Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, October 19, 2020

Yan Matan Zamani Complete Hausa Novel

adsense here

 

Yan Matan Zamani Complete Hausa Novel

💓*YAN'MATAN ZAMANI*💓

                Na.                                                                                                         

*biebie dee bukharee da samrah*.                                                                          

 _Da sunan Allah mai rahma mai jin Kai_ 1⃣-5⃣


  ```Yarinyace a tsaye da bazata wuce shakaro goma shashidaba(16) girgiza takeyi tana karkada kafafu irin na masifa dinan Chan sai gawani saurayi yafitoh da bazay wuce 23  zuwa 25 bah  naji takirashinda suna Ahmad, ahmad yakalleta yace yade zeemah lfiya naganki anan ya tanbaya saida tawani juya manyan idanunta sa'an tace dole kace haka ai Kayi alkawari baka cikaba kasan kuma nacema bikin saura kwana goma amma banjii wani motsiba nazo yanzo kuma kana wani borin kunya toh ni gaskia kayi magana inbazakamin ankon bane gara kafadamin tin da wuri nasan abinyi magana take cikin rashi kunya sai da ya dubeta da kyau cikin kulawa'yace haba zeemarhnaa mai yayi zafi haka ' hadda fada  sai da taturo bakinta gaba' sanan tace toh bayan kowa yan class dinmu sunyi saini salon su rainamin wayo saida yakara dubanta sanan yace ba mai raina maki wayo zeemarhna yanzo zanbaki 'kudin saida takaleshi hade da murmushi a fuskanta tace da gaske yace sosai zeemarh yannu yassa cikin aljihun wandansa ya zaro bama 7k yabata ansa tayi tana murna batare da addua ko godia ba tayi gaba abinta shidai binta yayi da murmushin jin dadi 


Ahmad ya kasace yanama zeemarh so mai girman gske Wanda duk abubuwanda takeyi baya gani sometimes yana ganin haka a matsayin yarintarta.ita kuwa zeemarh tinda Ahmad yabata kudinan bata tuna komai ba sai zarcewa gidan kawarta kuma aminiyarta wato salma tamanta da shara da wanke2 da mama tasakata shiganta gidan su salma keda wuya ta tarar da ummien salma tsakar gida gaisheta takeyi amma ita kuwa Ummie kirari take Mata"yan'mata adon gari in Baku ba gari in kunyi yawa gari yayi daidai"jin kirarin ne yasa salma fitowa daka daki tana murmushi tanacewa ummiena kenan itadai Ummie tabisu da murmishi jindadi sukuma suka shege daki suna magana kasa kasa

  

Sunshiga daki suka zauna bakin gado sai salma ta kalle zeemarh tace kee wllhi da matsala zeemarh tawaro manyan idanuwanta tace kardee bai baki kudinba ko baba ne yace bazaki bikin ba duk ta tanvayeta a rudee salma tayi smiling tace ai in wanan ne da sauki zeemarh tace please babe tell me mana wats going on salma tawani bata fiska tace wai mu duk kyan mu acee muna tafama da Samsung s3 Farty fa har tayi iPhone 7+ bama fa iPhone 5 ko 6 ba zeemarh ta kaleta tace ke inbanda abinki yarinyan da babanta keda kudi kuma tanada yayye itace auta fa  a gidansu salma takaleta gami da watsa mata harara tace kee ko kaffara bazanyi ba wlhy wani saurayin yasiyamata tajaa wani dogon tsaki mtwwwww

zeemarh tace ke kawalli kwantar da hankalinki'  very soon muma zamu faso gari. bara dai kiji yanzun nan ahmad yaban 7k nan' take salma ta waro idanuwa" ta hade rai wane xatayi kuka tace. kai nikam rashin wayar nan na nadamuna dayawa' kallemu fa'. ta tashi tsaye tareda girgiza jikinta tace kallemu da kyau' ba makosa kuma san kowa kin wanda yarasa. so ki kwantar da hankalinki mun kusan rike waya babba'. zeemerh ta qwale ido tace allah kawata' tace nataba miki' karyane. nan ta girgiza kai sukasa shewa. nan ummien salma ta shigo tace yan' matana wannan dariya haka dafatan de samuwa ce. nan salma tayi charaf ta amsa tace kai umma kin fiya ' surutu wlh. se ummien salma tace o' ni maryam naga takaina. nan zeemerh tace ummin mu kinsan kuwa bikin zee ya karato' ummi tace laaaa yar albarka ni nama manta'. se salma tace umma wlh ni wayama nakeso. umma ta dafe kirji tace kikace me'.tace umma waya. ummi tace lalle inba shekaruna zaki saida kisiyaba dame zakisai waya"?. se salma tace kai ummienmu afadi gaskia'. se ummie tace to uwata se naji shaka.nan duka sukasa dariya se chan ummi tace salamatu. salmah tace yade ina wannan din nan me zuwa da jan mota. sai zeemerh tace kai ummienmu wato idanki nakansa ummie tace yar jakar uba ba doleba. salmar tace ni kinma tunamin yau zanyi bako. zeemerh tace kawalli wane zezo tace dallah tsaya nan' nayi alhaji me sakin aljihu '. tace ke kawas amma ko labari bbu tace zauna nan.  ummie tace nide in kinje  kice Ina gaidashi kuma wlh in talakane' kika tasaya dashi banyafe miki ba. nan sukasa ihuuuuu wooo"  ummien mu allah bar manake ki huta. nan tayi dakinta .zeemerh tace k barinaje  nasan dd tana jirana nan sukayi sallama'.```


©*biebie dee*

07039732859.                                                                                                                                ©*samrah*.                                                                       09062056022

💓*YAN'MATAN ZAMANI*💓

              NA

*biebie dee bukharee da samrah*

  1⃣1⃣_1⃣5⃣



_Dedicated to our humble sister Ummu abdulnasee(Anty ainass and our hajjace(hajjanmu) thank you so much with your support, love n care_

❤❤❤❤









Haka dai sukai ta hiransu didi na Dada fasama zeemarh Kai ita ko tanata murmushin jin dadi 

     Next day

Yakasance Monday  su zeema nada sch sch kenan  da kyar a kasamu ta tashi sallah hakan yafarune sakamakon night subscription datayi kwana takusa a zaune tana downloading apps da kallo ta YouTube, ko da ta idar da salla baccinta takoma sai wajen 7 ta tashi tashiga wanka already Firdausee tagama komai nata ba ita tagama shiyawaba sai to 8 Firdausee har tagaji da jira bata tsaya yin breakfast ba dan tasan mama ba yadda zatayi taita batama Firdausee time ba sallama sukama maman suka nefe siden baban dan ansan transport money


Sun shiga dakin baban da sallama bayan yansa suka hada baki wajen gaidashi ya ansa hade dacewa nasan azeemace tasaki latti ko Firdausee ita dai Firdausee batace komai ba sai murmushi da tayi 500 yadauko kan bedside yamika masu game dacewa adawo lfya allah bada sa'a suka ansa mai da amin.waje kawai sukafita kasancewa suma mama sallama dama, sun fida ba dadewa sukasamu abin hawa sai sch ko da suka shigo sch din har anfara tare lati zeemarh batabi takansu ba taja hanun Firdausee sukai gaba kasancewar da Senior yar ss3 saida taga shigan firdausee class dinsu sanan ta nufa nasu class din tana shiga tayi dropping bag dinta kan dask tayi back seat inda taga *yan'matan*class din nasu da allama wani abun suke kallo tanakarasawa wajan salma ta tabo salma ta harareta cikin wasa tanacewa baby sai yanzo zeemarh tace wlh kibari kawai night subscription nayi wlh shiyasa namakara salma tace lallai komawa wajen zamansu sukayi bayan sun sauna zeemarh ta kalle salma tace baby da matsala faa,batakai da bata ansaba biology teacher ta shigo ajin duk yan class suka mike dan gaisheta ita ko zeemarh haushi tashi ankatse masu hira(niko Dee bukharee nace ba akwai break time ba...lol)


Anty hameeda bata bar class din ba sai 10am daidai fitantakenan akay ring ball brktime.bayan sumai da books dinsu cikin jaka salma ta dubeta tace mai matsala wai zeemarh ta gyra zama tace kudin dinki coz so nake amana dinki irin na yaran manya kaman na 4500 zuwa 5000 ko wani daya salma tace gskia ne kuma zeemarh takuma cewa so nake abinkinan na zee amira kaita tasan ba ita ita kadai ke sa expensive kayaba da unique dinki salma takuma cewa wlhy amma dai bari deeja ta shigo muji abinta zatace.


Fita sukayi wajen class suka zauna jiran deeja,basufi minti biyar da zamaba sai ga deeja tazo itama ta zauna tacewa daka scienceB nakaima teejee note dinshi salma tace bamu tanbakeki wanan bamu magana muke kan kudin dikin anko dan wlhy so nake amira kaita sai tace na ara mata style deeja tayi daria tace anwuce wajen ai zeemarh da salma suka kalleta tace yes babie nasamu talalan banza wlhy kuma yamasifan iya dinki kee fact plazan da yake nan yan gdansu amira kaita kee Kai dinki dan haka karku damu shi zanma dadi baki yamana daria sukasa gaba dayansu salma tace wlhy muna wuta (ni da samrah mukace munga alama)


Kawayen juna kenan,sunada yawa a group din nasu amma wayanan 3sunfi shakuwa,basusa komai a gaba ba sai rayuwan karya da daukan Kai sukai Inda Allah bai kaisubah sudai koda yaushe karfa a fisuu nasu matsalan kenan...

    


Hakadai sudukayta karatu har lokacin tashi yayi,ko a hanyama hiyan bikin sukaytayi har suka isa gida.zeemarh tashiga gidansu da sallama dakin mama tanufa bayan Tamata sannu da gda bayan mama ta ansa hade da tanbayanta ina ta tsaya har Firdausee tarigata dawowa xeemarh karya tayi tace bata gama note bane shine tace tawuce mama tace ai sai kiyi sauki kinga yanzo 3 saura kuma zaki islamiyyah ita dai zeemarh Allah Allah take mama tace wuce koda tashiga dakinsu bayan tayi wanka hijabin islamiyyanta tasa tayi side din didi,didi naganinta tawace baki tace jigass harkindawo kenan zeemarh tace eh mama maganan islamyya takemin kuma so nake mujee kukai dinki dasu deeja,didi tace jekikawai xanmata bayani zeemarh tayi murmushi tace toh sainadawo didi tace adawo lfya Allah bada sa'a....




© ~biebie Dee~

07039732859

~samrah~

09062056022

💓*YAN'MATAN ZAMANI*.💓.                                                                  NAA                                                                                                                                                                                                                          

*Biebie dee bukharee da samrah*

  6⃣-1⃣0⃣



                                                                                                                                                                                           _Actually yan uwa zakugamun chanza sunan littafin na' although it cox of some reason's' . coz yesmin tafeesu itama tana' novel yam'mata buh it's n't a big deal'. bygone b bygone's nomore' complain't. it ur honoured darling we dedicate this page for uy' YESMIN TAFEESU we LYSMC_💚


    ```"Haka tabar gidansu salma tana mai tunanin yanda bikin zee' zaikasancee. tashigo gidan nasu da sanda dan bataso mama tasan dawowanta,bata zarce ko ina ba sai dakin didi'


Fadowa dakin tayi babu sallama sai zubewa datayi kan kagon didin" ,didi' ta dubeta tace kekuma da ga ina kinshigomin ba ko sallama saikace nacimaki bashii ita dai zeemarh murmushi takeyi didi' tace kujimin yar banzan yariya ina magana kinamin murmushi watoh ga mahaukaciya ko,zeemarh ta rungumeta tace kakata ta kaina Allah barmin kee kiga yanda Zan rinka maki ruwan cash didi' tayi daria kadan tace jaa'ira ni dagani kwanci'ya takuma jikin didi abinta'. Didi' tashafa kanta tace wai daka ina kike saida nayi smiling kadan sanan tace wlhy daka gdansu salma naje kan maganan bikin kawarmu da za ayi ne didi' tace da kyw zeemarh tace yawwa didi' dan Allah rakani wajen mama saida "didi' tabata fuska tace mai kikayi wai zeemarh tace wlhy shara da wanke2 tasani natafi gdansu salma ko yanzuma batasan shigowana ba dakinji tafara min fada didi' taace Kai Amina akwai ta da sababi wlhy  tashi mujee tashinsu kenan sai ga Firdausee tashigo dakin didi' da sallama sai da ta gaisheta sanan ta dube yar'uwar tata tace sis kije kishiya islamiyya ankusa fara tare latti kuma kinsan yau sati Ana duka sai da zeemarh ta bata fuska sanan tace kije kawai zanzo sai nayi wanka 


Firdausee batakawo komai ba tayima did' sallama tayi tafiyarta. didi' ce takama hannun zeemarh suyi side din nasu basu gama Kara sawaba didi' tafara kiran Amina!Amina saiko gata tafitoh sai da ta kalle zeemarh ta wasamata wani uban harara sanan tasake gaisawa da didi' ."didi'  tace nasan kina ta nemanta wlhy nice na aiketa sai yanzo ta dawo nace Bari nasanar dakee kar kimata fada 


Mama tayi murmushi tace ahh ba komai zeemarh najin haka tashige daki, bayan didi' tawuce ne mama tashigo dakin tana kiranta saigata tafitoh tace mama gani mama tace bazaki islamiyya bane haka zeemarh ta marairaice fuska tace wllh nayi latti mama 3fa hartayi innaje duka za amin wlhy,mama tace wanan kuma kekika sani kizo kitafi kawai wanine yasaki lattin saida zeemarh tai tabama mama hakuri sanan ta barta


Wucewa dakinsu tayi da gudu tana jin dadin yayin da mama tafita da ido na cewa allah shiyamin zeemarh,tana shiga daki key ta dauko ta janyo phone dinta dake katifansu tanajin dadin barinta a gda da akayi WhatsApp tashiga taga chart din friends dinta a' group magana suke kan bikin zee. chan a group tana chat se taga nusy ta skul nasu tasa hotan wani a profile inta' tana kwance ta miki tace wow' nashiga uku' daman nusy tana online'. tace hi nusy" nusy tace babe ' ya akayi zeemerh tace dan allah nusy waye wannan' wlh daga ganinsa dan hutu ne' hehehehe kai zeemerh daga ganin sarkin pawa se miya tayi zaki' zeemerh tace wlh ni ba wannan ba' wlh daga ganinshi me kudi ne. Kuma da alamu zan wankesa" nusy tace k ' kirufama kanki asiri wannan babbab kaine' nan zeemerh tace habade. nusy tace wlh fa be ganin kan kowa da gashi'. mshcwww aikin kawai yaji kunya to' nusy tasa dariya tace kinci wuya bae' nan sukasa dariya. chan zeemerh tace k wai' ya preparation na bikin zee ne" nusy tace lol nifa nagama kome kawai tym nake jira" cox material din 4k dinnan ni wlh bemin ba cod less mom tadaukomin tace wai bataso nasa wannan 30k infada miki.' nan zeemerh ta hadiyi yawu" ji kk kut " tace lalle kina wuta allah sarki nikam' nan nusy tace keda salma ku zauna nan' barafa kiji k' kudi shine mahadin rayuwa " wlh shiyasa mum inmu takecin karanta ba babbaka ' . so nima dole na kwaikwayeta' zeemerh tace k anya za'a mutu kuwa'" nusy tace dallah so kk kiyi garding duniyar. nan suka dungi' hirarsu se wajen biyar zeemerh ta tashi daga chat' ko sallah bata samu ikon yiba"  ta hau' bacci seda mama tazo ta tadata sbd magrib yakawo kai' tana tashi tayi bayi tayi alwala tayi sallah'.  se dakin didi ' tana shiga tace didi' wlh yau kinsan me' tace a'a sekin fada tace hun' wlh sha'awar ice cream da shawar'ma nake" dd tace lalle tawan kice' yau insa rai' zanyi asuwaki da kayan dadi" ta cono bakinta tace' ni dan allah ki tsaya kiji' tace azaunema nake ' tace didi in kinaso kici kayan dadin nan tsaya kiji yadda' za'ayi " didi tace to'. aikam ta rada mata yadda zasuyi' nan suka kwashe da dariya didi ' tace yar kusun uwa ashe har yanxu kinaja' zeemerh tace ke kk ja balleni" tace haqqun zan cenki karfe". nan zeemerh tahau wanka tana fitowa ta sa riga da skirt' da mayafi' tana fita ta dagowa didin'ta hannu. tana fita tai hanyar waje tana sanda tana fita se gidansu' salma daman a waje taganta tana zance" ta karaso tace aminiyas ya akayi tace k klau' daman' saurayin salma da abokinsa yazo' abokin yaga zeemerh yace yana santa.' aikam nan tafara masa yanga da iyayi wai' ita alalle*YAMMATA* tacemai" bae dan allah shawarma da ice cream nakeso yace suje su' sha haka' salma tashiga itada saurayinta sukaje suka sha ice cream". basu tashi dawowaba  se 10tana shigowa tama didi flashing didi' nagani ta tashi taje ta bude' haka suka shigo kamar munafukai. Suna shiga daki didi tace ke' ina kayana nan ta dire mata tsarabarar' ta dunga sa mata albarka . Har suka kwanta' da safe kuwa tana tashi' instead tayi shara tayi mopping tayi karyan wai kanta na mata ciwo' fiddausee" tace sannu sis bara ni zanyi aikin zeemerh aranta  tace o'ni yarinya haka bata wayeba' mshcww! aikin banza' chan taje kitchen ta dauko breakfast din' da mama da firdausi suka hada ta kawowa didi.' tace didi's ga naki didi' tace kai jama'ar kullum ace mutum nashan abu daya nikam naga takai'na da tsufana banji dadi' zeemerh ta tsaya tana kallan kakarta ta" cikin so da kauna tace didi' allah barmin ke tace yan'nan allah baze barniba'.. daga tsakar gida sukaji muryar mama tana zeemerh dan allah zoki huran wuta'. Zeermeh tace nashiga uku' nikam mama batasan banda lafiya ba. kuma ni gaskia bansaba da wannan hura' wutar ba.' didi tace k kwanta abinki banni da amina.' Didi ta fita tace kai jama'ah amina bikiga yadda jikin yarinyar nan yakeba duk kinbi kin addabi mutane' .ki fito fili kice ladidi fito ki huran wuta.' Nibansan me zeemerh ta tare miki ba wlh'. wannan takura haka .' mama she is totally speechless tace didi dan allah kiyi hkr dan allah tace wlh inde' kika kara takurama zeemerh sekin gane bakida wayo' aikin kawai' mama. takasa mgn didi nashiga daki zeemerh ta taso da gudu ta rugumeta woooo kakus' allah 'barmin k.' tace didi anjima zanje inkai kudin anko didi ' tace kai jikalle amma yaushe zaki kai dinkinki' tace ai jibi nake sa rai' didi tace allah kaimu ammafa kada amiki kaya manya' kinganki bakida kiba kinjini ko' zeemerh tace wlh didi se ahankali' se kace kin manta wace ni' kinsan kayana ko tar shekara 11 zata iya sawa shiyasa' wani lokacin firdausee take samin kayana.......```.                                                                                                                                                                      ©*biebie dee*                                                                                            07039732859.                                                                                                                      ©*samrah*.                                                                                      09062056022

💓*YAN'MATAN ZAMANI*💓

                  NA

Biebie dee bukharii da

Samrah


1⃣6⃣_2⃣0⃣






  Tana Isa gdansu salman batare da bata lokaciba suka nifi gdansu deeja,deejan tayi farinci da ganin kawayan Nata ,zanasukayi sukafara hiransu batare da tunan zuwa gaida ummien deejan ba ita kuma deejan bata nuna tatamu ba sukaita hiransu.


Zuwa Chan deeja takira idris dan yazo ya ansa dinki nasu dan tamashi bayani tituni.


Ba'ajima sosai dagama wayan nasuba sai gashi yakira yake shaidamata gashi a wajee,saida suka tafa sukai shewa sanan suka fita suka sameshi bayan su gaisane deeja tace kasan dai irin dikin da zakamana murmushi yayi dejan tacigaba da cewa fitinanan diki zakayi Wanda duk cikin yan ~yanmatan~bamai irinshi Wanda xamu haska yafitoh da mu idris yayi dariya yace indai wananne karkudamu sallama su seemrh sukamai suka shige yayinda sukabar deeja da shi anan.



Ba jimawa sai gata tashigo salma ta dubeta tace badai harkungama tadinba,sai da deeja ta harareta tace mai Zan tsaya nayi toh ba dai dinki bane kuma munbayar ai shikenan ai koko so kike na tsaya yan layinan suta kallona daria sukasa xeemarh da salma sukace tsokanane ai zama tayi sukayta hiransu sai wajajan shida na yamma suka bar gdansu deejan ko wanansu tayi gdansu.


Zeemarh ta shigo gdan nasu da sanda kamar yanda tasaba side din didi zatayi sai ganin  mama tayi mama tace kekuma daka ina zeemarh tayi shuru takasa cewa komai dan duk rashin jinta tana tsoron iyayannata,mama ce ta matso kusa da ita hanunta takama suka nufi daki tin kafin sukai mama keta fada ta Inda takeshiga ba tanan take fita ba haka tayta Mata fada bar suka Isa dakin,didi ne taijii kaman Ana fada shine tafito ko ta tafito side din mama tayi ganin maman tayi sai fadan takeyi didi takalleta kekuma kedawa,mama tace waye kuwa banda yariyanan azeemah tarai nani a gidanan bata jin maganata Sam didi tace ni har yanzo baki fadamin abinda tayi ba kinata min jawabin da ba ganewa nakeyi bah.


Mama tace islamiyya nace tatafi shine tasa hijabin islamiyan tayo daminki wai ta manta da siran ta a dakinki bankuma ganinta ba sai yanzo,toh wlhy na gajii bababsu zanfadama wa.


Tin da mama ta Fara magana didi batace komai ba sai yanxo cewa tayi ai saiki ta fadan kuma shi inyatashi daukan matakin shi Abubakar din ya kashetaa aikin banza kawai 


Xuwa tayi tajaa hanan zeemarhn sukayi dakinta

Suna shiga zeemarh ta rugume ta tanacewa nagode. Sosai didina Allah yabarmu tare didi tace ni dalla dagani zeemarh tayi murmushi tace wlhy ina sanki didi tace nima inasanki sosai azeema,zeemarh tabata face tace ni karkikuma cemin azeema saikace yar daaa didi tayi murmushi tace nadena yar albarka.


Ahmad ney yayi sallama dakin didi bayan sun ansa yanema waje ya zauna ya gaida didi,didi ta ansa tana murmushi,haka sukaita hira har sai da sukaji kiran sallahn magrib suka tashi dan gabatar da sallah shikuma ahmad yayi masallaci.koda yadawo dakin didin yadawo bayan ya zauna zeemarh ta kalleshi tace nifa wunwa nakejii yaya sai da ya kalleta da kyau yace mekikesan cii saida ta juya idanu sanan tace shawarma da  suyan 111 yayi murmushi yace bakin kanwata da San dadi jita kaman suya murmushi tayi tace eh mana,waye baisan dadi didi tayi charaf tace babu wlhy yace shikenan innafita sallan isha Zan wuce dakanan zeemarh ta marairaice fuska kaman zatayi kuka tace yaya please zanje yace ba saikinyi kuka ba shikenan ki shirya kafin nadawo daka masjid.


Didi tace kanwanka kasani ko nifa mai zaka siyomin yayi murmushi yace duk abinda kikeso kakus dariya sukasa duka.


A bangaran mama kuwa wanan hali na uwar mijin ta na damunta ace Mata batasan gaskia Sam,amma dai zata tayasu da addua Allah ya shiryesu yakuma ganan dasu dan taga lamarin yariyantata da kakarta na da munta kuma yana bata mamaki( *nidai nace Allah kyw ta*) tashi mama tayi dan bata so tata tunani dakin su tashiga,ta shiga da sallama Firdausee tagani kan sallaya tana karatun Qur'ani  zamun waje tayi ta zauna bayan Firdausee ta kar aya tajuwo da fara'anta tace mama kinji ni shiru wlhy ina dan karatune mama tayi murmushi tace ba komai Allah bada lada Firdausee taca amin mamanmu wai ina sis tanda nadawo islamiyya ban ganta ba mama ta tabe baki tace kinsan yayar taki sai addua tana dakin didi Firdausee tace Bari na idar da sallah naje aiyi hiran da ni.


Yana dawowa yatadda zeemarh a bakin kofanshi har tashiya tana jiranshi saida ya kalleta yace minti 1 ina zuwa bajimawa yafitoh, bagaran mama yayi dan Mata sallama zeemarh ko tsayawa tayi bakin kofa dan ita wai batasan jaraban maman.sun fitoh tare da Firdausee, Firdauseen ne tamatsa kusa da zeemarh tana cewa I miss you sisi zeemarh tayi murmushi tace I miss you too sis kije kijirani dakin didi zamudan fita da yaya ahmad Firdausee tace no pee adawo lfya...

tace allah yasa'. nan ahmad ya karaso gurin zeemerh yace sis muje ?. tace muje toh nan suka fita.  suna fita yadauko motanshi dayake waje. yace muje tabude gidan gaba ta shuga tareda gir-gizanta. suna shiga tace yaya kasamin waka mana da AC . yace toh yanda kikeso haka zanyi'. suna tafiya tanabin wakan don ita duk wakar daya shigo ta iyashi'. har suka iso wani restaurant'. suna zuwa tace kai brother daga ganin gunnan za'ayi chilled. shide Ahmad murmushi yayi. Suka fito daga motan suna fita tafara taku dai dai'. irin na yayan manya har suka fito gun zamansu. suka zauna suna zama tafara kallon yanda kowa yake zuwa da fiancee insa. aranta tace kai inama nima inada hot booty. chan yace zeemerh nan tayi fir ta dawo daga duniyar tunaninta tace. emm yace me kike tunani tace bakomai yace akawo miki me dame. tace burger hot pizza da shawarma . ba tareda musuba yace drink fa? tace exotic tace toh. nan ya tashi yaje ya hado mata                                                                                                      "yana zuwa yace kin gaji ko tace habade ban gajiba'. Yayi murmushi suka fara cin abinsu. kamar ance daga kanki tana daga ido taga wani guy. shida budurwarsa sunzo. sunnata chilling sukazo dede gun ice cream taga sun siya . tareda siyan kayanci iri iri suka samuguri suka zauna. kusada desk nasu guy in yakecewa fiancee nasa'. baby nayi feeding naso zeemerh kam se kallonsu take totally speecless. haka harsun wuce tana kallonsu. can daya lura da haka ahmad yace zeemerh me kike kallo? nan tayi tsaki mchsw  nan tafara kora masa bayani. yace kai kanwata yanzu menene tace kaga ni wlh sun burgeni wlh. gashi daga ganinsu yan gayune'. yace kema ai yar' gayu ce tace bazaka ganeba. nan yace muzo mu tafi dare nayi tace toh. bangaren didi kuwa ita da firdausee se hira suketa yi.  inda firdausee take gayawa didi saura izu 20 haddarta ya hadu. didi tace masha allah haka akeso .chan didi tace yawwa firdausee zakiji bikin kawarsu zeemerh da za'ayi na *YAR' GATANNAN* firdausee tace didi biki fa kikace ni wlh banda lokacin biki. ba gwara nazauna ina tilawa naba. didi ta bude baki tace kuttisi lalle firdausee nidan allah yaushe zaki waye.                                                                                                              "tace ga zeemerh kullum tauraruwarta se haskawa take amma yarinya ance kanki a buhu. toh wlh ki gyara nide nagaya miki. se kace ba jinina a jikinki toh kigyara. itade firdausee ta kasama magana kasa' kasa tace dan allah  kiyi hakuri. kafin didi tace wani abu taji kamar karar horn in mota. a sukwane ta tashi tana cewa firdausee sun dawo fa. aikam tana rufe baki sega zeemerh tazo tana ran gwada tace hi didi's didi tace oho miki ya hanyar kice kinci dadi. tace sosai ma. daga gefe taga firdausee ta zuba mata ido'. zeemerh tace babe how far'. didi tayi caraf tace wlh yarinyarnan nada matsala. ta kwashe labarin hirar da sukayi ta bata. zeemerh tahau dariya tace wlh kema bakinki be gajia. wannan yarinyar nan ce zatazo bikin zee lallema. salan guys in gun su rainani. suka kwashe da dariya se didi tace ke ina tsarabana. tace ni kaza zan iya mantawa dakene nanta mika mata yogurt da meat pie. ta karba hadda godiya ta ciire ice cream dayaa ta mikama firddausee tana ansa.  tace nagode.....







© ~biebie dee~

07039732859

© ~samrah~

09062056022

*💓YAN'MATAN ZAMANI.💓*                                                                                         NA.                                                                                                                      biebie dee bukharii 

da

Samrah


*edited by*hajja ce ❤



*this page is for you Rabiatu Sk msh thank you so much for  d du'a we really appreciate*



2⃣1⃣ _  2⃣5⃣     



                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                       "haka rayuwa ta cigaba da kasan cewa kullum"

   'zeemerh tana abinda take so, in ance za'ayi mata fad'a didi tayi kyamas ta hana.                                                                                       

   'Rana bata kar'ya, saidai uwar diya taji kunya, ana saura k'wana hudu afara bik'in zee, don haka tun ran talata suka fara shirye shirye. 

   Kasan cewar a ran talatan deejah tak'ira idris akan ya kawo mata kayan nan haka daya kawo mata ta yabi kayan sosai saboda d'inki yayi matukar kyau sosai.  

   tace kai idris nagode allah ya biya zanga shegiyar da zatayi dink'in dayafi namu!" nan ta cewa mamanta mom please zanje gidansu zeemerh yanxu. mom tace adawo lafiya sbd mom irin matan nanne da basa takurama yaronsu.


    "tana fita tak'ira salmah" hello babe salma tace' how far?" deejah tace ke d'inki ya iso, da karfi tace dan allah kice yayi kyau, deejah "tace ink'in zo kin gani" kizo gidan su zeemerh ina chan. tace toh ai ko gaba da china  kike je zanzo".   

                                                                                                                                                                                              __"tana kashe layin tacewa umma zan fita. umma tace salamatu sai ina?" tace umma angama mana d'inkin mu wlh' irin d'inkin ya'yan 'manya biki ga dink'in ba, wlh kuma kyauta fa.umma tace dan girman allah ke dan allah.

   salmah tace au biki yadda ba?" tace a'a na yadda"!. tace kinga umma bara naje nagani kada suyi bani'. haka itama ta kwashi kafa ta tafi.    

                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                "koda deejah ta isa, gidan su zeemerh tayi sallama direct part in didi ta wuce" saboda zeemerh ta sabama kawayenta da zuwa part na didi, tana shiga ta ganta akan gado tana shan wankan, da gudu ta taso tana my deejar o'yoyo' tace ke dallah kada ki karyani d'in kunanmu aka kawo mana zeemarh' ta daka tsalle tace kai bestie kice zamu fice! da wankanmu' suka tafa tareda dariya".

    chan didi ta shigo deejar tace didin'mu ya kike?" tace yam'mata adon gari' ya k'inzo klau"? tace wlh lafiya lau, didi tace madallah se chan zeemerh tace wai' ke ina yar iskancan shiru. kaf'in tayi shiru sega salmah tayi sallama'                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                       

  "yeeeh babe mun gaji da jira" tace eyyah wlh a'a baza ku gane ba. saboda wallahi ina' tafiya ina gudu" don kawai nazo ayi dani'. nan suka tuntsire da dariya" suka hau gwada kayansu ko' kunyar didi basujiba". nan didi tahau fasa musu kai" kai

    *YAM'MATA* in baku babu gari!!! tace kai zeemerh duk ke aka cuta, bayan bangan shi kamar nasuba, "yama kuke cemai hipt" ko nan suka kwashe da dariya sukace allah bar mana ke didin'mu.

   "haka dai sukai ta hiransu da iya shegen su,su salma bazu bar gidan su zeemarh ba sai bayan sallan magrib.


A bangaran mama kuwa ba abinda ke shiga tsakaninta da zeemarh sai gaisuwa ita ko zeemarh hakan yamata dadi dan acewanta duk cikin friends  d'inta anfi samata ido. 


Mama kulin tana b'inta da addua dan taga kwana biyunan kanta Kara rawa ya keyi, kamar kulin yau ma zeemarh tace ta shigo dak'in mama da sallah Dame da gaisuwa Bata t'saya jin ko maman ta ansa ba tayi hanyan dakinsu mamace ta da katar da ita da dawowa tayi ta zauna mama ta kalleta da kyau tace ke a ganinki abubuwan da kikeyi kin kyau ta kenan yaushe rabon ki da islamiyyah ita dai zeemarh tayi shuru dan jikinta yayi sanyi mama nacikin mata nasihane baba ya shigo bayan duk sunmai sunnu da zuwa ya ansa yaneme waje ya zauna sanan ya kalle zeemarh yace naji duk abinda mamanku ke cewa kuma zanyi maganin abun nan ba da dadewaba didi ce ta shigo Baku sallah cewa take matakin kenan kace zakamata aure ko toh wlhy karma kafara shi Ahmad yaushe yafara aikin da har zai riketa Sam ba Zan yadda ba kaji nafada maka in bakin Ku bazai fada alkharee ba yai shuru kuma daka yau azeema tadawo hannuna da zama kar naji kar nagani zuwa tayi ta daga zeemarh sukai gaba shiko baba tinda didi tafara magana salati kawai yakeyi yarasa wace kalan U'wa Allah ya bashi marasan gskia mama tace hakuri zamucigaba da musu Allah ya shiryar da su.



ASALIN LABARI....


© ~biebie dee~

07039732859

© ~samrah~

09062056022

 


_Please ina rokon kusani a ddu'a ina fama da ciwan kai_


       *Biebie Dee*_thanks_

3/29/2017 2:49:18 PM: Biebiedee: 💓*YAN'MATAN ZAMANI*💓

             NA 

biebie Dee bukharii Da 

Samrah 

*mungode sosai da gudumawar da kuke bamu Anty aina'u (ummu_abdulnaseer)& Anty hajja ce  Allah saka da alhkharii ya kuma shiryamaku zuri'a Ameen*



2⃣6⃣_3⃣0⃣

   



Mal.Musa da hadiza Wanda akafisani da ladidi  sune iyayensu yan asalin garin katsina ne a karamar hukumar Mani.su biyune wajen iyayan nasu abubakar shine babba sanan Aminu mal.Musa bawani karfine dashiba yanade da rufin asiri.ladidi mace ce mai fada da shegen San abin duniya gata bata San gskia ko kadan.tinda tai haife Abubakar da aminu Allah bai kuma bata haihuwaba.


Yaran suntashi cikin tarbiyya da girmama na gaba dasu dakuma sanin yakamata,sun samu ilimin addini mai yawa dan ko wanansu tun yana shekara shahudu yayi saukan Qur'ani mai girma,aban garan boko kuwa secondary kawai sukayi suka Fara kasuwanci,cikin ikon allah suka samu budi da daukaka har  yakasance suke komai na gida.


Abubakar Nada shekara 25 yayi aure Inda ya aura Amina makotan juna ne akwai Kyakyawan mu amula a tsakaninsu.suna zaune lfya sunyi aure da wata shida Allah yama mal.Musa rasuwa rasuwan ya shigesu matuka 


Tin da mal.malan Musa ya rasu suka fara kasuwancin zuwa gari gari Inda Abubakar yazo Kaduna ya hadu da uban gida na gari mai kirkin gske hakade suketa samun budi da daukaka har allah yaba Abubakar gidan kanshi sai suka dawo Kaduna da zama.


Ganin rikon  gskia da manan Abubakar da dan uwanshi aminu yasa alhaji Sulaiman yabama aminu auran yarshi murjanatu suyi farin cikin da hakan dan ko wanansu yasan halin girma da mutinci.


Su aminu sunyi aure da sheka 1 Allah ya azurtasu da samun Dana miji Wanda yaci suna Ahmad a lokacin shekaran abubakar 6 da aure Allah baibasu haihuwa ba lokacinda ahmad yayi shekara daya dai dai aminu yanke shawaran bamu Abubakar shi murjanatu tabashi goyan baya Dari bisa Dari didi ma taji dadi susai.


Rananda aminu yabama dan U'wa nashi da Abubakar ba karamin dadi yaji ba hakama amina dan ko bakomai tayi Bari Bari hakadai komai keta tafiya cin rufin asiri da kuma temakon Allah.


Sunan didi yasamu asaline tin wata Rana da yan Mani sukazo Kaduna yaji suna tacewa ladidi sheken shi yakama didi.


Ahmad nada shekara 3 murjanatu ta sake hai huwa inda takuma samun da na miji yaci sunan mal.Musa suke kiranshi da daddy.a lokaci shekaran su mama Amina 9 da aure, sai asanan itama tasamu ciki sunyi farin ciki matuka sunkuma godema Allah,haka mama taita raynan cikinta har ya isa haihuwa,da temakon Allah ta haihu inda tasamu yan biyu dukka maza zokuga farin ciki a wajen su, ranan suna yara sukaci sunan Hassan da husssai.kusan a tare suka haihu da mama murjanatu dan sati uku ne tsakani itama nasamu na miji yaci suna Yusuf.


Yan biyu Nada shekara 2 mama tamuma samun ciki ananne ta haifi yarta mace San kowa kin Wanda ya rasa tinda didi ta daura ido a kanta taji ta masifar San ta da kaunanta da akazo sa suna ma didi ce ta zaba AZEEMAH.azemarh ta tashi ciki gata kowa santa yake barin ma Ahmad da didi jisuke kaman tasuce su kadai, ahmad nasan azeemarh sosai dan shine yake kiranta da zeemarh.tanada shekara 1 mama murjanatu ta haifi firdausee tinda baba yaga irin San da ahmad kema azeemah yakudura a ranshi sai ya aura mai ita ko da didi taji shawaran dan Nata tayi na'am da shii.


Yanxo haka Ahmad yama Karatunshi yana aiki a breach na MTN Musa(daddy) yana 300lvl a ABU Zaria su yan biyu da Yusuf suna 100lvl sai ita zeemaeh ss3 Firdausee ss2.


Salma kuwa ita kadai ce wajen iyayanta babanta dan Kano ne Ummie kuma yar zaria tayi haife2 da yawa amma duk ba sa tsayawa sai akan salma shiyasa ta daiki San duniya ta dauramata.  tin  tanada shekara 10 Allah yama babanta rasuwa dagin baban ta bayanda basuyi ba dan su anceta sutafi da ita Kano firr Ummie taki basu ita dan Ummie irin matanane marasa kirki ga shegen San raran masifa,shiyasa salma ke abinda tagadama Ummie bata Mata fada Sam.kawancensu tunsuna yara dan ma nisa sukeda shiba duk unguwa days suke,ko wanansu sunada kufin asiri kumai anamai komai dai dai yanda yakamata amma suu *yanmatan* basa gani gani suke ba a masu komai...


BACK 2 STORY...                                                                                                                                                      "suna shiga' daki. didi tace o' ni ladidi naga takaina". ace mutane se kace haihuwar syria, renon damo". ni wlh abun har mamaki yake bani yadda'. suke sa miki ido dayawa agidan nan'. zeemerh cikin ko in kula tace". wallahi kikace zakibi nasu zasu kasheki kwananki be kareba'. tace walllahi didi kinsan me! didi tace a'a sekin fada.. tace wallahi so nake in auri attajirin namiji' wanda ya gaji da kudi'. kuma ya gaji da haduwa'.                                                                                                                      "didi tace allah zeermerh' Saboda so nake ki huta kiji dadi kizama'. *YAR GATA* hutu ya nuna ajikinki'. didi yasa wani ihu irin nayan '. . kai diwiɗi' _lols wai sweety_'. zeemerh ta kyalkyala wani uwar dariya tace wayaga diwidi. "haka sukasha hiransu har dare yafarayi'. sunzo kwanciya' didi" tace ita allankatafir'.  yau kwadayi takeji kuma gaskia in bataciba da matsala'. zeemerh tace nikam didi' so kike ki kasheni'. kinsan kuwa da yaya nake samu yan' iskancan suke siyamin snacks innan". didi' tace zeemerh wallahi kwadayi nakeji' kuma ni wallahi kaza nakeson ci'. zeemerh ta dafe kirkirji' tace ashe zaki mutu". tace in kingama rigimar taki nadawo bara naje dakin firdausee nayi chat dina'. kamar an mintsineta tace kut'. *dana tafka babban kuskure*. don wallahi ba tantama baba ze karbemin wayana', nan ta dawo dakin tasa earphone a kunnne'. tanashan wakanta'. didi' har tagaji tayi bacci".                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                             "da safe kam as usually tana tashi'. tayi wanka tasa kayanta' . Tayi breakfast abinta ita' da didi'nta.  yau yakama laraba saura kwana 3 biki saboda' su zee yan bidi'a ne". event hudu ne. "traditional henna  bride' shower" party" dinner" se wedding fatiha wanda da yamma za'ayi mother's day".                                                                                                                  "tashirya tsaf abinta' takira salma ' kancewa gatanan zuw'. Salma tace toh se kinzo ina jiranki'. suna sallama da it'. tace didi kinga zanje gidansu salma daganan zamuje lalle da gyaran gashi'. Kusan 2k nakeso wallahi'. didi tace ina zuwa bara nakarbo miki'. zeemerh ta washe hakwara'. tace yawwa tawan ina jiranki'. tana fita tayi path in abba'. tana zuwa tace abubakari' sandan sikari'. dakaji kida se sikari'. ichan biyar kayi fure kayi ya'ya". shide yasan inde didi' tamai kirarin nan yasan kudi take nema'. yace didi ina kwana tana washe baki tace lafiya lau'. dan albarka'. tace dan allah bukar dubu uku nakeso'. yar kawata zatayi aure kuma wallahi tanamin abun arziki'. Shine nakeso nabata gudunmawa'. abbah yasan sarai ba haka take nufiba'. se yace toh didi yadda kikeso za'ayi miki. nan ya zaro 5k yabata'. yace ga wannan anyi kudin mota'. tana washe baki tace laaa anyi haka kuwa'. ta dungi samai albarka'. harta fito tana fita hadda tuntubenta ta karaso daki'. tace zeemerh ansamu fa'. zeemerh ta juya dara daran idonta' tace i love you so way much my heart beat'. didi tace oho miki nan ta zaro 3k tabata'. tace bara natafi nan didi tace tsaya kiji uwar zumudi'. wallahi inde aka miki lallan mara kyau sena ci ubanki kinjini ko' tace habaa didi in tamin mara kyau ai wallahi bazan bata sisinaba'. "didi tace yauwa yar' gari se kin dawo kinji zeemerh tace toh bye'                                                                                                                                                                                                                                                                      "nan takama hanya ta tafi". tana zuwa taga ummie na waje tana shara'. tana shigowa tace hi ummie". Ummie ta washe baki tafara mata kirari'. itakam se dadi takeji tana wani fari". chan tace ummie ina salma' Ummie tace wallahi' yanxu ta shiga wanka". tace kai wallahi tanada matsala' ita akomai nata setama mutane delay'."nan suka fara hira sosae abunsu'. tana bawa umma labari'. suna cikin' haka sega" salma ta fito' daga toilet'. tana ganinta tazo da gudu tace yar' halak harkin isu'. tace mushiga dan allah nan suka shiga daki'.....                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                      


© ~biebie dee~

07039732859


© ~samrah~

09062056022



  


_nagode sosai da addu'an Ku Allah saka da alkharee Alhamdulillahi naji sauki_ 

 

*Biebie Dee*

💓*YAN'MATAN ZAMANI*💓

                    NA

Biebie dee bukharee da 

Samrah



3⃣1⃣_3⃣5⃣







   Suna shiga daki batare da bata lokaciba salma tagama shirinta tsaf cikin pencil skirt baki da cape sai tayafa mayafi a saman kanta suyi kyw su dukka.samun Ummie sukayi a kitchen sukace toh bye dakatar dasu tayi game dacewa wasai kaikune sai da suka kalle juna sanan sukace muzamu Kai kanmu dan deeja tana jiranmu, Ummie tace duk uban gayunnan ai sai amaku dariya anga kunsa ko a napep wlhy gari tin wuri kukira wani ya kaiku a mutunce zaifi sallan juna suka karayi sanan sukace karkidamu munfasa zuwa a napep indai mundawo zamubaki labari sukayi ficewarsu salma ce tace nasan deeja har tagaji da jira kirata muji zeemarh tafitoh da wayanta kenan sai ka call din deejan yashigo batare dabata lokaciba ta dauka, zeemarh tace kifitoh titi gamunan.


Tin daka nesa suke aikama junansu murmushi, salma ne tace Kai babe wlh gown dinan ya cigeni zanzo musa labule dannima naje nayi yaki zeemarh tace waini bayyi kyw bane naji ba Wanda yacene sai da sukai daria sanan sukace aike ko bakiyi makeup kyw kike murmushi tayi najin dadi


Gyra tsayuwansu duk sukayi salma tace wlhy lift zamu tara dan bazamuje NNDC moll a napep ba deeja tace shege baby haka za ayi, sundan dade kafin wani nota kiran corola_s ta tsaya karasawa sukayi bude glass yayi salmace ta matso kallanta yayi yace *YANMATA*sai ina sai da tajuya ido sanan tace wafroad zamuje yace wajen ina tace NNDC moll Yace kushiga mana salma ce ta bude gaba tashiga yayenda zeemarh da deeja suka shiga baya batare da bata lokaciba suka fara tafiya.



Kallan salma yayi yace ya sunan sai da tayi murmushi sanan tace salma, daga ido yayi yana kanlan su zeemarh ta mirror din motan yace kuma suka fadamai yace nice names ni sunana Kabeer tahir ina aiki a UBA bank duk sukayi smiling sukace nice haka sukai ta hiransu kadan kadan har aka kawo.bayan yayi packing ne su zeemarh suka fita ya kalle salma yace please help with your number sai da ta juya ido sanan ta ansa wayan tasamai number din. Karasowa wajen kawayen nata tayi tana murmushi tace kuji min Kabeer dinan wai in mungama nakirashi yamai damu zeemarh ta harare ta tace yana hauka ai muna gamawa wani lift zamunema nasan hanyanan sai munsamu Wanda yafishi deeja tace wlhy karkiwani kirashi 



Suna nufar kofar tabude kanta suka shiga zeemarh tace wow dama mai wajenan ya aureni deja tace kindebo da zafi aini da zansamu mai kaikoni shopping wajenan sai ya raina kanshi salma tace sa a ranki har kinzo wlhy duk suka sa daria haka dai suka hau *lifter*din da zaikaisu second floor shagon saloon din tinkafin su shiga suka gyra mayafi da takun tafiyansu su a lole big girls *lol*suna shiga suka taddata nussy,billy,Amiera kaita,hawwee dadai wasu friends dinsu nan suka samu waje suka zauna bajimawa sai ga Farty tashigo nandukasu suka zauna sunata hira Farty da Amiera kaita sai snap sukeyi Ana posting.



Nandai akafara mawasu lalle wasu kuma gyran gashi su salma dai sai kanlan Amiera takeyi tana daukan picture lallan hawwee a phone dinta,a zuciyanta tace mama soon ko iPhone 5s ne wlhy.haka dai akaita lalle da saloon har kusan 2:30 chansai gawata budurwa tashigo bayan ta gaisa da ma'akatan wajen taje tasamu kawayen amaryan da mara'anta duk suka gaisa sanan tace ina fatan ba Wanda yabiya kudi sukace no tace yawwa bamuzata zakuzo dayawaba shiyasa bamufada ba kyautane ango yabiya ni cousin sis din zee ce sukace wow sanan tacigaba da cewa akwai wata mai lallen a gidama Inda mai soo 


Basubar NNDC ba sai after 3 gida ko wanansu zatayi dan dauko kaya dan da yanmanan za'a fara shagalin bikin.

"dayake kowacce. Lokacin da suka gama gwada dinkinsu' suka bawa deejah' ta tafi dashi' saboda sunaso su shirya achan gidansu' . Zeemerh tace didi kinga bara inzo inje gidansu deejah' achan zamu shirya". didi tace toh' yar albarka'. kai masha allah me lallan nan ta iya kunshi sosai' kai ɗiwiɗi da wankanki' har nagama hango irin kyaun da zakiyi' tace allah didi tace wallahi. tace bara kiga nikam na tafi' tana fita daman already salma na gidan'su deejer. tana zuwa tace dudes ya de' sukace wallahi kina bata mana lokaci kinsan zamu shirya muje. gidan makeup' kuma kinsan su amierah nachan ko' sukace please i don't want complain ' muyi abunda zamuyi please'.                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                          "nan suka dauko wani  gown pick  sai suka daura blue cape mai kyw sunyi kyw ba karya bawani heavy makeup sukayi ba acewansu sai gobe   wani uban high hll shoe's dukasa sunyi masifar kyau dukkansu deejar ta dauko samsung'  s6  edge'  data'aroshi wajen wani saurayinta tace hi guys look up'  nan tashiga daukansu selfie. wallahi yayi' Nan ko wacce tadauki black veil suka yafa a saman kansu   suka fito' suna fitowa sukaga ummie' in deejer sukace ummiezamutafi  gun bridalshower tace okay' come back safe' nan deejer ta  dawo tace' ummie please i need some cash' ummie tace bakya gajia wallahi nan ta zaro 3k tace here you go' ta kuma ciro 3k tabata tace kibawa friends inki' tace wow ummie nagode sosai' tareda hug inta'. dayake mijin zee yanada kudi sosai' haka yabada 100k na friends nata amusu make'up'.  cause su goma za ay'wa' nussy'billy'amiera kaita'hawwe' khady'farty'ayusher'salma'deejer'zeemerh'. ita kuma nata *JOEY'S GALLERIA*joey kawai zatama bridal in 350k na four day's.suna fita deeja takira wani saurayinta tace munfitoh anashi side yace muhadu a titi  haka suka karaso titin ba jumawa sai gashi ya karaso nan suka dau hanya bayan sungaisa dasu zeemarh.basu tsaya a ko ina ba sai malali GRA  a wani katafaran gida yayi parking,bayanso salma sunfita ya kalle deeja yace baby wani time zandawo saida tawani bata face tace karkadamu duk yanda ake ciki i'll let u kwn yace oky sukai sallama yajaa mota yatafi karasawa wajensu salma tayi suka shiga gidan,suna shiga su side din zee sukayi nan suka taddasu hawwee, nussy nan sukafara shewa Ana kashe salfie zeemarh ce tayi magana tace ina amaryan ne Amiera tace suna side din mommy Ana makeup muma ga missmienarh chain tanama su Farty dan itace zatama friends and relatives salma tace nice 1 damage inasan makeup dinta deeja tace ta iya ai suna cikin hiranne wanan buddurwa dasuka hadu wajen saloon tashigo da fara'arta tace OMG babies kunyi kyw wlhy suka washe baki suna thank you Chan tace kuyi hakuri dan allah anfasa using gown n cape yanxo pincil skirt ne ko trouser pick sai Riga blue Amiera kaita tace no pee nawa Zamu bada yanzo yayinda su slma ciki yayuya dan bawani enough money a hannusu ba amira tace baby talk sai da tayi smiling sanan tace you can call me haneefa, amira tace oky nice haneefan tace karkudamu kyuta ne da angama ma mun makeup sai yazo side din mommy ya ansa man su salma akawani basar wai oky( lol )  


Saiwajen 5:30 akafara evant din amarya zee tayi mafincikin ganin friends Nata,zee tayi kyw sosai joey tafitoh da ita ba karya wani shegen gown tasa white color har qasa sai head baby pink sarkanta da abin hannunta duk babypick ne sai wani uwan hill data hau ni wani Abu tadaura kan gown din an rubuta *bride to be* ajiki amarya zee tayi kyw har baza iya fadaba haka friends dinta da cousins nata mssmienarh tafitoh dasu waje yasha decorations yayi kyw shima pink and white nan akaita cin snacks da drinks... Bla. bla.bla ga music na tashi wakokin su wizkid,devido,tecto dai depphotos sai kashe pictures shima yakeyi sauransu su zeemarh sai kashe pictures akeyi kowa sai shagalinshi yakeyi hakade akaita bidiri har wajen 8:30 shima sanarwa akayi ina mai tafiya ga motoci ango ya aiko nan fa su zeemarh,salma,deeja nussy,hawwe suma amarya salma da sauran friends naso dandai su ba drive ne dasuba.


Suna barin wajen taron nussy tace kowa yashiga mota shidaya bikine na manyaa muma bamusan Wanda zamu chafko ba nan duk sukayi daria suka fitoh suna ma juma sallama sai sun hadu wajen kamu.

Waccansu mota daya tashiga wai kosuma zasu danko mai cash(Lol) haka kowani abokin angon yakaisu gida da sallaman sai sunhadu gobe...








© ~biebie dee~

07039732859

© ~samrah~

09062056022

💓*YAN'MATAN ZAMANI*💓

                     NA

Biebie dee bukharee da 

Samrah




3⃣6⃣_4⃣0⃣


Zeemarh na shiga  ko cire takanmi batayi sai zubewa datayi kan gadon didi tana wani shegen murmushi didi ta kalleta tace lafiyanki kuwa kishigo ba ko sallama bare sannu da gida zeemarh tace baza kigane ba didi tace gidanku dabazan ganeba daria zeemarh tayi sanan tace mai da wukar, saida tacire takalminta ta jawo kayanda tashigo dashi tashiga firfitoh dashi kallan didi tayi tace kiga Inda akee biki murmushi tayi sanan ta cigaba dabama didi labari komai didi sai washe baki takeyi snacks dinda zeemarh tazo dashi suka baza a plat sunaci ragowan zeemarh tace zataba Firdausee. Saida sukagama hiransu wajen 10pm san zeemarh ta tashi tashiga toilet tayi wanka gami da alwala, bayan tasa rigan baccinta sanan tajewo hijab din didi tashiga sallahn da ke kanta, tana idarwa ta kwanta gami da tunanin yanda gobe zai kasance.


Abangan deeja da salma ma hakance ta kasance, Ummie salma tinda taga kayanda salma tazo dashi tace kyw ta akabasu banda da snacks  da dai sauran abubuwanda akara ba ta rude sai addua take yi kema Allah hadaki da Wanda ya fina zee salma ta ce amiin ummie.itako Ummien deeja irin I don't care dinnance tadai cemata kar ta debu Mata fakara'u allallalurati haka kowa ya kwanta da cin burin gobe.





Tinda sassafe zeemarh ta tashi wanka tayi tashirya cikin wani red material fited gown dinkin yayi kyw sosai ya zauna acjikjnta das, dakin mama tanufa dan gaisheta tashiga da sallama neman waje tayi ta zauna sanan nafara gaisheta mama ta ansa ba yabo ba fallah,zeemarh ce tace ina Firdausee sai da mama ta kalleta da kyw tace yau Friday tatafi sch ke kibar zuwa ai zeemarh tace aa mama ba a komai sosaine kuma kinsan mune zamuyi waec mama tatabe baki tace da kyw ai saida zeemarh ta gyra zama sanan tace mama dama bikin Zainab ne yazo yau *kamu* gobe daurin aure da dinner sbine nazo nafadamaki kiroqi baba na kwana, harara mai lafiya mama ta sakar Mata tace bakida hankali gara kitashi kibar wajenan tinkafin babanku aminu yaji dan babanki ma nasan shi hadda duka zai hadamaki tashi tayi tafita ta na kuka, Karo taji tayi da mutin tana daga ido taga Ahmad tanbayanta yashiga yi mai yafaru banza dashitayi tawuce side mama murja yayinda Ahmad yashiga dakin mama, bayan ya gaisheta ta ansa cikin fara'a yake tanbayanta mai yasama zeemarh nan tafadamai koshi bai Goya bayan tajee ba yarasa mai ke damun zeemarh.



Tana shiga dakin mama marjan sautin kukanta ta Kara jin kaman kukane yasa mama murja fitowa daka bedroom ganin zeemarh tayi sai kuka takeyi tanbayantayi cikin muryankuka ta fadamata kalleta tayi da kyw sanan tace gara kiyi shuru tinkafin banku ya fitoh yaji wanan magana dankinsan ba karamin aikinshi bane yahanaki zuwa bikin gaba daya ko ai zeemarh tinda taji mama marjan tafara magana tashare idanunta tafida binda mama murjan tayi da kallo zeemarh duk ta chanza  halinta tasama wata iri wani lokacin intana abuukamar yar masu kudi ko yaran FGC dinne suka chanzata oho.



Dakin didi tashiga tanacewa duk sunki yanda didi tace ai nafadamaki kee nima basan kwananan nakeba hararanta zeemarh tayi sanan tafara cin idomie dinta.sai wajan 11 tafitoh dakin mama tayi tamata sallama batare da ta ansa ba tace karki Kai dare toh kawai tace anranta tana cewa sai kungani ai kawai,dataje dakin mama murjama haka tacemata akula da kyau kar akai dare haka tafita gdan tana gananan maganganu Wanda bamusan metakecewa ba.


Awaje ta ganshi Kai tadaga sama irin ita bata ganshiba murmushi yayi ya karasa Inda take yace shiga na kaiki sai da ta turo baki gaba tace gdansu salma zani dakachn zamutafi yace no pee shiga mujee.


Tana shiga tafa kwallamata Kira amaimakon salma tafitoh sai ummiece ta fitoh tana washe baki Kai yar tawa tahadu murmushi tayi kadan tace ina salma wai Ummie tace tana ciki muje.suna shiga taga salma ko shiryawa ma batayi ba zamatayi bakin gado batare datace komai ba salma ta kalleta tace yane Saki tajaa sanan tafara ba salma da Ummie labari salma tace yan gdanku Nada Marsala ummie tace dan ubanki da kina Kano kema ai dasai kinfita matsalan doguwan Riga tasa sai veil a saman kanta Ummie tace ni bangane ba bazakusa ankon bane wai shikin kosawa salma tace toh ba sai 4 za afaraba jan hannun zeemarh tayi tace muje dallah Ummie tace adawo lfya. Kodasukafita saida akabiya aka dauko deeja sanan suka nufa malalin gdan bikin.yau zeemarh ce ta ara phone din Ahmad bayan ya saukeso iPhone6 ce, suna shiga gidan Inda a kaba kawayan anarya suka nufa basu tadda yan group dinsu ba yawancin mutanandake wajen cousins din Zainab ne sai yan scienceB class mate dinsu haka dai akaita hira da ciye2 daukan pictures su zeemarh har anyi kawaye cikin cousins din Zainab sunyi sallan badadewa 1:30 missmienarh tazo dan farama friends n relatives makeup amaryama suna side mommy anfara Mata hakadai friends keta zuwa anata makeup sai wajen 4:30 bayan suyi sallah sanan akafara shirin tafiya wajen *kamu*Inda za ayi a *ceremonial canopies* dake Kaduna. Zeemarh tayi kyau cikin ankonta dikin yayi ba karya *yanmatan* sai yaba dinkin suke hadda amira kaita salma matayi kyw haka Deejaa kowama yayi kyau haka aka shiga daukan pictures Inda zakuga su zeemarh a pictures dinan karyane kuce suma bayan ran masu kudin bane.5:00 suka isa wajen sai da suka jira isowan amarya da ango,amarya Zainab tayi kyau ba dan kadan ba,haka suka shiga hall din Wanda yasha decorations.


Zama amarya da ango sukayi sanan friends suka sauna a kasa Inda suka bada ma'ana sosai hakadai akai ta shagali ga abincinan sai Wanda kakeso zakaci dipphotos sai kashe hutuna yakeyi sai ana gab dagama event din friends din ango sukazo nanfa aka shiga liki zeemarh,deeja,salma dasauransu naganin haka suka fada fagen rawan kaman ita yake jira nan yashiga Mata liki Ana haka phone din hanunta yakawo haske alamun Ana kiranta fitatayi a fagen rawan tayi wajee...








© ~biebie Dee~

07039732859


© ~samrah~

09062056022

💓YAN'MATAN ZAMANI💓

               NA

Biebie Dee Bukhari da 

Samrah



4⃣1⃣_4⃣5⃣




     Fita shima yayi koda yafitoh baiganta ba sai waige2 yakeyi.itako tana fita da dauki wayan mama ce ki cewa hala kwana zakiyi cemata yayi wai sina hanyan dawowa,tana gama wayan da mama kashe phone din tayi gaba daya wai kar adameta yaune kawai takeda guarantee dan tasan gobe ba barinta zuwa dinner zasuyi ba. Yanyan da zata maida ta hall din tayi har ta wuceshi yayi figir yasa gabanta ta goce yakuma shan gabanta cikin muryan iyayi tace lfiya cwayi baby kniyi kyau kinganni kaman baki ganeniba kinyi banxa bakinsan tin jiya naketa nunaninki ba tsayawa kawai tayi tana kanlanshi takasa cemai komai a wani bangaran kuma mamaki takeyi kamar wanan wai yana tunanunta tsayuwanta ta gyra sanan tace mai zancema toh saida yiyi murmushi sanan yace am *suraj*U saida ta juya idanu tace u can call me *zeemarh* uace wow nice name suna tsaye sai ga salma tafitoh ita da wani karasowa Inda suke su salman sukayi *suraj* yana smiling yacema *annur*meet my baby *annur* yayi smiling yace nice 2 meet u *zeemarh* tace nice 2 meet u too tanbayansu sukayin ko yanxo xasu tafi gida *salma* tace yes komawa ciki sukayi Inda sukama amarya da friends dinsu sallah nan zeemarh ke koroma su nussy, deeja, hawwee bayani daria sukayi deeja tace kuje kawai muma sai munyi duk yanda akeciki zamuyi chat haka suka fitoh da uban jaka a hanayensu Wanda akabasu na biki kayane a ciki dam.



Babu bata lokaci kowa yashiga Motan saurayishi sai gida 8:30 suka karaso gdan exchanging number sukayi sanan suka rabu. Haka *zeemarh tashiga gida dakin didi tanufa direct anan ta tadda su mama da mama murja, Firdausee na duba wani littafi da sallama ta karasa duk sukace sai yanzo banda didi nan zeemarh tashiga jero karya da ratse2 mamatace Allah shirya tana shiga ta ajee kayan hannunta tafada toilet wanka tayi da alwala rigan banci tasa tashiga yin sallanda ke kanta tana idarwa tafitoh waje da jakanda akabata a biki nan tashiga zazze abinda ke ciki tana numama sumama Allah yabasu zaman lfya sukace yayinda didi tarika kuranta abin zeemarh nadabada labari duk suru sumama sukayi dansunsan halin surukartasu.swiss atanfan dake cikin jakan zeemarh ta dauko taba Firdausee, Firdausee taji dadi sosai sai wanen 10 sukamata saida safe.


Daki sika shiga didi da zeemarh nanfa zemarh taitaba didi labari hadda Sabin saurayinda tayi didi tace Ahmad fa zeemarh ta bata fuska tace shikenan dan amin miji kuma bazN yi Samari ba, didi tace maida wukan nagane.chatin tafara Inda su deeja kebama su zeemarh labarin samarinda sukayi suma sai tsara yanda zasuci kudi sukeyi 11:00 sukama junasu sallama suka sauka online har ta gyra kwanciya wayanta yafara ringing tana dubawa taga *suraj*ne gyaran murya tayi sanan ta dauka sai  after 12 sukayi sallama.




Yau Friday daurin aurene sai dinner da dare Wanda tasan itabazuwa zatayiba.duk Kansu a gidan bikin suka hadu kasancewan kowa saurayinta yazo ya dauketa, sunyin kyau sosai haka amaryama anci ansa anata pictures sai after 6 akazo daukan amaryan daka gidanta a wuce dinner.zeemarh, Deja,salma,nussy,hawwee duk motan samarinsu sukabi danzuwa gdan amarya,gida yayi kyw ba karya ankashe kudi komai mai tsada ne, bata Dade sosai ba tamusu sallama tatafi yanan duk ta ansa numbers din Sabin friends datayi.


Bayan ta zauna kalleta yace nima bazani dinner ba tinda baxakiba saida ta ware idanu tace why smiling yayi sanan yace kinaso aita kallona ko murmushi tayi sanan tace nop

Kallan tayayi yace ina mukayi tace gida, sai da yabiya ta salwa kitchen yamata siyya sanan ya ajeta a uguwansu 


Bangaran su salma kuwa ansha lace dikin Riga da skirt suyi kyw sosai amaryar hartafi kukin yin kyau haka angonta ma sai 12:30 akatashi duk gidan amarya duka dawo,a daran salma da deja sukai tamasu sanding pictures dinda sukayin dan sukadai a yan group din nasu sukaje dinner



Washegarin budan Kai sai 4 zeemarh, nussy,hawwee sukazo gdan amaryan wajen 7am Anty Xee tashigo tace toh anriga ansallameku ga kudinku man na friends 350 yana hannun haneefa duk fitoh wasukayi Inda akaraba kudi kowannansu yatashi da 50k haka sukarbar gidan kowa najin dadi.yau basu nema samarinsuba dan so suke su tada kafin su Isa GDA salma tace waya wlh zan chanza zemarh tace bakida hankali ai su suraj ne zasusai mama waya nussy tace Ashe kingane deeja tace Inda zakuji tanawa mubari ran Monday inmundawo sch muhadu gdansu salma muyi magana duk sukace bazasuzo sch ba kawai suhadu gdansu salman 2pm  adaidai nan nussy da hawwee suka sauka yayinda su zeemarh akakarasan dasu drop din taxi duka dauuka su big girl...





~biebie dee~

07039732859

© ~samrah~

09062056022

💓YAN'MATAN ZAMANI💓

                  



® *PURE MOMENT OF LIFE WRITES*

 

Biebie dee bukharii da

Samra

       



4⃣6⃣_5⃣0⃣



    Haka sukai ta hira har suka Isa GDA. Ummie Salma taayi farin ciki da wanan kud'i da akabasu haka Ummie Deejama Zeemarh ko Inda zakuga didi sanda Zeemarh take nunamata kud'inan sai kunsha mamaki addu'a taketa zabgama family Zainab angonma yasha ba adadi.                                                                                                                                                                     "haka rayuwa tacigaba da tafiya. yau ta kama monday tun da safe data tashi Zeemerh tace' didi zanje school didi tasan anya ba wani abu Zeemerh zatayi ba. se sauri sauri take nan tagama shirinta tsaf tana fitowa tace didi dan allah ki' karbomin dari biyar so nake nasai math sets nawa ya lalace kuma da transport didi tace toh yanzu ya za'ayi? Zeemerh tace ki karbomin gun abba ko yaya ahmad'. didi tace toh bara inje in gwada sa'a. tana fita dedenan taga Ahmad', yace didi se ina? Ta cono baki tace ahmadu wlh dari biyar nakeso' zan sai takalmi zanbawa wata jikar kawata'. Ahmad yace to didi gashi' nan yabata kudin. tana shigowa Zeemerh daman tagama hada kayan da zatasa agidansu salma' tacire book in jakanta tasa kayanta nata aciki. didi tace gashi nakarbo miki' Zeemerh ta washe baki ta karba' tare da cewa didi to 8:00 zan makara sena dawo. didi tace adawo lafiya' tana fita tayi hanyar gidansu Salma'. nan taga ummi tana dama koko' Zeemerh tace Ummie ina kwana Ummie tace lafiya lau yau kuma se ina Zeemerh tayi fari da ido tace wallahi' so muke mu wanki wasu abokanan mijin Zee. ummie ta bude ido tace' ke dan allah' zeemerh tace ga zahiri kina gani kuwa. tace zauna nan Zmmie. nan ta shiga dakin Salma ta tarar da ita tana bacci' itama cire hijabinta tayi' ta hau bacci abinta. sau wajen 11:00 suka farka nan salma tace ke Zeemerh kice kinzo kinganni inta bacci tace nima wallahi baccin nayi nan tace bara naje nayi wanka'. Zeemerh ta ciro wayanta don tayi chat tana hawa online taga suraj yana online nan ta chanza dp don kada ya rainata tayi making story a whatspp inta.                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                            " hi baby ya kike                                " steady you.                                                  "yajin dadi ya gida' ya gajiya kuma ya school'?                            "cool wlhm                                   "wow nice dp yayi kyau sosae bae'.                                       "oh rily i knew' anyway thank's.                                      "please! bae inason ganinki yaza'ayi"?                                     "eyh may be yau cause' zanje restaurant' inason cin shawarma da hot dog' burger. baker namu yadena zuwa. gashi oven inmu' yana burning mutum.                    " eyyah oven na burning glowing skin princess' ina                      "don't mind i will' manage'.                   "yace nazo nakaiki?'.                        "no thank's driver'n mu ze kaimu don't worry'                      "yace wani time' zamu hadu?'.                                      "tace emm 3:00pm prompt'.            "yace tom se kinjini ko'.               "ok bye se anjima                                                                                                                                                                                                                                                                  "Suraj kam yana mamaki aransa yadda Zeemerh take da class' gata daga ganinta yar masu kudi ce'. wani lokacin har tunani yake anya bata fishi kudiba' cause yadda yaga duk da ya'yan' masu kudi take harkanta koda bikin zee '.                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                              "salma ce tashigo' yayinda zeemerh take' kiran deejah saboda yanxu wajen 12:40. ke wai dan allah yaushe zaku fito ni wallahi har' nafadama suraj' res zanje' kuma gaskia haka zakuyi' sede kunzo. nan salma ta karaso tace manyan kasa' iyayan karya yade Zeemerh tace ke ki shirya mana. nan salma ta shirya tareda kiransu Nusy. wajen 1:20pm duka suka iso.  nan suka amince da zancen Zeemerh chan Zeemerh tace toh yanzu wazai kaimu saboda kada muje already suna chan suzo su hangomu ana juyemu a taxi kinga kuwa ba kanta nan suka sa dariya duka'. Zeemerh tace ke Salma  ina kabeer tahir na  UBA. ki kirasa nan sukace kai kawarmu wallahi kina kamshi muna binki' da humra. nan salma takirasa daman yace yanxu yadawo gida mid break' tace toh godia nake. sunsha hirarsu 2 nayi sukayi sallama suka fice dede bakin titi yazo cikin wani _benz 250_ ash nan salma' aka shige gaba har suka karaso rest' in. ya hadu iya haduwa daman daya ajiyesu ya ciro 5k yabawa salma'. wai koda be dawoba tayi transport' tafito tana godia.                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                  "suna shiga kowacce ta kama table me mutum biyu ta zauna kowa ya fadi abunda za'a kawoma. seku rantse irin yayan attajiran nan ne hutu yagama ratsasu. nan zeemerh taga kiran Suraj ta daga yana tambayan wani direction take. suma sauran suka kira samarikan nasu . suna zuwa sukace gaskia abin table' innan yayi kadan we need more. da za suce a'a se kuma sukayi shiru . Annur ne yace hi suraj wallahi shisha nakeso i need it' . nan salma ta waro ido' Suraj yace then?. yace bara zan karbo' nan yaje ya karbo Suraj shima yace guy dan sammin nayi hat smoke style. sukasa dariya duka' suke sunce baza su shaba. cause suna tsoro. (biebee dee da samrah) mukace kuna tsoro kuka zonan din?. haka sukasha hirarsu se wajen 6:00pm sukace zasuje gida haka su suraj kowa yadauki fiancee' nasa. yakaita gida duka sunce zasuce extra lesson suka tsaya saboda ankusan fara SSCE. haka kuwa abakin titi suka ajiyesu zeemerh taje gidansu salma ta chanzo kayanta tayi gida. koda ta shiga taga didi na alwala tace kai mutumin nan allah ya saka mana ace wai beda method of teaching tun dazu yake mana abu daya fisabilillahi'. didi tace lafiya tace wallahi kinga didi' wani dan iskan malamin mune yamana wani wawan calculation wallahi har yanzu ban gane equation innan ba mshcww' didi tace ai malaman birnin nan basuda kirki ko kadan' addua zaki tayi kawai' abincinki yana kwano zeemerh tace me akayi' allah sa ba tuwo bane. didi ta 6ata fuska tace jalaffffttt  akayi' zeemerh tayi daria tace se kace yaki'. aranta tace chab' nayi dam mezanyi da wata jallop' ana zaune kalau' akai kasuwa.   



Kwanciya tayi tana tunanin yanda zata chanza phone, dan shi'ne damuwanta, zubur tatashi daka kwancen phone dinta tajawo ta shiga kiran layin suraj bai'yi picking ba har yagama ringing tsaki taja mtswww.

Instagram ta shiga tana ganin pictures, picture wani handsome guy tagani  an'sa a *naija peoples*nan tashiga account dinsa kasancewar anyin tagging dinshi batare da 'bata lokaci ba ta shiga liking posts din'shi sosai ya kasheta dan ya ha'du ba karya fresh guy ne ba na wasa ba. M.farooq sai nanata sunan take tana murmushi.

DM tashiga dan yima wa'yanda sukamata text reply. Request message tagani tsaki tajaa sanan tace duk kuyi kugama wlhy indai baku ha'du bah ko ba cash ai ba kanta, nan dai tashiga duba kamanin su ba laifi duk taga da abin Arziki duk tamai damasu da 'hey.

Call din nussy ne ya shigo 

Haffa

Nussy: when zamu kasuwane?

Zeemarh: muyi chat ta group plx.


Nan suka shiga chatting,already dama su Deeja na online. Sungama yanke Shawa'ran siyan kayan sawa da kudin, Zeemarh tace zama amira kaita maga ta gaimu wajen matan da take siyan kaya wajenta a uguwan rimi, dan bazamu siya made in Nigeria ba, duk sukayi daria.salma tace gara tasan muma bana wasa bane....

                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                 ~biebie dee~                                          07039732859                              ~samrah~                            09062056022

💓YAN'MATAN ZAMANI💓




® *PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*



*WRITING BY*

biebie dee bukarii&

Samrah



5⃣1⃣_5⃣5⃣





""""""""Haka dai sukai ta chatting daka k'arshe sukayi sallama, duk suka sauka online. Ahmad ney yashigo d'akin da sallama cikiciki ta ansa tacigaba da Danna wayanta,bayan ya zauna kallan ta yayi da kyau sanan yace Zeemarh kina ganin kin kyauta kenan? hararanshi tayi ta gefan ido sanan tace danayi me fa,zamanshi ya gyra sanan yacigaba da cewa ina ganinki da Samari da yawa kwna biyu kuma kinfi kowa sanin hakan baikamata ba, banza dashi tayi game da mikewa tace kacigaba da addu'a.tana gama fad'ar haka tayi waje abinta.Ahmad yabita da kallo a ranshi yana cewa mewanan yarinyan ke nufi ne.



Yanan zaune a d'akin sai ga D'idi tashigo, tsayawa tayi turus Nata kalanshi sanan" tace Kai kuma lfiya? yace wlhy" Zeemarh na Neman samin damuwa"D'idi ina yawan ganin ta da Samari kwana biyu nayi magana kuma wai nacigaba da addu'a, inaga su baba zanma magana kawai,D'idi ta kalleshi da kyau sanan tace kowa yad'ade dasanin Azeemarh matarkace d'an haka karkadamu, kuma inbayi addu'ar ba kuka zakayi ko mai" Ahmad yayi dariya yace hakane kakus "dan bani buta nayi alwala ankusa sallah.



Itako Zeemarh tabarin d'akin d'idin  side din mama tashiga bayan ta gaisheta sanan ta wuce dakinsu, anan  taga Firdausee sai note takeyi tsaki tayi sanan tace kedai kam baki gajiya da hada ido da books ne daka rubutu sai karatu, Firdausee tayi murmushi batace komai ba,Zeemarh ce ta gyra zama tace dan aje book dinan nabaki labari Firdausee tace yawwa dama nayi missing naki wlhy smiling tayi tace kinaji ko, nan tashiga bada labarin haduwar tada Suraj sai da Firdausee tagaji tas tace yaya Ahmad faa, Zeemarh tawani harareta "tace nacemaki auran Suraj zanyi kawai kudi zanci yanda *yanmata*keyi" Firdausee tace duk daka kinsan dai in yaganki dawani bazaiji dadi ba," Inda nice wlhy bazan kula kowaba tinda inada miji na a hannu Zeemarh tamata kallan bakida hankali sanan tace "kina da Matsala tashi tayi tabar dakin ,yayinda itakuma Firdausee ta shiga toilet danyin alwala.



Itama datakoma d'akin sallah tayi, tana idarwa tajawo phone dinta tahau chatting da friends Nata nan suka yanke shawaran Friday zasu siyan  kayan.tanan zaune a wajen aka Kira sallahn isha nan danan ta kabbara ta tashi, d'idi tace akawo abinci "Zemarh tace ni wlhy nakoshi" didi'n takuma cewa dakikaci mai? baki taturo

"D'idi tace toh Kira yayanki yasiyo maki wani Abu" ai d'idi bata gama rufe bakiba tafita 


D'akinshi tanufa baya ciki,kawai tawuce side din mama murja bayan ta gaisheta tace mama dan Allah yaya fa, mama tace k'irashi mana,nan tashiga k'iranshi yana d'auka tafita tabar dakin mama murja tabita da murmushi. Kashewa tayi dan bata jinshi, side mama tanufa nan taganshi zai fitoh karasawa tayi" tace yaya Kai naketa nema" yayi murmushi yace gani ai" tawani marairaice fuska tace wunwa nakeji "

Cewa yayi karkiyi kuka ga abunan nasiyo, rakani na kaima mama sai mukoma side didi," bayan sunkai ne suka nufi side d'idi anan suka baje anata hira sai 10:00 Ahmad yamasu sai da safe yawuce.yanafita wanka tayi tasa kayan baccin ta tajawo waya tashiga Instagram nan taga abin mamaki  *M.farooq* yamata DM d'adi taji sosai nanfa suka shiga chatting sai kod'ata yaketa itako sai dad'i takeji basuyi sallamaba sai da ya ansa digits dinta, ranan baccin murna tayi dan tanasan taga tana hurda da fresh guys batasan talakawa Wanda ko crdt din 200 bazasu iya turowa ba, Allah Allah take gari yawaye intaje sch tabama friends dinta labarin *M.farooq*.




D'awuri tatashi taga shirinta tsaf tanufi side mama dan gaisheta,side mama murja tafara shiga anan ta tadda  Firdausee bayan su gaida su baba ya dauko kud'i yabasu  a nan take fadamai sai 6pm zata tashi ita sabida waec lesson dasukeyi ku'di yabasu suyi godia suka nufi dakin mama Zeenarh ta gaisheta, sanan suka Mata sallahma suka fitoh.


Sunyi farinciki sosai da ganin junansu, sai da akafita break sanan Zeemarh tafara basu labarin *M.farooq* "Deeja tace Allah sa dai yanada sakin hannu" Salma tace inma baidashi ba sai ki shareshi ba" Nussy tace mai akeyi da tsiya" "Hawwee tace wlhy kuga dai bikin Zee ga mijinta bawani babbba amma akwai abin" nan duk sukasa daria.

"Salma ce tayi maga kunfa San yau sai 6mp muda gida dama munzo da waya mukira su Annur sukawo mana wani Abu Zeemarh"

tace nazo dashi zankira M.farooq ya kaimu wani waje" ubanme ake a lesson din hawwee "

tace bafa kutaba ganin juna ba"

"Deeja tace komai system ne fa "duk sukasa daria Amira kaita ce ta karaso tace "kuna jin dadi fa ankoma class kunan abin Ku, "Nussy tace mungaji ne" Neman waje tayi ta zauna tace babies akwai wani birthday da cousin Dina zatayi next week zakuzo ai," salma tace why not" nan Amira tashiga fadamasu iri Mayan yaranda zasuzo, dan gara kushiya da kyau Zeemarh "tace inmunje siyan kayan Friday sai muduba na birthday dakanan. sai after 11 suka koma class...






© ~biebie dee~

07039732859

© ~samrah

09062056022

💓YANMATAN ZAMANI💓



*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*



*WRITING BY* 

Biebie dee bukharii&

Samrah


*dis page is for you lovers Biebie Dee n samrah novel group thank you so much for d love n care we really appreciate*❤❤❤❤


_banmanta dakeba HAUWA IDIRIS ABUBAKAR mungodee sosai_😘😘


5⃣6⃣_6⃣0⃣



""""""Koda suka koma class dinma bawani maida hankali sukayi ba, ba sake fitabah sai 12:50 dan aiyi sallah, bayan sun idar da sallah ne suka nufi sch shop dan siyan wani abu, indomie n egg suka siya sai drinks mai sanyi suka koma class, anan fa suka bude sabon chaftan hiya "Zeemarh tace wlhy dole mushiryama birthday nan faa kinsan duk family Amira kaita masu kudi ne"Salma tace baby kedena bata bakin kii dole zamu shirya"Nussy tace Allah sa dai kafin birthday duk anchan zamana phone danni wlhy Samsung dinan kunya yake bani"Hawwee tace mai kika sani ni danaje wani birthday a maraka duk shegun yaran iPhone garesu inko kiga gansu da Samsung toh wlhy mai zafi, ai sai  nasa nawa a jaka kuma nasata silent dan kar sugani ma class Dina ya zube" Zeemarh tace yar banza da kin fitoh da shi ai "Salma tace rai ni kirkir kenan" duk sukasa daria. 




"Kee dan Allah in k'iranshi zakiyi k'ira musan madafa kina ganin yanzo 3 har yawuce kuma kinsan 4pm zamushiga lesson Salma ce magana"Zeemarh tace kee kincika masifa ba Wanda yayi magana a wajenan sai kee, ko dayake kinfinmu San abin duniya ai" Salma tacika tai fam batakuma cewa komai baa



K'iran number tashiga yi ringing 3 yayi picking "Zeemarh tace hw far"

"M.farooq "beautiful kina inane saida Zeemarh ta juya ido takale friends dinan sanan tace wlhy munfitoh sch muna wajen 111 zamusiya abu"M.farooq yace Kar kushiga ganinan" nan Zeemarh tayi wani shegen smiling sanan ta kalle friends nata "tace baby mujee duk suka mi'ke banda Salma "Zeemarh tace babymee bakinsan wasa ba sorry"Salma tayi smiling tace no wahala duk sukayi daria.


Sunkusa gate ne Zeemarh ta hadu da Fiddausee data wuce gida nan sukayi sallama"Zeemarh tace kigaida min da kowa"Fiddausee tayi murmushi tace saikace bazakidawo ba, bayan fiddausee tawucene "Hawwee tace itadai sister ki ba ruwanta  "Zeemarh tace hakane faa duk daria sukayi babu bata lokaci suka Isa 1_11 kancewan bawani nisane daka sch bah, daran su a napp kenan sai ga motan M.farooq yayi parking tin daka nesa suke sakarma juma murmushi k'arasuwa yayi "Zeemarh tace handsome"smiling yayi yace beautiful how u bare da ta ansa ba tace meet my friends,Salma,Nussy,Hawwee n deejah"duk yamika masu hanu suka gaisa.


Ciki suka shiga abinci kakawo masu mai lfya suka ci sama sama sanan yasiyamasu soya na 4k dakanan House of cake yakaisu haka ya siyan masu uban cupcakes masu masifan d'adi da tarkachan snacks.


Sai kusan to 5 yayi dropping dinsu kusa da sch sukai sallah yawuce sukuma suka shiga sch bayan class sukaje suka zauna suna k'ara firfitoh da kayan suna gani"Salma tace wlhy baby za'a dashi"Deeja tace sosai ma"Nussy tace bani ba abicin dare wlhy saide innaga abinci arziki yayi over a ciki"Hawwee tace koni wlhy" Itako Zeemarh sai wani smiling takeyi a dole tasamu friend mai kudi


Hakadai sukai ta hiransu a bayan class har 6pm tayi nan duk suka tashi suka nufi class dan d'anko bags dinsuu.


Abakin gate ney suka hadu da Amira kaita da Farty "Amira tace ban ganku a class din biology ba Zeemarh tace muje house of cakes ne "Farty tace shine Baku fadamana ba"Salma tace bamu zata zakuje bane akwai next time ai "Zeemarh tace yes" nan  sukama juna sallama sukai gida...





© ~biebie dee~🌸

07039732859

© ~samrah~😘

09062056022

💓YAN'MATAN ZAMANI💓




*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*



*WRITING BY* 

Biebie dee bukhare&

Samrah



6⃣1⃣_6⃣5⃣





""""""Tana Isa GDA Ana kiran sallan magrib babu b'ata lokaci toilet tashiga tayi wanka tafitoh da alwala bayan ta idar da sallah ne ta fufi side din su mama dan gaishesu 


Dakin mama Murja tafara shiga suka gaisa takuje ta gai da baba aminu anane tak'e fad'amai wai kudin lesson 5k "baban yace insha Allah zai bata gobe nan tayi godiya sanan ta nufi side mahaifiyar ta ta shiga da sallama bayan sun gaisa mama tama ya karatu nan Zeemarh tashiga bada bayanin k'arya wai suna shan wahala nan dai mama tamasu addu'an Zeemarh ta ansa da amin sanan" tace baba ya dawo kuwa" mama inyadawo mai zai maki "Zeemarh kudin lesson Zan ansa ko yau sai da akakusa dukanmu sai danace gobe zankawo aka barni kuma yawancin yan class din duk sunbiya sai mu harara mai lfiya mama ta ballamata"sanan tace  ke dai kenan Kai kanki Inda Allah bai Kai ki ba bakida wani magana sai na wasu, bak'i dube da na k'asa dakee sai na sama da ke rayuwace sai kitayi ai mudai Allah yagani muna iyaka 'kok'arinmu a kanku amma kee Sam baki gani ai sai kitayi Allah ba mai rabo sa'a, gadai Fiddausee kina gani ita ba ruwanta duk abinda aka d'a  ko akabata d'adi takejii tana godiya da addu'a k'eko ba haka abin yakee ba"haka mama taita ma Zeemarh fada daka karshe nasiha "mama tace in kinyi da kyau kanki inkinyi mara kyauma kanki,sai ki Bari inyadawo daka masjid anjiima kizo ki ansa kud'in"nan mama ta tashi tayi cikin bedroom itakuma Zeemarh tashiga dakinsu wajen Fiddausee 



Fiddausee tayi murmushi "tace

Sisi ya sch din "Zeemarh tace babu d'adi "Fiddausee tace sai hakuri kunkusa Fara exams din ai"Zeemarh tace saura 2weeks"Fidausee tace Allah bada sa'a"Zeemarh tace amin"


Nan ta dauko cupcakes guda 3 tabata Fiddausee tayi godiya "tace haka yayanmu yasiyo maki"Sai da Zeemarh ta tabe baki sanan tace"Nop,M.farooq ne wani friend Dina ne Fiddausee batace komai ba, haka sukaita zama shuru ba Wanda yakara magana, anan Zeemarh tayi sallah taci abinci kanacewan abincin yayi dadi sanan ta hansa kudinta wajen baba tamusu sai da safe.


Tashigo side D'idi tana murna zata had'a 10k data k'ara tasiya kaya.bayan ta zauna ne tashiga bama D'idi labarin m.farooq D'idi sai d'adi  takeji a dole jikarta Nada  white blood😃lol.haka sukai ta hira har 10 sanan Zeemarh ta dau phone tama Ahmad flashing yaki k'ira su d'ade suna hira sanan sukayi sallama takira Suraj nan sundade sainan k'iran M.farooq ya shigo sai after 12 sukai sallama, sanan ta shiga chatting, anan taka message din Haneefa da Zee dama kuma friends din nata duk suna online ba ita ta kwanta ba sai 2am.


*******************

Ummie Salma tace"kema karkiyi wasa kisamu min mai maiko kinsan dai yanda family babanki suka tsanemu dan haka dakinga mutin ba kanta kar ki d'ebo min masifa"Salma tace haba Ummie hadda fata kedai kita addu'a kawai kisa a ranki na aura mai kudi, mai yasa kikaga na maida hankalina a bikin Zee sabida nasan zandace ne, bagashi nahadu da Annur ba kikasan irin mutanan da zansani nan gaba"Ummie tace Allah dai ya kaimu ranan wlhy saina bama su uncles dinki mamaki.


Haka rayuwansu haita tafiya sudai basaso afiso kulin cikin labarin mutane suke burinsu sufita daban cikin jama'a ba laifi *Yanmatan*suna wuta sosai dan sunkara samun Sabin k'awaye yawanci kuma duk a social network suka by hadu wasu kuma wajen jamb registration, gashi yanzo sunfara WAEC *Yanmata* daka sch daban daban sunzo yin exams a sch dinsu sai Kara samun k'awaye sukeyi.


Zeenarh kaba daya ta chanxa ma Ahmad bata sakemai fuska Sam da yashigo side D'idi zatayi k'ayar ciwan kai ko tashige cikin bedroom.


Shiko Ahmad abin yadameshi sosai zaune suke shida daddy(Musa )k'aninshi Ahmad ne ya kalle daddy"yace kana ganin lokaci yayi da zanma su baba wanan maganan"daddy yace yes bro coz kaga dis year zatagama sch dinta inyaso ba sai tafara sai tafara zuwa KASU din inkunyi aure ba"Ahmad yayi murmushi yace yau insha Allah zanfara ma Zeemarm'n magana najii mai zatacee kafin nagayama su baba'n"Daddy yace toh Allah tabbatarmana da Alkhari"Ahmad yace Amin"haka sukai ta hiransu kar aka Kira sallah suka tafi masjid.


Chatting take da jin music hankalin ta kwance sai smiling takeyi, sallama yayi ta ansa  cikiciki samun waje yayi ya zauna mamakin halin Zeemarh yakeyi yariyan k'arama amma sai ji da Kai "Ahmad ne yace Zeemarh kallan shi tayi tagefen ido sanan "tace na'am ya aiki"lafiya kawai yace sanan yashiga mata bayani a kan maganan auransu aje phone hannu ta tayi tamai da hankalinta gareshi"tace zanyi shawa'ra" Ahmad yayi kasa da murya yachai wani shawara bayan duk family sunsan da maganan"Zeemarh tace nasani kadai bani time dan Allah yaya"yace shikenan Allah shigemana gaba"tace Amin a hankali" sun dan taba hira sanan yatace zai fita nan Zeemarh"yaya please credit wlhy banda subscription"Ahmad yace yau fa 4days dana saimaki data'n 2k"Zeemarh ta turo baki tacce phone Dina nacin data ne"Ahamad yace naga phone din"Zeemarh tamikamai maimakon yaga Samsung saiyaga iPhone 5s kallan tayayi "yace ina kikasamu phone"Zeemarh tawani had'e fuska tace brother k'awarmu ne yabamu ni da Salma,Deeja,

dasu Nussy"yace akan wani dalili"Zeemarh tace munmai wishing happy birthday ne shine dayatashi dawowa yakawo mana phone din ko D'idi ma ai tasani"nan D'idi tashigo "tace menasani"Zeemarh tace a kan wayan hannuna"D'idi ta washe baki "tace ohhh wlhy yaya'n halima dantabawa yabasu ai sunada kirki wlhy" nan Ahmad ya jefa Mata wayan yafita d'idi da Zeemarh suka bishi da kallo.


"D'idi tace gajimin yaro shi bai siyaba ansiya kuma yana wani d'aure fuska wai shi a dole kishi" Zeemarh tace kaman wani miji na ba nan tashiga fad'a ma D'idi yanda sukayi da Ahmad ita D'idi batace komai ba Zeemarh tacigaba da cewa"nifa bazanyi aure yanzo ba sai nakai 200lvl ko 300lvl duka duka ma bandade da kaiwa 17 ba yazo yafara maganan aure gara kije kisamu su baba kimusu bayani tin dawuri kafin ya rigaki.


Nan tatashi tayi toilet, tanada paper 2:30, tafitoh batare da bata lokaci ba tagama shirinta shaf tama su mama sallama tafitoh, a nan waje ta ganshi 500 yadauko ya bata tayi gdansu salma.



Kai kawai tasa tashige dakin batare da sallama ba Ummie ce ta dubeta "tace *yanmata*lfya kuwa"nan Zeemarh ta zaiyano masu komai"Ummie tace gidan Ku sunada takura dukaduka 17 kike  an fara samaki ido yaushe kikayin *yanmatanci*da har za a Fara zancen aure, na shiyasa koda abba'n Salma ya rasu ban koma Zaria ba dan banasa sa ido"Salma tace wlhy kincika magana"Ummie tace dan ubanki da badan niba dakina Chan ba 'yanci ai" Salma taja hannu k'awarta suka fita.


"Salma tace mai nadamuwa kinayi kamar bayar *zamani*ba babu auran da zakiyi Bari muje sch za'ayi talks da friends"


Sai 6:10 suka fito daka exam hall.nan sukasamu gefe Salmace ke zayyano ma kawayan nasu bayani"Amira kaita tace ni Daddy yace sai nagama degree ma kafin nayi aure"Nussy tajaa tsaki ta daura da cewa solution muke nema ba wani long story ba"Hannah tace toh inyada kudi ki ya'da mana"Deeja tace a branch din MTN take aiki dai"Farty tace kawai kubari gobe muhadu gdansu Salma yanyaso kowa yayin karya yace paper safe yakeda shi"duk suka ma'am da shawaranta...



~biebie dee~🌸

07039732859

~Samra~😘

09062056022

💓YAN'MATAN ZAMANI💓




*PUEE MOMENT OF LIFE WRITER'S*




*WRITING BY*

Biebie dee bukharii&

Samra





6⃣6⃣_7⃣0⃣





*this page is for you Ummu adulnaser&maryerm💞 thank you so much for d  love n care,*

❤❤❤❤❤❤❤





"""""'Salma na Isa GDA batare da b'ata lokaci ba ta fad'ama Ummie yanda sukayi da friends d'inta,nan fa Ummie aka shiga shiri ba kama hannun yaro.


Salma waya tashiga kiran samarinta  wai batada lfya, nan fa aikaita kawo mata abubuwa.




Kee nifa na gani da wanan iskancin naki acee mutin baida lokan komai sai na waya"Ummi'n Deeja ce ke magana tashi Deejan tayi dan tasan Ummie ba sauraran labarinta zatayi baa"cewa tayi Ummie gani sai da ta harare ta sanan tace kije ki had'amin salad yanan a kitchen kinsan abbanku yakusa dawowa, inkingama kije Chan ki'kara da wayan kee kika sani *Bata  damu da abinda  takeyi da wayan ba ita  dai aimata aiki, toh Allah samudace yakuma bamu ikon lura da nauyin da Allah ya d'aurama duk da dai ba wayanka bane bakuma da barar kaba, sai addu'a  Allah ya shegemana gaba amin*



Koda Zeemarh ta Isa gida batada wani walwala, bayan ta ajee questions paper a kan gadon D'idi, side din su mama tanufa dan yimusu sannu da gda.tanadawowa toilet ta shiga dan yin kanka damuma alwala,sai da ta idar da sallan isha ta tashi, kwanciya tayi gami da kashe phone dinta dan batajin dadi Sam.

D'idi tanamata hira dataga ba amsa takama gaba ta.




Dawuri ta tashi tagama shirinta tsaf, banyan tama D'idi sallama side su mama tayi duk ta gaidasu gami da ansan kudi(su Zeemarh San kudi lol)batabi takan Ahmed ba,dan haushi ma yakebata tayi gdansu aminiyarta Salma.


9:30 a gidan tayi Mata,fadawa d'akin kawai tayi nan ta tadda Salma sai chatting takeyi Zeemarh tayi dan tsaki" tace pls kikashe k'aran wayanki yanadamuna"Salma tace walhy wani gara ne"Zeemarh tace kina da Matsala gara fa kikace, inyazo kiyi yaya da shi"?Salma tayi murmushi sanan ta daura da cewa ai irisu sai dare suke zuwa dan k'ar aganki dashi da Rana class yazube" Zeemarh tace ya Allah kiyayye nakula irinshi"Salma tace kyau zanci ko haduwa?ai inkanada kudi muje xuwa kawai"Anan Ummie ta shigo tawani washe baki *adongari* yanzo kikazo kenan"Zeemarh tace eh wlhy ina kwana"Ummie ta ansa gami dakai dubanta ga Salma tace ginbiya kitashi kiyi wanka kar k'awannaku suzo kinan"Salma ta turo baki tace wlhy Ummie kincika sa ido"Ummie tace sa ido na dajin ubanki yar banza"


Saida tagama D'anne2 wayanta sanan ta tashi tashiga wankan,ita kuma Zeemarh ta kunna music a phone dinta 





Karfe 10:00 daidai tamasu dukkansu a gidan su Salma'n, nan fa Ummie ta shiga kaiwa da komuwa kawo wancen d'anko wanchan haka ta cikamasu gaba dakanyan motsa baki iri iri sanan ta wuce kitchen dan shiryamsu abinci mai lfya.



Nan fa mutanan naku suka hau magana"D'eeja ce tace wai kichai ma D'idi ke kinfada"Zeemarh tace itama wait San auran takeyi fah"Nussy tace lallabata zakiyi tinda kinga su baba'n kansu

A k'asanta suke"Hannah tace good idea"hakadai sukai ta maganganunsu wanda tinda suka fara Salma batace komai ba,



Saida duk sukai shuru sanan tayi gyranmurya"tace indai har abubuwanda su Hawwee sukace baiyi aiki ba kawai kiyi k'aryan Aljanu"Zeemarh ta waro manyan idanunta tace Aljanufa kikace "Salma tace yes babe, iyaka dakiji ance za a k'ira mai ru'kiya ki ma'kale murya kice kema malamacee daka saudiya"ai nan duk suka sa daria harda buga k'afa"Hannah tace ba kida mutinci kaskiya"Amira tace gskia ney ai"Farty tace wato kimai damu mahaukata munata zuba aske ke kingama samun solution"Deeja tace bar yar banza"Amira takuma cewa shiyasa Zee bata bani haushe datayi aure yanxo dan tasanu irin wanda akeso"Hawwee tace yaro da k'udi bah"Fauzee take ma da irinshine babu mai hanaki auran in bakiyin *yanmatancin*ba zaki rage zafi da cash"Salma tace wlh inbanda gidanku sunada takura mai akayi a *yanmatancin* dukanmu nanfa daka yan 17 sai wanda basukai 18 ba"Hannah tace a nama soyayyah yanzo ne? K'udinka soyayyanka"Zeemarh tace nidai ina San yaya Ahmad"duk sukaga uban tsaki"Fauzee tace ai sai ki aureshi"Zeemarh tace ai dan bansan iyan aure yanzo ney"Salma tayi tsaki tace babu San kenan inda kinasan shi ai yadda zakiyi"Farty tace wlhy"Salma tace ai ni indai kanada k'udi kobakada kyau da iya dressing kazo kawai u ar wlcm"daria duk dikayi,haka dai sukai ta hiransu da iya shege har 1pm 


Bayan Ummie takawo masu jolof rice mai lafya da ha'daden coslow da shege kunun aya,sai santi sukeyi sai dasuka gama sanan sukai sllah,a ka zauna zaman shafa powder.


Karfe 2:00 dai dai suka fitoh,sallma sukayima Ummie suka fitoh,bakin gate suka tsaka Farty na kashemasu selfie,sukai minti 10 xuwa 15 suna Abu d'aya sanan suka fitoh titi, taxi suka Tara sai sch...






_kuyi hakuri da wanan nayi typing mai yawa ya goge wlhy_😭😭😭

    _saikunsake jina_


*BIEBIE DEE na k'aunarku a duk inda kuke*❤❤❤❤❤❤



~biebie dee~🌸


07039732859


,

💓'YAN MATAN ZAMANI💓



*PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*



*WRITING BY*

Biebie Dee bukharii&

Samra


  _nagode sosai da kulawarki a gareni LUVLY_😘😘😘



7⃣1⃣_7⃣5⃣





""""K'arfe 6:00 dai dai suka fitoh paper, babu b'ata lokaci ko wancensu tayi gdansu


Zeemarh tashigo gida da fara'a sosai sai d'adi takejii har sai da Didi taso jin dalili amma Zeemarh "tace babu komai, sai da tayi sallan magarib sanan taje tayima su mama sannu da gida bata bar d'akin ba, sai da tayi sallah isha sanan tadawo siden Didi nan fa Zeemarh tashiga bama Didi labarin exam tana murmushi


Didi tayi magana"ni ko hala dai Ahmad ya fad'aki maki za'ayi maganan auranku ne, naga sai fara'a kikeyi Wanda bangane kanshii ba".


Phone d'inta Zeemarh ne yakusa fad'uwa a hannunta kallan Didi tayi a zabure bakin ta na tawa "tace au..ran waa..wai?"Didi tace kugamin y'ar banza, auran wa kuwa in ba ke da Ahmad ba, ko kinji na k'ira wani ne Wanda baki sani ba"?



Kuka Zeemarh tasaka iya k'arfinta tana cewa”wlh ba za'ayii ba duka duka shekaruna nawa da za'ayi min aure"?D'idi tace Dan gidanku k'wanaki ba k'awarku bace tayi auran, mutuwa tayii"?Zeemarh bata kuma jin mai Didi zatace ba tawuce d'aki tana kuka, yayinda D'idi ta shiga Neman number y'ayan nata Dan suyi magana.




Gama cin abincin shi kenan suna d'an hira da Mama, hiran sch din su Husain sai ga k'iran D'idi ya shigo,babu bata lokaci ya d'aga k'iran anan take cemai tanasan ganinsu yanzo shi da d'an u'wanshi"baba ya amsa da  gamunan yanzo insha Allah.






KO minti 8 batayi da k'iran yayan nataba sai gasu sun iso, sai da suka sake gaisheta bayan ta amsa ney take fada masu yanda zukayi da Zeemarh”baba Abubakar yace aikin banza ai, innaga dama bazatagama WAEC din ba za'a daura Auran"baba Aminu yace a'a yaya baza'ayi hakaba za abi komai a hankaki, mubari dai ko auran za'ayi sai ta kamnala duk exam dinta sai a zo afara magana"Didi tayi gyran murya ta Dora da cewa abinda Aminu ya fada yayi daida, amma kafin lokacin inaso ranan Satinan mai zuwa kowa ya zauna ayi magana,hadda  yaran gaba d'aya”duk suka Ansa da toh insha Allahu"sai da suka Dan taba hira sanan suka Mata sai da safe sukatafii.





Zeemarh tin da takoma d'aki sai dai ta kwashe fiye da minti 30 tana kuka, dataga kukan ba mafita bane shine tajawo phone dinta, anan taga missed call din mutane babu a da'di

Batabi ta Kansu bah data tabude tashiga chrtn, group dinsu ta shiga.




Allaman kuka tasa😭😭  gami dacewa”nashiga uku"nan duk Kansu sukaga message din kacencewansu always online ne su ( kaman...basai nafada ba tasan kanta😼lol)




"Deejaa tace ya akayi

 akayi mene faa"?

"Nussy tace meyafaruu"?

"Hannah tace sorry baby, wats going on"?

"Hauwee tace kumanta da ita inbaza tayi magana ba"

"Zeemarh tace sorry babies, wlhy Didi tak'i yadda har kuka nayi amma ko a jikinta, sai ma k'iran su baba tayi sukai magana Wanda bansan mai sukacee ba,  nadai jii wai za'ayi meeting ran satuday help me out ya zanyi yanzo pls"?

”farty tace zuwa anjima inkukazo bacci ki kuma lallabanta"

"Amira kaita tace dayafii kam"

"Salma tace ke bakijin magana kiyi abinda nace kawai, ko bahakaba babies"?

"Duk suka sah yh" salma tacigana dacewa kawai cikin d'arenan irin 3am ruwa 4am kifara shure_shuran  k'arya, kinga koda kinyi ran Saturday din Didi bazatayi mamaki ba tinda ta sabajinki kinayi, ke harda shure_shurema kiyi" dariya suka yii gama dayansu

"Zeemarh tace amma wlh bakida kyau" Salma tace gskiyane ai"






Nan Amina kaita tashiga masu sandin bags n shoes wai anti ta  ke siyarwa 8k ne bags shoes kuma 8,500





Kowannensu sai da ta zaba irin Wanda takeso, Amiran tace"in suntashi daka paper ran Thursday sai subiya su ansa Dan gobe basuda paper,





Zeemarh tinda taji advice din k'awar tata hankakinta ya kwanta, taji kaman wani abu bai faruba, haka dai taita chatn, kan snap da kuma IG.




Call din Suraj ne yashigo, bayan ta dauka suka gaisa 

"Suraj yace 2day kin b'oye"

"Zeemarh tace wlhy ina exams, kuma ina preparation din bikin cousin Dina da za'ayi a Kt"

"Suraj yace okey, when xamu had'u"?

Zeemarh tace Thursday in mun fitoh paper around 2:30"

"Suraj yace okey baby in munhadu ranan sai muk'arasa maganan bakin ko"?

"Smiling Zeemarh tayi sanan tace Allah kaimu"a ranta tana cewa nasamu nabiyan bag da shoe dinda Zan siya, haka dai sukai ta hira 11:30 sukayi sallama.





Mutane sukai 4 dasuka k'irata bayan Suraj amma duk basu da'de suna waya ba, Amma kafin suyi sallama sai datace a turomata crdt,haka kuwa suka suromata ta mtnVTU Zeemarh tatajin dad'i, nan tashiga tunanin tsiyar da zata shukama D'idi cikin dare, kallan Didin tayi Wanda sai sharan baccin ta takeyi hakalinta a kwancee "Zeemarh tace zakisani ney, nan ta gyra kwanciyan ta.... 










~biebie dee~

07039732859







_fans Ku bama Zeemarh shawaran yanda zata Kara tsoratar da D'idi_🤣🤣🤣🤣

🌸🌸🌸 'YANMATAN ZAMANI🌸🌸🌸




*PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*



*STORY &WRITING BY*

~BIEBIE DEE BUKHARI~





_kuyi hakuri da jina shuru dakukayi kwana 2, Abubuwa ne sukayimin yawa, Amma yanzo zakurika jina akai akai insha Allahu_ *love you all*❤❤❤❤❤


7⃣6⃣_8⃣0⃣







""""Zeemarh bata farkaba sai 3:30am daidai sai da ta kale Didi tayi murmushi sanan tasake uban k'ara tana shure shure tana wasu maganganu da ni bansan wani language takeyi bah,Didi ce ta tashi ba shiri, nan tashiga tofa Mata addu'a, Chan dataga abin na Zeemarh da gske ne ruwa ta d'ebo a cup ta karanta fatiha kafa 21, shafamata tayi sanan tazuba Mata sauran a bakinta.



Zeemarh batabar Didi ta huta ba sai da tajii k'iran sallan asuba, nan tashiga sauke nunfashi sanan ta gyra kwanciyan ta takoma bacci yayinda Didi ta shiga toilet Dan yin alwala.



Sai k'arfe 6:30 ta tashi, toilet tanufa direct Didi tabita da ido,

tana shiga bayan ta Danna key dariya tashiga iya a hankali tana kwatanta abubuwanda Didi tayi tana daria, buga 'kofan da akayi ne yadawo da ita hankalunta nan da nan tayi abinda zatayi ta dauro alwala tafitoh.


Bayan ta idar da sallah Didi ta kaleta"tace ni ko Azeemarh kina addu'a kuwa kafin ki kwantaa"?juyar da kai tayi gefe tace inayi mana,meye kikagani"?Didi tace kinga abubuwanda kikai tayine?kinbani tsoro wlhy"Zeemarh ta zazzaro idanu tace niii"?Didi tace k'arya zanyi maki"?Zeenarh tace bance ba amma dai abinne da mamaki"Didi tace nidai Dan Allah kirage Danna wayanan kirinka samun lokaci kina Dan karatunan kamar yar u'war ki fiddausee"Zeemarh tace mai kuma yakawo zancen waya?nalura kwana biyunan duk kin wani chanza,shi gidanan abi a hana mutun sukuni komai sa ido,duk friends Dina ba Wanda akema wanan abun sai ni"

tashi tayi ta haye gado, Didi tabita da ido👀 


Thursday paper safe sukeda shii 2pm suka fitoh nan duk suka samu waje suka zauna,nan Zeemarh ta shiga basu labarin abunda yafaru sai daria sukeyi hadda buga k'afa "Salma tace ai ba zaki k'ara yadda Dani ba sai Randa kikajii Didi tace a bar zancen"Zeemarh tace dako na maki kyauta"

"Nussy tace nifa yanwa nakejii"

"Hawwee tace ni bakuga na kasama magana ba"

"Hannah tace kutashi muje gdan aunt Dina musan abinyi"

"Salma tace Zamuci beter?"harara Hannah ta watsa mata"kee kaf yan gdanmu da kikagansu da yawa toh babu wacce take auran talaka, Dan babanmu bai yadda ba, dakinje marafa kikace gdan lashe money ansani"Dija tace toh ai kuna da kyau dole kulashe money"

"Salma tace muda bamuda shima sai mun lasa bare ku masu kyau"Zeemarh tace kunji inda a kasan darajar kyau ba irin gidanmu ba"

"Hannah tace ai da ke y'ar gdanmu ce sai kinfi kowa tsada".




Koda sukaje gidan aunt din Hanna sunci sunkuma gode Allah komai kakeso gashinan available,gidane babba a malali 5 bed rooms komai yajii ga motoci har 4, nan *yanmatan* sukai ta daukan selfie sai 4:30 sukafitoh Salma,Hawwee,Deeja,Nussy gidan su Amira kaita sukayi Dan Ansan kayanda suka siya Dan (Amira da Farty basuda paper kasancewansu yan science class) sukabar Zeemarh da Hannah suna jiran suraj.




Basu daidai suna jiranshi ba yazo,fitowa yayi daka cikin motan gami da ware hannayenshi, Kalan Hannah tayi,Hannah ta d'aga mata gira babu musu tace tayi hugging dinshi,hugging dinta yayi very tight yana cewa"i miss you babe"Zeemarh takasa cewa komai sabida ba sabawa tayi ba


Bayan sunyi breaking hug dinne Hannah tamatso suka gaisa"tace na d'ade ina jin labarinka sai gashi yau mun hadu"Sujar yayi smiling yace nice 2 meet u "

"Hannah tace nice 2 meet u too,Bari na karku buh plx karku d'ade kinsan anajiranmu.


Sunkai minti 15 sunadan hira daka karshe suraj yabata rafan 1,000 ya mata sallama yatafii.


Batakai da shiga cikin gidan bah "Hannah tace kinbani mamaki baby, boo dinki yazo wai hug ma sai yaro'ka"Zeemarh tace ni yaya Ahmad bayamin irin abunne"Hannah tace ai Dan k'auye ne shi amma irin abubuwanan ai noms ne.


Gidan su Amiran su'ka k'asa nan  Zeemarh tabiya kudinta cash hadda bama Hannah 5k bAki washe ta anshe Dan su Hannah akwai San ku'di.


Gidansu Salma tafara shiga ta'aje kayanta sanan tashigo GDA ta ha'de fuska tana shiga d'akin tayi wargi da takaddun hannunta gami da jaan tsaki nan Didi ta shigo "tace wai mutuniyass lfya kuwa tsaki tajaa ta shige toilet, wanka tayi tafitoh da Alwala, doguwar Riga tasa na bacci ta daura hijab ta hau Rama sallolinda ke kanta, bata tashi a wajen ba sai da tayi isha'i hijab din tayi wargi tashi gami da jaan wani dogon tsakii mtwsssssss Didi cikin tsawa tace"wai ke lafiyanki tsaki takuma yi sai da tajii alamun su baba da duk wani Dan gidan sundawo daka massalaci ta buga uban ihuu Wanda yajawo hankalinsu dukka.



Babu shiri su baba suka taho D'an ganin mekefaruwa nan sukaga Zeemarh na bori tana shure shure tana wani yare Wanda basu gane kanshi ba,Ahmad ya rude addu'a yake tofa Mata hakama Didi dasu baba, baba aminu ne dayaga abin bame k'arewa bane "yace Ahmad yaje ya k'ira uztaz Yusuf Zeemarh naji haka tashiga wani  gurnani kamar wata gardi tsawa ta daka ma Ahmad "kar kakuskura kafita Dan kana fita zamu dauketa,kar kukira mana kowa  Dan Nina mallamane, nan Zeemarh tawani nokee murya kaman na magee tana rero karatu.


Bayan tagama karantunne "tace wai itaa sunanta Fahiima kuma a madeena take"baba yace mai kukeso?mai kukazo nema"?nan fa Zeemarh ta dawo da muryar Hardin ta wai za'ayi mana abinda bamasoo ne,kallan Ahmad tayi gami da nunashi da hannu tanacewa kafita a idanmu wlhy inba hakaba saikuma tayi shuru"baba yace ina jii Zeemarh tace zamutafii amma in ank'ara zamudawoo"nan tawani zube sharaf kaman da gske..(lol)Didi tayi kanta baccin karya tashiga yii aranta tanajin d'adin burinta zai cika, nandai su mama da fiddausee sai toh fa Mata addua sukeyi tana jinsu a ranta "tace duk kuyi kugama dani kuke labari wani iskancinma sai ran Saturday murmushi tayi ta gyra kwanciyanta




_kubiyoni danjin abinda zai faruu_






~BIEBIE DEE CE~🌸


*Ina muku fatan Alkharee a duk inda kuke masoyana, Biebie Dee na kaunarku*❣❣❣


 



,

🍁🍁🍁'YANMATAN ZAMANI🍁🍁🍁





*PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*



*STORY &WRITING BY*

~BIEBIE DEE BUKHARI~



*this page is for you sweet sisters aunty aina'u(ummu_abdulnaseer)&unty rabilah(maman arfah) I love you so much*❤❤❤❤ *stay blessed*


8⃣1⃣_8⃣5⃣




"""""""Haka Zeemarh tasha baccinta, bata tashi ba sai k'arfe 7am, toilet tawuce direct wanka tayi gami da alwala, sai da ta shirya tsaf cikin Riga da skirt na atanpa d'ikin yasauna das a jikinta sanan ta shinfida sallaya tayi sallah.




Awaje ta tadda Didi tana tsince wake, musmushi Zeemarh tayi"tace kakus mai kuma zakiyi da wake"?kallanta Didi tayi da kyau kafin "tace wlhy marmarin fatan wake nakeyi su Amina basa San irin girkinan shine yau nakeson nayi"Zeemarh na daria tace ki k'ira yaya daddy(Musa) yazo maki da plantain sai muhada dashii, kinga yau zai dawo daka sch"Didi tace a'a y'an biyu Zan k'ira"Zeemarh tace ashe bazaki ci ba kuwa indai wayananne"Didi tace duk su Zan k'ira nabasu sak'o sai naga nawa yafi yawa"Zeemarh tace Bari naje na gaida su mama"Didi tace da kyau.


Side mama murja tayi,ta shiga d'akin da sallama bayan mama murjan ta ansa, samun waje tayi ta zauna sanan tafara gaisheta,ansamata tayi cikin sakin fuska Zeemarh "tace mam baba fa"?mama tace bai d'ade da shiga wanka ba y'ar gidan baba"Zeemarh tayi murmushi tace inya fitoh agaidashi,Bari naje nagaida mama"mama murja tace ki gaidamin ita"Zeemarh tace insha Allah"




Da sallama ta fa'da d'akin mama, Ahmad ne yayi saurin juyowa, murmushi ta sakarmai shima ya maidamata sai da ta zauna ta gaida mama da baba sanan Ahmad duk suka ansa fuskasu sake. Daki ta wuce wajen fiddausee, duka ta kaimata bashiri fiddause ta tashi "Zeemarh tace wlhy yunwa nakeji plx ki dafamin indomin ki mai masifar d'di"Fiddausee tace inkina so jirani nayi wanka na shirya nima"Zeemarh tace indai zakiyi ai mai sauki ne" 





Batawani d'ade sosai a toilet din bah ta fitoh, Shiryawa tayi cikin gown na atanpa d'ikin yayi kyau sosa Zeemarh tace"beautiful muje "fiddausee tayi daria tace ai kinfini kyau"haka dai suna wasa da daria suka wace kitchen nan fiddausee ta hadda indomie bayan sun gamane suka dawo Parlor man suka zauna  sunaci suna hira da sai k'arfe 12:00pm su baba suka tafin sallan juma'a 



Shara sukayi da mopping "Zeemarh tace sis muyi girki yau"fiddausee tace mai zAmudafa "Zeemarh tace muyi jolof rice da coslow"nan suka shiga kitchen suka Fara aiki,kamshin girkinne yafitoh da mama Dana cikin  d'aki kitchen tashiga nan taga Zeemarh sai yanka cabbage takeyi murmushi tayi sanan tace Allah muku Albarka suka ansa ta amin mamanmu"



1:30 sungama komai,coslow nan na Zeemarh yasha style sai daukanshi pix akeyi, abincin ta diba kadan a plate da coslow tayi side Didi bayan tagama cine tayi sallah "tace ma Didi zata gidansu Salma anso wani paper"Didi tace adawo lfya"



Fadawa d'akin tayi bako sallama" baby kina ina?"SAlma tace ina fa zaki ganni kishigo a harkitse"Zeemarh tace bawani kawai nak'osa na baki labari ney"Salma tace yauwa ya kukayi"?Nan Zeemarh ta shiga bata labari suna daria sai da sukayi mai isarsu sanan "Zeemarh tace wai ina Ummie ne"?Salma tace taje u/sarki biki wata y'ar group dinsu kee aura'r da y'arta "Zeemarh tace hala bikin na manya ne"?Salma tace yakike Abu kaman bakisan Ummie ba,tafini San kud'i fa"Zeemarh tace kedai bakida mutinci wlhy"Salma tace ai gskiya ne" 

"Zeemarh tace ba wajen zuwa ne?"Salma tace akwai wlhy Deeja nake jira sai gak"i *daraja super market*nakesan shiga kinsan nayi wani sugar daddy Hannah cee ta hadani da shii"

"Zeemarh ta harare ta sanan tace da banzo ba bazaki k'irani ba kenan"?

"Salma tace naga ai kina ma su baba tuggu ne nashi bazaki fitoh ba sai kin gama amma sorry besty" harara ta bata sanan tace"ance fa sugar daddies b'ata yara sukeyi"

"Salma tace indai baza'a level 3 ba ai da sauki,ke nidai inzai sake hannu muje zuwa kawai"

 Sallaman Deejay ne ya katse ta,Deeja na zama tace"ta Ahmed yakukayi ne"

"Zeemarhtayi musmushi tace hadda girki nayi yau Dan yaudara" duk sukayi daria k'iran Didi tayi a waya "tace Ummie ta aikesu kar ajita shuru"Didi tace adawo lfya.


Alhaji ya Kai su super market suyi shopping hadda na banza sanan yabama KO wannesu 10k tasaka crdt sai d'adi sukeji 

Gidan su salma ta aje kayan sanan tanufo gida.


Vail dinta a ajee kawai ta fa'da toilet wanka da alwala tayi gown tasa Mara nauyi sanan ta tafara sallah, bata bar wajen ba sai da tayi isha'i.


Waje takoma wajen Didi bayan Didi ta idar da sallah "Zeemarh tace abinci na"Didi tace su y'an biyu sunciye"Zeemarh tace aidama nasan sai su, ba'a wuce tayi"Didi tace insunjiki keda su ni ba ruwana"


K'arfe 9 dadai duk sukazoma Didi hira Zeemarh na zaune nacin indomie bayan duk ta gaidasu ta maida hankalinta kan abincinta "a *zuciyanta*tace wai nan duk sunzo meeting ne faa Zan Baku mamaki gobe, za'ayi komai ta k'are ne"

Kallan Ahmad tayi ta sakarmai murmushi shima murmushin ya Mata "a ranta takuma cewa dakanada ku'di da na yarda amma innaa badani baa....





*inayimuku fatan Alkhari a duc inda kuke masoyana*❤❤❤❤

















_Biebie Dee_🌸

07039732859

🍁🍁🍁'YANMATAN ZAMANI🍁🍁🍁




*PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*



*STORY&WRITTEN BY*

~BIEBIE DEE BUKHARI~🌸


8⃣6⃣_9⃣0⃣






""""""Haka dai akai ta hira har zuwa k'arfe 11mp kowa yama Didi sai da safe ya tafi Dan kwanciya.





Zeemarh bata kwanta ba sai da tagama wayanta da Samari da kuma chatn sanan ta kwanta da niyyan anjima ka'adan zata bama Didi tsoro.




Hanan ne kuwa yafaru k'iran sallan farko Zearmah ta tashi sai shure_shure takeyi da sambatu da yaree Wanda ita kadai tasan metake cewa





Haka Didi ta tashi sai addua takeyi Mata dataga abin bah mai k'arewa bane shine taje tak'ira su Ahmad, suma haka sukai tamata addu'a.






Zeemarh bata bar subah sai da tajii antada sallah sanan ta gyra ta kwantaa,nan da nan duk sukayi Alwala sukatafi *masjid*





Koda suka dawo daka *masjid* din d'akin Didi suka shugo nan sukaga Zeemarh sai sharar baccin ta takeyi hankali a kwance.






Zeemarh ba ta tashi ba sai 7:30 toilet ta wuce direct ta 'dauro Alwala, bayan ta idar da sallah phone dinta ta 'dauko, data ta bude ta shiga group din su 

"Babies yau akwai bala'i faa, bakuga yanda na basu tsoro da asbahi ba"jinsu shuru datayi tasan va su tashi ba, Snapchat tashiga tana ta haukanta tana cikin yin video ne tasa wak'an *sweetdrms* sai ga Didi ta shigo, tsayawa tayi kawai tana kallon ikon Allah Zeemarh KO sai music din takebi nata blushing






Sai da ta gama Didi tace" Anya Azeemarh kina ganin fa baki da lafiya amma da safiyar Allah kin kamajin wa'ka"Zeemarh tace kudai gidanan komai sa ido kai, dakayin good morning shine wani wa'ka ni gskia banasan haka" fita tayi fuuuuu tabar d'akin Didi ta bita da Ido

 





Side mama Murja tayi a parlor ta tarar da su, ta gai dasu tana murmushi duk suka ansa cikin sakin fuska "baba Aminu yace 'yar gidan baba mamanku tace kinzo nemana jiya ko"? Zeemarh tace ehh dama gaisheka kawai zanyi" baba yayi daria yace madallah sai da Zeemarh tashi tea sanan ta bar d'akin tanufi side mahaifiyarta,





Ta shiga da sallama bayan sun ansa ta shita sauna kusa da baba, sanan tafara gaisheda 'yan d'akin tinda kan mama da baba gar Yusuf 'yan biyu ne kawai ba ta gaida ba Hussain yace" ni shiyasa nafi shiri da feedy a kanki bakisan na gaba da ke bah Sam" Zeemarh tayi daria sanan tace very soon Zan zama yayarku koo baba"? Hussain kasa ce Mata komai yayi su Fiddasee KO sai daria sukeyi

"Mama tace kedai Allah shiryeki"Zeemarh tayi musmushi kawai, haka dai akaita hira har zuwa 12:40 nan duk mazan sukayi Alwala suka tafi *masjid* sai da suka k'ara gyara parlor'n sanan suma suka shiga d'akinsu Dan yin nasu sallan.





Kafin su baba su dawo daka *masjid* su Zeemarh sungama zuzzuba a abincin a food flask mama "tace duk sukai side Din Didi" 

Haka KO sukayi duk abinda za'a bukata sai da suka Kai suka ajee.





Koda su baba suka dawo side Didi sukayo direct already su mama na wajen

Bayan su zazzauna ne Zeemarh da Fiddause suka fara zuzzubawa sai da suka bama kowa sanan suma suka zuba nasu, nan Zeemarh ta fiddo phone dinta ta daukesu picture tana daria fiddausee tace" duk murnar ne haka"?

Zeemarh tayi murmushi kawai a ranta tace"zakuga murna kuwa" 

Whatapp ta shiga ta ma group din friends dinta sanding pictures din da ta sauka su Didi na cin abinci

"Babies za'afara meeting faa"

Hannah tace ai sai kik'ara shuka tsiya, ayi komai a gama yau ba sai gobe bah"

"Deejah tace da yafii kam"

"Nussy tace kida murmushi ne ko da suntashi na k'aryan zasuce bayin kanki bane"

Zeemarh tace ke da kikasan komai ai murna naketayi"

"Salmah tace please baby na yau nafi na kulin"

"Zeemarh tace don't worry booboo na"

"Amira kaita tace nidai kiyi sauri Dan yau munada fitah,

Coz wani yaron friend daddy yazo daka kano, yace yanaso nakai yaga kd"

"Salmah tace inkuma bakiyi sauri bah mutafi"

"Zeemarh tace bye sai nazo"






Hankalinta ta maida kan abinda Didi ke cewa,"tin dai dai Azeemarh da yardanta ai sai ayi kawai, inyaso sai ta cigaba da karatun a d'akin Ahmad KO hakan baiyi ba"? Tagama maganan duk tana kallan su.






Baba aminu yayi gyran murya sanan" yace hakan yayi Allah tabbar mana da Alkhairi" duk Kansu suka ansa da Ameen 





Baba Abubakar yace" ina ganin kawai ai anarana kawai inyaso sai ajee afadama yan manni kawai" Didi tace babu laifi"





Zeemarh shuru tayi taji iya gudun ruwansu ashe abin da gskene haka, Ai bata tsaya jin mai za'akuma cewa ba ta yanka uban k'ara Wanda yasasu rudewa gaba dayansu.





Magana tafara cin wani irin muryan Wanda ni kaina bangane ganshi bah " baza muyadda ba wlhy, bamu yadda ba wlhy, Kai Ahmad bamunce kafita har kanta bah? Zaburatayi data mike su baba suka riketa, cigaba tayi da cewa ai tinda baku janye ba muma bazamu FASA ba dauketa zamuyi bazaku k'ara ganinta ba" 

"Didi tana kuka tace bayan Allah Dan Allah kuyi hakuri"

"Wani daria zeemarh tayi tace inbaku fasaba muma baza mufasa ba"su mama da su Ahmad dai addu'a kawai suke tofah Mata Dan basuda bakin magana sai dai addu'an kawai.





"Ahmad yace indai har zaku barta nima na hakura"Didi ta daura da cewa Ehh Allah huce zuciyar kuu"

  Wani shu'umin karfi ne ya zo mata , tashi tayi da sauri tayi waje tana cewa sai munyi shawara"

Binta da ido duk sukayi suna kuma Addu'an Allah sa ta sawo.






Koda Zeemarh ta fita gidan su Salma ta wuce,ganinta kawai Salma tayi a gabanta Salma har Dan tsorata tayi Dan babu KO talalmi a k'afanta





Zama tayi sanan" tace anga wllh"Salma tace I see" daria sukayi sanan salma tace" Allah sa dai kinzo da phone dinki"Zeemarh tace ai muna gama chtn d'azo nasakashi a saman skirt Dina"

"Salma tace muje nakai ki toilet kiyi wanka mu wajee"


Sai da ta rakata har bakin toilet sanan tayo kitchen wajen Ummie,nan tashiga bama Ummie labari,"Ummie tace da gskiyanta su inbanda abinsu wake yayin wani auran zuminci"Salma tace Dana da abin arzikine ai sai ayi"Ummie tace aifa"



Tana fitowa Salma ta bata kaya gown na atanpa dinkin yayi kyau sosai tayi simple makeup tayi suma Ummie Sallama sukafitahh.....












~biebie deee~🌸

🍁🍁🍁'YANMATAN ZAMANI🍁🍁🍁




*PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*




*STORY&WRITTEN BY*

~BIEBIE DEE BUKHARI~


9⃣1⃣






""""""Gidan su Amira kaita sukayi, nan suka tadda Hannah,Nussy,Deejah,Farti.

Kayan motsa baki takawo masu sunaci sundan hira sama sama Chan Salma tace" wai ya sunanshiine"?

"Amira tace munnir"

"Zeemarh tace Allah sa dai yana da kyau"

"Deeja tace kedai matsalanki kenan"

"Nussy tace nidai atafi"

Nan duk suka tashii sukai waje.


Inda ake aje motoci nan sukaganshii,Munnirr dugo ne kuma yahadu ba k'arya kana ganinshi kaga marajii Wanda kanshi ke rawa,ga ku'di gakuma kyau


Amira ne tashiga yimai introducing friends nata 

Kalan Zeemarh yayi da kyau yace" your face look familiar"Zeemarh ta wani ware ido tace mee? Where? Maybe,"Munir yace maybe on Instagram or Snapchat, Zeemarh tace ohhhh maybe  su Amira sukai daria.





Mota yashige Amira ta zauna a side dinshi kallan tayayi yace"go Back joo, nan wajen Zeemarh ne" daria Amira tayi ta koma baya Zeemarh ta shiga gaba

Kasan cewa motar babbace tas ta kwace su.



Kawo sukayi har sai da sukagajii, pictures sunyi babu adadi haka snap ma sunbashi hakkin sa ku'di kuwa ankashesu abinda *Yanmatan* keso kenan

Suje side resort,salwa kitchen, frsh cafe, yom_yom daidai wurare da yawo house of cakes sukahe k'arshe nan suka jida uban snacks suka sai k'arfe 8:30 akai dropping dinsu gidan su Salma dukkansu Amira da Farty kuma suka wuce kasancewa area d'aya suke.



Suna shiga sukaga Ummie a waje gaisheta sukayi suka wace d'aki sai da suka zazzauna Deeja tace" baby when xaki gida ne"?

"Zeemarh tace sai gobe sun k'ara tsorata"

Ummie ce tashigo d'akin tana cewa" in banda abinki nanawa kuma?tsoro ai sungama tsorata awan kinawa da kikabar gidan"?

"Zeemarh na daria tace wama yasani"

"Hauwee tace muyi sallah mutafi plx"

"Deeja tace nidai sai naje gida gskia, Sulaiman nake jira yanzo zantafi"

"Nussy tace nima bari na k'ira Abdallah"

"Zeemarh tace kowa dai ya k'ira nashii"

Nussy "tace kusan menene?duk sukace nop

Ta daura da cewa yau naje gida wlhy nasan mama nachai tabata f'ada"Hauwee tace hakuri zasuyi muna hanya ai"


K'arfe 9 daidai kowaccesu saurayinta yazo ya dauketa.

Suna tafia Zeemarh Alwala tayi tafara zama sallolin da ake binta, banyan ta idar ne ta maida kayanta na dazo 

Zamata suka bude sabon chaptan hira ita da Salmah dakuma Ummie.




Bayan fitan Zeemarh gidan Didi ce ta kalle duk 'yayanta da ke zaune KO wannesu yasa tagumi tace" inaso kowa ya shafe zancen aure tsakanin Ahmad dakuma Azeemarh,banaso ba k'ara jii

  Mamace tayi gyaran murya tace cikin ladabi" Didi bai kamata kice haka bah kamata yayi a Fara nenan Mata magani ba wai kiddda da maganansu ba, sudama abinda sukeso kenan daka sunce Abu toh aiyi aiki dashii"

   



Baba ma ya daura dacewa "abinda Amina taf'ada shine dai dai, baba Aminu da mama Murja  sukace gaskiya ne'

  


Share hawayen da yazubu Mata tayi sanan tace" toh ni *Hadiza* kuma *lADIDI* nace anfasah" tashi tayi tabar wajen fuuuh


Ahmad ne ya kalle iyayan nashi yace" Dan Allah bama kar Wanda yadamu Allah sa hakane mafi Alkharee duk suka ansa da Amien Albarka sukai ta samashi daka kashe kowa ya bar wajen.


Yinin ranan KO wannesu yayishine cikin farkaba Allah sa Zeemarh ta dawo gida, koda suka dawo daka *masjid* sallan isha baba tace k'ar akulle gida maybe ta dawo.




Zeemarh KO haka sukai ta hiransu har 11pm sai a lokacin Ummie tace" tashi maza murakaki kije gida Ai kinbasu tsoro haka"

Nan duk suka fitoh wani flat shoe din Salma tasaka suka fitoh kasancewar basu da nisa basu da'de suna tafiya bah suka k'araso gidin su Zeemarh nan Zeemarh ta shire ta kamin tabama Salma sukai sallama tashiga gida.


Tashiga gidan tana wani shu'umin smiling, side din Didi tayi direct tana Isa bakin 'kofar bugawa tafara yii a hankali, kasan cewar idan Didi biyu tace" waye?Zeemarh tace nine cikin sanyin murya har ga Allah Didi ta bata tausayi dan tasan Didi na k'aunarta



Ba shiri Didi tazo ta bude 'kofa nan Zeemarh ta shige 

Bata tsaya a KO ina ba sai kan gado kwanciya tayi Dan tagajii Didi tayi nagana tace"Azeemah ina kikaje"?

"Zeemarh tace Didi kaina ciwo yakeyi, bacci zanyi"

"Didi tace toh Allah sawake kiyi addu'a"


KO da safe da sukaga Zeemarh ba k'aramin da'di sukaji ba,tin daka faruwar abin ba a kuma d'afa zancen Aure bah.Zeemarh hankalinta ya kwanta tayi fess.







********************

Life moved on abubuwa da dama sunfaru cikin har samun admission da *yanmatan* sukayi a kaduna state university wato *KASU*inda Zeemarh,Salma,Hannah,

Hauwee,Nussy da Deeja suke mass.com department,Farty da Amira kuma suna micro biology.


In kugaka *yanmatan* bazaku Gane subah coz sun k'ara haduwa most especially ma Zeemarh ta hadune ba k'arya Dan Zeemarh akwai kwai gashi bata cika makeup bah.

Samari kuwa sai abinda yayi gaba.duniyar Instagram Dana Snapchat kuwa *yanmatan* na bauta masu kadama Zeemarh taji labari Dan tayi popular ne ma....









_kubiyoni muje zuwa_



*fatan Alkharee ga dukkan masoyana*❤❤❤❤❤




~biebie deee~🌸

🍁🍁🍁'YANMATAN ZAMANI🍁🍁🍁




*PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*


 


 *STORY & WRITTEN BY*

BIEBIE DEE BUKHARI



*dedicated to memxyBBC,rahancy,Ummie  auta,and All d members ov Biebie deee &samrah novel group,thank you so much for d love n care.I really appreciate Biebie deee loves you more n more*❣❣❣💋💋


Page9⃣2⃣






""""""Zeemarh ce zaune a barandar d'akin Didi wani English novel ne a hannunta tana karantawa,tacin uban kwaliya kamar Wanda zataje wani wajen 

Maganan fiddause ne ya tsaida ita daka karatunda takeyi d'ago da kanta tayi sanan "tace mekikace"?

"Fiddause tace phone d'inki

 za ki aramin zand'an yi wani assignment ne"

"Zeemarh tace naki fah"?

"Fiddause tace wlh tanada matsala ne, mutuwa takeyi wit out any reason"

Amai makon Zeemarh ta bata phone din sai cewa tayi "ina saurayunki toh? Meye anfanin shi da bazai saimaki new phone bah? Sai shegen zuwa duk Friday da k'iran wayan tsiya, amma yakasa sai maki na arzikii, Ana hadaki da mutanan kirki Fir kice aa 

Ai gashinan sai fama kikeyi da wahalliyar waya, da kin yadda da Khalid Ali da kinan da babbar wayanki"

 


Tin da Zeemarh ta Fara magana Fiddause kallan ta takeyi cikin ta kaici sai da tagama maganan Tass danan Fiddause tace" wanan kuma ke yadama, ni nasan bazan rok'eka bah amma kabani Zan ansa, toh ma menene acin ro'ko inbanda zubar da mutinci, kuma da kike cewa Mahmud na zuwa duk Friday ina ruwanki? Ni a hakan yafimin danaje ina tara jama'a naita zuba k'arya kaman yanda kikeyi

Waya kuwa k'ire kayanki banso kema ai da bakisan zakiri'ke iPhone 6 din ba, kinga kenan everything is time, ni ma time yayi Zan ri'ke har naba wani" ta gama maganta fuuu ta wuce Zeemarh ta bita da ido tana tabe baki.


Tashi tayi ta shiga cikin d'aki inda Didi sai bacci takeyi, ta'ba Didi'n tayi Didi na bude ido Zeemarh tace" kitashi an k'ira sallah"Didi tace kee kinyi ne"?Zeemarh tace banayi" tashi Didi tayi tashiga toilet.


Zeemarh ko phone ta dauko tashiga chatn,k'iran Suraj ne ya katse Mata chtn din sai da tayi Dan tsaki Dan acewar ta yanzo tafi k'arfin Suraj tin da ta hadu da Al_mansur.

       Sai da tagama ya tsina sanan ta 'daga k'iran,

"Cewa tayi yadai"?

Suraj yace"baby wat hpn,kinshare ni kawai"

"Zeemarh tace nothing faa kawai sch/studies"

Suraj yace" oky zamu hadu yau?

Zeemarh "tace a ina"?

Suraj yace " duk inda kikeso, amma  inaso mufara shiga NNDC moll coz nabude shop na abaya inaso kije ki gani,Amma inkin yadda"

Smiling Zeemarh tayi kaman yana ganin sanan tace"no pee,Zan fitoh 3"yace oky "


Wani tunani Dan tunani ne yazo mata, tasan yau kam zataja kaya amma dai shima  sai yasan abinda ya Dan samu wajen ta duk da dai tasan bata tabayin zina bah amma anayin Dan Abinda ba'arasa ba, toh meyasa Yaa Ahmad bai taba min ba? Ta tanbaye kanta zuriyar tace tabata ansa da because he love you for d sake of Allah, jiitayi duk ranta ya baci tasan Yaya Ahmad mai k'aunar tane mai yasa zatamai haka? Takuma tanbayan kanta ita kanta tasan tana San shi amma San abin duniya da kuma rudin *matan zamani* bazai barta ta aureshi ba  Dan wani reasons dinta na banza da wofii, tsaki tayi kadan afili tace" nice first love dinka ai Dan haka one but me" sai tasaki murmushi takuma cewa kawai ba'ayi bani ba shiyasa nayi haka amma time is coming zamuyi aure" watsar da duk wani shawaran arziki da zuciyar ta yamata tayi tace "Allah kayafe mana"


Tashi tayi cikin sauri kayan jikinta ta chanza zuwa wani shegen gown tasaka red color shide kaman bubu amma kuma ba bubu bane, powder tasaka sai eye liner da eye maskara, sai red lipstick da tasaka babu karya tayi masifar kyau😍

Sai wani side bag da ta rataya black hannushi Chan ne 


Didi tagani kan sallaya "tace granny zanje sch yanzo salma tak'irani wai wani lecturer na Neman 'yan department dinmu plx kifadama su mama ina sauri bazan shiga bah" Didi tace toh adawo lfya ayi addu'a akuma kula" Zeemarh tace insha Allah" tayi gaba Didi tabita da ido tana murmushi.



Tana fida wajen gidan nasu ta manna space a fuskanta sai tayi kaman wata celebrity...lol k'iran shi tayi a waya babu bata lokaci ya iso nan zuka bazama bayan subar NNDC moll chicken republic sukaje take away sukayi suka nufi garden dinshi nan suka ta hiransu da Dan tabe_tabensu(Allah shirya)bata dawo gida bah sai Ana k'iran magrib, sai da tayi wanka tayi sallah sanan taje tama su mama sannu da gida tana dawowa d'aki phone dinta dauko tashiga wayan Nata na fama.

*********************Ahmad yasamu wata yarinya haleemah sister'n wani friend dinshi ce, tana respecting dinshi sosai haka shima batada San abin dunia sam duk abinda kadauko kabata sai dai tayi godia da addua Ahmad najin da'din halinta babu ruwanta very simple girl 

Haka sukai ta gudar da soyyarsu da Haleema cin kwanciyan hankali.


Babu Wanda yasan zancen daka shi sai mama Amina.Dan ko k'adan bai chanzama Zeemarh bah suna hira wasa da daria sometimes har assignment yana Mata Dan ko ba komai jini ba wasa bane


********************


Haka rayuwarsu tai ta tafiya inbaka da cash baka da wani sauran mutinci wajensu ko kanadashima in baiyi masuba sai dai su lashe ka Tass subarka sudai mutincinka ku'di ney.


K'awaye kuwa sai abinda yayi gaba yaran manya da yara irinsu barasa godiyan Allah . biki kuwa  indai da maiko suna hanyan zuwa

Sunsan mutane sai kace wasu 'yan siyasa.

  

 


Suna fitowa daka lectures Deeja ne ta kalle Zeemarh tace" wai zamuje kuwa"?Salma tace mai zai Hana ai kodan  na k'ara Baku labarinan"Hannah tace wai da gske Rahma Aliyu aure zatayi"?Salma tace ai shiyasa nakeso muje wani wajen da ba hayani ya na Baku labarin mijin ta, Abubakar na malali friend Dina ya sanshi"

Hauwee "tace yanada kudi ne"?

Deeja tace" irin na rage zafi bah" tashi duk matsawa wajen da ba hayani ya sukayi sai gumar bikin Rahma Aliyu sukeyi 



Ko da bikin yazo basuyi wani rawar hai bah a cewar su sunfi k'arfin duk abokanan angon. Ita dai Rahma anyi biki lfiya ankuma gama lfya komai yayi kyau dai dai ba k'arya



Haka rayuwar su tai ta tafiya kulin burinsu gaba yakeyi ba baya bah har suka shiga 200lvl inda Fiddaudee itama tasamu KASU tana ka'ranta political science.


Ranan da Ahmad yakawo Haleema gida Dan ta gai da su Didi da su mama hauka ne kadai Zeemarh batayi bah Dan bata dauka zaiyi aure haka da wuri bah.... 






 





Biebie deee ce

🍁🍁🍁'YANMATAN ZAMANI🍁🍁🍁



*PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*



*STORY & WRITTEN BY*

~BIEBIE DEE BUKHARI~





_this page is for you sweetheart Ummie Garkuwa, thank you so much for d du'a.I love you so much sweetheart stay blessed_❣❣❣❣



9⃣3⃣



"""""" D'aki ta shige Dan ko face din Haleemah baza ta iya kallo bah, sabida haushen ta datakejii.


Ahmad ne yashigo d'akin da sallama a kwance ya ganta, zama yayi a bakin gadon sanan yace"sisi gafa antynku na kawo maku bakifitoh kun gaishe ba" yatsina fuska tayi sanan tace wlhy kaina keciwa please ace inagaisheta" Ahmad yace eyyah sorry sis, Allah sawake" yafita Zeemarh ta bishi da wani dogun tsaki mtswwwww.


Ahmad ko a ranshi sai yaji kaman bai kyautama tama da yamata zancen Haleemah, duk yaji baiji da'di bah

 

Haleemah ko ta yaba sosai da halin mutincin family'n Ahmad, Dan ko wannensu sai da yabata abin arziki babu abinda yafi birgeta kaman yanda sukai tasaka Mata Albarka taji da'di sosai takuma jii sansu harcikin ranta.


Koda takoma gida haka taitabama su amminta labari Suma sai San barka sukeyi da k'ara sa Albarka.



Zeemarh yinin ranan bata fita bah, haka kuma batayi picking din call din kowa ba Dan batajin da'di Sam kowa da komai haushi yakebata



Hakadai tagama weekend d'inanan cikin rashin walwala har Monday. Koda suka fitoh lectures da friends dinta ke tanbayenta nan duk tabasu labari, Hannah tajee tsaki sanan tace"kisan kina sanshi wayahanaki auranshi"?Deejah tace shidai nagani" Salma tace ai sai ki dage da addu'a"Hauwee tace shedanne kawai, kinada kaman Al_mansur yaro da ku'di ga kyau abinda kike nema, mai zakiyi da wani Ahmad? Tsakanunku sai zuminci ai" Nussy tace gara ki natsu da kyau kikuma dawo daidai"Salma da Hannah sukace da yafi kam"Farty ce ta'karasu wajen su kallan su tayi dukka sanan tace" babies wats wrong"?Nussy ce ta Mata bayani

Kallan Zeemarh tayi tace" kar kibani kunya mana mai naki a ciki Allah sama ya aura Mata 4 a Rana d'aya dat he's problem"Zeemarh tace hakane insha Allah ya wuce" Salma tace good" 

Farty ce tayi magana" babies kutashi muje gidan wata cousin Dina Feenah amaryace daka abuja aka kawuta nan u/Rimi nan" Hanna tace Amira fa"? Farty tace wai bazata bah, shiyasa na anso car key d'inta sai Hanna ta jaa nata"

Nan duk suka tashi suka nufa inda sukai parking motan.Faty tashiga Zeemarh a gefenta sai Hauwee a baya.motan Amira kuma Hannah ce ke driving sai Salma a side dinta sai Nussy a baya haka suka dau hanya sai gidan cousin Farty, watou gidan feenah


Tinda ka bakin gate Salma da Hanna suka rude sai sanbatu sukeyi Dan gidan ya hadu ni Kai na sai da na Lora  horn sukayi mai gadi ya bude ai sai anan Zeemarh taga fasalin gidan Dan tinda suka Fara tafiya chrttin takeyi kallan Farty tayi tace" naso naga mai gidanan" Farty yayi daria tace kuma wlhy age mate din muce bah" Zeemarh tace Masha Allah Allah samu adanshinsu" Farty tace nima soon zanzo nayi auran tayi magana tana daria 


Kulle motan sujayi duk suka nufa 'kofan da zai kaisu cikin polon tsayawa duk sukayi Farty ta k'irata tace" kibude 'kofa batajira taji abinda zatace ba ta kashe k'iran, suna Kama wayan akabude 'kofan saide ba Feenah bace watace Wanda ita kanta Farty bata wani ganeta bah,  farace sosai duguwa tanada kyanta dai dai ita dakaninta kunga yar gayu kuma Wanda sukeji da naira, itama dai baza tawuce mate dinsu bah.  matsamasu tayi sukashige tana masu murmushi basukai da zama  sai ga feenarh ta fitoh daka kitchen da tray a hannun ta 

K'ara sawa wanan buduruwar tayi ta ansheta, a gabansu ta aje drinks ne da kayan motsa baki Zeemarh ce tace thank you murmushi kawai ta Mata 


Bayan sun gama gaisawa Farty tama Feenah introducing friends dinta ita kuma Feenarh tamasu introducing sister'n mijinta wato *Ramalurv* nan sukai ta hira Ramalurv da Zeemarh Dan har jininsu ya hadu k'iran Amira ne ya tsaye masu hira Zeemarh ta k'ira cemata suna ina gatanan k'araso wa" Farty ce ta ansa phone din tama kwatancen gidan ba a jima ba sai gata ta iso nan dai suka baje akai ta hira Ramalurv sai basu labarin samarinta takeyi da yanda take garasu dai 5pm suka fitoh sai da Zeemarh da Ramalurv sukai ansa number juna 



Ansa bikin Haleemah da Ahmad zukuga farin ciki wajen mama Amina kamar me, Ahmad yayi kokari sosai komai yasama Haleema dai dai  Dan da Zeemarh taga kayan auran tayi mamaki komai na cikin a kwanin unique ne mai kyau.haka dai akai ta shiri har biki yazo *kamu*  a Arewa house, kuma yayi kyau  sosai Amarya da ango sunsha kyau har sungaji 


Zeemarh tayi kyau sosai  dan Al_mansur yasakar mata ku'di banda kudadrn da wasu samarin nata suka bata, friends dinta duk sunzo su Salma duk sunsha kyau ganan gansu kaga manyan yara Ramalurv ma tazo gidan brother'n ta tasauka kwana friends din Zeemarh kawai abin kallo ne Dan sunhadu sunyiya dressing ba k'arya

Fiddause ma tayi kyau Abu dai yayi kyau sai San barka



Ankai amarya gidanta mai kyau anan kabala cstain, gida yayi kyau ko wa sai sa Albarka yakeyi.





Haka rayuwa yaita tafita Zeemarh Al_mansur na sakar Mata kudu tinda ya Lura abinda takeso kenan.


Salma ma tasamu wani alj.Yahya maikaci ne babba a NNPC 


Haka su Nussy, da Hauwee, ko wannesu akai Wanda ta ajee amma basubar cikin kudin Samari ba.



Ansa bikin Farty, suna gama exams dinsu za'ayi  *yanmatan* sai shiri sukeyi Dan a cewar su wanan bikin babba ne...



Zeemarh tace da sunshiga 300lvl zata tura Am_mansur gida Dan ayi maganan Aure Dan taga fiddause so take ta tura muhmud gida ita ko baza ta yadda da haka ba, gara taga yadda ake sauke akwatuna da yanda Mata ke baza kwalliya.


Cikin ikon Allah sungama exams lfya shirye_shiyen biki aka fara babu Kama hannu yaro Zeemarh kuln tana busy Dan sune *Amara 'kirjin biki* Ramalurv ma tazo da wata friend dinta *memxy* itama 'yar gayuce ta k'arshe 


Salma alhj.Yahya ya sake cash Dan Ummie ma tace itama zata biki acewarta Farty ma ai 'yartace tinda k'awar Salma ce

      Anko Salma tasiya Mata na iyaye 25k lace ne sanan Salman ta Kai Mata d'inki a ka zuba Mata stone work mai lfya( abin nema yasanu..lol)


Friends *laiyajey* ce zata masu makeup each dinsu 12k.  bride kuma *I.Laurah*ce zata yimata tindaka garin abuja a ka dauko ta, kowani event 150k ne, event 3 kawai za'ayi  sai yinin biki  Dan mijin Farty bayasan hayaniya sosai 


*bridal shower* suka Fara inda sukai masifar kyau kada ma Farty taji labari *l.Laura* ta fitoh da ita ba kadan bah, kyau d'inda Farty tayi yasa Zeemarh kudira a ranta itama *l.Laura*ce zata Mata .

 Next day akai kamu ranan ma sunyi kyau sunsha pictures kaman babu gobe, Snapchat yayi kuka haka Instagram da duk wani social network datakeyi sun San friend din Zeemarh na aure. Zee ma tazo da yaronta Fahad very cute boy dashi 


    Ran Friday aka daura aure, simple yinin biki sukayi sai dare suka wuce dinner nan ma sunsha kyau ba ka Dan ba Zeemarh, Ramalurv, memxy, Salma,Nussy,Hauwee, Hannah da Amira kaita sai kashe salfie Duke  da Amarya

🍁🍁🍁'YANMATAN ZAMANI🍁🍁🍁




*PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*



*STORY & WRITTEN BY*

~Biebie deee bukhari~





_thank you so much for d love n care Zee zee I really appreciate,stay blessed_💞💞💞💞


9⃣4⃣






""""""Angama komai lfya ankai Amarya gidan ta mai masifar kyau dake u/Rimi,gida yayi kyau haka kayan ciki ma komai dai Masha Allah.




Salma ce kwance da phone a hannu ta,chattn ta ke da wata sabuwar friend dinta Zeezeee a bikin Farty suka had'u, Ummie ce a gefe tana waya,ban Ummie ta gama wayanne Salma tace"Ummie komai na gidan Farty mai kyau ne, sai naji dama haka gidana zai kasance"ta k'arashe maganan tana kallan Ummie, gyara zama Ummie tayi sanan tace" wanan mai sauki ne ina adashi ai duk wata 20k kwasa 300k gakuma kud'in gidan hayanmu na rigasa 150k ne a shekara wanan a account nake zubawa, kuma kema ba zuba ma alhaj.yahya'n ido zakiyi bah dole kik'ara Jan wani Abu a wajan shi kee bama shi kadai ba duk Wanda kikasan xai baki toh ki jaa kinga duk sai muhada, Dan family babanki sunyi wuta su hadamu da 500k kinkuma San ba Isa zasuyi ba Dan haka gara ki rage kashe ku'di baki da aiki sai na siyan kaya, nan kud'in ki ke'karewa, toh indai kinason kayan d'aki irin na yaran manya su Farty dole ki Dage"tinda tafara magana take kallanta Chan tace"kar kidamu Daka yanzu zanchanza salo"Ummie tace da yafi Dan banaso ko gidan Zeemarh yafi na ki duk da dai ubanta na da rai amma banso tafiki" Salma tace kar kidamo kimai zaitafi dai dai, yanzo next week zantura Alj.Yahya Kano Dan magana tayi k'arfi" Ummie tace Allah Kai mu, nayi waya da uncle dinki bello ai" Salma ma tace zasuga biki" Ummie tace na 'yar gata kuwa Dan ni Kai na tsoro zanbasu daka su har 'yan Zaria"Salma tace yan black stomach bah" Ummie tace ai basu ga komai bah wlh"

Haka dai sukai ta hiransu Chan Ummie tafita gidan wata k'awarta,Salma ma kule gidan tayi tanufi gidan su Zeemarh.




Bayan taje ta gaida su mama side Didi tayo, da sallama ta fa'da d'akin Didi ta gani a Palo tana duba wani atanpa bayan su gaisa ne Didi ta kalle Salma tace" tayani duba a tanpanan yanada kyau kuwa"? Ansa Salma'n tayi ta duddu ba sanan tace" wlhy yana da kyau sosai Didi" baki Didi ta washe sanan tace yauwa haka nakesan jii, nima yamin kyau inaso ne naji Ko yan gayu zasuce yayi kyau" Salma tace yayi sosai kuwa" Didi tace" anko na kenan ni da k'awaye na in bikin Zeemarh" Salma tace ah abin nayi ne, anko hada tsoffi" Didi tace bangama tsofewa ba da saura na, bikin Azeemarh guda nak'i anko ai sai Allah yakamani "

Nan Zeemarh ta fitoh tana daria tace" gawas kinga su Didi wai hadda fidda anko ba'asa biki bah" Didi tace ai za'asaka ne" Salma tace Allah Kai mu" Didi ta ansa da amin amin.



D'aki suka shige duk kan gado suka haye Zeemarh tace"jiya su bobo sukazo da dare(al_mansur) da shi da wasu uncle dinshi naso nafada a group toh wlhy yak'i ya barni na huta sai waya mukeyi ko da kikashigima wayan mukeyi"

"Tace Ashe zakirigani nima next week su Alj.Yahya zasu kano,Allah dai yanuna mana lafiya kice zamu bada tsoro bikin Zeemarh guda ai sai muyi bura uba, amma fa za'ayi ruwan *'yanmata* a bakinan keda shegen friends" Zeemarh tace ki Bari kawai nan da nan Salma ta hau online tafesa ma friends da wasu friends dinsu Wanda basa group

Salma batabar gidan bah dai da Ummie ta k'irata nan tama su Didi sallama ta tafi.





*AGURGUJE*



yanzo haka ankawo kayan nagani ina so akwatuna 6 far da kaya ranan Didi tayi rawa ba k'adan ba friends dinta ko Su Deeja da sauransu sai daukan kayan suke ana tura ma jama'a wai tin kafin lefi kenan fa sunan da sukasakama kayan kenan

     Allah keda kulin sai friends din Zeemarh sunzo na yau da ban na gobe da ban gashi duk classy bebs ne babu ruwansu da wani kunya sai da takai har mama tayi magana shine suka rage zuwa amma  friends dinta  na gado kulin suna tare.



Kudi ankon Nata yakesake Mata bana wasa bah, Dan haka Zeemarh ba tada matsala a department dinsu kowa so yake yazo bikin ta saboda yanda take wanna a bikin wasu bare kuma na ta.




Kallan tayayi yace" gidan yayi miki ko a canza wani"?Zeemarh tace nop nan ma yayi 4bedroms ya isheni" smiling yayi Mata pictures ya mik'a Mata na furniture's ne ansa tayi tana k'ara kallan shi gira ya 'daga Mata sanan yace zaba wayanda kikeso nan duk ta xaba,mik'amai tayi yace sunyi maki"? Kai kawai ta 'daga mai kallan ta yayi gami da rike hannun ta sanan yace banaso a kawo ki da komai gidanan daka ke sai kayan ki ni xanyi ma babyna komai kar su baba su wahala hugging din shi tayi gami da cewa" I don't even know what 2 say sweetheart, I love you so very much babe u ar so sweet" al_mansur yace u don't have 2 thank me babe is my duty 2 take care of my sweetheart, I love you more

Breaking hug din sukayi suna saukema junansu wani irin smiling wananda ni *Biebie deee* nace perfect mach Dan wlhy sun dace ba kadan bah dukkansu yan gayu,hannunta cikin nashi suka fitoh suka nufi mota

Sai da ya bude Mata ta sauna sanan yakoma wajen zamanshi ya tada mota nan mai gadi bala ya wangade gate suka fitah 


Sai da suka biya side resort suka ci abinci sanan yakawo ta gida tare suka shiga.   


      Side din mama suka Fara shiga nan taga Ahmad yawani k'ara yau da fresh sai da almansur yagama gaida mama sanan suka gaisa da Ahmed, Ahmad sai wani cin magani yakeyi sama sama suka gaisa ko kallan Zeemarh baiyi ba Dan haushe ta bashi yau 


Side Didi sukayi nan fa Didi akaita zubah Ana washe baki Al_mansur bai bar gidan bah sai da akakusa magrib sanan yama didi 

Sallama game da Mata alheri kamar yanda yasabah




Yau biki saura 2weeks Dan haka a yaune za'akawo lefen Zeemarh, an gyara gida tsaf ko ina sai tashin 'kanshi yakeyi gida yashi fanti da gyara, gakuma abinci mai rai da lfya da snacks da kayan motsa baki iri daban daban da su mama suka bama *Anty hadiza* Dan tayi,abubuwa komai yayi kyau yakuma tsaru, mutace duk Ana zazzaune ciki hadda ummien Salma da Ummie Deeja duk sunsha kwaliya kadama Ummie'n Salma taji labari sai kace itace U'war amaryan

    Hakama k'awayan Zeemarh d'aki guda a ka nasu sai iya shege sukeyi

Da misalin k'arfe 3:5pm ne family ango suka Fara shigowa watau anties dinshi sunsha kwalliya ba na wasa bah nan fa aka Fara tarbansu da Mara'a suma fara'an suketayi, nan wasu Mata su 5 Wanda nake tunan yan aiki ne suka Fara shigo da akwatuna yayinda aka cika su Anty lubabatu,Anty Binta, da sauran su gaba da kayan motsa baki 


   Bayan duk sungama shigo dashin akwatunane guda 24 wato dozen 2 kenan, nan fa aka shiga bude kaya, kayane bana wasa bah, kayane na manya tin Ana 'kirgawa har akadena komai ne 24 tinda kan lece,super wax,super Holland, materials, shadda,jallabiya,Kai  kayane wanan gaskya baza su bafadu ba Dan bama Zan iya typing ba

  Haka shoes n bags  duk designers Dan duk babu irinsu Vinci's da wasu Vine duk babu irinsu sai uban ubansu irinsu Aldo,nine west dadai sauran su a bangarin kayan k'arau kuwa English gold ne da kuma normal gold sai fashion basu uban kyau da tsada,kayan cosmetics kuwa shima duk designers ne komai dai acikin kayan lefinan mai kyau ne kuma masu tsada nan fa friends akaita dauka a waya Ana posting a yanar gizo...lol

  Dubu 50 suka bada tukwici nan Didi ta k'ara 100k (Zeemarh ce ta bata,kud'i ne irin Wanda Almansur kenata taciro Dana account) nan dai sukai godia, basu tafibah sai dazukaje sukaga Amarya Zeemarh Anty lubabatu tace" Masha Allah 'dannawa ya iya zabe ita dai Zeemarh ai gum wai kunya 

 Hakadai suka tafisuna yaba halin girma irin na family amaryan dakuma iya tsara abu duk da bawani ku'di garesu ba amma komai yayi

 Suna tafiya Didi ya bude waje da rawa tana buda Ummie'n Salma ai rasa bakin magana tayi Dan taga abin bana wasa bane




Sada Zeemarh kefada masu baba Almansu yace basai anyi komai bah "cewa sukayi a'a dole ne sumata baba Aminu ne" yace tinda xaiyi ku'di a bata inyaso sai tayi wani abun dashi.

Hakakuwa akayi anabama Zeemarh kudin taje tazubasu a account.




*Rana bata garya* 

Saide U'war d'aya taji kunya inji hausawa yaune akafara gudanar da bikin Azeemarh dakuma Almansur k'awayen Zeemarh Dana gari gari mama daida tayi mamaki Irina 'yartata Dan bata zata San k'awayan na Zeemarh haryakai haka bah.su *Ramalurv,Memxy,feedy*duk sunzo daka abuja banda yan uwanta yan katsina da friends dinta na Kaduna  Kai dawasu ma Wanda a snap da Instagram suka hadu yau sukafara ganin juna.


 Itama *I.Laura*Almansur ya dauko mata dan komai takeso shiyakeyi ku'dinta baya ciwankai ko mai lalle Anty lubabutu ne ta daukota 

Ran *bridal shower* Zeemarh Tasha kyau kar gown TaSA red color mai masifar kayau,kanta yasha gyara Zeemarh kanan kagudu da ita Dan kyau sai friends  duk dressing white sukayi bikin Zeemarh yazagaye yanar gizo tindaka kan pre_weeding pic nasu dama abinda Zeemarh takeso kenan  *biebie nace tasamu*ga masu pictures dipphotos da mai gskiya sai kashe pictures sukeyi hakadai akaci kuma akasha komai gashinan kamar manza sai dare suka dawo wasgegari KAMU

   Ranan Riga da skirt Zeemarh tasa Wanda musanman Anty lubabatu da Anty Binta suka bama HOUSE OF KAYA yayi nayau gamu dakuma na dinner ranan ma tayi kyau har tagaji haka angonta maa

Amarya da ango nashigowa sai friends dasuke bayansu suma sunci anko duk sunyi kyau nan naga *Biebie dee&samrah novel group*duk sunfitoh da phone dunsu wasu na daukansu su  pictures wasukuma video suketayi 

Biki yayi biki k'awayan Amarya sunyi kyau sai kashe pictures akeyi su Hannah, Amira kaita,Deejah,Nussy,Salma, Hauwee,Memxy,Ramalurv, Halema dantabawa,Zeezeee, feedy gasunan dai ' *yanmata*ne babu adadi Farty matazo Zeee ma dakuma Rahma Aliyu haka Ahmad ma matarsh Haleemah haka fiddausee danata friends din kowa yayi kyau

Didi ma ba'a barta a baya bah Dan sai da tazo Ummie'n Salma ko harda tawagarta 

 Abinci kuwa gashinan saidai kagaci da ci haka naga su Ummie auta sai tura meat pie jaka takeyi lol...hakadai akaci aka sha akakumayi pictures akatashi lfya

         *Friday* bayan ansako da kada sallan juma'a ne aka daura auran Azeemarh Abubakar Musa Mani da angonta Almansur sulaumain namanya kansadaki dubu 50k

   Ai tinda da Didi taji andaura tasa rawa feedyce tace ",ddi rawakikeyi bah kida"Didi tace yoo Baku dauko bah" Salma tace su baba ne suka hanna ba laifimu bane"Didi da inna sadiya sukace jakar uba ai bazai yuwu bah musha anko babu duba inji goggo husaina" Didi tace kukira mai kidan kawai ina zuwa "baba tak'ara awaya tace zasuyi rawa babu yanda ya iyya dole yace eh"

        Su didi ansha rawa haka su Ummie Dan mace mai San bidi'ar tsiya.haka dai akaci yinnin Biki su ango  da friends dinshi ma sunzo duk anyi pictures.

           Karfi 6pm akazo daukan amarya,iyaye da yan U'wa sunyi Mata fada  haka mama Wanda saida tayi kuka,haka su baba ma suyi yimatama nasiha mai ratsa jiki sanan aka fufi da ita motan Didi tashiga Dan Didi tace ita zatakai Zeemarh har d'akinta"

Babu b'ata lokaci aka nufi u/sarki Dan Kai Amarya Zeemarh gidantah....










*fatan alkhari ga duk wani makarancin 'YANMATAN ZAMANI Biebie Dee ta gaisheku*






~biebie deee~🌸

🍁🍁🍁'YANMATAN ZAMANI🍁🍁🍁



*PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*



*STORY&WRITTEN BY*

~biebie Dee bukhari~



*I dedicate dis page 2 SADNAF AND AYSHA MUH'D(AUNTY)may Allah guide n protect u nw n forever*❤❤❤❤




_gaisuwa mai tarin yawa gareku 'yan U'wa Rabin jiki_

_Kamar yanda Allah_ _yahadamu a pure moment ina addu'an Allah ya hadamu a gidan Aljannah haka,Allah bar zumici, Allah kuma ya k'ara hada kawunan mu AMEEN_ MUCH LOVE💞💞💞






"""""""""Gidan Amarya Zeemarh gida ne na ban mamaki Dan bazan iya musaltamu Ku kyan gidan ba Ummie Salma motsi takasa Dan taga abun yanaso yayi yawa basu k'ara tabbatar da haduwar gidan ba sai da suka shiga ciki ni *Biebie* nace woww yanda na bude murya wajen k'iran wow sai da Memxy da duk mutanen wajen suka kalleni fuskewa nayi kawai na bisu ciki.komai na gidan mai kyau ne kuma mai tsada direct bedroom din sama akawuce da Zeemarh friends dinta na bayanta shima wanan d'aki abin kallo ne ni dai baxan iya fadaba sabida k'arancin lokaci nan fa 'yanu'wa da abokanan arziki sai zagawa suke Dan ganin gidan bedrooms 4 sai polo 2 na k'asa da na sama sai side mai gidan da ke sama shima Palo da bedroom sai kuma toilet haka dai aita sa albarka.

     K'arfe 7:30 duk yan kawo Amarya sunwuce Dana Anty Fatima, Anty Maryam sai Anty hafsa sai kuma friends dinta bayan mutane suntafi su Salma sufa Fara sagaye gidan, gida kuwa yayi kyau duk sukace ko Ramalurv da Memxy da suke yaran manya sun Lora gidan dan gidan k'arshe ne wajen kyau.



K'arfe 8:15pm Anty lubabatu ta k'ira Anty maryan Dan jin ko Amarya da friends dinta sungama shiri 

  Time din akema Amarya makeup ma friends ma basu gama shiri ba.



Kasancewar mai makeup din ta gwane baifi 1hr ba tagama tsarama Zeemarh kwalliya tafitoh tayi kyau kamar asace ta kafin 9:30 duk sungama shiryawa 

  Motan da ango keciki a kasa Zeemarh friends kuwa ga motoci nan kamar banxa sai wanda suka zaba.

      Kallanta yayi yana saukemata murmushi itama murmushin takemai,hannunta Yakama yashiga shafa xanan lallen gannunata kallanci tayi ido cikin ido tace" bobo na kayi kyau" smiling yayi Mata yace"kema kiyi kyau sosai haka dai sukata hiran soyayyansu har suka isa ceremonial canopies inda za'ayi dinner,already friends da duk sun iso nan Akasa Amarya da ango a tsakiya suka shiga ciikin hall din inda DJ yasamasu waqan I love my baby 

    Waje yayi waje, biki yayi biki komai sai hamdala aci ansha ankumayi pictures Zan iya cewa dinner duk yafi kyau su Salma ansha kwalliya haka Deeja,Hannah, hawwee,feedy,Zeezeee,nussy,Ummie, yan *biebie&samrah novel group* ma ba'abarsu a bayaba sunsha kwaliya 

Fiddause da Mahmud dintama susha kyau haka Ahmad da Haleemah


Hakadai taro yatashi kowa na San barka wasu na adduar Allah sa nasu yakasance haka wasuko zabin Allah kawai suke nema saimuce Allah bada zaman hakurii...




*AGURGUJE*

Yanzo haka anyi auran Salma wanda ko taka k'afar na Zeemarh bai iyaba shinadai yayi kyau Ummie tayi rawar gani awanan biki family dinta har mamakin irin ku'din da takashe sukayi dagin baban Salma ko ido kawai suka samasu.

  Ankai Salma gidan ta dake u/dosa itadai gidan yayi kyau amma baikai na Zeemarh ba,inda kunga Zeemarh lokacin bakin Salma zakuyi mamaki time din watanta u'ku da aure tayi kyau tayi fresh komai ta mai kyau ne ga mota Ana jaa mai uban tsada Didi ko kudi duk yawansu ba matsalar tabace Dan Xeemarh ta tsaya Mata

   Kafin dai su shiga 400lvl duk friends din Nata na gado  sunyi aure Hannah, Nussy,Deeja,kuma dukkansu basu kudi suke aure saidai Zeemarh duk tafi su...





Yau tananeman shekara d'aya kenan da aure a yanda tayi lissafi,Zaune take tana tunanin mijinta Almamsur wanda rabonta dashi tin shekaranjiya kafin ta tafi sch,bai kwana gida ba 2days tak'ira duk numbers finshi switch off,jawo phone dinta tayi dake kan center table trying number shi tashigayi cikin sa'a kuwa yashiga ringing 3 yadau ka

"cewa tayi lafiya baka dawo gida bah sweetheart"? Dana d'ayan 'bagaran yace"kee ni yaron ki ne dazakirika min ihu,ina ruwanki da dawowana gida" fit yakashe wayan

    Bin wayan tayi da kallo tana mamakin abinda Mijin Nata Almansur yace...







_kuyi hakuri da wanan Wlhy banajun dadi daurewa kawai nayi namaku wanan_

   _ina maku fatan Alkhari koda yaushe_

   

*stay blessed  biebie loves you*❤❤❣❣💋💋






~biebie deee🌸

🍁🍁🍁'YANMATAN ZAMANI🍁🍁🍁





*PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*




*STORY & WRITTEN BY*

~biebie Dee bukhari~





_thank you so much for d prayers lovers, really appreciate.I love you all_❤❣❤



*nagaisheki Salma 'yar mutan Gombe nagode sosai da k'aunar ki a gareni,nima ina k'aunarki da duk wani masoyina*💞💞💞💞




9⃣6⃣






""""""""Kwance ya ke sai wata Mace da ke gefenshi k'iranta yasa shi tsayawa daka abinda sukeyi kallan ta yayi Wanda naji yak'irata da teemah yace" kitashi kitafi" 'kin tashi tayi sai wani k'ara shigemai takeyi tsawa ya daka babu shiri ta mike rafan 1000 guda 2 ya dauko daka bedside drw ya jefa Mata ko kallo ku'din bai ishetaba bare ma ta dauka kallanta yayi" yace nak'ara miki ne murguda baki tayi sanan tace"kaikasan ku'di is not my problem, why don't u marry me duk muhuta,duk danasan Kai bamai halin kirki bane amma gara muyi auran a haka Dan nice na dace da matarka bawata stupid girl ba",

   Banza da ita yayi yashige toilet *Almansur Sulaiman Namanya* kenan shi 'da ne ga Alhaji Sulaiman da hajiya Mariya, Alhaji Sulaiman na manya fitacen Dan kasuwa ne, yanada kudi bana wasa bah. Almansur ne kadai 'Dan da Allah yabasu a duniya shiyasa suka dauki San duniya suka daura mashi komai yimai akeyi ba'ayimashi fada ko mai zaiyi kasancewar both family din nashi ba yara garesu ba shiyasa yatashi a sake kuma asangarce, duk karatunshi a an anan autside yayisubah koda yatashi dawowa 9ja sai yadauko duk dabi'un yahudu da nasara shine shan giya,chacha,Neman matan banza da duk wani 'dabi'a bara kyau iyayanshi basasan wanan halin nashi Sam amma babu yanda zasuyi Dan basa iyamai fa'da .

   Ko dayazomasu da zanchan zaiyi aure sunji dadi duk da sunsan yarinyarda zai auran ba 'yar wani da wata bane babu yandaa zasuyi hakasuka yadda dan basasan bacin ranshi Duk da sunsan irin sanda *TEEMARH*takeyimai(yariyan abokin babanshi).

Almansur yaro ne Dan bazai wuce 28yrs bah


Bayan yafitoh daka wankan saida ya'bata lokaci mai tsayi wajen shiryawa, yashiya cikin black pencil trouser sai t_shit mai k'aramin hannu sai ya daura top blue a sama mai long hang kanan nashi yasha gyra inkaganshi bazakataba cewa yayi Aure ba Sam, car key dinsa ya dauka yayi gaba...


********************

Zeemarh ko tinda tagama waya da Almansur taxama mutun_mutumi motsi mai k'arfi takasa kallan phone din kawai takeyi wata *zuciya*ne yace da ita k'ara k'iranshi dazo bashi bane, smiling tayi sanan tashiga k'iranshi, har yagama ringing bai dauka bah,haka taita ki'ra baidauka ba harsai da tagaji Dan kanta sanan ta tashi ta wuce bedroom Dan tayi wanka tashiga sch.









Jitayi gaba 'daya gidan yayi Mata girma, sauri sauri gudu gudu tagama shiyawa car key dinta kadauka tayi sch.







Bayan sun fitoh daka lectures ne Zeemarh ta kalle Deeja tace" mai yahana Salma zuwa sch ney yau"Deejah tace Allah shine mafi sani"Nussy tace Allah sa dai lfya"Hawwee tace amin"yarinyan Farty ce tafara kuka dake hannun Hannah Zeemarh tamiko hannu Zata ansheta nan danan tamiko hannu nan Zeemarh tashiga yimata wasa *iman* sai dariya takeyi kallan Farty Zeemarh tayi tace" plx kibani baby nush mana"Farty tayi dariya tace nayi ya da babanta"?ke kinki sai sisi kawai kikeyi ko amarcin kikeyi har yanzo shine bansani bah,gasu Hanna dasu Salma duk sunkamu" takarasa maganan tana daria smiling Zeemarh tayi tace Allah ne dai bai kawo bah, amma time nayi ni twins ma Zan Haifa duk dariya sukayi Nussy "tace toh sisters ni zantafi coz zanbiya hospital" Deeja tace nima wlh wai baki zaiyi girki zanyi gashi babu matayi shiwai bayasan mai aiki"Zeemarh tace Allah samudace" nan duk sukai sallah ma kowa tashige motanta tayi gida .





Zeemarh gidansu tanufa Dan a anashirin bikin fiddause da Mahmud, nan ta tadda matar yaya Ahmad aunty Haleemah da 'yarta afra  mai shegen wayo da suruto kamarsu daya da Zeemarh. Bayan taje duc tagaisa da mutan gidan nandai suka rubuta list din abubuwanda za'asiyo na biki nan dai sukadan yi hira Da aunty Haleemah sama sama Dan bawani shiri sukeyi bah cikin hiransu ne Zeemarh tace zatatafi da afra gidanta gobe ko jibi sai tadawo da ita sai Haleemah tace wai tak'ira babanta taji.cen Zeemarh "tace so nakema abani afran gaba 'daya”Haleemah tace Abuja xakibishi ko kijira yadawo sai kuyi magana Dan ta waya bazai yuwu bah(Ahmad yanzo a abuja yake aiki yasamu k'arin girma awajen aiki)

   Zeemarh tak'irashi yakumace taje da ita ba damuwa Haleemah najin haka tamasu mama da Didi sallama tajaa motarta tayi gida.Zeemarh bata iso gida basai after 6 wanka tayi ita da afra gami da sallah Already *Salma 'yar mutan gombe* mai aikinta tagama dinner saukowa k'asa dukayi taxubama afra tanabata kadan taci tace bataci nan Zeemarh ta hadata da kayan zaki dama abinda takeso kenan 




Saidatayi sallan Isha sanan tazauna cin abinci inda afra sai wasa takeyi *yar mutan Gombe* kuwa sai hira takema Zeemarh .







Bayan Zeemarh tagama cin abinci waya da dauka tashiga k'iran Salma, sai da tak'irata sau 4 Ana 5 tadauka Zeemarh "tace wai inakigashiga ta alhajj sai k'iranake babu ansa a maimakun Salma tabada ansa sai kuka tafeshemata dashi tashi tsaye Zeemarh tayi tace"lafiya,meyafaru,ko bakida lfyane"? Rage kukan tayi tace Friend Ashe Alhaji yanada Mata gaban Zeemarh ne yafadi dam tace inalillahi wanan maganan bazai yuwu ta wayaba zanshigo gobe insha Allah nan takatse k'iran tana mamaki irin wanan lamari ko da *Salma 'yar aiki*ketamata hira shuru kawai tayi







Sai 10:30 Zeemarh tadau afra ta kwantar da ita SALMA YAR AIKI ma taje ta kwanta wanka Zeemarh tasake gami da sakayan bicci mai kyaun gaske sai kamshi takeyi Palo takoma ta kwanta a 3 siter tanakalan wani film a zee world,bata dade da kwanciya a wajenba bacci yayi gaba da ita.








Bugun 'kofa tafaraji kaman amafarki, buga 'kofan akeyi bana wasabah nan da nan ta tashi tayi wajen 'kofan Dan tabude,tana budewa wazatagani Almansur ne a bige yashawo giya tsayawa tayi abakin 'kofan taki matsamai cikin zafin nama ya bangaje ta tafad'i har yayi hanyan sama sai kuma yadawo janta yashiga yi yanacewa wlhy sai kunbiyani kudina,yama za'ayi kuce kuncinyeni impossible wlhy janta yashiga yi tana tirgewa bata ankaraba taji ya dauketa da Mari gami dacewa muje sai kunbiyani kud'ina ai bashiri tashiga binshi bai ajeta a ko inabah sai cikin bedroom dinda suke kwana daa(Dan banace yanzo ba)hannu yami'ka Mata gami da "cewa give me all my money nafasa game din"nan tashiga dakko duk wani kudi datasan ta ajiye yana ri'ke da ita sai da tami'kamai dukku dadan sanan yasaketa yafita 


D'akinda ta kwantar da Afra takoma sai da ta babbatar ta saka key sanan tazube a kan gadon gami da sauke wani kuka mai tsuma zuciya,kuka takeyi bana wasa ba chan ta tanbaye kanta dama Almansur nashan giya,yana chacha?? Wai ya'akayi banga ko alamaba wata zuciyan tace ku'di yarufe maki ido"haka taita tunana tana kuka har bacci barawo yayi gaba da ita.







K'arfe 4 daidai ta tashi da matsanancin ciwan Kai(Allah sarki Zeemarh)tanan kwance har akayi k'iran sallan asba nan ta rarrafa tashiga toilet tayu Alwala tafitoh window ta leka nan ta hangeshi xai tafi masallaci a zuciyan ta tace"akwai Sallah amma babu hali" wata zuciyanne takuma cewa toh inkana sallan ai anasamaka ran shiryiwa wata rana " hawayene ya zubu Mata tasa bayan hannunta tashare sallaya ta shinfida tashiga sallah ta 'Dade sosai tana addua(abinda batayi da) kafin ta 'dago daka sujadan koda ta idarma sai datayi azkar,tadade sosai tana addu'a sai da gari tafara gske ta kwanta nan da nan bacci yayi gaba da ita 





Bata k'ara tashiga sai 9:43am shima Dan Afrah ta tashi ne,kallan Afrah tayi Tamata  smilliig itama Afran smillig take Mata toilet tayi da ita direct brush tayimata gami da wanka sanan suka fitoh shiryata tayi cikin wani shot gown baby Afff tayin kyau  sosai chocolate tabata sasan itama tashiga wanka bata jima sosai bah ta fitoh, shiryawa tayi cikin gown na atanpa 'dinkin A Shep, kayan yazauba ajikinta sosai ko powder bata saka ba ta dauki Afra sukai k'asa Dan yin breakfast, tana da lectures 12pm kum






     Bata yi tsamanin yanan ba kitchen ta wuce ta dauko Dan k'aramin cup wan da zata hadana babyAff tea, zamatayi a 'daya daka cikin kujerun sanan ta aje Afra kan 'daya tea tahada Mata sai tosted bread nan tashiga bata k'adan Tasha wai batasha kuma kallanta Zeemarh tayi "tace zan maki bulala fa" maimakon Tasha sai daria kawai take Mata itama Zeemarh daria tayi" tace zakisani  Afra ce tayi magana tace"mami shiweet Zeemarh tayi dariya tace" see your moth like shiweet,sweet not shiweet" tashi tayi da niyar daukoma Afra sweet daji ance "where ar u going"rudewa tayi nan da Da nan jikinta yafara rawa duk tarasama mai zatace  mai phone dinshi yadauka yana dannawa tanan a tsaye Afra ko tanacin pala wasanta taketayi kallanta yayi yace "samin abinci"nan tashiga zuba mai bayan ta gama tawuce sama da sauri  








Koda taje bedroom bayan ta daukarma afra kayan tsakinta abinda zata bukata ta dauka sanan car key tafita. Yaban inda ta barshi kitchen tashiga tama SALMA 'YAR AIKI sallama tafitoh nesa da shi kadan ta tsaya tace "Zan tafi sch" banxa da ita yayi sai tapping phone dinsa ya'ayi  zatakuma magana kenan yace" what d u want"tace banida mai a mota kuma motan nadan bani problem 2days" bai kalleta bah sai cemata yayi kisiiya ai kina da ku'di bai tsaya jin abinda zatace ba yayi gaba.









Kafin sufitoh har yawuce a ranta tace da dane fa shi zai kaini har sch amma ji yanzo gaba daya ya chanza,Afra tasa a mota itama tashiga suka tafi sai databiya ta bank ta cire kud'i sanan tayo sch.







Yau ko su 3 Kai sukazo Ita,Deejah sai Farty abin yabata mamaki bayan sunfitoh ne Zeemarh tace zataje taduba Salma nan Deeja tace zata farty kuma tace zatakai baby iman hospital batajin dad'i amma su gaisheta sukace zataji Allah ba babymush lafya" Farty ta ansa da anin



Motan Zeemarh suka shiga kasancewan Deeja batazo da natabah,tana zaune a gefe sai babyAff a ba tana surutanta gidan Salma sukayi direct a u/dosa, suna isa mai gadi yabude masu gate suka shiga bayan sunyi parking ne duk sukafitoh 

    A palo suka taddata dagani Tasha kuka kamar ba Salma yar gayu bah, tana gansu taje tayi hugging dinsu bayan takawo masu juice da cake ne Zeemarh" tace duk kingama wata kalla" Sakma tace ba dole bah Alhaji yahya dai Ashe matan shi biyu nice ta uku gashi yahanani xuwa sch ku duk yanda kukasan shidai bah haka yakema bah zan iya cewa hutun wata shida kawai nayi a gidanan nafara fuskantar bakaken halinshi, ga ruwa ga bakar mako da mugun hali, yaki daukarmin mai aiki ga cikinan nabani wahala" Zeemarh tayi shuru tace mukuma tamu kaddan kenan" Deeja tace wlhy koni hakane rowa yakemin ba nawasa ba da nayi magana yace ai da naci, dai dai da man mota ninakesiya dana yau ba sarki sai Allah nace nahakura" Zeemarh tace naku da sauki nifa Almansur masayi ne sai tafashe da kuka nan duk dukai ta bata hakuri bayan nan Zeenarh tace kilallabashi yabarki kicigaba da zuwa sch kibah komai zaki temaki kanki dakuma ummie"Zeemarh tace kifadama Ummie sai tarokeshi" Salmatace nanawa kuma ya raina Nata ai sai yagadama"Deejah tace insha Allah zai yadda" 

"Salmatace Allah sa motanama ko mai babu kuma nasan babani zaiyi bah" Zeemarh ta zuge jaka tabasu 5k dukkansu  tace"gashi kowa tayi manage nima cikin kud'inane da su baba suka bani nakayan d'aki sai Wanda Almansur yabani da,nasan yanzo abubuwa xasu chanza Dan yau ko ku'din manmota yak'ibani"Deeja tace ai mungode wlh, wai ace mutane duk sunchaza kuma bawai Dan basudashi ba"Salma tace rabon mumukacinye tin a waje"Zeemarh tace mudage da addu'a insha Allah,Allah xai yayemana"duk suka ansa da Allah sa" nan suka ma Salma sallama suka tafi,

    Suna tafiya Salma tak'ira Ummie tana bata labarin kyautan da Zeemarh tamata  sai godiya takeyi, nan tafadamata shawaranda suka bata Ummie" tace  zatak'irashi taji,inyace ma bazai biyabah ai sai akarasa biya daku'din hayan gidanmu" Salma tace Allah sa mudace nansukai sallahma



*****************

Al'amari na Almansur gaba yakeyi ba bayaba kulin Zeemrh cikin kuka takeyi gashi sisin nairansh yadena bata ga sha'anan bikin Fiddause. 

   Tafadama Didi damuwanta Didi tayi mamaki matuka da wanan hali na Almansur dakucema Zeemarh ta Dage da Addu'a Allah yamata zabin alkhari *ni biebie* nace AMEEN FA

  



shirye_shiryen bikin fidaudee aketayi da Mahmud ko naira 'daya Almansur bai ba Zeemarh bah yaushema yake kwana a gidan bare har ta tanbyeshi saide cikin ku'din ta dauko 50k sai wani lace da tasiyarmawa k'awar 100k  Almansur ne yakawo Mata lokacin suna zaman da'di shine tahada 150k tabada

       

Ahmad yayi rawar gani sosai a bikinan komai shiyayi Dan yanzo Ahmad Alhmduulillah yayi ku'di komai mai kyau da tsada yasiya ma fiddause(mahakurci mawadaci)haka muhmud yayi kokari sosai komai dai Masha Allah

    Anyi biki da komai lfya kuma yayi kyau babu wani k'arya sai abun ya birge Zeemarh, duk ta gaiyace k'awayenta kuma duk sunzo amma banda Hannah da Nussy Hannah mijinta bai barinta fitah Nussy kuma ba tajin dadi

      Ankai Amarya fidause gidan ta a marafa 3bedrooms gida yayi kyau haka kayan ciki ma..






















~biebie deee~🌸

🍁🍁🍁'YANMATAN ZAMANI🍁🍁🍁





*PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*



 *STORY&WRITTEN BY*

~biebie deee bukhari~


9⃣7⃣




"""""Yau inbata manta bah 3moths kenan da yin bikin Fiddause,amma Allah haryabata ciki, haka duk friends dinta gashi har sunkusa hyhuwa, ita KO tanan babu ko alama wanan Abu yana damunta duk DA tasan komai na Allah ne.tashi tayi ta haura sama,sch zatashiga sabida project dinta.


Zeemarh gaba 'daya ta chaza,tadawo very silent and simple.da tagama da sch, gidansu ta nufa bayan side mama Murja tafara shiga ta Dade sosai sanan tashiga wajen didi suka gaisa   nan didi kefada Mata Anty Haleemah batada lfya ta k'ira ta gaisheta,  sanan tawuce side din mama nan duk tayi xamanta har aiki tayima mama,sai Albarka mama kesamata Zeemarh taji da'di sosai, sai bayan sallan magrib da tagaisa da su baba sanan tamusu sallama tayi gida.



Tadawo gida da tunani fal a ranta bayan tayi sallan isha taci abinci bata tsaya jin surutun Salma 'yar aiki ba ta haye sama abinta,kwanciya tayi abinda yafaru tin kafin auranta tashiga tunowa da kallan tsiyar da tayi duk dan kar ta aura Ahmad, gashi Wanda ta aura yanzo auranta dashi bai tsinana Mata komai bah sai nadama da kuma danasani datakeyi ba tinyazu bah ita kanta tasan tana San yaya Ahmad amma San abin duniyanta dakuma reasons dinta na manza yasa ta makanta ba'kin ciki auran mai ku'din mai yimata komai,

   Ina ma takeganinshi,

  Tamanta 1lst da ku'dinshi yashiga hannunta ita kema manta komai, ah hakama wai gara ita da Salma ita Salma gatadai a gida mai kyau amma komai Ummie keyimata duk Kansu auran masu ku'din bai musu komai bah, share hawayen ta tayi Wanda yagangaro mata, phone dinta ta dauka tashiga Neman layin Yaa Ahmad ringing 3 ya dauka 

     Zeemarh tafara sallma cikin dauriya tace"Assalamu'alaykum"

Ahmad"wa'alaykissalm,Azeemarh kina lfy?yakuma gida"

"Lfyalau,ya jikin Anty Leemarh"

Ahmad yace toh Alhamdulillahi"

 "Toh Allah k'ara bata lfya,ya babyna"?

Ahmad yace Ameen amen,Afra nan lfya"

"Zeemarh tace toh ashafamin kanta, kuma agaida antyleenarh"

Bata tsaya jiran mai zaice bah ta kashe wayan.


Shiko Ahmad wayan yabida kallo yanakuma tuno yadda takemai magana kaman wani Abu nadamunta,tanbayan kanshii yayi toh mekeda munta?mai ku'di takeso kuma ta aura yanasane da duk wani k'aryan Aljanu dataketayi lokacin yanasane Aljanun k'arya ne danshi ba jahili bane yagane dalilin tanayin hakan shiyasa yasamata ido yakuma hakura da ita amma bawai dan baisanta ba, duk dadai abinda tamai yamai ciwo sosai amma yama kanshi al'kawarin k'iranta time 2 time dahakane zai gane damuwarta.






   Zaman Zeemarh a gidan Almansur zamana na kunci da ba'kin ciki dan lamari na Almansur kulin gaba yakeyi saidai kawai mommy shi da su Anty lubabatu suta bata hakuri dan sunsan tana fama

  Kwana 2 nanma batacika xAma a gida bah sabida savice din datakeyi A wani government sch KO  antashi kuma gida takewucewa 

 Ita kanta mama tagane 'yarta tanacin damuwa

dan taga gaba 'daya ta chanza Randa mama tanbayeta kasabama mama ansa tayi sai kuka kawai datakeyi,shuru mama tayi chankuma "tace didi tasani kuwa"?Zeemarh tace ehh" mama tace shikenan kiyi shuru Zan tanbayeta naji" addu'a mama tabata takumace tacigaba daneman zabin Allah" Zeemarh taji dad'i sosai har sanyi sai datajin a ranta takumayi nadamar abinda ta aikata a baya.



Koda didi tafadama mama halinda Zeemarh keciki ta tausayamata sosai takumayi alkawarin yimata addua.




Hakarayuwa taita tafiya abubuwa da yawa sunfaru game da rayuwan gidan Zeemarh dan yanzo su baba duk sunsani haka Ahmad ma da sauran yayenta ,Ahmad duk yafi nuna damuwanshi a kan lamarin.

    Hakadai Zeemarh taketahakuri sometimes kuma tasha kukanta Salma yar aiki bata jin dadin gidan Sam dan tasan antynta ba dadi takeji ba, tadai yi alkawarin tayata da addua dan shine kawai mafitah.

   


Allah ya sauka Salma lfya tasamu baby girl, tashi wahala sosai alhaji Yahya yarage mugun halinshi dan wanan Karon yadanyi abin kirki,ranan suna anyi dan abubuwa babu laifi yariya taci sunan sister alhaji Yahya wato rabi'a su Deeja,Hannah,Nussy,Hauwee duk da cikin su Zeemarh ne dai shuru, sunji dadin haduwa da junansu sunk'ara bama junansu shawara dakuma hakuri Farty matazo itadai batada matsala(kusan dama k'arfi ba daya ba) Amira kaita kuwa yanzo tana Dubai tana masters dinta 

    



Zancigaba anjima wlhy nagani🤣🤣🤣🤣

 KO zaku k'arasa da kanku????

Inajiran ansankuu

🍁🍁🍁'YANMATAN ZAMANI🍁🍁🍁




*PURE MOMRNT OF LIFE WRITER'S{P.M.L}*




*STORY & WRITTEN BY*

~biebie deee bukhari~


_this page is dedicate ga duc wani makarancin 'YANMATAN ZAMANI,  ILYSM all_❣❤❣❤❣


9⃣8⃣





""""""Haka dai akaiyi taron suna a katashi lfya,sai da su Zeemarh suka gyara maa Salma gida tsaf sanan dukkansu sukai nasu gidan.




Abubuwa da yawa yafaru ciki hadda gama sevice dinsu,fiddause ma takusa haihuwa,su Hannah ko duk sun haihu, yau a gida ta yini.

Zeemarh tadawo gida agajiye lis, dan 2days din nan batajin da'din jikinta

Bayan tayi salla da wanka palon k'asa ta dawo ta zauna nan fa Salma yar aiki tashiga zubo Mata surutu kamar radio mai jiini..lol

Zeemarh sai jinta  takeyi tana daria sai k'arfe 10:30  Sallma tama Zeemarh sai da safe tawuce dan kwanciya tea taha'da dan baza ta iya cin rice bah.


Tanan zaune har 11:00mp jitayi Ana tura 'kofan da k'afi zuwa tayi ta bude,hanya tabashi dan yawuce amma sai ya tsaya komawa tayi 2siter ta zauna aranta tace yau bai sha ba kenan, zama yayi a gefenta yace" bani ruwa" tashi kawai tayi bata ansa shi bah,tana kawo mai ruwan tayi hanyan sama hannunta ya ri'ke yace" what d u mean hum"kallanshi tayi cikin rashin fahimta gira ya 'daga Mata ko'karin kissing dinta yakeyi tayi fuskan ta gefe, jawota yayi da k'arfin kaske yace"hala kinmanta matsayi nane a wajenki,mijinki neni ko yaya nake dole kiyi abinda nakeso bai tsaya bi takanta ba yashiga yimata abubuwa da k'arfin gske kuka kawai Zeemarh keyi wani tsanar Almansur ne na musanman yak'ara shiga zuciyanta shigo baimasan mai takeyi bah abinda yagadama kawai yakeyi Chan ma daukanta yayi yai bedroom da ita.

 


Bayan komai yalafa Zeemarh Tasha kuka tayi nadama  babu adadi, dalilin kukantane ya saukarmata da ciwankai magani Tasha bacci  ya dan dauketa.


Ko da asbah data tashi sallah, da ciwan kai ta kuma tashi hakadai ta rarrafa tayi sallah tak'ara kwanciya,sai k'afe 9 tafarka shima k'arar wayanta ne yatasheta Yaa Ahmad ne kek'ira nan da dan ta dauka sallama tayi mai gami da gaisheshi, ansawa yayi sanan yace"meke damunki naji voice naki somehow diriricewa Zeemarh tayi chan tace banajin dad'i ne dogon nunfashi yajaa sanan yace" kishirya kije wajen doctor'n haleemah doctor buhari a prime hospital, zank'irashi nafada bashi zuwanki"Zeemarh tace toh nagode Allah bar zumici Allah shirya maka zuri'a" Ahmad ya ansa da amin 

Yaji dadin addu'an sosai murmushi yayi ya aje phone kan bedside Haleemarh ne ta shigo cikin d'akin zamatayi a side dinshi gami "dacewa abbanAff breakfast yayi ready fa" kallanta yayi yace sweetheart wats wrong wit u" leemarh tace nothing"gami da tashi hannunta yarike k'ara zaunar da ita yayi yamaida duk hankalinshi kanta sanan yace"tell me" hawayene yazubo Mata durkusawa yayi a gabanta yana share Mata hawayen chan tace"am pregnant sweetheart, amma kasan problem din,wlhy inaso na haihu da kai sosai kodan kyawun hakinka amma kana naka Allah na nashi"kuka takuma sawa hugging dinta yayi gami da shafa bayanta a hankali yashiga yimata magana a kunne" stop crying babe, insha Allah nothing will happen 2 dis time, inma cikin bai zaunabah munada enough time ai babyafff baby ce still,just 2n half yrs so please kibar kuka banaso yanada kyau k'arban kaddara mai kyau da Mara kyau" 'dago da kanta tayi tace"hakane insha na bari, amma inaso yaxauna cikinan" hancin ta jaa yanacewa"in mungama brkfst sai muje muga doctor" ta ansada yes sir" dariya yayi yaja hannuta sukatafi yin brkfst.




Itako Zeemarh bin wayan tayi da kallo tana mamakin kula irin nashi,tashi tayi tanufa toilet wanka tayi sharp sharp tafitoh tashirya tayi hospital.


Doc.Buhari yadubata yakuma cemata tarage damuwa magunguna yabata nan Zeemarh ta mai complain din rashin samun cikinta bayan anmata duk gwajin da yakamata doctor yace tadawo gobe nan tamai sallama tayi gida 




Su Ahmad sunje asbiti doctor yace babu wani problem zata haihu da yaddan Allah,da'din wajen Haleema ba'a magana haka Ahmad ma _saimuce Allah_ _raba lafiya_





Dawuri tashirya tayi hospital bayan sun gaisa kallanta doctor yayi yace"bincike yanuna mijinki na anfani da wani magani Wanda ciki bazai taba shiga bah,so yanzo dai tinda kekinshirya haihuwa saikije kisamu mijinki kimai magana" tinda yafara magana inalillahi kawai takeyi wasu hawayene yazubo Mata babu shiri ta gogesu gami da mikewa sallama tama doctor tayi gaba tana fita doctor yak'ira Ahmad ya fadamai komai ba k'aramin girgiza yayi ba tausayinta ne yakamashi a ranshi yace dole nashiga kd dis week ina San ganin wanan hatsa bibin Almansur din.



Itako Zeemarh gidansu tayi direct,palon mama Amina ta zube kuka takeyi gami dacewa"natuba kuyafemin hakkinku kadai bazai barni nazauna lfyaba,kutemakeni kuce kunyafemin ko zansamu salama arayuwata" mama Murja ce tazo ta rungumeta, mama ta tausayamata matuka bayan mama Murja ta zaunar da ita, Zeemarh tacigaba da cewa"tin da nafara girma bantaba ganin abinda kukemin ba,kulin burina bai wuce naga inasa komai mai tsada ba,bai wuce naga ina rike ku'dade bah,bai wuce naga nafi kowa bah, bai wuce naga nakai kaina inda Allah bai kayni ba, ashe komai da komai na Allah ne, mama Tasha bani misali da fiddause bana gani, gashi ita tanacikin kwanciyar hankaki nifaa? kulin damuwa abubuwanda nake tunani duk ba haka bane Ashe" kukane yaci k'arfinta tayi shuru duk kansu shuru sukayi kallamun na Zeemarh ya ta'basu cen tacigaba da cewa"ina ro'konku da Girman Allah kuyafemin bazan iya fadan laifin danayi bah, amma ina baku  hakuri wlhy natubah" 

Baba ne yayi gyran murya yace "Alhamdulillahi hakamukeso kuma ni Abubakar mahaifinki nayafe maki duniya da kuma lahira" hawayen farin ciki ne yazo ma Zeemarh tace" nagode sosai babana hakika kai mahaifine nagari Allah yaja kwana yak'aro lfya mai anfani"duk suka ansa da amin

Mama ta daura dacewa nima Amina mahaifiyarki nayafemaki duniya da lahira"dama abinda naketaso kigane kenan komai lokaci ne a rayuwa,kuma indai kasa San a abin duniya a rai karinka ganin ba dai dai bah kenan" Haka kowa yace yayafe didi ko shuru tayi dan Al'amarin na Zeemarh addu'a yafi bukata.



BYan angama yafiya nan Zeemarh taciro takadda tamik'a ma baba tashi tayi ta tafi side din didi,tashiga d'akin kwanciya tayi dan ta huta jintake kaman ansaukemata babban dutse a kaa.



Bayan su baba sun duba takadda nan sukeganin ashema hadda hawan jini da yad'an kamata sanadiyar tunani ai nafadama didi tasa kuka gami da cewa"wlhh bazai kassaramin jika bah, yakasheta a banxa damai zataji?shangiya ko chacha da meman matan banza?dole yayi anfani da magani mana dan kar yatara shegu, wlhy bazai yuwu bah dole tabarmai gidanshi,ishara iya ishara naganshi tinda a wani bangaren nice *SANADI*dan Hakka dole asan abinyi dan komaii tayi tanada hakki akanmu"kallen mama Murja tayi tace kinada nabar lubabatu ko Binta antishi ai"?mama tace eh" Didi tace samin anan na 'daya daka cikinsu"ansan wayan mama Marja tayi tasa Mata nan didi tashiga k'ira ringing 3 ta dauka bayan sungaisa didi tace"kakar Azeemarh k'ara gaisawa sukayi sanan didi tafada Mata komai,hakuri kawai Anty Binta taita bayarwa didi tace"yaxama dole kuzo aiyi magana dan yarinya bazai taitazama da aure ba"Anty Binta tace zasuzo gobe insha Allahu" 


Tana gama waya da Anty Binta Ahmad tak'ira ta fadamashi yanda sukayi da antyn Almansur din yace zaizo gobe shima nan duk sukatashi 



Didi tadawo d'aki Zeemarh na bacc kallanta tayi taga duc ta rame tashinta tayi dan taci abinci takumayi salahn la'asar.


Bayan taci abinci tayi salla ne didi tafada Mata yadda duk sukayi Zeemarh tace Allah kaimu lfya"

*********************

Koda Anty Binta ta k'ira hajiya Mariya ta fada Mata yanda sukayi da family Zeemarh kasa cewa komai tayi dan batasan inda zata ga Almansur ba bare har tamai magana daurewa kawai tayi ta ansa da toh Allah kaimu.


  Number mai gidan ta Alhaji sulaimai tak'ira bayan yadaukane take fadamai abinda kefaruwa" cematayayi tabari yadawo suyi magana".



Sai bayan sallan magrib ya iso gida, bayan yayi sallah yakuma ci abinci yashiga Neman layin Almansur cikin sa'a yasamu Alh.yace"kazo inasan kaginka"

"Almansur yace saide zuwa wajen 10 inzani gidan dan yanzo am busy"

Alh.yace Allah kaimu"

     Haka sukai ta zaman jiranshi sai 10:40 yashigo babu ko sallama alh.yarufeshi da fada yace" wai kai yaushe zakayi hankaline?,kashigo waje babu ko sallama bare gaishuwa" Almansur yace nifa sauri nakeyi" yana maganane yana 'kokarin tashi,koma kazauna mahaifin nashi yace"

  Kallan shiyayi nan yashiga karantumai abinda ke faruwa fuska ya 'bata yace"toh wai daddy mai zNyi ne" hajiya Mariyace tace" my boy inbakasanta kasaketa kawai kowa yahuta kafin suzo suce kayi abinda yafi wanan ma" bace komai bah d'akinshi na gidan ya nufa babu 'bata lokaci yarubutama Zeemarh saki batare da tunan komai bah,yanagama rubutawa yayi Palo wajen iyayen nashi a center table ya ajiya gami da cewa gashinan a kaimata bai jira mai zasuce ba tayi gaba abinsa.


Dafe kai alhaji yayi itako hajiya Mariya motsin kirki takasa Alh.yakaleta yace Allah ya sa adalilin sakinnan yaronan ya shiryu,gobe indan Allah yakaimu sai k'ira Binta kifadamata abinda yafaru ta ansa da Allah kaimu cikin sanyin murya



Koda safe Da Haj.Mariya tafamasu abinda yarafu Anty luba "tace sai dai muje tare hadda ke abasu hakuri dan sanin kankine abinda yayi bai kyauta ba"haj.Mariya tace bakomai ai sai muje.



K'arfe 2 daidai su Anty Binta suka Isa gdan su Zeemarh, sunshiga da sallama gabada side didi duk aka hadu Ahmad tin 12 narana ya iso bayan anyi gaishe gaishe ankuma basu abin motsa baki su Anti Binta rasa abincwa sukayi didi ce taganosu tace"ai karkudamu inma dakardane Allah sa hakane Alheri nan su Anty Binta suka mik'ata kadda dami da k'ara bada hakuri su mama sukace ba komai haka Allah yayi Allah sa hakane alkhari duk suka ansa da amin nan sukai masu salmasu tafi.

 Aranan Ahmad yasa aka kwasuma Zeemarh duk wani kayanta nasawa dakuma takardun makarantanta kayan gida dama banata bane,sanda akadawo dakayan tayi kuka tayi nadamar abinda tayi abaya nan dai ta lallashi kanta yayi shuru.

     

Rayuwa yayi gaba   Allah ya sauki fiddause lafiya tasamu ibahim khalil,su Salma sanda sugaji ansaki Zeemarh na tsuwace ta k'ara shigansu suma babu laifi yanzo abubuwa na tafiya Alhamdulilahi,sunsamu aiki suna taimakon kansu damuma iyayensu subarma Allah komai abinda yabasu dashi suke tak'ama sunrage bink'awaye babu ruwansu.

  Zeemarh ko yanzo watanta 2 da mutuwaan auranta babu inda takezuwa dan ita bata nemi aikiba tukunan,babu abinda takeburi yanzo da yawuce Yaa Ahmad yadawo gareta,da tadauki abun Abu mai sauki Ashe ba hakabane dan yanxo Ahmad bayawani sakarmata fuska daka gaisuwa sai kaisuwa abin  namatukar damuta sosai, ganan zatasama kanta tunanine tayanke shawaran shiga islamiyya 

Haka ko akayi Zeemarh takoma islamiya tana karatu sosai dan damuwanta yaragu sosai.

 

Cikin Haleemarh yanata girma saidai yau lafiyane gobe babu haka dai taita rainuncikin har ya Isa haihuwa.


Yau kwananta 2 kenan tana labor har anashirin yimata c.s ne haihuwar yazo Tasha wahala sosai kafin ta haihu akasamu babyboy.


Bayan angyrata ita da baby ta nan Ahmad yama yaro huduba da sunan mahaifin halemah wato isma'i taji dadi sosai nan da nan yashiga k'iran yan U'wa.


Ta haihu da kwana 2 suka dawo Kaduna su didi da Zeemarh kaman jira suke nan fa suka bazama ganin baby Zeemarh jitake kaman itace ta Haifa d'an, dan dad'i haka didi ma nan fa Zeemarh tashiga hidima da maijego da yaranta kulin tana hanyan zuwa gidan kafin suna sunyi wani irin sabo da haleema,fidausee ma tanazuwa kulin Khalil yayi wayo sosai.



Ranan suna anyi shagali Ahmad ya kashe ku'di sosai Zeemarh duk tayi inviting su Salma kuma duk sunzo haka duk friends din Anty Leemarh duk zeemarh ce takula dasu maijegoma Tasha kyau haka taro yatashi kowa yana San barka.


 Anyi suna da kwana 'daya ciwan ciki yakama Halermarh nan da nan Akai asbiti da ita nan likitoci sukafara aikinsu.Zeemarh ta tsorata sosai da Ciwan haleemarh ga  isma'l(boy sunanda Zeemarh tasamai)sai kuka yakeyi abanyanta dole madara tabashi sanan yakoma bacci


Sai k'arfe 9 nadare Haleemarh ta farka Ahmad ne a daya Daka cikin kujerun d'akin sai   kuma didi a gefe d'aya salati tafarayi sanan tace ruwa zanansha nan da nan didi tazuba tabata 

Bayan ta shane didi ta taimakamata ta zauna kallan didi tayi tace"dan Allah didi in bantashi ba Ahmad ya aura Azeemarh itace kawai zata kulamin da yarana kuma shima yanasanta nasani ai" Ahmad ne yatashi yace wai maihaka ne anata lfya kina ta wani aure kuma?,insha zakitashi"murmushi tayi tace nidai nafada ma kai koma ina Raye sai ka aureta,didi kina sheda ai" murmushi kawai didi tayi Ahmad yace"naji toh kwanta musmushi takuma mai tace nagode" komawatayi ta kwanta.



Damisalin k'arfe 10 nasafe Allah yayi ma Haleemarh rasuwa...Allah akbar.... 












~biebie deee~🌸


_inaganan sakon wayanda kesan kanin picture na follow me on Instagram_ 

@biebee__ or add me on Snapchat @ biebah3 


*much love*❤❤❤❤❤❤❤




_masuyimin messages kuk'ara hakuri nakusa insha Allah_🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀


,

🍁🍁🍁'YANMATAN ZAMANI🍁🍁🍁





*PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*

     *{P.M.L}*



*STORY & WRITTEN BY*

~biebie deee bukhari~




_this page is dedicated to All members of Biebie Dee novel thank you for d support, love and care ILYSM_❤❤❤❤❤❤



9⃣9⃣




""""""Allahu Akbar hakika rasuwan Haleemarh ya girgiza kowa dan yarinya ce mai ladabi dakuma biyayya, bata 'dauki duniya da zafi ba Sam.


Bazan iya fadamaku halinda Ahmed yashiga ba a wanan lokacin mutuwar ta bigeshi matuka haka didi da duk y'an gidan



Zeemarh Tasha kuka, sabida Ana gobe Haleemarh zata rasu wasiyya taitamata da tarikemata yaranta amana tabar Mata su har Abada k'arungume boy tayi tana zub da hawaye takuma kudira aranta zata rike su har *karshen rayuwarta*



Mommy ko mahaifiyar Haleemarh ba k'aramin tawakkali tayi ba duk da tasan tayi rashi 'ya tagari amma babu yanda zatayi Wanda yafi Santa ya daukayan sa,haka k'anen haleemarh sunji mutuwar 'yar uwarsu dan tana kyautata masu ba kadan bah.




Sai da duk wani d'an U'wa na jiki yazo yayima Haleemarh addu'a, mummy kasa fita tayi  sai a cikin d'aki tamata addu'a takuma Samata Albarka Mara adadi. 



Damisalin k'arfe 11:30 ne aka kai haleemarh gidanta na gaskia, sai a wanan lokacin Ahmad yafara hawaye shikanshi yasan yayi rashi babba

_sai muchai Allah jikan haleemarh da Rahma AMEEN_


Gidan su Ahmad ake 'karban gaisuwa dan haka 'yan uwa da abokanan arxiki sai zuwa ta'aziya sukeyi, ba'abar yan *Biebie Dee novel group* abaya ba mota guda duka zo gaisuwa dan suma Haleemarh ta mush alkhari.


Anayin sadakar uku kowa Yakama gabanshi, akabar Zeemarh da yaranta Afra da boy(isma'l) 


Tinda Halemarh ta rasu Ahmad yazama shuru_shuru gashi Afra naganinshi zatafara cewa daddy"ina mommy" saidai  yace mommy tayi tafiya"




Yau watan Haleema biyar da rasuwa Boy yayi girma sosai haka Afra ma suna samun kula sosai a wajen Zeemarh dan yanda take kuladasu ko kanta albarka.


Tsakaninta da Ahmad gaisuwa ce har yanzo inyayi magana mai tsaye" shine babu wani matsala ko" 

Ita tariga ma ta cire rai da wani Ahmad  tabarma Allah komai.



Yau Friday Zeemarh batada islamiyya, shiri suketayi zasuje wajen mummy mahaifiyar marigayiya, Afra sai da'di takeji za'aje yawo 

Tagama shiyasu tsaf itama ta shirya kanta sunyi kyau matuka,sallama sukama mutan gidan suka tafi.





Mummy taji da'din ganinsu sosai haka sisters haleemarh ma fauzeeya da fa'izah sai daukan boy sukeyi, sai k'arfe 4:30 sukama mommy salama suka fitoh.


Bayan sunrabu da Fauzeeya takoma gida,wata motace tayi parking a gabanta,Kama hannun Afra tayi suka matsa gaba,   

Jitayi nanacewa "dama kinhaifamin baby shine ko a sanar da mu"

Juwowa tayi danganin ko wanene AL_mansur tagani,matsawa tak'arayi sanan tace" Ashe shaye_shayen naka ya haukatar da kai haka"matsowa ya k'arayi yace"dan Allah Zeemarh kiyi hakuri nasan ban kyauta ba, amma please give me another chance" harara mai lafiya tabashi sanan tace" Wlhy ka haukace, ai ko zakabani duniya da kayan cikinta bani bakai" 'kokarin durkusawa yakeyi tai maxa tashige napep sukai gaba.

*toh pha*🙄🙄😂😂 AL_mansur manya mota yashige yabi bayan napep din da gudun gske.




Zeemarh nashiga gidan d'aki tashige da gudu didi ne tabiyota "tana cewa keko lfyanki"

 "Zeemarh tace wlh Al_mamsur nagani hadda cewa wai ashe na haifamai yaro" 

Dariya didi tayi sanan tace" lalle baida hankali, yamanta maganin da yake anfani dashi kenan"



Wayanta ta dauka tashiga k'iran Ahmad, fita tayi a d'akin dabataso Zeemarh taji mai zatace,ringing 2 yadauka didi tace" toh dama akan magananku da Zeemarh ne, inbakasan ta nabata daman kula masu Santa" gabanshi ne yafadi cewa yayi" nifa banasan haka, zan shigo kadunan gobe sai muk'arasa magana"

Didi tace" dayafima"


AL_mansur ne ya iso gidan yaro ya aiko "wai Ana sallama da Baba" didi najin haka tasa hijab tafita,daka gefe taganshi gaisheta yafarayi ai ko ansawa batayi ta fara zazzaga mai masifa, kasa magana yayi hakuri kawai yakebata ai kamar k'ara zugata yakeyi saidatayi mai  isarta sanan tace kadawo gobe, godiya yayi Mata yatafi.


Ai didi nakomawa gida Ahmad tak'ira ta fadamai "wai AL_mansur yadawo kuma da alama ya chanza hali dan haka tace ma yadawo gobe"


Sandarewa Ahmad yayi wani haushin didi yakamashii number Zeemarh yashiga Kira abinda yadade baiyi ba,sai da yamata 3 missed call 

Jefar da phone yayi gami da "cewa Didi hooo"😡




K'afe 9 a Kaduna yamai bayan ya gaisa da iyayenshi side Didi yayi bedroom yayi direct Zeemarh ya hango sai rawa takema boy Afra  ma namai, yadade sosai a wajen yana kallansu sanan yashiga jikawai tayi ance " ina kika yadda wayanki" diriricewa tayi Chan tace nifa bansani bah" na'kiraki ai baki daukaba" kallanshi tayi gira ya d'aga mata😉 

Smiling kawai tayi Chan yakuma cewa" banbaki daman kula kowa ba" shirutayi bata ce komai bah daukan isma'l yayi Afra a bayanshi suka fita.



Tsallen murna Zeemarh tasaka didi ce tashigo tanacewa" wai mai hakane kodan Jan ajii babu" Xeemarh tace kaku bazakigane bah"



Sai k'arfe 10 AL_mansur ya iso yaro ya aika, Baba yace yashigo bayan ya gaidasu cikin ladabi da biyya ne yace" yanaso yamai da Zeemarh yayi nadama Yakuma chanza hali,insha Allah babu abinda zai k'aa faruwa, yadora dacewa Ashe ta haihu bamusani bah"?

 Dariyansu na manya Baba yayi sanan "yace ai ba yaron ka bane, ko kamanta musababin mutuwar auran ne"?AL_mansur jiyayi kaman k'asa yabude yashiga  dan kunya,bakai da magana ba Ahmad yafado d'akin sai da ya k'ara gaida baba sanan  yace" ai da ka barshi yatafi baba dan munriga mum sasanta kanmu da Zeemarh" kallan shi Baba yayi batare da yace komai bah, Didi ce tashigo tace" hakane kuwa dama so nakezuwa anjima nayi muku bayani" nan dai Baba yaba AL_mansur hakuri,Ahmad ko lallanshi baiyi bah

Haka AL_mansur yatafi jiki a sanyaye .




Iyayan nasu ba k'aramin dadi sukaji da wanan labari ba, haka mama Amina taita sama Ahmad Albarka  nan dai aka tsaida ranan  daurin aure Friday mai zuwa tinda abin duk na gida ne.



Duk wanan Abu da aketayi Zeemarh bata sani bah tachan da yaranta,sai da dare suna zaune da Didi nan didi ke fada Mata yanda akayi rungumeta Zeemarh tayi tacewa" ina sanki yar tsohuwa ta"


Cikin Daren Zeemarh duk tafadama su Salma,Hauwee,Hannah, Nussy da deeja sun Mata murna sosai ba k'adan ba haka fiddausee ma taji dadi sosai.


********************

Gyra sosai takesha ciki da waje dan mama da hanta ke Mata haka mama Murja ma didi kuwa ba'a magana.


Shakuwa mai k'arfin gskene yakara shiga tsakan Zeemarh da Ahmad soyyan da sukeyi a cikin  1week dinan ko rabinshi basuyi da ba.


Shiye shirye akeyi bana wasa bah, murna wajen wanan family ba'a cewa komai,duk wani shiri nabiki da Ummie Salma akeyinshi babu ruwanta yanzo tsakanta da 'YAN MATA sai Allah kawo miji nagari. 



*Rana bata k'arya*sai dai uwar d'iya taji kunya, yau Friday kuma a yaune aka daura auran *Ahmad Aminu Mani da mamaryasa *Azeemarh Abubakar Mani*



Sai anjimankuu





_gaisuwa mai tarin yawa garwki masoyita Salma 'yarmutan gombe, ina Alfahari da samunki a matsayin k'awa Allah barmu tare_

🍁🍁🍁'YANMATAN ZAMANI🍁🍁🍁



*PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*



*LAST PAGE*

1⃣0⃣0⃣




_I dedicated this page 2 all members of PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S,Allah ya barmu tare yakuma k'ara hada kanmu AMEEN_


*Aysha Ali Garkuwa*

*Aysha Gana*

*samrah*

*Biebee*

*Ummie Garkuwa*

 *Zee yabour*

*Sadnaf (lalata)*

*Jannart*

*Hussnah Bauchi*

*zahrah. Surbajo*

*Nana fu'ad*

*Xarah*

*Deeja waziri*

*Ummeen Yusrah*

*MSB*

*Maryerm Abdool*

*Mommyn sultan*

*Anty khady*

*Rafee"at D/dikko*

*Mrs hamisu taura*

*salmah*

*Sumybash*

_kai wlhy kunada yawa,gashinan page d'inan nakune duka_



   




"""""And'aura aure lfya mutane da dama sun halarta  d'aurin auran,Ahmad baki yak'i rufuwa dan murna,haka Zeemarh ma,Didi ko hadda taka rawa dan murna.




Zeemarh tayi kyau bana wasa bah,kana ganta zakasan tana cikin farin ciki Mara musaltuwa,k'awayen ta na asali duk sunzo Salma,Deeja,Hannah, hauwwe,nussy,Farty 


Fiddausi gayya tayi ba kadan bah dan ita sai yanzo tasan sis dinta tayi aure .


Didi bata yadda bah sai da tasa aka d'auko DJ tayi rawa ba k'adan bah,ba'a bar yan *Biebie Dee novel group*,a baya ba suma sunzo sunkuma sha rawa.



Mommy da su fauzeeya ma duk sunzo Afra ma Tasha Kyau duk inda Zeemarh tayi tana bayanta.


Washegarin daurin Aure ne aka shirya gagarumin walima a k'auna garden inda mama ta gayyato Aunty Aina'u(Ummu abdulnair) tayi wa'azi a kan halin *'yanmatan*mu nayanzo 

"Tayi k'ira da surika godema Allah a duk halinda suka samu Kansu,banda kai kansu inda Allah baikaisu ba,banda bin k'awaye bargate dan anan ne ake haduwa da b'ata gari,banta rokon saurayi ku'di dan yana zubda mutinci,sukasan ce masu kallon na k'asa dasu ba na sama  dasu ba,kiyi kwaliya yanda za'asan ke mace ba ballagaza ba,ta kuma daura da cewa duk abinda zakiyi kina buduruwa ba madauwami bane, lokaci ne kawai gidan miji shine zama na har abada sanan ta k'ara Kira sosai a kan YANMATA dasurike mutinsu su akarshe tayi k'ira da iyyaye da sukara sa ido sosai a kan amanar da Allah yabasu _Allah sa mudace ya karemu yakuma tsaremu Ameen_

     Zeemarh jikinta yayi sanyi matuka sai taji kaman Ummu Abdul nasir da su takeyi haka su Salma godiya suka k'ara ma Allah da ya yayemasu damuwan su sunkuma dauki Alkawarin bama yaran su tarbiyya mai kyau.

  Haka akaci akakuma sha sanan akai addu'a sanan Akatashi walima.



Sai da Akayi d'aurin aure da sati d'aya sanan Zeemarh ta tare gidan ta dake u/Rimi dan tace baxata zauna a Abuja bah su boy ko mommy ne tayi gaba dasu gidanta sai Zeemarh dan kwana 2 za'amaido su.


   Har cikin daki Didi takawo Zeemarh sannan duk sukayi gida dama bawasu mutane da yawa bane.


Sai k'arfe 9 dai Ahmad ya shigo gidan sai da yayi Addu'a ya kulle gidan sanan yanufi d'akin  Zeemarh 

   Wanka zata shiga sai gashi hugging dinta yayi sosai magana yakeyi Mata a kunne Wanda bansan meyakecewa ba naga dai Zeemarh sai murmushi takeyin

   Bayan duk sunyi wanka sallah yajasu na nafila raka'a 2 bayan sun idar kanta yadafa yaita zuba Addu'a daka k'arshe yashafe.


Shida kanshi yabata   nama da frsh milk dayashugo dashi.


Sai da ya k'ara masu Add'a sanan suka kwanta, Ahmad da Zeemarh sun raya wanan dare cikin kwanciyar hankali dakuma soyya na gskia

*asuba nagari*


Soyyah sukeyi bana wasa bah kowan ne su bai San bacin ran d'an uwan shi.



Yau sati uku kenan da tarewar Zeemarh rigima takemai wai ita a dawomata da yaranta kallan ta Ahmad yayi yace" zamu dau'kosu anjima dan week dinan gaba d'ayanmu  Abuja zamu koma bazan iya zama ni kadai ba matata na wani U'wa duniya"

   Dariya Zeemarh tayi tace" kai sweetheart Kaduna ne U'wa duniya"? 

   Gira ya daga mata gami da cewa" baxakigane bah yarinya" haka dai sukai tahiyan su har sai da aka Kira salan magrib sanan Ahmad yatafi masallaci 

 Yana tafiya itama Salln tayi  yana dawowa suka nufa gidan mommy a nan suka tadda Daddy yazo wajen fauzeeya dama (tin bikin Ahmad da Zeemarh suka hada Kansu) 

 




Mommy nasiha ta k'arayi yi masu godiya sukayi Mata suka dauki su Afra suka nufa gidansu.

  Sai da sukaje side iyayensu suka gaishesu Daka k'arshe suka yada zango a side Didi nan Ahmad ke fada Mata xasu koma Abuja gaba d'ayansu Albarka tasaka masu sanan tace" dole asamo mai Aiki dan rainan su boy, sai 10 na dare sukama yan gida sallama sukai nasu gidan.



 Watan su hudu da Aure Xeemarh ta Fara laulayi Ahmad duk ya rude, sai da cikin ya girma sanan ta dawo normal, hakadai sukai ta rainan ciki har ya Isa haihuwa bata sha wahala sosai wajen haihuwa ba nan dai Zeemarh ta haufo baby gal San kowa kin Wanda baisamu ba..lol

Murna wajen Ahmad a cewa komai haka Afra da boy dan yanzo bai yayi wayo sosai shekaranshi d'aya da wata 4

 Ta haihu da kwana 1 suka dawo kaduna nan yan U'wa da abokan Arziiki sukai ta zuwa barka.


Ranan Suna yarinya taci suna Haleemarh murna wajen wanan family ba'acewa komai su fauzeeya ne abarorin (dan har anyi bikinsu da daddy) 


Haka friends  din Zeemarh dasu akai komai suna yayi kyau anci ansha dan Ahmad ya kashe kudi haka dai taro yatashi kowa yana San varka.


*******************

AL_mansur gyra halinshi halin yanzo ma sunyi aure da teemarh kuma suna zaune lafiya.



K'awayen na Zeenarh ko kanne tana zaune lfya a gidan ta da yaranta, basu da wani matsala sai wnda ba'a rasa bah.




*Bayan shekara 8*

 Watou in kuka ga Zeemarh bazakugane taba tayi wani fresh ta k'ara kyau da kaganta kaga batar manya ga kyau ga kuma naira.


Iyayansu ko duk sunkaisu makka,umara duk shekara

Tsakaninsu da yaran Add'ace kaawai dan suna kyautata masu  ba'kadan ba.



Zaune suke dukansu A babban Palo boy da Leemarh suna game,

 Afrah Da twice Bilal da Hilal tana koya masu Home work  

  Zeemarh ne tashigo palo sanye take da Riga da wando irin na sport 

 "Oya sport guys daddy na jiranmu"

 Afra ce tace" yeee wlhy ina gidan daddy"

  Boy yace mami am wit you" shafa kanshi tayi .

Tace "yes my son"

 Da gudu Zeemarh ta bar Palo duk suka bita A baya.


Inda zakuga yanda   Ahmad da  Zeemarh  da yaron su keyin basketball dinan zakuyi mamaki barin ma Zeemarh ko jikinta bataji

 Bayan sun gama wanka duk sukayi suka nufi family house dan gaida iyayen nasu Dama duk weekend suke zuwa


  Anan suka tadda faddause da yaranta nan fa Yaran suka bude sabon shafin wasa ina  cikin haka sai ga dddy da Anty fauzeeya sunzo.

Yusuf ma da matanshu nabila sai Hassan da Husain da aketa shirye shiyen bikin su yanzo 

 Nan duk aka baje a Palo Ana hira, Didi sai zuba take kanan ruwan fanfo,haka yara sukai ta rashin ji ga filinan enough dan tini yaran suka siyama iyayen nasu babban gida,haka dai akai ta hira sai dare kowa yayi gidanshi.



Soyyyan Ahmad da Xeemarh bazai fadu bah yanajij da ita haka itama yaransu kuwa Kansu ahade Zeemarh na kula da su Afra sosai dan basu taba maraici bah.

Yaran Zeemarh uku Haleema ce babba sai twice Bilal da Hilal sai kuma k'aramin ciki Wanda bamusan mace bane ko namiji _sai muce Allah raba lafya_


 *ALHAMDULILAHI*

Anan nakawo k'arshen litafina wato *yanmatan zamani*Abubuwan da nafada ba daidai ba Allah ka yafemin.

   Allah kuma yasa za'ayi anfani da darasin dakecikin wanan littafi Ameen.




_gaisuwa tamusanma ga_

_BIEBIE DEE&SAMRAH NOVEL GROUP_ 

 _HOME OF NOVELS_

_RAZ NOVELLA~2_

_SADNAF NOVELS_

_ZEEE&HUSSY NOVEL GROUP_

_MIEMIEBEE NOVELS GROUP_ 

_FADELA LAMIDO NOVEL GROUP_

_RUKKY&ASBAH NOVEL GROUP_

_EXCUSIVE NOVELS GROUP_

_STYLISH HAUSA NOVEL_

_HUSSANAH ONLINE NOVEL_


_DAMA WAYANDA BAN ANBATA BA DUK INA GAISHEKU FATAN ALKHARI KO DA YAUSHE_




_Bazan matanta da  kubah_

_Salma_

_Anty rabiela maman arfa_

_Anty Aina'u Ummu abdulnasir_

_Zee zee_

    _Nagode sosai Allah barmu tare meen_

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *