Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Monday, October 19, 2020

Yar bautar kasa Complete Hausa Novel

adsense here
Yar bautar kasa Complete Hausa Novel

 Compiled by Princess Aysha Muhammad

Copied by Umar Dalha


*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad Mahmud



*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*



*Bissimillahirrahmanirrahim*


Da sunan Allah Zan fara Da sunan shi zan gama insha Allahu.


Kada wani ko wata ya juyamin labarina ta kowacce siga in hakan tafaru nabar mutum da rabbil alamin.


Inkinji wani abu dayayi dede da rayuwarki arashi ne dan labarina ƙirƙirarre

              *1*

 



Salma ƴa ce ga malam hadi me walda da faci,suna zaune a garin kaduna cikin wata unguwa da ake kira hayin rigasa.


Malam hadi mutum ne me taƙawa da tsoron Allah duk da talaucinshi kullum cikin yiwa Allah godiya yake,dan wata rana ko,abinda zasu ci gagararsu yake.


Matarshi ɗaya da ƴaƴa biyu,Rakiya shine sunan matar tashi,wacce ƴaƴan ke kira da Umma,se Sahabi wanda shine babban ɗansa,sannan Salma,wacce tazama ƴar auta sabida daga ita Allah be ƙara basu haihuwa ba.


Salma ƴar kimanin shekara Goma sha shida,ta kammala makarantar secondry da ƙyar sabida iyayanta ba masu ƙarfi bane,amman suna da zuciyar  neman nakansu,tun tasowar Salma yarinyace da ta ɗauki ɗabi'ar ƙarya tasa a ranta,tana da rawar kai ga tsiwa da rashin kunya,bata da buri daya wuce ace gata a jami'a tana karatu uwa uba kuma ace ta zama ƳAR BAUTAR ƘASA,wannan shine fata da burin Salma


Da kyar tasamu tayi registration ɗin jam,kuma Allah ya taimaketa taci,tasamu Admission a Zaria,wato A,B,U,in kuka ga yadda kan Salma ke rawa zaku ɗauka har tashiga ma ta gama.


Duk wata kadara da iyayanta suka mallaka ita suka siyar,suka biya mata kuɗin registration,murna gurin Salma baa magana.


Tun shigar Salma jamia idonta ta ƙara buɗewa ta fahimci ba ƙaramin cutarwa bace data kasance ƴar talakawa,sam kalarta ba kalar talauci bace,sabida haɗuwa da tayi da ƙawaye ƴaƴan  masu kuɗi.


Salma duk wani abu da ake kira kyan sura ba abinda Allah be bata ba,tana da kyau na bugawa a jarida sede wani ikon Allah duk da wannan kyau na,salma sam bata da farin jinin samari,dan ko saurayi bata dashi,wanda ita anata ganin talaucin data  taso acikine yasa samarin basa kulata,hakanne yaƙara haddasa tsanar talauci a zuciyar Salma duk wani abu daze daidaitata da ƴaƴan masu kuɗi shi takeso kuma takeyi,matsalarta ɗaya bata da irin suturarsu,wannan shi ke kawo mata cikas a rayuwar datasa kanta aciki.


Abu dayakai abu Salma har sata tafarayi,kana sake da kayanka tuni zata gyara musu zama,in shaddace se takai a rina mata taci gaba da sawa ba me cewa tashice,inkuma atamfa ko materials ne se takai acanja mata ɗinki,yadda duk ƙwaƙwar mutum yasha Ƙarya yace tashi ce.


Satar takalmi da jaka kuwa ta jima dayin,degree a wannan fannin sede idan bata ganiba,shigar ta ce tasa ɗalibai ƴan uwanta ke ɗauka ƴar masu kuɗi ce.


Muje zuwa.


Surbajon kuce.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION


*See yourself as a light and you will shine,there is no one without a past,Don't be a prisoner to your past,move on, Allah is your witness*




*2*


Haka rayuwar salma taci gaba da tafiya,acikin jamia,har zuwa lokacin data kammala aka turasu service.


Salma tafi kowa ƙosawa ayi posting ɗinsu,har addua take sunanta yafito a verge A, Allah kuma yataimaketa sunan nata yafito inda aka turata garin keffi,cikin jahar nasarawa domin gudanar da bautar ƙasarta acan.


Salma sam bataso aturata keffi ba,Abuja taso akaita inda idonta ze ƙara buɗewa ,sosai.


Zaune suke ita da wata Aminiyarta,me suna Firdausi,wacce aka fi sani da fee-fee,makwabciyarsu salma ce,yarinya me natsuwa da kamun kai,sam halinsu yasha bambam da salma Allah ne de kawai ya haɗa jininsu suke ƙawance tun daga yarinta,makarantarsu ɗaya,ko hutu akayi tare suke tafiya,sede ɓangaran da kowa ke karanta da bam,ita firdausi,business admin take karanta,yayin da salma take karantar medical doctor.


Hira suke game da tafiyarsu bautar ƙasa,inda dukansu gari ɗaya aka turasu cikin hukuncin Allah,wato keffin ɗan yamusa.


"mtssuu,nide fee-fee gaskiya keffin nan bataminba,wlh,nibanma taɓa jin,sunan garinba inbanda da aka turamu can"salma ta faɗi cikin yanayin damuwa.


Dariya feefee tayi sannan tace.


"In banda abinki,Salma meye abun damuwa aciki mude ba iyakarmu  in mundawo daga inda muke service ɗin mu koma kamp ba,nide yamin wlh dan inason dama indunga zuwa garin da ban saniba"feefee ta ƙarasa zancan cikin dariya.


Tsaki salma ta ƙarayi,sannan tace.


"Ni wlh Abuja naso aturani,idonka zefi buɗewa".


"To inbanda abinki,ay tsakanin keffin da Abuja ba nisa,ɗari biyar ne kuɗin mota,sannan garin keffin fa,ance garin ƴan boko ne sosai,kuma babban garine,dan yawancin maaikatan garin ma a Abuja suke ayki,akwai manyan masu kuɗi a garin sosai,dan har ɗan takarar gwamna garesu agarin,sunan shi wadada,kinga ko in ace ƙaramin garine bazaa sami hakanba".


Murmushi  salma tayi tace.


"feefee,duk wannan bayanin a ina kika sameshi,naga kema kince bakisan garinba?"


"hhhh kede akwai sokuwa, kinmanta yaya nasiru acan yayi service ɗinshi?ay duk shine yabani labari,kinsan ko ba halinshi bane ƙarya bare ince ita yamin"


Farin ciki ne ya mamaye zuciyar salma sabida ta gamsu da bayanan feefee,dan tasan yayan feefee nasiru ba maƙaryaci bane.


Da wannan hirar da sukayi da feefee ne salma ta samu ƙwarin guiwar,tunkarar garin na keffi.


Shiri iyayanta suka mata sosai,gamida dayi mata nasihar taji tsoron Allah,takama mutuncin kanta,salma harda kuka na munafunci kamar ta yarda da shawarar iyayan nata.


Haka,suka kamo hanyar keffi ita da sauran ɗaliban da aka turasu garin.


Sanda suka shigo garin Abuja salma ji tayi kamar tace a sauketa a garin,dan haɗuwar garin,haka tanaji tana gani aka wuce garin batare da an tsaya ba.


Da la'asar suka isa, NYSC camp dake garin keffi.


Ranar lahadi ne dan haka masauki aka basu kamin gobe monday su gana da mahukuntansu.


Da kyar salma ta yarda ta kwanta,da dare yayi dan ita burinta,tafita ta zaga garin taga yadda yake.


Feefee ce ta hanata fita,amman ranta be soba,haka ta kwanta tana mita dan ba haka tasoba.


Washe gari da safe duk suka hallara a inda zaa faɗawa kowa inda zeje yayi aykinsa.


Babban Asibitin gomnati na garin aka tura Salma,me suna.F,M,C.


Tun daga bakin gate ɗin Asibitin salma ta fahimci asibitin babba ne duba da yawan jamaar dataga suna shige da fice aciki.


Haka taje tayi clearing komai aka nuna mata ɓangaran dazata dunga wakilta,inda babban likitan gurin bayanan yana ƙasar jamus,inda yaje wata seminer da aka haɗa ta manyan likitoci.


Muje zuwa.


Maman yusuf.


*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*3*


Yau da wuri salma ta tashi tayi wanka ta tsuke acikin uniform ɗinta na nysc,kaisu tayi aka rage mata tsawo da faɗin wandon,hakan yasa intasaka,wandon baya sauka har ƙasa,daga sama kuma ya kamata inda hips ɗinta ya bayyana sosai acikin wandon,haka itama rigar ta kamata sosai,bata ɗora ta samanba,hular kawai tasaka ta saki gashinta baya,se wani uban glass data rufe idonta dashi.


Tana gama shiryawa ficewa tayi,a waje suka haɗu da feefee,cike da mamaki feefee take kallon shigar salma,wacce ita feefee ɗin harda ƙaramin hijabi tasaka,kamin tasaka hular.


"Salma kinada hankali kuwa,wannan wacce iri ɗabia ce don Allah,yanzu da kikayi wannan shigar meye marabarki da arniya?karfa bautar ƙasa tasa kimance da tarbiyar da iyayanmu suka bamu".


Dariya,salma tayi sannan tayi ƙasƙas da cingam ɗin dake bakinta,sannan tace.


"banga laifinki ba dan kin faɗi hakan,danke kinga kinada farin jinin samarine shiyasa,niko ko kare be taɓa tsayar dani yace yana sonaba,dan haka dole inyi shigar dazan bayyana kyawun,surata ko Allah zesa wani yaganni yace yana so,ni kinga tafiyata nakusa yin latti"


Tana kaiwa nan tasa kai tayi ficewarta tana juya mazaune gamida karkaɗa na shanunta.


Feefee binta tayi da ido gamida jin ƙyamar hali da ɗabiun salma,adduar shiriya taimata sannan itama tanufi gurin nata aykin.


Salma ko tafe take a ƙafa tana baza takunta,wanda duk inda tawuce seta bar maza da baki buɗe amman ba wanda Allah yaba ikon yimata magana.


tana isowa bakin titi tsayawa tayi jiran masu mashin dan garin na keffi babu napep sede ƴan achaɓa.


wata arniyar motace tazo tawuce tagabanta da gudu,miyau ɗin salma seda ya tsinke gameda haɗuwar motar,jitayi dama tatace, har motar ta ɓace salma bata dena binta da kallo ba.


Jiki asanyaye tahau mashin tanufi gurin aykin,koda tashiga asibitin gabanta taji yana faɗuwa haka ta daure ta ƙarasa ɓangaransu,ba ƙaramin gigicewa tayiba da ganin motar data wuceta ɗazu a parking space ɗin gurin.


Shiga ciki tayi sede tayi mamakin ganin kowanne maaikaci yamaida hankalinshi kan,aykinshi saɓanin da da kowa ke shagalinsa.


Gurin wata nurse ta nufa tace mata.


"mary lafiya kuwa naga duka kowa ya natsu?kode wani patient ɗinmune ya mutu?"


Jawota gefe mary tayi sannan ta raɗa mata akunne.


"oga,ne yadawo un expected ɗazu ya shigo"


"Waye oga kuma?dahar zesa kuyi irin wannan natsuwar waye shi?"


Toshe mata baki tayi sannan tace.


"Babban doctor ɗin gurinnan shine yadawo daga seminar daya tafi"


Ido salma taware sannan ta kaɗasu cikin wani yanayi,sannan tace.


"ok badamuwa,amman kuncika tsoronshi dayawa sekace mala'ika"


"Nide baruwana kije ki kwashi gaisuwa,ga office ɗinshi can,kuma wlh kitaka ahankali bayason raini ko kaɗan,kuma beson surutu,gashi ke kuma shegen surutu ne dake,kuma shine ze dunga kula dake har kigama abinda yakawoki"


Dariya salma tayi sannan tajuya tanufi office ɗin da mary ta  nuna mata.


Da sallamarta ta tura ƙofar office ɗin tashiga,wani niimtaccen ƙamshine yadaki hancinta wanda ko baa faɗa mata ba turaren me tsadane.

idontane yasauka kan ɗan ƙarfen da ake rubuta suna dake,ajiye akan table ɗin dake gabanshi,wanda shi kuma yajuyawa table ɗin baya,yana jujjuyawa kan kujerar.


*Doctor Najeeb Hassan Alkanawi*


shine sunan data ga an rubuta ajiki.


a hankali ta furta,"Wow nice name".


Guri tasamu tazauna batare data jira ya amsa sallamar tata ba bare akai ga yabata izinin zama.


zamanta keda wuya taji wata murya wacce tunda take bata taɓa cin karo da namiji me daɗin murya irintaba.


"how dare you,to come to my office,and sit without my permission?get out right now,mtsssu useless"ya faɗi batare daya juyo yakalli koma wayeba,d ƙamshin turaran daya jine yas yagane macec ta shigo office ɗin,sabida turaran na matane.


Salma jikinta har ɓari yake tamiƙe tafice daga office ɗin zuciyarta namata zafi,kuka takeyi,sabida tunda take baa taɓa cin mutuncinta irin hakaba,take taji tsanar likitan tashiga zuciyarta me tsanani.



muje zuwa Surbajoce duk wuya duk runtsi.

👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA



Zahra Muhammad Mahmud


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION


*A jawo,A jawo,inde Ilahu ya riƙe farkon,wlh babu me iya tsinke zarena,zahra surbajo ce har abada#haka nake,aman wuta nake na ƙona kiɗa 🤷‍♀*



*4*


Guri tasamu a inda babu yawan mutane ta zauna tana share hawayenta,tsanar doctor ɗin naƙara shiga zuciyarta.


Mary ce tazo wucewa,taganta,da sauri ta ƙarasa gurinta.


"corper salma lafiya naganki zaune anan ko har doctor ya sallamekine?"ta tambayeta cike da kulawa.



Tsaki salma tayi sannan tace.


"wannan ɗan akuyar likitan bashida mutunci,karkiga irin korar dayamun ta wulaƙanci,kawai dan nashiga office ɗinshi batare daya bani izini ba harda cemin useless fa"


"kema salma me yakaiki,tun kamin kijefa seda na faɗamiki likitannan bayason raini kuma shi agurinshi abinda kikayi raini ne shiyasa yamiki hakan"marry ta faɗi fuskarta ɗauke da damuwa.


Wani tsakin salma tasaki sannan tace.


"can ta matse mishi,ni ze nunawa son girma uban waye beso a girmamashi,sallamafa nayi masa ma be amsaba".



Dariya mery tayi sannan tace.


"can ta matse mishi kode can tamatse miki,wlh kece zaki ɓata takardunki abanza,shiko aykinsa yake wahalarsa ta ƙare,yau inkika bari yatashi bakije kun ganaba wlh kin kaɗe".


Shuru salma tayi tana nazarin maganar mary,ita bawai karatun dazatayi asara bane yadametaba,babban tashin hankalinta ace yajawo an koreta a bautar ƙasa shine kawai tashin hankalinta.


jiki asanyaye ta juya takoma office ɗin,ta dunga sallama be amsaba seda takusa minti Ashirin atsaye sannan ya amsa yabata izinin shiga.


a ɗan tsorace ta shiga tasamu gefe ɗaya ta rakuɓe,bakinta na rawa tace.


"good morning sir".


ko kallonta beyiba yanata rubuce rubuce awani file sannan yace.


"who are you?"ya tambaya sanda ya ɗago ido yana kallonta.


wow ita salma ta faɗi,dan likitan kyanshi yakai kyau ta koina,duk da tanajin tsanarshi aranta amman hakan be hanata ganin shi da kyau ba,dan duk hassadarka ga wanda bakaso kasha ƙarya kace ɗuwawunshi ɗaya ne.


"am salma hadi,from A,b,u zariya".


ƙara ɗago ido yayi yana ƙaremata kallo,sannan ya yamutsa fuska yace.


"da kyau,amman ke ba musulma bace ko?"ya jeho mata tambayar batare daya kuma kallonta ba.


Ran salma inyayi dubu ya ɓaci,gameda rainin wayon da likitan yakeson yimata,amman dole tayi wani abu akai dan bazata barshi yaci bulus ba.


Murmushi tayi tana ɗan sosa kanta alamar jin kunya,sannan tace.


"Doctor kenan,ashe da gaskene da akace duk likitan daba musulmiba inyaga musulmi yana ganeshi,wlh se yanzu nayarda da hakan,da ban yardaba,se gashi naga misali akanka tunda gashi kallo ɗaya kamin ka gano ni musulmace,"takai ƙarshen zancan fuskarta ɗauke da keeler smile.


ko kallo bata isheshiba bare tasa ran,zenunamata ɓacin ranshi.


cugaba yayi da rubutunshi,seda yagama tsaf sannan yamiƙe ze fice,seda yakai bakin ƙofa sannan yace.


"Ƙarfe bakwai dot ake hallara agurin ayki,ko ranar sunday ne sede ki haƙura da zuwa service a ranar inkika kuskura kika ɓata lokaci koda minti ɗayane,zan koya miki hankali da yadda  ake magana da manya,duk da cewa ranar friday ba zuwa nakeba sabida masallacin jummaa dazanje,ki yi hattara,am najeebullahi Alkanawi,bana ɗaukar raini".


yana kaiwa nan yafice yabarta a office ɗin se juye juye take tabbas ta lura seta nuna mishi kalarta ta aynihine ze kiyayeta.



Tajima a officr ɗin tana tunani,kamin daga bisani idonta ya sauka kan wasu kuɗi dake zube akan table ɗinshi ƴan dubu dubu,wanda da gani tasan mancewa yayi dasu agurin.


Cike da faraa ta ƙarasa gurin kuɗi ta kwashe ƙirgasu tayi taga ten thousands ne,da sauri ta turasu cikin bra ɗinta ta fice daga office ɗin tanajin yau take sallah agurinta dama kuɗinta ya ƙare.


Tofa🤔


Surbajo ce har abada ba fashi.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*Gareku masoyana,don Allah,don Annabi,duk inda kukaga anzageni,karku ramamin,kubar mutum,da halin shi,kamar yadda kuka saba bani haɗin kai kuci gaba na in kunga sakon zagin kubarshi can inda kuka gano shi,karku damu da zagin nasu kamar yadda nima be dameniba,Sabida abun kunyane ga zaki ya tsaya musayar yawu da ɓera,surbajo ce#haka nake,atare abuge ba dama,abari in wuce ga haushi,Allah kaimin komai har Abada Alhamdulilahi*


*5*



Cike da farinciki salma takoma camp,tun a hanya ta tsaya ta sayi duk abinda bata dashi sannan ta ƙarasa.


Feefee tayi mamakin ganin salma da kudi wanda tasan bata dasu,dan haka tambayarta tayi.


"Salma ina kika samo kudi haka?"


Dariya tayi sannan tace.


"Tsinta nayi a gurin aykinmu"


"wacce irin tsuntuwace wannan,ta kuɗi me yawa,kuma waya faɗamiki,in ka cinci kuɗi ya zama naka ,ko cigiya nasan bakiyiba haba salma abun da kikeyifa be dace ba"


"To uwar ile,nide na tsinta kuma nakashe,karki dameni kuma,ke komai mutum yayi idonki nakai,pls kiɗan rage sa ido don Allah mtssuu"


Feefee bata sake magana ba,illah zuba mata ido da tayi.


Washe gari da asussuba salma ta shirya,ƙarfe shida tanufi gurin ayki,acan bakwai taimata.


A ɓangaransu ta riga kowa zuwa,dan haka office ta shige tayi zamanta.


Bata jimaba tafara jiyo hayaniyar mutane a waje,tana nan zaune marry ta shigo.


"Ah salma kene da sassafe haka kamar wacce ta kwana anan?"


Tsaki salma tayi sannan tace.


"Wannan ɗan balain ne yace kar in bari bakwai tayi banzo gurin Aykiba,shiyasa kika ganni anan da wuri"ta ƙarasa maganar cikin yanayin damuwa.


Dariya marry takeyi harda  tuntsurawa sannan tace.


" kin faɗa tarkon doctor,kita addua Allah ya rabaku lfy,dan bashi da daɗin shaani sam".


Shuru salma tayi kawai tan nazari a zuciyarta.


Doctor Najeeb se ƙarfe takwas ya iso asibitin kai tsaye office ɗinshi ya shige,yana zama,ya kunna computer dake haɗe da cct camara,dan ganin abinda ya wakana kamin yazo,


Ba ƙaramin mamaki yayiba sanda ya hangi salma tana kwashe kuɗin daya bari akan table jiya,wanda shi inbanda yanzu daya gani yama manta da kuɗin,sosai yayi mamaki,aranshi yace.


"she is so beautifull,but ba hali me kyau,iwill make sure that i play with her intelligent"yayi want keeler smile ta gefen bakinshi.


Jin doctor yazone yasa salma miƙewa tanufi office ɗinnashi,sallama tayi baa jimaba ya amsa yabata izinin shiga.


Tana shiga taga ya ƙureta da ido,har tsarguwa tayi ta kama ƴan soshe soshe alamun rashin gaskiya.


"have a sit".


taji yace,jiki a sanyaye tazauna,ta gaisheshi ya amsa.


Daga haka bece mata komaiba yafara duba marasa lafiya,wainda suke matane,kasancewarshi, doctor,wasu tambayoyin in yana yiwa patient ɗin har kunya suke ba salma shiko ko ajikinshi,itade tana sauraronsu tana jorting a littafinta na abinda take ganin bazata iya riƙewaba.


be dakatar da duba marasa lafiyanba,se da azahar,dan haka miƙewa yayi yacire agogonshi yashiga toilet yayi alwala ya wuce masallaci,yana sane yayi kamar yamanta da ogogon,wanda kuɗinshi yafi dubu ɗari.


Yana fita salma ta ƙarasa haɗa Takardun gurin ta adana,har ta miƙe zata fita itama,se idonta ya sauka kan agogon,tsayawa tayi tana kallonshi,tana tunanin ɗauka,tana jin tsoro.


Ƙarasawa tayi gurin agogon,sede abinda ta hanga aƙasan table ɗin yafi mata agogon,amfani,kuɗine bunch bunch na one thousands guda huɗu.


jiki na ɓari tasa hannu ta ɗauki ɗauri ɗaya,harta tafi sekuma ta sake dawowa ta ɗauki ɗaya yazama dubu ɗari biyu kenan,cikin aljihunta ta zuba kuɗin,tafice daga office ɗin da sauri.


Jakarta taje ta zuba kuɗin aciki sannan tayi sallah,ta koma office ɗin doctor tana ta adduar Allah de yasa be duba kuɗinshiba.


Shiko doctor duk yana sane ya ajiye kuɗin dan yagani iya ƙananan sata ta iya koko harda manya ma,ilai kuwa koda yadawo daga masallaci,dubawa yayi yaga babu dan haka kunna computer yayi dan yaga yadda abun yafaru.


Sosai yasha mamaki,daga ƙarshe abun yabashi dariya,ba abinda yafi bashi dariya kamar yadda ta ɗauki na farko har ta tafi taga be ishetaba ta dawo ta ƙara na biyu.


Kashe computer yayi yashiga tunanin ta ina ze ɓullowa wannan me hannun ɓeran da aka haɗashi ayki da ita.


Sallamar salmace ta dawo dashi daga duniyar tunanin,izinin shigowa yabata.


Tana shiga yamiƙe afusace,yace.


"uban waye ya dau..."bata jira yagamaba jikinta narawa bakinta na karkarwa tace.


"wallahi doctor ban ɗaukar maka kuɗiba"


Dariyace taso kamashi,ganin yanayin da salma tashiga,dakewa yayi yasake dakamata tsawa yace.


"kinji nace miki,an ɗaukemin kuɗine?baki jira nagama maganaba kin katseni,to cewa zanyi waya ɗauke takardun danake ayki akansu".


Wata uwar ajiyar zuciya salma tasaki harda dafe ƙirji ta jingina da bango ta lumshe ido na ƴan mintuna.


Dariyace sosai cike da cikin doctor amman se yadanne.


Salma baki na rawa gumi na keto mata tace.


"nice na kwashe na zuba maka a loka,bari in ɗauko,maka"kamar mazari tanufi lokar ta ɗauko takardun ta bashi,suka ci gaba da duba patients,lokaci zuwa lokaci doctor na lura da yadda salma take ta faman sakin ajiyar zuciya.


haka sukai ta duba marasa lafiyan har zuwa sanda sukayi changen duty.


Jiki na ɓari salma tafice daga Asibitin,aƙafa take tafiya,dan gaba ɗaya a rikice take tama kasa tsaida mashine ta hau,dan tunda take sata bata taɓa yin babba kamar wannan ba.


Motar doctor taga yasha gabanta kaɗan yarage ta saki fitsari a wando,sabida tsoratar datayi,kasa ci gaba tayi da tafiyar,shiko duk yanayin data shiga yana observing, da ƙyar ta ƙaraso inda yake taɗan rusuna ta gaisheshi.


"shigo in rage miki hanya"doctor yace batare daya kalletaba.


Da cewa zatayi ta gode,sekuma taji tsoron kar rsnshi ya ɓaci wataƙila ma yagano,ita ta ɗaukarmasa kuɗi ya tozartata a gurin,danhaka ba musu tashiga motar suka tafi.


Se ƙara rungume jakar ta takeyi takasa sakinta.


"Hala de jakarnan taki akwai wani abu me muhimmanci acikine ko?"doctor ya wurga mata tambaya.


A kiɗime ta waigo tana kallonshi tace bakinta na rawa.


"Aa wlh ba kuɗi bane acikiba"ta bashi amsa tana ƙara riƙe jakar da kyau.


"ke ko kode kunnenki beji dakyaune a ina kikaji na ambaci kuɗi?".


Jan bakinta tayi tai shuru,har suka iso camp ɗin yasauketa,har ta sauka daga motar,se ya leƙo da kanshi ta window yace.


"To akashe lafiya".


yana faɗin hakan,yaja motarshi ya barta agurin tana nazarin kalmarshi.


"akashe lafiya,to me yake nufi kenan?"salma ta tambayi kanta,rashin amsane yasa ta juya tawuce ɗakinsu.


surbajo ce,for life.

[8/11, 16:50] Umar Dalha: *👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad Mahmud


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION


*i don't need everybody in my life,i just need few people who truly understand me,#be your own bossssss*



*6*



Tana shiga ɗakinsu tayi sauri taciro kuɗin ta ɓoye acikin kayanta,wanka ta shiga tafito tayi sallah.


Tana idar da sallar ne tasamu natsuwa,dan haka kwalliya ta tsara a fuskarta,kamar amarya,sannan ta ɗauki wasu arnayan english wears ta saka,iya kyau tayi kyau,amman babu me kallonta ya ɗauka tasan abinda ake kira musulunci.


Tana ɗaura takalmi feefee tashigo ɗakin,cike da mamaki take kallon salmar.


Miƙewa salma tayi tacewa feefee.


"ƙawa zani shopping ne pls,kimana girki kan nadawo".


"salma kina nufin wai dawannan shigar zaki fita?anya kinada hankali ƙuwa,wannan shigar mijinki ne yafi cancanta daya ganta fa,wlh inkina yin haka bazaki samu miji nagari dazece yana sonkiba".


"Aniyarki tabiki wlh,miji nagari kuma har se nazaɓa,sabida yadda kike taƙama ke virgin ce haka nima,da ace iskanci nakeyi sekice bazan samu ba,nifa feefee kinfara wuce gona da iri,wanne irin wulaƙanci ne wannan,nayi kwalliya ko ɗan cewa nayi kyau bakiyiba,amman kinzo kina cikamin kunne,da zancen banza,tonide daga yau karki sake yimin haka,jikinki ko jikina?".


Tana kaiwa nan tayi ficewarta tabar feefee atsaye kamar gunki.


Tana isa bakin titi ta fara sauya takunta,dama ga rigar datasa koya ta motsa cibiyarta na fitowa,daga saman wandin kuma jigidar dake jikinta itama tafito,tana tafiya kamar wata tarwaɗa.


Tana isowa bakin titin taja gefe ta tsaya,tana taunar cingum.


Wata venz 4matic ce ta faka agabanta,sannu a hankali glass din yasauka,wani mutumine aciki wanda a haife ya haifi salmar.


A zaton shi ba musulma bace dan haka da turanci yamata magana.


"sexy baby barka da yammaci"


Ɗago ido salma tayi ta haskeshi dasu,sannan tadan murmusa,tace.


"yauwa suger daddy"


amsar tata dariya tabashi,dan haka yace.


"in bazaki damuba muje in rage miki hanya mana"


Su salma abin nema ya samu amman dayake baby ce me class setace.


"Ayya nagode kawai nima nan daka ganni driver na nake jira".


Har ga Allah ya amince da batun nata,dan batayi kala da ƴar talakaba.



"ay daganinki nasan akwai dalilin dayasa kike tsaye anan,amman don Allah kishigo na rage miki hanya".


Dakyar de yasamu ta amince,koda zata shiga motar seda tayi wani juyi da mazaunanta sannan tashiga,wani miyau mutumin ya haɗiye ba shiri.


"Ni sunana Alhaji Adamu canji,ni maaikacine a CBN,ina zaune a Abuja ne,yanzu haka dakika ganni nazo wani meeting ne nan,kefa ya sunanki".


cikin salon ɗaukar hankali,tace.


"Sunana salma hadi medala,nazo nanne bautar ƙasa daga jihar kaduna".


"wow nice name,ashema ke musulmace?"


"sosai ni musulmace,ilove fation ne kawai shiyasa kaganni ahaka"


"thas good,ina kika nufa yanzu".


"zani shopping ne wlh kuma inason in sauya wayata ne,shiyasa kaganni nafito yanzu".


"Ok ba matsala bari nakaiki,ay kin cancanci amiki komai"


Wani haɗaɗɗen super market yakaita,nan tashiga jidar kaya,na kwalliya dana ci,bayan tagama da wannan fannin,sukaje ɓangaran wayoyi.


Alhajin dakanshi ya zaɓar mata,iphone7 da kuma samsung galaxy s6 edge,salma ware ido tayi kawai tana kallon ikon Allah koda sukaje gurin biyan kuɗi akayi total ɗin duka kayan data siya da wayoyin,dubu ɗari huɗu da hamsin.


numfashinta be kusa ɗaukewaba seda taga Alhaji Adamu yaciro kuɗin yabiya cash.


Kasa magana tayi,binsa kawai take da ido har aka gama zuba kayan a leda,aka kaimusu mota,ko tafiya ta kasa yi dan haka Alhaji adamu,hannunsa yasa yakamo ƙugunta،salma kasa hanashi taɓata tayi,ahaka yajata suka bi hanyar fita,suna kaiwa bakin ƙofa suka ci karo da doctor najeeb shima yazo shopping.


Ba ƙaramin mamaki yayi da ganin yarinyar ahakaba,kallon tsana yabita dashi,yayinda itama,ta wurga mishi nata.


Duk da bata ji daɗin ganinta da yayi rungume ajikin Alhajiba amman bazata bari ya gane hakanba.


Shigewa ciki yayi sukuma suka fice zuwa mota.



Surbajo for life.

[8/11, 16:50] Umar Dalha: *👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*




Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



 *7*



Suna shiga mota Alhaji yaja suka tafi,se hannu yake miƙawa yana shafar cinyoyinta da saman wuyanta,sam salma takasa hanashi taɓatan dayakeyi.


(To dama taya zata iya hanashi taɓata bayan tadauki dogon buri game da rayuwarta,tunda ko tasamu,me kudi ay dole tasakar masa ragamar rayuwarta,kukan kurciya............).


A haka har suka iso kamp,complementry card ɗinshi ya bata,koda ta yunƙura zata fita a motar hannu Alhaji yasa ya shafo mazaunanta cikin wani salo,wanda ya tilastawa salma komawa cikin motar.


Hannu yasa ahankali yana shafa wuyanta har yaƙaraso kan ƙirjinta,salma najin daɗin abinda yake mata ba kaɗanba sabida shine karo na farko da hakan ta taɓa shiga tsakaninta da namiji.


Tura hannunshi yayi cikin rigar yadunga wasa da boobs ɗinta,itako wani irin numfashi take ja gaba ɗaya tafice a hayyacinta.


Seda yagaji dan kanshi da wasa da jikinta sannan sukayi sallama tafice ɗauke da ledojin da yaymata siyayyar.


Tana isa ɗakin tasami feefee na karatun qur'ani,wuceta tayi ta isa bakin gadonta ta shirya kayayyakinta sannan tasaka wayoyinta a charge.


Wankan tsarki taje tayi sannan ta ɗauro alwala tazo tayi sallah,feefee de binta kawai take da ido,ga abin magana amman tana gudun  kada cibi yazama ƙari,dole taja bakinta tayi shuru.



Abinci feefee taba salma ba kunya ta amsa tacinye,daga haka salma ta nunawa feefee tsarabar da Alhaji yay mata,ta haɗa harda kuɗin doctor data sato tace shi yabata,ta nuna mata ma complementry card dinshi daya bata.


Idon feefee kamar goriba sabida girman daya ƙara dan tsananin mamakin salma da takeyi,har salma tagama jawabinta feefee tagaza ɗauke idonta akanta.


"Salma iskanci kika fara sabida son abin duniya?"feefee tawatso mata tambaya.


"Bangane iskanciba,daga cewa anbani kyauta sekice iskanci nafara,?"


"Wlh salma koshine ya haifeki ƙarshe kenan,inde tarbiyya me kyau yakeson baki bazr baki duka wannan abubuwanba,karfa ki maidani yarinya,salma ba tun yau muke tareba,ko ummanki bazata faɗamin halinkiba,inde ba alada kika gamaba salma bakya jiƙa gashin kanki,hasalima a saloon kawai kike wanke gashi,yau gashi kin wanke a gida kuma ma da daddare bayan kindawo daga yawonki,dan haka nagano komai ayke ba yarinya bace kinsan abu mekyau daga yau salma bazan ƙara yimiki magana akan ki sauya halinkiba,akwai ranar ƙin dillanci ranar da hajar megari taɓace".


jikin salma yamutu murus,dan tasan intacewa feefee ba zina tayiba bazata yarda ba shine yasa ta tattara kayan ta adana tayi kwanciyarta,zuciyarta na hango mata abunda Alhaji yayi mata ɗazu tanajin daɗi.


Washe gari da wuri ta shirya,wata riga tasaka,wacce iyakarta guiwarta baƙa,wacce takamata sosai,sannan tasaka dogon takalmi shima baƙi,da jaka baƙa,ta gyara gashinta ya sauka gadon bayanta wani kuma tazubo tagaban kafaɗarta,sosai tayi kyau.


Koda zata fita abun mamaki yabata ganin feefee fuska ɗauke da faraa tanamata adawo lafiya,gamida koɗa ta da cewa tayi kyau sosai.


Hakanne yaba salma kwarin guiwar tafiya cikin kwanciyar hankali.


Tana isa office,su mary suks shiga koɗata,ita kum se wani efize takeyi ita ala dole ta haɗu.


Doctor kamar kullum ƙarfe takwas ya iso office,koda salma taje gaisheshi,ko alamar yaganta jiya da wani be nuna mata ba,haka har aka tashi agurin ayki.



Haka rayuwar salma tacigaba da tafiya doctor na ajiye kuɗi tana sata,kamin wani lokaci tazama babbar yarinya ga Alhaji dayake mata ruwan kuɗi,ko yaushe,feefee ko bata ƙara yiwa salma faɗan ta shiyuba,saurayi in yanuna yana sonta inde talakane,se tahaɗashi da ƴansanda tace fyaɗe yakeson yimata.


Mugayan halayenta ba abinda ya ragu sema ƙaruwa da yayi.


Yau weekend,salmace kwance akan gadonta suna waya da Alhajinta,wanda yawancin wayar,iskanci kawai suke faɗi.


"Baby yakamata wannan weekend ɗin kizo Abuja muyishi tare,wlh ina missing boobs ɗinki sosai".


"Alhaji kenan,ni wana sani a Abuja dazan zo weekend?boobs kuma ay kullum ina baka su ta waya,to me yayi saura?"


"baby i promise you inkikazo zan siyamiki mota,ladan zuwan dakikayi,yakike abu sekace ba babbar yarinya ba".


ihu salma tasaki awayar gami da cewa.


"Alhaji kana kasheni da daɗi,ayko inanan zuwa anjima,ammanfa kacika alƙawari"


"baki da matsala inde nine,"


haka sukayi sallama,suna ajiye wayar salma ta faɗa wanka,tana fitowa ta haɗe acikin riga da siket amman siket ɗin,mini ne dan ko guiwarta be kaiba.


Kaya kala biyu tasaka acikin jakarta,ta fice,a hanya suka haɗu da feefee.


"Ah a hajiya salma se ina kuma,akaci wannan wankan sikarin?"inji feefee.


Dariya salma tayi sannan tace.


"Kede bari wlh Alhaji ne da rigima,wai senaje gurinshi nayi weekend,shine yanzu zani"


Kai feefee ne yafara charge dajin batun na salma.


"kina nufin Yanzu gurinshi zaki kiyi kwana biyu kidawo?"


"to yazanyi feefee tunda ya buƙaceni,ay dole naje,"



"To salma adawo lafiya"tana faɗin haka tayi gaba abinta.


salma ko ajikinta,tahau mashin yakaita tasha,tahau motar Abuja.


Muje zuwa.


Surbajoce.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*


Zahra Muhammad Mahmud


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION


*8*


Tafiya sukayi ta tsawon awa guda suka iso birnin Abuja.


Koda salma tasauka atashar nyanya,guri tasamu agefen wani gidan mai takira Alhaji,ba jimawa ya iso gurin cikin wata arniyar jeep,range rover,Alhaji murna yake da ganinta bada wasa ba.


Haka yaja motar suka isa,hilton transcop hotel,dake Abuja.


Suna isa yayi parking a parking space,yazagaya ya buɗe mata ƙofa ya rungumota jikinshi sukayi hanyar shiga cikin gurin.


karab seji sukayi sunyi karo da wani mutum,juyowa sukayi duka sudashi domin aba juna haƙuri.

😳wa salma zata gani,doctor najeeb ne rataye da wani id card a wuyanshi alamar taro sukayi acikin hotel ɗin.


Binshi tayi da ido,duk kunya takamata,yanzu tasan kallon karuwa ze dunga yimata.


Doctor sosai abun yabashi mamaki,ashe yarinyar bin maza takeyi shiyasa take mummunar shiga,ji yayi ya tsaneta sosai a zuciyarshi,dan ya tsani,mace ballagaza,juyawa yayi afusace ya shige motarshi.


Ganin haka yasa Alhaji shima jan salma suka shige cikin hoteƙ ɗin.

 

ɗaki dama already yakama dan haka wucewa sukayi zuwa cikin ɗakin.


Suna shiga Alhaji ya rungumeta yana mata wellcome,nande suka taɓa ƴan wasanni,suka ci abinci,sannan,Salma tayi sallah,ta yi wanka tasaka sleeping dress.


Alhaji kamar tsohon maye haka yake binta da kallo itako se ƙara kaɗa ƙugu takeyi jigidar ta na ƙara tana daɗa ɗaga mishi hankali.


Jawota yayi jikinshi,yashiga wasa daita,takoina,har yayi nasarar rabata da rigar jikin ta,cigaba yayi da wasa da ita,tana biye mishi.


Sanda hannunshi yadauka akan fant ɗintane tayi sauri tariƙe mishi hannu,tadan ɓata rai tace.


"zan iya mallakamaka komai nawa amman banda nan gurin,duk wuya duk runtsi,banaso narasa farincikin daren farko agidan mijina dan haka ka kiyaye".


Maimakon taga yadamu seji tayi yace yana murmushi.


"Sory baby is a mistake,bazan ƙaraba".


Daga haka suka ci gaba da wasa da juna.suna tsaka da wasan ne wayar Alhaji tayi ƙara,ɗagawa yayi yayi magana,be ɗau lokaciba ya ajiye wayar.


zuwacan taji ana nucking ɗin ƙofar,dayake room and falor ne,Alhaji miƙewa yayi yafit,be jimaba yadawo ɗauke da wata ƙatuwar jaka dakyar yake ɗagata,yana shigowa da ita ya buɗe waldrope yasakata aciki,ya kulle yacire ɗan mukullin yasa a aljihunshi.


Hankalin salma nakan jakar sotake kawai taga abinda ke cikin jakar,Ba jimawa bacci ya ɗauke Alhaji,a hankali salma ta lalubeshi,ta ɗauki mukullin waldrope ɗin,ta buɗe,jakar ta buɗe a hankali.


Kuɗine aciki irin na ƙasar waje wato dollars,ido salma ta ware,gamida murmushi na farinciki.


"Tabbas inna ɗauke kuɗinnan nagama talauci a duniya"cewar salma a zuciyarta,dan haka komawa tayi a hankali tasawa Alhaji filo akusa dashi dan ya ɗauka itace.


Kayanta tasaka,ta ɗauki jakarta ta hannu sannan ta kinkimi ƙatuwar jakar,ta lallaɓa tafice daga ɗakin.


Daidaita tafiyarta tayi dan kar maaikatan hotel ɗin su ɗauka bata da gaskiyane,har tazo ta fice bawanda ya kulata.


Dayake ƙarfe shaɗaya na dare ne tana fitowa tasamu wani me taxi tace yakaita tasha konawane zata biyashi,ba musu yaɗauketa yakaita tashar.


koda sukaje tasha ba motar zuwa keffi dan haka,drope ɗin golf 3 ta ɗauka dan yakaita keffi adaren.


Nan suka tsadance ya ɗauketa,suna cikin tafiya ko nisa basuyiba,suka tarar da shinge na bincike wato jamian tsaro,koda suka ƙaraso se sukaga ashe hukumar,NDLA ce take binciken,sabida,sun kama wata mota ɗauke da hodar iblis,amman direban yagudu,shine suka bazu amanyan tituna suna binciken har dare.


Koda akazo kan motar su salma,bincike ƙaramar jakarta akayi baa sami komaiba,sannan aka buɗe babbar jakar,kuɗine aciki,da har sunce su wuce se wani jamiin yasake tsaidasu ya buɗe jakar,bindigar hannunshi yasa yana tona cikin jakar,ayko yana cikin dubawa,sega hodar iblis  wato cocane acikin jakar,me yawan gaske.


"you are under arrest"suka furta atare gamida baibaye motar da bindigu.


Tuni salma tajima da sakin fitsari a wandonta,kamin tayi wani yunƙuri,tuni sunrufeta da duka,ita da direban,ihu take tana faɗin suyi haƙuri amman kota kanta basayi.


A motarsu suka zubasu ita da direban dabejiba be ganiba aka wuce dasu,head quater na hukumar.


Surbajo ce.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad Mahmud


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION


*feedo yarficika,Allah yajiƙan mahaifiyarki,yasa aljannace makomarta,Allah yay mata rahama,Allah yasa Annabi ya karɓi baƙuncinta,ku kuma Allah yabaku ikon jure zafi da raɗaɗin rashinta,Muma Allah yajiƙan namu iyayen da ƴan uwa musulmai baki ɗaya,Ameen don alfarmar Annabi da Alqur'ani😭😭🙏*



*9*


Suna kaisu office ɗin kowa yayo ca akansu,masu duka nayi masu tsinemusu nayi.


Kamin wani lokaci halittar salma gabaɗaya ta sauya,dakyar aka samu aka shige da ita gurin shugaban gurin.


Duk tambayoyin da akemata takasa amsawa se kuka takeyi,har abin shocking seda aka samata amman sede ihu data dungayi tagaza amsawa,


ganin hakane yasa aka fara binta ta lallama,tabada shaidar ba ruwan direban daya ɗaukota,wanda shi tuni yajima da sumewa sabida dukan dayaci.


Asibiti aka wuce dashi,ita kuma batare da ɓata lokaciba aka gayyato ƴan jarida,suka fara ɗaukarta hoto,gamida rubuta laifin datayi,duk wanda yaga hoton ma baze ganetaba,dan fuskar ta kumbure gaba ɗaya.


kamin wani lokaci tuni anyaɗata a social media da gidajan tv,da radio,da jaridu.


Kowa se laantarta yake,amman har lokacin taƙi faɗin komai game daita.


Kotu aka turata,ananma ba magana sede kuka,dan haka alƙali yabada umarnin akaita gidan maza ajiya,har zuwa sanda ta shirya bawa kotu amsoshin datake buƙata.


Haka akasa salma cikin mota,aka kaita gidan yarin dake kuje,ɗaure cikin sarƙa.


tun salma na iyayin kuka har takoma tagaza yin kukan.


se alokacin take danasanin,bijirewa iyayenta,da aminiyarta feefee.


Ta tubarwa Allah gameda Halin datasa kanta aciki,danasani tayi ba adadi.


Bakomai yasa salma taƙi maganaba,se kunyar datakeji tace satowa tayi,wanda tasan kota faɗa a ƙasa irin ta nigeria,ba yadda zaayiba,sabida kullum a nigeria me kuɗi shine me gaskiya.


A ɓangaren Alhaji kuwa,tunda yafarka yaga ba salma ba jakar kayanshi yasan itace ta ɗauke.


Ranshine ya ɓaci sosai,dan dama dakyar yaronshi yagudu da kayan da aka kamashi,shine ita kuma zata sace,lalle se ya koyamata hankali.


Tv ya kunna yana kallon NTA abun dayagani ba ƙaramin kiɗimashi yayiba,salma yagani ana nunata amatsayin ƴar safarar miyagun ƙwayoyi.


Tabbas yasan in yabari be ɗauki matakiba tsab asirinsa ze tonu,dan haka da sauri yakira malaminsa,yashaida mishi komai kuma yabashi umarnin a rufe bakin salma karta kuskura ta kama sunan shi.


Ayko malamin beyi ƙasa a guiwaba ya rufe bakin salma inda yakai laya yasa acikin kabari,da nufin inde na kabarin zaa tambayeshi yabada amsa to itama zata amsa tambayar da ake mata a kotu.


Feefee kuwa ganin har monday tayi ba salma ba alamartane yasa tafara damuwa,takira numbarta duka akashe,sunƙi tafiya.


har tsawon sati guda bata ganta ba hakanne yasa takai report,gurin mahukuntansu.


Nanda nan aka bazu zuwa tashar mota dan,aji kode sunyi hatsarine.


Koda akaje tasha,anshaida musu motar batayi hatsariba,amman anfaɗa musu akwai motar keffi data taso daga Abuja,ranar Lahadi da yamma datayi hatsari takama da wuta kowa nacikin motar ya ƙone.


Jin hakane yasa feefee rushewa da kuka sabida salma tashaida mata kwana biyu zatayi a Abuja,dayake ran friday ta tafi da yamma.


da kyar aka rarrashi feefee tayi shuru,can Abujan aka tafi office ɗin ƴan union,inda aka buƙaci dasu bada list na fasinjan dake cikin motar datayi hatsarin,koda aka duba wani ikon Allah sun samu da akwai mesuna salma aciki duk da batasa number wayaba,hakanne yasa kowa ya amince salma nacikin motar datayi hatsari kuma ta ƙone ƙurmus.


feefee ta suma yafi so uku,dan daga ƙarshe dole seda aka dangana da ita da asibiti.


Shiko doctor rashin zuwan salma gurin ayki be dameshiba,dan yasan tanacan yawon barikinta.


Hukumar NYSC ce ta rubuta report gameda mutuwar salma ta tura asibitin datake service.


Sanda takardar ta iso office ɗin doctor ba ƙaramar razana yayiba,wato ashe ganin dayamata na ƙarshene,tunda ance a hanyar dawowarta ne tayi hatsarin.


Mutuwar salma ta shigi docto ba kaɗanba,musamman inyatuno mugayan halayenta,wanda ta dawo daga aykatawane ta mutu tausayinta na kamashi,adduar samun rahama yayi mata.


Daga haka aka shirya jamiai tare da feefee da kayan salma aka nufi gidan iyayen salmar.


Koda suka sanar dasu mutuwar ƴar tasu ba ƙaramin gigita sukayiba sunyi kuka kamar ba gobe.


Sahabi yace cikin kuka.


"ita da aka tura keffi me yakaita Abuja kuma?"


Da sauri feefee tabashi amsa da cewa.


"Anturata wani research ne agarin shine tsautsayin ya rutsa daita".



Nande akaita ƴan koke game da mutuwar salmar,dangi nakusa dana nesa duk sunzo taaziyya.


Kayan salma ko Akwati biyar,haka aka shigar dasu ɗakin mahaifiyarta.


Haka iyayenta suka cigaba da kukan rashinta harsuka dawo suka fawwalawa Allah.


koda wasa mahaifiyar salma ko wani nata basu taɓa shaawar buɗe kayan nata ba,dan daga ƙarshema,ɗakin da suke ajiye tarkace aka Kai kayan aka zuba.


A,B,U  zaria ma ta turo wakilanta yin taaziyar mutuwar ɗalibar tasu,harda kuɗi suka bada sadaka.


Feefee ta koma gurin service ɗinta amman kullum jitakeyi kamar zataga  salma,takasa sabawa da rashinta.


Salma ko tanacan gidan yari ana gana mata azaba sabida taƙi faɗin koda sunantane bare asan daga inda take.



muje zuwa.


surbajo for life.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*


Zahra Muhammad Mahmud


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION


*10*


Salma tayi kuka tayi kuka har ta godema Allah,tayi danasani mara iyaka,na halin data jefa kanta.


Tayi Allah wadai da duk wani me kwaɗayi da buri irin nata wanda ƙarshe ga inda yajefata.


Ba abinda ke ƙara sa zuciyar salma zafi kamar tinawa datayi yanzu ta tashi daga ƴar bautar ƙasa ta koma ƴar bautar gidan kaso.


Haka rayuwa taci gaba da tafiya sannu a hankali kowa yamance da wata salma ya rungumi rayuwarshi.


Salma yanzu an mance da ita ma a gidan yarin,dan alƙalin be ƙara buƙatar akawota ba,hakanne yajanyo zamanta a gidan yari ya kankama,dan tun tanasa ran zata fita har tacire,ta maida rayuwarta ga bautar ubangiji da neman yafiyarsa abisa laifin data aykata.


Yau su feefee suka gama service ɗinsu cike da nasarori,lokacin dasuka kamo hanyar zuwa kaduna inbanda kuka ba abinda feefee takeyi,sabida tunowa da tayi da ranar dazasu zo ga ƙugunta gana salma amman yau ba salmar akusa da ita.


Haka suka isa kaduna cike da nasarori na murnar kammala bautar ƙasa lafiya.


*BAYAN SHEKARA ƊAYA DA RABI*


Duk wani mahaluki dayasan salma yajima da mancewa da ita.


Tuni feefee tayi Aure,har tana da cikima tsoho,kuma tana ayki a wani kamfanin dake yin atamfa.


Doctor najeeb an daɗe dayimasa transfer daga Keffi zuwa Abuja,a international hospital dake Abuja Amatsayin babban likita.


Nigeria anyi zaɓe inda akasamu sauyin gomnati,wacce sabuwar gomnatin me adalci ce,dan abu na farko data fara yi shine.


Kama ɓarayin gomnati tana kaiwa prison tana kuma fito da masu gaskiya daga prison ɗin.


ana hakane tawagar dake binciken gidan yarin kuje ta iso shingen da su salma suke zaune,dayake da ƴan jarida suke tafe shiyasa akwai maaikatan gidan tv.


Ɗaukarsu suka farayi ana musu tambayoyi,koda akazo kan salma kuka kawai takeyi,ana mata tambaya amman tagaza cewa komai se kuka.


Cikin hukuncin ubangiji ana tambayarta ya suna tace.


"Salma Hadi"


"Daga ina kike,me kikayi aka kawoki nan?"wani ɗan jarida ya wurga mata tambayar


Takasa bada amsa se kuka takeyi,hakanne yasa ,suka juyar da tambayar ga jamiin dake kula dasu,inda yabasu amsa da cewa.


"ita wannan dakuke gani babbar ƴar safarar miyagun ƙwayoyice,shekarun bayane aka kamata da hodar iblis daga Abuja tanaso tashige da ita jahar nasarawa,kuma inbanda yau tunda aka kawota bata taɓa faɗin sunantaba,sede tayi ta kuka,ba irin azabar da baa gana mataba amman raƙi yin magana"


nande ƴan jaridar suka ci gaba da ɗaukar rahotonsu,har suka gama suka fice.


Doctor Najeeb ne zaune agaban tv yana kallon news daga tashar nta,da ze kashene amman headlines ɗin da presenter yakaranto sune suka ɗauki hankalinshi,inda yaci gaba da kallon tv.


"A yaune jamian da gomnati ta naɗa domin bincika gidajan yarin dake faɗin kasarnar suka isa gidan yari dake kuje,inda sukayi gagarumar nasarar tattaunawa da babbar ƴar safarar miyagun kwayoyin nan,wacce aka kama,shekaru biyu da suka wuce,wacce taƙi faɗin sunanta dakuma adireshinta,ga rahoton da wakilin mu ya ɗauko mana".


ƙara gyara zama doctor yayi yana kallon tv.


Gidan yarin aka hasko,tare da masu binciken dakuma ƴangidan yarin,ana musu tambayoyi,har akazo kan salma.


Ido doctor ya ƙuramata,yanaso yagano inda yataɓa ganin zoben dake hannunta na azurfa,dan tabbas yasan yataɓa ganinshi,amman ya manta ko a ina yagani.

Hankalinshine yaƙara tafiya gurin sunan dayaji ta ambata.


"Salma hadi"tabbas sunan yataɓa jinshi amman yamance ko a ina ne.


Bayanin da jamiin gidan yarin yayi shine ya ƙara sawa ƙwaƙwalwar doctor ɗaukar zafi,nason tilasta mata ta gano mishi me wannan sunan.


Fuskar salma aka cigaba da nunawa,wacce babu mecewa itace,kwayar idonta Doctor yaci gaba da kallah,zuwa can yamiƙe a razane ya furta.


 "Barauniya ta!!!!yes she is the one"


muje zuwa.


surbajo for life.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad Mahmud


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION


*11*



Gaba ɗaya yagama rikicewa yarasa abinda ke damunshi.


Waige waige yashiga yi yana neman wayarshi amman dayake  a ruɗe yake sam yagaza,ganinta,se zuwa can Allah yakai idonshi kanta.


Da,sauri ya ɗauka ya dubo wata number yakira ba jimawa naji yace.


"Hello barrister,kana gidane?"


Dagacan ɓangaren yace.


"eh ina gida,amman kasan ayni ba gwauro bane kamarka,ina fatan de bacewa zakayi zaka zoba?"


Se alokacin doctor yafahimci ashe darene ba safiya ba.


"Da safe in Allah yakaimu inaso mu haɗu"doctor ya faɗi cikin damuwa.


"ok baka da damuwa Allah yakaimu safiyar"


Daga haka kowa ya ajiye wayar.


Doctor safa da marwa yashiga yi,zuface kawai take keto masa.


"Me ya haɗa salma da hodar iblis,adaren daya ganta?meya hanata yin magana a kotu domin ayi bincike?"wani tambayoyin su doctor ya kwana yiwa kansa har garin Allah ya waye.


Da safe da wuri ya shirya ya wuce office ɗin Barrister,be zoba seda ya jirashi na tsawon awa biyu.


Koda barrister yaga yanayin doctor yasan yana cikin damuwa sosai,danga idonshi ya nuna beyi bacci bama jiya.


"bokan turai me yake faruwane?"barrister ya tambaya.


"Barrister komai ma yafaru,wallahi narasa natsuwa tun jiya dana kalli news da aka nuna gidan yarin kuje"


Wata dariya ce ta ƙwacewa barrister inda yace


"kaiko in banda shirme irinnaka ina ruwanka da gidan yarin?"


"Bazaka gane bane barrister,shekaru biyu da suka wuce lokacin ina ayki a keffi akwai wata ƴar bautar ƙasa da aka turo office ɗina daga A,B,U zaria,to yarinya irin wainda suka fiye son kuɗi ɗinnanne,dan sometimes inna ajiye kuɗi tana ɗauka,so biyu ina ganinta da wani Alhaji wanda ni zuciyata bata amince dashiba,ƙarshen ganina da ita,wani darene munje conference a Abuja,naganta tare da mutumin zasu shiga cikin,hilton transcop hotel,to abun mamaki,bayan sati ɗaya dayin hakan sega report daga Hukumar NYSC zuwa office ɗina wai tayi hatsari ta ƙone maana de ta mutu,tsawon wannan lokacin da aka ɗauka ina mafarki da ita tana miƙomin hannu da niyyar incirota daga wani kogi data faɗa,toni tunanina se yabani,maybe ana mata hukuncine game da satar datasha yimin dan haka sekawai nayi sadaka sannan nace na yafe mata,ti kwatsam jiya segashi naganta acikin gidan yarin wai shekaru biyu kenan da aka kamata da hodar iblis,kuma babu irin azabar da baa gana mataba amman taƙi yin magana,kuma koda aka nunota jiyan still kukan takeyi,barrister kaji abinda ya ɗaga hankalina"cewar doctor fuskarshi na nuna tsananin damuwar dayake ciki.


doguwar ajiyar zuciya Barrister ya yi,sannan yace.


"Gaskiya abokina wannan zancan adubane,zeyi wuya idan ba sato jakar tayiba tunda tanayin satar"


"wlh barrister nima tunani na kenan,wata ƙila gurin shegiyar satar tane taje ta satowa kanta masifa"


Shuru barrister yayi kana daga bisani yace.


"ka kwantar da hankalinka,insha Allahu se angano gaskiya,karkadamu yanzu kataso muje gidan yarin mu nemi ganinta,wataƙila mu tayimana bayani"


"To Allah yasa,amman mu biya ta office nayi signing semu wuce kuje ɗin"


Daga haka Asibitin da doctor yake ayki suka je yayi signing sannan suka fice zuwa gidan yarin kuje.


Koda suka isa basu sha wata wahalaba gurin samun izinin ganinta,sabida barrister babban lauyane kuma fitacce.


Gurin da aka tanada domin ganawa da masu laifin aka kaisu,sannan akaje aka taho da Salma ƙafa da hannunta ɗaure cikin sarƙa,koda akace tazo tanada baƙi ba ƙaramin mamaki tayiba dan tunda aka kawota kare bezo yace yan nemanta ba.


Koda aka kawota  gaban su doctor,agigice yake kallonta,sabida gabaɗaya,duk wannan kyan da kyan surar duk babu,takoma kamar tsohuwa sabida wahala


Sanda salma ta ɗago idonta taga doctor,wani kukane ya kubce mata,zubewa tayi agabanshi tana faɗin.


"Don Allah kayafemin,kagafartamin,wlh nasan hakkinkune yakamani shiyasa aka kawoni nan,kagafartamin,don Allah"ta ƙaras maganar cikin matsanancin kuka,ta ruƙo ƙafarshi.


Runtse ido doctor yayi yanjin kukan salma na taɓa zuciyar shi.


Hannuns yasa ya ɗagota ya zaunar da ita kan kujera,sannan,yasa hand carchiep yana share mata hawaye,riƙe hannun salma tayi wasu hawayen nabin fuskarta tace.


"shekaru biyu kenan ina irin wannan kukan,babu wanda,yataɓa gogemin hawayen sekai,Allah yasa kayafemin ne?"


Kai doctor ya ɗaga mata.


Shiko barrister,abun nasu  tv yazamar masa,danshi bema taɓa ganin masoya irin suba.


Gajiya yayi,da kallon nasu ya dakatar dasu,suka fara abinda ya kawosu.


Muje zuwa


Surbajo for life.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*


Zahra Muhammad Mahmud


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION


*Safina mum sultan,saly,Queen Aeanarh,wannan shafin nakune Allah yabar so da ƙauna,nagode sosai,kuma insha Allahu bazaku taɓe ba*


*12*


Natsuwa sukayi sosai dan su samu mafita.


Barrister ne yace.


"Malama,Salma,sunana barrister,kabeer,ni lauyane me zaman kansa,sannan ni amini ne ga doctor najeeb,inaso ki bani amsar duk wata tambaya dazan miki tsakaninki da Allah,kinyi alƙawarin bani amsar?"


Kai,ta daga masa tana kallon doctor wanda shima ita yake kallo.


"Me yasa kika jefa kanki cikin sanaar da bata dace dakeba?kina mace meyakaiki safarar miyagun kwayoyi?"


Kuka salma ta rushe dashi,cikin kukan tace.


"Wlh ni ba sanaata bace,hasalima ni bansan akwai kayan laifi acikin jakarba wlh"ta ƙarasa maganar cikin kuka.


"Jakar takice ko ba takibace?"


"wlh batawa bace"cewar salma


"to a ina kika samota?"cewar barrister.


Ƙasa tayi da kanta alamae kunya dajin nauyi sannan tace.


"Satowa nayi"


Runtse ido doctor yayi sabida maganar ta zafafa zuciyarshi.


"a ina kika sato"inje barrister


kuka ta fashe dashi,sam bakinta yakasa faɗin inda tasato jakar,duk yadda su doctor sukayi da ita dan ta faɗi inda ta sato jakar amman ta kasa.


Haka suka haƙura sukayimata sallama akan zasu dawo wani satin.


Koda suka taho a hanya doctor ya kasa magana,gaba ɗaya ranshi aɓace yake


Murmushi barrister yayi sannan yace.


"No wonder mutumina jiya ka kasa bacci,ashe amaryace ke hannun kwalawa,dole hankalinka yaƙi kwanciya"ya ƙarasa maganar yana dariya.


Tsaki doctor yayi sannan yace.


"kai daɗina dakai zancan banza wlh,to bari kaji ni wlh ba son salma nakeyiba,ba abinda zanyi daita,ɓarauniya ce fa"


"to su ɓarayin ba mata bane?,kuma zancan sata ay dana,kaida ganinta a yanzu kasan ko ɗaura mata kayan satar akayi a hannunta seta gudu tabarshi aguri,to kuma shine abun dogaro dan kawai tayi sata ada,ay yanzu ta tuba"


"to komade me zakace ni banasonta,kuma bazan taɓa sonta ba"


"hhhhh ah gaskiyane wannan arashin sonne ma jiya ka kasa bacci sabida kaganta acikin mayuyacin hali"


"wlh bana son salma tausayinta kawai nakeji amatsayinta na musulma"


"tausayi baya zuwa seda soyayya,mutumina kayarda kana cikin soyayyar salma kawai"


"karubuta ka ajiye,ni najeebullah,nafi ƙarfin salma nesa ba kusaba,na faɗa maka ni ba sonta nakeba,karka sake yimin wannan maganar pls"


Dariya yayi sannan yace 


"to tuba nake angon salma"


Tsaki doctor yayi sannan yamaida hankalinsa kan titi.


"Amman najeeb nayi mamakin abinda ya hana salma faɗin inda ta sato jakar nan,nifa ina ganin kamar anyi mata sihirin daya rufe bakintane,sabida inkayi laakari tana yunƙurin faɗi amman se ta kasa"


shuru doctor yayi yana nazarin maganar zuwacan yace.


"tabbas naga alamar hakan,to amman yazamuyi,yanzu?"


"ka kwantar da hankalinka kamance mahaifina malamine,aykawai gobe mu shirya muje katsina,gurinshi muyi masa bayani danni banaso mu shiga kotu asake ɗaga ƙara,sonake ayiwa shariar salma zama ɗaya tak dan asallameta da wuri,ayi ayi ashafa fatiha dannaga angon nata kamar amatse yake"


wani duka doctor yakaiwa barrister wanda saura kaɗan motar ta kwace a hannunsa.


Dariya barrister yadunga yiwa doctor shiko yasha kunu kamar be taɓa yin dariyar ba.


Washe gari da Asuba suka ɗauki hanyar katsina,sun isa lafiya.


Inda sukayiwa baban barrister bayanin abunda yakawosu,ayko beyi ƙasa a guiwaba yayi istahara ya tabbatar musu da hasashensu,daganan,rubutu yayi na ayoyin Allah,ya wanke yabasu yace abata tasha awanke mata fuskarta da rubutun.


ba yadda barrister beyi da doctor ba akan su kwana amman fafur yaƙi shide sede su tafi aranar.


Ayko dole barrister yabishi suka ɗauko hanyar Abuja,basu isoba se ƙarfe biyu nadare,barrister se mita yake masa da cewa.


"wlh akan taka amaryar baza ka illatawa tawa amaryar ni ba ehe" 


doctor yagaza bashi amsa haka sukayi sallama.


Washe gari takwas na safe a gidan yarin tayi musu.


inda doctor shida kanshi yaba salma rubutun tasha sannan ya wanke mata fuskar.


cikin hukuncin ubangiji tun kan su tambayeta tafara faɗin.


"jakar ta Alhaji Adamu canji ce ma'aikacin CBN"


Daga haka rakwashe komai ta sanar dasu tundaga ranar data fara haɗuwa dashi.


godiya suka yiwa Allah,daya bata damar faɗin sunan me jakar.


Daga gidan yarin,cbn sukaje neman Alhajin amman basu sameshiba dan haka hotel ɗin da abun yafaru sukaje.


Inda suka nuna katinsu na shaidar ayki sannan suka buƙaci da a nuna musu video na wunin ranar da abun yafaru.


Ansha wuya kamin asamo video ɗin,koda aka kunna.


Wani mutumne yashigo sanye da baƙaƙen kaya ɗauke da wata ƙatuwar jaka,wani ɗaki yanufa,abakin ƙofar ɗakin ya tsaya yakira waya,zuwacan sega Alhaji adamu canji yazo ya buɗe ya amshi jakar ya koma ciki shi kuma mutumin ya juya yatafi,baa jima sosaiba sega salma ta fito ɗauke da jakar tana ta waige waige alamar rashin gaskiya,zuwacan kuma seta daidaita tafiyarta tazo tawuce ɗauke da jakar.


gwauron numfashi suka ja dukansu,sannan sukasa aka dubo list ɗin sunaye na ranar,inda sukaga sunan Alhaji adamu canji shine yakama ɗakin da salma tafito daga ciki.


Da ƙyar manajan hotel ɗin ya amince ya basu list ɗin da plate ɗin video,seda suka sha fama dashi sannan yabasu amman dasunan aro.


Daga hotel,kotun ɗaukaka ƙara suka je suka shigar da ƙara inda aka tsadar musu da lokacin da zaa saurari ƙarar.


Amman kamin zuwan ranar,kotun taba hukumar ƴansanda umarnin atsare Alhaji Adamu kamin zuwan ranar.


Ayko cikin saa ƴansanda suka kamoshi a airport yana shirin bsrin ƙasar sabida yasamu labarin komai.


muje zuwa 


surbajo for life.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*


Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*13*



Rana bata ƙarya.


Ayaune dubban mutane suka hallara ababbar kotun ƙasa dake Abuja domin suraran shariar su salma.


An fafata ankai ruwa rana tsakanin barrister kabeer,da lauyan Alhaji Adamu,sabida ƙwararren lauya ya ɗauka, daga ƙarshede su barrister kabeer suka gabatar da shaidunsu,da hujjoji,wanda hakan shi yajanyo alƙali ya yanke hukunci batare da ɓata lokaciba.


Kotu ta wanke salma daga zargin da ake mata inda shikuma Alhaji aka yanke mishi hukuncin kisa ta hanyar rataya...


Haka kotu ta watse kowa se barka yakewa salma itako se kuka takeyi,na farin ciki.


Da kyar take taka ƙafarta sabida tsawon shekaru biyun datayi a gidan yari ɗaure take cikin sarƙa.


Ahaka suka fito harabar kotun,ƴan jarida ne suka zagaye salma suna mata tambayoyi,da sauri doctor yasha gabanta,ya kareta,sannan ya dakawa ƴan jaridar tsawa da cewa.


"Dalla malamai ku ƙyaleta,ina ruwanku dason sanin halin farincikin datake ciki,meyasa lokacin da aka kamata bakuje kunyi mata irin wannan dairar ba?to bazatayi magana ba"yana kaiwa nan yajata da ƙarfi suka bar gurin.


A mota suka sami barrister yana jiransu,doctor sakinta yayi yaje ya buɗe gaban motar yashiga,salma hannu tasa zata buɗe bayan motar,da sauri doctor ya dakatar da ita da cewa.


"ke gidan ubanwa zaki bimu kuma?ay mungama aykinmu,dan haka kibi wani sarkin bamuba,dan munan da kika ganmu babu wani me neman mata,acikin mu bare kice ko kinyi kasuwa ne,kuma babu ɓarawo anan bare kice zaki bimu mu ƙara miki sani akan harkar dan haka tun wuri ki kama kanki,useless kawai"


durƙushewa tayi agurin tana kuka jikinta se rawa yakeyi,numfashinta na haurawa sama zuwacan ta kife agurin a sume.


A gigice doctor ya buɗe motar yazo gurinta kinkimarta yayi yasaka abayan motar,sannan shima yashiga bayan ya ɗora kanta akan cinyarshi sannan kabeer yaja motar da gudu suka nufi Asibitin da najeeb yake Ayki.


A hanya kamin suje,najeeb yafara bata taimakon gaggawa,inda ya ɗora bakinshi akan nata yafara hura mata iska ta baki,sannu a hankali tafara numfashi sama sama,a haka suka ƙaraso asibitin.


Doctor be jira akawo gadon ɗaukar marasa lafiyaba dakanshi yaɗauketa yayi cikin Asubitin da ita kabeer na binshi abaya.


Hankalin doctor be kwantaba seda yaga salma ta dawo cikin hayyacinta ba abinda ke damunta.


Abinci yadunga bata abaki harseda tace ta ƙoshi sannan ya ƙyaleta,shide kabeer yana gefe,cikinshi ya cika da dariya amman ya danne shiyasa ya ƙosa su fita.


Allurar bacci doctor yamata,shima da kyar ta yarda,sabida tana kunyar yaga jikinta,shiko ko ajikinshi dan juyawa yayi yana kallon kabeer rai aɓace yace.


"Malam baka ganin zan mata allurane?dan Allah kaɗan je daga waje,haba mutum se shegen sa ido"


Ba musu kabeer yafita,sannan,doctor yajawota jikinshi ya matseta ya ɗaga doguwar rigar dake jikinta,yaɗan matsar da fant,ɗin yayimata allurar,sannan ya saketa se kuka takeyi.


Shiko ba abinda yafi bashi mamaki,se irin dattin da yaga fant ɗin yayi,hakan na nufin shikaɗai take sawa acan kenan,sosai ranshi ya ɓaci dan haka kwantar da ita yayi,yafara yimata general check off na cututtuka,inda yasamu,tana da maleria da typhod.


Magunguna ya ɗauko  da suka dace yabata tasha,sannan tafice daga ɗakin.


A harabar Asibitin suka haɗu da kabeer.


kabeer yana ganinshi yamiƙa masa key ɗin motar yace.


"Don Allah kaɗanyi driving ɗin inni nace zanyi komai ze iya faruwa" 


ba musu ya amshi key ɗin suka shiga motar yaja suka ɗau hanya.


Ay kabeer kamar jira yake,yafara tuttular da dariyar data cika mushi ciki.


shiko najeeb ƙara shan kunu yayi alamar ba wasa.


"wlh najeeb baka da kunya,wai har zancema son salma kakeyi amman ka ƙaryatani,inba sonta kake yiba ina ruwanka da ƴanjaridar ɗazu,?in ba so meyasa ka ruɗe sanda ta faɗi bayan kaine silar faɗuwar tata?inba so meyasa ka gaza jira mu iso asibiti kadubata,kafara bata taimako tun amota?,finally,meyasa kaji kishin inga jikinta sanda zakayimata allura?"kabeer ya faɗi yana dariya.


wani uban tsaki najeeb yaja,sannan,yace.


"Kaide anyi ɗan iska wallahi,inbanda kaiɗin,bakasan aykinaba,taya zanga mutum asume amatsayina na likita nawuce batare dana taimakeshi ba?kuma shi kenan danni ɗin ɗan iskane se inbari kaga jikin patient ɗina alhalin kaiba muharraminta bane?su kuma ƴan jarida in aka barsu ay zuwa zasuyi su yaɗa ƙarya da gaskiya,shiyasa na hana badan komaiba,sedan ƴar uwatace a musulunci,kainifa kabeer ka isheni wallahi banason salma bana ƙaunarta sam,dan bata jikin jerin matan danakeso,inkuma kasake magana wallahi sena saukeka a titi"


Shuru kabeer yayi amman fa bedena dariyaba,musamman sanda suka tsaya awani boutique,yatambayi najeeb mezasuyi anan,yabashi amsa da cewa.


"salma zamu siyawa kayan dazata canja najikinta sunyi datti"


Sosai kabeer yake dariya ahaka suka shiga gurin,yazaɓo mata dogayan riguna masu kyau guda biyar,sannan ya isa gurin su fant da bra,ido kabeer ya ware yana kallonshi,ba abinda yafi ba kabeer dariya kamar ganin yadda najeeb in ya ɗauko fant ko bra,seyayi ɗan tunani kaɗan,sannan se ya jujjuya,wani yaɗauka wani ya ajiye,hakanne yasa kabeer ya gano,doctor yana kallo salma aranshine sannan ya zaɓi wanda yake ganin ze mata daidai.


"mutumina kace abun yayi zurfi har haka ashe bansaniba,ah lalle salma tagama da zuciyarka sauran mata se haƙuri,princess over the universe ta iso"kabeer ya ƙarasa zancan yana dariya.


Duka najeeb yakaimasa,sannan yace.


"Tunda kazama maye bari na kyaleka duk abinda zakace kaje kaita cewa tunda de ni nasan basonta nakeba ay shikenan"


Har suka dawo Asibitin kabeer bedena tsokanarshiba,sanda suka shiga ɗakin tana bacci dan haka ajiye kayan sukayi,har zasu fita doctor yaga gashi ya rufe mata fuska,komawa yayi ya gyara mata,sannan suka fice.


muje zuwa.


surbajo for life.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*14*



Salma farkawa tayi taga leda akusa da ita,buɗewa tayi abinda tagani acikine yabata tabbacin natane,to amman waya siyo mata?.



Wanka tashiga,ta jima a toilet tana wanke jikinta,haka ta dunga zubar da ruwa baƙiƙƙirin sabida dattin jikinta,haka gashin kanta,tajima tana wankeshi,dayake a office din doctor ɗakin yake,tamkar de shine emergency ɗinshi,to komai akwai na amfani a toilet din,hadda hand drayer dan haka busar da gashin tayi.


Kusan awa biyu ta ɗauka a bayin sannan ta fito,


Fant tasak da bra ba ƙaramin mamaki tayiba ganin yadda suka mata daidai,dan ko ita taje siyowa da kanta tana mistakes,riga ɗaya ta ɗauko tasaka,rigar,ja ce da gyalenta shi kuma fari ,ajiye gyalen tayi,tafita zuwa cikin office ɗin doctor ɗin tafara neman ko turarene,ayko ta gano wani tafesa sannan tadawo ta ɗauki cumb tafara tace kanta.


Zafi take ji sosai yayin taje kan,amman haka ta daure tanayi ta runtse ido wanda kowa yaganta yasan ba ƙaramin zafi take jiba.


Doctor ne ya shigo ɗakin fuska ba walwala,itako sabida zafin da kanta yake mata batasan yashigo ba,zuwa yayi ya riƙe hannun datake taje kan dashi,da sauri ta ɗago kanta tana kallonshi,ganin shima ira yake kallone yasa tayi ƙasa da idonta.


"Shi taje kan dole ne se anyi shi tunda anajin zafi?"doctor ya faɗi rai aɓace,


Shuru tayi ta ƙara yin ƙasa da kanta,dan yanzu gaba ɗaya nauyinshi takeji.


"kar in kuma ganin hakan,inba hakaba rai ze ɓaci,taso muje kici abinci"yana gama magana yajuya yayi gaba,miƙewa tayi ta yafa gyalen rigar tabishi abaya ƙafa ba takalmi


Yana gaba tana binshi abaya har zuwa harabar asibitin se alokacin ya lura ƙafarta ba takalmi,miƙa mata takalminshi yayi yace tasaka.


tsayawa kallonshi tayi ganin ba wasa afuskarne yasa tayi saurin zira takalmin shikuma yaci gaba da tafiya ba takalmi har suka isa motarshi.


wani gurin saida takalma ya tsaya,ya fita zuwacan se gashi yadawo,da sabon takalmi aƙafarsa sannan itama ya siyo mata nata aka sako a leda.


Restaurant yasamu me kyau ya tsaya sukaci abinci sannan suka fito suka shiga mota.


Hanyar kaduna taga ya ɗauka,wani farincikine ya lulluɓe zuciyarta yau,zataga iyayenta,ɗa aminiyarta.


Suna tafe a hanya ko tari tayi,seya waiga ya kalleta,amman bazeyi magana ba ahaka har suka iso garin kaduna,waigowa yayi yakafeta da ido hakanne yasa tagane Address yake nufi tadunga nuna masa.


Ayko haka ta dunga yimasa kwatance har suka iso ƙofar gidan,sahabi suka samu zaune agaban gidan yakasa kayan miya yana siyarwa.


parking Doctor yayi,da gudu salma tafice amotar,ƙafarta sanye cikin takalminshi tanufi yayan nata tana kiran sunan shi.


A gigice sahabi ya ɗago yana kallonta,naso me karatu yana gurin yaga iri. Tafiyar yajin da sahabi yayi da kayan miyan daya kasa,gurin kwasawa da gudu zuwa cikin gidansu.


Duk miskilanci doctor seda yadara,da gudu itama salma tabi bayan sahabin zuwa cikin gidan.


Lokacin babanta yafito daga bayi ganin sahabi da gudune yafara tanbayarshi ko lafiya,ganin salma da gudune yatabbatarmishi dacewa tabbas ba lafiya.


Dagudu mahaifiyarta ta fito daga kitchen ta burma ɗaki hakanne yasa su sahabi maramata baya,suka shige suka kulle ƙofar.


Zuwa ƙofar ɗakin tayi tana bubbugawa tana cemusu itace ba mutuwa tayiba amman ina ba wanda ya saurareta dukansu se karatun qurani suke kai kace a masallacin harami🤣🤣


Magiya bawacce bata musuba amman bawanda ya saurareta,haka ta juya tafice daga gidan tana kuka.


Doctor koda ya hangota tana kuka murmushi yayi dan yasan zaa rina,fita yayi a motar yaje yasha gabanta,jan hannunta yayi suka koma cikin gidan.


Sallama yashigayi,amman jin sautin karatunsu ba ƙaramin dariya yabashi ba amman daurewa yayi beyiba yaci gaba da sallamar.


Da kyar sahabi yace sadaƙallahul azim,ya amsa sallamar,leƙowa yayi ta window ganinshi tare da salma ne yasa yamaida windon ya kulle ya ɗauko sabuwar sura ya ɗora daga inda ya tsaƴa.


Sunfi awa uku atsaye suna musu magiya sannan suka yarda suka fito,da gudu salma tanufi mahaifinta da zummar rungumeshi,ayko ya beyi ƙasa a guiwaba ya kwasa da gudu ze koma ɗakin,yana faɗin.


"wayyo Allah na nashiga uku,gurina aka aykota,Allah ka kawomin agaji"


da sauri salma takoma ta tsaya akusa da doctor,ganin hakane yasa baban nata tsayawa yana mazurai.


Duk abinda yafaru doctor yakwashe yasanar dasu,inda ya kama hannun salma ya miƙa musu yace su taɓa suji ita mutumce.


Da ƙyar suka taɓa  ay suna taɓawa suka rungumeta suna kukan murna.


Ranar wuni sukayi tattalin salma,inda tanemi yafiyarsu game da bijirewa tarbiyyar da suka bata.


mutanan gari se zuwa ganinta akeyi,feefee ma baa barta abaya ba.


Kowa se murnar ganinta yakeyi,shaf salma ta mance da doctor dake ɗakin sahabi yana hutawa.


Se bayan sallar magrib data fita raka feefee ne ta hangi motarshi,gabantane ya faɗi,da sauri sukayi sallama da feefee ta nufi ɗakin sahabin.


Azaune tasameshi yana duba wayarshi,tana shiga ya miƙe yace mata.


"To Allah ya kyauta gaba,saduwar alkhairi"yayi hanyar waje ze fice.


Bakin salma har rawa yakeyi,gurin furta.


"Don Allah doctor kayi haƙuri"


Dakatar da ita yayi ta hanyar ɗaga mata hannu,buɗe labulen yayi ze fita amman se jiyayi anriƙe masa hannu da sauri ya waiga.


salmace durƙushe akan guiwarta,idonta na zubar da hawaye,tace.


"kamin dukkan halacci,banida bakin godemaka,bani da abin biyanka dashi,sede Allah ne ze biyaka,don Allah doctor karka tafi acikin darennan,inajin tsoro kar wani abu ya cutar dakai,don Allah badan niba ka kwana gobe katafi"


ganin yadda ta marairaicene yasa doctor,komawa ya zauna wanda shikanshi,besan sanda yayi hakanba kawaide yabi umarnin zuciyarshine.


Ayko haka doctor ya kwana agidan nasu salma batare da nuna kyama,agaresuba,mahaifanta se godiya suke masa harda kuka,shi kuma se tsintar kanshi yayi dajin kunya da nauyinsu.


Washe gari da sassafe ko salma be jira tazo sun gaisaba yayi sallma da malam da sahabi ya ɗauki hanyar Abuja.


*Wai waye doctor najeeb*


muje zuwa,



Surbajo for life.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*masoyana ina alfahari daku ako ina kuke,nima ina sonku,gaskiya bazan ɓoye mukuba,comments ɗinku nayau yamin daɗi ba kaɗanba,Allah yasa ku ɗore ahaka,sabida comments shike ƙara mana ƙarfin guiwa,nagode nagode nagode sosai,dan wlh ban ɗauka ana karanta littafin kamar hakaba,naji daɗi Allah yabarmu tare,burin surbjo kenan kullum sanya farin ciki da walwala acikin zukatanku,domin mantar daku ɓacin rai,love you all*.



*15*



Najeeb Hassan Alkanawi shine cikakken sunanshi.


Saurayine ɗan kimanin shekaru talatin da biyar da haihuwa.


Ɗan garin kano ne,acikin anguwar nasarawa GRA gidan mahaifinshi yake.


Mahaifinshi Alhaji hassan Alkanawi,hamshaƙin me kuɗine ajihar ta kano,mahaifiyar najeeb ta rasu tun yan da shekara goma aduniya.


Yataso a hannun kishiyar mahaifiyarshine me suna hajiya kaltum,sam hajiya kaltum bata ƙaunar najeeb ko kaɗan,duk wani abu daze zama sanadin farincikin shi bata sonshi,kuma setasan yadda tayi ta hanashi samunshi.


Najeeb mutumne miskili me haƙuri,ko kaɗan amman beson raini,mhaifinshi nasonshi yanamasa duk abinda yakeso,amman in hajiya kaltum tagani kotasan zaamasa seta hana.


Dayake Alhjin tsoronta yakeji.


Dakyar njeeb yasamu yagama karatunshi har yasamu ayki,najeeb kyakkyawne ajin farko,duk abinda ake kira kyau ajikin ɗa namiji najeeb ya mallakeshi.


Kyanshine ya janyo hajiya kaltum jin,shaawar haɗa shinfiɗa dashi.


Tun tana ɓoye mishi nufinta har tazo ta bayyana masa face to face,ranar najeeb kwana yayi kuka sabida be taɓa ganin balai irin wannan ba.


Su uku ne agurin mahaifinnasu,shi da ƙannasa mata guda biyu hassana da ussaina,wainda suke ƴaƴa ga hajiya kaltum.


Mahaifinshi mutum ne me tafiye tafiye,shiyasa da zaran yabar ƙasar hajiya kaltum se ta buɗe babin iskanci.


so biyu tanayin tsirara agaban najeeb wai dole sai ya kwanta da ita.takaicin hajiya kaltum ne ya haddasawa najeeb kamuwa da ciwon zuciya.


Sabida ita seda yasauya keys ɗin ɗakinshi amman kamar tsafi seta sama cikin dare sede yajishi rungume ajikinta.


so tari najeeb yasha kwana acikin lambun gidansu,sabida balain hajiya kaltum.


Tunda tafara nuna masa mugayan halayantane yafara neman transfer daga asibitin murtala na kano zuwa keffi,dan yafiso yayi nisa da gidan.


Cikin hukuncin Allah yasamu transfer ɗin ya haɗa inashi inashi yabar garin kano zuwa keffi tunda yakoma keffi da ayki se yayi shekara bezo kanoba,kuma ko yatashi zuwa se yasan mahaifinshi na gari yake zuwa.


Wannan hali na hajiya kaltum ne yajanyo najeeb ya tsani soyayya,sam sho ko macema bata birgeshi,sabida gani yake duk halinsu ɗaya.


Sanda yafara ganin salma yayi mamaki daya amince tazauna a office ɗinshi.sabida shi a ƙaidarshi baya lura da coper tamace sede namiji,sabida yatsani yin alaƙa kowacce irice da mace.


To amman abin mamaki yagaza korar salma kamar sauran.


yarasa dalili duk ranar dayaga salma tayi shiga mara kyau,wuni yake ya kwana cikin takaici da baƙinciki.


Uwa uba kuma idan yaganta da Alhaji Adamu,har ƴar matashiyar hauka yake aɗakinshi,sabida baƙin ciki.



Tunda yasamu labarin mutuwarta,yazama wani iri sam bashida natsuwa da kwanciyar hankali kullum cikin yimata addua da sadaka yake,kuma koyaushe se yayi mafarkinta,se ya dangana hakan da sa tunaninta arai dayayine.


Shiyasa randa yaganta a tv ya ruɗe sosai.


Besamu kwanciyar hankaliba seda yaga ya kuɓutar da ita.


*CIGABAN LABARI*


Awa biyu doctor yayi ahanya sannan ya iso Abuja.


Office ɗinshi yanufa yafara duba marasa lafiya,har zuw lokacin da,ze tashi.


Yana barin office ɗin gurin barrister kabeer yanufa sabida sunyi waya yashaida mishi yana hanya inya iso zezo gurinshi.


muje zuwa.


surbajo for life.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhamnad Mahmud


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*16*



Yana shiga office ɗin barrister,tunkan yazauna barrister ya kwashe da dariya yana faɗin.


"najeebullahi na salma me abun mamaki,naku salon ba irin namu bane,laila majnun"yasake kwashewa da dariya har yana dukan table.


Haushine yaka najeeb,game da haɗashi da salma da yayi,dan haka miƙewa yayi ze tafi.


Da sauri kabeer yasha gabanshi yana dariya,yace.


"haba angon salma,banason wulakanci,yazaka kaje kayi kwanan soyayya,sannan dan wulaƙanci katashi zaka tafi baka bani labariba"ya ƙarasa maganar yana dariya sosai.


Bige hannunshi najeeb yayi sannan yace.


"uban waye yayi kwanan soyayyar,dahar zan baka labari?ni wallahi ka isheni da zancan yarinyarnan nasha faɗa maka ba sonta nakeba meyasa bazaka gane bane?"najeeb ya ƙarasa maganar cikin ɗaga murya.


Dariya kabeer yayi sannan yace.


"Ay danna fahimcekanne yasa nake fitoma da abun dake danunka wanda kai kaƙi amincewa dashi,shiyasa nake saka ahanya gudun aykata,danasani anan gaba"


Tsaki najeeb yayi sannan yace.


"inde akan salma ne babu ni babu danasni har abada,karubuta ka ajiye,kuma zancan kasani a hanya ma be tasoba,dan haka kabarni da damuwar tawa dakai ka hangota wacce ni bansan tana damuna ba"


Shide kabeer inbanda dariya ba abinda yakeyi gaba,ɗaya yakasa magana.


 A fusace najeeb yabar office ɗin yatafi gidanshi,dan ya lura kabeer ɗan rainin wayone dole yataka masa burki tun wuri.


Koda ya koma gidan gaba ɗaya ya rasa sukuni,salma kawai yake gani a fuskar shi,yayin da muryarta ke masa gizo a kunnensa.


A taƙaice de ranar beyi bacciba salma ce kawai aranshi.


Itama salma anata ɓangaren,koda ta tashi akace mata yatafi sam bataji daɗiba,dan yanzu bata gajiya da kallo dajin muryarshi,haka ta wuni tamkar mara lafiya.



Da safe doctor daya isa office ɗinshi ɗakin da salma ta kwanta ya shiga,ledar kayan daya siyamata yagani a ajiye akan gadon.


Ɗauka yayi yaje yasa a mota yadawo yafara duba marasa lafiya,wuni yayi yana kewar salma.


A daddafe ya iya yin sati ɗaya,ranar daya cika sati yakama hanyar kaduna.


Be jimaba ya isa,seda ya isa ƙofar gidanne kuma ya daburce yarasa mezece ya kawoshi,zama yayi amotar yana kallo ƙofar gidan inda sahabi ke zaune yakasa kayan miyansa.


Dayake bada motar daya kawo salma yazoba shiyasa sahabi be gane shiba,daɗin daɗawa glass ɗin motar baƙine,shine yabashi damar kallon komai batare da ansa yana yiba.



Salmace ta fito daga gidan  sanye cikin dogon hijbi har ƙasa,hannunta riƙe da qurani,tagaban motarshi tazo ta wuce dan haka binta yayi baya dan yaga inda zata.


wata makarantar islamiyya yaga ta shiga,awa biyu yayi yana jiranta zuwacan segata ta fito ta kama hanyar gidansu sake binta yayi har suka dawo gidan,tashige gida shi kuma yayi parking.


najeeb yarasa abinyi,gashi laasar har tayi,be samu mafita ba,dan haka shahada yayi yafito yanufi sahabi.


Sallama yamasa cike da faraa sahabi ya ams yace.


"kaine tafe da yammacinnan?"


"munzo ɗaurin auran abokinmune,shine nace bari inbiyo mugaisa da baba"



"ikon Allah gaskiya ka kyauta wlh,sede baba bayanan yaje kano taaziyya,se mamace kawai muje ku gaisa"


Riƙe da hannun juna suka shiga cikin gidan.


Shigarsu tayi daidai da fitowar salma daga wanka ɗaure da tawul ko cinyoyinta be gama rufewa ba, dayake toilet ɗin atsakar gida yake.


batasan sunshigoba se aykin girgiza kanta takeyi,tanaso ta rage ruwan dake kan nata.


Tunda suka shiga idon najeeb ya,sauka akan fararan cinyoyin nata masu kyan tsari,wani abune ya,tsirga masa tundaga saman kansa zuwa tafin ƙafarsa,sam yakasa ɗauke idonshi akanta.


Shiko sahabi cikin masifa yatunkareta da niyyar dukanta yana faɗin.


"waike salma ubanwa zaki nunawa boko da wayewa,banace kar insake ganinki ɗaure da tawul zaki wanka ba,amman dayakw kinga ba yanzu zan shigoba shine kika ɗaura ko?"


Ɗagowa tayi daniyyar bashi haƙuri,karab idonta yasauka akan na doctor,da wani mahaukacin gudu ta faɗa cikin ɗakinta tamaida ƙofar ta rufe,jikinta se ɓari yake,shiko sahabi yaɗauka shi ta gudarwa danhaka juyawa yayi yana faɗin.


"ƴar nema yau da kintsaya dana koyamiki hankali"


Ɗakin mahaifiyarsu yashiga yaɗauko tabarma ya shimfiɗawa doctor sannan yakoma yatasota dayake bacci takeyi.


Tayi murna da ganin doctor ba kaɗanba,rasa inda zata sashi tayi,sun ɗan taɓa hira sannan yamiƙe ya ajiye musu kuɗi kimanin dubu ɗari biyar yace aba baba yaja jari.


Da kyar suka amshi kuɗin sunata samasa albarka,sannan sahabi ya rakashi mota,har yashiga,se sahabi yace.


"kaga har zaka tafi baku gaisa da salma bari inturota ku gaisa ay ba daɗi kazo baku gaisaba" 


Yana kaiwa nan yajuya yashiga cikin gidan,yadunga kwala mata kira,fitowa tayi sanye da doguwar riga,ta yaf mayafi a kanta,bejira me zatacw ba yace.


"maza kije ku gaisa da najeeb sauri yake ze koma"


Yana gama bata umarnin yashige ɗakin mahaufiyarsu,ita kuma takama hanyar zuwa gurin najeeb ɗin.


koda tazo ƙofar gidan kasa ƙarasawa gurinshi tayi,dan ba ƙaramin kunyar haɗuwa dashi takeba,


Tun fitowarta najeeb yaganta,tunda ya lura bata da niyyar ƙarasowa ne,se yamata full light da fitilar motarshi kasancewar duhun dare yafara.


Hannu tasa takare hasken,jikinta har rawa yake,shiko waya yasa ya ɗauketa hoto ahakan,batare data saniba,horn yamata,da sauri tacire hannun data rufe fuskar,sake yimata wani hoton yayi.


Itako salma ganin yaƙi,dena haskatane yasa ta gane kiranta yakeyi,dan haka cike dajin kunya ta ƙarasa gurin motar.



Muje zuwa.


Surbajo for life.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*MY BABY MANAL ALLAH YABAKI LAFIYA,DON ALFARMAR ANNABI DA AL-QUR'ANI,AMEEN😭*



*17*



Koda ta ƙaraso gurin motar tsayawa tayi tana rufe idonta,


Najeeb buɗe ɗayan ɓangaran yayi amman bece mata ta shiga ba.


Jiki asanyaye ta shiga cikin motar ta zauna,ta maida murfin ta rufe.


Rusunar da kanta tayi sannan tace.


"doctor an wuni lafiya?ya bayan rabuwa?"


Shuru yayi be kulata ba,ƙarshema se yayi adjusting ɗin kujerar ya kwanta,ya lumshe idonsa,


Salma duk ta takura,dan ita yanzu cika mata ido yakeyi,gawata uwar kunyarshi da take ji datake hanata sukuni.


"Doctor dan Allah kayi magana mana"salma ta faɗi cikin wani salo wanda ita kanta batasan tayiba.


Da sauri doctor ya buɗe idonsa yana kallonta sabida salon yadda tayi maganar ya shigeshi.


"in nayi maganar me kikeso nace"cewar doctor cikin muryar da ke nuna kulawa.


shagwaɓe fuska salma tayi sannan tace.


"Haba doctor yanzu abinda zakace ɗinma nizan faɗa maka?"


Idonshi ya ɗan lumshe yana kallonta,sannan yace.


"To ayni ban iya surutubane shiyasa nace ki faɗamin abinda zance"


Turo baki gaba tayi sannan tace.


"to kace komai mana"


"to nace komai"doctor ya faɗi yana haska fuskarta datasha kwalliya da wayarshi.


"Wannan kwalliyar wakika yiwa?"


Zaro ido salma tayi sannan cikin inda inda tace..


"ba wanda nayiwa kawai de nayine"


Tissue ya miƙa mata yace.


"to amshi ki goge tunda bawanda kikayiwa"


"in nashiga gida zan goge"salma tabashi amsa.


Shuru yayi yana binta da ido,ya rasa yanayin dayake tsintar kanshi in salma tana magana.


Hannu ya miƙa sit ɗin baya ya ɗauko ledar kayanta data manta.


miƙa mata yayi ta amsa taɗan buɗe dan ganin abinda ke ciki,ay tana buɗewa taci karo da fant ɗinta nagidan yari wanda farine azabar datti ta maidashi ash,ay salma bata tsaya wata wataba tabuɗe motar riƙe da ledar ta kwasa da gudu zuwa cikin gida.


Ba ƙaramin dariya gudun nata yaba doctor ba,da ƙyar yaja motar yabaro ƙofar gidan,yakama hanyar,kano sabida mahaifinshi yadawo yana gari.


Salma ko bata dena guduba seda ta dangana da gadonta.


Dariya da kunyane suka dirar mata lokaci guda,haka taita darawa ita kaɗai aɗaki.


Miƙewa tayi takai wandon da doguwar rigar data fito dasu daga gidan yarin,taje tasaka a shara sannan taje ta buɗe ledar  ragowar  kayan daya siya matane aciki,se sabon takalmin daya saimata ranar dazasu zo kaduna ta manta dashi a motar shi.se rafer ta kuɗi kimanin dubu hamsin,se waya ƙirar samsung galaxy s7edge.silver colour.


Ɗaukar kayan tayi gaba ɗaya taje ta nunawa ummanta da sahabi,sosai siyayyar tabasu mamaki.


bama kamar ummanta dan cewa tayi.


"salamatu kode sonki yakeyine,wannan bawan Allahn,inde ba so ba ay hidimar tayi yawa"


"wlh umma ba sona yakeyiba,kawai de halinshine kyauta koda besan mutumba"



Fatan alkhairi sukayi gameda hakan sannan salma taba sahabi kuɗin tace yaƙara ƙarfin jarinshi yakoma kasuwa da saida kayan miyan.


Da ƙyar sahabi ya amshi kuɗin,shima seda ummansu tasa baki,godiya yayiwa salmar sosai.


Daga haka ta kwashe sauran kayan tawuce ɗakinta,farincikine fal zuciyarta,dan ita babu abinda yafi burgeta a tsarabar kamar wayar daya siya mata.


Koda taje saka charge ganinta tayi acike wato anmata chargen ta,harda sim card aciki na mtn.


Game tayi taɗan duba abinda baa rasaba ta ajiye wayar tayi sallar ishai sannan taje tayiwa ummanta seda safe,tadawo ɗakinta ta kwanta,ba jimawa bacci yayi awon gaba da ita.


Shiko doctor be isa kano ba se shaɗaya na dare,kowa yayi bacci dsn haka shima ɗakinshi ya buɗe ya kwanta bayan yayi wanka yayi sallah.


koda ya kwanta sam baccin ya gudu,tunanin salma da muryarta kawai yakeyi,ganin ba sarki se Allah ne yasa ya jawo wayarshi yafara kiran layin daya samata a wayar,seda yakira har so uku bata ɗagaba,da kamar ya haƙura sekuma yasake kira,ayko kamar jira yana kira ta ɗauka,tayi sallamah cikin muryarta ta bacci.


Shuru doctor  yayi yana sauraron saukar numfashinta.itace ta katse shi da cewa.


"doctor ko kayi bacci ne?"


"waya ce miki shine ya kiraki"cewar doctor.


murmushi salma tayi sannan tace,


"sabida sanin danayi shikaɗai ze iya kirana ta layin da shine ya siya kuma ban ba kowa"


"hmmm to sannunki,da gudu,watarana inkina irin wannan gudun sekin fasa baki"


Dariya salma tayi batace komaiba.


shima shuru yayi beceba


"doctor naga abin arziƙi nagode Allah ya ƙara buɗi"


hakade yadunga sata magana shide sede yayi shuru,salma bata fargaba sejin saukar numfashin shi takeyi alamar yayi bacci,dariya tayi  takashe wayar itama ta kwanta.


muje [truncated by WhatsApp]

Z*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*


Zahra muhammad Mahmud


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION


*Shafin nakine ke kaɗai,kawata takaina,Allah yaƙara ɗaukaki duniya da lahira yakareki daga sharrin duk wani me sharri,Ameen,MRS FAWWAZ Allah yabarmu tare#ana tare*


*18*


Koda asuba tayi doctor yafarka,yaga wayarshi yashe akan fulo dariya ce ta ƙwace masa,wato suna waya da salma ne bacci ya ɗaukeshi,sede wani abu daya bashi mamaki shine,rabonshi dayayi bacci me daɗi irin haka tun kamin salma ta ɓace,dan yaji daɗin baccin sosai.


Alwala yayi yatafi masallaci,bayan an idar da sallah,kai tsaye ɓangaren mahaifinshi yashiga sabida beganshi  a masallacinba.


A falo ya tsaya yanata sallama amman shuru bawanda ya amsa,dan haka ya juya ze fita,hajiya kaltum yagani tsaye abakin ƙofar fitar tana mishi murmushi.


Haɗe fuska najeeb yayi sabida ya tsaneta ba kaɗanba,raɓawa yayi ze fice,seji yayi ta rungumoshi,tana mishi kukan kirsa.


"Haba najeeb meyasa baka da tausayine,shaawarka kullum ƙaruwa takeyi araina,don Allah kadaure ka kwanta dani ko so ɗayane"tana magana tana ƙoƙarin shafo ƙasan  wandon shi.


Agigice najeeb yatureta daga jikinshi,rai aɓace yace.


"kaltum kifita harkata ni ba mazinaci bane,kuma ko da ni mazinacine bazan haɗa shimfiɗa da mahaifina ba,wawiya shasha kawai"


"Najeeb ni kake yiwa wannan ɗibar albarkar"


"anmiki ɗin uwatace ke dabazan miki ba,dabba kawai,wallahi nan gaba ma sena zagi uwarki inde baki fita harkata ba"


"na nawa kuma ay sede kar akuma yanzunma kazagi uwar tawa ay,sede kasani,wallahi matuƙar baka biyamin buƙataba,sekayi danasanin zuwanka duniya,kuma wallahi kaida aure sede kaga anayi,inko kayi,matar hotoce agurinka,dan babu wacce ta isa ka shigeta seni"


"Tur dake wallahi,sede kisani,ay bakece Allah ba,tunda ko hakane muzuba nida ke shegene ze fasa"yana gama faɗa mata haka ya hankaɗeta,ya fice daga falon ita kuma ta faɗi ƙasa.


A fusace yaje gurin me gadi yana tambayarshi ko abbanshi yafitane.


"Ranka ya daɗe cikin dare direba yakaishi airport wai yatafi wata ƙasa amman bansan sunanta ba"cewar me gadin.


da sauri yanufi ɓangarenshi,wanka yayi ya shirya,yaɗauki key ɗin motar shi ya fice daga gidan ya kama hanyar Abuja yana me danasanin zuwan shi.


Anata ɓangaren salma itama tashi tayi cike da nishaɗin wayar da sukayi da najeeb in ta tuno ranta se ya mata sanyi.


koda taji shuru be kirata ba ita seta gwada kiranshi.


Adaidai lokacin shi kuma najeeb ya iso kawo kaduna,jin wayarshi na ƙarane yasa yakalli inda wayar take.


*Up to now*shine sunan daya bayyana akan screen din wayar tashi.


Murmushi yayi,danshi kanshi sunan ya bashi dariya.


Katse wayar yayi,yakirata inda ya tsinkayo muryarta tana faɗin.


"doctor ina kwana,ya bacci"ta ƙarasa maganar cikin sigar zolaya.


Wani sanyi yaji yana ratsashi yayinda ya mance da duk wani ɓacin rai dake damunshi,kasa yayi da muryarshi kamar mejin bacci yace.


"Salmah kin fara rainani ko?"


Numfashin salma seda ya ɗauke yadawo,sabida yanayin da ta shiga sanda taji sunanta a bakin doctor wanda bata taɓa jin yakiraba,da kyar ta saisaita natsuwarta tace.


"nidin banza,har na isa na raina ka"


Maganar tamasa daɗi,dan haka gefen titi yasamu yayi parking sannan yace.


"to faɗamin,ya akayi kikasan nayi bacci?"


"numfashinka naji yasauya alamar kayi bacci kuma inata magana naji shuru,shine yasa nagane kayi baccine"ta faɗi cikin muryarta me daɗin saurare.


murmushi yayi sannan yace.


"kice laɓe kikemin kenan awayar,to asheko kinaso na laɓaɓaki"


Dariya salma tashigayi harda hawaye.


Doctor shuru yayi yana jin dariyar tata,dan yasan ba iya maganarshi bace tasata dariyar.

Zuwa can de tace.


"da kana karanta novels se ince acan kajiyo wannan kalmar,dan wlh da lokacin ina cikin wani group na novels na surbajo,to admin ɗin batason mutum yana online amman bazeyi magana agroup ba shine tasa dokar duk wand takama yana laɓe seta laɓaɓashi waje,"ta ƙarasa maganar tana dariya.


Murmushi yayi,dan ya fahimci salma har yanzu da akwai yarinta atattare da ita.


"To kika sani ko nima surbajonce ta koyamin?"


dariya salma tasake yi sannan tace.


"tab ayko bade surbajonmu ba,kaide kasan inda ka koyo kayanka"tayi maganar cikin shagwaɓa.


kawar da hirar yayi da cewa.


"to ƙanwar surbajo me kikaci yanzu da safennaɓ?"


"lah banci abinciba,gashi nande ina ƙarasa haɗawa"


"me kike haɗawa?"


"wainar shinkafane,da miyar taushe"


"zaki sammin naci nima?"


"hhh doctor kenan kaida kake Abuja taya zakaci wainar dake kaduna"


"jiya ba Abuja nawuce ba,na shiga kanone nagaida Abbana,yanzu haka ina kawo kaduna,sede in rowa zakimin?"


"babu rowa tsakanina dakai har abada,komai kakeso kawai kafaɗe shi kanka tsaye,ni kuma zanbaka"


"to ki kawomun wainar junction ɗin bakin ruwa inna ƙaraso seki bani naci,ki tafi da kwanunkan"


"haba doctor yazaayi kaci abinci a titi,kabiyo ta gida mana kaci"


"inada uzurine salmah,ki kawomin inda nace"


"Amman de doctor..."


Katseta yayi dacewa.


"Salmah"cikin wata siga data tilasta mata yin shuru,jin tayi shurune yasa yace.


"zaki kawomun ɗin?"


"Eh zan kawo maka"


"to kiyi sauri"


daga haka sukayi sallama ya ajiye wayar,jinshi yake kamar wani sabon ango tada motar yayi yaci gaba da tafiya.


Be jimaba ya isa bakin ruwan,parking yayi daidai tahir plaza,yana jiranta.


Ita ko suna gama wayar gurin ummanta taje ta sanar da ita komai,dan haka umman fitowa tayi ta amshi suyar wainar,ita kuma salma,ta ɗebo kuloli tazuba wainar da miyar datasha naman kan rago da manshanu,a basket tazuba harda plate da cokali,sannan taje ta sauya kaya taɗan shafa hoda ta ɗauki,abincin ta fice,drope ɗin napep ta ɗauka,dan haka bata jimaba ta iso bakin ruwan.


kiranshi tayi awaya ya faɗamata inda yayi parking,dan haka ƙarasawa tayi gurin,tana zuwa ko ta hango motarshi a gurin,ƙarasawa tayi.


Tunda ta nufoshi yake binta da kallo,ba abinda yafi ɗaukar hankalinshi se yanayin tafiyarta,ga kayan data saka fited gown ce wacce tafitar da shape ɗinta da kyau,se siririn mayafi data rufa akanta zuwa kafaɗarta,tayi masa kyau sosai,sede sanda idonshi ya sauka akan wasu maza da suka zuba mata ido se yaji duk ranshi ya ɓaci.


kamin ta iso,ya buɗe motar yafito,yakoma gidan baya,dan haka tana isowa itama ƙofar bayan ya buɗe mata.


shiga tayi da sallamarta tazauna,sannan ta ajiye kayan abincin aƙasan kujerun sabida motar jeep ce to akwai space.


"wayace ki sako wannan mayafin?"


"wlh sauri nakeyine shiyasa nasakosho kuma napep na hawo tundaga gida zuwa nan ɗin"salma ta faɗi kamar me shirin yin kuka.


"zubamin abincin,Allah ma de yasa yayi daɗi kar inci,in haɗu da bacteria"


murmushi salma tayi ta zuba mishi abincin ta miƙa masa plate ɗin gabanshi,amman se yaƙi ɗauka,binshi tayi da ido,tace.


"doctor lafiya kuwa?"


yamutsa fuska yayi sannan yace.


"Hannuna ba awanke yakeba,kuma ni ban iycin waina da cokali ba,so ayki yasameki dan haka kibani da hannunki"


murmushi salma tayi sannan tace


"to ayga ruwa seka wanke hannun"


"nufinki infitar da hannuna waje ina wankewa,ayko bazan iyaba,in bazaki bani bane to na haƙura da abincin"


kunya duk ta gama kam salma haka ta ɗauke plate ɗin ta matsa kusa dashi,tafara bashi abincin abaki,bako kunya yadunga wangale baki yana amsa,har tagama bashi,koda yazo cin naman ba ƙaramin daru sukaib,dan miƙa mushi cokalin tayi yaci dashi,sam yaƙi ams haka tadunga bashi har yagama ci,zat jiye hannunta,yayi sauri yariƙe,wai dole se ya tsotse hannun sabida,ya ƙarasa ladanshi🤣tanaji tana gani ya suɗe hannun tas,sannan yasha ruwa,ya goge bakinshi da tissue.


me makon taga ya sallameta setaga ya jawo kayan abincin yazuba wani sannan yasa hannun nashi dayace ba wankakke bane ya ɗebo abincin yanufo bakinta dashi,ƙuri tayi da ido tana kallon ikon Allah


"zaki amsane ko sena ɗura miki?"


da sauri ta buɗe baki yasakamata wainar,haka yadunga bata har seda tace ta ƙoshi ya ƙyaleta.


wanke hannunshi yayi awajen dayace baze wankeba,ita kuma ta haɗa kwanukan acikin basket ɗin,duk atakure take ta ƙosa ta fice daga motar.


"kinsn ko kabeer yanzu in yaganki baze ganekiba dan haka bari inmana hoto tare sabida innaje na nunamasa yadda prisoner ɗinshi ta kile" dariya salma tayi da sauri ta yunƙura zata sauka a motar,jawota yayo da ƙarfi ta faɗo jikinshi,ɗago da kanta tayi tana kallonshi,shima ita yake kallo,ahaka yaɗaukesu hoton,ganin hasken camera ne yasa salma ɓoye fuskarta ƙirjinshi,shima sake ɗaukarsu yayi ahaka sannan yasaketa.


turo baki salma tayi gaba sannan ta ɗauki kwanunkanta seda taji ƙafarta aƙasa sannan ta waiga tace.


"wannn ay cin zaline,mutum yagama maka bin kirki kuma kaci zalinshi"tana kaiwa ƙarshe tayi saurin ficewa a motar,


Dariya abun yaba doctor sosai.


buɗe motar yayi shima yafice,yaje inda take,dariya take masa shima dariyar yayi sannn ya ɗaukar mata drop din napep,seda tashiga tazauna,sannan yasa hannu yaja hancinta yace.


"to mara kunya ki gaidamin da ummana d Abbana,da sahabi"yana gam magana ya ajiye mata kuɗi akan cinya ya juya ya nufu motar shi Ya tada ita ya kama hanya,yana jinshi cikin matsanancin farin ciki.


muje zuwa


surbajo for life

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*Don Allah masuyin editing na yar bautar kasa kudena kubarmin shi ayadda nayi editing din kayana,pls🙏*


*19*


Ya isa Abuja lafiya itama ta isa gida lafiya.


Asibiti yafara zuwa ya sallami marasa lafiya sannan yanufi gidanshi.


Yana isa gida ba jimawa kabeer yazo gidan,da murna suka tarbi juna.


Zama sukai suna hirar rayuwar duniya,danshi kabeer bemasan doctor yayi tafiya har ya kwana ba.


Kamar wanda aka tsikara doctor yaje ya ɗauko wayarshi ya nuno hotunansu ya miƙawa kabeer yace.


"ka gane ta jikin hoton nan kuwa?"


Kabeer ko mamakine danƙare a fuskarshi dan besan doctor yanada budurwar da sukayi shaƙuwa kamar haka ba,


Murmushi kabeer yayi sannan yace.


"haba abokina no wonder kace ba son salma kakeyiba,ashe already anjima da cinye zuciyar taka,kana da gaskiya me mace kamar wannan ba abinda zeyi da salma,gaskiya tayi ba ƙarya,wannan tashiga taroce,kamin lokacin auren tun yanzu naɗauki nauyin events guda uku dazaayi lokacin bikin"


Dariya doctor yakeyi sosai sannan yace.


"daɗina dakai wani sain kai gabi ne,dama seda na faɗamata bazaka gane taba inka ganta,to wannan ta jikin hoton salma ce"


Ido kabeer yaware sosai gamida zooming din hoton,da idonta yagane salma ce,wani ihu kabeer ya saki yana dariya yafara nuna najeeb da hannu yace.


"kana shaaninka mutumina,kagama pretending ɗin kadawo kan hanya kenan,yanzu ka amince kana sonta,tunda gashi harda su runguma ana selfie"kabeer ya faɗi yana kyalkyala dariya.


"ni kaifi ɗayane,bana sauya maganata,sabida gaskiya itace nagartar namiji,wlh kabeer bana son salma bana sonta,kuma bazan taɓa sonta ba,ni tausayinta kawai nakeji,taya zan so salma mahaukaci ne ni?wlh bana sonta,ko hoto dakaga na ɗaukemu,zata gudune nikuma na kamota shine tafaɗo jikina,kuma badan komai naɗaukaba sedan nazo na nuna maka"najeeb yayi maganar ranshi aɓace.


Kabeer dena dariyar yayi ya tsaya yana nazari akan aminin nashi,tabbss aminin nasa yanada matsala,wato ya fahimci sam najeeb bemasan meye soba bare yasan yanayinsa,tabbas yasan najeeb aduniya babu wanda ze gwada masa son salma,to amman matsalar yaƙi yarda da so ɗinma bare ya amince sonta yake,tabbas amininsa yana cikin tsaka me wuya matuƙar Allah be buɗe masa idonsa ya fahimci son salma yakeyiba,sabida duk ranar daya rasata ze shiga tashin hankali,wanda baze masa kyaiba.


ɗagowa kabeer yayi asanyaye yace.


"calm down abokina se yanzu nagano matsalarka,zantaya da addua kuma zanci gaba da tunasar dakai abinda baka amince dashiba,insha Allahu komai zezo da sauƙi"


Dariya najeeb yayi sannan yace.


"kanka akeji"


Daga haka hira suka shigayi.



Tun daga wannan lokacin,azahirin gaskiya duk wanda yaga salma da najeeb yasan masoyane,amman agurinsu su kuma ba haka bane.


Salma nason najeeb kamar ranta,shikuma anashi ɓangaren,tausayinta yakeyi,wanda ita bata gane hakanba ɗauka takeyi sonta yakeyi,shiyasa ko saurayi tayi bata kulashi.


Duk ƙarshen sati najeeb,na hanyar kaduna zuwa gurin salma,har su kansu iyayen salma sun ɗauka najeeb sonta yakeyi.



Se su kwana su yini suna waya da juna ko gajiya basayi,koda feefee ta tambayi salma tsakaninsu,kai tsaye salma ta shaida mata soyayya sukeyi.


ganin irin sintirin da najeeb yakeyine duk sati daga Abuja zuwa kadunane yasa mahaifin salma tuntuɓarta yaji tsakaninsu,dan haka yasa aka kiramasa ita.


"Salamatu,meke tsakaninki da najeebullah ne?"cewar mahaifinta .


Ƙasa salma tayi da kanta alamun jin kunya da ƙyar tace.


"Baba sona yakeyi"


Murmushi yayi sannan yace.


"kekuma bakya sonsa ko?"


cike da kunya tace.


"nima ina sonshi"


"to Alhamdulillahi,nayi farinciki,to amman salma kinsan baze yiwu muzuba muku ido ba dan haka inyazo wannan satin nida kaina zanmasa magana yaturo magabatansa atsaida magana,hirar ta isa haka atiti kuje gidanku ku cigaba".


daga haka ya Sallameta.


Ranar salma har zuba ruwa tayi a ƙasa tasha dan murna,koda suna waya da najeeb seda ya fuskanci tana cike da farinciki ,danhaka yace mata.


"hala tasamune kike ta farinciki haka?"


dariya tayi sannan tace.


"kaide bari wlh ay dawa tayi nama ne"


Dariya yayi sannan yace


"Ah tunda hakane,shafamin nawa tun yanzu,kar kamin inzo yaƙare"


dariya salma tayi tace.


"Sha kuruminka,babu me taɓawa se kazo,kaine ma zaka fara taɓawa"


"Har kinsa naƙosa satin yazo nazo"


Haka de sukai ta hirar su irin ta masoya a zahiri.



Wannan satin shi da kabeer suka zo.


murna gurin salma baa magana,nan tashiga ɗawainiya dasu,har tausayi taba kabeer,sabida ya fuskanci ba ƙaramin so takewa najeeb ba.


seda sukayi sallah azahar sannan mahaifin salma ya buƙaci ganawa dasu,


Zaune suke atsakar gidan su salma suda mahaifin nata inda mahaifin salma yafara da cew.


"Najeebullahi kimanin shekara ɗaya kenan kana tare da salma,batare da ka turo magabatanka an tsaida maganaba,shiyasa nacewa salma ta turomin kai dan nayi maka magana,soyayyar awaje taisa haka,gwanda amuku aure inyaso sekuyi agidan auranku,dan haka katuro magabatanka,atsaida magana,dama kiran danamaka kenan"


Tunda Abban yafara magana zufa take ketowa kabeer,yayinda shiko gogan kanshine yaɗau charge,dan haka beyi ƙasa aguiwaba yace.


"baba ni duk wannan bayanin naka banganeshiba,ita salmar ce tace soyayyace tsakanina da ita?"


murmushi baban yayi sannan yace.


"ita tashaidamin kuma dama idanuwana sunjima da gani,danhaka katuro magabatanka kawai ayi magana"



Ran najeeb gaba ɗaya yagama ɓaci inbanda salma ta ɗaukeshi mutumin banza ubanme zeyi da ita.


"baba nifa bason salma nakeyiba,taya zatace sonta nakeyi,kwatankwacin wannan maganar babu ita atsakaninmu"najeeb yafaɗi ranshi aɓace.



"baka sonta meyasa kake,zuwa gurinta duk sati,kuma kake ɗawainiya damu da ita gaba ɗaya,kaga najeebullahi karka maidani sakarai wanda besan abunda yakeyiba,yazaka ɗauki tsawon lokaci kana huremata kunne taki sauraran kowa alhalin kaibada aure kake sontaba,sannan yanzu kazo kana faɗamin ba sonta kake yiba"


Afusace najeeb yace.


"ya isa haka baba kar kayi yunƙurin cimin mutunci akan abinda bedace da aci mutuncina dominsa ba,ni mahaukacin inane zanso salma har inyi shaawar ajiyeta amatsayin mata agareni uwar ƴaƴana,?baba kode kamantane,?salma shekarunta biyu agidan yari adalilin sata,bayan wacce tajima tanayimin kamin Allah yatoni asirinta,bafa iya sata salma ta iyaba salma taƙware a harka da maza kalakala,ni ganau ne ba jiyau ba,kuma shikenan dan tsabar sonkai irin naka seka ce ni nafito na aureta,in gaskiya kake yi ka nemo me irin halinta ka aurawa sahabi mana".


Tunda najeeb yafara magana mahaifin salma ke zubar da hawaye,yayin da kabeer se hana najeeb yin maganar yakeyi amman yaƙi denawa,kuma tunda yafara magana akan kunnen salma taji komai.


kuka takeyi numfashinta na sarƙewa,daƙyar tajanyo akwatin kayanta ta ɗauko wata jaka,cike da kuɗi kimanin miliyan ɗaya ɗori,ta ɗauko jakar tafito dagudu zuwa tsakar gidan,kuka take kamar ranta ze fita ta ajiye jakar akan cinyar najeeb tace cikin kuka.



"ƙarya kake najeeb kana sona wlh karya kakeyi,inde sabida satar danayimakace to ga kuɗinkanan karka kuma kirana da ɓarauniya,najeeb nimesonkace,karka lalata farincikina,ka saurari zuciyarka najeeb ni takeso kar ka...."numfashintane ya ɗauke ta kife agurin.


A gigice najeeb yayi kanta da sauri babanta yadakatar dashi da cewa.


"inka kuskura kataɓamin ƴa,wallahi se ka raina kanka,kuma yanzu base anjimaba ka ɓacemin da gani,wanda besan darajar manyaba"


Najeeb hankalinshi nakan salma,wacce jini yake fitowa ta bakinta,duk yagigice ya rasa abinda kemasa daɗi,kabeer ne yayi yunƙurin bada haƙuri amman ina be sauraresuba dole kabeer yaja najeeb daƙyar suka nufi hanyar fita,har sunkai ƙofar gidan Abbah yabiyosu,yabasu jakar kuɗinsu,dakyar kabeer ya amsa suka nufi mota,najeeb se tirjewa yake baze tafiba,dakyar kabeer yasashi amota,suna tsaye aka fito da salma akasata a napep,aka wuce da ita asibiti rai a hannun Allah.


Najeeb hawaƴene kebin fuskarshi wanda besan dalilinsuba,ahaka kabeer yaja motar suka ɗau hanyar Abuja.




    *INTERMISSION*




Surbajo for life.


*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*




Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*20*



Tunda suka ɗau hanya bawanda yacewa ɗan uwansa ƙala,se najeeb daya kifa kanshi akan cinya yanata kuka.


"Dallah malam kacikamin kunne da kuka,ubanwa ya sa ka aykata abinda ka aykata,wlh ko yanzu salma ta mutu kaine ka kasheta,wawa kawai wanda besan abinda yake ba"cewar kabeer cikin matsanancin fushin dake nuna gab yake daya doki najeeb din.


Shiko najeeb a gigice ya ɗago yana kallon kabeer  yace bakinsa na rawa.


"Kabeer salma bazata mutu ba,salma rayayyace batayi kala da mutiwaba,kar ka kuma alaƙanta tata da mutuwa"


"dallacan yimin shuru kai har kanada bakin magana yanzu,bayan kasa mahaifinta kuka,ita kuma gatacan rai a hannun Allah ,ay wlh ko hakkin hawayen mahaifin salma najeeb bazaka zauna lafiya ba,ace ayi mutum kamar jinin firauna,wacce irin maganace banyimaka akan salma ba,meye ban faɗa maka ba,amman dan tsabar bakasan darajar manyaba ina hanaka magana ƙara ɗaga murya kakeyi kai ga isasshe,wlh kanka kama,ba ruwan kabeer,kuma wannan hawayen da kakeyi,wlh kashirya,seka zubar da dubunsu anan gaba"kabeer ya fadi cikin kakkausar murya.


Najeeb ya kasa magana ware ido kawai yakeyi,yanaso ya hango abinda yayi ba daidaiba a maganganunsa da baban salma,amman shi a iya ganinshi,ba abinda yayi gaskiyar abinda ke ransa ya faɗi.


Har suka isa Abuja najeeb bedena kuka ba,shi kuma kabeer bedena zazzaga masa masifa ba,ƙarshema a bakin titi yasaukeshi,se taxi ya hau ya ƙarasa gidanshi.


Salma ko,likitocin sunyi nasarar daidaita numfashinta,sede ta kamu da ciwon zuciya me tsanani.


Ummanta se kuka takeyi,tana Allah wadai da najeeb,da yaudarar dayazo yay musu.


koda sahabi yaji abinda yafaru jiyayi kamar yay tsuntsu yaje yasami najeeb yaci mutuncinsa,sosai ranshi ya ɓaci.


Haka sukai ta jinyar salma,har tsawon watanni uku a asibiti sannan ta samu sauƙi aka sallamosu.


Tunda ta dawo gida sam batason hayaniya,ko hira ta daina yi da kowa kullum tana ɗaki tana tunani,bata taɓa tsammanin najeeb ze tozartata da ita da iyayentaba,segashi yashayar da ita mamaki,tunda yasanya mahaifinta kokawa a dalilinsa.


tsanarshi ce me girma ta mamaye saman zuciyarta,jitake kamar ta kasheshi.


haka rayuwa taci gaba da tafiya,yayinda najeeb yazama kamar wani mahaukaci,ga kabeer ya fita a harkarsa ko a waya yasashi a black list bashida ikon kiranshi.


Salma itama koya kira layinta sede ace baya ayki,sabida tajima da yarda layin.


yau da sassafe ya shirya yanufi gidan kabeer,sede yasha mamakin,samun mummunan labari agurin megadin gidan nacewa kabeer sati guda kenan da barinshi gidan,sabida ammishi transfer daga Abuja,amman besan inda ya koma ba.


jiri ne yafara ɗibar najeeb ,adaddafe,ya shiga mota ya koma gida.


koda ya isa gida kuka yake kamar yaro ƙarami,ji yake kamar yabar duniyar,yanzu ina ze nemo kabeer yabashi haƙuri su shirya?.



kimanin watanni takwas kenan da faruwar lamarin.


Inda mahaifin salma ya matsa mata akan tafito da miji shi yagaji da ganinta ahaka,inba hakaba ze kaita ƙauyensu ya aurar da ita sadaka.


Sosai batun ya ɗaga mata hankali,dan zuwa lokacin bata da saurayi.


Cikin hukuncin Allah ta haɗu da wani kamal,abokin sahabi,suka fara soyayya dashi,ba laifi tanason kamal shima yana sonta.


Har iyayenshi sunzo antsaida maganar auransu,murna gurin salma baa magana,dan dama zaman gidan ya isheta sabida sa'anninta duk sunyi aure sun haihu se ita tarage agida.


Ranar ɗaurin aure jamaa ba masaka tsinke dangin ango da amarya kowa ya hallara,anɗaura aure lafiya,kowa se murna yake.


wani mutum ne yaja mahaifin kamal gefe yamasa kuskus a kunne.


Ayko tuni mahaifin kamal yafara balai akan dole kamal seya saki salma.


koda aka tambayeshi,dalili se cewa yayi ay tsohuwar karuwace,kuma tsohuwar ƴar safarar cocaine,dan haka baze gurɓata zuriar shi da ita ba.


Haka ya tasa kamal akan dole seya saki salma,haka kamal yana kuka yarubuta takardar sakin yabayar.


Koda labarin ya isa cikin gidan su salma mahaifiyarta rushewa taƴi da kukan takaici.


itama salma sanda aka bata takardar sakin sumane kawai batayiba amman kuka tayishi ba adadi,Allah ya isa ko tajawa najeeb ita tafi kwandon dubu,dan shine yafara yimata tambarin karuwanci gashi nan yana binta.


Haka taro watse kowa se gulma yakeyi.



Tundaga wannan lokacin,mutane sunfi,shida dasuka fito neman auranta ana fasawa in sukaji labarinta,salma tarasa inda zata sa kanta duniyar tamata zafi,kuka yanzu tayishi har ta dena.


Tacire aure aranta dan ko kauyansu da mahaifinta yakai tallanta sadaka bawanda ya amsa sabida sunsami labarinta.


wasa wasa ko fita seda ta gagari salma sabida da zaran ta fita yara sukw binta suna jifa wai ga karuwa ga yar cocaine.


Bata da sakat ko mahaifiyarta tadena shiga taro,sabida da zaran tashiga zaa fara yada mata da habaici.



Yau kabeer ne yakamo hanya zuwa gidan su salma dan yasake ba mahaifin salma haƙuri,koda ya iso ƙofar gidan,parking yayi agefe,yana shirin fitowane,ya hango wata budurwa yara sunbiyota da gudu suna mata waƙar,"ga yar cocaine taƙi aure,waze aura?se ɗan banza,waye banzan?me bin mata"haka yaren suke cewa se jifanta sukeyi har sun fasa mata goshi,sun yaga mata hijabi,


koda suka ƙaraso kusa dashi seyaga ashe salmace yaran suka biyo,da gudu tashige gidansu,sannan yaran suka juya,da sauri kabeer yakira wani yaro me wayau acikinsu yatambayeshi.


"Abokina me wannan tamuku kuke mata waƙa haka kuna jifanta?"


dariya yaron ya kwashe daita sannan yace.


"wannan dakake gani,sau bakwai ana taruwa ɗaurin auranta ana fasawa,wanima seda aka gama ɗaurawa aka saketa,sabida ansamu labarin ashe tsohuwar yar cocaine ce kuma tsohuwar karuwa,sata kuwa ko ɓera albarka"


Hasbunallahu waniimal wakil,itace kabeer ya furta da ƙyar,sallamar yaron yayi yakoma cikin motarshi yakife kanshi akan sitiyari yana kuka,na tausayin salma da iyayenta.


"ina najeeb zekai alhakin salma da iyayenta"itace tambayar da kabeer yayiwa kanshi,jiki a sanyaye yaja motarshi yabar ƙofar gidan yana kuka na tausayin wainnan masoya dake cikin jarabtar ubangiji,yanajin haushin najeeb matuƙa amman yasan ba laifinshi bane haka Allah ya tsaro musu,amman dole zeyi iya bakin ƙoƙarinshi wajen ganin yashawo kan matsalar.



muje zuwa


surbajo for life.


*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad Mahmud


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION


🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻


*DUK WANI MASOYINA YATAYANI JAJE WLH YANZU HAKA ZUCIYATA BUGAWA TAKE DA ƘARFIN TSIYA,INADA DARI BAKWAI A WAYATA,TO KUMA DATAR DUBU DAYA NAKE SAWA,SENAJE TA MOBILE BANKING ZANYI RECHARGEN NA 300 KUNGA YAZAMA DUBU DAYA KENAN,TO WLH TASHIN HANKALIN DAYA SAMENI BAZE MISALTUBA,MEMAKON INSAKA DARI UKU SENASA DUBU UKU,WLH BAN LURABA SEDA BANKI SUKA TUROMIN ALERT,INA CIKIN TSAKA ME WUYA😭😭😭😭😭😭😭ATAYANI DA ADDUA ALLAH YABANI HAƘURIN JURE KADDARAR DATA FADAMIN,DON ALLAH*


*Wannan shafin nakine masoyiyata,Allah yakara daukaka,yakareki daga sharrin duk wani abun ki,MAMAN AHMAD(MARDIYYA KAOJE)MARUBUCIYAR MUMTAZ,CHAIR LADY SURBAJO NA GAISUWA🤝*



*21*



Kai tsaye gida kabeer ya wuce,matarshi a ruɗe ta taryo shi,tana tambayarshi abinda yafaru dashi taga yana kuka.


Be ɓoye mata komai ba yasanar daita,itama rushewa tayi da kukan na tausayin salma dan tafijin tausayinta.


Sati guda tsakani,kabeer ya ɓoye number yakira najeeb,dakyar ya ɗauka,jin muryar kabeer ne yasa yamiƙe zaune yana faɗin.



"haba friend yanzu har abun yakai ga haka ka gudu kabarni bacin kasan banajin daɗin rayuwa idan baka?"


"dalla yimim shuru se zuba yake kamar famfon daya lalace,niba wannan ce tasa nakiraka ba,tambayarka zanyi,yanzu ka amince kanason salma ko baka aminceba?"


Shuru najeeb yayi kanshi na mishi zafi zuwacan de yadaure yace.


"Don Allah barrister kada kabari salma tashiga tsakanina dakai,dan wlh azahirin gaskiya ni bana son salma bantaɓa sonta ba kuma bazan taɓa ba har abada,nide kawai nasan ina jin tausayinta"doctor yaƙarasa maganar yana kuka.


kabeer bece masa komaiba yakashe wayarshi,koda najeeb yaji yakashe wayar wani kukan ne yasake ƙwace masa.


Haka rayuwa taci gaba da tafiya,najib cikin tashin hankali,salma cikin tsana da tsangwama ta mutanan gari.


gaba ɗayansu sunyi baƙi sun lalace,bama kamar najeeb wanda gaba ɗaya yazama tamkar mahaukaci kuma ya rasa meke damunsa,ba irin gwajin cututtukan da beyiwa kanshiba amman results ɗaya yake samu,zuciyar shi nason wani abu.


Amatsayinshi na likita yasan matsalace babba to amman yarasa gano abinda zuciyar tashi takeso bare yabata.



Kabeer ne zaune agaban mahaifin salma suna tattaunawa,da ganin yanayinsu kasan sunɗan jima da fahimtar juna.


(abinda me karatu be saniba shine,kabeer tsawon wata guda kabeer ya kwashe yana zuwa gurin mahaifin salma yana bashi haƙuri,)


murmushi mahaifin salma yayi sannan yace.


"kabeeru kenan,to ay ko wani kazo nemawa auran salma zan bashi bare kuma kai da kanka,dan haka ka kwantar da hankalinka,inde kashirya kaje kasanar da magabatanka,azo ayi maganar,amman katabbatar kafaɗa musu komai game da salma".


godiya kabeer yayi sosai,daganan kai tsaye katsina yawuce gurin iyayensa,yamusu bayanin komai be ɓoye musu ba.


Dayake mahaifinshi malami ne me tsoron Allah,be ƙi ba.


Sati guda tsakani iyayan kabeer sukazo aka tsaida maganar,suka biya sadakin salma,


Bayan tafiyarsu mahaifinta shima yaje yayi bincike akatsinan yatabbatar da mutanen kirki ne


Wata guda tsakani,jamaa suka taru domin shaida ɗaurin auran salma da kabeer,


yan unguwar se gulma sukeyi,sabida suna ganin shima auran fasawa zaayi,sede ga mamakinsu anɗaura aure lafiya antashi bawani tashin hankali,ataƙaice ma har dangin angon sun koma gida.


Anata ɓangaren,salma kuwa,ta ɗauki auranta da kabeer da matuƙar muhimmanci ko kaɗan bata ƙin auran,sabida ko ba komai yacireta daga ƙuncin datake ciki.


Haka aka cigaba da shagalin biki kowa se murna yake,karfe huɗu aka kawo motar ɗaukar kaya,akaje aka shirya gidan amarya a unguwar malali GRA dake kaduna sabida kabeer dama kaduna yadawo da aykinshi,yayin da gidan uwargidanshi kuma yake a gomna road.


Yasha fama da Aisha matarshi kamin ta Amince ya auri salma.dan cewa tayi sede yasaketa.


Gidan amarya ba laifi yayi kyau sosai,daidai namasu ƙaramin ƙarfi,duk da cewa gidan namasu babban ƙarfine amman iyayenta sunyi ƙoƙarin tsara gidan da abinda Allah ya hore musu.


ƙarfe takwas nadare,motocin ɗaukar,amarya suka iso,inda aka ɗauki amarya tana ta kuka zuwa gidan mijinta kabeer.


ikon Allah.


surbajo for life.


*🙆🏻Y'AR BAUTAR K'ASA*




Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*22*



Haka ƴan kai amarya suka watse suka barota tana ta kuka.


Misalin sha ɗaya na dare ango yashigo ɗakin shi kaɗai,hannunshi ɗauke ɗa ledar kaji.


Sallamah yayi yashiga,bakin gadon yaje yazauna,yayi shuru,ita kuma se kukan ta takeyi.


Zuwa can de yadaure ya matsa kusa da ita,mayafin kanta yacire yajawota jikinshi yafara rarrashinta,da kyar yasamu tayi shuru,


Dakanshi yaɗauko plate yazuba kajin yadunga bata abaki har ta ƙoshi,daga haka brush sukayo da alwala sukayi sallah sannan suka kwanta.


Jawota jikinshi kabeer yayi yarungume sukayi bacci.


Haka rayuwa taci gaba da tafiya,kabeer kullum cikin nuna ma salma soyayya yake ba abin data nema tarasa,itama sosai take nuna masa kulawa,


Tuni yase mata mota yasiyawa iyayenta gidan dasuke ciki yasa aka gyara masu gidan sosai,


Rayuwa tayiwa salma daɗi sede abu ɗaya ne yake hanata jin daɗin giɗan mijin,shine rashin  kusantarta da kabeer bayayi,ita kuma macece me ƙarfin shaawa,amman haka ta haƙura dan ko maganar bayaso tamishi,se ya ɓata rai yace mata shi badan haka ya aure taba,ganin ranshi na ɓaci Ne yasa tadena yimasa magana ta koma faɗawa Allah damuwar ta.


Tuni salma tamance da wani najeeb arayuwarta.


Anashi ɓangaren najeeb yakoma kamar mahaukaci ko aski bayayi gashi duk yacika masa fuska bashida natsuwa duk a firgice yake.


Yanzu sauƙinta ɗaya suna waya da kabeer harma yabashi address din gidan shi dake kaduna.


Yaude Abujar tayiwa najeeb zafi dan haka shiryawa yayi yanufi Kaduna gurin Kabeer ko zeji daɗi.


Koda ya iso kaduna,se yacintsi kanshi dazuwa gidan su salma,koda ya isa yaci saa babanta yananan,dan haka gurinshi yanufa duk da sauyar gidan tabashi mamaki.


baban salma be gane najeeb ba seda najeeb ya gabatar da kanshi.


Da sauri yajawo shi jikinshi yarungumeshi yana  faɗin.


"najeebullahi najima inason ganinka amman Allah be nufa ba se yanzu,kayi ciwone naga ka lalace haka?" 


Kuka najeeb ya rushe dashi yana ƙara rungume baban yana neman gafarar shi abisa rashin kunyar daya masa.


Dariya baban yayi sannan yace.


"najeebullahi,bakamin laifiba,ko fushin danayi dakai rainane ya ɓaci ba komai ba,amman yan zu bana tare da ɓacin ran komai,nayafe maka tun tuni"


har cikin gida yashigar dashi gurin mahaifiyar salma dakyar ta amince tayafe mishi,haka shima sahabi dakyar ya amince,daganan ne najeeb ya buƙaci ganin salma,itama yabata haƙuri,cikin faraa mahaifinta yace.


"wai ay salma shekararta guda kenan agidan mijinta,ay tayi aure"


Jirine yafara ɗaukar najeeb kamin wani lokacin yazube ƙasa sumamme,a gigice suka ɗebo ruwa suka shiga yayyafa masa,be jimaba ya farko yana wani gunjin kuka ,ƙafar mahaifinta yariƙe yana kuka yace.


"baba meyasa ka aurar da salma? meyasa baba?"


tambayar sosai tabashi mamaki,amman se yace,


"sabida ta isa aure shiyasa na aurar da ita,danko calender ce ita watarana zan gaji da kallonta nayaga kona ƙona"


Najeeb kasa magana yayi,cikin fushi yamike yafice daga gidan suna kiranshi amman ko waigowa beyiba yaje yashige motarshi yatada daita yabar anguwar.


yana tafe yakira kabeer yace mishi gashinan zuwa gidan shi.


Sosai kabeer ya firgita da zuwan na najeeb,kamin yayi wani yunƙuri najeeb ya iso gidan.


jin nucking yasa kabeer daurewa yaje ya buɗe masa ƙofar,yana buɗewa najeeb yarungume kabeer ya rushe da kuka dakyar kabeer yajashi zuwa cikin falon suka zauna,cikin kuka najeeb ke faɗin.


"kabeer iyayen salma sun cuceni,sun aurawa wani salmata,kabeer ina zan saka rayuwata,?"yaƙarasa maganar cikin matsanancin kuka.


a daidai lokacin salma tashigo falon sabida tajiyo sautin kuka daga ɗakinta,sanye take cikin riga da wando three quater tayi kyau sosai,har ta shigo falon basu saniba.


Najeeb ne yafara ɗsgo kanshi arazane sabida yajiyo ƙamshin salma,koda ya waigo ido cikin ido sukayi shida ita,azabure ya miƙe ya nufeta tana ja da baya da sauri kabeer yace.


"kada ka kuskura kayi gangancin taɓamin mata"ya faɗi sanda ya ƙarasa ya rungumo salma jikinshi,ita kuma se wani ƙara shigewa jikinshi takeyi.


*Tassssssssssss*


Najeeb yaɗauke kabeer dawani gigitaccen mari,sannan yaje yacukumi kwalarsa,yace.


"kada ka kuskura kasake maimaita wannan kalar wasan agabana,nakiran salma matarka"


Tassssssssss.


yaji shima an ɗaukeshi da mari,koda ya waiga salmace sannan tace cikin ɓacin rai.


"wannan ne ganganci mafi muni dazaka kumayi agabana na marin mijina,kai waye dazaka shigo har gidanmu kana cimana mutunci?"


Tsananin mamaki najeeb yakasa magana bakinshi rawa yake kamat mazari,da kyar yace.


"kina nufin kabeer shine wanda kika aura?"


"kana mamakine?"kabeer yabashi amsa.


"kabeer kagama dani duniya da lahira,bani da wani abu dazan iya yimaka,kayimin abinda ko maƙiyina baze yimin ba,duk wani abu dazanyi maka baze gogemin duhun dakasa azuciyata ba"


Be jira abinda zasuce ba yafice da gudu ya faɗa motarshi,da gudu kabeer yabi bayanshi dan yasan komai ze iya faruwa inyabarshi yatafi,sedr kamin ya iso najeeb yafice da mahaukacin gudu,daga gidan,


Da gudu kabeer ya koma cikin gidan ya ɗauko key din motarshi shima yatada yabi bayanshi,


Gudu suke sosai yayinda najeeb ko gabanshi ba sosai yake ganiba,a haka har suka iso gadar Abuja junction,wanda najeeb yajima da sumewa a motar dan haka,kabeer se gani yayi sunyi taho mu kara da tirela,wanda hakan yajanyo motar najeeb ta faɗa ƙasan gadar wacce ƙasanta titine,wata tirelar ce tayi tafiyar yaji da motar ta wancakalar da ita gefen titi.


Ihu kabeer yakeyi,iya ƙarfinsa,yafito daga motarshi,da gudu ,jamaa suka riƙeshi dan kan titi yahau be saniba.


Da ƙyar aka ciro najeeb acikin motar,wanda dagani base an faɗiba babu alamun rai atattare da[truncated by WhatsApp]


*👩🏻‍💼YAR BAUTAR KASA*


Zahra Muhammad Mahmud


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION


*23*


Emergency aka tafi da gawar najeeb,wacce ke ta faman zubar da jini.


Kabeer ko ihu yakeyi gaba ɗaya yafice daga hayyacinshi,


Likitoci ne akan gawar najeeb suna bincike,cikin ikon Allah sesukaji jijiyar bayan kunnenshi  na bugawa.


Da sauri suka jawo kayan ayki suka shiga ceton ranshi,inda cikin nasara bugawar zuciyarshi yadawo,amman da sauri da sauri,alamar dake nuna zuciyar bata da lafiya.


Tsawin awanni uku numfashin shi yaƙi daidaita,duk wani abu da suke tunanin yimishi sunyi amman abun yaci tura.


Gwaje gwaje suka shiga yimasa,anan suka fahimci akwai abinda yakeso be samuba,dan haka da sauri suka nufi kabeer,wanda ke birgima akasa kamar yaro,suna zuwa ɗaya daga cikinsu yace masa.


"we dont have enough time,only one hours remain for your patient,based on our investigation,we find out that there was something he needed on this earth urgently,and he couldn't obtaind it,but if you know the actual thing he needed,you are free to bring it right now,Becouse that is the only solution to save his life"


Tunda likitan yafara magana kabeer yake gyaɗa kai kamar ƙadangaren,yana gama saurarar su yajuya da wani mahaukacin gudu,ya faɗa motar shi,ko murfin be jira yarufe ba ya finciketa da mahaukacin gudu se a hanya ya rufe murfin.


Cikin minti goma ya iso gidan shi,koda yafita be jira yarufe motarba,ya ruga da gudu zuwa cikin gidan.


A falo yasami salma se kuka take yi fuskarta tayi jazir,yana shiga tamiƙe da sauri tace.


"ya kashe kanshi ko?,don Allah kasanar dani a halin dayake ciki jikina yana bani wani mummunan abu yasami doctor"taƙarasa maganar tana kuka me nuna zuciyarta nacike da fargaba.


Jawota yayi da ƙarfi yana shirin ficewa da ita waje,da sauri ta ƙwace takoma gefe tace.


"ina kakeso ka kaini?"


Hawaye ke zuba a idon kabeer kamar ruwa yace.


"salma gurin najeeb zan kaiki"


"a matsayinsa nawa agurina dazaka kaini gurinshi"


"salma najeeb yana sonki,kuma kema kina sonshi don Allah ki taimakeni kar na rasa najeeb,in wani abu yasameshi bazan yafewa kaina ba"kabeer ya faɗi yana kuka.


"tun wuri ka gyara maganarka ni ba son najeeb nakeba tausayins kawai nakeji,ni mahaukaciyar inace zanso mutumin da besan mutuncin iyayena ba?"


"ƙaryane salma,wlh kinason najeeb,kullum dasonshi kike kwana kike tashi,najeeb yana cikin halin buƙatarki akusa dashi,kitaimakemu"


"kabeer na fahimci bakasan darajar auren dake kainaba,shiyasa kakemin zancen wani ƙato"


"salma nifa na aurekine dan najeeb, ina tsoron wani ya aureki,lokacin da najeeb ya waiwayeki kuma yarasa ki,shiyasa namasa adashin gata dake wanda yaune ranar daze kwasa,salma komai namiki namikine dan son da najeeb yake miki,inde akan aurena dakene yasa kikace bazakije gurinshi ba,salma nasakeki saki uku "kabeer ya furta yana kuka.


Arazane salma take kallonshi bakinta na rawa tace.


"what do you mean Kabeer,ashe duk soyayyar daka nunamin ƙaryace?kayine dan abokinka,kabeer banmaka laifin komaiba kasakeni,saki irin na wulaƙanci me naimaka kaida abokinka dakukeso kuga kun jefa rayuwata cikin ƙunci?"


"salma akan najeeb zan iya yin komai,ina nufin komai"ya faɗi cikin ɗaga murya.


hannunta yaja tasake kwacewa tana kuka.


Cikin tsawa kabeer yace.


"Salma fitar najeeb dazu daga gidan nan,sunyi karo da tirela,inda ta wurgoshi shida motarshi ƙasan gadar Abuja junction,inda wata tirelar tasakeyin tafiyar yaji dashi da motar tashi,ankaishi asibitin garden city,likitoci sunyi iyayinsu,najeeb yayi numfashi amman yaƙi yi,salma likitocin sun shaidamin awa ɗayace taragewa najeeb a duniya matuƙar baakai masa abinda yakeso kusa dashiba,ze mutu,kece wacce najeeb yakeso batare dayasan yana yi ba,saura minti goma shabiyar yarage najeeb yabar duniya,nasan zakiyi alfahari da cewa najeeb yaceto rayuwarki daga gidan yari,shi kuma kinyi sanadin turashi lahira"ya ƙarasa maganar yana kuka.


Da wani mahaukacin gudu salma tafice daga falon,binta yayi abaya,motar dayazo acikinta taje tashige,ƙafa ba takalmi,kai ba ɗankwali,sanye da wando three quater da riga armless.


kamin kabeer ya ƙaraso taja motar tafice daga gidan da mahaukacin gudu.


Ta nufi Asibitin garden city dake kaduna,inda aka kwantar da najeeb.


Koda kabeer ya iso yaga tafice wata motar yaje yashiga shima ya fice da gudu,sede shi ba Asibitin yanufa ba gidan iyayen salma yanufa.


Tofa🙆🏻


muje zuwa,akwai bidiri.


surbajo for life.

.*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION


*duk meson ayi adding wata number agroup pls yaba wata admin din baniba,ni sim card dina yacika da numbers,masu bina naturo yar bautar ƙasa ta pc kuyi haƙuri ku tambaya a group bana turawa ta pc,ku kuma masu shi don Allah in antambaya kubayar ni uzuri yamin yawa,pls*



*24*




Tana isa asibitin,tayi parking,bata tsaya kulle motar ba ta ruga da gudu zuwa cikin asibitin kamar mahaukaciya,dama gata akwai gashi.


Wata nurse ta tare tana tambayarta najeeb,ayko ba musu takaita ƙofar ɗakin dayake ciki.


Tura ƙofar tayi da gudu tashige cikin ɗakin,da sauri likitocin suka waigo suna kallonta,itako ko kallonsu batayi.


Ƙarasawa tayi jikin gadon najeeb ɗin tana kallon yadda aka naɗe jikinshi da bendeji sabida raunukan dayaji,ga karaya da yayi a ƙafarsa,duk wanda yaga najeeb awannan yanayin se ya tausaya masa bare salma masoyiyarsa,


Kuka take kamar wata zararriya,hannunshi ta kamo tana kiran  sunan shi cikin kuka,amman shuru bemasan tanayiba.


Naurar jikinshi ce tafara ƙara alamar lokacin da aka ɗiba yayi,gaba ɗaya likitocin sun rude,


Faɗi suke,"we lost him"


A gigice salma take kallonsu,dubanta takai fuskar najeeb,da sauri takifa fuskarta akan fuskarshi,ta haɗa bakinta danashi tashiga hura mishi iskar bakinta daƙe shiga cikin huhunshi.


Yitake iya ƙarfina tana gunjin kuka.


Tarin da najeeb yafarayine ya maido da hankalin salma dana likitocin,da sauri suka janye salma suka samasa oxygen a bakin.


Da kyar yake zuƙar numfashin,salma se kuka takeyi gwanin ban tausayi,likitocin se alokacin suka fahimci ciwon so ne yskama najeeb me tsanani.


shiko kabeer yana isa gidan su salma shima ko ƙofa be rufeba ya ruga kofar gidan inda babanta ke zaune shida wasu dattawa suna hira.


Da gudu kabeer yazube agabanshi yana haki yana kuka yace.


"Baba don Allah karka tambayeni dalili,nasaki salma saki uku,batare dana ɗora mata iddah ba,a iya zamana da ita,najeeb yasamu labarin ni salma take aure,yabar gidana afusace sanadin hakan yayi taho mu kara da tireloli har guda biyu,yanzu haka yana asibiti,cikin halin mutuwa ko rayuwa,baba in har ka amince masoyine ze ita ceto masoyinsa daga gidan yari,baba ka aurawa najeeb salma,idan har ka amince da natsuwa da tarbiyyar najeeb baba ka aura masa salma,in babu salma arayuwar najeeb baba mutuwa zeyi,katausayamin nida aminina ka aura auren salma da najeeb yanzu"kabeer ya fadi cikin kuka.


"Jamaa salati goma ga Annabi"cewar baban salma.


"S,A,W"Sauran mutanen suka amsa,


Hannu yasa a aljihunsa yaciro kudi dubu biyar yamiƙawa kabeer,kabeer hannu na rawa ya karɓa,


"ni malam hadi ina nemawa ɗana najeeb auren salma agurinka"


Bakin kabeer har rawa yake yace.


"Ni kabeer naba ɗanka najeeb auran salma abisa sharudda kamar haka"


Nan aka lissafo hakkonkin aure,baban salma yace.


"na amsa masa"


kamin wani lokaci me tsayi angama ɗaurin auren najeeb da salma,kabeer rasa bakin godiya yayi da gudu yamiƙe yanufi motarshi da sauri baban salma da sahabi suka bishi yaja suka nufi asibitin.


Koda suka shiga ɗakin salma ce zaune kan kujera ta kifa kanta akan goshin najeeb hannunta riƙe da hannunshi,gashin kanta ya zubo yarufe fuskokin nasu,


Kabeer ganinsu ahaka seji yayi wasu hawaye na farinciki sun kama shi,yau yayiwa najeeb abinda ze godemasa,yayiwa najeeb abinda har ya mutu baze manta dashiba,yayiwa najeeb abinda ze dauwama cikin farin ciki,wato aura masa salma.


Har suka shigo salma batasan sun shigoba  hankalinta nakan najeeb,tana tunanin yaushene ze farka.


Mahaifin salma da sahabi seda suka koka ganin halin da najeeb yake ciki adalilin salma.


jansu waje kabeer yayi,suka zauna,wayarshi ya dauko yakoma gefe yakira mahaifin najeeb.


Bayan sungaisa,kabeer yakwashe komai yasanar da mahaifin najeeb ɗin tun farkon haɗuwar najeeb da salma har zuwa yanzu da aka ɗaura musu aure.


sosai hankalin mahaifinshi yatashi,anyi saa yana ƙasar,dan haka yashaidawa kabeer nan da awa biyu ze iso.


Suna nan zaune jugum jugum,har awa biyun ta cika,mahaifin najeeb ne yashigo Asibitin da gudunshi.


Da sauri kabeer yatarbeshi,yakaishi ɗakin da najeeb ɗin yake,sede har lokacin gashin salma yarufe fuskar najeeb baa gani yayin da itama tata baa gani,


Kabeer ne ya ƙarasa kusa da kunnen salma yace mata ta tashi ga mahaifin najeeb.


Hannunshi ta saki amman se taji shi yayi sauri yariƙe nata,da sauri ta ɗago kanta tana duban fuskarshi,


ba salma kowa seda yayi mamakin ganin idanun najeeb a buɗe yana kallon salma hawaye nazuba ta gefen idonshi.


Da sauri mahaifinsa yamatsa kusa dashi yana masa sannu.


Binsu kawai yake da ido amman ba baki.


likitocinne suka zo suka korasu waje,sannan aka canjawa najeeb ɗaki zuwa wani na musamman wanda babu me shiga sede me jinyarsa wato salma.


Guri suka samu suka keɓe aka sake maimaitawa mahaifinshi komai,ga mamakinsu be ji haushin aurawa njeeb salma ba,sema godiya daya dunga yiwa mahaifin salma harda hawayensa.


Muje zuwa.


Surbajo for life.


*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*




Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*PLS MESON BOOK DINA YATAMBAYA A GROUP,NI BANA TURAWA PC,SABIDA NAYI ME WUYAR TUNDA NATURO GROUP,ADDING NUMBERS KUBA WASU ADMINS DIN KOWANNE GROUP DINA AKWAI ADMIN KUBASU,NI WLH UZURI YAMIN YAWA,KU KUMA ADMINS IN ANBAKU KUSA KA,AMMAN ADMIN DIN SURBAJO HAUSA NOVELS(MY SCRET)KARKIYI ADDIN DIN KOWA ACIKIN SA,AMMAN SAURAN AYI,PLS🙏*



*25*



Waya Alhaji hassan yayi yasanar da hajiya kaltum halin da ake ciki,harda auren da aka ɗaurawa najeeb din.


A wayar harda kuka tayi na tausayin najeeb din,tana kashe wayar tamiƙe afusace tana kai kawo.


"najeeb kayi kuskure daka faɗa tarkon son wata ƴa mace baniba,wlh inde sunana kaltum,sena hanaka jin daɗin auran da kayi dani kake magana"sune kalaman sa hajiya kaltum ke furtawa cikin fushi.



Salma kowa yaganta se yaɗauka tare suke ciwon,dan itama bakinta ya kulle tadena magana sede ido,babu yadda baayi daita ba akan  taje gida tabar kabeer yakula dashi amman fafur taƙi amincewa,dan ko ma ta miƙe zata yi wani abun sede tayi da dabara dan hannun najeeb riƙe yake da hannunta kowannen motsinta akan idonshine,sede inyayi bacci ne take da lokaci.



Hajiya kaltum tazo dubashi,yayinda taga salm seda numfashinta yakusa tafiya,sabida ganin ƙirar da Allah yay mata,take taji kishi da tsanarta sun baibaye zuciyarta,inda ta ayyana ko tawacce hanya seta rabasu.


Wasa wasa seda najeeb yayi wata uku a Asibiti sannan yafara magana,amman be fiye yiba yafison yayi shuru.


Idan kabeer yazo dubashi rufe idonshi yakeyi sabida ji yake kamar zuciyarshi zata fito inya kalleshi,yatuno yanzu fa kullum seya kwanta da salma seyaji kamar yakasheshi.


kabeer yasan najeeb na kishi dashine shiyasa be masa magana,dan haka be damuba illah dariya ma da abun yabashi.


Mahaifin najeeb ganin yasamu sauƙine yasa yakoma kano,yasa aka,ginawa najeeb plat me kyau da tsari acikin gidanshi,abisa jagorancin umarnin da hajiya kaltum tabashi,sabida da awaje ze gina masa,se tsautsayi yasa yafaɗa mata,ayko ta shiga ta fita.ba abinda baa zuba acikiba na more rayuwa,sannan dakanshi yaje kasuwa yasa aka haɗa lefe nagani na faɗa,dazeje duba najeeb din yakai gidansu salma da kuɗi milyan daya amatsayin dukiyar auren salma.


Yau aka sallami najeeb a asibiti,babu mecewa yayi ciwo,yawarke garas.se ƙafarshi dayake ɗan ɗingisawa


Tun da daɗewa yake so yasamu wanda ze tambaya meyasa salma take kwana agurinshi,amman yarasa wanda ze tambaya.


Tun safe kabeer yazo awata mota marcedez venz 4matic,fara,me baƙin glass anyiwa motar decoratin da kayan decorating,dasu balam balam kalar bulu da fari,number motar ansa,

*NAJEESAL* gaba da baya,se wani rubutu da aka rubuta happy marriage life najeesal.


motar se ɗaukar ido take gwanin sha'awa.


a daidai ƙofar fitowa daga reception din asibitin,yayi parking ɗinta,sannan ya shimfida bulu fin carfet,aƙasa zuw ƙofar tundaga bakin motar,shima karfet din an rubuta,happy marriage life najeesal da farin rubutu.


Shiga cikin Asibitin yayi lokacin,najeeb na zaune shuru yana kallon salma dake ta ƙoƙarin zuge zip din rigarta amman takasa,


Miƙewa yayi ahankali ya ƙarasa gurinta seji tayi yacire hannunta yaja mata zib din sannan yakoma ya zauna.


Kabeer ne yashigo ɗakin da sallamarsa,hannunshi riƙe da flawer me kyau itama blue da fari,najeeb na ganinshi yakauda kanshi gefe.


Dariya kabeer yayi ya ƙarasa gurinshi yace.


"Ango kasha ƙamshi,ina tayaka murnar fara sabuwar rayuwa Allah yasanya alkhairi abokina"ya miƙa masa flower din.


kan najeeb ne ya ɗaure dajin maganar kabeer,kallo yabishi dashi,kabeer ganin najeeb beda niyyar amsar flawer ne yasa yakamo hannunshi yasaka masa.


Sannan yace su taso karsuyi dare a hanya.


Salmace tafara miƙewa,amman shi najeeb beda niyya ganin hakane yasa salma matsawa kusa dashi ta miƙa masa hannun ta alamar yakama.


shashin da kabeer yake ya kalla sabida yanajin tsoron riƙe hannunta agabanshi.


gyaɗa masa kai Kabeer yayi dan haka, kama hannun nata yayi ta miƙar dashi tsaye suka fice daga ɗakin.


kowa se barka yake masa nasamun sauƙinsa.


koda suka iso bakin ƙofar fita sosai abun yaba najeeb mamaki ganin nurse din asibitin tsaye gefe da gefe na asibitin sina watsa flawer  akansu,


*NAJEESAL* me hakan ke nufi cewar najeeb.


Haka suka taka har gurin motar aka buɗe musu bayan motar suka shiga,aka dunga watsawa motar flawer,kabeer ya shiga yajasu,zuwa gidan su salma.


Nasiha baban salma da mamanta suka musu,se alokacin najeeb ya fahimci an ɗaura masa aure da salma ne,


kallonsu yake kamar wawa,danshide yasan ay se anyi iddah ake ɗaura aure tosu nasu meyasa aka ɗaura bayan salma batayi iddah ba?.


Kanshi a ɗaure yafito ƙofar gidan,shi besan ma me zeyiba,kowa yace su ɗaura mishi aure da ita oho,shifa ba sonta yakeba,amman ba komai,ya amsa amman se ta gane kurenta dan yafahimci itace tace tana sonshi.


Salma se kuka takeyi haka aka rakota zuwa mota da kayanta na sawa da kawo mata na lefe da kuma nasawarta na gidan kabeer,akasa a both din motar.


Key din motar kabeer ya miƙawa najewb yace yana dariya.


"ba wanda yafika sanin darajar salma dan haka nasan senafi kowa iya janta a mota,"ya miƙa masa key din.


amsa najeeb yayi rai aɓace dan haushin kabeer yakeji sosai.


shiga mazaunin direba yayi salma tashiga gefe aka kulle motar.


ƴan uwan salma mutum huɗu da,zasu rakata kuma suka shiga motar da kabeer yasa aka kawo  masa yabi bayan najeeb abaya,suka kama hanyar kano raka ango da amarya.


Muje zuwa.



surbajo for life.


*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*



Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*Yasmin tafeesu natayaki murnar kammala littafinki na bakar alada,Allah yasa kifi haka,Allah kuma yakara haɗa kanmu up up up da bazarmu writers association,atare abuge ba dama,abari mu wuce ga haushi,taken mu kenan*


*26*



Suna tafe bawanda keyiwa wani magana salma se danne danne take awaya hankalinta kwance,waigowa najeeb yayi ya kalleta yayi tsaki sannan yace.


"jibeta don Allah,sekace ba ita bace take ta rusa kuka ɗazu,ashe na munafunci ne"


Ɗago idonta tayi tayi masa fari cikin wani salo,wanda ya haddasa kan motar kusan kwacewa a hannun najeeb dan har sun sauka a titi.


Da sauri yadawo kan titi,su kabeer dake binsu abaya har sun fara sallallami.


Murmushi salma tayi sannan tace.tana ƙara kaɗa masa ido.


"to dan kuma nayi kuka ɗazu cemaka akayi dauwama zanyi inayin kukan,wancenma danayi dan kar ace banyi bane"


Tsaki yasake yi yace.



"Allah de ya tsinewa munafuki,kuma naga alamun kina cikinsu"


Shewa salma tayi sannan tace.


"doctor kenan,ay gwanda kalar nawa munafunci,so dubu akan naka,sabida ni nawa be illatani ba"


Wani uban birki yaja,sannan ya koma gefen titi yayi parking.


Jawota yayi jikinshi da ƙarfi ya zazzare mata ido gami da cukuikuyeta acikin gyalen data rufa,yace.


"Ni ne munafukin?munafuncin me nayi da har ya illatani?"ya faɗi cikin fushi.


Ido salma tashiga zarewa,dan gani take dukanta zeyi.


Su kabeer parking sukayi suma fitowa yayi ya nufo motar dan ganin meke faruwa,ta glass din gaban motar yaleƙa ganin salma rungume jikin najeeb ne yabashi dariya wato soyewarsu sukeyi shiyasa suke tsayawa,


Juyawa yayi kawai yakoma motarshi yaja yayi gaba abunshi,koda yan uwan salma suka tambayeshi murmushi kawai yayi yace.


"kunsan yau yafito dags asibiti so yagajine shine yake ɗan hutawa"


Shuru sukayi shi kuma yaci gaba da tuƙinshi.


shiko najeeb yaƙi sakinta wai dole se ta faɗa masa munafuncin da yayi har ya illata shi.


Kuka salma tasa masa na shagwaɓa tana ƙoƙarin kwacewa daga ruƙon daya mata shi kuma yaƙi sakinta.


Nanfa suka shiga kokawa,har cikin saa hannun najeeb ya sauka akan boobs ɗin salma.


taushinsune yasa najeeb sakinta da hanzari yaja gefe yana bin boobs din da kallo,yana tunanin inda yaji taushin,


Salma komawa gurin zamanta tayi tana zumɓuro baki.


Najeeb kamar wanda shocking yaja sam yakasa motsin kirki kawai ya kafe ƙirjinta da kallo,bin idonshi salma tayi ta gane inda yake kallo ajikinta,dan haka da sauri ta kife fuskarta akan cinyarta.


Se lokacin najeeb yadawo daga inda yatafi,jiki asanyaye yatada motar suka ci gaba da tafiya.


Har suka isa kano bawanda yasake magana.


Suna isa jamaa suka zagaye motar anayiwa amarya sannu da zuwa.


kai tsaye gurin hajiya kaltum aka kaita aka damƙa amanarta,sannan aka je gurin mahaifin najeeb da ita yamusu addua sosai,daganan aka kaita parta dinta,


Ɗan ƙara gaggara gidan yan uwan nata sukayi sannan kabeer ya kwashe su zuwa kaduna dan ba kwana zasuyiba.


Haka suka tafi suka barta tana ta rusar kuka.


Najeeb be shiga gidan ba se bayan sallar ishai,koda yashiga a falo yasami salma tana kuka,tsayawa yayi yana mata kallon mamaki,kasa jurewa yayi yace mata.


"kince wancan kukan kinyine dan kar ace bakiba,shi kuma wannan da kikeyi tun ɗazu na uban menene?"


ɗago ido tayi ta wurga masa harara,gamida murguɗa masa baki tace.cikin kukan,



"shima wannan irin wancanne,meye damuwarka?"


"Damuwata kidena kukan dan kin cikamin kunne,"


"in bandena ba me zaka iya yi?"


"wlh na jaki zakici,danni banason hayaniya"


Ayko salma ɗaga sauti tayi na kukan harda shure shure da ƙafa.


Najeeb gurinta ya nufa cikin fushi,ganin hakane yasa salma kwasawa da gudu,ta haura sama inda ɗakinta yake,mara mata baya najeeb yayi shima da gudun,dan so yake ya koya mata hankali.



muje zuwa.


Surbajo for life.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*




Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*Idan kinsan zaki zageni akan wannan littafin,to kidena karantawa,daga page 26,dan ba abinda zaginki zema surbajo,hasalima inkin zageni akan wani kika ɗora,dan ba daran da jemage be ganiba,karkice zaki fake da cewa gyara zakimin dan kunruga dakun gama gyara surbajo tun a ummu aymana,dan haka ki riƙe gyaranki,gyara inba na Allah ba surbajo bata sonshi bata karɓarshi,kowa ya iya allonsa ya wanke*


*27*



A tare suka shiga ɗakin shigarsu keda wuya aka ɗauke wuta,asakamakon hadarin daya haɗu tun ɗazu.


Najeeb acikin duhun yafara lalubenta amman be kamata ba,salma ko nacan tsakiyar gado azaune tana masa dariya a hankali.


Wata tsawa aka saki wacce ta razana salma,ƙara ta saki,gamida rikitowa daga kan gadon,tana neman najeeb.


Ayko cikin saa suka haɗu,rungumeshi tayi jikinta na rawa,tana kuka sabida salma babu abinda yake firgitata irin tsawa.


Alaramma ɗan I don't care kuwa,jin salma ajikinshi,se da haddasa mishi jin shocking.


Ya rasa meke damunshi,inde yajita ajikinshi se yaji gabanshi yatashi,tsintar kanshi yayi da rungumeta da kyau ajikin shi,itako bata dena kuka ba sabida baa dena yin tsawar ba.


Haskene ya gauraye dakin sakamakon generator da aka kunna,se kuma ruwa ya tsuge kamar da bakin kwarya,ƙara shigewa jikinshi salma tayi.


Jansu yayi zuwa kan gado nan ma bata sakeshiba,sabida gabaɗaya tagama firgicewa,janta yayi ya kwantar da ita akan gadon,yana shirin miƙewa ta janyoshi da ƙarfi yadawo,yamata runfa da faffaɗan ƙirjinshi.


Lafewa salma tayi a kasan ƙirjin nashi,shiko doctor yadda yaga tana zufa ne abun yabashi mamaki,dan haka ɗagota yayi yamiƙa hannu ƙasan bayan ta ya zuge zip ɗin rigar jikinta,ahankali ya zare rigar.


Hasbunallahu wani imal wakil,


Idon doctor idon boobs ɗin salma,wainda suke acike fam fam,suna kallanshi,farare dasu,asakamakon rashin saka bra da tayi,dan dama bata fiye sawa ba.


👀 doctor ya zuba musu,tunda yake be taɓa ganin boobs irin na salma ba,to dama a ina ze gansu,hannunshi yaji yanaso ya taɓa,amman yanajin nauyin yin hakan,ita ko salma tunda yacire mata rigar,shaawarta ta motsa,dan dama ita tana da ƙarfin shaawa,so take ko wasane doctor yayi da ita amman ina shi gabin bemasan me take nufi ba,ganin haka ne yasa salma amfani da kissa irin ta mata.


kuka tasake sawa tana gaggantsarewa,harda ƴar zabura takeyi,aruɗe najeeb yake tambayarta dalili,amman takasa magana se nuna mishi take daidai boobs ɗinta tana kuka,da sauri najeeb yasa hannunshi akansu,domin duba abinda ke faruwa.


Sede saukar hannunshi akansu yasa yamanta me yaje yi gurin,tsintar kanshi yayi da murzasu sannu a hankali.


wani numfashi salma tafara saukewa wanda at the same time irinshi doctor ke saukewa.


Ƙara shigewa jikinshi takeyi,dan sosai takejin daɗin murza boobs din dayake yi,sabida rabonta da amata hakan,tun Alhaji adamu,dan kabeer be taɓa yimata ba.


Najeeb fa baa magana seda suka ɗauki lokaci me tsayi ahaka,salma duk tagama releasing,se lokacin najeeb ya lura da abinda yakeyi,azabure yamiƙe tsaye,yana kame kame yama rasa me zeyi,wai shi dayazo yayi hukunci shine ya ɓuge da murza boobs,taya haka ta faru.


Kallo yabi salma dashi wacce ke kwance tana juyi akan gadon kamar tarwaɗa.


Da sauri ya ɗauke idonshi daga dubanta asakamakon zillon da hajiya babba tafara yi acikin wandonshi.


"wanne iskancine yasa kika cire riga?"cewar najeeb cikin fushi.


Dariya salma ta kwashe da ita sannan ta sakko akan gadon tana ƙara girgiza boobs ɗin tace.


"Ay ni yadace inmaka wannan tambayar,wanne iskancine yasa kaciremin riga?"ta ƙarasa maganar tana dariya.


Shuru najeeb yayi dan se yanzu yatuno shi yacire rigar,amman se yafara bori. Kunya da cewa.


"kede akwai jarababbiya wlh,ubanme zanyi da jikin naki da har zan cire miki riga,?second hand din?"


Murmushi salma tayi ta tako zuwa gabanshi,duba takai kasan wandonshi,dariya tayi,sannan tace.


"Ay jarababbiya se jarababbe,saura kuma ay dole se saura,ni banason wani dogon turanci kawai kaje kayi wankan tsarki Alhaji"


Rai aɓace najeeb ya ɗago yana kallonta yace.


"ubanme zesa inyi wankan tsarki,?"


Ba kunya salma ta tsafko ƙasan wandon tana dariya tace.


"wannan zaka wanke"


A ruɗe najeeb yakai dubansa gurin,ajiƙe yake sannan gashi a miƙe suk da wanduna biyu ne ajikinshi hakan be hana agani ba.


wata kunyace ta kamashi,da gudu yafice daga ɗakin yanufi nashi.


itako salma kwashewa tayi da dariya ta faɗa kan gado,wayarta ta jawo,ta kira feefee,ba jimawa ta ɗaga.


"amarya da kiran waya ƙarfe goma na dare?"cewar feefee tana dariya.


dariya salma tayi,sannan takwashe yadda sukayi da najeeb ta faɗa mata.


"Ay dama na faɗa miki,kicire kunya,tunda kallon karuwa yake miki to kinuna masa karuwancin acikin gidanshi,karki sake ki ɗaga masa ƙafa,duk abinda ze rikita mishi tunani shi zaki dungayi,wlh,ko yana da dangantaka da firauna dan taurin kai,se ya sakko,kuma bashi kaɗai bama,wannan matar baban nashi naga se wani cika take tana batsewa wlh karki kuskura kibarta taci kasuwarta akanki,dan ba zamanta kikeyiba,danna lura akwai makirci atattare da ita,kuma yanzu ki tashi kiyi wanka,ki ɗauki wankan sikari,kibishi ɗakin nashi,ki goge masa lissafi"


Dariya salma tayi sannan tace.


"Feefee wai dama kinsan wainnan abubuwan amman muna nysc baki taɓa koyamin ba?"



"salma kenan,ay nawuce da saninki,naƙi koya mikine alokacin danna lura kanki na hayaƙi,amman yanzu tunda kinshiga daga ciki kullum in aka koyomun,zan koya miki"


"Au koya miki akeyi?don Allah wa ke koyar dake,sirrin rikita oga?"


"hhhh ay anbarki abaya,kinmanta group ɗin surbajo,da novels dinta,koda yake naga kinfi shekara uku da fita agroups ɗin nata shiyasa baki sani ba,amman ay surbajo tayi arayuwa wlh"


Dariya salma tayi gami da cewa.


"Allah ya shiryeki feefee,naga lokacin bakiyi aureba amman shine kika baza kunne kina koyon abun masu aure,bakya gudun ki lalace"


"salma kenan,ay lalatacce haifarsa akeyi,tun usuli,yanzu ke alokacin ay baki karantawa,amman wacce irin tsiyace baki tsulaba,ni kuma danake karantawa,adanasu nayi zuwa gidan mijina sannan nafara amfani dasu,wanda kema gashinan sunmiki rana,dan haka,nide novels din surbajo se godiya wlh zan tura number ki asaki a group din,danni ba kullum zan koya miki ba"



hakade suka ɗan taɓa hira sukayi sallama,wanka salma tashiga,tana fitowa ta haɗe,acikin wata arniyar marroon ɗin rigar bacci wacce gaba ɗayanta net ce,panta kawai tasa,tafeshe jikinta da turaruka,tanufi ɗakin najeeb.


muje zuwa.


Banason comments da thanks,adunga sharhi,dan musami ƙwarin guiwar ɗorawa daga inda muka tsaya.



surbajo for life.

*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*




Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION


*BABU ME GANE DAN ISKA SE DAN ISKA*



*MAMAN ZARA NAGA SAKONKI NAGODE NIMA INA SONKI,KINASO MUDUNGA COMMUNICATING,AMMAN BAKI TURO SAKON DA NUMBER KI BA,SO INKINGANI SEKI TURO NUMBERKI,SURBAJO NA MARABA DAKE*



*28*



Sanda najeeb ya isa ɗakinshi,ji yayi duk kunyar duniya kamar shi aka ɗorawa musamman daya cire kaya yaga irin ayka aykar dayayi.


Wanka yashiga,be jimaba yafito ɗaure da tawul,yayinda yake tsane jikinshi da wani tawul din.


Gurin wadrop yaje yabuɗe ya ɗauko kayan shi na bacci ze saka,


Kwance tawul din yayi yana ƙoƙarin zura wandon.


Dariyar da salma ta ɓoyece ta fito,A ruɗe yakai dubansa kan gadonshi salmace kwance tana kallonshi tana dariya.


Rasa inda zesa kanshi yayi da bsƙin ciki da takaici,yau akaron farko wata mace taga tsiraicinshi.


Da sauri yazura wandon yasaka rigar,sannan yafara magana cikin fushi.


"Ke nifa ba ɗan iska bane,taya zaki dunga yimun abu sekace tsohuwar kilaki,wlh kishiga taitayinki inba hakaba zakisha wuya wlh"


Tasowa salma tayi tana matsowa gabanshi,runtse ido yayi dan beson kallonta.


"To ay doctor ina maka hakane,sabida nasan kai baɗan iskan bane inda ɗan iskanne ay base na wahal dakainaba,kuma iskancin mace agun mijinta ay shine me kyau,dan haka wlh yanzu nafara,nida kai naga me gajiya ya sakko"


Tana kaiwa nan ,gurin kayan kallon ɗakin taje ta kunna,ta jona wayarta da speekers din tasaka waƙar Ado gwanja,me taken,yan mata girgiza nan,nan tashiga bin kiɗan tana girgijewa,hankalin doctor in yayi dubu yatashi,musamman ganin yadda salma ke kaɗa na shanunta da kuma mazaunanta.


kasa jurewa yayi da sauri yaje yakashe kayan kallon sannan yace.


"ke baki da hankaline shadaya na dare ki kunna mana kiɗa sekace kanwar dujal?" 


Matsowa gurinshi salma tayi ta saqala hannunta a kafaɗarshi,taci gaba da mamin din waƙar da bakinta,tana goga masa na shanun a ƙirjinshi.


Doctor fahimta yayi salma balai take nema,dan haka,surarta yayi gaba ɗayanta ya kwantar akan gadon,yace.


"masifa de akwance take Allah ya tsinewa me tada ita,na lura so kike na biye miki ajiyo mu to badaniba,kwanta kiyi bacci,nagani kin iya girgizawa,base kin sake nunaminba,jarababbiya kawai"


dariya salma take masa buɗe baki yayi zeyi magana da sauri ta haɗe bakinsu guri ɗaya,hmm naso ace kunga idon doctor a lokacin.


Tun yana basarwa irin beso ɗinnan harde yazo yana maida martani,haka sukasha romance ɗinsu,har bacci ya ɗaukesu,rungume da juna.



Da Asuba najeeb ne yafara farkawa,jin hannun shi ysyi akan wata dunlop da sauri yakai dubansa gurin😁ba dunlop bane boobs ne,daya kwana matsawa.


Da sauri yacire hannunshi,shuru yayi yana tunani,meyasa yake shiga wani hali aduk sanda jikin salma ya raɓeshi?meyasa baya iya fushi da salma?yarinyar fa tafara burgeni meya janyo haka?wani shashine na zuciyarshi yabashi amsa da cewa.

kabar mata gidan,kawai shine zaka samu natsuwa,inba hakaba mahaukaci zata maidaka.


da wannan shawarar yamiƙe yaje yayi wanka,yayi alwala,yazo yafice masallaci.


salma miƙewa tayi itama,koda taga baya dakin tasan masallaci yanufa,kallon yadda ya zamemata riga tayi ta kwashe da dariya,wato doctor bemasan sanda yacire mataba,acikin bacci yafara wasa dasu duk be saniba,maida rigar tayi tawuce ɗakinta,da sauri tayi wanka tayi sallah,sannan ta tsantsara kwalliya,cikin riga da wando,wainda suka fito da ƙirarta,baza gashinta tayi gadon bayanta,ta feshe jikinta da turare,.


Ɗakinshi taje ta gyara ta wanke toilet din ta frshe ɗakin da airfreshner,daga haka tarufo ɗakin,taje ta gyara nata,sannan tanufi kitchen.


Nanfa salma tashiga baje fasaharta a fannin girkin,(inkuna so zaa dan dunga koyar da girkin,agajarce,)kamin wani lokaci gida ya buɗe da ƙamshi.


Najeeb be dawo daga masallacinba,se bakwai da rabi na safe,tundaga falo yafara jiyo ƙamshi,take miyau dinshi ya tsinke,hanyar kitchen ɗin yanufa dan yaga waye ke wannan aykin


da cikar hips dinta yagane,najeesal ce,tsayawa yayi yana kallonta,jikinta ne yabata ana kallonta,da sauri ta waigo ganin shine tsaye yazuba mata na mujiyane yasa tarugo zuwa gareshi,ta maƙaleshi,tana fadin.


"haba hubbi shine kaje kayi zamanka a masallaci ko kazo katayani aykin ko"ta faɗi cikin sigar shagwaɓa,harda bubbuga ƙafa akasa,


Sosai ta burge najeeb,jawota yayi jikinshi,yace.


"To uwar neman faɗa,me zan tayaki,naga kamar kin gama"yafaɗi yana kureta da ido.


Murmushi tayi,sannan taɗan goga na shanunta,a ƙirjinshi tace.


"nagama amman ay bankai dinning ba,dan haka,goyani zakayi nikuma nadunka ɗauka ɗaya baysn ɗaya muna kaiwa dinning muna dawowa"ta faɗi tana sake matsarsa.


Tsintar kanshi yayi damata murmushi,sannan yace.



"to ay bacemin akayi inje zan ganiba,dazan goya ki abayana,keda wainnan maka makan cinyoyin naki,salon ki karyani,to badaniba wlh"yana kaiwa nan yayi sauri ya ƙwace jikinshi yafice daga kitchen ɗin.


Da gudu salma tabi bayanshi,suka haura saman tare,ruwan wanka ta haɗa mishi,dayasha turaruka kala kala,ba ƙaramin daru sukayiba,dan salma dagewa tayi bil haqqi itace zata mishi wankan,seda yasa ƙarfi ya korota daga toilet ɗin yakulle ƙofar,yayi wankanshi,kamin yafito ta ajiye mishi kayan dazesa,harda takalmi da agogo.



koda yafito gurin cin abinci,haka tasashi agaba ita akan cinyarshi zata zauna,rasa yadda zeyi da ita yayi haka dole yabarta ta zauna.


ayko zamanta keda wuya iska tafara kumbura wandonshi,salma taji alama,amman sema ƙara wani juyi take akanshi,doctor de gaba ɗaya yazama wani gaula



da kanta tadunga bashi abincin har ya ƙoshi shima yabata.


sungama ci kenan,sega hassana ƙanwar doctor ɗauke da plaks ɗin tea,ɗaya hannun kuma biredi,wai shine abincin amare,salma amsa tayi takai kitchen.


koda ta buɗe plaks ɗin ruwan bunune amman duk burtsatsi kamar na magani,dan haka juyeshi tayi a sink ta kora masa ruwa.


biredin tasa a shara.


Anata ɓangaren hajiya kaltum tacika da murna da hassana tace mata,taga salma ta shiga kitchen da plaks ɗin,zata haɗo musu tea,bakomai yasata murnaba,illah dan tazuba maganin da wani boka yabata da zummar inde,najeeb yasha to ba makawa se yazo gareta,


Dan haka da sauri ta kora su hassana ɗakinsu ita kuma ta shige ɗakinta dama megidan Asubar fari yatafi Abuja.


Tana shiga ɗakin,tayi tsirara,tayi matsi da wasu magungunan,sannan ta haye kan gado taja bargo,tana jiran isowar najeeb.


itako salma,gyara komai tayi,tawanke plaks din,sannan taje gurin najeeb dake zaune yana kallon sport tace.


"kataso muje mugaida su Abba kamin yafita"


"Abba bayanan yaje Abuja,dan haka ni ba inda zani"



"to muje mugaida hajiya"


"se kin dawo"yabata amsa rai aɓace kamar anturo masa da mutuwa.


Miƙewa tayi jiki asanyaye taje ɗakinta,ta ɗauko hijab,sannan ta ɗauki plaks ɗin tanufi cikin gidan domin gaida hajiyar.





muje zuwa.



surbajo for life.


*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*




Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION.



*29*



Cikin natsuwa salma take tafiya har ta shiga falon gidan.


Sallama tayi,amman ba kowa daya amsa cigaba tayi da sallamar,zuwacan sega hassana tafito,tagaisheta.


Salma ta tambayeta mamansu,nuni hassana tamata da ɗakin maman nasu ,nufar ɗakin salma tayi.


Tana isa ƙofar ɗakin,ta cinkayo muryar hajiya tana waya,ɗan saurarawa tayi kaɗan.


"haba hajiya yahanasu,ni ta wasa ce,ay tuni nazuba musu aruwn tea kuma hassana tace taga alamun zasu sha,ay tunda na lashi takobin kwanciya da najeeb domin kawar da matsananciyar shaawar dake damuna,wlh ba makawa senayi,yanzu haka ko kaya babu ajikina jiranshi kawai nake yazo na kwashi gara,dan bazan taɓa bari yakusanci matarshi ba"


Jikin salma rawa yake kamar mazari,ga salma dama akwai ɗan banzan kishi,plaks ɗin hannuntane ya kubce ya faɗi kasa ya fashe,ɗa gudu tajuya tafice daga gidan tanufi nata tana kuka.


A falo tazo ta wuce shi a 360 ta haura sama,a firgice najeeb yamiƙe,ya leƙa waje yaga ba wanda yabiyota,kulle ƙofar yayi sannan yabita saman.

  

Kuka take kashirɓan,tana kwance akan gado,


"lafiyar ƙalau kuwa kikewa mutane gudu agida yanxu kuma kina kuka?,keda waye?"


Salma cigaba tayi da kukanta,shikuma najeeb arayuwarshi ba abinda ya tsana irin kukan salma,dan haka hannu kawai yasa yaɗauketa cak yanufi ɗakinshi da ita.


Akan kujera ya ajiyeta,yanufi fridge ya ɗauko ruwa yazo yabata abaki,sannan yajawota,yana shafa gashin kanta,yana ɗan bubbuga bayanta,yana hura mata iska akunne,da ƙyar yasamu tayi shuru sannan yace


"to ya akayi,kike kuka faɗamin?"


Wasu hawayene suka biyo fuskarta,cikin kuka tace,


"doctor ni masoyiyarkace tun da jimawa,meyasa ni baka sona baka ƙaunata?"


Shuru yayi yana kallonta tausayinta na ƙara shiga zuciyarta,jawota yayi sosai ajikinshi,yana shinshina wuyanta ya raɗa mata akunne.


"salma ay inaga ko bana sonki ay ina tausayinki,me kuma kike so namiki bayan haka?"ya ƙara shigarta sosai,


"soyayyarka nakeso doctor bana son komai se ita,inba soyayyarka bazan ci galaba a yaƙin daya tunkaroniba"


"salma waishi wannan son dakuke magana akai don Allah ki sanar dani alamunsa,ni wlh bansanshi ba"


Cike da mamaki take kallonshi,najin cewa wai besan soba,cikin natsuwa tace.


"doctor,zan faɗa maka alamunsa,amman inde nagama faɗamaka,zaka faɗamin wacce alama kakeji game dani,ka amince?"


Kai ya gyaɗa mata yana murmushi.


"in ka kamu dason mutum,mace ko namiji,nafarko zaka dunga jin haushin shi batare daya maka komaiba,aduk lokacin daka ganshi ko aka ambaci sunan shi gabanka seya faɗi,zaka kasance meyawan son ganinshi koda bazaka ce masa komaiba,zaka dunga ɗawainiya dashi koda be tambaya ba,zaka dunga tausayinshi,kishinshi me tsanani ze kamaka,dazaran yashiga damuwa,baka samun natsuwa sekaga yafita,da zaran jikinku ya haɗu guri ɗaya ji zakayi kamar anmaka shocking,duk inda akwai so akwai shaawa me ƙarfi,in masoyinka yay maka laifi baka iya hukuntashi bare kayi fushi dashi,dazaran ka rasashi,inso yakai so to mutum har rayuwarsa yake rasawa,wani kuma yayi yunƙurin kashe kanshi,wannan sune alamu naso,duk wanda yasamu kansa awannan jerin to yana cikin son abun dayakeyi dominsa,kai wanne kakaji game dani,nide duka inaji game dakai,kaifa?"tayi tambayar hawaye nabiyo fuskarta,ga mamakinta shima kukan yake.


Rungumota yayi da ƙarfi jikinshi,yana faɗin.


"salma duk abinda kika lissafa,tun farkon ganina dake nake jinsu game dake,ko kuɗi danake ajiyewa ki ɗauka ina ajiyewane sabida na lura ɗaukar nasaki farinciki,ina ajiyewane sabida gudun karkije ki ɗauko na wani asirinki yatonu asaki acikin damuwa,salma inde wainnan sune alamu naso,toni son danake miki,dubun wainnan ne,wlh inasonki salma koda wasa banaso narasaki,rashin sanin meye so ɗinne yasa nabarki atun farko,salma ki gafarceni,ni mutum ne me tsananin kishi bazan iya haɗa shimfiɗa dakeba alhalin nasan wasu sunrigani,amman batun so na amince salma kece rayuwata,farin cikin ki shike haska lamurana"yaƙarasa zancan yana kuka,itama kuƙan take tace.


"naji nayarda doctor daduk bayaninka,zancan bazaka iya kwanciya daniba ma duk na amince,sede kasani meyi baya faɗi,akwai lokaci"



Begane manufarta ba,danhaka rungumeta yayi sosai ajikinshi,yanzu ya amince shi masoyintane,na sosai da sosai,dama kabeer ya faɗamasa be yarda ba yaukam ya yarda ɗari bisa ɗari.


Miƙewa salma tayi zata fice aɗakin,da sauri yakamota ta dawo,akan cinyarshi ya ɗorata,yace yana dariya.


"Angona ina kuma zuwa?"


Ido taware sannan tace.


"Ango kuma kamar ya?"


"Hhhh ay dole nakiraki ango tunda ko alabari,bantaba jin amarya irinkiba,acting dinki na angwayene,to kinga ni kuma amaryar na koma shiyasa nakiraki da angona"yaƙarasa batun yana dariya.


Dariya tayi tace.


"to ay yanzu ka amshi abunka,rashin amsar dabakayi bane yasa ni na amsa gudun kar nabarshi ya faɗi abanza".


"wannan gaskiyane,daga yanzu najeeb ya amshi aykinsa,ni angon salma ne na har gaban abadan,sabida dan ita akayine,kamar yadda itama danni akayota"


miƙewa tayi zata fice,riƙota yayi yace.


"wai ina zakine kike ta wannan sauri?"


shagwabe fuska tayi sannan tace.


"wankafa zanyi,kuma ka hanani tafiya"


"namma ay akwai gurin wankan,kiyi anan"


murmushi tayi,sannan tace "to"



Miƙewa tayi,tafara cire kayan jikinta agabanshi,baya ta juya masa,koda zata cire dogon wandon dake jikinta,haka tawani gaggantsare,ta cire ta cire rigar,ta tsaya daga ita se fant da bra wainda suma kuma duk net ne,ji taƴi an rungumota ta baya.


"Baby su wainnan dasu zakiyi wankan ne?"

Yana maganar yana ɓalle bra din har yagama cirewa ya wurgata kan gado,hannunshi,ya ɗora akan na shanun,yana wasa dasu,cikin wani salo wanda salma bata taɓa sanin dashi ba.


kasa tsayuwa tayi dan haka zamewa tayi ta zauna agefen gadon.



doctor wanda zuwa lokacin idanuwanshi,sunyi ja,sun kankancw sabida shaawa,binta yayi kan gadon,kwantar da ita yayi yaci gaba da wasa da ita.


uhm,su salma abun nema yasamu,nanfa itama taci gaba da ɗan shafo,shi dakyau,najeeb tsintar bakinshi yayi yana sucking boobs din salma,daga shi har ita suna enjoying abun.



sun jima ahaka,sannan kowa yakwanta yana maida numfashi.


Najeeb ne yafara tashi,yanufi toilet,ya haɗa musu ruwan wanka,dawowa yayi ya ɗauketa,suka shiga toilet din tare.



ba abinda yabashi dariya kamar yadda salma ta tubure ita bazata cire wandonta ba,sabida kar yaganta wai sede tayi wankan da wandon.


Kamo ta yayi yatube wandon ta ƙarfi,sannan yafara yimata wankan tana ta yimasa kuka,kuma ta rufe idonta,wai bazata kalleshiba.


shiko ko ajikinshi,wanketa yayi tas shima yayi wankan,sede akwai wani abu da yayi observing sanda yakewa salma tsarki,wanda ya ɗaure masa kai,amatsayinshi na doctor yasan ajikin virgin kawai ake samun hakan.


Naɗota yayi a tawul suka fito se mita take masa ,shide dariya kawai yake mata,shiryawa yayi sannan yaɗauketa zuwa ɗakinta itama yashiryata.




muje zuwa


surbajo for life.


*👩🏻‍💼Y'AR BAUTAR K'ASA*




Zahra Muhammad Mahmud



DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION



*DON GIRMAN ALLAH,BABBA DA YARO MATAN AURE,ZAWARAWA,YANMATA,MAZA ,DA KOWA DA KOWA,DUK WANDA SURBAJO KO LITTAFINTA YATAƁA BATAWA RAI,YAYIWA GIRMAN ALLAH YA GAFARTAMIN,KUYAFEMIN DON ALLAH,NIMA NAYAFEWA KOWA,ALLAH YASA MUYI KYAKKYAWAN KARSHE,🙏🙏🙏*



*KHALEESAT HYDAR NAGODE DA SHAWARAR KI GARENI,INSHA ALLAHU DAGA YAU BAZAKIJI AN KUMA  KUKA DA SURBAJO BA HAR ABADA,NAGODE DA SAMUNKI A RAYUWATA*



*last page*


*30*



Hajiya kaltum jin shurun yayi yawane yasa tamiƙe,ta ɗauro zani ta leƙo waje.


Da plaks tafara cin karo,kuma afashe,da sauri ta nufi dakin su twins dan taji ko waye yakai flaks din


Hassana ce ta shaida mata salma ce tazo kawowa da kanta.


Wani gumine ya karyowa hajiya,sabida ts gano salma taji maganarta,shine ta firgita ta yadda flaks din.


To yanzu yazatayi,haka tashiga safa da marwa agurin cikin tashin hankali tsoronta kada salma ta tona mata asiri,zuwacan wata zuciyar tabata shawara kuma tagamsi da ita.



Salma da najeeb ko falo suka dawo suna kallo,yana rungume da salma ajikinshi,basu da damuwar komai,shafo fuskarta yayi yace.


"Baby na,yadace fa na waiwayi office,duk da sunsan banda lafiya,amman yana da kyau tunda yanzu na warke nakoma bakin ayki"


Turo baki gaba salma tayi sannan tace cikin shagwaba.


"to amman ay yanzu kuma hutun amarci kakeyi,dan tuni ka gama na jinya"


Dariya yayi sannan yace.


"wanne amarci kuma babyna,aysu basu san dashi ba,dan haka zan koma inde baso kike su koroniba"


Miƙewa tayi daga jikin nashi,tana bubbuga ƙafa akasa tana kuka tace.


"wlh baze yiwuba,sede katafi dani inde kanaso nabarka katafi,"


Jawota yayi yamaida ita jikin nashi yace.


"to iya rigima naji zan tafi dake,amman kibari,nafara zuwa nayi gyare gyare a inda zamu zauna tukuna ko"


hakade salma taita rigimar sesun tafi tare yana rarrashinta,dakyar ta amince yafara zuwa seya dawo su tafi tare.


Koda lokacin girkin rana yayi tare suka shiga kitchen,yana tayata har suka gama,sannan sukajw sukayi wanka tare,suka zo suka ci abincinsi.


Washe gari da wuro najeeb ya tafi Abuja,bayan yasha rigima agurin salma.



Tafiyar najeeb ba jimawa,hajiya kaltum ta shigo part din masu.


A falo tasamu salma,wacce keta faman shan kukan tafiyar mijinta.


ko sallamah batayiba,tacewa salma.


"ke ina mijinki?"


A firgice salma ta juya tana kallonta,da har zata juye mata kwandon masifa sekuma ta fasa,setayi kasa dakai,alamar girmamawa,tace.


"hajiya yatafi Abuja"


"jiya me kikaje yi kofar dakina?"


"najeeb ne yace naje na gaisheki"


sosai maganar taba hajiya mamaki,cikin zumudi tace.


"Shi najeeb dinne yace kije ki gaisheni?"


Kai salma ta ɗaga mata.


"to meyasa kika yadda flaks agurin har ya fashe?"


"danaje ina ta sallama baki jiba,nikuma jin shuru danayine yasa na ajiye flaks din agurin na dawo,gurin tahowane hijab dina ya riƙeshi yafadi,ganin bansan inda abin shara yake bane yasa nabarshi,agurin nataho,amman don Allah kiyi haƙuri."


Wani sanyine ya ratsa zuciyar hajiya najin cewa salma bataji maganarsu ba.


Kan kujera taje ta zauna,sannan takamo hannun salma tace.


"yata Allah ƴamiki albarka,ina fatan de kunsha tea jiya?"


"eh munsha hajiya,wlh najeeb ma yana gama sha,anan yay ta juye juye,wai inkira mishi hajiya ita yake buƙata,kuma baze iya zuwa gurinta ba,sabida halin dayake ciki,to hajiya ni bansan wacce hajiya yake nufiba,hakanne yasa nabashi lemon tsami da kanwa,dan suna maganin ciwon ciki,to daya shane yadawo hayyacinshi,"


Ran hajiya ne ya ɓaci jin cewa salmace ta ɓata mata show jiya,amman seta kauda bacin ran tace.


"Ayya ay kinyi kuskure,in irin haka tasameshi,karki sake bashi kanwa,akwai maganin da ake amso masa,inde yakuma yi ki kirani,kinji ko yata"


Kai salma ta gyada mata cike da ladabi.


Sun jima suna hira hajiya da salma,sannan hajiya ta tafi.


Bin bayanta salma tayi da wani malalacin murmushi,tace a fili.


"hmmmm yaro besan wuta ba se yataka"


Haka rayuwar salma takasance agidan kullum suna manne awaya ita da doctor,yayinda hajiya kuma ta dage gurin zuga salma,wai tadena kwalliya da kananan kaya,kuma tadena bari suna zama giri ɗaya da najeeb,sosai salma take nuna mata gamsuwarta game da shawarwarin.



Shiko najeeb tunda yakoma Abuja ko baccin kirki bayayi,sabida sabon dayayi da wasa da jikin salma,gashi yanzu wata azababbiyar shaawarta ke taso mishi,wacce har ciwon mara take sashi,gashi salma koda yayi nisa da ita seta kirashi video call,in banda boobs da laps di ta ba abinda take nuna mishi,ko ta ajiye wayar ta miƙe tacire kayanta tsaf duk yana kallo,wai azuwan zata wankane,ko kuma taita yimasa sexy dance.


Ganin dayayi yana ƙoƙarin susucewane yasa ya tattaro nasa ya nasa ya dawo kano.


Ranar salma tashi tayi da ciwon mara wanda take fama dashi aduk lokacin da zatayi alada.


koda najeeb yashigo gidan,takasa zuwa ta tarbeshi,dan haka shida kanshi yabita ɗakin,a kwance yaganta akan tiles tana ta faman juyi,da sauri ya ɗagota yana tambayarta ko lafiya.


nuni kawai take masa da mararta,da sauri ya ajiyeta yaje yakwaso kayan aykinshi yazo yadubata.


kanshine ya ɗaure naganin matsalar salma,matsalace da yanmata suke fuskanta,wanda da zaran namiji ya kwanta dasu shimenan ta kau.


jiki asanyaye ya gyara salma yabata magunguna tasha tadamu bacci.



kitchen yashiga,ya haɗa musu abincin da zasu ci,sannan yaje yayi wanka yakoma ya samu salma ta farka.


Tana ganinshi ta rugo da gudu ta rungumeshi,tace ashagwabe.


"se  yau nake ganinka ko?"


hancinta yaja ya kara rungumota,yace.


"tunda lafiya tasamu ay kyayi complain yanzu mana,Amman dazu ko magana bakyayi"



dariya tayi tasake shigewa jikinshi,tace.


"to ay amfanin likita akusa kenan,gashi nasamu sauƙi"



hakade sukai ta wasanninsu irin na masoya,daganan ya danganata da toilet ya wankota fes yashiryata,yajata sukaje suka ci abinci,salma se santi takeyi.


hajiya kaltum,tunda tadamu labarin dawowar najeeb,tasake ɗaura ɗamarar cimma manufarta.



salma itama tagama haɗa duk wani tarko datakeso hajiya ta faɗa.



Yau tunda safe najeeb yake fama da ciwon mara,adaddafe yakeyin komai,ahaka salma tashigo ɗakinshi tasameshi.


A ruɗe ta isa gareshi,tana tambayarshi abinda ke damunsa.


"salma shaawace tamin yawa,duba da shekaruna talatin da shida bantaba kusantar mace ba,narasa yadda zanyi,salma,ke kuma kishi baze bari na samu natsuwa daga garekiba"da kyar yakarasa furta maganar.


miƙewa salma tayi,tacire kayan jikinta tana kuka dan batason ganinshi cikin damuwa.


daƙyar ta iya janshi zuwa kan gado,idonshi arufe yake shikadai yasan wuyar dayake sha,salma rabashi tayi da kayan shikinshi,sannan tafara kissing din koina najikinshi,sannu ahankali,harta gangaro kan hajiya babba,tunda bakinta yasauka agurin,najeeb yaji wani abu nafita ajikinshi da gudu,wani nishi yasaki,yakamo salma yadawo da ita gabanshi,shima yashiga romance dinta,sannu a hankali,har ya iso babban gareji,da kyar ya iya karanta adduar saduwa da iyali,dannan ya afka ciki.



Se alokacin salma ido yaraina fata,ihu take tana dukanshi amman najeeb bemasan tanayiba,dan abinda yakeyi,yatafi da jinshi da ganinshi,da hankalinshi.


salma ta wahala ahannunshi,kuka tayishi har muryarta ta dishe,da kyar najeeb ya iya haƙura da ita,mirginewa gefe yayi,ya lumshe idonsa hawaye na farinciki na zuba afuskarsa.


Salma cikin ta kaura yayi laasar,godiya tadunga yiwa Allah dabesa tasha wannan,azabar abanza ba,wajwn siyar da mutuncinta awaje,taga taɓewa da rashin hankalin matan dake siyar da budurcinsu awaje,se yanzu taƙara sanin darajar budurcinta.


jawota doctor yayi yarungume ajikinshi yana kuka,yace


"Agaskiya salma kinshayar dani mamaki,koda wasa ban taɓa tsammanin zan sameki a virgin ba,ina miki kallon wacce tagama zubar da mutuncinta awaje,don Allah kigafartamin,nayarda salma danke akayini,nima kuma danni aka yiki,bansan irin son danake miki ba,salma,baya ga mahaifiyata,kinfi kowacce mace daraja,agurina,don Allah kiriƙeni amana"


Rungumeshi salma itama tayi tana kuka.



sunjima suna musayar kalaman soyayya,kana daga bisani, yakaita toilet sukayo  wanka.


fitowarsu kenan suka jiyo sallamar hajiya afalon,da sauri salma taja najeeb kan gado tace."zauna anan kajirani,kuma bance ka shiryaba kajirani,zanzo na shiryaka"



kai kawai ya ɗaga mata,ita kuma tajuya tafice zuwa falon.



"ina kuka shige inata sallama baku jiniba?"cewar hajiya tana yiwa salma kallon kurulla.


murmushi salma tayi,sannan tace.


"wlh hajiya nashiga wankane,fitowa ta kenan naji shigowarki"


"Allah sarki,haka yayi kyau,ina mijin naki fa?"


"inajin yana ɗakinshi,kinsan ni ba shiga harkarsa nakeyiba bare insan inda yake"


murmushin jin daɗi hajiya tayi sannan tace.


"haka yayi kyau shiyasa nake,sonki,bari induboshi adakin nashi,dama zan faɗa masa sakon mahaifinsane,"


"to hajiya afito lafiya,nima bari naje na shirya,dan bacci ma nakeji wlh,ta iya yiwuwa kamin kifito ma nayi baccin,"



"Gaskiyane ay gwandama kiyi kwanciyarki ki ki huta ze fiye miki"


Mikewa salma tayi tashige ɗakinta yayinda hajiya tanufi dakin najeeb ko kunya babu.



Salma nashiga dakinta wayarta ta ɗauko da niyyar zuwa tayi musu video,amman ƙarar buɗe get din gidanne,yaja hankalinta ta leƙa ta window,


Motar mahaifin najeeb tagani,tana shigowa alamar dawowarshi daga tafiya kenan.


Wani murmushi ne ya kubce mata danhaka ajiye wayar tayi,ta gyara daurin towel dinta da kyau,sannan ta runtuma da gudu zuwa gurin Alhajin.


Itako hajiya,tana shiga ɗakin najeeb,tafara cire kayanta,najeeb dake kwance daga shi towel,idonshi arufe,koda yaji motsin shigowa,be buɗe idonshiba,dan,azatonshi,salma ce.


Hajiya tsirara tayi sannan tanufi gadon,tana zuwa kwaciya tayi abayanshi tafara shafashi,shide se murmushi yakeyi azatonshi salmace,hannu yasa da niyyar shafo boobs ɗinta.


Jindayayi ya shafo wasu yanusassun silifas ne yasa ya buɗe idonshi da sauri,ganin hajiya kaltum kwance kusa dashi,besan sanda ya wuntsulo daga kan gadonba,


Ja da baya yakeyi,tana binshi har suka kai jikin bango,kokawa suka fara,nason kwance masa towel da hajiya katum keson yi.


Itako salma da mahaukacin gudu ta isa gurin Alhaji tana haki tana kuka.


Fitowarshi daga mota yayi daidai da zuwanta,agigice yake tambayarta,abinda yasameta,amman salma se hakin karya takeyi tana yimasa nuni da gidanta,bakinta na rawa tace.


"Abba najeeb hajeeya"


Daga haka seta juya da gudu,Alhaji,yarda jakar laptop dinshi yayi tabi bayanta da gudu shima dan ya lura,wani abune yake faruwa daya gigita ta.


Atare suka isa ƙofar dakin najeeb,adaidai lokacin,Alhaji yayi tuntuɓe yafaɗi kamin yatashine yajiyo muryar hajiya tana fadin.


"Najeeb baka da tausayi da imani,sama da shekara goma ina fama da shaawarka amman kaki kabiyamin bukata,sabida ni ko garinnan bakason zuwa,indan mahaifinkane ay baya nan kuma ba ganewa zeyiba,katausayamin najeeb ka kusanceni yau kawai,katausayamin shaawarka kasheni zatayi inba kwanta daniba."


"Allah yaymin tsari da sharrinki hajiya,wlh koni fasiƙine bazan haɗa shimfiɗa d mahaifina,Kibar ganin bantona asirinkiba,nabarine Allah yatona ki dakanshi,wlh bazan taba yafe miki ba"najeeb yaƙarasa maganar yana kuka.


Afusace Alhaji yatura ƙofar yashiga dakin daidai lokcin hajiya na ƙoƙarin kwancewa najeeb towel.


Tana ganinshi tayi sauri tasakeshi ta nufo Alhaji tana kuka tafada jikinshi,tace.


"gwanda da Allah yakawoka,Alhaji,da yanzu danka yamin fyade,gashinan yajima yana kawomin farmaki,bantaɓa amincewa dashiba,shine yau yakirani awaya akan inzo beda lfy,zuwana kenan shine yake ƙoƙarin haikemin taƙarasa maganar tana kuka"


A gigice najeeb yake kallon mahaifinshi,bakinshi na rawa yace.


"wlh Abba sharri takemin ita....."


"Yimin shuru"Alhaji ya dakatar dashi,hajiya harta fara murna,se jitayi,Alhaji yazuba mata wani wawan mari.


Daga haka yarufeta da duka,yana faɗin.


"tsohuwar munafuka ay naji komai,Allah yaisa tsakanina dake,ashe kece silar da najeeb yake gudun zama tare dani,Banyafe miki ba kuma nasakeki saki uku,bakar matsiyaciya annamimiya"


Be jira komaiba yajuya yafice daga dakin hawaye nafita a idonshi.


Fitowarshi ce tasa salma shiga ɗakin tana dariya,gaban hajiya taje ta tsuguna tace.


"to tsohuwar kilaki,se abi wani sarkin ba mijina ba,ayni salma nawuce da saninki,tun ranar danaje gaisheki naji duk wata manufarki akan mijina,shiyasa na lashi tokobin kawo karshen makircinki,mijina nawa ne ni kadai,babu wata mace data is ta lashi zumarshi seni,shiyasa nashirya miki gadar zare kuma kika faɗa ciki,nida kaina naje nakira Abba yazo yagani da idonsa,kuma Alhdllh tunda bayan ganin har mataki ya ɗauka yanzu base anjima ba kitashi kificemin daga ɗakin miji kamin inmiki nawa dukan na kamaki da nayi da laifin neman mijina"


Cikin kuka hajiya kaltum ta mike tasa kayanta tafice daga ɗakin tana ɗingishi.


Salma jitayi anrugumota ta baya,juyawa tayi suka rungume juna ita najeeb,kuka yakeyi yace.


"salma narasa bakin gode miki,kamar yadda na cetoki daga gidan yari yau nima salma kin cetoni daga sharrin kaltum,kuma kinshayar dani zumarki wacce babu wacce ta taɓa bani seke,mezanyi miki salma na faranta miki"


"kasoni ni kaɗai azuciyarka,shine kabiyani,kuma shikadai ze sani farinciki"


Rungumeta yayi da kyau ajikinshi yana faɗin.


"ni nakine har abada salma".


Itako hajiya kaltum tana fita,mota tasamu lode da kayanta,ko cikin gidan Alhaji be bari tashiga ba yadanna kanta aciki yace amaida ita ƙauyensu,can danmarke.


Tana kuka tana danasani tashiga motar,su twins se kuka sukeyi,haka aja jata akayi kauyensu da ita.


Alhaji,kiran najeeb yayi yasa masa albarka,sannan yabashi haƙuri gsmida neman gafarar shi,akan abinda yafaru.


Soyayya najeeb da salma suke bugawa tagani ta faɗa(ba halin in fadi🤐).


Mahaifin najeeb da kanshi yasa aka ginawa najeeb danƙareren asibiti nashi nakanshi,sannan akayo order ta kayan ayki daga turai,madu kyau da nagarta,aka ɗauki kwararrun maaikata,sannan akasawa asibitin suna.

Najeesal special hospital.


Najeeb sosai yayi murna,haka salma itama ta tayashi murna sosai.


Sunkaiwa kabeer ziyara,inda najeeb yadunga jin kunyarshi shiko se tsokanarshi yakeyi yana masa dariya.


Rokon shi najeeb yayi akan yanemi transfer zuwa kano,dan abotarsu takoma kamar da,ba musu kabeer ya amince da hakan.


Yau salma da zazzabi ta tashi da ciwon kai  ga kasala,se shagwaba takewa najeeb shikuma duk ya ruɗe.


Gwata yayi,inda gwajin farko,ya hango ciki ɗan wata biyu manne a mararta.


Farincikin dayayi baa magana.


Tundaga wannan lokaci daga salma har najeeb basu da magana seta cikin,siyayyar haihuwa ba irin wacce basuba,se jiran baby.


Lokacin haihuwa nayi,Allah yasauki salma lafiya abisa taimakon najeeb,tasamu ɗa namiji,me kama da ubansa.


Tun a asibiti,najeeb yamasa huɗuba da sunan kabeer,suna kiranshi,mujaheed.


Ranar suna anyi bidiri birede,inda najeeb ya yanka shanu biyu da raguna biyu amatsayin hakika.


Kabeer ko liyafa yashirya tagani ta faɗa,a niima hotel,wacce besamu yamusu ta aureba ita yashirya a ranar sunan.


Fadin kyau da najeeb da salma sukayi yazama kauyanci,anci ansha,angodema Allah.


Su feefee ma baa barsu abaya ba,sunzo suna.


Atawagar yan suna,harda  members na surbajo hausa novels groups,bawanda bezoba.


Haka rayuwa taci gaba da tafiya,tuni najeeb yaje A,b,u aka gyara takardun salma,aka bata shaidar ta kammala degree dinta,inda tafara ayki a asibitin najeeb din.


Alhajee mahaifin najeeb yasamu wata matar me tsoron Allah ya aura suna zaune lafiya.


Iyayen salma ko saudiyya najeeb yabiya musu harda salma dashi,suka tafi,suka dawo


Albarka kullum cikin samusu ita iyayensu sukeyi.


Sahabi ma ya angwance da amaryarsa me suna laila,se fatan,Allah yabasu zaman lafiya.


Salma da najeeb sun ɗinke sun zama tsintsiya maɗaurinki daya,babu mejin kansu,yayinda dukansu suke alfahari da junansu.


*ALHAMDULILLAHI,ANAN NAKAWO KARSHEN WANNAN LITTAFIN,LADAN DAKE CIKI ALLAH YABANI,KUSKUREN DANAYI ALLAH KA YAFEMIN*


*READERS NA GODE DA BANI LOKACINKU DA KUKAYI,ALLAH YASAKA DA ALKHAIRI*


*LABARIN ME TSAYINE,AMMAN NAGAJARCESHINE,SABIDA SAUƘAƘAWA,NASU BURIN CIN MUTUNCINA DAUKAR ALHAKINA*


*KUGAFARCENI,BOTH READERS AND WRITERS,IN HAR DA RABON SURBAJO ZATA CIGABA DA NOVELS,ZAKUGA TACI GABA,IN KUMA TA DENA KENAN KUYAFEMIN*


*HAR ABADA INA ALFAHARI,DA LITTAFIN UMMU AYMANA,INASONSHI,INA ƘAUNARSHI,BANA DANASANIN RUBUTASHI,KO KADAN,HAKA SHIMA YAR BAUTAR KASA,INA ALFAHARI DASU,*


*ALLAH YASA WANDA NAYI DOMINSU SUN DAUKI DARUSSAN DAKE CIKIN LITTATTAFAN,AMEEN*


*NA BARKU CIKIN AMINCI,ALLAH YASADAMU CIKIN AMINCINSA,HAR ABADA INA SONKU MASOYANA*


*MISS YOU ALL MY FANS😍*


*SURBAJO FOR LIFE*.



Compiled by Princess Aysha Muhammad

Copied by Umar Dalha

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *