yakara fashewa da kuka cos shi mutum ne mai tausayi dukda he's stubborn, duk ta koma kama ba itaba dukkan face dinta yayi ja, sai haki take,
"Go back to the bed!..." Ya daka mata tsawa, ihsan ko kallon inda yake batayiba ta sauka kasa
"We're so sorry..." Muhammad Yafada,
"Sorry my ass...." Ayan da suka rike ya fada  da karfi,
"Where is the love you always claim you have for her?....we are disappointed in you..." Yusuf ya fada mashi,
"I don't care....she's a whore....Kuma wallahi ban aurenki...and sai na samu abinda nakeso ki ba yauba....." Yafada yana kokarin kwacewa daga rikon da sukayi mashi,
"Ubanwa yace dole sai ka aureta?...if you can't marry her you let her be...." Muhammad ya fada mashi,
 "No!...she played with my heart... She toy with me...zan nunamata  ba kowanne namiji akaewa wasa da zuciya ba...Ku sakeni...." Ya fada cikin ihu Kuma yana hawaye,
"Pls stop this..." Muhammad ya fada yana kara rikeshi sosai don kokarin kwacewa yake, ihsan dai ahankali ta fara takawa tana tafiya kaman mai jin sanyi, tana dafa bayanta dake mata ciwo, Ayan gani yayi da gaske fita zatayi yayi kukan kura ya kwace daga rikonsu, kafin su kama shi ya kama ihsan, wani kara ta karayi, rungume tayi yayi ta baya ya matse mata ciki sosai, Yusuf da Muhammad rikeshi sukayi suna kokarin kwace hannun shi daga jikinta amma ina
"Kai kasheta zakayi?..." Muhammad ya tambayeshi cikin tashin hankali, ihsan kam daura hannun ta tayi kan nashi, numfashi ta na Neman daukewa, Sakin jikin ta tayi, da kyar suka cire hannun shi daga nashi, yake jiki tayi ta fadi kasa tana
"Pls...Ku bari ..kawai ya karasani.....Ku tafi ya ida nufin shi kaina...." Tafada tana haki,  cikin kuka ya fara cewa
"Wallahi sai nayi ruining dinki....you destroy my life and I must destroy you... Ke kin yi kadan ki kashe min zuciya in kyale ki,..." Yafada yana kuka, har lokacin bakinshi da Muhammad ya nausa bai bar jini ba, ihsan kwantawa tayi nan kasa bata tashi ba cos at that moment she has given up on life, kawai she prefer to die,
"Pls...come and kill me...." Tafada cikin kuka,
"Don't worry... Bazan kasheki ba... Amma I will make sure you never cheat on any man again..." Yafada yana kuka shima,
"Pls Ku bar wannan maganan hakan nan...kiyi hakuri.. Duk abinda ya faru sharrin shaidan ne..." Inji Muhammad,
"No... Ba sharri shaidan bane...she caused it...wallahi ina nan ina sonta don Allah... Ita stupid.. Filthy.... Slut tana chan ta fucking wani..." Ihsan kara fashewa tayi da kuka tana imagining why is Ayan telling her  such horrible words
"And so what?...dole akayi ma?...if you can't you quit..." Yusuf ya fada cikin fada, shima Ayan cikin ihu yace
"I won't until am done with her..."
"To bisimillah..." Yusuf Yafada mashi, ahankali ihsan ta kara mikewa tayi juyo ta kalli Ayan da suka rike gam tace
"Why are ...you spoiling ...my name...why?..." Tafada cikin kuka sosai, baki Ayan tabe tare dacewa
"Ki tambayi saurayin ki ya fada maki abinda ya turo mani...ask him cos he's the one that betrays you not me..." Yafada cikin kuka
"Allah yaisa tsakanina dake...you have hurt me beyond words... Wallahi I will not marry you..." Inji Ayan cikin kuka, ihsan dan girgiza kai tayi
"Daman ko Kaine autan maza.....gara inbi duniya da in aueeka...." Itama ta fada ciki kuka
"Daman ke yar duniyar ce...Kuma ki bar ganin wayan nan wawayen sun rike ni...ko ba yauba sai nayi maki abinda bazaki kara shaawan namiji ba...." Yafada
"Haba Ayan... In rai ya baci ai hankali bai gucewa...ina iliminka....ina addinin ka?...ina trabiyan ka?...Wallahi ba haka kake ba...." Inji Muhammad, bai idaba Ayan ya ce
"She made me the way you see me...her love is destroying me...wallahi wannan yarinyan ta cuceni...she deceived me...." Yafada cikin kuka sosai, har lokacin bai bar kokarin kwacewa daga rikon da akayi mashi ba, ahankali ihsan ta mike ta fita daga dakin, Yusuf nason zuwa ya dauke ta amma yasan muddin suka saki Ayan babu abinda zai hanashi kamata, "wallahi Ku sakeni kar ta tafi...." Yafada yana kallon ihsan data kusa fita daga dakin
Kara rikeshi sukayi har singlet dake jikin shi yayi tearing amma bai bar kokarin kwacewa ba, saliva din bakin dake hade da jini ya zubda ya kalli Yusuf yace
"Wallahi muddin wancan yarinyan ta tafi ban ciwa burina ba...sai na ragargaza rayuwa tasnem..." Ya fadawa Yusuf Sannan ya kalli Muhammad dake shake dashi yace
"In har baku sakeni ba...if she leaves this house unscrewed by me...wallahi babu abinda zai hana dalla dalla da rukayya..." Yafada yana kuka,
"Don Allah calm down... You are better than this..." Muhammad ya fada mashi cikin kwantar da murya,
"No...baku San abinda tayi ba....that bitch allows her bastard boyfriend send me her nude pic with her video in shower...can you believe that?..." Yafada cikin kuka kaman ranshi zai fita, Yusuf da Muhammad kallon juna sukayi, ahankali Yusuf yace
"An auri karuwa dake zaune a hotel balle wacce ka zaune a gidan iyayenta?... Kawai that does not justify your action... You are nothing better than her now..." Inji Yusuf, kafa Ayan yasa ya harbeshi,
"Wallahi kilan sharri akayi mata....you should have investigate...." Muhammad ya fada, kai ya daga ya watsa mashi harara yana cewa
"You guys are dump ass...wane investigation zanyi ga zahiri?..what haven't I done?...kunsha ganina ina kuka saboda ita...I loved her so much but she betrayed me..." Kuka ne yaci karfin shi yayi shuru Sannan yacigaba dacewa
"Her love and charm have ruin my perfect life... Na tsani kaina...I hate life...ta gama dani...Wallahi bazan yafe mata..." Yafada cikin ihu yana hawaye.


Ihsan zama tayi kan daya daga cikin kujeran tana kuka tana hawaye, gani taje bazata kara tsanan mutum kaman yanda ta tsani Ayan ba, tana zaune tana sauraron abinda yake fadawa su Muhammad, ko kadan bata yarda da gaske yake ba kawai ta dauka yana yi mata sharri ne kawai, ahankali ta gama saka toms dinta ta tashi da kyar ta dauki gyalenta tare da bag, ko yafa shi batayi na ta fara tafiya har lokacin tana jin Ayan nacewa
"Ta cuceni!!!!..." Fita tayi daga wanna falon ta shiga babban falo tana tafiya ahankali tana hawaye, tunani take daman haka namiji suke, ita ba Ayan kawai ta tsana ba, she hates all men, sai shessheka take.

Ayan kwantawa yayi kasa yacigaba da kuka kaman zai mutu zuciyanshi sai bugawa yake da karfi, sakin shi sukayi yacigaba da kuka, Muhammad shafa bayanshi ya dingayi. Ganin bai mikebayasa Yusuf barin dakin da sauri, bakin gate ya hangi ihsan tana tafiya ahankali tana yafa Vail dinta, da sauri ya karaso gurin ta
"Kiyi hakuri.. Duk abinda zaiyi kyau sai ya fara samun matsala...pls kiyi yafe mashi kar ki fadawa kowa wannan maganan cos abun kunya ne..." Yafada mata, ihsan dai kuka kawai take bata daga kanta ba, da sauri ya wuceta ya bude mata mota, bata shiga ba ta cigaba da tafiya ahankali
"Pls ki shiga in kaiki hospital..in baki drugs you must be feeling sore..." Ya fada mata. Bata daga kanta ba ta girgiza mashi kai kawai,
"Pls...in kinawa Allah ki shiga..."  Yafa yana rokanta, amma bata kara cewa komai ba tacigaba da tafiya amma hawayen ta basu tsaya ba
 Da kyar Yusuf ya shawo kanta ta shiga mota ya tafi hospital daita, tambayan ta yayi ko taci abinci amma bata amsaba sai hawaye take da gani Kuma hankalin ta bai jikinta.parking yayi ya barta nan cikin mota ya shiga office dinshi ya hada cool tea tare da drugs ya kawo mata, Maganin ta amsa tasha da tea Sannan ta maida mashi sauran tea din. Maidawa yayi office dinshi Sannan ya fito yaci karo da safeena, da sauri yace
"Safeena.. Mun gode...Allah saka da alkhairi, .." Sannan ya fita ya shiga mota, hanyan gidansu amma ta fada mashi ba gida zata ba, tambayan ta sunan unguwan da zata yayi ta bashi sunan unguwan su husna, ahankali ta bude bag dinta ta dauko wayanta, ganin tayi 10 minutes after 5 Sannan ga miss call din mom guda uku, hanki ta dauko ta goge hawayen ta tayi dailing number mom, ringing biyu mom ta amsa
"Wai ina kika ajiye wayanki ne?.." Mom ta fada cikin fada, daidaita muryan ta tayi Sannan tace
"Cikin bag dina..."
"Ya akayi baki dawo gida ba har yanzu?.. Ko baki baro kasuwan ba?.." Mom ta tambayeta, shuru tayi for a while Sannan tace
"Yanzu ina kan hanya amma gidansu husna zani tukunna..."
"Baki gani dare na gabatowa?...ki yi sauri ki dawo gida..." Mom ta umarceta,
"Ok..." Ta fada har zata katse wayan mom tace
"Ya akayi muryan ki ya shake kaman kinyi kuka?.." Da sauri ta ce
"Mom mura ne ya kamani yanzu nan..."
"To kiyi sauri...zansa inna ta dafa maki pepper soup kafin ta tafi..."
"Ok mom..." Ta fada Sannan ta kashe wayanta, wasu new tears na rolling idanuwanta.


Ayan mikewa yayi ya cire singlet dinshi da su Muhammad suka yaga ya wurgar Sannan ya fita daga dakin, Muhammad sai binshi yake a baya bangaren daya cire kayanshi ya shiga ya dauko three quarters dinshi tare da rigan ya saka ya koma part dinshi ya dauko car keys daga kan dinning ya fito da sauri Muhammad ma binshi yayi yana cewa
"Kayi relaxing nan..duk Wanda ya ganka yanzu yasan da akwai problem.. You face is swollen.." Ya fada mashi, ko kallon shi baiyi ba ya shiga cikin mota ya figeta ya bar wurin, ko kulle doors din baiyi ba. Direct hospital ya nufa yana shiga cikin ya fara kiran safeena da karfi, da sauri ta taho gabanta na faduwa,
"You are fired..get out of my hospital before I do something stupid..." Ya daka mata tsawa, baki kawai ta tabe ta bar wajen.

💚💛❤🖤💙💜
KAWARTA CE SANADI
💚💛💙🖤💜❤



®zuwairat(ummu Maryam)




3⃣4⃣




 _My sweet *hajjace* wannan shafin is dedicated to you, Allah ya bar zumunci ya kara tsarewa_





Office dinshi ya shiga direct bathroom ya shiga ya wanke bakinshi yaga har lokacin da akwai jini bakinshi, tsayawa yayi yana kallon kanshi cikin mirror dake jikin bango, shi kanshi yayi mamakin yanda ya koma tamkar ba shiba
"Look at what you did to me..." Yafada yana hawaye, ruwa yasa ya wanke fuskan shi tare da dauro alwallah ya fito, nan office dinshi yayi sallan ya zauna kan praying mat yana aduan Allah ya cire mashi son ihsan cikin zuciyanshi, yana aduan Allah ya mantar dashi ihsan don ko kadan he don't want her but his heart is telling him something else. Hada kai da gwaiwa yayi ya dinga kuka zuciyanshi na harbawa da karfi. Ji yayi andora hannu kan shoulder dinshi ahankali ya daga kanshi  ya kalli Muhammad dake Neman zama, daure wet face dinshi yayi ya ture hannun shi daga shoulder dinshi,
"Get out of my office..." Yafada babu wasa, banza yayi ya zauna nan kasa ya fara cewa
"Guy abinda kayi yau is very bad...gaskiya you own ihsan an apologies...." Wani irin mugun kallo Ayan yayi mashi
 Yacigaba da kuka kaman maraya,
"You need to calm this temper of yours...assuming bamu zo da wuri ba da kayi babban kuskure...dakayi abinda zaiyi hunting dinka for the rest of your life..." Afusace Ayan yace
"It will never hunt me...because she deserves it.. " ahankali Muhammad yace
"What if she's innocent.... Da wane ido zaka kalleta bayan ka ci mata mutunci?.."
"Da na dinga crawling bayanta har sai ta yafemin.. Da sai na nemo Wanda ya turo min wannan pic da video na aika dashi lahira koda kuwa nima zaa kashe ni...." Yafada cikin kuka, kara dafa shoulder shi Muhammad yayi
"Kayi hakuri.. Ka barwa Allah komai... Indai Allah ya kaddara ihsan ce uwar yayanka nothing will stop it...not even if she's a porn actress..." Kai Ayan ya girgiza yana cewa
"I can't...ina kishin duk abinda nake so...bazan Iya aurenta ba...wallahi in na aureta it will hunt me...kawai Allah ya zabawa kowa Wanda ya dace amma I can't be with her..." Yafada yana kuka, Muhammad patting dinshi ya dingayi shi Kuma yana kuka kaman wani karamin yaro.


Har suka isa gidansu husna bata bar hawaye ba shima Yusuf hakuri ya dinga bata yana rarrashin ta kan halin Ayan Sannan Kuma yana shaida mata Ayan bazai taba  jin wata duniya kaman yanda yake sonta ba,
"Duk abubuwan da yayi maki duk cikin sone..." Yusuf ya fada mata yana murmushi, ihsan kam cewa take inda zai bude zuciyanta yaga yanda ya koma da ko kadan ba zai furta sunan Ayan inda take ba.
Parking yayi kofar gidansu husna ta fito shi Kuma ya koma, tana shiga falo taci saa ba kowa da gudu ta shiga dakin husna, kwance ta tarda husna ta kafe kai da pillow, kuka ihsan ta fashe dashi Wanda yasa husna daga kanta ihsan taga fuskanta jike sharkaf da hawaye, da sauri ta mike zaune tana goge fuskan ta,
"Babe lafiya kuki kuka?..." Dake mamakin kukan da take ta tambayeta, murmushin karfin hali husna tayi Sannan tace
"Mestral pain..." Tafada tana kallon fuskan ihsan, da sauri ta rike face dinta tana kallon yanda fuskan ta yayi ja
"Babe what happened to you?..." Ta tambayeta sounding tensed but deep inside she waiting to hear good news, ihsan fadawa tayi jikin ta tana kara fashewa da sabon kuka,
"Is Ayan..."
"What about him..." Ta tambayeta,
"He's a monster....he  tries to rape me..." Da sauri husna ta dafe chest dinta saboda kishi da haushi,
"What!!!..." Ihsan kara volume din kukanta tayi tana cewa
"Wannan bai bani haushi kaman yanda yake kirana karuwa ba...." Cikin kuka ta nuna kanta tan cewa
"Wai ni ...karuwa....he calls me a bitch.... Slut...filthy... Dukni kadai...pls tell me friend ina kama da karuwa?...do I look like a whore?..." Kuka ne yaci karfin ta ta dafe kanta
"Yes!...yes!!!!..finally...." Husna ta dinga maimaitawa cikin ranta, azahiri ta fashe da kuka tana cewa
"Daman that guy never loves you..."
"He said saurayina ya turo mashi nude pic da video dina....Imagining me naked in another man's shower... Ayan yaci Mun mutunci... He slapped me over and over again... Menene laifina...menayi....who is behind my happiness... Indai somebody is doing this to me that person will never find peace... Yanda na ke kuka ya rabbi yasa mutumin yayi fiye dani...yanda akayi SANADI wahalata sai ya fini wahalaa..." Tafada cikin matsanacin kuka, husna rike ta tayi ranta kwal
"Haba babe ...kin manta da kaddara?... Kar yanayin da kike ciki yasa ki manta da kaddara... Kawai Ayan mugune... Babu wani nude pic da video... Ko ya nuna maki?..." Ahankali ihsan ta girgiza mata kai
 "You see...kawai he is making it up don ya bata maki suna..." Tsaya kallon ihsan dake kuka kaman ranta zai fita tayi
"Babe did he succeed.." Kai ihsan ta kara girgiza mata tana cewa
"Babu irin zalunci da baiyi min ba...ya jani kasa...yaja kashina...in ba don Allah yasa friends dinshi sun zoba....by now da yayi disvirgining dina....I don't know what is wrong with me....duk suitor dina guduwa suke and the last one tries to rape....wallahi ban aure...zan zauna gidanmu har Allah ya dauke raina..." Ta fada cikin matsanacin kuka, husna rungume ta tayi Wanda yasa ihsan cewa
"Wassshhh...." Dasauri husna ta kalleta
"Menene?..." Boobs dinta ta nuna
"Ciwo suke yi min...." Tafada cikin shessheka., husna bata rai tayi tana tunanin yanzu Ayan ya taba jikin ihsan kawai sai taji wani irin kishi,
"Daman na fada maki bashi da mutunci... Ji yanda yake CI min mutunci agabanki AI ba haka sauran samarin ki suke ba...ni yanzu tausayin ki nakeji in har anyi auren..." Ta fada don jin abinda ihsan zata ce, da sauri ihsan ta kalleta
"Wallahi ko shine autan maza...bazan aure shi ba...babu Wanda zai Iya sanin how dangerous Ayan is...nayi experiencing violence dinshi ...duk macen da zai aura is in trouble..."
"Hmmm...finally... Alhamdulillah... Yanzu son Ayan kawai zan nema...." Husna ta fada cikin ranta, ihsan tace
"Ni yanzu ban San yanda zan fada masu dad ba....ban Iya fada masu yaso raping dinta..." Da sauri husna tace
"Ai ya zama dole...ki fada masu..."
"No I can't..."
"Why..." Ta tambayeta tana hararan ta
"Cos am ashamed of myself... Kinsan ban fadawa mom zan bishi wani waje ba....nidai gaskiya I can't tell them the truth... Kawai zan fada masu banason shi...ko dayake shima yace ta fasa so ko ni ban fadi ba shi zai fadi..." Husna lumshe idanuwa tayi saboda murna, ihsan tana kuka har aka kira sallan magrib sai lokacin tayi alwallah tayi sallan asar da magrib, jikin ta kam tamkar tayi accident saboda yanda each and every joint nata yake mata ciwo. Sai datayi salla Sannan ta mike da kyar tana cewa
"Babe zan tafi...Allah yasa kar mom ta gane wani abu ya faru..." Tafada husna Vail ta dauko suka fito falo
"Wai ina mami?.."
"Tana unguwa...tun dazun na tafi..."

Haka husna ta rakota har ta hau abun hawa tana goge hawaye saboda bakin ciki abinda ya sameta, ita ba kukan mari ko wani abu take ba illa kukan sunayen da Ayan ya dinga kiranta dasu. Husna kam da gudu ta shiga gidansu ta kunna waya ta fara kwasan shakiti bobo saboda farin ciki.


Tana isa street dinsu ta hangi motan Ayan tsaye gefen titi kusa da masjid, wani irin kallo tayi wa motan kaman shine Ayan din.

Tana zuwa gida ta tarda su mom da sauran siblings dinta a falo, yafa Vail dinta tayi yanda bazasu ga face dinta ba  gaida mom tayi mom ta amsa mata bata kalleta ba, hanyan stairs tayi
"Wai wane irin iskanci nae zaki rufe fuskan ki, da sauri ta bude amma bata tsaya ba ta shiga dakinta, gaban mirror ta tsaya tana kallon kanta tana hawaye.


Atakaice dai aranar babu Wanda yayi bacci cikin su, Ayan kwana yayi yana kuka likewise ihsan da kyar bacci ya dauketa shikam ko bacci baiyi ba har garin Allah ya waye, husna ma batayi bacci ba amma ita over joy ne ya hanata bacci sai tsalle2 take saboda farin ciki
Da safe Ayan ya tashi yayi sallah yayi wanka ya sanya jallabiya cos bai da niyyan zuwa aiki. Part din Umma yaje ya gaida ta amsa sam babu walwala fuskanta daman tunda taga ihsan ta fita daga gidan ta fita harkanshi, yanzu ko yanason yayi mata magana bai iyawa saboda yanda take hada rai, zama yayi amma ko kallon inda yake batayi ba, idanuwanshi sun kumbura ga rama dayayi amma dayake bata kallon shi bata saniba, antymu ce ta sauko falon ta ganshi, wurin shi taje ta zauna kusa dashi tana kallon face dinshi, ahankali ta dauki hannun ta ta dora gefen bakinshi dake kumbure har lokacin
"Yaya what happens to you?..." Tafada kaman zatayi kuka, hannun ta dake kan bakinshi ya rike yana murmushin karfin hali
" ya akayi ne sweetheart... "
"Yaya...bakinka is swollen... Idanuwanka sun kumbura..." Umma dake jinsu banza tayi kaman bataji abinda suke cewa ba,
"Ba komai..." Kai ta fara girgizawa ta juyo ta kalli Umma,
"Umma kalli bakin yayi..." Da sauri ya riketa yana cewa
"Ki bar fadawa Umma... Yanzu bata sona..." Ya fada, Umma daga kai tayi fuskan ta daure
"Tashi ka bani wuri..." Ta daka mashi tsawa,
"No Umma... Inason muyi magana..." Yafada cikin sanyin murya, Umma kura mashi ido tayi tana mamakin abinda yasa ya koma haka, amma dayake zuciya gareta sai cewa tayi
"Nace ka tashi ka bani wuri..." Hawaye ne suka fara taruwa idanuwanshi
"Wai Umma me nayi maki...kin juya min baya now that I need you most... Wallahi ban tashi sai na fada maki abinda ke damuna ..." Yafada hawayen na idda gangarowa,
"To bazaka tashi ba kenan..." Umma ta tambayeshi, shuru yayi yana goge hawayen shi, antymu kam fashewa tayi da kuka ganin he beloved elder brother is crying, Umma mikewa tayi tana cewa
"Na bar maku falon...." Tafada ta hau upstairs abinta, Ayan goge wa antymu hawaye yayi ya mike ya fita, part din Abba yaje yayi sallama ya shiga Abba na zaune ya zauna nan kasa, daman sun gaisa so Abba kallon shi yayi yace
"Dafatan babu wata matsala..." Abba ya tambayeshi, kanshi kasa yace
"Abba... I have something to tell you and Umma..." Yafada muryan shi na rawa
"Ok...kaje ka kira ummanka..." Abba ya fada mashi
"Abba.. Ko naje bata kulani...bansan abinda nayi mata ba..." Abba bai kara cewa komai ba ya dauki wayanshi ya kira Umma kan tazo yana son ganinta



Itama ihsan tana tashi taga iskana daukan ta saboda rabonta da abinci tun tea datasha hospital, salla tayi ta fito falo,  [12/27, 14:09] ‪+234 814 199 1000‬: 💚💜💛🖤❤💙
KAWARTA CE SANADI
💛❤💚🖤💙💜



®zuwairat(ummu Maryam)




3⃣6⃣




 _Wannan shafin na kine *Hauwa* you are the best among all my group admins, Allah ya barmin ke Kuma ko gobe ki cigaba da fidda duk marasa magana ehe INA bayanki 100%_  😉



Da sauri ya bar gidan ya kaman hanyan gidan kakar shi, kofar wani medium house yayi horn aka bude mashi gate, parking yayi cikin gidan ya fito maigadi sai gaidashi yake amma sauri ya hanashi ji balle amsawa, cikin falon yashiga ko sallama babu Hajiya dake zaune wata yarinya tana gyara mata alaiyahu ita Kuma tana yankawa cikin wata medium bowl ta daga kai ta kalleshi tare dacewa
"Amma jakkanshin ka yayi yawa...yanzu ko sallama baka Iya yi ko?.." Tafada cikin tsiwa, Ayan komawa baya yayi tare da yin sallama don yasan halin Hajiya tana Iya koranshi amma dayake yasan shine mai naiman alfarma sai yayi obliging, murmushi tayi
"Ko kaifa... Angon satin..."sai Kuma tayi shuru kaman wacce tayi mantuwa
" sauran kwana nawa ma?.." Ta tambayeshi, baki ya ga tabe .
"Nima ban Sani ba..."
"Rashin kunyan zakayi min kenan ..tambadade kawai..." Daure fuska yayi mussanman saboda mai aikin Hajiya dake zaune tana sauraron su, Ayan shuru yayi don baisan ta inda zai fara fada mata abinda ke tafe dashi ba,
"Hajiya wurin kinazo..." Yafada ahankali,
"Yo gani zaune?...ko.daukan ka zanyi don kazo wuri na?.." Ta fada tana yankan allaiyahunta,
"Ai magana nazo fada maki..." Yafada yana kokarin kuka intensionally saboda Hajiya ta tausaya mashi cos itace last hope dinshi, da sauri ta ajiye yankan ta kalleshi,
"Lafiya dai ko?.." Da sauri ya girgiza mata kai
"Babu lafiya..."
"Inna lillahi waina ilaihi rajuun!..." Tafada tana dafe kirjinta, sauran kadan da Ayan ya kufce da dariya amma dayake tashi matsalan is weighing him down sai ya dake,
"Wa ya rasu?..." Shine tambyar data yi mashi, galla mata harara yayi tayi sauri nunashi da wukan da take yankan dashi ta ce.
"Ka kara hararata sai na cire maka idanuwa Dan ubanka..."
"Kiyi hakuri Hajiya...zuwa nayi ki ceci rayuwata...." Yafada cikin sanyin murya,
"Wai yaushe zaka bar sakarci...ka taba ganin inda mutum ya ceci rayuwan mutum?... AI Allah kadai ke da daman ceto..." Tsoki yaja cikin ranshi Sannan yace
"Ke tashi ki bamu wuri zamuyi magana..." Ya fadawa mai aiki Hajiya, ahankali yarinyan ta mike ya barsu falon, tana fita Ayan ya fashe da kuka yana durkusawa gaban Hajiya, Hajiya sai salati take
"Hajiya auren dole su Abba suke son suyi Mani..." Ya fada cikin kuka, surprised look ne kwance kan fuskan Hajiya, ashar ta saki Sannan tace
"Amma Yunusa bai da hankali... Bayan wannan yarinyan daka fiddo shine ya kara nemo wata Kuma bai fadamin ba?..." Ayan tabe baki yayi tare da hararanta ta kasan ido Sannan yace.
"Ai ita din ce banason ta yanzu..." Bai idaba Hajiya tayinmashi dakuwa
"Kai kaci uwaka...yarinya daka yi min  fitsara saboda ita zakace bakaso?.. Amma ka cika Dan iska Wallahi..." Da sauri Ayan ya kara fashewa da kuka yana cewa.
"Ni yanzu banason ta..Dan Allah ki fada masu kar su yi min auran dole..." Yafada cikin kuka, baki Hajiya ta bude tana kallon ikon Allah, shidai sai kuka yake yana Dan daga kai don kallon Hajiya sauran kadan da dariya ta kufce mashi saboda yanda ta saki baki,
"Ikon Allah.. Yanzu duk son da kake mata shine yau kake zaune kana kukan araba auren?.. To da akwai babban magana..." Inji hajiya, Ayan shuru yayi yacigaba da kuka Hajiya tacigaba dacewa
"To meye dalilin?..." Ta tambayeshi da sauri ya fara cewa
"Hajiya yarinya ce ko kadan bata jin magana...yar duniya ce...Sam bata dace dani ba..." Yafada still yana kuka,
"Uhumm...daman na fada maku ayi bincike amma kukace kunyi....ni nasan da akwai matsala,..."
"To yanzu meye abunyi?.." Ya tambayeta yana goge hawayen shi don yasan ya kawo kuka inda zaa goge mashi hawaye,
"Ai ba wani abinyi sai dai a fasa auren... Baiyuwa a aura maka sauran wasu...ina...bazata sakuba..." Wani murmushin jin dadi Ayan yayi
"Yauwa... Daman nasan bazaki yarda ba..." Yafada yana dariya kaman bashi bane ke kuka few seconds ago,
"Amma har kusan zagina kayi don nace akara bincike..." Inji Hajiya data cigaba da yankan allaiyahunta,
"Kiyi hakuri.. Sai yanzu nagano... Yanzu yaushe zaki je?...don yau sauran sati uku...har lefe  naga an gama hadawa kai wa kawai zaayi..."
"Yau din nan zanje...." Da sauri yace
"To zan jira in kin gama in kaiki..." Yafada yana relaxing kan kujera,
"To shikenan......" Tafada tana kiran mai aikinta
 Mikewa yayi ya shiga cikin daya daga cikin rooms dake wurin ya daka tsalle ya hau kan gadon Hajiya , Hajiya dake falo ji tayi tim,
"Wallahi kana karya min sai ka sayi sabuwa zaka bar gidan,..." Hajiya ta fada mashi da karfi, da sauri shima yace
"Wannan ba matsala bane...kema kin San bani da matsalan kudi..." Y amsa mata yana kwance kan gado, shuru yayi yana tunanin ayya zai samu farin ciki muddin aka raba auren shi da ihsan kuwa?, yanzu kwana uku kawai bai ganta ba amma ji yake kaman ya shekara bai ganta ba. Baki ya tabe tare dacewa
"Allah raka taki gona cos in so cuta ne hakuri ne Maganin shi...."


Sai bayan sallan asar Hajiya ta gama abinci pounded yam da vegetable soup, har kuryan Hajiya mai aikinta ta kawo mashi abincin, hannu ya wanke yaci sosai don gani yake his problem is solved Sannan rabonshi da abinci tun kafin su abincin da ya danci lokacin daya kai ihsan gidanshi, tea kawai yake sha shima not always.

Biyar saura quarter suka bar gidan tare da Hajiya dake sanye da doguwar rigan atampa tare da very long hijab my Jan kasa sai hannun ta dauke da wani dangwalelen bag irin na tsaffi.
Kofar gidansu yayi horn, kafin maigadi ya bude sai da ya kalli kofar gidansu ihsan kafin ya shiga ciki. Dadi yaji dayaga motan Abba alaman ya dawo, yana parking ya fito ta budewa Hajiya kofa abinda baiyi sai cewa tayi
"Munafiki wai har da bude min mota..." Tafada tana fita daga cikin motan. Bayanta Ayan yabi da harara sannan ya shiga part dinshi itakuma Hajiya ta shiga bangaren Abba. Relaxing yayi yana jiran outcome.
Ko sallama babu Hajiya ta shiga part din Abba alokacin Umma ta hada mashi ruwan wanka ta fito kenan, surprise ne kwance kan faces dinsu cos basu expecting dinta,
"Ah...Hajiya sannu da zuwa...har kinji lefe ya hadu kenan...." Inji Umma, wani irin harara ta watsa mata, Abba durkusawa yayi gaisheta amma ko amsawa batayi ba ta zauna Sannan tace
"Ku zauna...muyi wata magana..." Tafada fuskan ta daure, Umma kam ta gane Ayan ne ya kai karansu. Ahankali su biyu suka zauna kasan carpet gabanta, kallon kowanne su tayi Sannan tace
"Yanzu in ba don kun raina ni ba har a binciko wani abu game da yarinyan da wannan shegen yaron zai aura...amma Ku jajirce sai ya aureta?.. Don Baku nemawa yaranku mata ta gari?..." Da sauri Umma tace
"Me aka binciko Kuma?.." Dakuwa Hajiya tayi mata
"Kin ci gidanku...ba ya binciko yarinyan yar iska ce ba?..." Da sauri Abba ya girgiza mata kai
"Sam ba haka bane hajiyata ta kaina..." Da sauri Umma ta amshe ta fara cewa
"Karya yaje ya fada maki...shi da kanshi yake iskanci daita..." Da sauri Hajiya tace
"Subhanallahi!..ban gane ba...."ta fada tana dafe kirjinta,  Umma tace
" da idona naga yarinyan tana barin bangaren shi da daddare..shine don ya gama daita yake cewa bai aurenta,..." Da yace
"Kinga Hajiya hakan ai bai kamata ba ko?.." Da sauri ta gyada mashi kai
"Inafa zaiyuwu.....amma wannan yaron dan rainin hankali ne...shine yaje ya tisoni gaba wai zaayi mashi auren dole...to gaskiya yazama dole ya aureta...Ku barni da shege...inji Hajiya tana mikewa, da sauri Umma tabi bayanshi tana kallon Abba bakinta dauke da murmushin mugunta.
" Hajiya taho muje ki fara ganin lefen..tunda kinzo.....daman da daddare nace a sanyosu mota akawo maki ki gansu..." Umma Tafada mata suna fita daga bangaren Abba. Hajiya bata musaba suka shiga part din Umma. Nan aka bude mata bags ta fara kallo tafi hour tana kallon lefen cod duk Wanda ta dauko sai ta tambayi Ku dinshi damuna sunan campanin da aka sayoshi, kunji tsokuwa da wayewa. Tana gamawa ta dauki jikanta ta yi hanyan bangaren Ayan, Ayan da yayi relaxing yana jiran result har bacci yabfara dauke shi, ko kofanshi bai rufe ba, haka ya bawa Hajiya shigowa kawai daga bag dinta tayi ta rankwala mashin ita ga kai
 Cikin bacci Ayan yaji kaman an naka mashi stone ga kai, da sauri ya bude ido,
"Daman haka kake Dan ubanka?..." Tafada tana shake shi, kallon Umma dake tsaye bayan Hajiya yayi tayi mashi gwalo, hawaye ya farayi yana cewa
"Wallahi Hajiya duk abinda suka fada maki ba haka yake ba..." Ya fada cikin kuka, girgiza shi Hajiya ta farayi tana cewa
"Lahhh...daman da ganin wannan manyan idanuwan na yan iska ne.....ka gama kwalwale yar mutane zaka gudu ko?...to ka saurareni da kyau...baka isaba Wallahi ..shege mai kan doya..." Tafada tare da sakin wuyanshi, Umma kallon shi babu yabo babu fallasa Sannan tace
"Kuma anjuma kaje chan gidan ka fada mata zaa kawo lefe gobe...kaji ko baka jiba?.." Ta daka mashi tsawa, cikin kuka yace
"Naji Umma..." Hajiya kallon yanda yake hawaye tayi Sannan tace
"Wannan yaron anyi munafiki Wallahi... Jibi yanda yake kuka kaman mace...Kuma nasan ko wata tara yarinyan batayi zata haihu amma sai kuka kawai yake..." Hararanta Ayan yayi hannu ta daga kaman zata bugeshi ya jabaya da kanshi
"Wallahi ka shiga hankalin ka..banza mai bakin fuska..".Hajiya ta fada tana fita daga dakin, Umma takowa tayi ta zo kusa dashi Sannan tace
" wallahi ka kara kai wannan maganan wani wuri ni Kuma bazan fasa fada masu halinka ba...so is left for you.. In ka gan dama ka tafi katsina kai kara su fada masu zanyi...idiot of the last order... " Umma ta fada Sannan ta fita daga dakin. Ayan tagumi yayi yana hawaye.
"This is not happening to me...." Yafadawa kamshi
[12/27, 14:10] ‪+234 814 199 1000‬: 💜❤💛🖤💚💙
KAWARTA CE SANADI
💛💚💙🖤💜❤



®zuwairat( ummu Maryam)




3⃣8⃣



 _Gaskiya masoya na gaji da listing sunaye cos yawa gareku nasan kunfi dubu goma so in nace za kira suna_ _one after the other zai zama bata lokaci amma wannan page is dedication to *bilkis yahaya bello* da my besty *Maryam Musa waziri,* _
M _y *Maryam* Allah ya...ya...ya...in short say ameen kawai cos kinsan aduan me nake maki. Love you all_





Wacegari kam tun da wuri gidansu ihsan ya cika da mutane sai aikace2 ake saboda yan kawo lefe likewise gidansu Ayan shi kam Ayan yana mamakin yanda zaa kai lefe baa sanar ba don ko kadan baisan Umma taje gidan ba.

Sai karfe 11 ihsan ta kunna wayanta bayan ta yi wanka ta shirya cikin swiss lace ta koma kan gado tana jiran wayanta ya gama kunnuwa ta kira husna ta sanar daita the latest news. Bayan wayan ya gama booting tayi dailing number husna, daga chan bangaren husna dake zaune kan dinning tana breakfast tayi saurin daukan wayan cos yanzu basu fiya wayaba cos babu nothing new, husna na picking ihsan ta fashe da kuka tana cewa
"Babe na shiga uku na lalace..." Da Sauri  hudn ta mike ta shiga dakinta tare da kulle kofan
"Babe ya akayi?... Ko iyayenshi sunzo ne?..." Ta tambayeta tana zama bakin gado, cikin kuka ihsan tace
"Umma...tazo..." Da Sauri husna ta saki murmushi tare da lumshe idanuwa tana jiran kawai komai ya lafa ta je Maiduguri wurin grandma, ihsan ta cigaba dacewa
"Yanzu could you believe jiya umma ta fada jiya zasu kawo lefe jiya?..." Da Sauri husna ta dafe kirjinta tana mikewa tare dacewa
"What!!!!!..." Tafada cikin tashin hankali, ita Kuma ihsan was thinking saboda abinda Ayan yayi mata take wannan ihun, Kara rushewa da kuka ihsan tayi tana cewa
"Yes...yanzu nashiga uku...imagining me cikin gida daya da Ayan bayan duk abinda yayi min...wallahi babe har yanzu jikina bai bar min ciwo ba...." Husna data fara hawaye tace
"Babe ya zam dole ki fadawa su mom gaskiyan abinda Ayan yayi maki...bakisan mata nawa yayi wa haka ba...he's a molester...he don't deserve you..." Tafada cikin kuka,
"Babe am scared... I don't know what to do....I hate Ayan and am afraid of him..." Bata idaba husna ta katseta dacewa
"Pls ki fada masu gaskiya...wallahi I think that is the only way out...pls kar a hadaki da wannan azzalumin...." Ta fada sounding caring whereas she fighting for chance
"Ban Iya fada masu...kin San halinim...tana iya kasheni inhar taji nabi Ayan wani waje...." Ta fada cikin kuka sosai,
"Zan fada masu..." Ta fada da Sauri ihsan tace
"No!..."
"Then kin fi son ki aureshi kenan..." Tafada kaman ta fashe don bakin ciki,
"No...I will find another way out..."
"Babu wani way out...daman kilan you enjoyed what he did to you..." Tafada tare da Jan tsoki ta kashe wayanta, ihsan data bude baki zatayi magana taji husna ta kashe wayan ta.
 Wurgar da wayanta tayi ta zauna ta hada kai da kwaiwa tana kuka tana tunanin ya zaayi ita da Ayan su zauna gida daya bayan duk abubuwan da yayi mata,
"Inama ya mutu kaman Mahmoud..." Tafada cikin kuka da matsanacin haushin shi, tasan muddin akayi auren nan itace abar tausayi don yanzu tafi son shaidan fiye da Ayan, bata manta yanda ya dinga bugata da bango.ko da kasa ba, she wish she can stop this marriage from happening, Dan ajiyan zuciya ta saki   tana tunanin kilan a fasa don ita har yanzu bata fidda rai ba.

Husna na kashe wayan ta wurgar da kanta kan gado ta fara kuka kaman Mara hankali ,
"Wayyo....wayyo... Wayyo... Mutuwa zanyi..." Ta dinga maimaitawa tana kuka kaman ranta zai fita, saida tayi mai isanta Sannan ta kira grandma ta shaida mata har yanzu baa fasa auren ba, nan grandma ta kashe waya ta kira mami ta fada mata tanason ganin husna saboda da akwai abinda takeson bata saboda rashin manema, nan take mami ta amince kan zata zo jibi.


Around four gidan su Ayan ya cika saboda yan kai lefe dukda ba nesa zaa kaiba hakan bai hanasu sakawa a mota ba, bakin window Ayan koma yana kallon ikon Allah don bai  taba ganin inda aka kai lefe batare da an sanar ba don baisan  Umma ta je gidan ba.
 Hada kai da window yayi yana kallon mom Yusuf da Muhammad da bakin su bai rufuwa saboda  farin ciki yayi sai tunanin irin zaman da zasuyi da ihsan yake shi abinda ke kara bata mashi rai shine yanda ya tsani auren dole amma gashi shima auren dolen zaayi mashi, yasan confirm ihsan zata wahala hannun shi cos shi kadai yasan tanadin dayayi mata in har ta amince ta shigo gidan amatsayin matarshi, murmushin mugun ta yayi yana cewa
"In ba don wannan yar iskan ta saba da iskanci ba AI duk abinda nayi mata ya isa ta fadawa iyayenta a hana auren amma dayake she's expert shine tayi shuru... Hmmm I make sure is the worst mistake of your life... I will teach you a lesson Kuma wallahi sai na auro yarinya sabuwa ba second hand mai kama da saboba..." Ya fadawa kanshi tana kallon motan da aka saka kayan suna fita daga gidan while manyan mata na biye da motan a kasa sai guda ake, daurewa yayi yana cewa
"Ku kuna murna ni kuma da ya kamata inyi murna ina bakin ciki... What sort of life is this?...." Ya tambayi kanshi, komawa yayi ya zauna yana daukan wayanshi, number Muhammad yayi dailing yana cewa
"Suma banzaye sun wani manta dani kaman kanwar uwarsu ce halima...." Yafadawa kanshi.


Agidan su ihsan kam suma mutane are ready don amsan lefe gidan cike da family and friends especially masoyan ihsan, anyi abinci kala2 da abunsha kala2, mutane kam sai mamakin wannan lefen suke cos duk ya dara Wanda sauran suitors dinta ke kawowa komai, ihsan kam tana sama ta hada kai da gwaiwa ba kuka taje ba amma she's lost in thought. Sai bayan sallan ishai su anty suka koma gidansu,sama mom ta hau ta tisa ihsan gama kan tazo ta ga kayan, tana kuka tana kallon su.

Gidansu Ayan Kuma Muhammad da Yusuf sunzo sai mamakin yanda ya koma suke har Muhammad nacewa
"Ka kashe kanka a banza kan wannan auren...haba wallahi kafi karfin wannan abun da kake ..." Ayan daga big eyeball dinshi yayi ya kalli Muhammad Sannan yace
" sai yanzu nasan cewa in zaka so mutum ka soshi daidai..don in ka tashi kinshi ka kishi daidai... Wallahi yanda naso ihsan haka na tsaneta...pls Ku fadawa su Umma kar su hada auren nan kar inyi committing suicide... " yafada cikin daci, Yusuf tabe baki yayi Sannan yace
"Ina mamakin yanda akayi ihsan ta amince zata aureka bayan rashin m da kayi mata...ai wallahi ko Kaine autan maza ban aurenka..."
"To ka fada mata ta fasa mana...I don't care saboda gani nake kun fi dacewa cos na lura ko kadan baka ganin lefenta..." Tsoki Yusuf yaja Sannan yace
"Ba wai banason laifinta bane...kawai you are taking things too high...kawai ka bari in ka aureta kaji ba yanda kakeso ba you can let her go or better still get another wife...amma duk kabi ka damu mutane speculation not facts...." Da Sauri Ayan yace
"Am not speculating... I know what am talking about... Kawai banason in nuna makune amma Wallahi wani ya turomin nude pic da video dinta in shower..." Baki Yusuf ya kara tabewa
"That's your businesse..." Yafada not believing abinda Ayan ya fada
 hira suka dingayi inda Ayan na jadadda masu bayason auren su Kuma suna fada mashi yayi hakuri sai bayan sallan ishai suka tafi, still aranar babu Wanda yayi bacci cikin su uku amma husna tafisu shigan tension.
The following day husna tazo ganin lefe babu Wanda zai gane she's a monster cos fuskan ta dauke da murna na gaske amma deep inside she's boiling saboda haushi da bakin ciki, suna zaune upstairs suna hira inda husna ta nace kan ta fadawa su mom gaskiyan abinda Ayan yayi mata ita Kuma tana cewa she can't


Ayan na dawowa daga masjid cos nan kadai ke fidda shi daga part dinshi cos yanzu banda masjid babu inda yake zuwa, kawai haka nan sai yace
"Lets talk..." Yafada yana daukan wata karamin waya dake kan drawer, number ihsan ya saka yayi dailing.

Suna cikin hira wayanta ya fara ringing, dauka tayi taga babu sunan mayar da wayan tayi ta ajiye bata yi picking ba
"Babe your phone is ringing... Kiyi picking mana..." Husna ta fada mata,
"Bai da suna...yanzu I don't want to pick any how call.."
"Pls pick up... Kika San ko is somebody important?.." Husna ta fada sounding caring, daukan wayan husna tayi don kar ta tsinke tayi picking tare da sawa a speaker, daga chan bangaren Ayan cewa yayi
"Halima kina jina?..." Yafada babu yabo babu fallasa, da Sauri ihsan tafara cewa
"Babe kashe...pls off it..." Tafada tana kokarin amsan wayan daga hannun husna , da Sauri husna ta dauke wayan tana cewa
"ki saurari abinda zai fada maki mana..." Duk Ayan yana jin abinda suke cewa, baki ya tabe Sannan yacigaba dacewa
"Wato dayake kin cika yar iska shine after every thing kina da effort din amsan lefen da aka kawo ko?..." Ran ihsan mugun baci yayi hannu ta mikawa husna ta bata wayan Sannan tace
"Wai who is speaking..." Ta fada sounding firm and strong, Dariya Ayan yayi Sannan yace
"ZAKISAN KONI WAYE muddin kika yarda akayi auren nan..." Itama ihsan wani irin dariyan rainin hankali tayi ta kalli husna Sannan tace
"Babe wai wane buntsuru ke magana?..." Da Sauri Ayan ya mike tsaye yana jin ihsan ta kirashi da buntsuru,
"What did you just call me!!..." Yafada afusace, ihsan baki ta tabe tana cewa
"Ni har yanzu bangane Dan akuyan dake magana ba...anyway I have better things to do..." Tana kaiwa nan ta katse wayan, da Sauri Ayan ya wurgar da wayan ta watse
"Did she just call me a he goat?..." Ya fada yana nuna kanshi in disbelief,
"Hmmm..." Kawai ya dinga sauke ajiyan zuciya saboda yanda heart dinshi ke harbawa.

Bayan sallan magrub husna tazo tafiya ihsan ta rakata har bakin gate Sannan tace zata koma ciki, bata rai husna tayi tana cewa
"Kam amma baki da mutunci...yanzu inzo gidan Ku amma bakin gate zaki rakoni?..." Ta fada cikin baccin rai, da Sauri ihsan tace
"Wallahi babe na mance rabon da in taka waje,..ina tsoron in hadu da wannan shegen..." Baki husna ta tabe
"Pls ki rakani..." Tafada tana Jan ihsan waje, Allah ya taimaka ta rufe kanta small Vail, bata kara cewa komai ba ta fara binta suna hira, daga nesa Ayan dake dawowa daga masjid ya hango su, dukda gari ya fara duhu yasan ihsan ce tafe, da Sauri ya koma gefen wani umbrella tree ya saya kanshi don kar su ganshi Kuma luckily basu ganshiba,
Suna hiransu har suka wuce inda yake tsaye, murmushin mugunta ya saki yana lumshe idanuwan saboda kamshin perfumes din ihsan that is in resistable. Yana ganin sun wuce shi Yayi Sauri kama hanyar gidansu, da Sauri ya dauki mota ya dawo ya tsaye still under tree lokacin gari ya gama duhu

Sai da suka kai bakin titi husna ta samu abun hawa bayan sun Dade tsaye suna jira, nan husna tashiga sukayi bankwana don ta fada mata zata Maiduguri the next day, kan hanyan ta na dawowa tana ta Sauri don street dinsu is quite and lonely, Ayan na ganinta daga nesa ya fito ya tsaya yana jiran isowanta, kaai tana zuwa inda yake tsaye bata ankaraba taji an kamata,
"Who do we have here..." Yafada , jin muryan Ayan yasa ta bude baki zata saki ihu wani irin mari ya dauketa dashi yana cewa
"One word from you wannan buntsurun sai yayi maki rashin mutunci da har ki mutu bazaki  mance ba...do I make myself clear?..." Da Sauri ta gyada mashinkai tana dafe da inda ya mareta,
"Good...yanzu enter..." Yafada yana bude mata mota.
[12/27, 14:10] ‪+234 814 199 1000‬: 💙💚💛🖤❤💜
KAWARTA CE SANADI
💙💜❤🖤💛💚




®zuwairat(ummu Maryam)






3⃣7⃣




 _Wannan shafin is in dedication to you *Aisha qazafi* , Allah ya kara zumunci, ya bar kauna._





Few seconds yana zaune inda yake yana hawaye aka bude curtains dinshi, Hajiya ce ta kara shigowa tace
"Kai Dan ubanka zo ka maidani..." Tafada cikin fada, kallon ta yayi da disgusting look Sannan yace
"Ina?.."
"Gidan ubanka..." Ta amsa mashi atakaice,
"Babu inda zani..." Ya amsa mata fuskan shi daure,
"Ai wallahi baka isaba ...yanda kaje ka daukoni haka zaka maidani ko Kuma in ta dukan ka da wannan jakan..." Ta fada tana nuna mashi bag dinta, banza yayi daita yacigaba da hawayen shi, gani yayi ta nufo shi da sauri ya mike yana cewa
"Babu inda zani..."
"Nace ka wuce ka maidani...." Ta fada tana kara dososhi, da sauri yace
"To ki bari inyi alwallah.. Ai magrib ta gabato..." Sai lokacin ta yarda ta fita, shi Kuma yana kumbure2 ya shiga bathroom yayi alwallah ya fito Sannan ya dauki car keys
 Driver's seat ya zauna, Hajiya dake jira a bude mata tabishi da zagi sai dai Umma ta bude mata, afusace ya figi motan don ta baya ya fita daita, salati Hajiya ta fara amma ko sauraron ta baiyi ba ya cigaba da tuki kaman racer, daman yasan Hajiya batason tuki high speed Sannan batason waka cikin mota, da farko wakan barmani choge Ku kama Sana'a mata ya saka ya kalli Hajiya ta glass Sannan yace
"Hajiya ga wakar Ku marasa Sana'a..." Yafada yana kallon reaction dinta ta glass,
"Uwarka ce bata da Sana'a..." Ta amsa mashi,gani yayi bata bata rai ba da alaman tana jin dadin wakan, chanza wakan yayi zuwa da toofan ya kura volume ya cigaba da tuki da gudu Hajiya sai kwace mashi albarka take amma ko ji baiyi saboda yanda ya kura volume, gashi ko bump sai dai ya hau da gudu sai da ka ga Hajiya rana up and down saida tayi dana sanin hawan motanshi.

Sai 8:30 ya dawo unguwan su, bai tsaya gidaba ya wuce gidansu ihsan,  zama yayi yana tunanin irin rashin mutunci da zaiyi mata in har ta yarda ta fito, wayanshi ya dauko ya fara Neman number ta.

Ihsan kam ganin yunwa zai hallakata kuma babu mai kallon ta yasa ta sauko downstairs duk su mom da sauran yan gidan suna zaune falo,ahankali ta taka cikin kasaita as usual ta shiga kitchen mom tabi bayanta da harara, tana shiga ta bude fridge ta dauki mulmulen fura guda daya ta saka cikin blender Sannan ta dauko yoghurt daya 33cl ta juye ciki tayi blending smoothly ta juye cikin cup ta dauko ice cube daya ta jefa ciki ta fito rike da cup, mom na ganinta ta tabe baki,
"Ai da kin cigaba da hunger strike mana...shegiya kawai..." Mom ta fada, kanta kasa ta hau upstairs tana sipping furan,zama tayi  kan kujeran mirror tana kallon kanta tana mamakin yanda ta Kara ramewa, tana cikin shan furan wayanta ya fara, jin ringing din yasa gabanta faduwa don bata chanza kala ringing Ayan ba
 Da Sauri ta dauki wayan tayi rejecting kiran Sannan tayi deleting number dinshi ta kashe wayan gabaki daya.  Ayan dake zaune cikin mota tabe baki yayi ya fito, bakin gate dinsu yaje ya buga dukda yasan bude take, maigadi ne ya fito suka gaisa
"Aa baka shigowa yau?..." Ya tambayi Ayan, murmushi kawai yayi Sannan yace
"Sauri nake ne...pls wannan yarinyan tana nan?..."
"Eh tana nan..." Ya amsa mashi
"Dan Allah ka kira min ita..." Ya fada mashi Sannan ya koma cikin motanshi ya hakimce, da Sauri my gadi yayi cikin gida,sallama yayi ya shiga falo inda su mom suka amsa mashi,
"Hajiya ina Hajiya karama?..." Ya tambayi mom,
"Tana dakin ta...ya akayi ne?..."
"Alh Ayan ne yake kiranta...."
"Ok..." Ta fada Sannan ta kalli Janna
"Ki je ki fadawa ihsan Ayan na jiranta...." Ta fadawa Janna, mikewa tayi ta hau upstairs.

Ihsan dake zaune har lokacin ta najin kaman zaa bude kofan ta tayi saurin hayewa kan gado tayi kaman tana bacci, kiranta Janna ta dingayi tayi banza daita kaman bataji gajiya Janna tayi ta koma falo ta shaidawa mom cewa ihsan tana bacci
"Wallahi karyane..." Shine abinda mom ta fada tana mikewa.

Sama ta hau ta bude kofa dakin ihsan ta ganta kaman tana bacci, kiranta tayi sau daya taji shuru, hannu ta daga ta falla mata bugu nan take ta mike tana kuka,
"Dan ubanki ki wuce Ayan na Chan yana jiranki..." Mom ta fada mata atakaice, cikin kuka ta fara cewa
"Cikina ke ciwo..."
"Karya kike munafuka....maza tashi yanzu nan before I descend on you...." Da Sauri ta mike tana kuka, hijab kawai ta saka kan long gown dake jikinta, tisata gaba mom tayi har falo tana kuka ta fita waje, tana zuwa waje ta goge face dinta ta daure tamau tana duba ta ga Ayan amma babu shi, maigadi ta tambaya ya shaida mata yana waje, Kara daure fuska tayi tana cewa
"Ka kirashi mana..." Tafada kam batason magana amma deep down ko ganin shi batason yi, maigadi na fita ya shaida mashi yanda tace shima bata rai yayi yana cewa
"Ka fada mata bani da time...in zata fito ta fito in Kuma bata fitowa ta fadamin..." Yafada yana karasa maganan da tsoki, maigadi tsaya kallon shi yayi yana mamaki, acikin ranshi kam cewa yake
"Allah kasa ba fasa wannan auren ma zaayi ba...ihsan yar baiwar Allah..." Ya fada cikin ranshi Sannan ya bude kofa ya ta shaidawa ihsan yanda yace, tsoki taja tana juyawa zata koma ciki tare dacewa
"Ka fada mashi ba fitowa zanyi ba don haka yasan inda dare yayi mashi..." Ta fada tana shigewa falo abinta, da Sauri mom ta kalleta
"Har kinyi me?.." Ta tambayeta afusace, da Sauri ta fara cewa
"Sako ya bani...ya tafi..." Ta fada kaman zatayi kuka, kallon rashin yarda mom tayi mata amma batace kala ba , simi2 ta hau sama.
Maigadi na fadawa Ayan abinda tace ya tabe baki ya figi motanshi yana cewa
"Saukin ki kar ayi bikin nan..Wallahi.." Yafada yana kaiwa kofar gidansu
 Horn yayi aka bude mashi ya shiga ciki part din Umma bayan yayi parking a lot, zama yayi kusa daita ta koreshi tana cewa
"Kaje inda na fada maka?..."
"Naje bata fito ba..." Ya fada in I don't care tune, hararan shi Umma tayi tana cewa
"Ka maidani abokiyar wasar ka ko?..." Da Sauri ya girgiza mata kai yana cewa
"Wallahi Umma naje bata fito ba...wallahi da gaske naje..." Ya fada yana defending kanshi cos ya lura Umma bata yarda da shi ba,
"Zakaci ubanka ne..." Tafada tana mikewa, upstairs ta hau shi Kuma ya fita daga wurin ya koma part dinshi, ba da dadewa ba Umma ta sauko da long hijab hannun ta rike da pause da Sauri Ismail ya biyota yana cewa
"Umma zan biki..." Yafada looking ready to go, bata kalleshi ba ta fita ya bita da gudu. Part din Abba ta shiga ta nemi izinin fita Sannan ta fito hannun ta rike da hannun Ismail.

Bakin gate dinsu ihsan ta tura tashiga ciki, daga nan tayi hanyan falon su har lokacin su mom na zaune falo sallama tayi duk suka amsa mata suna kallon especially mom that looks so surprised to see her.
Ah ah...Hajiya ke da kanki a gidan nan?..." Mom ta fada tana mikewa,  dariya kawai Umma tayi tana cewa
"Aikam dai..." Gaisawa sukayi cikin girma da arziki mom kam sai tunane2 take don gani take maganar auren su ihsan tazo yi mata, zama tayi kadan tana dan shan ruwan da mom ta kawo mata Sannan tace
"Ina kuka ajiye min daughter... Naga kowa nan amma babu ita?.." Tafada da murmushi fuskan ta, ita mom murmushi tayi Sannan tace
"Daughter dinki tana dakinta...." Dariya Umma tayi Sannan tace
"Gaskiya baki son daughter ta...kawai sai ita kadai daki?... Ai kuyi Ku gama nan da sati uku zan dauki yata..." Tafada cikin raha ta kara da cewa
"Daman aro na Baku..." Dadi mom taji cikin ranta don sai yanzu hankalin ta ya kwanta cos she was thinking something else,
"Yanzu Ku raka ni dakin daughter ta..." Inji Umma, da Sauri mom ta mike tana cewa
"Bari in kirawo maki ita..." Itama Umma mikewa tayi
"Ai ba cewa nayi Ku kirata ba...dakinta nace Ku raka ni..." Tafada cikin faraa, Dariya mom tayi
"To shikenan..." Hanyan upstairs mom tayi Umma tabi bayan ta, Ismail Kuma ya zauna yana wada da handsome.

Tunda ihsan ta hau upstairs take zauna kan gadonta ta hada kai da gwaiwa tana kukan bakin ciki tana mamakin abinda Ayan yazo yi gidansu Kuma tasan ba abun arziki ya zai dashiba Kuma she don't care, abinda ke bata mamaki shine har yanzu the wedding is not yet off.
 Bata ankaraba taji an bude kofan ta, da Sauri ta daga kai tana kallon mom batasan Umma na bayanta ba da sauri ta fara goge hawayen ta, jin sallama Umma yasa tayi Sauri sauka daga kan gado tana goge hawaye, Umma kallon ta tayi tana mamakin yanda ta rame ta kara haske kaman ba itaba, da Sauri ta durkusa ta gaida Umma, ta amsa tana zama kan kujeran gaban mirror tare da bawa mirror baya, ihsan kasa tashi daga durkushen tayi har saida Umma tayi mata izinin mikewa,  ahankali ta mike tana mamakin abinda ke tafi da Umma, hanyan waje tayi Umma ta kalleta tana cewa
"Ina zuwa Kuma?..."
"Ruwa...ruwa zan dauko maki..." Tafada muryan ta na cracking,
"Yi zamanki...nasha ruwa..." Ta fada mata, ahankali ihsan ta  koma ta zauna gabanta na faduwa,
"Sai a tafi a bamu wuri da daughter ta ko?.." Ta fada tana dariya, itama mom Dariya tayi tana cewa
"Ai shikenan..." Mom ta fada tana fita daga dakin, Umma tashi tayi ta koma gefen ihsan da Sauri ihsan ta koma kasa, Umma dadi take ji har cikin ranta ihsan zata kasance cikin family dinta,
"Daughter me ya hadaki da Ayan..." Shine tambayan da Umma tayi mata, kanta kasa amma kasa cewa kala tayi, shoulder dinta Umma ta kama Sannan tace
"Take me as your mother... In Ayan yayi maki abinda vau kamata ba zan yi Maganin shi..." Ihsan dai shuru tayi hawaye na taruwa idanuwanta ji take inama tana Iya fadawa Umma gaskiyan abinda Ayan yayi mata, amma she won't dare,
"Yazo dazun?..." Umma ta sake tambayan ta, kai kawai ta gyada mata,
"Meyasa baki fita ba?..."
"Na...fita....shine...bai shigo ba....waje ya tsaya...." Ta fada muryan ta na rawa,
"To naji...banason sanin abinda ya hada Ku...amma inason in fada maki..ko mai na duniya hakuri akeyi...mahakurci mawadaci...kinji ko?..." Da Sauri ta gyada mata kai,
"Good ..Kuma daga yau inason duk ranar da Ayan ya fada maki ko yayi maki abinda bai kamata ba kar ki fadawa kowa ki fadamin... Na isheshi Riga da wando,...so Kuma gobe zaa kawo lefe...Kuma..." Aikam ihsan fashewa tayi da matsanacin kuka tana cewa
"Umma Dan Allah... Kar a hada ni ...dashi..."
"Why?.." Umma ta tambayeta, kuka tacigaba dayi batace kala ba. Umma dai tunanin kilan abinda yayi mata lokacin da tazo gidan ne yasa tace kar ahadasu don haka cewa kawai tayi
"Kiyi hakuri...ihsan inason ki tamkar yanda nake ji da yayana cikin raina Kuma nasan you are the best choice for Ayan..." Magana Umma ta dinga fada mata har ta samu ihsan tayi shuru, tambayan ta tayi kota yi sallan ishai ta amsa mata da eh, mikar daita tayi ta umarceta data kwanta Sannan ta kawo mata blanket tare da tofah mata adua kamar yanda takewa su salma da sauran su Sannan ta kashe wutan dakin ta kawo kofa ta sauka downstairs.

Nan ta fadawa mom gobe zaa kawo lefe Kuma ta fadawa mom su dinga hakuri da halin Ayan inda mom ta shaida matabashi da matsala ko kadan. Mom raka Umma tayinhae waje Sannan ta dawo gidan ta shaidawa dad yanda sukayi da umma. Ihsan kam kaman Umm  cuta ta bata Maganin bacci nan take bacci mai nauyi ya dauketa batare data shaidawa husna halin da ake ciki ba.

💚💛🖤💜❤
Masoya naga abun arziki dukda basanwacce ta turomin ba amma INA godiya Kwara.
[12/27, 14:10] ‪+234 814 199 1000‬: 💜❤💛🖤💚💙
KAWARTA CE SANADI
 💜❤💛🖤💚💙




®Zuwairat ( ummu maryam)



3⃣9⃣


Masoyana kuyi min afuwa, naso da kun bari na gama da zai fi muku dadin karantawa. Nana, xaly.da dei sauran dubban masoya wannan shafin naku ne..... Allah ya bar mu tare.





Shiga tayi ya rufe motan shima ya shiga, ihsan duqar da kanta qasa tayi tana share hawayen dake zuba daga idanun ga stananin tashin hankali dake ciki. Kallonta Ayan yayi ya yastine fiska yace kamar mutuniyar arziqi ahaka, karuwar banza har kina.da bakin da zaki qira ni bunsuru ko dai so kike in nunamiki halin bunsuru.. ihsan daga kai tayi ta kalleshi da sake sauke kai tace kome zaka min Allah na gani amma ina rokonka.kadena min laqani da karuwa dan ina da mutunci na.
Ayan murmushin yake yayi yace maqaryaciyar banza wai ke duk batunnan inma dan in aureki ne  ni  bazan hada zuriya da tambad'ad'd'iya irinki ba, nasoki so na hakika amma rayuwar da kika zab'awa kanki kawai sai kuka ya kupce masa.
Ihsan daga kai tayi tana masa kallon mamaki, baki ta sake tana kallonsa,  cikin rawar murya tace wai kai wayace maka ni karuwa ce  da mutunci na da komai tunda kace baka sona murabu lafiya amma sau biyu kayi yunqurin yi min fyade Allah na starewa. Sannan ni ban alaqanta ka da wani suna ba sai kai. Wayace maka i karuwace dawa nake karuwanci alhalin bayan kai babu namiji da yatab'a dafa hannuna bayan kai. Katuna sanadin riqe hannuna da kayi abaya shi yasa nake qiranka da dan iska har kamareni sabida haka. Ko dama don kiranka da nayi dan iska shiyasa ka shigo rayuwata don karama. nan ihsan ta saki kuka mai stuma zuciya.
Kallonta yayi na mintuna kadan sanan yace Halima anyi min 1st warning, na wastar anyi min na biyu still na wastar sai aka nuna min zahiri. Halima  nude pics dinki na wayana ki staya kina raina min hankali.
Atake ihsan ta d'ago kai tana dafa qirji tare da fad'in ni d'in? Staki yaja yace zan dalla miki mari banza karuwa. Kasa cewa komi tayi ta qara.fashewa da kuka. Wallahi qarya kake min ni ba 'yer iska bace nayi imani da Allah nan dai Ayan yaciro wayansa ya bude ya miqa.mata yan cewa meye wannan atake ta bude idanunta data fara kallon video da abinda aka rubuta aqasa nan take  numfashinta ya dauke ta sume.wayan ya zame ya fad'i. Ayan da ya zuba mata idanu ya tabe baki da nuna ko in kula haka yaja mutar ya isa kofar gidansu ya zagaya ya sauketa ya kwantar aqasa ya shiga motar yabarta anan.
Husna kuwa har tayi nisa ta sai sai ta kasa daurewa tace da me keke ya juya da ita haka kuwa ya juya adaidai kofar gidansu Ayan ta staya ta sallami mai adaidaita sahu. Nan ta gusta kai ciki tako yi sa a mai gadi ya shiga kewaye. Nan ta shiga farfajiyar gidan ta kai bakin main palor tayi sallama aka amsa mata sai kuma ta staya kamar mai wani tunani  an umma da taji shiru ta taso tazo bakin qofar dan ganin wake sallama.
Tace shigo mana. A firgice husna ta daga kanta ta kalle matar sai matar ta riko hannunta suka shigk tare. Umma tace ke wacece daga ina. Nan taji gabanta ya fadi. Sai ta niqe. Tace ina wuni umma ta amsa sannan tace sunana Fadila. HALIMA ce ta aikeni. Wace halima umma ta tambaya. Tace Ihsan wacce aka kai lefenta daga gidannan. Shirun da umma tayine ya bata damar ci gaba da zubo zance tun zuwan ihsan gidan da abinda Yan yamata da fitan da tayi daga gidan tana kuka har yadda ya yawdare ihsan ya kaita gidan da yadda su yusuf suka kwaceta da qer. Ta qara dacewa dan Allah umma tace in rokeki kan kar ahada aurenta da Abubakar dan zata kshe kanta.. nan take umma ta dafe kirji. Abba dake zaune agefe yana jinsu amma husna bata sani ba. Nan ya mike ya doso wurin su. Da ganinsa husna ta dauka ayan ne ta kwashi kafa tayi waje da gudu ko takalminta bata staya dauka ba.
Ayan kuma ya dawo gida ya zauna. Nan kuma yaga bai kewta ba idan wani yazo ya dauketa fa kawai sai ya tashi yayi waje.
[12/27, 14:11] ‪+234 814 199 1000‬: ❤💙💜🖤💛💚
KAWARTA CE SANADI
💛💚💙🖤💜❤



®zuwairat( ummu Maryam)



4⃣1⃣





 _Wannan shafin Kuma is for yan *Zuwairat novel 2,* Allah ya bar so da kauna_


 _To masoya masu son shiga groups dina kuyi hakuri contact dina is over full, that's why amma yanzu ga number wata kanwata duk mai son shiga tayi mata magana amma pls banda maza cos matar aurece_
 *08100050153*




Husna takowa tayi wurin su Ayan ya Kara daure fuska, ihsan tsaya kallon ta tayi tacikin net dake kanta, hannun ihsan ta kama tana kuka itama ihsan kuka take daman yanzu yazama hobby dinta,
"Babe am so excited for you..." Ta fada mata cikin kuka,
"Pls kin bar fushi dani?.." Ta tambayeta, ihsan Dan goge hawayen ta tayi tare da gyada mata kai, Ayan Dan tabe baki yayi ya dan yi kasa2 da murya Sannan yace
"Ke ban son gulma...ki koma wajenki..." Yayi directing maganar shi to husna, kura mashi ido tayi for just a few seconds tana kara jin sonshi na ratsa ta, da Sauri ta kauda kanta tana goge hawaye, barin wajen tayi Yusuf yabi bayanta da kallo. Introduction akayi inda Muhammad ya bada history din Ayan ita Kuma husna ta bada tarihin ihsan. Ayan kam sai latsa waya yake cos he absent minded at that moment kawai sai ga message din Umma na warning nan take ya ajiye wayan.
Sai karfe 6 aka dauki amarya aka maidata gida, ruwan wanka mai hade da wasu expensive and pleasant kamshi aka hada mata, dakinta duk yan uwan dad da mom ne sai wasu course mate dinta tare da husna, husna kallon kafanta dayasha kunshi tare da kanta dayasha wonderful kitso da akayi da zallan gashinta tayi sai ta kara fashewa da kuka, duk dakin juyowa sukayi suna kallon ta, ihsan dake daure da zani zuwa kirjinta tana niyyan shiga bathroom kallon itama tayi,
"Wannan kukan fa?.." Anty Zuwairat ta tambayeta, cikin kuka ta fara cewa
"Kawai missing dinta zanyi..." Ta fada cikin matsanacin kuka bakin ciki ihsan zata gidan Ayan, baki Anty ta tabe
"Yo in banda abinki ai yau ranar murna ce..Kuma kema aduan Allah ya kawo maki naki zakiyi ba kuka ba...so pls banason ganin wannan hawayen..." Ta fada mata atakaice, husna goge hawayen ta tayi ita Kuma ihsan dake tausayin kanta da na KAWARTA ta shiga bathroom tana kuka, gama wanka tayi sai zuba kamshi take amma taki fitowa zama tayi nan ciki tana kuka, har kusan hour bata fito ba saida Anty taje bakin bathroom din ta buga da karfi ta fito kanta kasa, nan aka zaunar daita aka kara gyara mata fuska, Sannan aka dauko wata pure white Arabian gown mai dauke da alkabba shima white aka saka mata,
 Anty koran yanmatan tayi ta zaunar da ihsan ta fara cewa
"Daughter kina jina?..." Kai kawai ihsan ta gyada mata Sannan Anty ta fara cewa
"Kinga aure ibada ne...kisan cewa babu komai cikin ta sai hakuri...banda yiwa miji rashin kunya ko taurin kai...kisan cewa miji is always ahead of you.. Kar kiyi ta kaman kyau ko wani abu, muddin yaga nakedness dinki ya gama dake so dole ki sauke kanki ki zauna dakin mijin ki..yi nayi bari na bari..did you hear what I said?.." Ahankali ta gyada kai tana kuka,
"Kuma ki kasan mai rike sirrin mijinki...banda yi mashi gardama... Kome yake so indai ta hanyar kwanciya ce indai bai sabawa addini ba kar kiyi mashin gardama cos you are completely his property... Still ina kara fada maki ban da taurin kai... Don yanzu mostly abinda ke kashewa mata aure kenan taurin kai...kina ganin you too big to apologize.. Well for your information you are special when he hasn't get into your pant amma the moment he gets there you are done with so kawai ki sauke kanki kiyi ibada ki nemi aljannanki...." Kukan ihsan ne yasa ta Dan dakatar sa maganar ta, daga mata kai tayi ta goge hawayen ta Sannan race
"Kuma daga kaman yana da rawan kai don haka kome zaiyi maki ki dau hakuri... Duk wani zargi da yake maki za gushe muddin ya sameki budurwa..." Ihsan kam imagining take kwanciya da Ayan azzalumi, ita kawai tsoron shi takeji har na tashin hankali don batasan irin abinda ya tanadar mata ba. Anty na kai Aya suma sauran family suka dinga bata shawara kala kan zamantakewan nan akace ta fito akaita wajen mom, dakin tashiga mom na ganinta ta fashe da kuka, kaman kafan mom tayi tana cewa
"Mom dan Allah kar a tafi dani....pls mom.." Cikin kuka itama mom ta kara bata shawara kala2 Sannan zo daga ta aikam rike mom tayi gam tana cewa
"Mom fitsari zanyi..." Duk mutanen dake dakin Dariya suka farayi. Da kyar aka dauketa daga  dakin aka kaita wajen dad shima bayan some fatherly advice aka dauke ta ihu take yanmata sai Dariya suke mata, da Sauri mom tabi bayansu ta fadawa Anty a fara kaita wajen Umma kafin su wuce.

Shima Ayan yana chan yayi kneeling gaban Umma da Abba ana yi mashi warning tare da advice kan zaman aure, ba karamin advice ya sha ba inda har ya fara Allah yaisa tsakanin shi da Wanda ya turo bashi pic din ihsan don da bai Sani ba da hankalin shi bai tashi kaman yanda yake yanzu, amma yanzu kyaman ta yake don gani yake she been screwed  over and over again
Ji yayi Umma nacewa
"In ka zalunceta ban yafe ba..ka riketa tamkar yanda zaka rike salma kanwarka...ban da cuta ko cutarwa banda zalunci cos I know you with stubbornness...kaji ?" Umma ta tambayeshi, kai ya gyada mata.
"To Allah yayi maka albarka ango..." Abba ya fada yana murmushi. Bai mikeba ya tashi ya zauna nan kasan carpet sai sukaji ana horn a gate, mai gadi ne ya bude aka shigo da motan dake dauke da amarya, ihsan sai kuka take wata yayar mom da wata antynta suka fito da ita adaidai lokacin da Umma ta fito daga part in Abba, ganin ihsan yasa ta saki guda don jindadi, riketa tayi ta tare da rungume ta,
"Kun kawo min yata Dana baku aro..." Umma Tafadawa su Anty, Dariya kawai sukayi suna cewa
"Ai dole a kawota ki samata albarka..." Suka fada mata,
"Naji dadi wallahi.." Umma Tafada tana kaita part din Abba, Ayan dake zaune inda Umma ta barshi taga ta shigo hannun ta rike Dana ihsan, dan daure fuska yayi Umma zauna daita tayi
"Ga daughter..." Ta fadawa Abba, Abba murmushin jindadi yayi yana sa mata albarka, sai da ya gama Umma ta rike mata hannu
"Follow me..." Ta fadawa Ayan Sannan suka koma part din Umma, nan Umma ta zauna ta bawa su biyu advice sosai ihsan sai kuka take, sai da ta gama Sannan ta kara da cewa
"Ki tashi a kaiki gidanki..." Da Sauri ihsan ta kama kafanta tana cewa
"Umma yunwa...nakeji..." Tafada cikin kuka, dukda ran Ayan na bace sai da yayi dariya, itama Umma Dariya tayi
"Daughter kina jin yunwa..." Da Sauri ta gyada mata kai,
"To ki je gidanki zaa a kawo maki abinci.." Da Sauri ihsan a girgiza mata kai,
"Nan..zanci..." Ta amsawa Umma, Umma dai dariya kawai take don ta gane manufarta, dakinta ta kaita yan kai amarya sai jiran amarya suke.
Umma da kanta ta kai mata pepper soup, amma ihsan ko spoon daya batayi ba sai wasa take da spoon, kallon Umma dake kallon ta tayi tace
"Umma don Allah in zauna nan dake..." Tafada cikin sanyin murya, murmushi Umma tayi ta amshi plate daga hannun ta
 Tare dacewa
"Daughter kin San gidan miji shine darajan ya mace...kiyi hakuri a kaiki..daga baya kin zo kinji?..." Cikin kuka ta gydawa Umma kai,
"That's my daughter..." Mikar daita tayi suka je bakin motan da aka kawota ta shiga Sannan suka kama hanyan gidanta.
Ayan kam  komawa  part dinshi  yayi ya kwanta tare da yin rubda ciki yana tunanin irin plan dayayi wa ranar auren shi amma sai gashi ba yanda yaso bane.

Mutanen da basu je gidan ba sai mamakin kyau da tsarin gidan suke, husna ji tayi zata collapsing saboda bata taba zuwa gidan ba sai yau, bango ta dafa ta shiga main falo tana hawaye amma babu mai ganin ta saboda mutane da yawa sukazo. Banda kallon gidan babu abinda take yi ita kam ihsan babu abinda take tunawa kaman irin wahalan datasha ahannun Ayan ranar daya kawota gidan nan amma shine yanzu aka kawota gidan as his wife, ta zauna daga ita sai shi
"Allah have mercy on me.." Tafada suna shiga cikin daya daga cikin bedroom dake dauke da royal bed, kan gadon aka zaunar daita tana kuka, advice aka kara bata Sannan suka tafi ya rage daga husna sai wata cousin din ihsan. Ihsan kamewa tayi waje daya tana jiran abinda zai biyo baya.

Bayan su Muhammad sun ajiye yan dauka amarya sukazo daukan Ayan,  yana kwance har bacci ya fara daukan shi yaji an bude kofa, tashi yayi yana kallon su,
"Kai ango tashi mu kaika dakin amarya..." Muhammad that looks exhausted ya fadawa Ayan yana zama kan kujera, daure fuska Ayan yayi
"Ku tafi mana...ai ba dole bane Ku kaini after all nasan hanya..." Yafada yana Kara kwanciya,
"Kai dalla ka tashi ko mu hada ka da su Umma..." Yusuf ya fada mashi, jin an kira Umma yasa ya mike ahankali ya chanza kaya zuwa shadda, suka bar gidan amma suna zuwa kofar gidanshi ya hanasu shiga, kayan ciye2 da su Muhammad suka saya suka mika mashi kaman bazai amsa ba ya amsa fuskan shi daure. Ciki yashiga ya kulle gate.  Ahankali ya taka ya shiga main falo, mamakin uban kayan wurin yayi ya Dan tabe baki ya zauna kan wani hadadden royal cushion yana imagining how he wish they is no case at hand da yau he would have been the
bi most happiest man on earth. Ahankali ya mike ya ajiye ledan kan dinning Sannan yayi hanyan part dinshi.
 Har ya kai bakin kofan shi ya tuna da magana Umma kan ya kula da ihsan kaman salma yasan duk yanda yake fushi da siblings dinshi bazai taba barin su da yunwa ba, tunawa yayi da ihsan sanda take fadawa Umma tana jin yunwa kawai sai ya kara fashewa da Dariya, komawa yayi ya bude hanyan part din ihsan, nan ma saida yaga kokarin iyayen ihsan don falon ma ba karamin haduwa yayi ba, hannuwanshi ya maida cikin aljihunshi yana kallon daki Sannan ya taka zuwa daya daga cikin bedroom din ya bude sai yaga wata irin beautiful Italian bed ne amma babu kowa, daya ya kara budewa yaga babu kowa sai gadon gargajiya kawai sai ya saki murmushi ya nufi daya ya bude da Sauri ihsan data hada kai da gwaiwa ta daga kanta tare dasu husna, yana ganin su Husna yayi kicin2 da rai, shiga dakin yayi ba ko sallama ya fara cewa
"Wai motan maida mutane gida basu isa bane?..." Ya tambayesu, dukkan su Kansu kasa amma banda husna data kura mashi ido tana kallon lips dinshi dake glowing cikin hasken dakin, shima kura mata ido yayi yana intimidating dinta da idanuwanshi amma bata dauke idanuwanta ba, nuna ta yayi da yatsa yana cewa
"Stop looking at me like that... A said motan da ya kawo sun kare ne da na ganku anan?.." Yafada a tsawace, da Sauri cousin din ihsan ta mike, kallon husna da bata da niyyan mikewa yayi yana cewa
"Ke tashi ki barmin gida...and for the record.. You are not welcome here..." Aikam husna fashewa tayi da kuka bakin ciki ta mike ta dauki bag dinta da Sauri ihsan ta sauko daga kan gado tana kuka sosai, hannun ta Ayan ya kama ya wullata kan gado yana cewa
"It's just us now... You know what that mean..." Ya fada yana daga mata gira.



 *Pls banji dadi sosai in case zaku jini shuru tomorrow insha Allah*
[12/27, 14:12] ‪+234 814 199 1000‬: 💛💙💜🖤💚❤
KAWARTA CE SANADI
💙💜❤🖤💚💛

®zuwairat(ummu Maryam)

4⃣2⃣

 _Wannan Kuma nakune yan *Zuwairat fan 1 to 8,* kuyi hakuri ko one alphabet ne Ku dauka cos nasan kuna da yawa over, Allah ya taimaka ya bar zumunci_

 _Kai jamaa daga na baku number kanwata sai Ku kashe mata waya da  kira? To ta ajiye sim din don haka kuyi hakuri, pls kar wacce ta bi private in yi adding dinta don nima contact dina is full. Nagode da so da kaunan da kuke nunamin._

Ihsan kara fashewa tayi da sabon kuka tana gyara gown dinta da ya danyi sama saboda yanda Ayan ya wulla ta, Ayan tsaya kallon astonishing face dinta yayi for a moment yana mamakin kukan da take,
"Wai precious kukan me kike?... Kina kukan missing guys dinki ne ko kina kukan I might not be a man enough for you...well kwantar da hankalin ki...zan nuna maki nafi sauran guys dinki...amma after every thing sai kin biyani cos am a virgin..." Ihsan kuka kawai take amma deep down tana son Ayan ya kusance ta ko Dan ya bar zarginta.. In Kuma ta tuna irin mugunta shi sai ta gwammace ya cigaba da zarginta don ko mutuwa bata tsoro yanda take tsoron Ayan,
"Yanzu muje kici abinci...cos they is a long night ahead.." Ya fada mata yana tunanin irin dalla dalla da zaiyi mata don before he was thinking bazai kusance ta ba saboda yana kyaman ta amma he was wrong, ganin yanda take sheki yasa ya chanza mind dinshi, kallon ta yayi from her face to her chest ahankali yayi biting lower lip dinshi yana cewa
"Ki taso kici abinci..." Ya fada fuskan shi daure, cikin kuka tace
"Na koshi..." Kallon ta yayi yakara hade rai
"Baa fada maki baayiwa miji gardama ba?.. Ko kina tunanin ni saurayin ki ne!.." Ya daka mata tsawa, da Sauri ta ja baya saboda yanda voice dinshi ke tashi
"Kina cin abinci ko sai na saba maki kinsan halina ba sai an fada maki ba..." Da Sauri ihsan tace
"Zan...ci..." Ta fada cikin kuka,
"Good...follow me..." Ya fada yana barin dakin, da Sauri ta mike tana kuka ta ajiye alkayba kan gado daga ita sai hulan gown dake jikinta fari tas, Ayan main falo ya fita ya zauna kan dinning yana bude kayan da aka  sayo, jin bude kofa yasa ya kalli ihsan dake fitowa tana goge hawayen ta,
"Ke dauko min plate da cup..." Yafada mata, babu musu ta koma ciki ta duba dukkan room amma babu kitchen, kara fitowa tayi Ayan kallon ta yayi
"Wai INA plate din?..." Ya fada ciki tsawa,
"Ban ga kitchen ba..." Ta fada cikin sanyin murya, kura mata ido yayi for a few minutes ya dauke kanshi yana tsoki,
"Pls ina kitchen yake?.." Ta tambayeshi muryan ta na cracking,
"Ban saniba ...pls give me plate before I descend on you..." Ya daka mata tsawa, rawa jikinta ya fara ta nufi hanyan part dinshi sai ta tuna kikan irin part dinta ne sai ta bude middle door nan taga kitchen hade da store, plate ta dauko tare da cup ta daure shi a sink Sannan ta fito dasu jikin ta sai rawa
 Ayan sai kallon yanda take rawa kaman Kazan da aka tsoma a ruwa yake, wani irin dariyan rainin hankali ya saki yana cewa
"Sai wani kyarma kike kaman ba ke bace mai.kirana da bunsuru..." Yafada yana kara daure fuska, ihsan ajiye plate din tayi gabanshi zata koma ya kama hannun ta yana kallon face dinta, ahankali ya daga hannun ta zuwa wurin nose dinshi, ahankali ya lumshe idanuwan yana cewa
"Baby wannan kamshin can make man go gaga..." Yafada in a naughty way, Sannan ya saki hannun ta,
"Serve me..." Ya umarceta, ba musu ta matso kusa dashi ta fara zuba mashi, Ayan sai kai hancin shi jikin ta yake yana lumshe idanuwa yana cewa
"Kawai am feeling as I should chew you raw...wallahi wannan kamshin daban ne...kin taba shafa irin wannan turaren when visiting your boyfriend?..." Ya tambayeta cikin tsawa, jikinta na rawa tace
"Pls..." Da Sauri ya kamata ya dorata kan lap dinshi yana cewa
"Shush...tell me the truth..." Ya daka mata tsawa idanuwanshi da chanza kala, ihsan sabon kuka ta fara sai shessheka take, Ayan tsaya kallon ta yayi yana mamakin yanda wasu suke tamkar su sukayi creating Kansu,
"I wish you heart is as pure as your face..." Yafada cikin whisper idanuwanshi lumshe bakinshi kan chest dinta,
"I wish we are all new...precious kar kiyi fushi dani..imagine ace you were in my shoes...kin yi karatu cikin inda yan mata ke walking half naked amma kika kama kanki all because you don't want Allah to give you a second hand person as a partner.. Amma after everything you still end up with a slut... What will you feel?..." Ya tambayeta, cikin kuka ihsan tace
"Am..not...a...slut...." Tafada tana kuka kaman ranta zai fita,  bakinshi ya Dora kan nata amma baiyi kissing dinta ba yace
"We shall see..." Yafada ya bude idanuwan shi tare dacewa
"Feed me..." Ya umarceta, kokarin mikewa daga kafan shi tayi ya riketa
"Sit here and feed me..." Ya fada atakaice, ba musu ta cire hulan dake kanta ta goge swollen face dinta Ayan kallon kitson kanta yayi ya kara kai bakinshi kan gashi ta sai lumshe idanuwa yake yana shakan kamshin, ahankali ihsan ta fara debo pepper chicken don ta kai bakinshi sai taga his eyes are closed, shuru tayi itama tana kallon shi, ahankali ya bude ido yaga tana kallon shi
"Admiring this fresh boy ko?.." Ya fada yana bude mata baki don ta sa mashi abincin, shima  daukan nama yayi ya kai bakinta amma taki bude bakin,
"Open.." Ya fada mata, ahankali ta bude bakinta cikin mugunta ya tura mata nama Wanda tafi karfin bakinta
 Ahankali ta fidda ta ajiye ta cigaba da feeding dinshi yana ci yana lumshe idanuwa kaman mai jin bacci, saida yaci sosai ya bukaci ta zuba mashi non sugary drinks ta zuba ta bashi yasha enough Sannan ya bude idanuwa ya fara kallon chest dinta yana tunanin an gama latse su,
"Muje ki koya mani abinda ban Sani ba kin San am novice..." Yafada yana kara noticing wani abu game da kanshi, ya lura tunda ihsan ta zauna kanshi Kuma he's feeling horny he should rise as a man amma nothing, kawai the is in his heart but not down there, amma still he wasn't thinking is something serious, kawai he thought is stress,
"Stand ya umarceta,.." Mikewa tayi daga kafan shi ta fara tattare wurin da ta bata, Ayan relaxing yayi yana kallon medium sized hips dinta, tana kai plate kitchen ya mike ya shiga part dinshi ya rage kayan jikin shi ya rage daga shi sai boxers, ihsan na tsaye bakin kofan kitchen tana adua kala2 cikin ranta, Ayan ta gani ya fito da boxer da Sauri ta sauke kanta gabanta na faduwa, karasowa yayi kusa daita ya fara kokarin daga kanta amma taki, bata ankaraba ya hada ta da bango yana cewa
"Do me..."
"Wayyo "ihsan ta fada saboda yanda kanta da bayanta yayi magana, bakin su y hade yafara kissing dinta in a rough and arrogant way, kuka ta hawaye kawai ta fara amma batayi yunkurin hanashi ba, daman she promise herself one thing shine bazata hanashi abinda yayi niyya ba amma when he's done she will make sure be regret it, yana kissing dinta ya kaman boobs dinta da two hands dinshi yana wasa dasu in a mean way, ihsan sai kuka take tana aduan she should survive through the night, kawai wasa yacigaba dayi Kuma ba wai an ahankali ba no, cikin mugunta da zalunci, ihsan sai hawaye kawai take amma banda kuka don sam babu baki Ayan ya mallakesu, duk yanda yake murza mata jiki cikin keta bata yi yunkurin hanashi ba, ahankali ya fara slowing down yana noticing abinda ke faruwa don har wannan lokacin babu erection tattare dashi, tsayawa yayi likeda ita a jikin bango yana tunanin hope something is not wrong with him, still romance ya cigaba amma still nothing,
" inna lillahi waina ilaihi rajuun!!!.."  ya fada cikin ranshi, Dan tureta gefe yayi ya koma ya zauna nan kasa, da Sauri ihsan ta shiga part dinta tana hawaye

"What happening to me?..." Ayan ya tambayi kanshi, da Sauri ya mike ya shiga part dinshi yana cewa
"What is wrong with me?...something is definitely wrong... This is not me..."
 Yafada yana cire boxer dake jikin shi, kanshin ya fara kallo yana cewa
"This can't be me...something is wrong..." Ya fada yana kallon nakedness dinshi,
"Oh my Allah what is wrong with me!..." Ya tambayi kanshi cikin tashin hankali, ahankali ya fara sauke ajiyar zuciya yana cewa
"Calm down.,is nothing serious... Maybe saboda you are tired of seeing her naked..." Yayi assuring kanshi, haka ya dinga tawa kanshi hankali Sannan ya kwantawa kanshi hankali.

Ihsan kam tana shiga ta kwanta tana kuka ahaka har bacci yayi gaba daita, Ayan kam ko kadan bai yi bacci ba cos yana gani Yana da matsala babba while wata zuciya na fada mashi ya kwantar da hankalin shi don is nothing, ahaka ya kwana yana tunanin kala2 he couldn't believe ya kwana cikin gida daya da ihsan without anything, yanda ya Dade ya hakkon ta.

Sai 7:30 ihsan ta tashi, da Sauri ta shiga wanka ta fito daure da towel, gown din jiya ta maida ta fita don tambayan Ayan kibla, bakin kofan ta tsaya amma ta rasa courage din shiga, tafi minti biyar tsaye bakin kofan Sannan taga bude ahankali gabanna faduwa ta shiga falon da sallama shuru taji alaman babu kowa, ahankali ta karasa bakin kofan da ya taba kaita don ta tabbatar nan ne bedroom dinshi, bakin kofan ta tsaya rana sallama amma babu amsa tayi sallama kusan sau biyar babu amsa Sannan ta bude kofa, ahankali ta shiga da Sauri ta juya baya don Ayan ta gani zaune babu komai jikinshi Kuma da alaman baya cikin hayyacinshi, shigan ihsan dakin ya maidoshi hankalin shi, gani ta juya baya yasa ya saki tsoki yana cewa
"Ke baki Iya gaisuwaba?..." Ya tambayeta bai da niyyan rufe jikinshi, ihsan dai jikinta kyarma kawai yake, bata kalleshi ba ta ce
"Ina kwana?.." Hararanta yayi,
"Haka ake gaisuwa?..." Yafada yana kallon bayanta ji yake he should just drag her to bed and do what pleases him with her amma the man in him is disappointing him, da Sauri ta Dan durkusa ta kara gaidashi amma still bata juyoba, baki ya tabe yana cewa
"Munafuka kawai...uban me ya kawoki dakina?... " da Sauri tace
"Pls ina ne kibla?..."
"Inda kike kallo yanzu..." Ya fada mata atakaice, da Sauri tayi niyyan fita amma sai yace
"Ihsan.. Da kin idar da salla ki zo...don I need to give you my house rules and regulations..." Yafada yana mikewa, ihsan bata bashi amsa ba ta fita daga dakin shima bathroom ya shiga ya sakarwa kanshi ruwa.

Bayan ta idar da salla ta bude wardrobe dinta ta dauko skirt da riga na material mai tsada ta saka ta daura dankwali anyhow amma still she looks beautiful, gaban mirror ta tsaya tana tunanin what to do next don ita a yanzu her life seems upside down amma one thing she is happy about shine yanda tayi tunanin Ayan zai yi mata ba haka abun ya kasance ba don tana tunanin he won't take it easy with her amma sai gashi ta kwana lafiya, tana cikin tunani taji an bude kofa da Sauri ta juyo tana kallon Ayan dake sanye da three quarter na Burberry da pure white polo
"Me nace maki dazun?..." Ya tambayeta, da Sauri tace
"Yanzu nan...na idar da salla.." Tafada muryan ta na rawa, harara ya watsa mata
"Amma Dana shigo ba salla kike ba..you were busy admiring you innocent beauty... Anyway ki biyoni..." Yafada yana fita daga dakin, bayanshi tabi da harara Sannan tayi saurin binshi, a main falo ya zauna ya Dora kafa daya kan daya yana girgiza su ahankali kaman wani sarki, ahankali ihsan ta rako ta zauna kan wani kujera tana tunanin abinda zai fada mata yanzu Kuma, kallon ta yayi suka Dan kurawa junansu ido sukayi for a while ihsan tayi saurin dauke kanta
"Kina jina?..." Ihsan daga mashi kai tayi kaman wata sakara,
"First of all... Nayi niyyan daukan mummunar mataki kanki for playing with my heart... Amma ki godewa Umma don ta yi min kashedi da hakan..nace kaidai fadi gaskiya... Don haka zan baki rules Wanda in kika bi zamu zauna lafiya har Allah yasa  in yafe maki abinda kika yimin ko Kuma ince har Allah yasa in samo wacce ke daidai dani...na farko..kar kiyi min magana in bani nayi maki ba..if you need anything put it in writing..
 Na biyu kar ki sake ki fita bada izini na ba...na uku banson zuwan kawayenki na banza nan gidan...na hudu kar ki dafa abinci dani...ki dafa daidai yanda zakici...na biyar banson kazanta...you make sure you take care of my part every day...na shidda kar ki kulle any part na gidan nan cos gidana ne Kuma ina iya shigan duk inda nake so at any time.. And the last one shine zaki dakatar da zuwa school until further notice... " da Sauri ihsan ta kalleshi hawaye na taruwa idanuwanta,
"Pls...zan bi all instructions dinka...amma pls kar ka dakatar min na zuwa makaranta..." Harara ya watsa mata
"Eh wato don ki fake da school kiyi abinda kika saba ko?..to not under my watch.. Kuma wallahi ko daidai na kofar gida kika fita kare bazai ci abinda zanyi maki ba...am I clear?..." Cikin kuka ta gyada mashi kai,
"Good... Any questions?..." Ya tambayeta, ahankali tace
"Ina Iya gaidaka?..."
"No need..." Ya amsa mata atakaice, ihsan dai tasan aure kaman yanda iyayenta suka fada mata ibada ne, Kuma ita she was expecting more than this
"Alhamdulillah..." Ta fada cikin ranta amma ko kadan bata ji dadi hanata zuwa school dayayi ba amma an fada mata ba ayiwa miji gardama Kuma an fada mata the patient dog always eat the fattest bone. Door bell da aka latsa ya maidota cikin hayyacinta, ahankali Ayan ya mike ya nufi kofa ita Kuma ta mike ta nufi part dinta
[12/27, 14:12] ‪+234 814 199 1000‬: ❤💙💜🖤💚💛
KAWARTA CE SANADI
💛💚❤🖤💙💜


®zuwairat( ummu Maryam)



4⃣0⃣



 _Wannan naku ne yan *Zuwairat novel 1* sarakunan surutu, kowacce ta dauki word daya kilan ya ishe Ku, in bai isheku ba just let me know, I love you, Ku kuma yan saudiya kuyi mana adua Allah yasa mu adanshin ku._


Kuka sosai mom take Wanda hakan yasa hankalin ihsan yatashi,
"I know he raped you...shiyasa kika tsaneshi all of a sudden... Kin cuci kanki...da kin fadamin yace ki rakashi wani wuri da ban taba yarda ki bishi..amma dayake bani da daraja idonki kika tsallakeni kika fadawa kawar ki..." Mom Tafada cikin kuka tana doso inda ihsan take,hannu ta fara yarfawa tana cewa
"Wallahi mom kiyi hakuri... Sharri shaidan ne...wallahi baiyi nasara ba..." Wani irin mari mom ta dauketa dashi
"Yau saikin fadamin wacece uwarki..." Mom ta fada tana descending kanta da duka, banda ihun ihsan babu abinda kake ji, mom na dukan ta ita kanta tana kukan bakin ciki, da kyar Anty tan amshi ihsan daga hannun ta,
"Nasan he used her...shiyasa shi kanshi ya barzuwa...to listen to me...ahaka zaki aure shi... Bari ubanki ya dawo" mom Tafada cikin kuka tana kokarin fita daga dakin, Anty rike ta tayi ta zaunar daita kan kujeran mirror tana cewa
"Sis kiyi hakuri... Don't let my brother know about this... Dole at times mu rufawa yaran mu asiri ..." Da Sauri mom tace
"Ai ita bata rufawa kanta asiriba...gashi ta fadawa kawa abinda bata fadamin ba...wallahi ranar data dawo babu irin magitar da banyi mata ba amma kiri2 tace babu komai... I beg my daughter to tell me what the problem is amma taki fadi..." Yanda mom k e magana kasan ranta bace yake matuka, dafa shoulder ta Anty tayi tana cewa
"kiyi hakuri...yaran zamani sai hakuri..mu lokacin mu bamu da kawaye sai iyayenmu mata... Pls kinga yanzu sauran few days bikin kar ki fadawa yaya kar a samu matsala,.. Kawai muyi fatan ayi wannan auren lafiya..in sunje Chan suyi settling Kansu..." Tafada tana share hawayen dake fuskan mom, barin wajen mom tayi ta koma wajen ihsan dake kukan bakin ciki saboda amanarta da husna taci Sannan kukan yanda tasa mom hawaye, hannun ihsan Anty ta kama
"Hajiyata...ki fadamin gaskiya.. Nothing but the truth.. Yayi raping dinki?.." Da Sauri ihsan ta girgiza mata kai tana hawaye, cikin kuka ta fara cewa
"Cewa yayi an turo...mashi... Nude pic dina...yace na
..." Kuka ne yaci karfin ta, Anty kallon mom dake hawaye tayi Sannan tace
"Sis what is she talking about?.."
"Oho mata...AI ban San matsalar ta ba...ita tasani..." Mom ta amsawa Anty atakaice, cikin sanyin murya Anty tace
"Na gaske ne ya nuna maki?..." Da Sauri tace
"Aa..bai nunamim ba...nasan karya yake..." Tafada cikin kuka sosai , shuru Anty tayi tana murza hannun ta ahankali
"Hajiyata.. Kinsan wannan rayuwan mutum baida amini kaman uwa...don ita kadaice zata rufa maki asiri.....yanzu duk yanmatan da kike gani uqayensu ne aminansu... Kar ki bari wata ta kara Sani wata matsalan ki sai da amincewar mahaifiyarki...kina jina?.." Da Sauri ihsan ta gyada mata kai tana cewa
"Mom kiyi hakuri...ban karawa..." Tafada cikin kuka, Anty tacigaba dacewa
"In kina jin kunyar mahaifiyarki..kina Iya fadawa janna...itama yanzu ba yarinya bace...you can share some of your problem with her... Daga wajenki zata samu experience na rayuwa..." Inji Anty,
"Ai wannan yarinyan bata dauki janna bakin komai ba..ban tana ganin su suna hira na minti daya ba..." Inji mom,
"Haba hajiyata...that is very wrong and bad...kin taba ganin inda sisters da sauka sha nono daya suka tonawa junansu asiri?..." Kai ihsan ta girgiza mata,
 Anty tacigaba dacewa
"That is because nonon uwar is like a convernent...da akwai bond.. pls don't let a third party in your life... Wasu suna Neman uwa ke Kuma kina dashi but you are taking it for granted..." Anty ta fada mata cikin tattausan lafazi, Anty matsawa tayi kusa da kunnen ihsan Sannan tace
"Yanzu baby in banda abinki..kina ganin wancan kawartaki zata ji dadi da kullum ke ake sawa biki?.." Ihsan tsaya kallon Anty tayi don ko kadan bata taba tunanin husna zata Iya bakin ciki da wani samun nata ba, nace pls dummy think again,
"Wallahi kawaye are dangerous.. Pls daga yau kar ki kara sharing anything secret...kinji?..." Ahankali ihsan ta gyada mata kai,
"Good gal...yanzu kije ki bawa mom hakuri..." Tafada tana goge mata hawaye, ahankali ihsan ta sauka daga kan gado  ta je gaban mom dake zaune har lokacin hawayen ta bai tsaya ba, kneeling tayi gaban mom tare da dora hannun ta kan laps din mom ta fara cewa
"Mommy.. Am sorry... Kiyi hakuri.. Bazan karaba ..." Tafada cikin kuka sosai, mom goge mata hawaye tayi
"Ambaby..kinsan I love you... Ki bar boyemin komai... Am you mother.. I will never lead you astray..." Mom ta fada mata cikin whisper,
"Am sorry...kawai inajin kunyane.."
"No...share every thing with me...I mean everything..."
"Yes mommy... Pls don't tell daddy..." Mom shuru tayi batace kala ba, Anty daga ihsan tayi ta zaunar daita kan gado ta cigaba da bata advice kala2, daga baya mom mikewa tayi ta a barsu nan, suna cikin hira husna tashigo sai sukayi shuru, husna Dan Satan kallon ihsan tayi suka hada ido aikam wani irin disgusting look ihsan tayi mata Wanda yasa gabanta faduwa, Anty barin dakin tayi husna ta zauna kusa da ihsan, aikam ihsan mikewa tayi ta bar mata dakin, harara ta husna tayi
 Dakin janna ta shiga tana shiga husna ta biyo ta zauna kusa daita ko kadan fuskan ihsan bai da kyau don ko kadan batason ganinta dafa shoulder dinta husna tayi da Sauri ihsan ta buge mata hannu
"Babe ba dai kina fushi daniba?..." Ta tambayi ihsan, banza tayi daita
"Haba pls kar kiyi fushi,..." Bata idaba ihsan ta mike ta daga mata hannu tare dacewa
"Pls...stop it...na fada maki sirrina...ki tona min asiri... Kin hadani da mom..kin kyauta...ai gobe ma rana ce..." Ihsan ta fada mata tana kara barin dakin, dakinta ta koma ta kwanta, husna shigowa tayi ta fara hada bag dinta ko kallon ta ihsan batayi ba har ta gama ta dauki bag dinta bata cewa ihsan zata tafi ba likewise itama ihsan bata cemata sai anjuma ba, tana sauka downstairs ta fashe da kuka, mom tambayan ta tayi matsalan sai ta fada mata abinda ihsan tayi da Wanda ihsan batayi ba, rarrashin ta mom ta tayi amma kiri2 taki ta tafi, Janna kam ranta kwal cos ta gaji da zariyan husna gidansu.

Yau aka fara wedding event inda har lokacin ihsan da husna basu shirya ba, da kauyawa party aka fara inda Muhammad da Yusuf sunyi rawar ganin don su duka zama tamkar Ayan don har dinki su suka am so da dukkan event din da zaayi Ayan kam ko ajikin shi, da kyar suka samu ya shirya cikin kayan da aka tanada saboda kauyawa  party, gidansu cike da guys sai zolayan Ayan suke amma ko Dariya baiyi balle ya amsa masu, wani farin guy cewa yayi
"Wallahi yanda kake wannan kumbure2.. In har muga ka matar ka da ciki sai mun cima uwa ....." Banza yayi dashi, Muhammad ne ya je wurin Umma dake zaune cikin mutane ya rada mata magana cikin kunnenta, sai Umma tace
"Ka kira min shi..." Ta fada mashi, da Sauri ya koma bayan minti biyar sai ga Ayan tafe da riga daban da wando sai wani faded cap, su salma sai Dariya suke mashi amma sai kara murtuke fuskan yake, Umma na ganin shi ta mike yabi bayanta, wani daki ta shiga yana biye daita, yana shiga ta kulle kofan Sannan ta nuna shi da yatsa tana cewa
"Kasan wallahi ka shiga hankalin ka...sai kumbure2 kake salon ka nunawa mutane bakason aurenko?..to wallahi in har kayi misbehaving har a gama auren nan ban yafe ba...in har ka fada mata wata magana Mara dadi ko da batanci ban yafe ba..." Ayan kallon Umma kawai yake hawaye na taruwa idanuwanshi,
"Kaji ko baka ji ba?..." Da Sauri yace
"Naji..."
"Very good.. Now saki ranka..." Ta umarceshi, Dan sakin ran yayi amma still fuskan babu kyauwun gani
"Shegen ko ina ka dauko wannan fuskan oho ..." Tafada tana barin dakin, Ayan tsayawa yayi ya shanye hawayen Sannan ya fita daga dakin ya fito suka tafi.

Itama ihsan gidansu cike da yanmata kala2 masu aji da swags, shirya ta akayi cikin local dress sai hawaye take, husna bata zo ba daman she can bear seeing ihsan da Ayan don haka sai ta gane da abinda ihsan tayi mata, mami har kusan dukan ta tayi amma dayake taurin kai gareta kaman arnan farko kin zuwa tayi.
Awajen party kam ko word daya bai hada Ayan da ihsan ba kowa harkan gaman ta yake don ko minti talatin ihsan batayi wajen ba ta koma cikin mota ta zauna.

A haka aka dinga wedding events su biyu na haduwa amma ba mai cewa juna kala, shi Ayan yaso ya dinga yi mata rashin mutunci amma bayason Allah yaisan uwa ta nishi don haka ko inda take bai kallon gashi ba karamin haduwa suke ba don sai ya dinga Satan kallonta yana mamakin yanda ta koma amma fa kyauwunta na dan rikatashi, guys sai zolayan Ayan suke suna cewa
"Ashe kana da ido?..."
 Suka fada cikin faraa.

Ahaka akayi all events banda husna. Yau aka daura aure kan sadaki dubu 50 inda ba karamin mutane suka hallaci daurin auren ba don street dinsu cike da motoci, Ayan kam sai ajiyan zuciya kawai yake. Itama ihsan kuka kaman ranta zai fita, sai da taga zata sha duka tayi shuru, daman reception follows immediately after dauri aure, kwalliya ake mata amma hawaye bai Bari, daga karshe dai da light makeup aka barta inda tasha blue gown mai hannun net, fadin haduwan ta is a waste of time amma ta hadu sosai shima Ayan shiryawa yayi cikin blue suit tare da taimakon su Muhammad.

Dukan tsiya mami tayiwa husna Sannan ta shirya cikin angon su ta taho sai kuka take amma ba kukan dukan mami take ba, kukan yanzu ihsan ta zama matar Ayan despite all her effort kawai take, tana zuwa t and j concept ta shiga hall inda Ayan da ihsan ke zaune kan reserved area, fuskan ihsan lullube da net, sai share hawaye take, Ayan dake zaune kusa daita najin shessheka da takeyi, Dan matsawa yayi kusa da kunnenta Sannan yace
"Is not late..all hope is not lost... In jar kika mike ki ce bakison wannan auren cikin wannan mutanen.. Ni Kuma nayi maki alkawarin baki takarda yanzu nan cikin mutanen nan...pretender...." Yafada Sannan ya maida idanuwanshi kan mutane yana murmushi kaman maganar kirki ya fada mata saboda yanda Umma ta tsare shi da idanuwa, husna kusan sumewa tayi ganin yanda Ayan ke radawa ihsan magana cikin kunnenta,
"Wallahi ba destiny ba...ko uban meye...sai na raba Ku..." Tafada thinking acikin ranta ta fada not knowing she is sanyin it loud amma still dayake dubunta bai cika no body heard her saboda sound of music
[12/27, 14:14] ‪+234 814 199 1000‬: 💙❤💜🖤💚💛
KAWARTA CE SANADI
❤💜💚🖤💛💙

®zuwairat( ummu Maryam)

4⃣3⃣

 _To yan *team ihsan and Ayan* da yan *KAWARTA CE SANADI fan group* wannan page nakune, thanks for the compliment, inason more than yanda kuke sona, Allah ya bar zumunci_

Yana bude kofa yaga antymu da driver din Umma niki2 da manyan food warmer, da Sauri antymu ta shiga cikin falon bakinta bude,
"Yaya..gidanku is beautiful... Pls in zauna nan?..." Ya fada tana karewa falon kallo, Ayan daure fuska yayi
"Kin gaidani?…." Dasauri ta dawo ta durkusa ta gaidashi, sai lokacin ya sakar mata fuska, antymu sai kallon falon take kaman wata yar kauye, abinci suka jera kan dinning Sannan antymu tace
"Yaya ina Anty ihsan?.."
"Tana dakinta..." Ya fada yana zama kan dinning,
"Bari inje in gaida ta..." Ta fada tana kokarin barin inda Ayan yake, da Sauri ya rike mata hannu
"Kiyi feeding dina tukunna..." Ya fada mata, babu musu ta dawo ta zauna, abincin ta bude naman ta saba serving da feeding dinshi so wannan ba wani abu bane wajenta, sai da ta bude ta sauka daga kan dinning bayan ta tambayi Ayan inane kitchen ya nuna mata taje ta dauko plate da ruwa daga cikin fridge ta dawo ta fara feeding dinshi sai hira suke tana bashi abinci, bai wani ci sosai ba yace ya koshi, sai lokacin ta mike ta nufi hanyan part din ihsan baya Ayan ya nuna mata wurin. Da sallama ta shiga da Sauri ihsan dake kwance kan long kujera ta mike zaune tare da goge fuskan ta da Sauri don kar a gane tayi hawaye, murmushi ta sakar mata tare matsa mata don ta zauna kusa daita, gaidata tayi kaman yanda ta gaida ayan sannan ta zauna, fuskan ihsan dauke da murmushi kaman ba kuka take kafin ta shigo ba
"Anty Umma ta bani abinci in kawo maku...har yaya yaci.. Kema taso kici..." Antymu ta fada mata, ihsan dai bataci komai ba Kuma batajin yunwa saboda abinda ke damunta ma is enough for her, amma batason yiwa antymu gardama sai cewa tayi
"To...amma ki kawo abincin nan?.." Ta fada mata, da Sauri ta mike ta fita ta tarda Ayan ya koma falo ya zauna idanuwanshi lumshe kaman mai bacci, daya warmer ta dauko ta kai part din ihsan ta kara dawowa ta dauki sauran. Anan bangaren ihsan suka ci abinci tare da antymu dukda ihsan bawani ci tayi ba. Suna gamawa antymu ta tattare wuri ta dawo suka kunna kallo. Ayan dake zaune falo ko minti goma baiyi ba bacci ya daukeshi.

Abangaren husna kam sabuwar wahala ta shiga don kuka ta kwana yi tamkar ance her days are numbered, yanda taga rana haka taga dare, sai bayan sallan asuba bacci ya dauketa, bata farka ba sai after 11 da Sauri ta dauki wayanta ta kira number ihsan don samun rahoton yanda suka kwana jiya,
Ihsan dake zaune da antymu taji karar wayanta a bedroom da Sauri ta je ta dauki wayan
"Babe ya kike?.." Ta tambayeta cikin sanyin murya, daga Chan bangaren husna ta sakarwa wayan harara Sannan tace
"Lafiya lau amarya..how was your night?..."
"Alhamdulillah..." Kawai ihsan ta amsa mata, husna bata rai tayi cos that is not what she wants to hear
 "Bangane alhamdulillah ba...kunyi first night jiya kenan?.." Ihsan dan Dariya tayi har zata fada mata exactly abinda ya faru juya sai Kuma ta tuna da irin advice da aka bata especially kan rike sirrin miji,
"Hmm babe you are funny... Kawai sai in kama fada maki abinda mukayi jiya?..." Tafada tana dariya, husna zaro idanuwa tayi don anata tunanin anyi an gama,
"Yanzu babe daga aure har kin chanza min...yanzu kina son ki nuna min kin fini wayewa yanzu..babu komai.. Daman Ayan bayason friendship dinmu, yayi succeeding wajen raba mu..." Tafada kaman zatayi hauka don at that moment ranta baki wulik,
"Ba haka bane...kawai dai..." Sai Kuma tayi shuru,
"Hmm wato jiya Ayan ya gane you are innocent kenan..." Ahankali ihsan tace
"Aikam dai..." Da Sauri husna tace
"Pls tell me...babe kunyi XXX jiya?.." Husna ta tambayeta tana dafa kirjinta saboda yanda take bugawa da karfi,
"Hmmm...babe wannan Kuma sirri ne..." Ta amsa amsa mata
"Yanzu Ayan ya kwanta dake?.." Husna ta tambayeta sounding annoyed, Dan bata rai ihsan tayi
"Babe wai wane irin tambaya ne wannan?.. Ai babu dadin ji ma Wallahi..." Kawai husna fashewa tayi da kuka tana cewa.
"Yanzu shikenan har nayi laifi?..before muna sharing everything.. Yanzu don kinyi aure banyi ba shine kike Neman juyamin baya ko?..ba matsala.. Nima watarana zanyi aure..zanji yanda kuke ji..." Ta fada cikin kuka sosai , duk jikin ihsan mutuwa yayi don tana ganin she's not been fair
"Kwantar da hankalin ki..babu abinda nake boye maki...babu abinda ya shiga tsakanina dashi..." Tafada mata, husna Dan cire wayanta tayi daga kunnenta ta saki ajiyar zuciya tare da murmushi Sannan tace
"Lallai...har ina tunanin kin wuce wurin ace har yanzu novice ce..." Dariya ihsan tayi Kawai,
 "Yo ina angon?..."
"I think yana main falo..."
"You think Kuma?..." Husna ta tambayeta sounding relieved,
"Babe zan kiraki anjuma INA da bakuwa..." Ta fada mata, bata tsaya sauraron amsarta ba  ta katse wayan ta, husna ajiye wayan tayi tana dariyan jindadi, amma still har yanzu bataki ihsan ta bar gidan ba
"One step at a time.. Baby..." Ta fadawa kanta.

Sai 12 Anty ta tafi tare da driver har lokacin Ayan bai farka daga bacci ba, tafiya tayi bata tasheshi ba don tasan halin yayanta bayason ana katsemashi  bacci.

Antymu na tafiya ihsan ta kwanta itama bacci ya dauketa.

Sai bayan sallan zuhr Ayan ya tashi tare da adua, ya shiga part dinshi ya watsa ruwa tare da alwallah ya fito ya saka jallabiya ya fita zuwa masjid bai dawoba sai da yayi sallan asar. Yana zuwa shiga part din ihsan ya ganta kwance kan kujera tana bacci, karasowa yayi ya dalla mata duka a bombom tayi saurin mikewa
"Kinyi salla?.." Shine tambayan da yayi mata, da Sauri ta mike tana kallon time, ko kallon shi batayiba ba shiga bedroom tayi alwallah tayi sallan zuhr da asar Sannan ta shiga wanka ta fito tare da gyara face dinta Sannan ta chanza kaya zuwa doguwar gown.
Ayan zama yayi nan falon ta ya dauki wayanta dake kan kujera ya fara bincike yana duba contact dinta ko zaiga komai suspicious amma bai ga number wani na miji cikin wayanta ba don har number dinshi babu cikin wayanta,
"You are good in covering your track..." Ya fada yana ajiye wayan, relaxing yayi ita Kuma ihsan ta fito babu dankwali kanta, bata kalleshi ba ta fita main falo yabi bayanta da kallo yana tunanin nothing is standing in he's way tonight, ihsan kitchen ta shiga ta na kallon yanda aka cika kitchen din da kaya kala2, wasu kayan ma batasan sanda aka sayesuba, cikin store ta shiga ta shima lode da kayan abinci kala2 don tunda ita kadai zata dinga ci sai sunyi years kafin su kare. Yunwa takeji amma batasan abinda zata girka ba, tsayawa yayi for moment kaman mai tunani Sannan ta dauko snacks da aka hada mata Sannan ta hada extra thick tea ta fito falo rike da plate da cup, bata zauna kan dinning ba ta zauna kan kujera tana cin abinta tare da sha tea,
"At least am having a little bit of rest of mind ..." Ta fada cikin ranta, saida ta gama ta maida plate kitchen ta dawo tayi relaxing hankalin ta kwance, shima Ayan falon ya dawo ya zauna bayan ya kunna kallo, few minutes later da zaman shi ihsan ta mike ta bar falon.

A wannan Daren ma sai da Ayan yayi kokarin kwanciya da ihsan amma to no avail, sai lokacin ya tabbatar his in trouble, kallon ihsan dake kwance kusa dashi yayi yace
"Ke what have you done to me?..." Ya tambayeta muryan shi na rawa kaman zaiyi kuka,ihsan sai batasan inda ya dosa ba so bata amsa mashi ba, da Sauri ya girgiza ta yana cewa
"Tell me what you did to me...why haven't I been able to sleep with you?..."
 Ya tambayeta cikin tashin hankali, ko.kadan bata gane inda ya dosa ba, da Sauri ya tashi daga kan gadonta   kasancewan dakin ta ya sameta, barin dakin yayi ya nufi part dinshi yanda yake tafiya is enough agane something is wrong with him
"Am I impotent?..." Shine tambayan da yayiwa kanshi , da Sauri Kuma yace
"No... It can't be...ya zaayi all of a sudden ace am impotent?...no..no...no..its not possible..." Dafe kanshi yayi Kawai sai ya saki kuka yana cewa
"Wa zan fadawa I can't be able to perform as a man?... Wa zan fadawa wannan abun kunyan?... Inna lillahi waina ilaihi rajuun!!!..." Yafada cikin matsanacin kuka,
"Ya Allah wake me from this bad dream... It can't be real..." , sai sweating yake dukda sanyin dake dakin, da Sauri ya shiga wanka tare da alwallah ya fito ya sanya jallabiya
 Praying mat ya dauka ya fara jero sallan nafula daga baya ya dauki alquran ya dinga reciting yana kuka, still a wannan ranar ma baiyi bacci ba kwana yayi tana adua don yasan ba lafiya.

Ahaka rayuwarsu ya cigaba da gudana inda kullum Ayan sai yayi kokarin amsan hakkin shi gu ihsan amma bai iyawa har ya hakura ya bar damunta don gani yake abun ya zama abun kunya, har sukayi sati biyu babu abinda ya shiga tsakanin su Kuma ba wai bayaso ba  amma the man in him is never rising, yanzu kam ya shiga damuwa sosai  don duk ya rame ya koma kaman ba shi ba har wasu hospital ya je aka duba shi aka tabbatar mashi he's okay don bai da medical problem, Kuma yana jin kunyan yafadawa kowa wannan matsalan, yanzu ya kusa sati daya bai ga ihsan ba Kuma bai da niyyan ganinta cos he's a shame of himself.

Ihsan kam ta fara dawowa jikinta don no more cry the only time take dan raba kuka shine duk sanda Ayan ya nuna yana bukatan wani abu daga gareta amma banda wannan bata da anymore problem besides yanzu hankalin ta kwance yake don kusa sati daya kenan bata ganin Ayan Kuma ko ajikinta duk rana zata shiga part dinshi ta gyara mashi gado tare da kula da part din amma bata ganin shi haka na faruwa saboda  Ayan bai dawowa gida sai dare.
Sai ta dafa abinci daidai bakinta mai shegen dadi ta cinye abinta Sannan ta bi lafiyan gado.
Yau tana kwance bayan ta idar sa sallan ishai sai tunanin abinda yasa Ayan bai kusantanta, ajiyan zuciya ta saki tana jin wani irin dadi cikin ranta. Wayanta ta dauka tayi dailing number mom bayan mom tayi picking sun gaisa as usual mom ta fara cewa
"Baby ina mijinki?..." Ahankali ihsan tace
"Ban Sani ba" da Sauri mom tace
"Bangane baki Sani ba?...what do you mean by that?.."  Shuru ihsan tayi mom tace
"Am asking you..." Ahankali ihsan tace
"Mom ban San inda yake ba....yanzu...satina daya ban ganshi ba...".
" subhanallahi... Wane irin rashin hankali ne wannan?... Ya zaayi kice baki san whereabouts na mijinki ba?..." Ahankali ihsan ta katse mom dacewa
"Ai mom bai fadamin ba..."
"Keep quite... In bai fada maki ba ke baza ki kirashi ba?...imagine sati daya baki ga Wanda ya ajiyeki gida ba Kuma you don't care...wane irin habit ne wannan?.. In short let me ask you...kin na bashi hakkin shi?.." Da Sauri ihsan ta kama bakinta tana mamakin dalilin dayasa mom tayi mata irin wannan tambayan,
"Am asking you!.." Mom ta daka mata tsawa,
"Ai mom..." Sai Kuma tayi shuru
"Ai... What?.." Mom ta tambayeta,
"Ai mom..bai...iyawa..." Ta fadawa mom Kuma at the same time tana kama bakinta
[12/27, 14:14] ‪+234 814 199 1000‬: [12/14, 3:43 PM] Ummu Maryam: 💛💙💜🖤💚❤
KAWARTA CE SANADI
💜💚💛🖤❤💙




®zuwairat(ummu Maryam)




4⃣4⃣






 _Wannan Kuma nakune yan *Zuwairat ummu Maryam page,* inason Ku dukda kuna Dan batamin rai amma da ga kun dan fara chanzawa, Allah ya karemin Ku a duk inda kuke ya karaso da kauna tsakanin mu. I love guys more than silver and gold_


 Da Sauri mom tace
" what do you mean by that?... " ihsan shuru tayi tana Dana sanin fadawa mom wannan statement,
"Am listening..." Taji mom na cewa,
"Mom babu komai..."
"Stop telling me babu komai... Shine bai bukata ko ke ce kike hanashi..." Mom ta. Sake tambayan ta, itadai ihsan kunya kawai takeji don batasan ta yanda zata fara fadawa mom cewa duk sanda Ayan yayi wasa daita bai Iya kusantan ta ba
"Ni ban hanashi..." Ta fada muryan ta na rawa,
"To naji kince bai iyawa ...me hakan ke nufi?..." Ihsan shuru tayi tana turo baki,
" am asking you... " taji mom na cewa
"Nima mom ban Sani ba..." Ganin ba gm fadawa mom zatayi ba yasa mom tace
"Kuma kince sati daya baki ganshi ba kin kirashi?..." Da Sauri ihsan ta Dan tabe baki Sannan tace
"Ai mom nan gidan yake kwana...kawai dai bamu haduwa ne..." Ta fada in I don't care tune,
"Kinga ihsan ki shiga hankalin ki...in mijinki bai nemeki ba ai ke sai ki nemeshi...yanzu ki kashe waya ki kirashi..." Ta fadawa ihsan,
"To..." Ihsan ta fada mata Sannan ta katse wayan ta ja bargo ta rufe kanta don tasan ko amafarki bazatayi gigin kirashi ba cis she following his own rules, bata Dade da kwanciya ba taji kaman an bude kofan falon ta, da Sauri ta lumshe idanuwanta kaman mai bacci, Ayan ne ya bude kofan bedroom dinta ya shigo, har lokacin bata bude idanuwanta ba, ahankali ya shiga dakin yana kallon fuskan ihsan dake kyalli, har yanzu he can't believe wai he's living under the same room with wannan astonishing beauty amma he couldn't do anything with her ba,
"Ya Allah why?... Why zanyi aure amma in kasa kwanciya da mata ta?... Ya ilahi in don nace zan yi mata dalla dalla ne ka gafarta min....pls I need to be with her..." Ya fada cikin ranshi at the same time hawaye na gangaro fuskan shi, ahankali yataka zuwa bakin gadon ya tsaya yana kallon ta for a mom Sannan ya zauna, legs dinshi biyu ya maida kan gado ya matsa kusa daita, ihsan data lumshe idanuwan najin jikin shi kusa da nata gabanta ya fara faduwa as usual, jawota yayi jikin shi ahankali ba kaman yanda ya saba fixgota ba, har lokacin bata bude idanuwan ta ba, jikinta ya fara shafa kaman yanda ya saba Sannan ya yi kokarin hada bakinshi da nata sai yau ta gumke bakinta, hannun yasa ya fallawa bayanta bugu tayi saurin bude baki tana fashewa da kuka, ahaka ya yi yanda ya gandama da da duk ilahirin jikinta amma still babu komai,
 Dakatawa yayi, Jim kadan ai ya fashe da kuka, ahankali ihsan ta bude idonta tana kallon shi Dan juyowa yayi ya kalleta sukayi ido hudu nan taga yanda ya koma kaman ba shi ba duk ya rame ya kode, kaman ta tambayeshi matsala amma sai ta tuna ya fada mata kar tayi mashi magana in ba shi ya yi mata magana ba, ahankali ta juya kwanciyan ta tare da juya mashi baya, Ayan tsaya kallon ta yayi yana hawaye,
"Ya Allah ka kubutar dani daga wannan matsalan..." Ya fada cikin rashi, ahankali ya mike daga kan kan ya fita daga dakin yana kuka, part dinshi ya koma yayi alwallah as usual ya hau kan praying mat dinshi ya dinga adua kan Allah ya yaye mashi wannan matsalan da yake ciki.


The following day ya fita bayan ya shiga kitchen ya soyawa kanshi plantain ya hada tea yasha ya dauki key dinshi ya ya tafi hospital daman all this while yana zuwa office saidai bai fiya aiki ba sai in dai emergency ne.

Ihsan ma farkawa tayi tayi sallan ta kaman gyara part dinta dukda babu wani kazanta sai ta shiga wanka ta fito ta shafa mai don mostly yanzu mai kawai taje shafawa bata kwalliya amma fuskan ta gwanin kyau,  fito tayi ta nufi part din Ayan shima ta gyara mashi gado ta linka kayanshi ya da bari kan kujera ta maidasu cikin wardrobe ta wanke bathroom dinshi, saida ta gama ta dauko burner ta turare koina na gidan kaman yanda ta saba Sann ta shiga kitchen ta wanke plate da cup tare da frying pan da Ayan yayi amfani da shi don mostly shi ke hadawa kanshi simple abinci kaman indomie da kwai da sauran su. Saida ta gama da gyaran kitchen ta dora abun breakfast.


Ayan na zaune office kawai bai cikin hayyacinshi cos duk Wanda ya ganshi yasan he's thinking, Muhammad ne ya shigo da sallama amma Ayan bai amsa ba saboda he's absent minded, Muhammad zama yi Kuma  bai ida zama ba shi ma Yusuf ya shigo suka gaisa da Muhammad yana kallon Ayan
"Wannan fa?..meke damunshi?..." Ya tambayi Muhammad,
"Hmmm ai kasan haka yake this days..in short tunda akayi auren nan he has turned to a different person entirely ...." Inji Muhammad, Yusuf dai kurawa Ayan ido yayi for a moment Sannan yace
"Kilan yana regretting abinda ya dinga yiwa ihsan ne...maybe he have found out the truth.
." Yusuf ya fada atakaice, Ayan dai shuru yayi yana jin su cikin ranshi kam cewa yayi
"I wish..." Dan buga table Yusuf yayi yana cewa
"Kai fadamana what you are up to..." Yafada yana kallon Ayan, shima Ayan daga red and weak eyes dinshi ya kalleshi
"Ku kyale ni pls..." Yafada masu yana relaxing cikin kujeran shi,
"Ya zamuyi mu kyale ka?... In har mun kyale ka that means we're not friends... Jibi yanda ka koma... Da gani what ever is wrong with you is not something you should keep to your self...talk to you cos kasan bamu taba baka wrong advice ba..." Muhammed Yafada mashi tana dora hannun shi kan  hannun Ayan dake kan table, ahankali Ayan ya zare hannun shi ya harde su kan kirjinshi.
 "Pls talk to us..." Yusuf ya kara fada, Ayan banza yayi dasu,sunfi minti ashirin sunayi mashi magiya kan ya fada masu abinda ke damunshi amma ko kallon su baiyiba balle ya fada masu, tsoki Yusuf yaja ya mike,shima Muhammad mikewa yayi, ahankali Ayan daga kanshi ya kallesu Sannan yace
"Ba wai banason fada maku problem dina bane...kawai am thinking.. Kilan kuyi joking in my mystery..," da Sauri Muhammad ya zauna yana cewa
"Haba guy...ya zaayi muyi joking da abinda is weighing you down...kasan that is not possible..." Yafada ahankali, Ayan daga kai yayi ya kalli Yusuf dake tsaye har lokacin Sannan ya fara cewa
"I haven't been able to sleep with ihsan..." Ya fada muryan shi na cracking, Yusuf Dan Dariya yayi tare da daga kafada in so what manner Sannan yace
"To Dan wannan ai ba wani abu bane...ai bakason auren so ko baka kwanta daita ba babu case..." Ya fada in I don't care tune, Ayan daure fuska yayi shi Kuma Muhammad ya wullawa Yusuf disgusting look Sannan ya kalli Ayan yace
"What exactly do you mean by that?...." Ya tambayeshi yana gyara zaman shi, Ayan kallon Yusuf yayi
"Ka fita daga office dina..." Ya fada mashi babu wasa, Yusuf tabe baki yayi ya zauna tare da harde hannuwanshi kan kirjinshi
"Ban fita..." Yafada atakaice, Ayan kallon Yusuf yayi yana huci amma ko kallon shi Yusuf baiyiba,
"Guy manta da wannan lunatic din...talk to me..am here for you..." Muhammad ya fadawa Ayan in a calming tune,ajiyan zuciya Ayan ya saki Sannan yace
"Tunda na auri ihsan i ..." Sai Kuma yayi shuru, da Sauri Muhammad yace
" go on...am listening... " Ayan shuru yayi don bai San exactly what to say ba don shi kanshi kunyan fruta word din impotence yakeji,
"Pls talk to me..." Muhammad ya kara fada mashi, shidai Yusuf har lokacin harde hannuwanshi yayi yana girgiza kafa ahankali, Ayan kallo Yusuf da Muhammad yayi Sannan ya ce
"I have...suddenly... Become impotent...." Ya fada kaman zaiyi kuka, da Sauri Muhammad ya mike tsaye yana cewa
"What!!!!" Ya fada cikin tashin hankali, Shikuma Yusuf tuntsurewa yayi da Dariya tare da tafa hands dinshi yana cewa
"Joker..."ya fada yana Kallon fuskan Ayan don ganin how serious he is, ganin shi yana hawaye yasa Yusuf yayi shuru yana cewa
" wait a minute.. Are serious?... " cikin kuka Ayan ya daga mashi kai, idanuwa Yusuf ya zaro,
"Since when?..." Yusuf ya tambayeshi cikin tashin hankali, don shi Muhammad kasa magana yayi yana jin the word impotent na yi mashi yawo cikin kunne, cikin kuka Ayan yace
"Nayi noticing hakan ...4 to 5 weeks back... Saidai ban maida hankali ba...sai yanzu... Am having urges amma babu erection..." Ya fada cikin matsanacin kuka,
"Inna lillahi waina ilaihi rajuun!!!..." Yusuf da Muhammad suka dinga maimaitawa, da Sauri Muhammad yace
"Have you been to any hospital?..." Ya tambayeshi tension na rising cikin muryan shi, kai Ayan ya daga mashi yana cewa
"I have been to four hospitals..."
"Then me suke fada maka?.." Yusuf ya tambayeshi,Ayan yana goge hawaye yana cewa
"Sun ce I am medically alright... Doctor James ma cewa yayi it might be a spiritual problem..."
"Subhanallahi!!..." Yusuf da Muhammad suka kara fada cikin tashin hankali, ahankali Yusuf ya fara cewa
"Amma gaskiya guy you are a dumb ass...ace kana cikin irin wannan matsalan for almost a month amma baka fada mana ba?.. What are friends for?...forget cewa I can be a jerk at times amma you know we always have your back..." Yusuf ya fada cikeda tausayin ayan
 Cikin kuka Ayan yace
"I don't know it is very serious until now...", shuru dukkan su sukayi banda kukan Ayan babu abinda ke tashi, few minutes later Muhammad yace
" yanzu meye abinyi?..."
"I don't know... Am confuse... Why me...." Ayan ya fada cikin kuka,  ahankali Yusuf yace
"I think my fadawa su Abba..." Da Sauri Ayan yace
"No...I can't... Am a shame..." Bata rai Yusuf yayi
"Meye abun kunya?...ai duk Wanda ya boye ciwo to ya boye mai magani..yanzu ai ya zama dole mu fada mashi ...you know what an old man see sitting down a child will not see even if he climes an iroko tree...so kawai yanzu muje office din Abba..." Inji Muhammad, shidai Ayan shuru yayi tana tunanin ta ya zai fadawa Abba bai Iya kwanciya da matarshi,
"Guy gaskiya that is the only solution for now... Kawai muje I will do the talking..." Inji Yusuf.
Da kyar suka shawo kan Ayan ya amince su tafi office din Abba. Suna isa secretary tasansu so ba saida appointment ba, direct suka shiga office din Abba, Abba dake zaune yana latse2 a system dinshi ya daga kai yana kallon su waye suka shigo mashi office ba tare da secretary ta kira shi ba, ganin su Ayan yasa ya saki ranshi, dukkan su durkusawa sukayi suka gaida dashi ya amsa hankalin shi kan Ayan da kanshi ke kasa kaman wani munafuki,
"Lafiya dukkan Ku kuka bar wajen aikin Ku?..." Abba ya tambayesu yana kallon agogon hannun shi, ahankali Yusuf yace
"Gaskiya Abba ba lafiya ba..." Nan Yusuf ya warwarewa Abba duk abinda Ayan ya fada mashi, Abba na sauraron shi amma yana kallon Ayan da kanshi ke kasa yana hawaye, sai da Yusuf ya kai aya Sannan Abba yace
"Abubakar..." Abba ya kira Ayan, ahankali Ayan ya daga kanshi  ya kalleshi da wet face dinshi,
"Da gaske ne abinda Yusuf ya fada?..." Abba ya tambayeshi, ahankali Ayan ya sauke kanshi kasa Sannan ya dagawa Abba kai,
"And you don't think I should know sai yanzu?..." Abba ya fada cikin fada,da sauri Ayan ya Dan ja baya saboda yanda ya razana da tsawan Abba,
"Abba am sorry.... I don't know its serious..." Ya fada cikin matsanacin kuka
 Abba kura mashi ido yayi for a while Sannan yace
"Are you impotent tun da chan ko kuwa yanzu ka fara samun matsala?..." Abba ya tambayeshi,
"Yanzu ne..." Shuru ne ya biyo baya kan Ayan kasa sai hawaye kawai ke malala fuskan shi, Abba shuru yayi kaman mai tunani Sannan yace
"Ka je wajen doctor James..." Bai idaba Ayan ya ya katse shi dacewa
"Naje..."
"Then me ya fada maka?..."
"He said am medically OK...kawai wai it might be a spiritual problem..." Ya fadawa Abba, Abba kam jimamin wannan alamarin kawai yake, few minutes of silence Abba ya dauki wayanshi yayi dailing wata number ya kanga wayan a kunnenshi for few seconds Sannan yayi sallama bayan anyi picking, gaisawa sukayi Sannan yace
"Baba daman dankane bashi da lafiya shine nace yazo yayi maka bayanin abinda ke damunshi..." Inji Abba, shuru yayi for a while Sannan yace
"To shikenan... Yanzu zai zo insha Allah..." Abba yafada Sannan ya katse wayan, kallon Ayan yayi Sannan yace
"Kaje wajan Baban tukuntawa ka fada mashi abinda ke damunka..." Abba ya fada mashi atakaice,
"To Abba..." Ya fada Sannan ya mike suma su Muhammad suka mike, Ayan bathroom din Abba ya shiga ya wanke face dinshi Sannan ya fito suka kama hanyan tukuntawa.

 Wajen karfe 11 ihsan na zaune falon ta na farko tana kallon wani program taji anyi knocking kan kofanta, Dan mikewa tayi tana tunanin who it could be, tana bude kofa taga husna tsaye, da Sauri ta daka tsalle suka rungume juna don tun ranar da aka kawo ihsan da Ayan ya koreta bata kara dawowa gidan ba sai yau amma kullum sai sunyi waya saboda samun information, kallon ihsan ta yi tana shiga falon rai ta sai konewa yake saboda yanda ihsan ta fara murmujewa,
"Kai babe wannan glowing haka anya Ayan baiyi ajiya ba?..." Ta tamb looking for more information dukda ihsan na fada mata babu abinda ya shiga tsakanin su amma bata yarda ba don yanda ta ganta ta chanza kaman ba ita da ta kare kaman kudin guzuri bace, ihsan dai Dariya tayi bata ce kala ba amma hannun ta rike Dana husna, husna sai bin bayanta take da harara, sakin hannun ta ihsan tayi bayan sun isa tsakiyan falon husna ta zauna tana kara karewa falon kallo cos aranar da sukazo darene amma yanzu ta kara ganin uban kayan da akayiwa ihsan,  Dan baki ta tabe tana kallon ihsan data nufi kitchen, gidan sai kamshi kawai yake, mikewa tayi tabi bayanta zuwa kitchen, ihsan na tsaye tana saka fruit cikin juice mixer, murmushi kawai ta sakarwa husna, ita Kuma husna kallon jerin wuka dake kitchen din tayi tana tunanin
"In na dauki daya daga cikin wannan dukan nayi slicing throat dinki ai babu Wanda  zai gane nazo... " ta fada cikin ranta,
"Amma that might be my next plan...in har wannan baiyi aiki ba..." Ta kara fadawa kanta,
"Babe ya mami da lil sis?.." Ihsan ta tambayi husna tana juye juice cikin jug,
"Lafiya lau...sunce in gaidaki..." Tafada tana karewa kitchen din kallo, cup ta dauko ta zuba drink din ta fara sha
"Babe me zan dafa maki?.." Ihsan ta tambayeta hankalin ta kwance saboda tasan dukda Ayan ya bata rules tasan bai dawowa yanzu, Dan hararanta husna tayi tare da tabe baki
"Masu gidan miji..har da wani me zaki dafamin..."
 Dariya ihsan tayi tana cewa
"Ai kusan ince yanzu ne first time dinki nan gidan so ai dole in karramaki..." Ihsan ta fada,
"Me dame gareki naci?..." Husna ta tambayeta,
"Snacks ne kawai amma ina da duk wani raw food items da kike shaawa..." Ihsan ta fada tana Dan jingina da kofan store dinta,
"Lallai kam kina hutawan ki...ina kayan abincin suke?..."  Nan ihsan ta bude mata kofan store taga kayan abinci kala2 kaman a restaurant, wani irin haushi ne ya kara kamata
"Ki dafa min duk abinda zakuci da rana..." Ta fada tana fita daga cikin store din,
"Ban ma San abinda zanyi da ranar nan ba..." Inji ihsan dake biye da husna a baya
"Me mijinki keso yaci?.." Husna ta tambayeta, ihsan baki ta bude zata fada mata Ayan bai cin abinci ta sai Kuma ta tuna da abinda husna tayi mata na tonamata asiri sai tace
"Ai bai da choice.. Kowanne irin abinci CI yake..." Ta fada kaman gaske, wani irin haushi husna ta kara ji
"Wato har abincin ta yake ci... Gaskiya I have big work to do..." Ta fada cikin ranta,
"Bari in dafa mana fried Rice and chicken sai mu hada da coconut juice..." Ta fada da sauri kaman wacce ta tuna abu,
" ki bari sai later...yanzu ki nunamin gidanki..." Husna ta fada tana sipping drink dake hannun ta,
"Ok.. Follow me..." Ihsan ta fada tana catwalking, part dinta ta nuna mata duk lungu da sako dake gurin Sannan suka fita wajen compound ta nuna mata suka zagaye gidan, ihsan kam sai tunanin Ace Ayan ya dawo yanzu kawai take
"Da na lahira sai yafini jin dadi..." Ta fada cikin ranta,
 Bayan sun dawo falo husna ta nuna part din Ayan tace
"Ba ku nunamin chan ba.." Ihsan kallon inda husna ke nunawa tayi Sannan tace
"Part dinshi ne..."
"Ki nunamin mana...ai ni in nayi aure babu inda zan boye maki a gidana...." Ta fada, ihsan dai shuru tayi
"Plssss.," tafada mata,
"Well muje in nuna maki..." Ihsan ta fada tana mikewa itama husna cikin jindadi ta mike tabi bayanta. Ihsan na bude kofa husna ta lumshe idanuwanta saboda kamshin perfumes din Ayan data ji,
"I love you..." Ta fada cikin ranta, nan ma saida suka gama zagayewa Sannan suka koma falo, suna hira har ihsan ta hada masu delicious lunch sukaci. Sai bayan sallan asar husna ta bar gidan, wani irin jindadi ihsan taji da Ayan bai kama ta ba
[12/18, 7:49 PM] Ummu Maryam: 💙💛💜🖤💚❤
Masoya ya kuke ya Karin hakuri dani?  To INA kara Baku hakuri saboda rashin jina da kuke, well am not feeling well Kuma ina dawata commitment ne, Ku cigaba da hakuri dani, wannan na don kar kuce na manta da Ku yasa na turo wannan so Ku kara hakuri dani am assuring you zaku ji dadi fiye da yanda kuke thinking, and pls fans na bude website dina mai suna www.ummumaryam.com, so masoya inason Ku leka Chan kuyimin like da comments, I really want to see how many lovers I have before I started doing something on the web site, love you wujiga2
[12/27, 14:14] ‪+234 814 199 1000‬: ❤💙💜🖤💚💛 KAWARTA CE SANADI 💙💚❤🖤💛💜 ®zuwairat ummu Maryam) 4⃣5⃣ _Wannan shafin Kuma nakune yan *Zahara Surbajo novel group,* I wish ina Iya listing names dinku amma you are too many to be mentioned, amma I love all of you more than anything_ Yusuf ne ya dinga driving kasancewan sun taba zuwa gidan oonce or twice da Ayan, Ayan na baya yayi relaxing kaman mai bacci amma ba bacci yake ba. Yana jin anyi parking ya bude ido, "Har mun iso?..." Ya tambayesu, "Yes..." Muhammad ya amsa mashi yana fita daga cikin motan, shima Ayan fitowa yayi suka nufi wani gidan mai bushiyan bedi tare da wasu old men zaune kan mat, daya daga cikin mazan kallon su Ayan yayi ya saki murmushi yana cewa "Har kun zo?..." "Eh..baba..." Yusuf ya amsa mashi, dukkan su uku gaida su sukayi tsohon da sauran mazan dake zaune gurin suka amsa Sannan tsohon ya mike ya kalli Ayan "Mu shiga ciki..." Ba musu Ayan ya bishi, su Kuma Yusuf suka koma cikin mota Cikin wani karamin daki dake zauren gidan suka shiga , dakin babu komai ciki sai tabarma babba sai Kuma alquranai da yawa kaman inda ake fansansu, "Baban ka ya fadamin kana da wata matsala... Ina sauraron ka..." Baban ya fadawa Ayan, cikin nutsuwa da jin kunya Ayan ya fadawa tsohon abinda ke damunshi, shima tsohon jimamin maganan Ayan kawai yake "Kana mafarkin kwanciya da mace?.." Tsohon ya tambayeshi, ahankali Ayan ya girgiza mashi kai, "To wannan abun da akwai hannu ciki..amma kar ka damu...mu baa taba a zauna lafiya saboda muna da alquran mai tsarki Sannan Kuma mun san adua takobin mumini ne...don haka zamu tashi tsaye babu dare babu rana..mu cigaba da adua indai yin mutum ne Allah zai tona asiri ko waye... Don haka ka kwantar da hankalin ka...kaji ko?.." Ahankali Ayan ya daga mashi kai "Nagode baba..." "Yauwa Dana...Kuma kaima ka dage da adua... Jibi yanda ka koma saboda tashin hankali....ka bar tunani.. Ko don kana kallon tsaleliyar budurwa baka iya aikata mata komai yasa kake tunani?..." Tsohon ya fada cikin zolaya, Ayan sadda kanshi kasa yayi yana murmushi, Dariya tsohon yayi kafin yace "AI nasan dalilin kenan...yaran zamani ..." Ayan dai murmushi kawai yake, "Yanzu ka dinga bada sadaka sosai...kaji ko?.." "Eh baba..insha Allah....." "To madallah..." Ahankali Ayan ya mike tare dayi mashi godiya ya fito ya shaidawa su Muhammad yanda sukayi da tsohon Sannan suka wuce. Office suka koma amma still Ayan bai komai. Bayan sallan ishai ihsan ta shiga wanka ta saka kayan bacci mai silver colour, kayan sai salki yake, Dan kwantawa tayi hannun ta kan maranta gashi kan ta na ciwo, kawai juye2 take kan gado saboda menstral pain dake damunta, daman ta saba duk wata sai tayi shi Allah ya taimaketa ba sosai yake mata ba amma still is a little bit on bearable. As usual sai dare ya dawo gida parking yayi ya bude bayan motanshi ya dauko wata Leda Sannan ya shigo falon, direct kitchen ya shiga ya bude fridge ya zuba kayan fruits da yakawo Sannan ya tsaya yana kallon kitchen din, gani yayi plate biyu da alaman ihsan tayi bakuwa yau, cold tea ya hada ya sha daga nan inda yake tsaye ya ajiye cup cikin sink inda sauran plate suke Sannan ya fito, part din ihsan ya shiga, ko sallama baiyiba ya shiga bedroom din dayasan take, daga nesa ya hangeta kwance idanuwanta lumshe, ta ciza bakinta na kasa which makes her look sexy,ahankali ya taka zuwa inda take, zama yayi bakin gadon, duk ihsan najin zuwanshi amma tayi pretending tana bacci cos ko ta bude ido ba magana zatayi mashi ba, hannu ya daga ya fallawa ass dinta duka da Sauri ta mike zaune tana shafa inda ya bugeta, idanuwanta duk sunyi ja, sai turo baki take kaman zatayi kuka Kuma at the same time tana shafa inda ya bugeta, Ayan kura mata ido yayi yana kallon yanda idanuwanta suka chanza, "Hey ..what's the matter with you?.." Ya tambayeta Banza tayi dashi don ta dau aniyan bazata yi mashi magana ba no matter the conditions, ita tana ganin kokarin ta don batasan zata iya zama very gentle ba, Ayan kam kurawa beautiful pecky nipple dinta dake eyeing dinshi ta cikin riganta yayi, ahankali ihsan ta rufe chest dinta ganin irin kallon da yake mata, "I said meke damunki?..ko you are missing sex?.." Ya tambayeta kai tsaye, ihsan Dan tabe baki tayi tare da kauda kanta gefe, da Sauri Ayan ya maido fuskan ta inda yake "Are you horny....naga your eyes are red?.." Ihsan banza tayi dashi, Ayan kam har son jin muryan ta yake don tunda ya fada mata rules dinshi bai Kara jin uffan daga gareta ba, "To ki biyani inyi servicing dinki..." Ya fada kaman bai da wata matsala, ihsan dai bata tanka mashi ba saboda ciwon maranta ma is enough for her, Ayan ganin she is not saying a word yasa shi cewa "Who came to this house today?..." Da Sauri ihsan ta kalleshi gabanta na faduwa, "Yes...you think I don't know?.. Yanzu fadamin Wanda ya zo yau..." Ya fada yana kama bayan wuyanta, kuka ihsan ta farayi amma batace kala ba "Na lura you are stubborn... Ki fadamin Wanda yazo gidan nan yau ko Kuma na lahira yafiki jin dadi..." Ya fada yana kara rike wutan da karfi, kara ta saki ganin da gaske Ayan yake yasa tayi saurin cewa "Husna ce..." Da Sauri Ayan yace "Hus...me?..." Ya tambayeta sounding very angry, cikin kuka tace "Husna..." Bata idaba ya dauke ta da mari, "What did I tell you?..." Da Sauri ihsan tace "Kace...kar... Kawayena...su zo ...nan...gidan..." Ta fada cikin matsanacin kuka at the same time hannun ta kan cheek dinta daya Mara, gashin kanta ya rike yana cewa "Wato ihsan Kin rainani ko?...har in fada maki kar ki bari banzayen kawayenki su zo nan amma dayake ke yar iskace shine kike gayyato su gidana ko?.." Ya fada da karfi yana Jan kanta da karfi, ihu kawai ihsan take kaman ranta zai fita, "Wallahi...ban gayyato ta ba....da kanta tazo..." "Da tazo baki fada mata nace she's not welcome?... Baki fada mata mijinki ya hanata zuwa nan gidan?.. " ya fada yana kara Jan silken hair dinta, "Wayyo...kayi hakuri..." Ta fada cikin wahala,. "Good..." Ya fada yana sakin kanta, mikewa yayi ya koma tsaye Sannan yace "Come here!..." Ya daka mata tsawa, da Sauri ta sauko kasa ta tsaya gabanshi tana kuka hannun ta dafe da kanta, "Kneel down..." Yayi commanding dinta, da Sauri tayi kneeling jikinta sai rawa yake, "Kama kunnenki..." Ya kara commanding dinta, still bai idaba ta kama kunnenta, "Now repeat after me...daga yau..". Da Sauri ihsan tace " daga yau" Ayan ya cigaba dacewa "Bazan Kara barin wata karuwa ta shigo gidan nan ba..." Cikin kuka ihsan tace "Bazan kara ...barin...wata karuwa...ta shigo ...gidan...nan..ba..." Ayan yace "Duk ranar Dana bari wata karuwa ta shigo gidan nan ka ciremin kunne daya..." Da Sauri ihsan ta daga wet face dinta tana kallon shi "Say it!.." Ya daka mata tsawa, da Sauri tayi repeating abinda yace cikin kuka, Ayan ya kara cewa "Kuma duk ranar da na kara karya wata doka ka cire min boob daya..." Yafada babu wasa, ihsan Kara kallon shi tayi tana hawaye, "Bazaki fadaba sai na cire maki hakora?.." Ya fada cikin fada, da Sauri ihsan tace "Duk...ranar...da na kara..karya...wata..dokarka..ka..cire..min..." Sai tayi shuru "Bazaki karasa ba?..." Ya daka mata tsawa, Da Sauri tace "Boob...daya.." "Good..Yafada yana dariyan keta " yanzu nuna min Wanda zan cire in har kika kara breaking rules dina" Yafada kaman gaske, Banza tayi dashi ta cigaba da kuka, "Nace ki nunamin Wanda zan cire in har kika kara karya dokata..." Da sauri ihsan ta nuna mashi right hand boob dinta, cikin zalunci ya kama wannan boob data nuna mashi ta saki ihu tana cewa "Pls...stop...zafi..." Ta fada cikin kuka, tsaya kallon ta kawai yayi yana imagining ranar da Allah zai nasara kanta, "Very soon I will give you a day to remember.. Say yes sir..." Cikin kuka tace "Yes sir..." Dan Dariya yayi ya bar dakin at that moment sai ya manta matsalan shi, ihsan bayanshi tabi da harara tana ganin ya fita tace "Mugu azzalumi... Sai Allah ya sakamin...bunsuru kawai..." Tafada tana mikewa daga inda yasata kneeling, ga ciwon kai gana Mara Sannan ka na Ayan. Aranar haka ihsan ta kwana babu dadi gashi ciwo maranta sai karuwa yake. The following day Ayan bai fita ba don kwana yayi adua da rokon Allah don haka bai kwanta ba sai bayan sallan fajr, ihsan kam ko tashi bata iyawa tana kwance har karfe 11. Around 11:30 su Muhammad sukazo gidan kasancewan ranar asabar, suna waje suka kira Ayan Wanda hakan ya tadashi daga bacci, picking yayi suka shaida mashi suna waje, nan ya basu izini su shigo falo su jirashi, mikewa yayi ya. Shiga bathroom tare da sakarwa kanshi shower ya fito daure da towel, ko mai bai shafa ba ya saka jallabiya ya fito ya samesu,. "Ango..ango..ango..." Yusuf ya fada cikin zolaya, wani irin kallon haushi Ayan yayi mashi, nan suka fara hira "Wai ina amarya take?.." Muhammad ya tambayeshi, banza yayi dashi, "Am talking..." Muhammad bai idaba aka bude kofa part din ihsan, dukkan su kallon ihsan dake sanye da long Arabian gown sukayi, kanta rufe dan small Vail, Ayan tabe baki yayi ya dauke kanshi, Yusuf da Muhammad murmushi suka sakar mata, itama tana daga kai ta gansu ta sakar masu murmushin karfin hali tare dacewa "Aa sannunku da zuwa.." Gaidasu tayi in a respectable way amsawa sukayi ana wasa da dariya "Me zanyi offering dinku..." Ta tambayesu, "Anything sis.." Yusuf ya amsa mata, "Ok then.." Ta fada tana barin wurin ahankali saboda ciwon maran da take, amma haka ta hada masu juice ta kawo masu cos she respect then saboda ceton ta da sukayi lokacin da Ayan yaso dagargaxanta Sannan har yanzu bata bar jin kunyan su ba. "Bari in hada maku lunch..." Tafada tana barin wurin, Ayan dai shuru yayi Yusuf kam yana shan drink din yana dagawa Ayan gira. Suna nan zaune ihsan ta hada masu lafiyayyen jelof rice with salad sai fried chicken, zubo abincin tayi cikin warm ta ajiye kan dinning table Sannan ta koma ta dauko plate biyu da spoon, serving dinsu tayi su biyu Kuma ta tabbatar babu sauran abincin Sannan ta dawo wurin su a falo tace "Lunch is served..." Tafada da faraa fuskan ta , "So soon?.. Well done..." Yusuf ya fada mata, bata kara cewa komai ba ta bar wajen ta dauki abincin ta ta koma part dinta, Yusuf da Muhammad tare da Ayan mikewa sukayi, suna zuwa suka ga two plate na abinci, ko kallon Ayan basuyi ba suka haye kan dinning suka bude plate data rufe abincin dashi Nan take Ayan yaji yana salivating, "Woww..wannan abincin is something else..." Muhammad ya fada yana kai loma bakinshi, Ayan komawa yayi ya zauna ya barsu nan kan dining, gashi ba karamin yunwa yake ji ba Kuma kamshin abincin ya bade koina na gidan amma pride bai barin shi ya fada mata ta bashi, haka ya zauna yana hamma while Yusuf da Muhammad suna shagalin su Kuma duk loma sai sunyi santi, tsoki Ayan yaja ya shiga kitchen ya hadawa kanshi tea ya dauko bread ya zauna nan falo yana ci, Dariya suka dinga yi mashi. Bayan sati daya prayers koina kan matsalan Ayan, Umma nayi, Abba nayi...su Muhammad da Yusuf nayi Kuma an bawa malamai kudi suma suna tayawa, Ayan kam sai da rana yake bacci amma dare kwana yake in praying mat. Yau husna da family dinta na zaune falo suna kallon series around karfe 7:30, kanwar husna mikewa tayi ta shiga ciki, ba a Dade ba ta dawo falo Sannan tace "Sis on nake...Kuma bani da sauran pad..pls ki taimaka min da naki..." Ta fadawa husna, husna da idanuwanta ke kan screen kaman her life depends on it tace "Ki duba cikin purple bag dina dake rataye jikin bag hanger..." "Thanks sis..." Ta fada ta bar wurin, dakin husna ta shiga ta bude bag din da husna tayi mata discribing, tana dauko pad dinta ta bude ta dauki daya Sannan ta zo maida sauran nan taji abu gefen bag dinta, budewa tayi ta dauko wannan makullin, "Kome sis take da wannan abun cikin bag dinta?.." Ta tambayi kanta, kaman ance ta bude kawaisai ta bude shi Sannan ta maida., friends in har kana adua da akwai abubuwa da dama da Allah ke warware maka ba tare da sanin ka ba. Adaidai wannan lokacin Ayan na kan dawowa daga masjid kawai sai yaji kaman an zare mashi wani abu ajikin shi, nan take ya kama adua, haka ya dinga praying har ya iso gida ya zauna falo, kawai sai yaji yana samun erection, cikin tsoron kanshi ya kalli joystick dinshi.
[12/27, 14:14] ‪+234 814 199 1000‬: 46


KAWARTA CE SANADI


®zuwairat( ummu Maryam)



_Wannan shafin is for you the most lovable group members, *Khaleesat hydaar novel,* Wallahi har ga Allah your comments always make my day, Allah ya tsareku ya biya maku bukatunku na alkhairi. I really love, Kuma da gaske nake ba wasa ba. Ya rabbi ya barni da Ku._

Shi kanshi sai da ya tsorata da yanayin shi don it was unexpected, Dan dafa joystick din yayi don tabbatar he’s not dreaming,
“Alhamdulillah.. Alhamdulillah… Alhamdulillah… Am OK again…” Ya fada cikin jindadi, dan zama yayi for a while yana murmushi, ahankali ya mike yana kallon gaban jallabiya shi, part dinshi ya shiga ya wuce bedroom dinshi, zama yayi kan kujera yana cewa
“Yarinya you are in big shit…” Ya fadawa kanshi, mikewa ya karayi ya cire jallabiya ya daura towel Sannan ya dauki wayanshi don at that moment ji yake he can walk saboda yanda mood dinshi ke kara chanzawa, kan kujera ya zauna ya kira number ihsan,
Alokacin ihsan ta idar da salla kenan tana nan zaune kan praying mat, sanye take da kayan.bacci green, kayan bai da tsawo sosai haka yasa ta daure zani samanshi tayi sallan, jin ringing wayanta yasa tayi saurin mikewa cos tana tunanin yan gida ne, tana daukan wayan taga babu suna amma ta gane number Ayan ne, talk it an a ta ajiye bata dauka ba, Ayan ganin ringing yake ba response yasa yayi kokarin mikewa don ya sameta amma ina, kunya taje ji yayi tafiya a yanayin shi, kara dailing number ya karayi yana cewa
“Pick…pick….pick up I have a surprise for you…” Ya fadawa kanshi.

Ganin wayanta na ringing again yasa ta tayi picking don kar ya sameta cos ta san yana gida, tana picking taji Ayan na cewa
“Kizo ki gyaramin gado na…Kuma if you waste my time you are in trouble…” Yana kaiwa nan ya katse wayan, ihsan cire waya tayi daga kunnenta tana kallon wayan cos ko kadan kaman ba muryan shi ba, tabe baki tayi ta fita daga dakinta har alokacin tana sanye da zani sai kanta da mini hijab data yi salla dashi, part dinshi ta shiga da sallama amma babu kowa falo ba tare da fargaban komai ba ta shiga bedroom dinshi , gani tayi yana zaune yana ganinta ya dora kafa daya kan dayadon kar ta ga yanayin shi, gadon ta kalla taga gyare yake amma dayake batason rigima sai ta duka ta fara gyara gadon,kawai bata ankaraba taji Ayan ya kama mata waist,ihu ta saki don ko kadan bata lura da shi ba, kawai direct zaninta ya cire ya wurgar nan take ihsan ta fara kuka tana yarfe hannuwanta, ko kallon ta baiyiba ya daga ta tsaye ya turata yayi jikin bango kallon yanayin shi tayi taga San yau she’s in trouble, kuka tafarayi sosai don yanda ya danneta da bango yana rough and mean play daita, jikinshi sai rawa yake, bakinshi ya hada da nata ya fara daga kafanta daya daga inda take tsaye, zare bakinta tayi tana cewa
“Dan Allah… Kayimin rai…kayi hakuri…. Or pls take it easy…” Tafada cikin tashin hankali,
“Really?..” Ya fada cikin gurnani kaman zaki,
“I have always promise you.. Rough and bad sex…Kuma babu abinda zan fasa har sai na koya maki hankali…” Ya fada yana kara daga kafanta yanda zai yi daidai da satin waist dinshi, kokarin connecting kanshi yayi daita yaji hakan bazai yuwuba, da Sauri ya birkitata tare da komawa bayanta dukar da ita yayi ya fara kokarin connecting kanshi da ita ihsan sai ihu take tun kafin ya kai koina, bai saurareta ba yayi forcing kanshi, wani razanannen ihu ihsan ta saki, nan take jikin ta ya saki, Ayan dai bai San inda hankalin shi yake amma yasan something is wrong somewhere. Kara thrusting yayi ihsan ta kara sakin ihu, da Sauri Ayan ya fara cewa
“Who…did…this… To me?…” Yafada kaman zaiyi kuka,
“Who ruined my ..happiness… My joy…my everything…” Yafada yana fashewa da kuka, ihsan kam batasan inda take ba duniya ko hell, idanuwanta bude amma bata gani, the only thing take ji shine azaban da take ji under her, Ayan kokarin slowing down yayi amma abinda da novice kasawa yayi, tun ihsan na ihu sai tayi shuru tana jiran numfashin ta na karshe ya fita, kafin Ayan ya samu nutsuwa ta fita hayyacinta, ahankali ya tashi yana cire hannun shi dake kan waist dinta ta fadi kasa, Ayan kallon kasa yayi yaga jini,
“Precious… Precious..” Ya fara kiranta yana girgiza ta at the same time yana kuka, gani ko motsi batayi , da gudu ya dauki towel dinshi ya daura ya debo ruwa ya Dan watsa mata, kawai sai ta saki ajiyan zuciya, tana kara fashewa da kuka Mara sauti, tallabo face dinta yayi nan kasa yana cewa.
“I will not forgive.. Who make me suspect you…am.so sorry… I was misled….” Yafada cikin kuka, hannun shi ta ture jikin ta na rawa tana kuka tayi kokarin mikewa, kara tallabo face dinta yayi
“Precious… I know am a monster…but you need my help now…” Yafada cikin kuka
Kara tura hannun shi tayi tabude baki zatayi magana amma ta kasa sau hawaye kawai take, ahankali ta mike zaune Ayan ya Dora kanta kan kirjinshi yana shafa kanta ahankali sai ruwan hawaye yake,cikin kuka ta kara tureshi tana cewa
“Ka dade ..kanason….cutar..dani…Kuma…you have… Succeeded….sai ka zuba ruwa kasa kasha …” Ta fada tana kokarin tsayawa, Ayan hada kai da gwaiwa yayi yana kukan bakin ciki, gani yake in da za a bashi Wanda ya turo mashi pic da video din ihsan da babu abinda zai hanashi sa mashi wuka. Kokarin daukan zaninta tayi amma ta kasa, Ahankali ta fara taka tana dafa bango, da Sauri Ayan ya mike ya gyara daurin towel dinshi ya dauketa wani irin karta ta kai mashi a fuska, ji yayi kaman an yageshi da razor amma bai saketa bahar sai da ya ajiyeta kan gado ya shiga cikin bathroom ya hada mata ruwan wanka amma yana fitowa yaga babu kowa, da Sauri ya nufi part dinta har bedroom dinta ya shiga babu kowa sai kukanta dayaji a bathroom dinta, kokarin bude kofan yayi amma yajita rufe, kai yq hada da kofan ya cigaba da kuka yana cewa
“Wallahi ihsan sai nayi Maganin makiyanki…sai na nemo Wanda yayi sanadiyar Sani CI maki mutunci…pls baby am sorry.. Ki yafemin… Bazan kara ba…” Ya fada cikin kuka sosai, ihsan dake hadawa kanta ruwan wanka don tana da knowledge kan irin wannan don ta sha karantawa a novel yanda amare ke yi on their first night, tana kuka ta cika bathtub da ruwan dumi Ahankali ta shiga ta saki ihu, duk hankalin Ayan ya tashi saboda irin kukan da take
“Baby pls open…let me help you… Remember am a doctor.. Pls..” Ya fada cikin kuka, ihsan ko jin shi batayi saboda abinda ya isheta daban, haka tayi relaxing cikin bathtub din dumi na shiganta nan cikin ruwan wani irin wahalallen bacci yayi gaba daita, Ayan kam yafi hour tsaye yana jiran fitowa ihsan amma shuru, buga kofan ya dingayi yana cewa
“Precious ki fito in nuna maki my reasons… In dai har kin ga laifina duk hukuncin daya dace dani kiyi min… Pls open..” Ya fada cikin magiya amma ina ihsan ta dade da bacci don haka batajin shi.

Sai wajen karfe goma da rabi husna ta tashi daga falo ta shiga dakinta ta kwanta, bag da sis dinta ta dauki pad daga ciki ta gani sai lokacin ta fara aduan Allah yasa kar sis dinta ta dauki key din don ta san halin ta da inquisitive, aikam tana bude bag din key ta fara ganin bude. Wani irin kara ta saki tana cewa
“Shikenan.. Kin kasheni….wayyo kin kasheni..”tafada hawayen bakin ciki na malala kan fuskan ta, da Sauri ta nufi dakin sis dinta data dade da bacci tun a corridor take cewa
” Wallahi yau sai na kasheki….sai na kasheki…ubanwa yace ki bude makullin da kika gani cikin bag dina…” Ta fada tana shiga dakin, aikam haye kan sis dinta tayi ta shake wuyanta tana cewa
“Yau kasheki zanyi…watarana kin kara taba abinda ba naki ba…” Tafada tana kara shaketa , itakam batasan hawa ba taji husna na Neman aikata barzahu da karfi ta tureta ta saki ihu Wanda hakan yasa mami taho wa da gudu tana cewa
“Inna lillahi waina ilaihi rajuun….” Tafada data ga husna na kara danne wuyan sis dinta, wani irin mari ta dauke husna dashi Wanda yasa ta sakin sis dinta ta zube kasa tana kuka
“Me tayi maki zaki kasheta?..” Mami ta tambayeta cikin fada, husna batace kala ba sai kuka kawai take Kuma ba kukan Marin mami take ba no, kukan an bude zuciyan Ayan kawai take,
“Me kikayi mata?..” Mami ta tambayi lil sis dake rike da wuyanta tana kuka,
“Banyi…mata…komai…ba…” Ta fada da kyar don har lokacin numfashin ta bai dawo daidai ba, mami kallon husna dake kuka kaman ranta zai fita tayi ta sake cewa
“Baki fadin abinda tayi maki?…” Husna ko kallon ta batayi ba ta mike tana kuka ta bar dakin, dakinta ta koma ita Kuma mami na biye daita,
“Wallahi ban yarda …ko an bude zuciyanka..sai na mallakeka..you are mind and mind alone…wallahi only death will make me give up…amma wallahi you are mine…” Duk maganar da take kan kunne mami, da Sauri mami ta riketa tana cewa
“Who is yours?..” Husna shuru tayi tana kaf2 da idanuwa kaman munafuka, girgiza shoulder dinta mami tayi da karfi tana cewa
“I said who is yours!…” Mami ta fada cikin irin muryan da husna bata Santa dashi ba, da Sauri husna tace
“Ba kowa…” Mari mami ta dauketa dashi
“Tell me before I strangle you to death…” Mami ta daka mata tsawa, da Sauri tace
“Ayan!…” Da Sauri mami tace
“Which Ayan… Badai mijin daughter ba?..” Cikin kuka husna tace
“shi…I love him….” Haba wani irin mari mami ta dauketa dashi sai dai.kawai ta ganta tana swinging sama saboda yanda ta fita hayyacinta
[12/27, 14:14] ‪+234 814 199 1000‬: DECEMBER 20, 2017 11 COMMENT(S)
kawarta ce sanadi 47

💙💜💛🖤❤💚
KAWARTA CE SANADI
💜💛❤🖤💚💙

®zuwairat?(ummu Maryam)

4⃣7⃣

_Wannan Kuma nakune *dukkan writer* s dake kaunar yan uwansu tsakani da Allah ba don munafurci ko ganin idoba, Allah ya kara mana baseera mai amfani, ameen_

“Repeat what you said!…” Mami ta fada tana kokarin shaketa, cikin kuka husna tace
“Wallahi shi nake…” Kara dauketa da mari mami tayi ta kara cewa
“Repeat it…” Wannan Karin husna goge idonta tayi Sannan tace
“I love him…” Marinta mami zata sakeyi sai ta kauce tana cewa
“Ko.kasheni zakiyi bazai hanani furta son da nakeyi mashi ba…wallahi shi nake so Kuma babu wa da ya isa ya hanani samun shi…” Yanda tayi maganan kaman yar kwaya yasa mami raxana don idanuwa ta dinga zarowa kaman mai aljanu tana cewa
“Tun kafin ihsan ta San da zaman shi nakeson shi…Kuma …”
“Shut up!!!!..” Mami ta daka mata tsawa,shuru tayi tana kara fashewa da kuka, itama mami fashewa tayi da kuka tana cewa
“Bazan you can be this dangerous ba…nasan am not an angel amma bakin halina bai kai naki ba…ya zaayi ace mijin the only best friend you have kike so…tirrr da hali irin naki….wallahi in fada maki yanda nake ji da ihsan ban ji dake..don haka tun kafin dare yayi maki ki fidda shi daga cikin ranki…” Tafada tana nunata da yatsa, cikin raki da ihu husna tace
“I can’t!!!… Kuma ihsan is no more my friend… Kiri2 tana ganin son.Ayan a idona amma ta aureshi..Kuma wallahi for that I will teach her a bitter lesson…” Mari mami ta kara dauke dashi Wanda ya fi biyun farko zafi
“Kullum kina gidan su ihsan Ashe don wata manufa kike zuwa?… To listen attentively… Ayan can never be yours…ihsan owns Ayan.. Wake up from this dream don nothing is consuming as hatred..zaiyi consuming dinki while better things will pass you by…Kuma INA fada maki.. Kar in kara jin wannan maganan…” Mami ta fada cikin kuka don ita yanzu tsoron yarta take, husna zaro ido tayi tana cewa
“Ihsan will never own Ayan… Ayan belongs to me… He’s mind..and nobody can stop it…” Aikam.haye kanta mami tayi ta fara dukan ta kaman babu gobe amma husna bata bar repeating
“Ayan is mine ba…” Mami gajiya tayi Dan kanta ta kyale ta, husna mikewa zaune tayi tana cewa
“Zanbi hanyar da Kuma koyamin har sai na samu Ayan…” Da Sauri mami tace
“Wace hanya you daughter of Jezebel…” Husna Dariya tayi kaman wata mahaukaciya tace
“Haba sweet mami kin mance kin koya min anything is possible saboda herbalists… Kin nuna min malamai can make dream come through… Don haka am stepping up above you…” Tafada tana kallon mami babu ko digon tsoro a idanuwanta, mami baki ta kama tana kuka tun yanzu ta fara nadama tarbiyan data bawa husna, Ahankali ta mike ta kama husna aikam sai husna ta tureta mata hannu tana cewa
“Ki kyale ni…don babu abinda zaki fadamin da zai hanani aiwatar da abinda nayi niyyan yi…”
Tana kaiwa nan ta bar mami zaune dakin tana kuka ,
“Inna lillahi waina ilaihi rajuun!!…” Mami ta dinga maimaitawa don tasan she is reaping what she sow tun yanzu, don yanzu ta lura husna will be more dangerous than python.

Ayan dai zama yayi har bacci ya fara dauke shi shima nan bakin kofan bathroom, da Sauri ya firgita yana kallon agogon bango, gani yayi har after 10, da Sauri ya mike ya kara dan buga kofan yana cewa
“Precious pls what are doing to yourself?… Pls am so sorry…” Yafada Ahankali amma shuru, da Sauri ya fita daga dakin daya tuna spare keys, da gudu yaje ya dauko su ya dawo, Allah ya taimakeshi da akwai label jikin su , key yasa ya bude aikam yanayin kwanciyan ihsan cikin bathtub yasa shi shiga tashin hankali don tamkar gawa, da gudu ya karaso ya dauke daga cikin ruwan har lokacin ruwan da Dan dumi amma ba sosai ba, abinka da farar mace duk kasan idanuwanta sunyi ja, tanajin an dauke ta ta bude ahankali, ganinta hannun Ayan yasa ta kara fashewa da kuka,
“Shuuu…” Ya fada mata cikin sanyin murya, kuka ta cigaba dayi har ya kwantar daita kan gado, fita yayi daga dakin ya koma side dinshi ya yi wanka ya fito ya saka jallabiya ya bude wata drawer ya dauko pills Sannan ya fita, kitchen ya shiga ya hada tea ya nufi bedroom din ihsan, tana nan yanda ya kwantar daita saidai ta lullube kanta da duvet, bakin gadon ya zauna yana kallon face dinta cikin tausayi da jin haushin kanshi saboda irin rashin mutunci da ya dinga yi mata, Ahankali ya shafa face dinta yana cewa
“Baby ki tashi kisha magani…” Yafada cikin whisper, ihsan bata bashi amsa ba, kara maimaitawa yayi amma sai ta juya mashi baya, duk yanda Ayan yaso ta sha pills ko kallon shi batayi ba balle ta amshi Maganin tasha, gajiya yayi ya ajiye su ya kashe wutan dakin ya kwanta, aikam nan take ihsan ta mike zaune fuskan ta babu walwala ko kadan ta fara cewa
“Baka gama zalunci ba?…” Shima Ayan mikewa yayi
“Baby am so sorry.. Wallahi abinda nayi maki is not on purpose.. Kawai anyi misleading nawa…am sorry.. Ki yafemin… Wallahi bazan bar Wanda ya shafa maki baki a idona ba…pls ki bani hadin kai mu gano wannan makiyan…” Bai idaba yaga ihsan na kokarin sauka daga kan gadon, da Sauri ya kamota ya rungume, sai kuka take,duk yanda yake lallashinta abanza…saida ya zaro mata ido ta lafa jikin shi don dukda tana jin haushin shi ko kadan bata bar tsoron shi ba.
Kara mike zaune yayi yana cewa
“Oya drink this…” Yafada yana mika mata magani fa tea, cikin kuka ta amsa tasha, tsaya kallon yanda cikin ta ke rawa yayi ya fara cewa
“Baby nasan nayi maki laifi…amma ki bari in gama fada maki komai…in har lokacin baki bar ganin laifina ba…then ki dauki duk matakin da kikeso…kin San I love you… Ban taba dreaming for second zan iya hurting dinki ba…wani ya samun hatred dinki cikin zuciyata…” Ihsan dai shuru tayi tana hawaye don ko kadan batason jin muryan shi, she despise him so much amma what can she do, tallabo face dinta yayi yana kallon yanda idanuwanta suka kumbura, kura mata ido yayi yana tunanin who could hate this angel so much to the extent of sharing her nude pic, bakinshi ya kai saitin swollen red lips dinta yace
“Babyna am sorry… Kome kikeso zanyi….ki bar kuka pls…” Batace kala ba kawai dai kuka, the more tana kuka the more hankalin Ayan ke kara tashi Kuma zama daita ahaka with her sleepy eyes and her naked skin makes him want more amma he don’t ever want to hurt her again, kissing dinta yayi for as long as he could remember, saida yaji numfashin ta na nema dauke wa ya zare bakinshi ya mannata kan chest dinshi yana tunanin he’s the luckiest man alive, cikin whisper yace
“Babyna pls just tell me want you want… Da ina tunanin zan baki wata kyauta amma yanzu abinda nayi maki yafi karfin wannan abun… So pls just say what you want..” Yafada yana kara turata cikin jikin shi, ihsan daure fuska tayi tan hawaye, idanuwanshi lumshe yana cewa
“Zan saya maki mota…” Bai idaba yaji ihsan nacewa
“Banaso….” Dan Dariya yayi
“To zan bi maki hajj…” Kara cewa tayi
“Banaso…..”
“Then what do you want?…” Yafada yana daga ta don kallon face dinta,
“Leave me alone…” Tafada mashi atakaice,
“You know I can’t… Kawai rest you have heard enough today…gobe zan nuna maki abinda aka turo min…” Karamin bakinta ta tabe ta juya ta kwanta abinta, kara matsawa kusa daita ya rungume ta, gabanta ne ya dinga faduwa saboda yanda take jin shi.

Ahaka suka kwanta cikin dare ya kasa dole ya tashi ya bar dakin don yasan in har zai kwanta tare daita dole sai Kara Kuma that will be the last thing he will do right now.
Da asuba ya tashi ya sake wanka tare da alwallah ya saka jallabiya Sannan ya koma part din ihsan, direct bathroom yashiga ya hada mata ruwan wanka
Dakin ya dawo ya zauna bakin gadon ya dan taba forehead dinta Ahankali ta bude idanuwanta da sukayi mata nauyi, tana ganin shi ta daure fuska, shidai murmushi yayi yace
“Good morning baby…” Yafada cikin whisper, kauda kanta gefe tayi bata amsa mashi ba, yaye blanket yayi yana cewa
“Tashi kiyi wanka kiyi salla…” Kara maida blanket din jikinta tayi tana turo baki, kara yayewa yayi ta maida kawai sai ya dauketa
“Put me down…” Ta daka mashi tsawa , Dariya yayi ya ajiyeta, tafiya ta farayi tana dingishi
“Sorry…” kawai yake ta maimaitawa amma ko kallon shi batayi ba, tana shiga bathroom ya bude wardrobe dinta ya fiddo mata long gown ya ajiye Sannan ya koma part dinshi ya goge kasan tiles dake da jini ya tafi masjid.
Kan praying mat ya tarda ihsan daman already ya dauko wayanshi, zama yayi nan kasa yana cewa
“Precious let me show you what I have been talking about…” Ya fada yana bude inda aka turo mashi, ihsan dai kauda kanta gefe tayi bata amsa mashi ba, bude pic din yayi yace
“Precious kalli…” Bata daga kai ba Dan matsar da wayan yayi kusa daita amma ta Dan matsa baya bata daga kai balle taga abinda yake nuna mata,
“Baby am serious… Just take a look…” Yafada mata amma bata kalla ba, Dan dauke wayan yayi yace
“Did you know about it?…” Ya tambayeta cikin sanyin murya, still bata kalleshi ba Kuma bata ce kala ba, chanza pic din yayi ya maida video ta, wannan wakan da take in tana wanka ta faraji, Kuma muryanta sak, Ayan kura mata ido yayi don yaga reaction dinta, ihsan dai kafa kunne tayi tana jin wakan, da Sauri ta juyo ta fixge wayan daga hannunshi, idanuwa ta bude tana kallon kanta naked in shower, hannu tasa ta dan murza idanuwanta don tabbatar she’s not dreaming, Ahankali hannun ta ya fara kyarma ta daga kai ta kalli Ayan ta Kuma kallon video, idanuwanta Sam babu hawaye sai dai waje suke kaman zasu fado, bakinta na shaking ta fara cewa
“My…bathroom… This is my bathroom…” Ta fada Sannan ta kwala ihu Wanda yasa yan cikin Ayan kadawa, da Sauri ya amshi wayan daga hannun ta, tsayawa tayi tana kallon shi har lokacin babu hawaye idanuwanta wani irin kara ta kara kwallawa Ayan yayi saurin rike, jikinta sai kaf2 yake kaman mai convulsions,
“Wayyo… Wayyo.. Wayyo… Who?…” Tafada bakinta na shaking, Ayan rungume ta yayi yana hawaye, tureshi tayi ta kara cewa
“Who?…who…did..this?….” Ta tambayeshi tana zaro mashi idanuwa, cikin kuka yace
“I don’t know… Turomin akayi..they told me you are their leftover…” Fa Sauri ihsan tace
“Me…a leftover?…” Ta fada hawaye na zubowa idanuwanta lokaci daya,. Da Sauri ta mike tana cewa
“Yanzu ..kasha…ganin nakedness dina?…” Ta tambayeshi tana tsaye kanshi, daga wet face dinshi yayi yana kallon ta, da Sauri tayi hanyan waje, at that moment ta mance da ciwo dake gareta, da gudu ya bi bayanta ta fixge
“Don’t touch me…” Ta fada cikin matsanacin kuka, kamata yayi
“Baby ina zaki?…” Ya tambayeta cikin tashin hankali don tamkar mahaukaciya ta koma mashi,
“Gidan mu…zani…sai sun fadamin Wanda…yayi min …hakan..” Tafada in a pitiful way, kara kamata Ayan yayi ya rungume ta gam, yana cewa
“Don’t worry… I will do whatever it takes to find out who did this… Wallahi that is a promise…” Ya fada cikin kuka,
“No…just leave me…ban zama…gidanmu zani…” Tafada tana kokarin kwace kanta daga rikon da yayi mata amma ta kasa, Ayan sai ya tsani kanshi saboda yanda take kuka, sai Dana sanin fada mata yanzu yake,
“Am sorry.. Kukanki is too much… Pls just keep calm and leave everything to me…” Cikin kuka ta daga kanta ta kalleshi da idanuwanta da suka chanza kala
“How many people have seen me …nakedddd…” Tafada kaman ranta zai fita, Ayan kamata yayi yana cewa
“I don’t care how many people have seen you naked…ke matata ce Kuma I love… Am sorry for all you have been through…I will teach your enemy a lesson of a life time…” Yafada yana shafa bayanta Ahankali, bata bar kuka ba amma ta kafe ajikin shi, ko kadan batayi tunanin husna ba, hannun ta ta zagaye waist dinshi dasu ta daga kanta Ahankali tace
“Pls..who did this to me?…” Ta tambayeshi, Kara kwantar da kanta yayi kan broad chest dinshi yana cewa
“I don’t know.. But I know it’s someone close to you…” Ya fada cikin whisper, cikin kuka ta kara cewa
“Like who?..” Ta tambayeshi muryan ta na cracking, shuru Ayan yayi for a while Sannan yace
“Maybe husna…” Ya fada har cikin ranshi, da Sauri ta daga kanta ta kalleshi tare da girgiza mashi kai tana cewa
“It can’t be possible….”
[12/27, 14:14] ‪+234 814 199 1000‬: DECEMBER 20, 20171 COMMENT

kawarta ce sanadi 48


KAWARTA CE SANADI

®zuwairat (ummu Maryam)

_ Alhamdulillah, alhamdulillah,
Alhamdulillah
Alhamdulillah_

“Yes she can..” Ya kara reassuring dinta, dukan shi ta farayi tana cewa
“No..she can’t …she is my best and only friend…” Ta fada kaman zatayi kukan jini
“Don’t worry…I will find out… Just relax…” Yafada yana shafa bayanta
Haka ya dinga rarrashin ta amma bata bar ba, har karfe 9:30 na safe bata bar kuka ba duk hankalin Ayan ya tashi ba don kuka kawai take amma babu hawaye idanuwanta sun kumbura sosai, Ahankali ya mike ya kalleta
“Precious me zakici?..” Ya tambayeta yana kama hannun ta, daga kai tayi ta kalleshi amma bata amsa mashi ba,
“Pls baby enough of the tears…ki fadamin abinda zakici…” Ya fada yana murza hannun ta Ahankali,
“Ban..jin….yunwa…” Ta fada cikin shessheka, Ayan kallon tausayi yayi mata Sannan yace
“Baby you just make me regret for telling you… Kawai da nayi shuru na bar duk Wanda yayi hakan da Allah.. Amma kawai inason kisan ba haka nan nayi maltreating dinki…pls am sorry.. I own you now Kuma am telling you ki bar komai a hannu na…” Yafada mata Ahankali, ihsan dai shessheka kawai take,
“Bari in sayo mana breakfast…” Ya fada mata tare da kissing din goshinta ya fita, ko kayan jikinshi bai chanza ba ya dauki key na mota ya bar gidan. First hospital ya biya Don daukan Maganin bacci kwata2 ya mance da irin kayan da ya saka, sai Sauri yake zai shiga office dinshi Yusuf ya hangeshi, tun daga nesa Yusuf yake yi mashi kallon mamaki don he looks happy and a little bit messed up, yana shiga office Yusuf yabi bayanshi, cikin wani cabinet ya dauke wata magani yana juyowa sai ga Yusuf ya harde hannuwanshi yana kallon shi,
“What are you up to…” Yusuf ya tambayeshi, Ayan dai shuru yayi zai wuce Yusuf ya Dan rikeshi,
“Zaka fara ko?.. What is the problem…” Ayan tsayawa yayi for a while kawai sai ya saki murmushi, shidai Yusuf kallon shi kawai yake kaman he’s seeing him for the first time, kai Ayan ya daga ya kalli Yusuf daya saki baki yana kallon shi Sannan yace,
“I am a man again…” Da Sauri Yusuf ya zaro idanuwa yana cewa
“Really?…” Kai Ayan ya gyada mashi yana murmushi, Dan kara matsawa kusa da Yusuf yayi Sannan yace
“And we heard our …first night… Yesterday…” Wani irin tsalle Yusuf yayi yana cewa
“Yesssss….tell me about it…” Hararan shi Ayan yayi Sannan yace
“News monger….nothing for you..amma inason in gode maka da Muhammad for you friendly advice and support.. Wallahi dana rasa ihsan danayi asara…thank you so much …” Yusuf Dariya yayi yana daga mashi gira daya Sannan yace
“Wani yana santi kenan… Well alhamdulillah… Amma Kuma hope babu wata matsala cos your eyes are a little bit swollen…”
Shuru Ayan yayi ya Dan sadda kanshi kasa, Ahankali Yusuf ya dafa shoulder dinshi
“Guy anything?…”
“I told her somebody sent me her nude pic…” Ya fada cikin sanyin murya, daure fuska Yusuf yayi
“Wai da gaske ne?…”
“Yes…ba da wasa nake ba…you know I can’t joke about something like that…she has been crying all morning…” Tsoki Yusuf yaja Sannan yace
“Amma you are such a joy killer…da sai ka kyaleta da abinda ya dameta not add more salt to the injury…” Yusuf ya fada mashi,
“I know.. Amma I need to tell her the reasons behind my behavior… I was rough and mean last night… I really hurt her and…I had to tell her…”
Ayan ya fada kaman zaiyi kuka, Yusuf shuru yayi Sannan yace
“Amma am still wondering.. Who could do such… Gaskiya we have to find out..” Da Sauri Ayan ya gyada mashi kai,
“That’s compulsory.. I have to go..xan nemo mata abinda zata CI…” Ya fada Sannan ya fita daga office din.

Wacegari husna ta tashi da matsanacin ciwo kai daga jiki saboda irin dukan data sha hannun mami amma tana tasha ta shiga bathroom da gudu ko brush batayi ba ta fito ta saka gown ta yafa Vail ta dauki bag dinta ta fita ko fadawa mami batayi ba din tashin hankalin data saka kanta, adaidaita ta tsaida ta hau ta fada mashi ya kaita unguwan su ihsan. Karfe 10 saura quarter ta sauka daga adaidaita gaban gidansu ihsan, daman basu fiye kulle gate ba don haka bata samu matsalan shiga ciki ba, a bakin kofan falo ta tsaya ta yi knocking tana kokarin gyara face dinta don kar ihsan ta gane tana cikin matsala, gajiya tayi da knocking ta bude kofan ta shigo falon, bata ga kowa ba direct hanyan part din ihsan ta bi tana cewa
“Babe kina inane?…” Ta fada on top of her voice, ihsan dake kwance tana kuka zuci taji kaman muryan husna, Ahankali ta mike tana goge face dinta don batason ta gane halin da ake ciki don for that moment she don’t want to talk much talk less of telling her what she’s been through From yesterday to now, tana takawa Ahankali ta fito falo, itakuma husna ta bude kofa kenan taga ihsan ga yanda ta koma idanuwanta sunyi kuru2 da Sauri ta karaso wajenta, itakuma ihsan dan sadda kanta kasa tayi tana murmushi,
“Babe kece da sassafen nan?..” Ta fada tana kokarin daidaita voice dinta, husna tsayawa tayi tana kallon yanda take tafiya nan take ta gane ya sadu daita Kuma ta gane asirinta ya kusa tonuwa, dafata husna tayi ta tana cewa
“Babe lafiya?… What’s wrong with you?…” Husna ta tambayeta sounding caring, ihsan kara murmushi tayi tana cewa
“Babu komai… Pls sit…what can I offer you .,” ta fada muryan ta da rawa,
“Babe pls what’s wrong?..” Daga kai ihsan tayi tana kallon ta for a moment Sannan tace
“What did you see?…” Tambayan ta ta tsosawa husna rai amma ta sai tayi pretending tace
“Your eyes are so so so swollen.. And tafiyanki kaman mai tatata,..kodai..kodai?…” Ta tambayeta kawai don taji zahiri,.
“Ni dai ki fadamin abinda zan yi serving dinki dashi…”
Husna na zama tayi gabanta na faduwa tace
“Yanzu babe baki fadamin abinda ke damunki?..” Itama ihsan zama tayi Ahankali tana dafa kujera Sannan saida ta dan chiza lips dinta saboda yanda take ji Sannan tace
“Nifa na fada maki babu abinda ke damunna…” Dariyan karfin hali husna tayi Sannan tace
“Da gani wata taci kwakwa jiya…har tafiyan ki ya chanza… Hmm am happy kin San saboda me?…” Husna ta tambayeta, ihsan daga kanta tayi tana kallon husna, alokacin sai maganan Ayan daya fada mata yana zargin husna ta fado mashi
“What if he’s right…” Da Sauri Kuma ta dauke maganan daga zuciyanta
“Not at all… Never..” Ta fada cikin ranta,yanda ta kurawa husna ido yasa gabanta mugun faduwa
“Babe wannan kallon fa?…kaman baki ta taba ganina ba?..” Ajiyan zuciya ihsan tayi tare da sakin murmushi Sannan tace
“I just zoom out for a second… What where you saying…”
“Hmmm kawai ina farincikin Ayan zai bar zargin ki tunda ya ganki intact…Kuma am thinking karya yake don nasan …”
“He showed me… Da gaske ne…” Tafada tana fashewa da kuka, da Sauri husna ta dafe kai tana cewa
“You mean da gaske ne antura mashi…me ma yace?…” Ta tambayeta kaman batasan the whole thing ba, ihsan. Dai kuka ta cigaba dayi, husna rungume ta tayi ihsan ta cigaba dacewa
“Who would hate me so much to spread my nudity…who?…” Ta tambayi husna cikin kuka, itama husna fashewa tayi da kuka amma nata kukan na bakin cikin Ayan ya kusanci ihsan ne Sannan tasan her games are almost over,
“Never…” Ta fada cikin ranta azahiri tace
“I don’t know… Something is wrong somewhere… Inna lillahi.. Dole ayi bincike… Dole a San abinyi…subhanallahi…” Yanda take magana nan take Dan zargin da ihsan ke yi mata ya gushe cos she’s such a drama queen, it will only take the will of Allah to identify her true colour, ihsan goge hawayen ta tayi tana cewa
“You need to see what Ayan did to me last night… Sauran kadan daya kasheni… All because he thinks am a slut… Duk Wanda yayi min wannan abun will know no peace… Sai yafini toxarta duniya da lahira…” Cikin kuka husna tace
“Insha Allah… Allah zai toni asirin ko ma waye… Wallahi tausayin ki kawai nake…imagining namiji yayi forcing kanshi on you…Allah sai ya saka maki…gaskiya dole ayi investigation…” Ta fada cikin matsanacin kuka,rungume juna sukayi suna kuka, bayan kaman minta ashirin husna tace
“Bari in tafi in barki ki huta…you need to rest…” Husna ta fada tana mikewa, Ahankali itama ihsan ta mike daman she wants her gone kafin Ayan ya dawo, taka mata baya ta farayi cikin ran husna sai ci yake da bakin ciki saboda ji take bata taba jin tsanar ihsan cikin ranta kaman na yau ba, she can’t believe yanzu babu wata zargin tsakanin ihsan da Ayan ba, yanzu tasan son da yake mata na yanzu sai ya fi Wanda yake mata wannan lokacin, suna zuwa main falo ta juyo ta kalli ihsan dake tafiya ahankali
“Babe ki koma ki huta…sai munyi waya…” Ta fada mata,
“To shikenan.. Ki gaida mami da lil sis…” Baki husna ta tabe
“Lil bitch dai…” Ta fada cikin ranta tana barin falon . ihsan zama tayi nan falo tana tunanin halin husna , kawai sai ta fara tuna yanda husna ke son jin every details of what ever she did, while ita ki kadan bata damuwa da alamuranta, ajiyan zuciya ta Dan saki tana lumshe idanuwa.

Husna na fita waje ta jara fashewa da kukan bakin ciki, ji take kaman ta je gida ta kwantar da lil sis dinta ta yanka wuyanta saboda yanda take jin haushi.
“I have to take this to the next level… I have to go to the extreme..” Tafadawa kanta tana fita daga gate din, tana tafiya tana tunanin meye next plan dinta don yanzu ita gani take malamai ko bokayen hausawa bazasu Iya yi mata irin asriin da take so na, Dan jingina tayi da bango gidan ihsan tana tunanin abinyi , tafi minti ashirin nan tsaye Sannan ta daga kai tana cewa
“Yes..I have to meet madam chinyere…nasan igbo Dana asiri sosai… Su kadai ne solution yanzu…”
Ta fadawa kanta.
Ayan dake dawowa ya hangi wata daga nesa tsaye jikin gidanshi, Dan bata rai yayi yana mamakin who it could be?, yana zuwa kusa daita ya gane husna ce, Kara murtuke fuska yayi, husan na daga kai ta ganshi ya taho, da Sauri ta bar wajen tafara tafiya sai murmushin karfin hali kwance kan face dinta.
“I will definitely hold you when I have a good evidence against you…” Ya fadawa kanshi yana fita daga cikin motan don budewa kanshi gate, ko kallon inda take baiyi ba ya shiga motanshi ya shiga cikin gidan.

1 Comment
[12/27, 14:14] ‪+234 814 199 1000‬: DECEMBER 20, 2017 3 COMMENT(S)
kawarta ce sanadi 49

💙💜💛🖤💚❤
KAWARTA CE SANADI
💚❤💜🖤💛💙

®zuwairat( ummu Maryam)

4⃣9⃣

Yana parking ya fito da kayan breakfast daya sayo mashi ya shiga falo da sallama for the first time, ihsan daga weak body dinta tayi ta dan amsa mashi amma bai fito ba ta maida kanta kan kujera tare da lumshe idanuwa, Kusa daita yazo yayi mata kiss a cheek Sannan yace
“How are you feeling?..” Ya tambayeta cikin whisper, banza tayi dashi, kiss ya kara yi mata wannan Karin a bakinta Sannan ya mike, kitchen ya shiga ya sa ruwan zafi a gas Sannan ya fito da plates da fork ya ajiye kan dinning table, chips and salad yayi serving Sannan ya koma cikin kitchen ya juye ruwan zafi cikin flask ya ajiye kan tray tare da cup sai kayan tea ya dawo ya ajiye kan dinning, ihsan kam tana zaune sai shessheka take dukda ba kuka take, bata minti biyu sai ta saki ajiyan zuciya, Ayan ne yazo wajenta, dagata tsaye yayi yana cewa
“Let’s eat…” Yafada yana kissing wuyanta,Ahankali tayi kokarin zare jikinta daga nashi tana cewa
“Na koshi…”,
” no baby… Let’s go inyi feeding dinki…” Ya fada mata cikin whisper, bata Kara cewa komai ba ta bishi kan dinning, tea my kauri yahada Sannan ya dawo ya zaunar daita kan kafanshi ya fara bata abinci, spoon uku kawai ta amsa tace ta koshi, kara forcing dinta yayi ta kara amsa kadan Sannan ya bata tea tasha, shima ci yayi ya koshi Sannan yabata magani ba gardama ta amsa tasha Sannan ya dauketa kaman wata baby yana cewa
“Baby waya zonan bayan fita ta?…” Ya tambayeta muryan shi cool kaman ba mean and wicked Ayan ba, banza tayi dashi har suka kai daki ya kwantar daita shima ya kwanta,
“Me husna tazoyi ??..” Ya sake tambayan ta Ahankali, kallon shi tayi tace
“Ya akayi kasan ta zo nan?…” Ta tambayeshi cikin sanyin murya,
“Waje na ganta…” Dan bata fuska tayi
“Ban gane waje ka ganta ba…”
“Eh..I saw her out side this gate…” Da Sauri ihsan tace
“Tafi minti ashirin da tafiya kafin kazo…”
Shuru Ayan yayi kaman mai tunanin wani abu Sannan yace
“Wallahi Dan waje na ganta jingine da bangon fence.. Tana ganina ta fara tafiya…” Ya fada yana Dora hannun shi kan cikin ta, ahankali ta ture hannun shi Sannan tace
“Kilan mai kama daita ka gani…” Ta fada tana gyara kwanciya ta, Ayan Dan komawa zaune yayi yana tunani, shidai kawai he don’t like husna and he believe she’s up to no good, matsawa yayi kusa daita sosai yana tsaya kallon face dinta for a while Sannan yace
“Baby …ina zargin wannan husnar…” Yafada yana kallon reaction din ihsan, gani tayi ta hade rai, amma bai fasa abinda yayi niyyan cewa ba,
“I have weird feeling about her…kinsan bata barin gidanku… Cos in ba itaba babu Wanda zai daukeki naked …am sure of what am saying…” Ihsan Kara hade rai tayi, baki ta tabe Sannan tace
“Kai dai kawai you hate her…you never liked her…why would she do such a thing?…”
“Because I think she …loves… Me?..” Ayan ya fada atakaice, da Sauri ihsan ta mike zaune, kurawa Ayan idanuwa tayi tana mamakin statement dinshi,
“Meye tsakanin ka daita?…” Ta tambayeshi tana shirin kuka, shoulder dinta ya dafa Sannan yace
“Babu komai..amma nasha kamata tana yimin kallon so…lokacin da aka kwantar daita hospital I notice something…” Da Sauri ihsan ta fashe da kuka tana cewa
“Ashe daman soyayya kuke?…” Da Sauri Ayan ya rufe mata baki,
“Never.. Kawai am telling reasons da zaisa ta iya aikata wannan abun… Pls don’t misquote me…” Kuka tacigaba dayi tana cewa
“Am confuse… I can’t believe husna can do such thing to me…no..no..no.
.” ta fada tana kokarin fidda zargin husna daga cikin ranta,
“Then wa kike ganin zai daukeki pic naked kina bacci?.. Who did you think will do such if not a close person…” Cikin kuka ihsan tace
“I don’t know… That’s why nace ka barni in tafi gida in dubo ko da akwai hidden camera a dakina….pls…” Da Sauri ya rungume ta yana cewa
“Shush…let’s not talk about this anymore… Amma I want to ask you a question… Can you perform dua?..” Ya yi mata maganar cikin kunne, ihsan shuru tayi Sannan ta girgiza kai, face dinta ya tallabo Sannan yace,
“Dole kiyi yanzu…I.want you to know we have big problem.. In har bamu gano Wanda ya dauke pics ba bamu tsiraba cos bamu San abinda zaayi planning next ba…so yanzu zamu bar zargin kowa…we should be stead fast in praying.. Allah zai kawo mana mafita.. Alright?…” Ihsan kura mashi ido tayi for a moment tana tunanin she still hates him for what he did to her, amma Kuma she’s loving his comfort, he’s such a comforter,
“Ok…” Kawai ta fada Ahankali,
“Good…Kuma zan bada kudi a dingayi mana adua a mosque har Allah ya toni asirin makiyan mu..” Yafada mata yana kama hannun ta, Ahankali ta kara gyada mashi kai, face dinta ya kama yayi mata kiss for a while yaga tana lumshe idanuwa yasan he’s drugs is working, ahankali ya kara cewa
“Yanzu baby baki fadamin kyautan da zanyi makiba for making me the most happiest man alive…” Ihsan turo baki tayi ta janyae hannun shi daga fuskan ta tana cewa
“Ni ka kyale ni…mugu kawai…” Dariya yayi yana cewa
“Ai ba bunsuru kike cemin ba..well na nuna maki what he goat are capable of…” Yafada yana dariyan jindadin shi kanshi ya mance rabonda yayi irin shi, he’s so happy don gani yake he can’t be happier, jawota yayi jikin shi yaji har jikinta ya saki
Dan tureshi tayi ya kara jawota,
“Ka bari…”
“Me?.. Ya tambayeta cikin whisper, idanuwanta lumshe tace
” touching me…” Ayan dai sai kallon bakinta yake kaman zai cinyesu
“Am your husband…”
“Just go to you room..” Ta fada in sleepy tune,
“My room is anywhere you are…” Ya fada yana kara jawota jikinshi, ko minti goma baa karaba bacci yayi gaba daita Ayan sai kallon face dinta yake yana murmushi ko na meye oho, daga baya shima bacci yayi gaba dashi

Husna kuka ta dinga yi har ta isa gida, afalo ta tarda mami, mami na ganinta ta mike tsaye tana cewa
“Where the hell are you coming from Dan ubanki…” Ta fada tana zuwa kusa daita, husna Dan matsawa baya tayi tana cewa
“Daga gidan ihsan nake…” Daure fuska mami tayi kaman mai bori ta fara cewa
“Ubanme kika jeyi?…” Ta fada cikin tashin hankali don yanzu gani take husna na iya illanta ihsan don har yanzu lil sis dinta bata bar complain din wuyanta ba,
“Ba komai…” Da Sauri mami ta dalla mata mari tana cewa
“I said me kika je yi…” Ta fada on top of her voice, sabon kuka husna ta fara tana cewa
“Nidai babu komai…” Nunata da yatsa mami tayi tana cewa
“You see from this day on…ban yafe ba in har kika je gidan daughter… Tunda you are now as dangerous as the devil himself… Kina jina!…” Ta daka mata tsawa, da Sauri husna ta gyada mata kai amma cikin ranta cewa take
“Daman if am done with her bazata zauna gidan ba balle inyi visiting dinta…sai dai ita tayi visiting dina….” Ta fada cikin ranta tana shiga dakinta. Mami tabi bayanta da harara.

Daman koda ta fita bata tafi da waya ba so tana shiga daki ta goge hawayen ta Sannan tayi dailing number wata mata Wanda akayi storing da madam, few seconds later akayi picking,
“Madam good afternoon…” Daga chan bangaren aka amsa dacewa
“Afternoon.. Pls who is this?..” Husna hararan wayanta tayi Sannan tace
“Na mi…husna ilyasu from sociology department… Wacce kika bawa number dinki lokacin da nace wata rana zan zo gidan ki…”
“Ohhh…ya kike…” Matar ta fada cikin hausanta Wanda ko kadan bai fita,.
“Hmmm ba lafiya ba
…I seriously need your help…” Ta fada Ahankali,
“What is the problem?…”
“Pls ..I want …you…to tell me…in da akwai wani herballist da kika Sani….” Da Sauri Matan tace
“Jesus….herbalist Kuma?…” Husna tabe baki tayi
“Eh herbalist.. Ina cikin damuwa… Pls help…”
“Kuma you think a herbalist can solve your problem?… Just leave everything to God…”
“Pls madam tell me inda akwai wani da kika Sani koda baki zuwa…pls am dying…” Tafada tana fashewa da kuka, matar shuru tayi for a moment Sannan tace
“To AI Kuma kuna da boka..kije wurin su mana….” Da Sauri husna tace
“They are not active… Na yare nakeso…”
“Amma ain’t you young for all this?… What could lead you to such character…” Cikin matsanacin kuka husna tace.
“Am dying ..pls just tell me…”
“Na you sabi… Anyway.. Da akwai
Wani Dana ji ana bada labarin shi amma gaskiya ban taba zuwa ba…” Da Sauri husna tace
“Pls a ina yake….”
“I think a sabon gari yake… Naji ana kiranshi da ebube,….” Wata irin ajiyan zuciya husna tayi tana cewa
“Thank you so much…” Tafada tana katse wayanta, time ta kalla taga
11:10, kayan jikinta ta chanza zuwa skirt da riga na swiss atampa dinkin ya amsheta sosai, gyara face dinta tayi Sannan ta dauki Vail ta yafa ta fito falo, alokacin mami ta koma dakinta, lil sis dinta dake zaune ta watsawa harara Sannan tace
“Am not done with you…” Ta fada tana shiga dakin mami, mami na ganin ta ta hade rai,
“Mami zan shiga school.. Ki bani tp…” Ta fadawa mami babu alaman matsala tattare daita, hararanta mami tayi
“Munafuka babu school din da zaki…”
“Mami Wallahi school zani…yanzu wata course mat dinmu ta kirani ta fadamin zamuyi test karfe 2… ” kura mata ido mami tayi husna ta kara cewa
“Wallahi da gaske nake…” Tsoki mami taja ta dauki purse dinta ta dauko 1k ta bata,
“Mami wannan bazai isheni ba…zanyi tp Sannan Kuma banci abinci ba…” Mami batace komai ba ta Kara mata 1k da Sauri ta fita daga dakin.

Tana zuwa bakin titi ta shiga adaidaita tare da fada mashi ya kaita sabon gari, nan suka fara tafiya, suna zuwa sabon garin ta kara kiran madam ta tambayeta ko zata iya Dan yi directing dinta, madam ma saida takira wata akayi mata kwatance Sannan ta kira husna ta fada mata, discription da aka bata ta bawa mai adaidaita har suka isa gaban wani gida mai kyau, biyar mai adaidaita tayi ta fito tana kalle2 , duk yawancin wurin Igbo’s ne, wani ta tambaya gidan ebubu aka nuna mata wannan gidan mai kyau, bakin gate tayi knocking after few minutes aka bude mata ta shiga cikin gidan, Wanda ta bude mata ta tambaya in shine ebube kallon ta saurayin ya tsaya yi har na Dan lokaci Sannan yace
“Ba ni bane…yana ciki…” Ya fada mata yana mamakin what could such lovely lady zatayi a such a dangerous place.
“Pls nunamin….” Ta fadawa saurayin. Babu musu ya shiga gaba ta bi bayanshi har zuwa cikin falon, wani mutum ne Wanda bazai fi 40 …45 kallon husna yayi ya basar, saurayin daya kawota komawa yayi ya rage daga ita sai ebube,
“Good afternoon…” Ta fada mashi muryan ta na rawa,
“Afternoon.. How may I help you…” Ya tambayeta atakaice,
“Pls can I sit?…” Ta tambayeshi, kai ya gyada mata, zama tayi kan daya daga cikin kujeran Sannan ta fara fada mashi abinda ke tafe da ita
“Saurayina kawata ta kwace min…as am telling you… Sunyi aure..pls help me…” Ta fada tana kuka, mutumin kura mata ido yayi yana kallon ta kawai sai cewa yayi
“Kice mijin kawarki kikeso ba kwace maki shi tayi ba…” Yafada in a very clean Hausa kaman ba Igbo ba, idanuwa husna ta zaro tana ganin tazo inda ya kamata,
“Now me zanyi maki….” Ya tambayeta, cikin kuka ta fara cewa
“I want him to be mine…inason ya manta ya taba son ihsan..I want to be more valuable to him than his parents…” Ta fada cikin kuka, mutumin Dariya yayi Sannan yace
“As simple as abcd…” Yana fadan hakan husna ta fashe da Dariyan jindadi, da Sauri tace
“Me zan biyaka?..” Ta fada cikin jindadi, mutumin kura mata ido yayi yadan lashi lips dinshi Sannan yace
“You…” Dasauri husna ta kalleshi don Sam bata gane inda ya dosa ba,
“Ban gane ba….”
” I will sleep in you…asmau…” Ya kira sunanta direct, gaban husna ne yayi mugun faduwa, ta daga kai ta kalleshi,
“Inna lillahi…” Ta fada cikin fargaba,
“What…is not hard…that is the only way da zanyi maki aiki without delay…da kin bani hadin kai yanzu zuwa gobe kizo ki amshi charm da zakiyi amfani dashi, …” Husna dafe kirjinta tayi saboda yanda yake harbawa da karfi, da Sauri ta girgiza kanta tana cewa
“I can’t…” Bata idaba mutumin ya katse ta dacewa
“Don you are a virgin?… How many virgins mukayi harka dasu …use what you have to get what you want…that’s is the policy…” Ya fada mata, kai dai kawai husna ta cigaba da girgizawa,
“I can’t…zan nemi wani wurin… I just can’t….” Ta fada tana mikewa,
Kallon ta mutumin yayi yana Kara biting lips dinshi a hankali,
“Babu inda zakije da zaayi maki aiki kaman yanda zanyi maki…badai cikin garin nan ba…duk am on top of them…. Come let me show you something…” Ya fada yana mikewa, husan Dan Jan baya tayi , gaban wani madubi dake falon ya tsaye yace
“Ba wannan mutumin kike so ba?…” Ya fada yana nuna madubin, husan kallon madubin tayi sai taga Ayan kwance rungume da ihsan duk sai bacci suke hankalin su kwance, husna Kara fashewa tayi da kukan kishi da bakin ciki Sannan tace
“Eh..shine…pls ask for something else…not my virginity…I cant loose it..” Cikin kuka,
“You don’t have anything to offer me except for that… In kina iyawa good ..if you can’t.. Then you are free to go…” Ya fada yana komawa seat do shi, husna kneeling tayi gabanshi tana cewa,
“Pls kayimin rai…am dying of his love….” Mutumin banza yayi daita ya dauki wayanshi yana latse2,
“Pls help me…”
“Pls young lady you are disturbing me…am done..you can leave…” Ya fada mata atakaice, husna zama tayi nan kasa ta cigaba da kuka at the same time tana tunanin abinyi don confirm tasan son Ayan zaiyi sanadin mutuwanta muddin bata sameshi ba, Ahankali ta daga wet face dinta ta kalleshi,
“Zanyi…” Ta fada cikin matsanacin kuka
[12/27, 14:14] ‪+234 814 199 1000‬: kawarta ce sanadi 50

💙💜❤🖤💚💛
KAWARTA CE SANADI
❤💚💛🖤💜💙

®zuwairat( ummu Maryam)

5⃣0⃣

Murmushi mutumin yayi yana Dan lashe lips dinshi yana imagining irin garan da zai kwasa jikin husna, itadai husna kuka kawai take, at that moment ji take inama she could just forget about Ayan and go with her dignity amma ina??? Ta bari wannan hatred and jealousy of ihsan yayi consuming dinta, ebube mikewa yayi ya tsaya kanta yana kallon ta, husna Kuma sai kuka take kaman ance dole, sai tunanin kar mami ta gane take
“Don’t worry.. I will go easy on you…and am sure you will enjoy it..” Yafada yana dafa shoulder dinta,da Sauri ta Dan buge mashi hannu ta daga kanta tana kallon shi tare da watsa mashi kallon tsana da kyama dukda baida makusa amma ita ko cup din ruwa bata Iya sha da irin su amma gata zatayi zina da irin su, daga ta tsaye, Ahankali ta kara ture hannun shi, kara Dora hannun shi ya kara yi ya dinga shafa shoulder ta Ahankali, husna sadda kanta kasa tayi tana hawaye
“Let’s go inside my dear…or kin fi son nan?…” Ya tambayeta yana kokarin jawota jikin shi, husna tirjewa tayi daga wet face dinta tayi ta kalleshi
“Pls…” Bata idaba ya katse ta dacewa
“Don’t worry… I will be gentle…” Ya fada yana kama hannun ta, zare hannun ta tayi ta daure fuska tayi,
“Follow me..” Kawai ya fada ya kama hanyan daya daga cikin dakunan wurin, husna ta fi minti biyar tsaye Sannan ta bi bayanshi tana kuka,
Tana shiga dakin ta ganshi zaune daga shi sai singlet da boxer, gabanta ne ya kara faduwa tana tunanin is this really happening to her?, hannuwa ya bude mata alaman ta fado mashi amma tayi tsaye ta Dan daga kanta ta kalli agogon daki taga after 2, ganin bata da niyyan zuwa yasa ya taso ya wani kamata ya wulla ta kan gado, wani irin kara husna ta kwalla da Sauri ya sa yatsa kan bakin shi Sannan yace
“Ni na kawoki?..” Da Sauri ta girgiza mashi kai,
“Am I forcing you?..” Ya sake tambayan ta, da Sauri ta kara girgiza mashi kai,
“Then why do you want to make look like a rapist…if you are not interested.. The door is open.. Get out!…” Ya daka mata tsawa, da Sauri ta kama bakinta tana cewa
“I…will….not… Cry…again…” Ta fada hawaye na flowing face dinta, daga kanshi yayi ya kalleta ya Kara lashe lips dinshi Sannan yace
“Good…now come here” yayi commanding dinta, kara mikewa tayi daga kan gado ta zo ta tsaya gabanshi at that moment tayi deciding she will be strong afterall tasan ko ba virginity muddin ta gama da Ayan he will not care if she’s a virgin or not. Hannu yasa ya bude zip din rigan ta, daman bata sa bra ba don haka yana fidda rigan ta yaga naked boobs dinta husna dai lumshe idanuwa tayi bata cewa kala Kuma at the same time babu hawaye a face dinta, nan ya fara wasa da boobs dinta husna dai kaman baby doll ta koma don sai yanda yayi daita, wasa ya dingayi daita har ya cire skirt dinta ya cire pant dinta ta tsaya naked, duk abinda yake yi mata bata bude ido ba balle taji kunyan ko wani abu, shidai kaza ce ta fado daga sama gasassa don haka babu part of her body da bai taba ba, sai nishin dadi kawai yake, kama ta kashe shi takeji don haushin nishin shi dake sauka kan wuyanta amma who is she to say a word, haka ya gama
Romancing dinta ya kwantar daita, saida yazo introducing kanshi ta gane abun ba wasa bane, don duk da yayi alkawarin taking it easy ko.kadan bai yi wasa daita ba, he was rough and mean, sai ihu take tana cewa
“You…promise… To be….gentle… Pls…don’t…kill… Me…” Ta fada kaman numfashin ta zai dauke saboda yanda yake riding dinta babu wasa, amma sai cewa yake
“Aikinki na daban ne….” Sai ihu take shikuma yana santi kaman novice, sai bayan hour daya ya samu nutsuwa, alokacin kam husna ta jigata ta koma kaman ba itaba, kuka take amma babu hawaye, sai ajiyan zuciya take kaman wacce ta tayi gudu at 360, duk bedsheets din ya bace da jini, yana gamawa ya kwanta gefe ko kallon inda take baiyiba, bathroom ya shiga ta fito, ya kalleta Sannan yace
“Go and clean up kizo ki tafi…zan fita…jibi ki zo ki amshi charm da zakiyi amfani dashi…” Ya fada mata atakaice, Sannan ya nufi inda kayan shi suke ya saka ya bar mata dakin, husna sai ta fara Dana sanin abinda ta aikata, sai taji she hate herself for who she has become, kokarin mikewa tayi amma bata iyawa, hannuwanta ta fara yarfawa tana cewa
“Na shiga uku…na lalace….wayyo…na kashe…kaina…mami..zata ..gane…” Ta dinga maimaitawa, ganin ta dade bata fito ba yasa ebube ya Kara lekawa dakin kan gado ya ganta har lokacin ta hada kai da gwaiwa tana kuka,
“I said clean up…” Kai ta daga ta kalleshi
“I can’t move…” Ta fada gwanin ban tausayi amma sai cewa yayi
“What do you want me to do?… Carry you?… Pls be fast I want to go out…” Ya fada Sannan ya koma falo, da kyar husna ta mike tsaye tana kuka ta taka da kyar ta shiga bathroom tana durkusawa tana ihu tana tunanin ta yanda zata fita daga gidan ta kai gidansu baa gane halin da take ciki ba, ruwa ta zubawa gabanta ta kara sakin wani karan, kasa wanke private part dinta tayi saboda azaba da radadi ta fito tn dingishi, da kyar ta saka kayanta ta dauki bag dinta ta rataya ta fita tana dingishi, falo ta tarda ebube zaune ya Dora kafa daya kan daya yana girgiza su Ahankali, yana ganin ta fito ya kauda kanshi gefe husna wucewa tayi yaga yanda take tafiya kaman wacce akayiwa circumcision,
“Pls walk well don’t let people know what happened…” Ya fada in I don’t care tune, husna Dan kokarin daidaita tafiyan ta tayi amma a banza, duk Wanda ya ganta sai yasan something is wrong with her, tana tafiya tana tunanin abinda zata fada in taje gida don tasan bazata Iya pretending nothing happened ba
Ahaka ta dinga tafiya tana dingishi Sannan tana kuka, duk Wanda yazo wucewa sai ya kalleta amma ko daga kai batayi balle ta kallesu. Ahaka har Allah ya kawo mai adaidaita ta hau ta fada mashi inda zai kaita,

Sai around two Ayan ya tashi ya kalli ihsan data makale jikinshi kaman chewing gum ya saki murmushi tare dacewa
“Kaman ba ita bace mai yimin yanga ba dazun…” Yafada kasan makoshinsh, wayanshi dake gefe ya dauka yayi dailing number umma, bayan ya gaidata ta amsa kaman bata so don har yanzu bata bar fushi da Ayan ba don apart from his problem gani take kaman bai bar zalunta ihsan ba har yanzu,Ahankali ya fara cewa
“Umma pls..in anyi lunch.. Ki bada a kawo mana…” Yafada cikin sanyin murya,
“Akawo maka don kasa Nafisat tayi feeding dinka ko?..” Ta fada cikin fada don antymu ta fadawa Umma abinda ya faru ranar da ta kai masu abinci, Dan Dariya Ayan yayi Sannan yace
“No Umma… Ihsan batajin dadi ne…” Da Sauri Umma tace
“What’s wrong with her?…” Dan murmushi yayi yana shafa face din ihsan dake bacci kaman baby yace
“Wai kanta ke ciwo…”
“Is it serious?..” Umma ta tambayeshi, Ahankali yace
“Aa….Umma kinsan me?..” Ya fada cikin excitement, Umma girgiza kai tayi tare dacewa
“No…” Ahankali Ayan yace
“Umma…am man again…” Yafada yana rufe fuskanshi kaman Umma na zaune gabanshi, duk yanda take jin haushin shi saida tace.
“Really?..” Da Sauri yace
“Yes Umma…”
“Kai alhamdulillah… Alhamdulillah…” Tafada Sannan ta katse wayanta, Ayan ajiye wayan yayi Sannan ya tallabo face din ihsan yana kallon ta , ahankali yayi owing bakinta yana Dariya, bude ido tayi ta kalleshi, dukda tana jin matsanacin bacci hakan bai hanata wulla mashi harara ba, Dan lip dinta na kasa ya chiza Ahankali Sannan ya zare bakinshi yana cewa
“Baby let’s pray…” Ya fada mata Sannan ya mike ya rike hannun ta ya mikar daita, Dariya yayi don yanda take lumshe idanuwa
“Har yanzu bacci kike ji ko?..” Ya tambayeta yana kaita bakin kofan bathroom, Ahankali ta gyada mashi kai Sannan ya bude mata ta shiga shima ya part dinshi ya koma ya alwallah ya fito ya tafi masjid,
Ihsan na idar da sallah tq zauna tana tunanin mafarkin datayi just a while ago, mafarkin looks so real, don kaman zahiri haka take ganin mafarkin, husna ta gani tana kokarin kwace white rose dake hannun ta, Kuma she looks very serious a mafarkin, sauran kadan ta kwace Ayan ya tadata daga baccin, Dan bakinta ta tabe tana cewa
“It’s just a dream.. Kuma mafarki bai zama gaskiya da rana..” Ta fadawa kanta cikin murya kasa2, Ahankali ta kwanta nan kasan tana Kara cewa
“That white rose is so beautiful.., ” Tafada fuskan ta dauke da murmushin jindadi, har ta fara lumshe idanuwa Ayan ya dawo daga masjid, bude kofan da yayi yasa ta bude idanuwanta, ta kalleshi Sannan ta maidasu ta lumshe,
“You are not sleeping now sai kinci abinci…” Yafada yana karasowa wajenta, zaunar daita yayi ta daure fuska,
“Wai why are frowning?.. Ko nayi wani laifin ne?…” Yafada yana cire mata hijab din kanta, banza tayi dashi,
“Pls baby tell me if you are still angry with me…” Ya tambayeta Ahankali, kura mashi ido tayi tana tunanin sanda gane warning dinta kan kar ta sake tayi mashi magana, sai Kuma ta tuna da irin countless Marin datasha wurin shi
Ahankali tace
“Why are you nice to me?..” Ta tambayeshi, baki ya bude don tambayan ya bashi mamaki, hannun ta ya kama Sannan yace
“Because you are my wife…” Dan baki ta tabe Sannan tace
“Am I not your wife when you slap me?… Ko am not your wife when you gave me your house rules and regulations… Nidai ka kyaleni because I am obeying your rules…” Ta fada tana zame hannun ta daga nashi, da Sauri ya kara kama mata hannun yana cewa
“No more rules..” Da Sauri ta girgiza mashi kai
“No… Ko because am a virgin… In haka ne then you never loved me…you just love the virginity…” Tafada sounding very serious, da Sauri Ayan yayi kneeling gabanta yana cewa
“No…I love you… ”
“No…you don’t.. If you really loved me da ka fadamin exactly abinda ke faruwa…da ka zaunar dani ka tambayeni why I was bathing in another man’s shower.. Amma no…you decided to rape me…you called me all sort of names..and you want me to forgive you just like that..” Da Sauri ya dafa shoulder dinta ta ture hannun shi Sannan tace
“Leave me alone…” Bai kara tabata ba yace
“Baby am sorry.. Just put yourself in my position… Son da nake maki ne yasa na rude… I was so confuse..pls ki yafemin… Nayi mistake da ban yarda dake ba or better still tambayeki ba..pls ki yafemin…” Yafada har lokacin kneeling yake gabanta, Dan tabe baki tayi ta kalleshi eyeball to eyeball Sannan tace
“Just leave me alone for now…am very furious right now.. Kawai I feel xan Iya yi maka abinda kayi min…” Da Sauri Ayan yace
“In zagin Dana yi maki ne ..ki rama na yafe…in Marin Dana yimaki ne still ki rama wallahi na yafe…but pls don’t do anything else.. Kinsan we still have problem at hand…we need to put our head together…” Ya fada yana Kara kama hannun ta, Ahankali ta Kara zare hannun ta tace
“Nidai ka kyale ni….in Kuma idanuwa zaka zaro min kaman yanda ka saba to bisimillah…” Ta fada atakaice,
“Ok then…zan kyaleki..amma we still share the same bed…same plate of food…” Da Sauri tace
“No…I think now you follow my rules..” Tafada da gaske with courage, yanda tayi maganan yasa Ayan sakin dariaya,amma ganin babu alaman wasa tattare daita yasa yace
“Ok ma’am…anything you say…amma pls don’t be too harsh on me ma’am…” Yafada cikin zolaya, ihsan kara hade rai tayi, Ayan na nan inda yayi kneeling ta mike ta haye kan gado ta rufe kanta da bargo,
“Ma’am.. Can I stand up now?..” Ya tambayeta,
” I didn’t ask you to kneel..” Ta amsa mashi atakaice, Ahankali ya mike ya koma bakin gadon ya zauna jin batace kala ba yasa yadan kwanta sai cewa tayi
“Ka barmin dakina…”. Tafada tana kara dunkule kanta cikin blanket, ba musu ya mike ya bar dakin tare da jamata kofa. Falo ya koma ya shiga daya daga cikin bedroom dinta ya shiga yayi kwanciyan shi.
Sai wajen karfe uku aka kawo abinci daga gida, dakinta ya shiga ya tada ta amma sai bacci bacci take.
[12/27, 14:14] ‪+234 814 199 1000‬: DECEMBER 20, 2017 0 COMMENT
kawarta ce sanadi 51

💚💛💜🖤❤💙
KAWARTA CE SANADI
💛💜❤🖤💙💚

®zuwairat(ummu Maryam

5⃣1⃣

Murmushi Kawai tayi ya shiga bathroom dinta ya wanke bakinshi Sannan ya koma falo ya jera abincin kan dinning ya zauna yaci ya koshi, relaxing yayi har aka fara kiran sallan asar Sannan ya shiga dakinta har lokacin tana kunce cikin blanket, yaye blanket din yayi yana cewa
“Ma’am is time for prayer…” Ya fada Sannan ya shiga bathroom dinta ya daura alwallah ya fito har lokacin tana zaune idanuwanta lumshe,
“Time is going…” Yafada yana barin dakin, bayanshi tabi da harara sannan ta mike da kyar tashiga bathroom ta dauro alwallah tayi salla ta mike ta nufi falo don ji take kaman an
Yaye mata kayan cikin ta saboda yunwa, tana zuwa falo ta ga mini dinning dinta shake da food warmer da Sauri ta karasa ta zauna ta bude tayi serving kanta ta fara cin abinci, sai da ta koshi Sannan ta mike ta shiga bedroom dinta, bathroom ta shiga ta sake wanka, tana wanka tana kuka abinda ke damunta, ita har yanzu bata yarda cewa anyi sharing nude pic dinta ba,
“Who???…” Kawai take maimaitawa tana durkushe cikin bathtub, kuka take kaman babu gobe,
“Ya Allah who?…” Ta sake fada cikin matsanacin kuka.
Ayan na dawowa daga masjid ya leka ta don tabbatar tayi sallan, yana ganin gadon wayam yasa ya koma part dinshi ya sakarwa kanshi ruwan dumi, after fifteen minutes ya fito daure da towel, mai ya shafa Sannan ya fesawa naked skin dinshi perfumes don yasan ba mata Kawai suke gayu ko fesa perfumes don burge maza ba,suma mazan suna gayu don su burge matayensu, sai da ya gama wankan turare Sannan ya bude wardrobe dinshi ya dauko wasu new jeans da bai taba sakawa ba ya sa tare da polo shirt blue in colour, gaban mirror ya koma ya dauki wata enchantment powder dake kan mirror ya zuba a hannun shi ya shafa a fuska kaman mace, imagine a black guy with a little bit of white powder on his face,b karamin kyau yayi ba saida ya tsaya ya kalli kanshi gaban mirror sosai yana shafa well groomed beard dinshi yana murmushi.

Sai bayan sallan asar adaidaitan da dake dauke da husna ta iso kofar gidansu, tun suka taho take kuka har mai adaidaita yake tambayanta lafiya amma ko kallon shi batayi ba ta cigaba da kuka don ita kadai tasan abinda take ji, har yanzu mamaki take how comes she agreed to her own destruction so easily , Ahankali ta fiddo kafanta daya szai ji take kaman zaa cire mata cinya, da kyar ta kara fiddo daya t bude bag dinta ta bawa mai adaidaita 1k Bata tsaya amsan change ba ta juya zata shiga ciki, mai adaidaita ya tsaya kallon bayan skirt dinta dake jike da jini, husna tsayawa tayi ta kasa tafiya saboda yanda take jin kumburin gabanta har laps, hannuwanta ta fara yarfawa tana kara fashewa da kuka,
“Sannu …” Ya ce mata Sannan ya ja adaidaita sa ya bar wajen, da kyar husna ta Iya kaiwa bakin gate din su ta tura karamin kofan tashiga ta fadi nan kasa tana kuka kaman wacce akayiwa albishir da mutuwa, daman that was her plan don tasan babu yanda zaayi ta boye wannan matsalan, maigadi ya ganta ta taho yana ihu yana cewa
“Subhanallahi!!!…” Da karfi,Wanda yasa mami da lil sis din husna fitowa da gudu, aikam ganin husan kwance kasa yasa su sakin ihu husna kam rufe ido tayi ta dinga kuka tana cewa
“Mami…mami…mami…” Da gudu mami ta karaso wajenta ta riketa tare da cewa
“What!…” Kawai ta Iya fada saboda tashi hankali, Ahankali husna ta nunawa mami gabanta, idanuwa mami ta zaro tana cewa
“Inna lillahi waina ilaihi rajuun!!…. What happened… To you…” Ta fada cikin tension
“Raping…dina…aka….yi..” Bata idaba mami ta daka tsalle ta fadi kasa ta fara kuka, shima mai gadi kuka yake sai sis dinta, dukkan su kuka kaman gidan mutuwa,da Sauri mami ta mike ta ce
“Ina kikaje?… Ina akayi maki fyade?…” Ta tambayeta tana kuka, cikin kuka ta fara cewa
“Taxi…nahau…to..ban kara…sanin…halin.. Da..nake ciki ba…sai…yanzu… Na ..ganni kofar…gida…” Tafada tana shessheka, mami mikar daita tayi taga bayan skirt dinta wet da jini, wani irin kara ta kara saki ,
“Inna lillahi waina ilaihi rajuun…. Waye ya cuceni?…na shiga uku na lallace…” Mami ta fada cikin kuka sosai,ahaka ta kama hannun husna suka shiga cikin gida ita kam husna Dan ajiyan zuciya ta saki da mami Bata zargi komai ba, dad dinta mami ta kira ta shaida mashi halin da ake ciki, shima doc ta kira yazo gidan don bai gari, drugs ya rubuta mata Sannan ya shaida a dinga sata a ruwan zafi, mami dai cewa tayi kar a fadawa kowa wannan abun kunyan, so ya zama family secret, husna dai jibi take jira ta amso abinda zatayi Maganin Ayan dashi.

Ayan part din ihsan ya koma yaga har lokacin Bata cikin dakin, bakin gadonta ya zauna yana jiran fitowan ta daga bathroom, Kawai sai yaji kukanta, da Sauri ya bude ya shiga gani yayi tana durkushe cikin bathtub tana kuka kaman babu gobe, da Sauri ya karasa ya zauna daga bakin yana cewa
“Precious lafiya?..”sai lokacin Tasan da akwai mutum wurin, daga kanta tayi ta wulla mashi harara tana cewa
” get out…” Banza yayi daita ya dafa wet and naked shoulder dinta,da Sauri ta buge mashi hannu tana cewa
“Stop it…get out?….”
“No!…you stop it…” Ya daga mata tsawa, nan take ta rufe fuskan ta da tafin hannun ta biyu ta cigaba da kuka,
“Wai what is the problem…” Banza tayi dashi ta fara cewa
“Bazan yafe ba…I will never forgive Wanda yayi disgracing dina…..bazan taba yafewa ba….Allah ka saka min…Allah ka sakamin an cuceni….Allah ka tozarta duk Wanda ya toxarta ni….Allah kaisan min….” Tafada cikin matsanacin kuka, Ayan sai shafa wet hair dinta yake Ahankali, saida ta kai aya Sannan yace
“Ameen.. Ameen… Allah zai amshi aduan ki…Allah yana amsan aduan Wanda aka zalunta…we will keep praying until Allah reveals who’s behind this… Kiyi hakuri… Ki bar kukan nan haka nan pls….” Yafada mata Ahankali, hannun shi dake cikin gashin kanta ta ture tana cewa
“To ka fita….”
“Only if you stop crying…” Ya fada mata , shuru tayi
“Good girl….oya yi Sauri ki fito..am waiting for you…..” Ya fada yayi kissing kanta dake cikin cinyanta Sannan ya fita, ya koma ya bude wardrobe dinta ya fiddo mata gown ya ajiye mata Sannan ya koma falo, tana fitowa ta zauna gaban mirror tana kallon swollen eyes dinta har lokacin Bata bar cewa
“Allah ka sakamin ba…” Tana magana daya har ta shafa mai ta kalli kayan daya ajiye mata ta tabe baki Sannan ta bude wardrobe ta dauko wani Riga da skirt na material ta saka ta fito ba dankwali kanta, Ayan na zaune falonta ta wuce kaman ba kowa, bayanta yabi da kallo har ta fice main falo, murmushi ya saki yabi bayanta, kitchen ta shiga ta taga tana tunanin abinda zata hadawa kanta, tana cikin tunanin Ayan ya shigo kitchen din,
“Thinking of what we will use for dinner?..” Ya tambayeta,banza tayi dashi har lokacin, waist dinta ya kama, da Sauri tayi kokarin tureshi amma kaman Ba mutum take turewa ba, nuna shi tayi da yatsa tana cewa
“Ka rabu dani…” Kama yatsan yayi cikin bakinshi ya fara tsotsa kaman lollypop, kokarin zame hannun tayi ya kara kamawa gam, don kanshi ya saki hannun ta yana murmushi,
“Kinsan baby we should go out…let’s eat dinner in any of the restaurant around…” Yafada yana shafa waist dinta Ahankali, ita dai daure fuska tayi bata ce kala ba,
“Pls baby let’s go out..I want to cruise with you…” Yafada bakinshi saitin wuyanta, Dan tureshi tayi kokarin yi saboda yanda turaren shi ke son maidata restless, amma ko gizau, matseta yayi gam da jikinshi yana shafa tip of his nose a wuyanta yana shakan kamshin perfumes dake jikinta,
“Baby…” Yafada cikin whisper, itadai tana tsaye kaman doll Bata motsi balle ta yi komai, Ahankali yake shafa waist dinta zuwa bayanta, Kawai sai ta tsinci kanta da lumshe idanuwa, wuyanta ya dinga kissing zuwa wajen bakinta amma sai ta kauda kanta gefe daya,
“Pls baby ..let’s make love…” Ya fada mata cikin whisper, idanuwa ta zaro, da Sauri ta girgiza kanta tana cewa
“Pls stop… It…” Dariya yayi
“Do you really want me to stop?…” Ya tambayeta yana biting shoulder ta Ahankali,
“Yes…stop it…..” Ta fada muryan ta na rawa,
“Ok..I will.. Stop…amma kiss me first…” Yafada sounding very commanding,
Ihsan Kara kauda kanta gefe tayi yakara maido face dinta saitin fuskan shi, lumshe idanuwa tayi ya fara lashe lips dinta yana cewa
“Open your eyes and give me a kiss…or am going down now…” Yafada in a naughty way, turo baki tayi ya kama bakinta ya fara kissing dinta Ahankali in a passionate way, ihsan ji tayi kafanta bai daukanta kokarin tureshi take amma abanza, ganin tana son sulbu mashi ya sa ya daga ta ya dirata kan kitchen counter ya cigaba da abinda yaje da bakinta, zip din rigan ta ya fara kokarin zagewa, da Sauri ta kama mashi hannu dukda bata da bakin magana, Ahankali ya zage zip dinta ya ya fara shafa bare back dinta, ganin ya maido hannun shi kan kirjinta yasa ta gane he’s serious, da Sauri ta tureshi daga inda yake tsaye yadan yi baya, hakan ya bata daman maida numfashin ta ta fara cewa
“What are you doing?..” Tafada Bata Iya kallon shi directly, Dariya yayi ya kara nufota,
“Hakkina zaki bani…” Yafada babu wasa, turo baki tayi zata fara kuka ya Kara fashewa da Dariya
“What?… Ai kinsan ya rataya wuyanki yanzu…dole ki dinga kwantar min da hankali duk sanda am in need…” Yafada yana kara kama waist dinta daga inda take zaune, fashewa tayi da kukan gaske tana cewa
“Yanzu bayan duk abinda ka yi min jiya?… Because ba sona kake ba…shine kake kara requesting wani?…yanzu nasan you never loved me…Kawai jikina kakeso…” Ayan kura ma sweet lips dinta ido yayi yana kallon yanda take hawaye sai ya saki murmushi tare da tallabo face dinta ya fara cewa
“Son kenan… In badan inason ki Kuma INA tausaya maki ba..ai na yanzu na wuce round biyar…amma dayake ni adaline gashi ina binki Ahankali,…” Goge mata hawaye yayi Sannan yacigaba dacewa
“Don’t worry…zan barki ki kara warkewa zuwa gobe but only if kin yarda muje yawo daga nan muci abinci kafin mu dawo…kin yarda?…” Ya tambayeta, daga manyan idanuwanta tayi ta harareshi Sannan ta gyada mashi kai,
“Good…yanzu ki koma ciki ki tsantsara kwalliya… Ki sameni…” Yafada yana direta kasa, Ahankali ta taka zata bar kitchen din Ayan ya bi bayanta ya fallawa bombom dinta slap yana Dariya tare dacewa
“My very own ass…” Ihsan kam haushi kaman ta mutu amma Bata da bakin magana, haka ta shiga ciki ta gyara face dinta tayi light makeup ta daura dankwalin material data saka sai ta dauki Vail Dan karamin ta yafa Sannan ta dauki wayanta ta fito, yana ganinta ya saki baki ya taho ya dauketa in a bridal style suka fita zuwa wajen motanshi.

Haka suka dinga yawo sai bayan sallan ishai suka dawo gida inda da kyar ihsan tasha hannun Ayan don ba karamin headache ya bata ba. Ganin in ya zauna nan yana iya kara forcing dinta yasa ya koma dakin shi amma karfe 1:20am ya koma part dinta ya tadata kan ta tashi suyi sallan dare, dayake ihsan bata saba ba sai taji wahalan tashi amma sai ya tuna mata ta tashi ta kai kukanta ga Allah kan matsalolinta.

Husan kam ba karamin wahala tasha kafin a gama gasata ba, mami kam tayi kuka har ta godewa Allah, babu abinda take cewa sai
“Allah yaisa….” Through out ranar husna bata ci abinci ba saboda yanda ta wahala, amma duk halin da take ciki ji take kaman ta jawo jibi don ta koma ta amso Maganin
[12/27, 14:14] ‪+234 814 199 1000‬: DECEMBER 20, 2017 5 COMMENT(S)
kawarta ce sanadi 52

💛💚💜🖤💙❤
KAWARTA CE SANADI
💛💚💜🖤💙❤

®zuwairat( ummu Maryam)

5⃣2⃣

Wace gari su Ayan basu tashi da wuri ba saboda sai bayan sallan fajr suka kwanta, ihsan ce ta tashi wajen karfe 10: da kwata, da kyar ta kwace kanta daga jikin Ayan ta shiga bathroom tayi wanka ta fito daure da towel, da Sauri ta shafa mai ta saka Riga da wando Indian dress ta shiga kitchen, plantain daya ta dauka tayi pealing ta yanka ta Dan sa salt ta ajiye Sannan ta kunna gas frypan ta Dora ta zuba mai takara kunna dayan kan ta Dora ruwan zafi, atakaice within 15 minutes ta hawa kanta plantain da kwai sai tea mai kayan yaji, tana ajiyewa kan dinning Ayan ya fito daure da towel daga part dinta, da ganin shi kasan wanka yayi, yana ganin ihsan kan dinning ya saki murmushi yana zuwa inda take zaune, kallon plate daya da cup daya dake gabanta yayi ya kalleta yaga ko daga kai batayi ba balle ta gaidashi
“Precious.. Can’t you greet?…” Ya tambayeta yana zama kan kujeran dake kusa daita,
“Good morning…” Kawai ta fada tana kai cup bakinta, bai amsa ba ya tsaya yana kallon ta, shi har yanzu he couldn’t believe wai tana fushi dashi bayan duk explanation din daya Bata, Kuma yasan ya nemi yafiyan ta amma still she’s still mad at him,
“Babu ina breakfast dina?…” Ya tambayeta yana daukan cup din tea data ajiye, ko kallon shi batayi ba ta dauki plantain daya hade da kwai ta kai bakinta, cikin kasaita tayi chewing ta hadiye, shima Ayan daukan daya yayi ya kai bakinshi yaga ihsan ta hade rai,
“Precious wai bakiyi breakfast dani ba?..” Ya tambayeta cikin sanyin murya, Dan tabe baki tayi Sannan tace
“Kace kar inyi abinci da kai…Kuma baka fadamin in farayi da kai ba…” Tafada tana kurban tea ahankali kaman bataso, murmushin karfin hali yayi Sannan yace.
“Yanzu precious har yanzu baa wuce wurin ba?…na fada maki no more rules..”
“Sai ka zaunar dani ka fadamin ka warware rules din tare da listing rules din kaman yanda ka zaunar dani ka kafamin rules din…” Ta fada atakaice, Ayan zama yayi yana kallon ta Kuma kallon mamaki don tamkar ba ita ke maganan ba, he couldn’t believe yanda bai tolerating yana iya hakuri amma sai ya kara murmushi Sannan yace
“Ok..daga yanzu babu wata doka a gidan nan…ni dake zamu zauna as every lovely couple suke zaune…” Yafada Ahankali,
“Hmm AI ba haka ka fadamin lokacin da ka kafa dokan ba..you listed the rules and now I want you to list them again…” Tafada tana cin abincin ta kaman baita ke maganan ba,
“Ok..na daya ki dingayi min magana at anytime you want…na biyu kiyi abinci dani..kome kikaci nima zanci…na uku kome kike bukata ask me directly not in written… Na hudu duk inda zaki muddin bai haramta ba na yafe maki ki je…na biyar na amince zaki cigaba da karatunki…na shiga still stands saboda dole ki gyara part dina…so I think that’s all…are we good?…” Banza tayi dashi ta cigaba da cin abincin ta,
“Yanzu zakiyi min breakfast din?..” Ya tambayeta kaman wani karamin yaro
Murmushin gefen baki ihsan ta saki rana cewa
“AI saidai ka tari lunch Kuma saboda you broke the rule after breakfast…” Dariya Kawai Ayan yayi ya mike don ko kadan Bata bashi haushi mussanman in ya tuna irin abinda yayi Mara lokacin daya kawota gidan nan, har yau bai bar godewa Allah ba da bai barshi ya aikata wannan abun dayayi niyyan yi ba, yana daure da towel ya shiga kitchen shima yayi pealing plantain ya soya Sannan yayi tea amma nashi tea baiyi mashi dadi kaman na ihsan ba cos ita tasa kayan kamshi.
Tana gamawa ta gyara wajen wajen ta koma dakinta, ta zauna tana danne2 waya.
Shima Ayan bayan ya gama ya shiga part dinshi ya ya saka kaya ya fito ya sameta part dinta ya zauna gefen ta Sannan yace
“Kinason zuwa gida?…” Aikam da Sauri ta gyada kai kaman agama lizard, Dariya yayi
” ok, ki shirya in kaiki…amma I want you to promise me one thing.. ” Yafada yana kama hannun ta, kura mashi ido tayi tana sauraron abinda zai fada mata,
“Promise me bazaki fadawa mom ko wata ko wani abinda ya faru tsakanina dake ba..” Da Sauri tace
“Kaman me?…”
“Kaman your nude pic.. Da sauran su…” Ihsan shuru tayi don ita babban abinda yasa take son zuwa gida shine don ta fadawa mom da dad abinda akayi mata amma kaman ya gane sai ya kafa mata doka,
“Pls let me tell them ko Allah zaisa su tayani da adua…” Tafada kaman zatayi kuka,
“No..they is no need…Kawai mu cigaba da adua it’s OK… Pls just promise me bazaki fada masu ba…” Shuru tayi for a while Sannan tace
“Alright.. I promise…” Tafada ba don ta so ba.
“Good wife…yanzu ki shirya…” Bai idaba ta ta mike ta shiga bedroom dinta, after 20 minutes sai gata ta fito tana glowing cikin shadda data saka, murmushin jin dadi yayi ya mike ya mika mata hannu, ba musu ta saka hannun ta cikin nashi , rungume ta yayi ya hada bakinshi da nata ya fara kissing dinta, ganin yana nenan zuge mata zip din riga yasa ta fara kokarin kuka, yana Dariya ya kama hannun ta suka fita daga cikin falon.
Gaban mota ya bude mata ta shiga Sannan ya shiga suka bar gidan, suna kan hanya ya kalleta
“Baby ina zaki fara zuwa?…” Shuru tayi for a while Sannan tace
“Duk inda kace…” Murmushi yayi saboda yanda yaji dadin maganar ta,
“To zan ajiyeki gidanku… Amma da karfe biyu dot ki tafi gidanmu.. Anan zanzo daukanki….is that OK?..” Kai ta gyada mashi, yana cikin tuki chan kusa da wani supermarkets ya tsaya ya umarceta data bishi, babu musu ta bishi, shopping yayi cike da Leda biyu suka dawo cikin mota
“Ki kai daya gidanku daya Kuma ki kaiwa Umma…” Yafada yana tada motan, murmushi Kawai ta saki Sannan tace
“Thank you…”

Sai around 12 suka iso gidansu ihsan, parking yayi suka shiga tare ya gaida mom cikin girmamawa ta amsa cikin jindadi don ba karamin farinciki tayi dataga ihsan ta chanza ba , nan falo ya barta yafito mom ta ture ihsan data rakashi, bankwana sukayi ya tafi gidansu ya gaida Umma, Umma sai zagin shi take tana cewa
“Shege ga auren da bakaso nan anyi maka Kuma har ka fara ajiye kumatu…” Ayan dai Dariya Kawai yake, ya fada mata ihsan zatazo shi Kuma zai wuce hospital, Umma ba karamin dadi taji ba dataji ance daughter zatazo daman she have something special for her
Har baki mota Umma ta rako shi ya shiga ya tafi looking so happy and excited.

Husan ce zaune ta rafka uban tagumi tana tunanin irin dabaran da zatayi wa mami ta barta ta fita gobe don amso Maganin, Ahankali ta mike daga kan gado tana takawa Ahankali ta fito ta tarda mami a falo zaune da gani tunanin halin da husna ke ciki Kawai take, tana mamakin dalilin dayasa Bata da maneman aureta Sannan Kuma ga rashin virginity dinta, ajiyan zuciya mami ta sauke tana kallon husna na tafi fito, Ahankali ta zauna kusa da mami
“What?..” Mami ta tambayeta Ahankali, husna fan sadda kanta kasa tayi Sannan tace
“Mami ina tunanin yanda zan iya zuwa rubuta test gobe a school…” Tafada cikin sanyin murya, da Sauri mami tace
“But you must be very stupid ….test ko na shiga aljanna ne ai sai haka…ahaka kikeson zuwa makaranta dayake baki da kunya baki da hankali…” Husna fashewa tayi da kuka tana cewa
“To mami ya zanyi da rayuwata?… Bani fa miji…bani da virginity.. Sannan certificate da nake kokarin amsa ma yanzu zai lalace min….” Ta karasa maganar ta cikin matsanacin kuka, Kawai sai mami ta rungume ta, suka dinga kuka kaman gidan mutuwa,
“Mami Dan Allah ko driver ne ya kaini ya maidoni….yanzu na fara samun sauki…” Tafada tana rungume da mami , Kawai response din mami Kawai takeson ji don yanzu tamkar her life depends on it take ji, mami patting bayanta ta dingayi tana cewa
“Are you sure kina iya zuwa?..” Da Sauri ta gyada mata kai,
“Mami.I will manage…banason in kara shekara daya saboda carry over…” Tafada cikin kuka,
“Ok then…amma ki kara dage da shiga ruwa kafin goben …”
“Ok mami…” Tafada tana mikewa, dakinta ta koma tana kokarin daidaita tafiyan ta. Allah Allah kawai take garin Allah ya waye tayi embarking kan dangerous mission dinta.

Mom kam dakinta ta kai ihsan bayan ta fadawa mai aiki ta hada mata lunch mai rai da lafiya, mom shawara ta dinga Bata kan zamantakewan aure Kuma ta tambayeta ko tana samun matsala ta ce mata no, har lokacin taso ta fadawa mom abinda ya faru amma ta tuna kar wata rana ya hanata zuwa.
“Hope kina amfani da kayan da aka hada maki?..” Mom ta tambayeta, shuru tayi bata ce kala ba,
“Da alaman baki sha kenan?..” Mom ta sake tambayan ta, mom mikewa tayi ta bude fridge ta dauko peak milk Sannan ta bude bag dinta ta dauko wani magani ta hada ta bata ta sha. Sai 1:50 bayan taci tasha Sannan tayi bankwana dasu mom ta kama hanyan gidansu Ayan, Umma kam tamkar ta cinyeta saboda murna, sai nan nan take da daita, pepper soup tasa akayi mata, ihsan ta koshi amma dole ta kara ci, itama Umma wani sirrin perfume ta bata Sannan ta kara hada mata Maganin da kindrimon Nono ta bata ihsan ta amsa tasha tana
“Allah gani gareka…” Tafada cikin ranta
Tana zabgawa cikin ta magani. Suna zaune da Umma bayan sallan asar Ayan ya dawo daman an ajiye mashi abinci, as usual antymu tayi feeding dinshi sai kallon ihsan dake zaune kusa da Umma yake.

Sai bayan sallan ishai suka tashi tafiya , perfumes kala2 Umma ta bawa ihsan, antymu ta bisu har bakin mota ta kama hannun ihsan Sannan tace
“Anty zan biku tunda gobe babu school…” Da Sauri ihsan tace
“Yes pls…” Ayan chanza fuska yayi saboda ko kadan baison abinda zai bata mashi fun,
“Ki Bari zanzo in daukeki next week..” Yafada yana bude mota, Umma dake tsaye Dariya tayi tana cewa
“Kinga Allah ya kara …ya samu wacce ta fiki ya fara dumping dinki…” Umma ta fada tana gwalowa nafisat idanuwa, dukkan su Dariya sukayi banda antymu data marairace fuska,
“Don’t worry.. Zan zo daukanki…kinji…” Ya fada mata Sannan ya shige motanshi, itama ihsan shiga tayi jikinta babu kwari don ita taso Nafisat tabi su, waving dinsu umma ta dingayi har suka fita daga cikin gidan.
Sai nine suka iso gida bayan sun shiga falo ihsan tayi hanyan part dinta rike da kayan da Umma ta bata, Kawai sai taji Ayan ya amshi ledan ya ajiye gefe ya dauketa in a bridal way, surprise look ne kwance kan face dinta
“Pls put me down…” Tafada sounding like the boss, Dariya Ayan yayi yana cewa
“Turaka zan kaiki….”
“Meye turaka?…” Cikin Dariya yace.
“Inda mata ke zuwa amsan vitamins….” Kofa ya bude ya shiga daita falon shi, tun daga nan ya fara kissing dinta har lokacin yana dauke da ita,
“Yau zan shayar da ke dadi…ke zaki dinga kawo kanki.daga yau…” Yafada yana shiga bedroom dinshi, kuka ta fara yi tana cewa
“Ni dai ka kyale ni..mugu…wallahi banso…” Tafada cikin kuka, bai ajiyeta koina ba sai kan gado, button din riganshi ya cire ya daka tsalle ya haye kan gado ya jawota jikin shi yafara kissing dinta, Kawai ihsan sai ta fara lumshe idanuwa don she was enjoying every touch, ganin Bata hanashi yasa ya fara rage mata kayan jikinta, bakinshi ya kai kan nipple dinta ya fara wasa dasu kaman zaa bashi award, ihsan kam ba karamin dadin abun takeji ba don ji take kaman kar ya bari, riganta ya cire ya cire mata wando ya fara kokarin cire pant dinta da Sauri ta rike mashi hannu tana girgiza kai,
“Pls..stop…zafi…” Tafada muryan ta na rawa, saitin kunnenta ya kai bakinshi yana licking kunnenta yana cewa
“Don’t worry… I will be gentle…” Yafada mata cikin kunnenta yana kissing earlobe dinta
“Pls..forgive me…for been rough and mean…last time….” Yafada yana kissing wuyanta, ahankali ya kara cewa
“Have you forgiven me?..” Ya tambayeta yana kissing face dinta, jikinta na rawa ta gyada mashi kai,
“Thank you…” Ya fada yana hade bakinshi da nata, saida ya tabbatar ya kashe mata ciki da romance ya tabbatar she wants him but couldn’t ask Sannan yayi introducing kanshi Ahankali, ihsan sai bangaro kirjinta take don kaman ta amshe farat daya takeji, murmushi Ayan yayi ya tsaya yana kallon yanda take licking lips dinta da kanta, kara hade bakinsu yayi sannan yayi thrusting gaba daya, rikeshi tayi gam kaman zaa kwace shi, Ayan sai ihu yake don dadi, ihsan kam tun tana tunanin she can hide how she feels kawai sai dai taji muryan kanta tana
“Pls…take ..me..all.” Ayan bude idanuwa yayi ahankali yana kallon idanuwanta dake lumshe yace
“Really?..” Dan bata fuska tayi batare data bude idanuwa ba tace
“What did I say?..” Ta tambayeshi tana haki kaman wacce tayi gudu,
“You said I should take you all…” Yafada mata cikin kunnenta,
“Then hold on tight… Let me take you away from the agony of this world” ya fara yana wasa da each and every part of her chest, aranar Ayan bai maida hankali ga kanshi ba, sai da ya tabbatar ya bawa ihsan all the attention she deserves, sai da ya tabbatar tasamu orgasm Sannan ya fara sata abubuwan da yakeso Kuma ya tabbatar mata this is what she should be doing to him to make him crazy, after every thing ya jawota jikin shi sai bacci, karfe 1 na dare ya tashi yayi wanka ya fito ya saka jallabiya ya hau kan praying mat ya fara adua as usual
[12/27, 14:14] ‪+234 814 199 1000‬: ❤💙💜🖤💚💛
KAWARTA CE SANADI
💙💚❤🖤💛💜



®zuwairat ummu Maryam)




5⃣ 3⃣



 _Wannan shafin Kuma nakune yan *masoyan ihsan da ayan* I wish ina Iya listing names dinku amma you are too many to be mentioned, amma I love all of you more than anything_



 Husnah ne cikin adaidaita sahu tanata aiyanawa aranta irin yadda xata juya ayan dan tanaga her dream come true,kasancewan sun taba zuwa gidan oonce or twice da Ayan, Ayan na baya yayi relaxing kaman mai bacci amma ba bacci yake ba. Yana jin anyi parking ya bude ido,
"Har mun iso?..." Ya tambayesu,
"Yes..." Muhammad ya amsa mashi yana fita daga cikin motan, shima Ayan fitowa yayi suka nufi wani gidan mai bushiyan bedi tare da wasu old men zaune kan mat, daya daga cikin mazan kallon su Ayan yayi ya saki murmushi yana cewa
"Har kun zo?..."
"Eh..baba..." Yusuf ya amsa mashi, dukkan su uku gaida su sukayi tsohon da sauran mazan dake zaune gurin suka amsa Sannan tsohon ya mike ya kalli Ayan
"Mu shiga ciki..." Ba musu Ayan ya bishi, su Kuma Yusuf suka koma cikin mota
 Cikin wani karamin daki dake zauren gidan suka shiga , dakin babu komai ciki sai tabarma babba sai Kuma alquranai da yawa kaman inda ake fansansu,
"Baban ka ya fadamin kana da wata matsala... Ina sauraron ka..." Baban ya fadawa Ayan, cikin nutsuwa da jin kunya Ayan ya fadawa tsohon abinda ke damunshi, shima tsohon jimamin maganan Ayan kawai yake
"Kana mafarkin kwanciya da mace?.." Tsohon ya tambayeshi, ahankali Ayan ya girgiza mashi kai,
"To wannan abun da akwai hannu ciki..amma kar ka damu...mu baa taba a zauna lafiya saboda muna da alquran mai tsarki Sannan Kuma mun san adua takobin mumini ne...don haka zamu tashi tsaye babu dare babu rana..mu cigaba da adua indai yin mutum ne Allah zai tona asiri ko waye... Don haka ka kwantar da hankalin ka...kaji ko?.." Ahankali Ayan ya daga mashi kai
"Nagode baba..."
"Yauwa Dana...Kuma kaima ka dage da adua... Jibi yanda ka koma saboda tashin hankali....ka bar tunani.. Ko don kana kallon tsaleliyar budurwa baka iya aikata mata komai yasa kake tunani?..." Tsohon ya fada cikin zolaya, Ayan sadda kanshi kasa yayi yana murmushi, Dariya tsohon yayi kafin yace
"AI nasan dalilin kenan...yaran zamani ..." Ayan dai murmushi kawai yake,
"Yanzu ka dinga bada sadaka sosai...kaji ko?.."
"Eh baba..insha Allah....."
"To madallah..." Ahankali Ayan ya mike tare dayi mashi godiya ya fito ya shaidawa su Muhammad yanda sukayi da tsohon Sannan suka wuce. Office suka koma amma still Ayan bai komai.

Bayan sallan ishai ihsan ta shiga wanka ta saka kayan bacci mai silver colour, kayan sai salki yake, Dan kwantawa tayi hannun ta kan maranta gashi kan ta na ciwo, kawai juye2 take kan gado saboda menstral pain dake damunta, daman ta saba duk wata sai tayi shi Allah ya taimaketa ba sosai yake mata ba amma still is a little bit on bearable.
 As usual sai dare ya dawo gida parking yayi ya bude bayan motanshi ya dauko wata Leda Sannan ya shigo falon, direct kitchen ya shiga ya bude fridge ya zuba kayan fruits da yakawo Sannan ya tsaya yana kallon kitchen din, gani yayi plate biyu da alaman ihsan tayi bakuwa yau, cold tea ya hada ya sha daga nan inda yake tsaye ya ajiye cup cikin sink inda sauran plate suke Sannan ya fito, part din ihsan ya shiga, ko sallama baiyiba ya shiga bedroom din dayasan take, daga nesa ya hangeta kwance idanuwanta lumshe, ta ciza bakinta na kasa which makes her look sexy,ahankali ya taka zuwa inda take, zama yayi bakin gadon, duk ihsan najin zuwanshi amma tayi pretending tana bacci cos ko ta bude ido ba magana zatayi mashi ba, hannu ya daga ya fallawa ass dinta duka da Sauri ta mike zaune tana shafa inda ya bugeta, idanuwanta duk sunyi ja, sai turo baki take kaman zatayi kuka Kuma at the same time tana shafa inda ya bugeta, Ayan kura mata ido yayi yana kallon yanda idanuwanta suka chanza,
"Hey ..what's the matter with you?.." Ya tambayeta
 Banza tayi dashi don ta dau aniyan bazata yi mashi magana ba no matter the conditions, ita tana ganin kokarin ta don batasan zata iya zama very gentle ba, Ayan kam kurawa beautiful pecky nipple dinta dake eyeing dinshi ta cikin riganta yayi, ahankali ihsan ta rufe chest dinta ganin irin kallon da yake mata,
"I said meke damunki?..ko you are missing sex?.." Ya tambayeta kai tsaye, ihsan Dan tabe baki tayi tare da kauda kanta gefe, da Sauri Ayan ya maido fuskan ta inda yake
"Are you horny....naga your eyes are red?.." Ihsan banza tayi dashi, Ayan kam har son jin muryan ta yake don tunda ya fada mata rules dinshi bai Kara jin uffan daga gareta ba,
"To ki biyani inyi servicing dinki..." Ya fada kaman bai da wata matsala, ihsan dai bata tanka mashi ba saboda ciwon maranta ma is enough for her, Ayan ganin she is not saying a word yasa shi cewa
"Who came to this house today?..." Da Sauri ihsan ta kalleshi gabanta na faduwa,
"Yes...you think I don't know?.. Yanzu fadamin Wanda ya zo yau..." Ya fada yana kama bayan wuyanta, kuka ihsan ta farayi amma batace kala ba
"Na lura you are stubborn... Ki fadamin Wanda yazo gidan nan yau ko Kuma na lahira yafiki jin dadi..." Ya fada yana kara rike wutan da karfi, kara ta saki ganin da gaske Ayan yake yasa tayi saurin cewa
"Husna ce..." Da Sauri Ayan yace
"Hus...me?..." Ya tambayeta sounding very angry, cikin kuka tace
"Husna..." Bata idaba ya dauke ta da mari,
"What did I tell you?..." Da Sauri ihsan tace
"Kace...kar... Kawayena...su zo ...nan...gidan..." Ta fada cikin matsanacin kuka at the same time hannun ta kan cheek dinta daya Mara, gashin kanta ya rike yana cewa
"Wato ihsan Kin  rainani ko?...har in fada maki kar ki bari banzayen kawayenki su zo nan amma dayake ke yar iskace shine kike gayyato su gidana ko?.." Ya fada da karfi yana Jan kanta da karfi, ihu kawai ihsan take kaman ranta zai fita,
"Wallahi...ban gayyato ta ba....da kanta tazo..."
"Da tazo baki fada mata nace she's not welcome?... Baki fada mata mijinki ya hanata zuwa nan gidan?.. " ya fada yana kara Jan silken hair dinta,
"Wayyo...kayi hakuri..." Ta fada cikin wahala,.
"Good..." Ya fada yana sakin kanta, mikewa yayi ya koma tsaye Sannan yace
"Come here!..." Ya daka mata tsawa, da Sauri ta sauko kasa ta tsaya gabanshi tana kuka hannun ta dafe da kanta,
"Kneel down..." Yayi commanding dinta, da Sauri tayi kneeling jikinta sai rawa yake,
"Kama kunnenki..." Ya kara commanding dinta, still bai idaba ta kama kunnenta,
"Now repeat after me...daga yau..". Da Sauri ihsan tace
" daga yau" Ayan ya cigaba dacewa
"Bazan Kara barin wata karuwa ta shigo gidan nan ba..." Cikin kuka  ihsan tace
"Bazan kara ...barin...wata karuwa...ta shigo ...gidan...nan..ba..." Ayan yace
"Duk ranar Dana bari wata karuwa ta shigo gidan nan ka ciremin kunne daya..." Da Sauri ihsan ta daga wet face dinta tana
[12/27, 14:14] ‪+234 814 199 1000‬: KAWARTA CE SANADI 54
December 23, 2017 By Zuwairat Yunus
KAWARTA CE SANADI
®zuwairat( ummu Maryam)
Nan take jikin husna ta fara rawa har ta saki abinda ke hannun ta, Ayan kura mata ido yayi yana tunanin ko idanuwanshi ke deceiving dinshi don gani yake idanuwanshi basu gane mashi daidai ba, ahankali ya dinga zuwa inda take tsaye yana kallon ta, ahankali ya daga kai ya kalli katifan shi dake dage Sannan ya Kara kallon abinda ke kasa, tambaya ce kwance kan face dinshi, gyara towel dinshi dake Neman kwancewa yayi ya murza idanuwanshi don kara tabbatar he’s not dreaming, abinda ke kasa ya fi dauke mashi hankali don tasan ba abun arziki bane,
“Ke….” Aikam nan take husna ta kusa sakin fitsari saboda yanda taji muryan shi kaman na hungry lion, hannuwa ta fara yarfawa jikin ta na rawa kaman ana kada mazari.
“What.. are ….you… doing …in… my.. room?…”” Ya tambayeta yana counting words din daya bayan daya Sannan ya nuna Maganin da ke kasa
“And what is that?…” Ya daka mata tsawa,
“Na shiga….uku…Wallahi it’s not.. What…you…” Tafada tana yarfa hannuwanta, da Sauri ya daga mata hannu yana kara gyara towel dinshi dake Neman faduwa, wurin Maganin dake kasa yazo ya kare mata kallo aikam da Sauri husna tayi kokarin fita daga dakin, wani irin fixga yayi mata tare da bugata da bango Wanda yasata sakin wani irin razanannen ihu, hannu yasa kan bakinshi yace.
“Just one word from you.. And you are finish… Now kneel…” Yafada atakaice, dukda azaba ciwon kai da takeji saboda yanda kanta ya bugu bai hanata kneeling da Sauri ba,
“You know.. Na Dade ina aduan irin wannan moment din…alhamdulillah.. Its here…” Yafada fuskan shi dauke sa murmushin keta, kofa ya tafi ya kulle ya dauki key din Sannan ya bude wardrobe ya dauki jean da t-shirts ya shiga bathroom cikin minti daya ya fito, laptop dinshi ya dauka ya sa video ya ajiye inda zai fuskanci husna Sannan ya dauki belt dinshi ya maida wurin karfen kasa, husna kam ji take inama tana iya janyo mutuwa da ta gwammace ta mutu kawai,
“Yanzu hukuncin da zanyi man depends on the way you answer any question I ask you…in kin fadi gaskiya..zai zo maki da sauki..in Kuma kinyi min karya the reverse will be the case….” Yafada hankalin shi kwance, husna sai yarfe hannuwa take,
“Questions number one…meye wancan?..” Yafada yana nuna abinda ke kasa,, da Sauri husna ta kalli Maganin
“Wannan?…” Tafada muryan ta na raw, aikam Bata ankaraba Ayan ya sakar mata karfen belt ga kai, baki ta bude zata saki ihu ya saka yatsan shi kan bakinshi
“Shush…” Yafada babu wasa, da Sauri husna ta hadiye kukan,.
“Don’t answer my question with questions… Wallahi you don’t know what am capable of.. Yanzu zan sake tambayan ki for the last time.. Menene wancan kike kokarin sakawa under my bed?…” Bai idaba husna dake hawaye tace.
“Ma…ga…ni…” Ayan gyara tsayuwanshi yayi
“Maganin meye?…” Ya tambayeta atakaice, husna shuru tayi, belt ya kara dagawa sama da karfi ya buga mata wurin karfen, wannan Karin saida tayi ihu amma ya Kara dora yatsanshi kan lips dinshi yace
“Shush…now answer me..na meye?..ko.kasheni kikeson yi?…” Da Sauri husna ta girgiza mashi mai, duk abinda suke camera laptop dinshi na daukan su,
“To na meye?..” Ya sake tambayan ta, still shuru tayi ya fara buga mata belt din
“Wallahi .zan fadi…wayyo zan fada maka…pls ” tafada cikin matsanacin kuka don Ayan buga mata belt yake kaman yanda solder ke yi in sun kaman hardened criminal
“Ok..am listening..” Yafada yana harde hannuwanshi cikin hammatanshi,
“Na mal…ka…ka…ne…” Tafada cikin kuka sosai. Gira daya Ayan ya daga dayaji statement dinta,
“Wa kikeson mallakewa?…” Bai idaba tace
“You….” Tafada da Sauri don ko a lahira batason Ayan ya kara tabata da wannan belt din don har gaban goshinta inda yaje kwakaa belt ya fara kumburi
“Me…” Ya tambayeta yana nuna kanshi da yatsa,cikin kuka ta gyada kai, kura mata ido yayi for a while Sannan yace
“Why?…” Ya tambayeta babu wasa, shuru tayi tana kuka, aikam nan ya kara lafta mata belt ga baya faduwa tayi kasa tana shafa inda ya bugeta, da Sauri ya ajiye belt din ya shaketa ya karayin kneeling da ita Sannan ya koma ya kara dauka belt din yace
“Am listening.. Mene dalilin ki da kikeson mallakeni?…” Da Sauri husna ta fara cewa
“I love you…na dade inasonka…tun ranar farkon dana ganka na …fara..sonka…. I loved you…even before you start loving ihsan…” Bata idaba ya kara buga mata belt,
“Banason in karajin sunan ihsan bakinki….” Ya daka mata tsawa,da Sauri ta kama bakinta tana hawaye,
“Well mu bar wannan maganan tukunna… I will visit that again…let discuss something else… Now ki fadamin.. Waya turomin nude pic din ihsan?..” Ya tambayeta atakaice, husna sai shessheka take ta kasa magana, kafa ya daga ya harbeta
“Talk before I kill you…”
“Ni…” Ta fada da Sauri, Dariya Ayan yayi
“Daman I said it…now tell me mutum nawa kika taba turawa nudity din ihsan,…” Husna girgiza kai tayi
“Kai kadai ne…” Ayan ajiye belt din yayi ya hayeta ya shake mata wuya idanuwanshi kaman garwashi, husna zaro idanuwa tayi don ko numfashi Bata iyayi saboda yanda ya shake mata wuya, Ayan gani yayi duk idanuwanta sun fito waje, ganin in bai saketa ba yana Iya kasheta yasa yayi controlling kanshi ya saketa ya mike ya kara daukan belt din, husna kam kasa numfashi tayi, rike wuyanta tayi tana hakki kaman wacce ke daf da mutuwa
“Am listening.. A said mutum nawa kika turawa nudity din ihsan..” Ya sake repeating question din. Husna kasa magana tayi saboda yanda numfashin ta ke sama da kasa.
Ihsan kam tana shiga bathroom ta yi wanka ta fito daure da alwallah mai ta shafa ta saka doguwar Riga tare da Dan gyara fuskan ta duk Bata damu da whereabout din husna ba don a tunanin ta tana zaune falo, tana gama kwalliya ta hau kan praying mat tayi salla Sannan ta mike ta dawo falonta, Still gani tayi babu husna wurin, main falo ta shiga taga babu husna ta tsaya kaman tana tunanin
“Wai mafarki nayi?…” Ta tambayi kanta tana kalle2,
“Babe…” Ta kira ta tana shiga kitchen amma still babu husna,
“Inna lillahi… To meye haka?…” Tafada tana kara komawa main falo, ahankali ta taka ta fita waje rana kalle2, gabanta ne ya fada faduwa don tasan ba mafarki tayi ba,
“Na shiga uku…” Tafada tana komawa falo tare da Sauri ta kulle kofan ta zauna tana dafa kirjinta don ko kadan batayi tunanin zata shiga part din Ayan ba balle taje chan, kitchen ta shiga gabanta na faduwa har store dake next to kitchen ta kalla amma babu kowa, nan ta tsaya tana tunani, ahankali ta fara adua cikin ranta. Bayan kaman minti biyar ta fara tunanin abinda zata dafa kafin Ayan ya dawo not knowing yana Chan yana ballan burouban husna.
Da kyar husna ta Iya cewa
“Wallahi.. Wallahi… Wallahi… Kai
.kadai..na…turawa…” Tafada har lokacin hannun ta dafe sa wuyanta,
“Ok..I believe you…yanzu fadamin… Me waya turomin mutane suyi warning dina kan in rabu da ihsan?…” Cikin kuka husna tace
“Nice….” Tsaya kallon ta yayi yana mamakin how dangerous some people close to you can be,
“Me ihsan tayi maki?…” Ya tambayeta atakaice, husna shuru tayi tana haki don har lokacin Bata dawo hayyacinta ba, kara lafta mata belt yayi ta saki wani irin wahalallen ihu Mara sauti
“I said me ihsan tayi maki?…”
“Ba..by…ko…mai…” Tafada kaman mai cutan asma,
“Wake sa ake fasa auren ihsan?..” Ya kara tambayan ta
“Ni…ce..” Tafada cikin kuka,
“Any nagode da kikasa aka fasa sauran auren… Yanzu fadamin meyasa bayan aurena na ihsan na kasa kwanciya daita?…” Ya sake tambayan ta yana daga belt, da Sauri husna tace
“Ma..kul…li…. Na..saka…maka….” Tafada da kyar, wuyan riganta ya shake ya fara dukanta da belt da dayan hannun, saida yayi mata ligis Sannan ya saketa, lokacin ko kuka husna bata Iya yi nishi Kawai taje jini na fitowa daga bakinta, kujeran gaban mirror ya dauko ya zauna gabanta ya daga jaw dinta Sannan yace
“Ki kalleni da kyau nayi maki kama da Wanda zakiso?…waye ni?…” Ya tambayeta, shuru tayi don ko magana Bata iyayi, belt ya kara kwada mata
“I said wayeni!!..” Ya daka mata tsayawa
“Mijin… Kawata….”
“Good…ni mijin kawarkine..amma kike son mallakeni?… Kike furtan kina sona?…ko kadan ihsan batason abinda zai taba ki Ashe ke munafurtan ra kike…kullum kina gidansu saboda ki ga in tasamu wani cigaba ki wargajeshi ko?….kullum kina manne daita saboda ki samu daman zaluntanta…to yau zan koya maki hankalin da ko shaidan da kanshi yazo maki da aiki sai kince kin tuba…” Yafada yana kara mikewa,
“Yanzu zan yi maki bulala Dari don in tabbatar maki am not the man for you…” Husna data jigata sai jini ke fita ta bakinta gaban goshinta ya kumbura, cikin ya mintuna face dinta ya chanza kaman ba ita ba saboda yanda face dinta ya kumbura amma ko kadan Ayan bai ko tausaya mata ba,
“Ki dinga counting.. Kuma dakinyi batal zan dawo farko…”
“Pls…” Bata idaba ya zula mata belt
“Pls..am ..sorry… Sharrin… Shaidan… Ne…kayi…hakuri…” Ta fada da kyar, ko jinta Ayan baiyi ba ya zula mata belt yana cewa
“Count…” Yafada da karfi.
Ihsan kam bayan ta gama jimaminta ta dauko kasa daga fridge ta raba biyu ta maida rabin sannan ta yankan sauran ta wanke ta Dora kan gas Sannan tayi seasoning dinshi,albasa ta dauko ta fara yankawa, Kawai sai ta tuna bata gyara part din Ayan ba especially gadon don tunda ta bar dakin ta koma dakinta Bata Kara shiga part dinshi ba, da Sauri ta karasa yankan albasan ta juye kan kazan Sannan ta fito ta kama hanyan part din Ayan, tun a falo take jin Ayan nacewa
“Count…” Kuma sai taji kaman saukan bulala, da gudu ta karasa bakin kofan ta buga da karfi
“Waye?…” Ta tambaya cikin tashin hankali, Ayan na jin muryan ihsan yace
“Precious.. Ki kiramin iyayen husna..ki kirawo dukkan people that matters…” Yafada yana dukanta kaman hes life depends on it, husna najin muryan ihsan tayi karfin halin cewa
“Pls…ki ..tai ma..ka..min….” Tafada cikin wahala, ihsan najin muryan husna ta fashe da kuka tana dukan kofan da karfi,
“What are you doing….” Tafada tana buga kofan da karfi, amma Ayan ko kallon kofan baiyiba ya cigaba da dukanta da belt, ihsan sai buga kofan take da karfi tana ihu tana kuka amma a banza, ganin hakan yasa ta koma part dinta da gudu ta dauki wayanta ta kira Umma tana kuka ta fada mata ta kira Ayan ya kyale husna ya kulle ta cikin daki yanason kasheta, ta fada mata tana kuka sosai, tana gamawa ta koma bakin kofan Ayan tana bugawa da karfi tana kuka kaman ranta zai fita
“Pls..ka bude…don Allah…” Ta fada tana kuka, Ayan kam idanuwanshi sun rufe baiji bai gani, sai dukan husna da ko motsi batayi Kawai yake.
Umma kam cikin tashin hankali ta kira su Yusuf da su tafi gidan Ayan da akwai matsala, bayan kaman minti sha biyar Ayan bai bar dukan husna ba ita Kuma ihsan da bakin kofan sai ihu take tana tsalle tana rokan Ayan daya bude kofan amma a banza, jin ana buga kofan falo da karfi yasa tayi Falo da gudu tana kuka ta bude kofan ganin Yusuf da Muhammad yasa tayi saurin cewa
“Pls..Ku taimaka min…zai kasheta…” Ta fada tana shige masu gaba har bakin kofan, har lokacin Ayan bai bar dukan husna da ko motsi batayi ba, buga kofan su Muhammad suka shiga yi amma a banza, Da karf su samu kofan ta bude da tsiya, da gudu ihsan ta shigo Ayan ko kofan bai kallo ya cigaba da dukanta, ihsan na shiga dakin taga husna kwance jini na fita daga bakinta ko motsi batayi, nan take ta yanke jiki ta fadi kasa.
[12/27, 14:14] ‪+234 814 199 1000‬: ❤💚💜🖤💛💙
KAWARTA CE SANADI
❤💚💜🖤💛💙



®zuwairat(ummu Maryam)




5⃣5⃣





Basma yar lele muna ji dake kaman yanda kike ji da mu Allah ya sada mu da alkhairi ameen🙏👏


Jin tim yasa Ayan juyawa da Sauri su Kuma Muhammad sukayi kan husna da in take kwance ya bace da jini,
"Subhanallahi!..." Kawai suke ta maimaitawa, Ayan kam ajiye belt yayi yayi kan ihsan da gudu yana kiranta tare da jijjigata,
"Wai kai wane irin jaki ne?..." Yusuf ya fada da karfi yana inspecting husna da har lokacin Bata yi, Ayan ko kallon su baiyi ya tashi da gudu ya dauko ruwa ya dan yayyafawa mata Sannan ta bude ido, da Sauri ta tureshi tayi kan husna da Yusuf ke rike sa wrist dinta yana duba vital signs, fuskan husna ta tallabo taga face dinta kaman ba ita ba saboda yanda face dinta ya kumbura ya chanza kamanni, ihsan kara fashewa tayi da kuka tana kallon Ayan,
"Wai me tayi maka zaka kashe ta?.." Yusuf ya sake tambayan shi cikin fada, Ayan dai kallon ihsan da red eyes dinshi Kawai yake kallo yana tunanin yanda zataji in ya fada mata husna ce SANADI wahalan ta, bai ankaraba ihsan ta rike mashi Riga tana kuka,
"Me tayi maka?..." Ta tambayeshi cikin kuka, rike hannun ta yayi, fixge hannun ta tayi ta fara  dukan kirjinshi tana kuka tana cewa
"Laifi tayi don ta zo gidan nan?..." Kara rike hannun ta yayi yana kokarin rungume ta amma ta tureshi tana cewa
"I hate you...I hate...na tsaneka..." Tafada tana kara komawa wurin husna da su Muhammad keta kokarin suga ta farka, daga ta zaune Yusuf yayi ya rike bayanta yaga jini, ahankali ya bude bayan ta yaga duk fatan bayanta a kumbure saboda belt. Ayan kashe camera laptop dinshi yayi ya dauki bag din husna dake kasa ya dauki wayant,
Ihsan hada kai da gwaiwa tayi ta dinga kuka, Ayan duba number da husna ta  saving da sweet mother yayi ya tura message kaman haka
" _Ku taimaka min.. Mijin ihsan zai kasheni... "_ ya turawa mami ya ajiye ya dawo ya rikewa ihsan hannun ta kara fixge wa tayi
" monster leave me alone....." Tafada tana mikewa tsaye, barin dakin tayi Ayan yabi bayanta yanason fada mata abinda husna take mata amma he want her to see it for her self, tana kuka ta dauki wayanta ta kira mom, daman abinda Ayan ke so kenan don yanason dukkan su su taru gidan kafin ya nuna masu,  mom tana picking ihsan ta fara cewa
"Mommy... Ku taimaka min... Ayan ya kashe husna..." Ya fada cikin matsanacin kuka, Bata jira abinda mom zatace ba ta kashe wayan ta zauna kan kujera tana kuka, ayan zama yayi gefen ta ya dafa shoulder ta yana cewa
"Baby ki bar kuka...zaki godemun in kin gan abinda husna tayi ..." Buge mashi hannu tayi tana cewa
" kome tayi bai kamata kayi mata wannan hukuncin ba...I hate you..." Tafada tana kara mikewa don komawa part dinshi, rike mata hannu yayi
"Baby..your so called friend has been behind all your problem..."
"Daman ba tun yau ka nuna baka kaunar husna ba...ba sai kayi mata sharri ba...wallahi sai an hukunta ka kan abinda kayi...daman you are dangerous.. Sai yau ka kara tabbatar min da haka..Kuma Wallahi ban zama da kai...." Tafada tana kuka Sannan ta bar dakin, Ayan dai murmushi yayi yana godewa Allah dayasa ya dauki video abinda ya faru da babu abinda zai fadawa ihsan ta yarda dashi
 Zama yayi kan kujera yana shafa beard dinshi ahankali fuskan shi dauke da murmushin jindadi don har cikin ranshi yake jin nutsuwa na ratsanshi, sai yanzu ya yarda cewa ba haka nan jinin wasu bai haduwa ba, da akwai dalilin hakan don shi tunda yake bai taba jin ya tsani mutum kaman yanda ya tsani husna ba, haka nan he despise her so much that he don't want to set his eyes on her,
"Wai I love you...na dade ina kaunarka..." Yafada yana Dariya
"Zo ki soni..shaidaniya...wannan kadan kika gani..." Yafada yana relaxing, sai lokacin ya tuna baiyi sallan zuhr ba, da Sauri ya mike ya shiga bathroom din ihsan ya dauro alwallah ya fito yana zuwa main falo ya fara jin kaurin kaza da Sauri ya shiga kitchen yaga abinda ihsan ta Dora ya kone, kashe gas din yayi ya bar gidan yana
"Alhamdulillah..."


Ihsan komawa tayi dakin har lokacin husna bata farka ba Kuma bakinta bai bar fidda jini ba wayanta ne ya fara ringing ta dauki wayan taga mami kasa picking tayi sai kuka Kawai take,
"Pls..do something..." Ihsan ta fadawa su Yusuf tana kuka,
"I think dole mu tafi da ita hospital...." Muhammad ya fada, ihsan rufe bakinta tayi da tafin hannun ta tana fashewa da sabon kuka,  Yusuf kallon ihsan yayi
"Wai sis me ya hadasu har hakan ya faru?..." Cikin kuka ihsan tace
"Babu abinda ya hadasu...daman baya son ganin ta...kullum fadin how much he hates her Kawai yake...danasani na fada mata ta bar zuwa nan gidan...its all my fault..." Ihsan ta fada cikin matsanacin kuka, kai Yusuf ya girgiza yana cewa
"Ba laifin ki bane...Kawai mijin ki ne Dan iska...wai yana ina?..." Ya tambayi ihsan, kuka ta cigaba dayi Bata amsa mashiba,
"Let's take her to the hospital..." Muhammad ya sake fada,  dagata zaune Yusuf yayi ya dauketa in a bridal style, shi Kuma Muhammad ya bude mashi kofa ya fita daita, da gudu ihsan ta shiga part dinta ta dauko hijab suna saka ta mota Ayan ya dawo daga masjid, fuskan shi daure ya rike hannun ihsan dake Neman shiga mota, tsalle ta farayi tana cewa
"Mugun ka sakar min hannu... Wallahi ka sakeni sai naje hospital din...." Ta dinga fada tana ihu amma ko saurareta bai yiba ya jata falo Yusuf binshi yayi da harara yana cewa
"Monster in disguise..."


Ihsan na ihu ya kaita falo ya wullata kan kujera,
"Sit here..." Yayi commanding dinta Sannan ya shiga part dinshi few seconds later ya fito rike da laptop dinshi, budewa yayi ya kunna
"Now ki kalla..." Ya kara commanding dinta don yasan halin ihsan dole sai da zafi, tana hawaye ta fara kallo, tunda daga inda Ayan ya fara tambayan husna menene akasa, ihsan daga kai tayi kalli Ayan da disbelieving look,
"Yes its real..." Yafada yana zama gefen ta, jin husna na cewa Maganin mallakane yasa ta sake fashewa da matsanacin kuka tana cewa
"Ba gaskiya bane..." Tafada cikin kuka, shafa shoulder dinta Ayan yayi yace
"Just keep quiet.. Ki kalla.. There is more..." Yafada mata ahankali, haka ta dinga kallo tana hawaye amma Bata kuka, Ayan gani yayi hannun ta na rawa kaman mai jin sanyi, da Sauri Ayan ya dauke laptop din yayi kneeling gabanta
"Baby am so sorry.. Allah ne ya amsa aduan mu..." Ihsan shuru tayi still jikinta na rawa
"Bakiyi saa kawaba...amma ina tabbatar maki na koya mata hankalin da bazata kara zuwa inda muke ba..." Ayan ya fada mata yana kama hannun ta, itadai ihsan shock is written all over her, bakinta sai rawa yake kaman mai convulsion, suna cikin haka Umma tazo,
 Babu sallama ta shigo falon taga Ayan yayi kneeling gaban ihsan,
"Wai meke faruwa?..." Ta tambayesu, sai lokacin ya san da mutum, da Sauri Ayan ya mike ya gaidata, fuskan ihsan sharkaf da hawaye, har lokacin ihsan bata motsa ba,
"Don't greet me..ka fadamin abinda ke faruwa.." Umma ta fada tana kallon ihsan data kurawa waje daya ido Bata ko kaftawa, da Sauri Ayan ya kunnawa Umma abinda ya faru tsakanin shi da husna, Umma sai salati Kawai take,
"Inna lillahi..waina.. Ilaihi..rajuun..." Tun Bata kai koina da kallon ba,
"Wai ya suke da yarinyan in question?..." Umma ta tambayi Ayan,
"Aminiyarta ce..." Ya amsa mata, Umma kama hannun ihsan tayi ta share mata hawayen face dinta, har lokacin ihsan bata ce kala ba Kuma Bata kafta idanuwa ba wuri daya Kawai ta kurawa ido tana, Umma cigaba da kallon video tayi tana salati,
"Amma wannan yarinyan tayi karanta da irin wannan halin...halinta is too mean and Dan....." Bata idaba ba mom din ihsan ta shigo da sallama, amsa mata sukayi amma banda ihsan da har lokacin shock bai saketa ba, durkusawa Ayan yayi ya gaidata ta amsa tana kallon ihsan data kurawa waje daya ido, itama kunna mata video Ayan yayi ta fara kallo sai ta fashe da kuka tana cewa
"Subhanallahi...yarinyan nan bata sati Bata zo gidana ba...har mamakin irin amincin su nake..Ashe tana da plan ...Allah yaisa tsakanina daita...ta cuceni..." Mom ta fada cikin kuka, dafa shoulder ta Umma tayi ta dinga rarrashin ta, duk abinda suke idanuwa Ayan kan ihsan tana mamakin yanda ko kifta idanuwa batayi sai hawaye Kawai ke fitowa daga idanuwanta, babu kunya ta kara kama hannun ta,
"Ihsan..." Ya kirata amma yaga bata tanka ba,
"Ko in kaita hospital?..." Ayan ya tambayi su Umma, Umma zata bude baki tayi magana mami ta shigo da ka ganta kasa cikin tashin hankali take,
"Ina husna take..." Ta tambaya cikin tashin hankali, sai lokacin Umma ta kalli Ayan
"Yanzu tana ina?... "
"Hosp..." Ya amsa mata atakaice,
"Da ka kyaleta.. Da ka bari hukuma ta hukunta ta..." Inji Umma, cikin rawan jiki mami tace
"Pls..me tayi?..." Ta tambayesu muryan ta na rawa, mom kallon ta tayi Sannan tace
"Ashe husna dake bin ihsan bumper to bumper ba don Allah bane sai don ta hallakata?... To alhamdulillah.. Allah ya toni asiri ta..." Mom ta fada mata atakaice, hankalin mami kara tashi yayi tana tsoron kar ace husna kokarin kashe ihsan tayi saboda son da take wa Ayan, kallon ihsan mami tayi ta kalli mom
"Pls Ku fadamin exactly abinda ke faruwa ko.na samu sukuni..."
"Nuna mata..." Umma ta fadawa Ayan, Ayan kara bude video yayi ya koma wajen ihsan dake hawaye har lokacin Bata motsi, mami tana kallo tana hawaye, har inda husnan ke cewa ita ta hana ihsan aure, hannu mami ta dora bisa kai tana cewa
"Nashiga uku na lalace...wannan wace irin rayuwa ce wannan... Inna lillahi.. Nasan ina da nawa matsalan amma am not as dangerous and wicked as this..." Tafada cikin matsanacin kuka, Umma tausaya mata tayi tana cewa
"Kiyi hakuri... Yaran ne ka haifesu amma baka haifi halin su ba..Kawai sai adua..." Umma ta fadawa mami dake kuka kaman ranta zai fita, kallon ihsan mami tayi ta fara cewa
"Daughter.. Allah kadai yasan yanda nakeson ki har cikin raina.. Bazan taba yarda husna ta cutar dake da sanina ba...Allah kadai ne shaidata...wallahi ban taba sanin komai ba...Dan Allah kiyi hakuri Ku yafe mata..." Tafada tana kallon Ayan,
"Ba komai.. Ai she have leant her lessons..." Ayan ya fada yana kallon ihsan, dake hawaye, yana mamakin yanda hawayen face dinta basu kafewa, farat daya ihsan ta saki kara tana cewa
 "Kin..Cuceni....na yarda dake...na fada maki sirrin da ban fadawa mahaifiyata ba...na dauke ki da daraja fiye da kanwata...kin cuceni... Amma da
Akwai Allah.. Allah zaiyi min sakayya..I will not forgive you for what you need to me..." Ta kare maganar ta cikin kuka, rungume ta Umma tayi tana lallashinta, Ayan kam ji yake kaman ya kori dukkan su don yaji dadin petting Matan shi, mami kuka, mom kuka sai kuma ihsan dake kuka kaman ranta zai fita,  mami Bata nemi jin inda aka kai husna ba ta bar gidan tana hawaye itama mom fita tayi ya rage daga ihsan dake lafe jikin Umma tana kuka sai Ayan, da kyar Umma ta shawo kanta tayi shuru Sannan ta tafi tana cewa zata aiko masu da abinci, tana fita Ayan ya dauki ihsan ya kaita har bedroom ya ya zaunar daita kan gado yana kallon ta, zama yayi gefen ta ya jawota jikinshi
"Kiyi hakuri.. Nasan haka Allah ya kaddara amma kawa bata kamata Tasan komai naki ba...na fada maki bason ta amma you think haka nan nake fadi..." Ihsan daga red eyes dinta tayi ta kalleshi Sannan tace
"Ya zaayi in Sani bayan she's so good to me?... Kullum kara shige min take don ta san sirri na...sai yanzu na tuna ranarda ta daukeni pic,...husna is do wicked... I hate her with passion.." Dariya Ayan yayi yana shafa kanta
"Now we are even..."

***************


Rabe kam yanzu ya koma mahaukaci zalla yanzu da kazo unguwan su kace a kaika gidansu " sonta nake" da gudu zaa kaika saboda  Yanda koina a area dinsu aka sanshi da yawo da kwalin juice. Inna kam har kauyensu taje wurin wani malami inda aka shaida mata asiri ya sha Kuma sai yahadu da wacce tayi abun zai samu sauki, inna kam kuka tayi godewa Allah, Kuma tana danasanin Satan gidan aiki don tasan in da Bata dauko wannan juice din ba da Bata jawa kanta ba, gashi ba abun ta fadi gaskiya ba, Kuma tana mamakin waye ya zuba Maganin cikin lemon wani lokacin takanyi tunanin kilan mom ta zuba ta ajiye don ta bawa dad.

Yau tana cikin aiki a gidansu ihsan taga mom ta fita bayan mom ta shaida mata ta kuka da gida da yaran zataje da dawo, bayan hour daya da rabi mom ta dawo tana kuka ta shiga falo, da Sauri su Janna da sauran yaran tare da inda suka tareta da tambayan abinda ke damunta, nan mom ta fada masu duk abinda ya faru tsakanin ihsan da husna, nan take inna ta fashe da kuka tana cewa
"Na shiga uku.." Tafada cikin kuka , kneeling tayi gaban mom, mom kallon mamaki tayi mata tana cewa
"Lafiya?.."
"Hajiya ki gafarceni...na Dade ina yi maki laifin sata...kullum ban barin gidan nan sai na dauki wani abu na abinci daga gidan nan.." Tafada cikin matsanacin kuka, mom tsaya kallon ta tayi tana mamakin where this is coming from, inna ta cigaba dacewa
"Na akwai ranar da na dauki lemon kwali daga nan gidan ..Dana kai gidana sai Dana ya shanye ..tun ranar yake cewa sonta nake...nayi bincike aka shaida min cewa asiri yace..Kuma ance sai yaga wacce tayi abun zai samu sauki..." Ta kare maganar ta cikin kuka, Umma jimamin abinda inna ta fada Kawai take, tasan husna is behind it
"To Allah ya yafe mana gabaki daya...yanzu meye abinyi ?..." Mom ta tambayi inna
"Dan Allah ki fadamin inda husna take in kaishi don nasan itace SANADI..."
"To shikenan.. Amma yanzu ance husna tana asibiti..."
"Don Allah ki sa akaini asibitin.." Inna ta fada cikin kuka,
"To..." Mom ta amsa mata ta kara dacewa
"Amma Dan Allah kar ki kara daukan wani abu nawa ba tare da sani ba..." Da Sauri inna tace
"Insha Allah..."

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *