Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Sunday, January 24, 2021

DA SANNU COMPLETE SABBIN HAUSA NOVELS

adsense here

DA SANNU COMPLETE SABBIN HAUSA NOVELS

        GODIYA



Godiya ta tabbata ga Allah ubangijin halitta daya bani damar Rubuta wannan littafi,  tsirada aminci su tabbata ga Shugaban'mu Annabi Muhammadu (S.A.W)

Da iyalan gidan sa Da Sahabbansa, da wayanda suka bashi gaskiya har zuwa Ranan Alkiyama  Amin.



        

       SADAUKARWA



Na sadaukar da wannan littafin ga iyayena "Alh Umar Muhammad da "Hajiya Lauratu nagode kwarai da tarbiyar da kukai Mani ubangiji yasa kugama da  duniya Lafia Amin.


Wannan labarin kagaggene bawai yafaru da gaske bane, saidai nayi shine akan irin "mutanan nan masu saurin yanke hukunci batare da bincikeba, nasama wannan labarin Nawa suna DA SANNU dafatan zaya fadakar.



Sannan wannan labarin ina kirane ga masu kudi dasuyi koyi da halin irin Na Alh Ya'u Na KaKa, suka sance masu taimakama talakawa kamar yanda wannan bawan ALLAH yayi acikin wannan littafin

Wannan shine littafina' nafarko inafata zaya fadakar daku,kuma ban rubuta shi doncin zarafin wani ko wata KO kuma wasuba, saboda haka duk Wanda yaga halayya ko kuma suna sundace dashi to arashine ba dashi akeba nagode.





_edited by Zainuddeen Zain_







-------------------------------------------

® *~PEN WRITERS ASSOCIATION~*



_PEN: THE STRONGEST WEAPON_

-------------------------------------------




Bismillahirramanirhim




Mama! Mama!! Mama!!! Ina mama kam tayi nisa domin kuwa ko motsi batayi.



Tafdijam! Babbar magana... wai Dan sanda ya ga gawar soja. 



Ai kuwa tuni Abdul-jabbar ya yi kukan kura ya chakumi wuyan Dan siririn nurse da sai rabon idanu yakeyi a firgice, yana cewa "ai wallahi tun da Kayi sanadiyar mutuwar maihaifiyata, to kai ma sai nayi Ajalinka. Dan iska kawai sai na kashe ka".



ko kafin jama'a su kawoma Dan siririn nurse dinnan agaji, tuni ya fara jin kamshin mutuwa, domin kuwa  bakaramin, shake sa Abdul-jabbar ya yi ba.



Dakyar wasu nurses su hudu suka kwache shi daga hannunsa, daya daga cikinsu ne yace "lafia me ke faruwa ne cayode?"




Dan siririn nurse da aka kira da suna Cayode bai samu damar bayar da amsa ba kasancewar yanachan yana kokarin nemo numfashinsa da yake Neman kubucewa daga gareshi.



Abdul-jabbar ne cikin tsananin bacin rai yace "ka duba abun da ya yi Mani", ya nuna musu in da Mama take kwance magashiyyatan




 Da sauri suka hada baki suka ce "subhanallahi! Ai mu bamu kula ba sam, ya akayi haka ta faru?"



 

Gaba dayansu suka nufi in da take kwance. Abdul-jabbar cikin kidimewa bayan ya daga hannunta ya juyo ya kalle wadanda sukayiwo ca a kanta, yace "ta mutu"

💞💞💐💐💞NU"

💐💐💞💞N

💞💞💐N

💐💐SA

💞DA                   💞

                    Page💐2

💞DA"                 💞

💐💐SA

💞💞💐N

💐💐💞💞N

💞💞💐💐💞NU"




               NA





💐 *MEENAT UMAR FARUQ* 💐




```Dedicated to my lovely sisters may aljannah be your final destination with other Muslims ummah, Ameen.```







_edited by Zainuddeen Zain_






-------------------------------------------

*~PEN WRITERS ASSOCIATION~*



_PEN: THE STRONGEST WEAPON_

------------------------------------------




_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_






✍🏾


  




Abdul-jabbar ya zabura tareda cewa "ta mutu KO"?



Ya nufi Cayode yace ba fa zan yardaba, har ya fara cakumar wuyansa da niyyar ya kai masa wawan naushi, sai wani yace "Kai Ina fa ganin kamar bata mutu ba".




"Musa yi sauri ka kira doctor" daya daga cikinsu ya fada.




Da sauri Musa ya nufi office din har da sassarfa, sai ga su tareda doctor, da sauri yace "A'uzubillahi! Me yasa me ta"?  Sukace "wallahi bamusani ba", daya daga cikinsu yace ina ganin kamar ta mutu fa", doctor yace "what"?




 Da sauri ya tsuguna gabanta tareda daga hannunta, yai shiru, cen ya mike yace "Musa Kai maza  ka dauko(stretcher) ayi maza a kaita emergency room, oya please hurry up"



Yace "OK sir", da sauri yaje ya dauko, har da hadawa da gudu suka nufi emergency room da ita, doctor na bin su a baya shima Abdul-jabbar yana biye da su, yace "don Allah doctor hide nothing from me, is she dea"?




Ba tareda doctor ya kalleshiba yace "no bata mutu ba", a dai dai lokacin da suka isa emergency room din, har doctor zaya shige room din sai ya juyo, ya dafa kafadar Abdul-jabbar yace "don't worry we will do the best we can to see her alive"  yace "OK", da sauri doctor  ya shige room din.




Yabar Abdul-jabbar tsaye cikin tsananin tashin hankali da tunani, a ransa kuwa cewa yake "shin idan har  Mama ta mutu yaya zaiyi"?




Ji yayi gabansa ya fadi, da sauri ya furta "innalillahi wa'inailaihi raji'un!", yace "ya ubangiji ka ba Mamata lafiya Ameen".




Ji yake kirjinsa yana mashi zafi kansa sai sarawa yake, abubuwa sunyi mashi yawa zucci-zucci sai kai da komowa sukeyi a kansa. Ya kasa me ke yi masa dadi,ga matsalar Humaira Wacce kanta ne ya dawo Nigeria, Ga shi tun bai je ga warware matsar ba sai kuma ga wata ta bullo, duk ya rame yayi fayau dashi kamar yayi shekara yanayin jinya,

Shiru tsawon wani lokaci yana tunani, a ransa sai ya saka wannan ya kulla wanchan.




Cen sai ga doctor  ya fito,

kafin doctor ya karaso gurin, Abdul-jabbar ya kare mishi kallo, Dogo ne yanada kiba kadan Wanda takarama tsayinsa kyau, wankan tarwada ne bai cika dariya ba yana saye da farar T-shirt me dogon hannu da bakin wando hannun sa yana rike da  lab court, Yai ma Abdul-jabbar nuni da hannu alamar ya biyo shi da sauri, yabi bayanshi zuwa office din, mai girima ne an shinfide shi da carpet,  akwai Kujeru masu laushi guda biyar da suka kewaye office din, sai wasu kananan kujeru dake gefe, table din me girmane cike yake da takardu,

Akwai laptop akai sai kuma wani Dan karamin katako me dauke da sunan shi.




Ya kalli Abdul-jabbar tareda zare dan karamin glass din dake manne a ldonshi yace "Bissimilla have a sit,"

Abdul-jabbar  yazauna a hankali, tareda karanta Dan Karamin katakon Da akayima rubuta da manyan baki kamar haka,    DOCTOR I. S. G.  Ya tsurama Abdul-jabbar ido yace "munsamu ta farfado saidai nayi Mata alluran bacci saboda tadan samu Hutu,  nan da awa daya zata  farfado normal insha Allahu kar ka samu damuwa kaji KO, Saidai  wane irin abu ne kai mata Wanda ya sa ta tsananin firgici, har ya sa ta tayi dogon suma haka?"  

A dai-dai wannan lokacin ne aka turo kofa  aka shigo office din, Dan siririn nurse din nan ne, hannunshi rike da (files) suka juya gaba daya suna kallonshi.

Yayin da Abdul-jabbar yake yi masa kallon tsana, shi kuma doctor kallon tambaya yakeyi masa, Cikin bacin rai Abdul-jabbar yace "wannan Dan iskan shi ne sanadin faruwar komai", doctor yace "kamar ya fa"?




"Muna tsaye muna jiran Result sai ga shi ya kawo yace sai sakamako yanuna cewa ina dauke da kwayoyin cutar nan me karya garkuwan jiki,

wai kanjamau shi ne ta fadi ta suma".




Doctor yace "what"?




Eh! Haka ya fada,

Yakalli Cayode da yai tsuru-tsuru da idanu kamar makaryaci.




Cikin tsananin takaici doctor yace "are you stupid 

Shi ne joy chukuma"? Yayi tsuru da ido ba tareda ya bada amsar tambayar da akai masa ba, 

Yadaka masa tsawa "Ina magana kayi mini shuru". Ya kalli Abdul-jabbar yace "kai ba sunan ka Abdul-jabbar 

Ahmed ba"?



Ya ce "eh! Sunana kenan", ya kara kallon Cayode yace "ba nace ne ka kira shi ba Shi ne kaje Kai abun da ban sa ka ba ko? Saboda tsabar iskanci salon kabatawa mutane aiki ko"? Cayode zai yi magana doctor yace "shut up you stupid, and give me the files"ya mika masa hannu alamar ya bashi files din, Cayode ya mika masa ya karba yace "oya get out of my office, mahaukaci kawai", cikin sauri ya fita tareda cewa "sorry sir".




Abdul-jabbar ya bishi da harara yace "banza kawai Wanda baisan Aikinsa ba",

Doctor ya maida hankalinsa ga Abdul-jabbar yace "don Allah Kayi hakuri, wannan ba shi ne result din ka ba sakarci ne kawai irin Na Cayode, nace masa ne fa ya kiraka, Sha-sha-sha ne aikin da aka sashi daban Wanda yaje yayi daban,  please sorry".




Yace "it's OK, dama dai Mamana  nake ji",  "kar ka damu zata farfado ai very soon inshaa Allahu ba tareda wata matsala ba, then, sai abu na biyu, abokina, damuwarka tayi yawa matuka, har tana barazanar haifar maka da ciwon zuciya, Wanda inhar zaka cigaba da sa damuwa acikin ranka to komai yana iya faruwa. Saboda haka ya kamata ka cire komai daga cikin ranka, Yanzu haka ma dole sai na rubuta maka wadan su magunguna Wadanda   za ka samu Relief, saboda condition din da ka ke ciki yanzu.




Ko kadan Abdul-jabbar  bai yi mamakin abin da doctor  I .s. g. yace ba, dama yasan za'ai haka donmin shi a zaton shi ma doctor zaice masa Abdul-jabbar ai zuciyarka ta kumbura sosai saura kiris ta fashe,

Saboda tsananin tunani da damuwa to kuma sai aka samu akasin haka. 

Ya kalli doctor yace "to nagode doctor kwarai da gaske, kuma in Allah ya yarda zan yi kokari nai aiki da abin da kace", yace "OK to Bari na rubuta maka maganin".




Yayi rubutu a takarda ya bashi, ya karba yace "nagode sosai fa, sai kudin Mama nawa zan bayar"?

Doctor  I.s.g yayi murmushi yace "ba abin da za a bayar", "a ah doctor ayi haka"? "Eh! ka bar shi kawai ba komai,"  Abdul-jabbar ya sake yin godiya, A hankali aka turo koda aka shigo doctor ya kalli Wanda ya shigo yace musa ya akayi ne"? "Sir matan nan ce ta farfado", "OK to gani nan zuwa" yace "OK sir"  tare sukafita da Abdul-jabbar.

💞💞💐💐💞NU

💐💐💞💞N

💞💞💐N

💐💐SA

💞DA"

                          💞

                  Page💐3

                           💞


💞"NU

💐💐N

💞💞💐N

💐💐💞💞SA

💞💞💐💐💞DA"






                NA






 💞 *MEENAT UMAR FARUQ* 💐






```This page belongs to my Aunty khadeeja lbrahim Godabe A b u Zaria, pls come back soon we miss youuu```







_edited by Zainudeen Zain_





-------------------------------------------

*~PEN WRITERS ASSOCIATION~*



_PEN: THE STRONGEST WEAPON_

-------------------------------------------




✍🏾




_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_




    

Tana zaune ta zabga uban tagumi sai kace wadda akayiwa mutuwa, gaba dayan su suka karasa wurin doctor, yace "Hajiya kin tashi" tace "umm!"





Abdul-jabbar yace "sannu Mama bata amsaba, saidai tsuramasa idanu da tayi kamar bata taba ganin sa ba.





Ya sake "cewa sannu Mama ya jiki"?




Tayi ajiyar zuciya tareda cire tagumin da tayi, tace "sannu Ina ciwo ne? Ai kai ya kamata Ayiwa sannu ba ni ba, domin kuwa Kai ke dauke da cuta. Yanzu saboda Allah abin da ya kai ka America ke nan"? Nan ta fashe da kuka tana cewa "nikam wallahi da nasan abin da za kaje kayi kenan, tovda ban yar da ka tafi ba, ga shi yanzu ka dauko wa kanka cutar da batada magani. kuma ka sani sarai ita wannan cutar in har takama Mutum to lahira ne direct ba tsayawa, amma shi ne ka kwasowa kanka saboda kasan koka Mutu ba kada hasara KO"?  ta sake fashewa da wani sabon kukan"




Doctor yace "kwantar da hankali Hajiya", tace "kyaleni Likita, ai ni wannan yaron ya chuceni", yace "Hajiya da kin saurareni kiji abin da zamfada miki"




Ta fyace majina da gefen zani tareda share hawaye, tace "Ina saurarenka". Cikin shesshekar kuka.

Yace "kina ji ko"?



Ta kada Kai, yaci gaba da cewa wannan ba result din shi ba ne.



Akasi aka samu amma shi baya daukeda wannan cutar". 




Ta daga Kai da sauri ta kalli doctor tace "a ah Likita kar fa ka yaudareni kar ka kuskura  Kayimani karya"


 


Yace "Allah Hajiya da gaske nakeyi ai ba zanyi miki karya ba"




Tace "to ya akayi ya rame yayi baki? Na tabbata domin  ba kasan shi ba ne kafin ya tafi shi yasa, amma ai ba haka yake ba".




Yace "zazzabi ke damun sa da ciwon Kai shi ne ya sashi ya rame" (ya fada Mata haka ne saboda hankalinta ya kwanta domin idan ya fada Mata gaskiya zata koma rikicewa ne).



Da kyar ya samu ta yarda sannan ta sauko daga kan gado, ta kalli  Abdul-jabbar tace "Allah ya rufa maka asiri da yanzu sunan ka gawa".




Ta mayar da dubanta ga doctor tace "to ka bashi magani"?  Yace "eh! Na rubuta masa ya siya", tace "to madallah Likita mun gode kwarai DA gaske".




Shikam Abdul-jabbar bai ce komai ba saboda tsananin mamaki, aranshi kuma fadi yake "Ashe Mama tana sonshi haka?

Ah! tana sonka mana ga shi ta nuna damuwarta a kanka,

Daga ance kana dauke da cutar H.I.V duk ta rikice".

Yayi ajiyar zuciya a hankali, hakan yasa yaji  sanyi a ranshi yau Mama ta nuna masa kulawa ya saki sanyayyan murmushi.




Tace "to ai sai mu tafi ko"?  Yace "to", suka fito doctor ya kara jaddadawa Abdul-jabbar kan yayi kokari ya sayi magunguna, yace "ai zan siya insha Allahu".




Mama tace "Ya sunan Likita ne"? Yayi murmushi yace "sunana Ibrahim", tace   "A ah Ashe sunan Babana ne to mungode sosai Dattijon kirki".




Yace "Lah! ai ba komai sukayi musabaha da Abdul-jabbar  yace sai anjima, mun gode fa doctor" yace "nima nagode", suka tafi.




Sunkusan fita daga harabar asibitin sai ga Cayode, Abdul-jabbar ya watsa masa harara.




Da sauri Cayode ya matsa gudun kada Abdul-jabbar ya sake shakesa, ita kam Mama bata kula ba har sukafita.




Yabi bayansu da kallo yace "Kai Ka ga Mutum sai karfin tsiya kamar Zaki?, yanzu ba domin su Musa ba ai da tuni na zama Dan gida a barzahu".

Yayi kwaf "Kai wannan guy din akwai shegen karfi,

a tafi dai Allah ya raka taki gona"

(Su Cayode anji Hausa har da su karin magana).




Mama tace "to yanzu sai mubiya Kasayi maganin KO"?




Yace "Mama ni fa akan sauri KO wallet dina ban dauko ba, tun da kika matsamank sai natashi muntafi"




Tace "to ai kai dinne wallahi kamar Wanda bai san ciwon kansa ba, ba kaga yadda kadawo ba ne shi yasa".




Yayi murmushi yace "to mu tafi idan naje nayi wanka da sallah sai naje (LUFHAT PHARMACY) na siyo tunda suna kawo magunguna masu kyau", tace "to Ai shikenan".




Ya tare musu Dan a-dai-dai-ta sahu yace ya kaisu kurmin mashi me adai-dai-ta yaja suka tafi. 




Koda suka isa gida Abdul-jabbar dakinsa ya nufa, ita kuma Mama ta shiga cikin gida, "assalamu'alaikum", "a ah! Baba Lami Ashe kin zo"? "Wa'alaikumussalamu", eh! Hajiya kun tafi kenan"




Baba mai gadi ne yace mani  maigidana ya dawo, amma Kuma kumfita tareda shi nace to KO lafia"?




"Wallahi maigidan naki ne ya dawo ba lafia, shi ne nace yatashi  mutafi asibi".

💞💞💐💐💞NU"

💐💐💞💞N

💞💞💐N

💐💐SA

💞DA"

                       💞

             Page 💐 4

                      💞


💞DA"

💐💐SA

💞💞💐N

💐💐💞💞N

💞💞💐💐💞NU"





               NA





💞 *MEENAT UMAR FARUQ* 💐






```This page belong to my best friends, Maryam Aliyu Bala Mrs Shehu Maigishiri Minna and Maryam Muhammad Mrs Mamman gas knt```






_edited by Zainuddeen Zain_






 "Tun da na ga alama ba hankali ya ishe shi ba",  Baba Lami tace " rashin isasshen hankali fa, me ya faru ne"? Likita yace "zazzabi ne da ciwon Kai ke damunsa ya ma rubuta ma shi magunguna"




"Allah sarki maigidana yana ina ne yanzu"? Yana dakinsa zai yi wanka ne", "to Allah ya kara sauki" tace "amin".




Ko da ya shiga dakin sai ya gan shi tastas ko'ina an share an goge sai kamshi ke tashi, kamar kantin turare, yayi murmushi yace "Baba Lami kenan Allah dai ya biya ki"




Ya shiga wanka ya dauki tsawon lokaci kafin ya fito, sai da ya gama shirinsa tsaf sannan ya nufi cikin gida, sai faman kamshin turare yake.




Tana zaune tana kallon tashar MBC 2 duk da cewa ba jin abin da ake fada take yi ba, hakan bai hanata maida hankali ga kallon film din da ake yi ba.




Jin kamshin turarensa ya sa ta dago Kai ta kalleshi tareda amsa mishi sallama.

Tace "sannu maigidana ka fita Ashe kuma baka ji dadi ba, to yajiki"?




Yayi murmushi yace "Baba Lami kenan uwargida sarautar Mata ko ankiya bale an yarda, ba fa wani rashin lafia ba ne sosai, zazzabi ne da  ciwon Kai, kuma da zarar na sha magani insha Allahu zansami sauki".




Tace "Kai maigidana ai shi ciwo komai kan-kantar shi to ciwo ne, ba ga shi nan ya sa duk ka rame kayi duhu ba? Kaidai Allah ya raba mu da cuta kowane iri ne". Yac "Amin".




"To ai ke baki sanibane", tace "me kenan fa"? 

Yace "tunaninki naketayi achen shi yasa kika ga na rame" yakai karshen maganar shi da dariya, ita ma dariyar take yi tace "kaidai fadi gaskiyarka na daure"? 

Yace "a sakeni". 



"Kodai kana tunanin Humaira"?



A ransa yace "kamar KO kinsani", amma a fili kuma cewa yayi "ga uwargida wake ta amarya"?

Tace "umm-umm! kodai anata amarya wa ya ke ta uwargida", yace "a ah! Tun da ba a kama amarya ba ai kin ga dole a rike uwargida da kyau KO ya kika ce?




Tace "hmmm! To na yarda kadan amma fa kasan halinku maza, da kunyi amarya to kuma shikenan uwargida ta zama kwandon shara".

 



Ya kyalkyace da  dariya yace "Kai Baba Lami harda wani kwandon shara"? Tace "eh! Haka kuke yi sai kaga anatayiwa uwargida wulakanci".




Yace "a ah! Ni kam ba zanyi haka ba", tace "umh-umh! Fa", Yace "insha Allahu", "to shikenan  Allah yasa haka amin".




Haka nan sukaci gaba da barkwanci har Mama ta fito. 




Yace "ni zamfita zambiya gidan Y.Y.K,  saboda bai san na dawo ba, (abokinsa ne Y.Y.k wato Yusuf Ya'u Na kaka)




Mama tace "au! Dama ba kuyi waya ba"?

Yace "eh! Nayi ta neman line nasa ban samu ba", "to ka gaishe mini da Ummi ai duk bayan kwana biyu-biyu yakan kawota ta yini,

(Ummi diyar Y.Y.K ce sunan mahaifiyarsa ne wato Hajiya Karima) yai murmushi yace "to za ta ji, ya kallo Baba Lami yace "uwargidasss na tafi", A dawo lafia Ina gaida amarya domin dai yau nasan Chan za'ayini ko"?




Yai murmushi yace kin Amince in naje na yini a chan kenan"? "Na Amince tun da dai an dade ba a ga juna ba"




"To kin kyauta an gode miki, zamfada Mata cewa uwargidanta na gaisheta, sannan kuma tace ta bar miki ni, duk yafada yana dariya.



Da Sauri tace "ni"? to bamfadi haka ba nikam ba zambar Mata kai duka ba", 

Ya fita yana dariya Itama dariyan takeyi  hada Mama na taya su.




Da misalin karfe 3:30pm na rana, Humaira ce ke yin wanke-wanke abakin fanfo jikinta ya bata kamar ana kallonta cikin sauri ta kalli bakin kofa, aikuwa sukai ido hudu da mutumin da batai tsammanin ganinshi a wannan lokacin ba, batasan lokacin da ta saki kwanan da ke hannunta ba ta nufi in da yake tsaye, har ta kusa kaiwa gurinsa, ko me ta tuna sai kuma ta ja ta tsaya tayi shuru Chan kuma sai ta fashe da kuka.

💐💐💞💞NU

💞💞💐N

💐💐SA

💞"DA         💞

          page6&8 💐

                     💞   

💞"DA

💐💐SA

💞💞💐N

💐💐💞💞NU



             NA



💞MEENAT💐 UMAR💐 FARUQ💞




 this page belong to All people of kontagora.



---------------------------------------

PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------



✍🏾



only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers




T"ace dakatafi kabarni mana yau shekara kusan hudu sannan kadawo ,


 yakada Kai yace OK shine yabaki damar kibarmani yarinya tafada tarkon wani kato KO? 


To aigashinan ya yaudareta ya cuceta DA sauri ta katseshi dacewa cuta kuma? Yace eh cuta mana idan ba cuta da kuma yaudareba, yaza'ai saida yabari tafara sonshi sannan zaya gudu yabar da gyanbo acikin zuciya, 


domin Na tabbatar haryanzu baza'arasa sauran son shi acikin zuciyartaba.


Yanzu kiduba kiga yadda yarinya takoma duk tarame sobada Allah,

Kuma dakike cewa natafi nabarku shekara hudu, aisanin kankine saida na shekara biyu agidan yari.


 Yace nibaki   kyauta maniba wallahi yarinyar daya kamata ace antakura Mata tayi karatu, amma Sam ba'ayi hakaba saikawai kuka barta tana soyayya  kuka hada,


 takatseshi

 D"a sauri tace  muka hadata dame? Yace da abunda yafi kafin kwakwalwarta mana, tace a ah muba ruwanmu tahada kanta dashidai.


 Yace Kuka hadata dashidai dabaku yardaba aibazata tsaya tasaurari saurayiba, Ita kam umma sai tayi shuru tana saurarenshi batareda tasake cewa komaiba, yanatayi can saiyaja tsaki mtsww.


Ta kalleshi aranta tace wanzami kenan bakaso ajikinka, saikuma tai murmushi abayyane tace daga dawowa kuma saifada? 


Yace haba umman yara yabazanyi fadaba saboda Allah. tace wato kar'abarta sake tsayawa da saurayi kenan KO?


 Yace eh kusan hakadin nakenufi. Au zubamata ido zamuyi muna kallonta bazamu yimata aureba ka kenufi? 


Nagaya miki baza aimata aureba? Aure kam tunda shiya haifeta aidolenta itama tayishi amma aisai'ajira hartakai munzalinyi ko?  


  A"to Inbaka fadiba hakaba to yaza'ai kamar Humaira amatsayinta Na ya mace acekuma baza   A"barta ta tsaya DA saurayiba,


Y"a kalleta ya girgiza Kai Yace Asma'u wai maiyasa ki keyimini hakane nadawo zamufara

 sa'insa dake kenan? kinga indamuke samun matsala dake Inna ce ga yadda za'ayi saikice maniba hakaba, 


 Yacigaba da cewa yaza'ayi ace kamar Humaira tahada Dan taura biyu abaki akema kinsan bazaiyi yuba. Tace kamar yaya Dan 

 taura biyu abaki?   


 Yace yazata hada karatu da kuma soyayya shin karatu

 zatayi KO soyayya? Saiki zaba Mata daya  domin  kuwa kece kika kamata Da hartasamu damar kula samari, saboda haka nan Ina sauraranki zabar Mata daya daga cikin biyu kinjiko? 


Ta"kallesa saitaga kamar ransa yabaci, tayi murmushi tace Abban yara kenan to yaizafi?  Yabata amsa dacewa aibazafi acikin magana ta sai, tace akwai mana ba gashi nan kabata raiba.


Ya" tsura Mata ido cikin bacin rai Yace ya bazan bata raiba Asma'u meyasa zakiyi Mani haka?

Kinsan halinmu sarai bawai bakisaniba,


 baikamata ace kamar Humaira tafara daukar matsalar da namiji ba, common fifteen years  fatake tama Kai shabiyar dinma kuwa? 


Tace batakaiba tukun na saura wata hudu, yace to kinjiba amma kika barta tadauki abunda KO yar shakara talatin saitayi da gaske zata iyamasa,


 To ballan tana Humaira yar sha hudu dawani abu yaja tsaki mtsww, yaci gaba dacewa nidai Asma'u baki kyauta miniba wallahi KO kadan,


Yayi shuru Na tsawon wani lakaci batare daya sakecewa komaiba. Tace to kayi hakuri Abba Humaira nayi kuskure amma insha Allahu haka bazata karafa ruwaba kaji? 


 Aima tundaga wannan yaron bata Kara kula kowani saurayiba, har lokaci baice komaiba, tace naji kayi shuru ko haryanzu fushin kakeyi?


Y"ace a ah bafushi nakeyiba kinsan nibanason abunda zaibatama Addana rai duk sai naji rayuwana yabaci,


T"ace ato kariga kasan halin kayanka da sa'abu cikin rai, Kaga gakawa zuccinka gana karatu sannan kuma gawan nan yaron datasashi arai, gajarabawa badole tarameba, 


dama jibi zasu gama jarabawa idan Allah yakaimu narai lafia. 

Yayi murmushi Yace Amin  Allah sarki Adda Humaira na hakana me sunanta kedason karatu, inaganinma idan jarabawarsu tafito D"a kyau America zankaita  tayi karatuta achan I hope dai tarubu jamb?


Tace eh tarubuta Amma duk makarantun dake kasarnan  Najeriya basuyiba,  


meyasa  zakakaita America kasar masu jajayen kunne kasar dabasuda tarbiyya, meyabaka sha'awa dazaka kaita Chan taikaratu?


Yace saboda inas on tayi karatunta me kyau  cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, 


kuma insha Allahu nasan tarbiyyar damukai Mata bazata zubarba dayardan Allah,

Sannan kuma aigidan ubangidana zata zauna bawai waniguriba, 


kuma bawanda zayata kuramata akwai yarinya agidan tsarartace don Itama natafi shabiyar dinba, zataji dadin zamadasu kwarai da gaske domin basuda matsala wallahi kedai kawai

 kiyimata addu'a. 


T"ace audama Chan katafi Kai zamanka hankalinka akwance Mukuma muna nan duk hankalinmu  atashe, Kai kuma babu abunda yadameka?


Yace umman Adda Humaira meyasa kikemaida hannun agogo bayane? angaya miki nima danake Chan  hankalin nawa akwance take? To barina fadamiki hankali na ba'akwanche yakeba, akoda yaushe hankali na atasheyake saboda bansan halinda kuke cikiba, bantaba kwana nashi batareda nai tunanin kuba, 


 kuma cikin raina akoda yaushe, nima bantaba   zatan tafia wata kasa nabarkuba, Bari kinji nagaya mini yadda akai harnatsin kainan   America agidan yari nahadu da wani Mutum da  matsalasa tai kusan daya datawa,

Yakece mini shikam najiriya kasarsace amma wallahi yagaji da ita, saina tambayesa saboda meyasa yafadi haka?  


Sai"yacemun saboda yawancin mutanan dake cikin ta  macutane azzalumai.

Don haka shikam idan har Allah yasa yafito daga gidan yari lafia, to zayayima kanin mahaifinsa  magana yahadasa dawani abokinsa, datake can America dazama. Hakanan kawai naji nasamu kaina iname cemasa nima inhar dahali to nimazan bishi mutafi tare, domin kuwa nima,


Alokacin naji kasar Tafitamun arai. Harmadai idan natuna cewa ba'asan inda yar'uwata takeba duk sai naji hankali na yakara tashi, domin kuwa nasan banida kowa sai Allah saikuma ku,


 don haka sai kawai nayanke shawarar nabishi mutafi tare saboda nayi imani Allah zaikulamun daku kuma inada tabbacin cewa Malam zaya kuladaku,


Koda muka isa mutumin mesuna Alh jamilu yakarbemu DA mutunci, yakuma Samar mana Aiki munkuma samu alkhairi aciknsa sosai, 


Wanda harna keta aiko sako ta gurinta Alh musa kusan sonawa, Amma sai akoma mundashi waibasu ganeshiba, sai sakon karshene sannan akaganeshi saidai kuma baiyimun yanda naceba, 


domin kuwa cewa nayi yasaimun fili atudun wada yaimun gini amma wai duk fadin garin Kaduna babu filin daza asaimun  saida akatafi garin yola saboda tsabar walakanci irin Na Alh musa,


 Yaja tsaki mtsww ainasan da yola nace agina akaduna. Tace menene laifin Alh musa anan ? 


 hakanan dayayi shine dai-dai haka akeson abokina kwarai yasa abokinsa hanyar gaskiya bata karyaba, 


Abban Humaira lokaci yayi daya kamata kakoma mahaifarka hakanan, komai yaizafi maganinsa Allah yar'uwarka inhartana Raye aduniya Koda shekara nawane inhar Allah yakaddara zaku gamu, tofa bamakawa sai kun gamu idan kuma Allah bai kaddara kugamuba tofa bawanda ya'isa yahadaku.


Y"a kalleta yace nasan da haka Umman Humaira tun bayanzuba, saidai zanzauna ayolane bawai don inasoba, 


domin kuwa sam bazatai mun dadin zamaba Tace hakuri zakai ka kuma daure kazauna hakanan tunda mahaifarkace,


Yace to yana iya tunda shima Malam yace dole saina koma candin dazama, yanzu kifito muje kofar gida kiga motar Dana siya Tana nan waje gurin Malam,


Sannan kuma gobe KO jibi in Allah yasa munaciki masu yawancin rai zantafi Zaria Nagano babana, 


 "Malam kuma yace dole za'asamu wasu daga cikin almajiransa atafidasu Chan yola don susauke Alkur'ani maigirma agidan,


 domin kuwa yace bai kamata ashiga gidan hakanan ba Humaira ce tashiga dakin tareDa sallama  suka asma,


Yai murmushi yace zonan Adda Humaira ta harkingama wanke-wanken kenan? Tazo gefensa tazauna tareda cewa eh nagama, 


Yace to yaya jarabawa ummanku tace jibine zaku gamako? Tace eh to me'ake karantawa? tace Abba medicine  nake karantawa, 


Ban mantaba domin kace abunda kakeson nakaranta kenan, Yace Karatunda kikeyi mewuyane sannan kuma kika hadashi dawani abun maiwuya sosai meyasa kikai haka Humaira? 


Da sauri ta kalleshi tareda cewa Abba wani iri abune nahada dashi mewuya sosai? Yau murmushi yace nifana Fara tambayarki, 


Amma bakibani amsaba sai kema kika tambayeni? To nibari nabaki Amsan taki tambayar inanufin soyayya,Dasauri ta kalli inda umma take, ita kam umma harara tawatsa Mata ahankali ta sunkuyarda Kai kasa batare datake komai ba.  Yace Na tambayeki? 


Tace eh zaki'iya tauna Dan taura biyu abaki? A ah  bazan iyaba?  yace why? Tace Abba gaskiya is two big, Yace good,  ummanku tafadamun abunda duk yafaru. Saboda haka,


A"bunda nakeso dake yanzu shine kirabuda dukan wasu samarin dakikasani,kimaida hankalinki akaratu kinsan inda zankaiki kicigaba da karatunki?


 T"ace a ah to America zankaiki  tai murmushi harsaida wushiryarta yabaiyana , Abba nice zantafi America karatu? Eh ko bakison zuwa ne?


 Lah Abba wallahi inason zuwa, yauwa toshike nan  kinga inhar Allah yakaiki lafia to kimaida hankalinki kan karatu kiyi shi sosai. Inharki kayi yadda nakeso to nima zanyi miki duk abundanc kema kikeso kinajiko? Addan Abba. 


T"ace eh Abba insha Allahu zakasameni maibiyayya akan dukan abunda kace, Yace yauwa Adda Humaira Allah yai muku Albarka yabaku abunda kuke nema Na    alkhairi tace Amin, Abba amma zakudinga zuwa kaida umma Da yah Himu KO?


 Yai murmushi yace karkidamu agidan ubangidana Zaki zauna, akwai yarinya agidan kusan sa'arkice batada matsalar sannan kuma duk lokacinda kikeson ganina zanzo kinjiko ?  


Tace to Abba, to katashi muje kuga motar suka ce to, Sukafita dukansu don ganin motar.


koda Abdul-jabbar ya'isa gidan  Y Y k afalo yatarar dashi zaune shida matarsa Jamila,


 yanaduba wasu takardu ita kuma Tana kallon wani India film, ita kuma ummita kuma Tana kan dan kekenta tana wasa, Yai sallama suka asma Y Y K ya kallesa fuskasa cikeda mamaki, Jamila tace   a ah.

?💐💞💞NU

💞💞💐N

💐💐SA

💞DA"

                💞 

        Page💐5

                💞

💞DA"

💐💐SA

💞💞💐N

💐💐💞💞NU




              NA



💐MEENAT💞 UMAR💞 FARUQ💐





This page belong to my best friend LARAI IBRAHIM RIBAH Dan Fodio university of sokoto.




edited by Zainuddeen zain




-------------------------------------

PEN WRITERS ASSOCIATION



PEN: THE STRONGEST WEAPO

-------------------------------------



✍🏾




only the exquisite and whizkid writers are opportune to be writers




D"a sauri yakarasa wajanta yaca a ah haba Adda ta yahaka kuma bakiyi murnada dawowata bane? 

Ta girgiza Kai alamar   a ah,


Yadago kanta tareda share Mata hawaye yace to menene kuma abun kuka? bagani nadawoba,


 Pls stop crying, kinsan banason ganin hawayanki ko?

Cikin kukan sha'gwaba tace  pls Abba  karka Kara tafia kabarmu  Allah daka tafi munsha wahala sosai.


Y"ace ainadawo kenan babu inda zankara tafia nabarku Ina nan taredaku insha Allahu kinjiko? Tadaga Kai alamar to,


Yace to ya isa hakanan  yasake cewa to kiyi dariya mana naga open teeth din nan dana Dade banganiba,


Aiko ta Saki dariya harsaida wushiryarta din yabaiyana, 

Yace yauwa Humaira Addan Abba kokefa Ina umman kune bangantaba? tace tana nan cikin dakin gwaggo,


To ita gwaggon kumafa?  Taje unguwa OK to Bari nashiga wajan umman taku tace to.


T"ana zaune bakin gado, yayi sallama yashiga sanin muhimmancin sallama yasata amsa,  amma inbadan hakaba dako sallamarsa bazata amsaba.  


A"hankali yakarasa wajanta yacire Mata tagumin zabga, yace umman yara tagumi bayada kyau.


Batace masa komaiba yasake cewa umman yara yanasa meku inafata nasameku lafia?


Malam yafada mini cewa Himu Na yana    A. b. u Zaria KO? 


Aini ba abinda zancewa Malam saidai nace Allah yabiyasa ubangiji yasa Aljannar fiddausice makomarrr, maganar ta tsaya masa sakamakon hawayen daya gani suna sauka afuskarta,


Yace a ah umman yarakuma yahaka kuma?

Yanzu Adda Humaira ta tareni da kuka sannan kuma kema dashi zakitareni? Inagadai ga dukkan alama bakuyi farin cikin dawowa taba kenan KO?


T"ashare hawaye dagefen zaninta, tace yanzu saboda Allah da Annabi abunda kayi ka kyauta maiyasa zakai mana haka?

 

A" lokacin da muke bukatarka akusadamu, A"sannan ne Kai kuma kayi tafiyarka kabarmu,

Haba Abban yara shekara hudu kenan fa,


Sannan kuma don munyi kuka kakecewa bamuyi farin cikin dawowar kaba?


To munji bamuyi farin cikinba Kaga Kai kuma ba saika komaiba, tunda kaima ga dukkan alama ba kayi ninyar dawowabako?


Y"ayi murmushi tareda Kama hannunta yace haba umman yara meyai zafi haka shiba wutaba?


Shin bazakiyi mini uziriba saboda Allah? Kisa nima ba'ason raina natafi nabarkuba dolece tasani yinhaka,

Ya kuma yin murmushi yace habawa uwar yayana bansanki

 dafishiba,


Kinsa meye? Fishin  baiyimiki kyau saikika fito MA'U yafada cikin zolaya yana dariya, 

Cikin jin haushi tace karyayi kyaudin aibawai nayi bane don yayi mini kyau,

Kayi saika ce Kaine  mutumin nafarko da kaddara ta taba fadamawa,


Y"ace to naji amma yanzu dai kiyi hakuri nasan nayi laifi ayafemini kaina bisa wuya, bazan Kara tafia mainisa irin hakaba insha Allahu kinji?

Asma'ul'Husna uwargidan Alh mahamud umman Ibrahim da Aishatul'Humaira, 


T"ayi murmushi tace aifa za'akin baki agurinku maza kamar ganga,


Badole nayi hakuri tunda kasan bayadda zanyi dakai,


Ni'abinda mayake bani mamaki  kai kasani sarai dacewa, kowani bawa da irin kaddaran da Allah kedora masa, 

Allah baitaba dorama bawa abunda yafi karfisaba,


Duk abunda Kaga ubangiji yadorama bawonsa to yasan zaya'iyane shiyasa  masa,

Amma kai duk sai kamanta da haka KO?


Yace amma dai kinsa tunda ban taba shiga irin wannan haliba aidolene najigata KO?


Tace eh yadda baka taba shiga ba hakanan wanima baitaba tunani KO kwatan kwacin shiga irin nakaba,

Amma Allah mai iko dayatashi sai no yasakashi cikin wani halin Wanda yafinakama nesa bakusaba ya kumayi hakuri,


Saboda yasan akwana atashi Allah zayafitar dashi daga cikin wannan halin.


Y"ace to shikenan naji mubar wannan maganar, ubangiji ya yayemana matsalolin Rayuwa, tace to Amin don Darajar Annabi.


Y"ace naca miki Malam yafada mini ankai Himu A.B.U Zaria bakice mini komai ba kinata fishi, 


Sannan naga Adda Humaira tarame shinwa haryanzu mutanan basubarta bane?

Wai shin me mutanan nan suke sone da bazasu barmini  yata tahutaba?


(Yananufin mutanan boye)


T"ayi murmushi tace    a ah baruwan mutane

Indai wayan mutanan ne, dataimakon Allah dana malam sukarabu da'ita, 

  I tace dai dasa Abu cikin rai.

Yace menene yasaka acikin ranta dayasa tarame haka?   


Tace

Komai  maimata sashi cikin rai,

Kasanta da kawazucinka gakuma tadason karatu, 

Sannan kuma gawani yaro dayazo yanasonta itama Tana sonshi sunyi nisa dason juna, tosaikuma dagabaya tagane yanada Mata,


Yace matar tashi I tace zata hanasu cigaba da son junansu?


 Ta"ce eh to kusan hakadin ne tunda had gida tazo tacimini mutunci, takumace Humaira tafita Mata harkar mijinta inba hakaba kuma zata nakasata.


Dasauri yace me Tana haukane? saboda mijinta yace yana son Adda Humaira shine zata nakasata, 


tace eh hatafada,

Yaja tsaki mtss yace saboda yana aurenta shikenan kuma sai akace karya kula wata ya mace ko,


To afadamata namiji mijin mace daya ne?

Waima yar gidan waye datake ikirarin zatanakasa mini Adda Humaira ta,


T"atce wallahi bansan KO yar wayaba, Amma dai daga ganita ba gidan mutunci tafitoba, domin shigarta baikama da yar mutunciba ,


 kamar ba matar aureba wallahi yarinyar tacimun mutunci sosai  Wanda tunda nake ba'ataba yimini irinsaba, 


Toni kuma danaga haka sai nace tafita Mata harkar mijinta tunda bashi kadai bane DA namiji,    saboda dai  nibanason ta shin hankali, 


toshinefa tasama kanta tunani DA"damuwa harda zazzabi tayi, aimayanzu tadanyi dama-dama.

Yana tsaki mts tareda cewa Ai wallahi duk laifinkune dagake har Abba Himu,

Kema kinfi Himu laifi sosai saboda Allah Humaira gudanawa take da harza'abarta ta tsaya da saurayi, (class 2) fanabarta ya kuma cewa ke haryanzu bakisan halinmu  bako?

D"asauri tace halinkufa kace hmmm nikuwa nasanshi domin  kuwa kayimin nagani. 

 Cikin bacin rai yace me nayi miki?

?💐💞💞NU

💞💞💐N

💐💐SA

💞DA           💞

            Page9-12💐

                      💞

💞DA

💐💐SA

💞💞💐N

💐💐💞💞NU




               NA


💞MEENAT💐 💐UMAR💞 FARUQ💐



    

dedicated to my Aunty Hajja from Maiduguri live in Saudi Arabia we miss you so muchhh i greet my little sister's fatima zahra and lsrah





edited by Zanuddeen zain



---------------------------------------

PEN WRITERS ASSOCIATION


 

PEN THE STRONGEST WEAPO

----------------------------------------





✍🏾




only the exquisite and whizkid writers are opportune to be writers





Jamila tace a ah mutanan America saukar yaushe? Yace dazu nadawo wallahi ya maida hankalisa ga ummita datake daga masa hannun alamar ya dauketa,


Yai dariya yace ummita kinsani ne? Jamila tai dariya tareda cewa bata ganka tsaye ba mai daukar ta sutafi yawo.

Ya dauke  yana murmushi yace baby ummita yawo kikeso atafi?

Yadagata sama yana mata wasa Tana bangale baki Tana dariya, Yace mutafi yawo tadaga Kai alamar eh,


Y Y k Yace kajita harda saurin cewa eh KO? to babu inda Zaki yarinya sai danbanzan yawo sai kace taci kafar kare.

Abdul-jabbar yace Mutum da kafarsa sai ahanasa yawo, ah gaskiya abar Mutum yawala.


Y Y K Yace Ai wannan yawon tane yawuce misali in yanzu kabarta tafita tosai kafita nemanta,

Shiyasa nace Mamanta tadaina barinta tanafita tunda kafafunta kaikayi  suke mata.

Hakanan ran nan  tafita ba Wanda yasani saboda baba maigadi yakewaya bayi, 


kuma yamanta bairufe kofaba kawai tafita  ingayamaka mukaita nemanta, bamu gantaba Kai ranan hankalinmu yatashi wallahi sosai  hartsawon wani lokacifa bamu gantaba, sai chan mukaganta abayan layinmu taci kuka takoshi Tana zaune akofar wani gida hartafara gyangyadi sannan muka daukota ,


Abdul-jabbar yace kai! Kai!! Kai!!! ummita Ashe kintaba bachewa tace eh suka kyalkyace DA dariya, Jamila tace aiwajan nan duk jinta take atakure,


Yace ummita kidaina yawo kinji?  tace to idan kinayawo sai anyanke kafafunki kuma shikenan bazaki sake ganin mom and Dad ba ko kinason kidaina ganinsu? 


Tace a ah Daddy Adena KO?  Sukai dariya Yace yauwa my gud gal, Jamila takawo masa Ruwa da lemon juice tareda soyayyen nama ta'ajiye kan table din dake gabanshi, 


T"areda cewa muntsaya sauraran wannan me surutun bankawo maka ruwa ba, 


Y Y K yace kai ni surutunta har mamaki yakeban yarinya sai sai dankaran surutu saikace parrot,Yai murmushi yace aifira mukeyi KO ummita?


Tace eh aje gidan Ajiya ko? tananufin Hajiya "karima , Jamila tace aifa haryanzu yawon dai yana nan Oya tashi muje muyi karatu ki kyale daddy yasha ruwa tace to,


Y"asauketa ta kalleshi tace daddy anyi kalatu  yace to my gud gal kiyi dayawa kinjiko?


 Yace to Daddy ankalanta inji Yace eh, domin kuwa duk yagane gwarancin datakeyi tace ABCDE ta kuma cewa 12345 hartana nunamasa yan yatsunta alamar 5 kenan,

Yatafa Mata tareda cewa eyye gud gal  kin iya amma kikarayi sosai, zamuje gidan Hajiya kuma musiyo sweet aizakisha KO? tace eh , to kiyi karatu dayawa kinji KO? Tace to,Jamila tace nidai mutafi Sarkin surutu


Y"a tsiyaye lemon yasha Y Y K Yace Ina dalta boy? Yace  afilin jirgi muka rabu dashi nace ya tsaya kwana gobe sai yatafi Yace a ah shi bazai tsaya ba.

Ya'ajiye cup din yayi murmushi tareda cewa yah akayine Nawa naga kanata kallona kodai nasake makane?


 Y Y K Yace kwarai kuwa da gaske kasake mun, naga duk karame kayi duhu meya farune kodai kayi rashin lafia ne achan? 


Abdul-jabbar ya girgiza Kai alamar a ah Cikin tsananin mamaki Y Y K Yace yazakace a ah? Alhalin kowa yaganka yaga Wanda bashi da lafia,


Abdul-jabbar yace daga dawowana KO ruwaban shaba "mama tace waibani DA lafia, don karnace mata a ah tace nai Mata karya sai kawai nace Mata eh,

Amma ni lafia ta qalau,


Y Y K Yace OK  naji lafiyarka qalau to amma menene yasaka kayi wannan ramewa  da duhu haka?

Kamar Wanda yatashi jinya Kaga kanka kuwa a mirror?


Abdul-jabbar ya tsurama Y Y k ido Na tsawon wani lokacin batareda Yace komaiba,


Chan Yace Nawa narasa gane awani matsayi nake a gurin my cool, domin kuwa yanzu nasan tana daukata mayaudari ko maciyi Amana tunda banfada Mata cewa nayi aure bako?

Nikam babu abunda zancema wannan yar iskar yarinyar itada uwarta  saidai Allah ya'isa tsakanina dazu,

Saboda duk wani abunda yafaru tsakanina DA my cool to sune silar komai,

Nibansan ma ya'akai tasan ina neman my cool ba, ban kuma San ubanda yanuna Mata gidan suba DA hartasamu damar zuwa taci musu mutunci,

Saboda haka don Allah katashi muje karakani nabata hakuri,


Domin Nikam Ina Matukar son mesanyina inayimata son Dani kaina basan iyakarsaba,

Wanda inaji ajikina muddun narasata to bansan yadda Rayuwata zata kasanceba.

Don haka katashi mutafi kajiko Nawa? Yafada fuskarshi cike DA tausayin kansa,


Shikam Y Y K tunda Abdul-jabbar yafara magana gabansa kefaduwa, (Aransa kuwa fadi yake wato angudu ba'atsiraba kenan abunda yake gudu shine keshirin faruwa,)


A hankali ya kalli Abdul-jabbar din duk sai yabashi tausayi, aransa yake cewa Yace lafiar sa qalau Alhalin kuma yana dauke DA babbar cuta maiwuyar magani,


Domin kuwa SO babbar cuta ne tabbas SON "Humaira Yai masa mugun kamu, yaki fadamasa ne don karya shiga wani hali, amma kuma duk dahaka saida yashiga.

Ya katsemasa zanchan zuci datakeyi dacewa Nawa tashi mana mutafi,


A"hankali Y  Y K Yatashi jikinsa asanyaye hannun shi rikeda takardu yanufi ciki,

Akangado yajefa takardun yafara safa DA marwa,


 Jamila kallesa tace baban ummita meke faruwa meyasami "Abdul-jabbar din naga yarame ko bashida lafia ne? 

Y"a tsura masa ido tareda cewa maman ummita Nawa baida lafia, tace maiyake damunsa? 


Yace abunda yake damunsa yanada wuyar magani,

Tazaro ido alamar tsoro tace wace irin cuta ce haka mewuyar magani? 


 Yace "SO"yanada wuyar magani matukar bakasamu abunda kake Soba

Maganinsa daya shine hakuri,


Amma narasa ta yadda zanfahimtar DA Nawa" yagane cewar "Humaira kam tai masa nisa saidai Yai hakuri,

Saboda haka fadamun maiye abunyi maman ummita Ina mafuta?

Domin kuwa Yace saina tashi munje natayashi bata hakuri,


Kinsan abunda Yace min kuwa? Tace a ah Yace muddun yarasata "Humaira to shikam baisan ya rayuwarsa zata kasanceba,

D"on haka fadamun yazanyi?


Jamila tadafe kirji tareda cewa munshiga uku yanzu kafada masa ne cewa Humaira suntashi kaikuma ba kasan inda sukako mana?

Yace banfada masa komaiba,


  tace toh"

 yanzu kaje kutafi in kuka aikai- yaro yakirata akace muku bata nan suntashi, nasan zai tambayeka mai yasa baka fadama saba, Kaga sai kace kayi hakane saboda karya shiga wani hali, saikaji maizai cemaka,


Y"ai ajiyar zuciya Yace kinaganin hakan shine mafita?


T"ace kwarai kuwa saboda masu Karin magana sunche zuwada Kai yafi sako,  Kaga idanyagani da ido sa zaifi yarda akan kafada masa, duk dadai nasan bazai karyata kana koya kagani?


Yace to shikenan Bari mutafi sai mundawo kenan tace to adawo lafia Yace Allah yasa yafita.



💞💐LUFHAT ce 💞💐

💐💐💞💞NU

💞💞💐N

💐💐SA          

 💞DA

                  💞

       Page13-15💐

                  💞

💞DA

💐💐SA

💞💞💐N

💐💐💞💞NU


             NA 


💞MEENAT💐 💐UMAR💞 FARUQ💐




-----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION 



PEN THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------




only the exquisite

and whizkid writers are opportune to be pen writers





✍🏾






Y Y K ne yake Jan motar yayida Abdul-jabbar kegefensa, Yace aika Nawa baka sani ba? 


Yace inasondai nasani yanzu, Yace Mama takwasheni zuwa wani private hospital   adubani tunda wai nibansan ciwon Kainaba,

Infadamaka koda mukaje munsamu ganin doctor munajiran Result, nan yasanar dashi abunda yafaru tsakanisa DA Nurse kayode.


Y  Y K Yace amma dai wannan baisan kan aikinsa bako? Abdul-jabbar yaja tsaki mtsww tareda cewa yaushe fa sai iskanci kawai yasani,


Y Y k kalleshi Yace aikama iskan cinka yawane dashi ba yanzu Na tambaye cewa bakada lafia ne, amma sai kace waikai lafiyarka qalau. 


Yai murmushi yace Nawa kenan karka samu damuwa bawani rashin lafia bane sosai, zazzabi ne da kuma ciwon Kai  aima doctor yarubuta mun magani danasha Zan warware in sha Allahu, 

Kuma danaga my cool zakaga nakoma normal maisanyina aikagane KO? yafada yadaga masa gira tareda yin dariya.


Y Y k ya hararesa Yace abunda zakace kenan tunanin "Humaira ne yasaka duk karame kayi duhu, karka wani lakawa zazzabi da ciwon kai, kaibaka kankabane shiyasa wallahi duk kayi wani iri sai kace bakai ba, 

Nidai abunda nakeso dakai karinga daukar komai dasauki kadaina daukar abuda zafi.

Abdul-jabbar ya kada Kai Yace Nawa kenan bazaka ganeba neshiyasa amma bakomai mutafi kawai,


T"saye suke suna jiran yaron dasuka aika

Chan sai gashi yafito daga gidan,  yana yarwakarsa.

Koda yakarasa gurinsu sai Yace ance waibabu "Humaira anan gidan,

 

Abdul-jabbar ya watsama yaron harara Yace kufa yaran nan wani lokacin kiwiyar tsiyane gareku,

Yaza kace nan gidan babu "Humaira? Yace Allah kuwa haka akacemun,

Yace toh" munji yimaza katafi mungode,


 Shikam yaro yai tafiyarsa.

Yaja tsaki mtsww Yace Nawa Kai kaji wannan yaronko? kilama a zaure ya tsaya yadawo yacewa mutane wai babu "Humaira agidan,

Ya kuma cewa shegiyar kiwiyace kedamun wasu yaran wallahi, Shidai Y Y k ummh kawai Yace


Kai! Kai!! Kai!!! Yakira wani yaro dayake kokari wucewa tagabasu, yaron Yace gani, Yace don Allah kashiga gidan Chan kace ana sallama da "Humaira kaji KO?  Yace to.


Shuru Chan saiga yaron yafito wani saurayi Dan kimanin shekara shabiyar yana biyedashi abaya, suna karasowa gurinsu sai kawai wannan saurayin Yace habawa malamai  wannan wani irin abune haka saboda Allah da Annnbi?

Saunawa za'afada muku cewa babu wata "Humaira anan gidan iye? 

Ance babu ankuma cewa babu amma bakuyar daba, shi in akwai za'aboye tane? 


Ya kalli Y Y k Yace tareda nunasa da yatsa Yace kaidai mutumin nan kacika dan banzan naci, saunawa zanfada maka? kazo ka kuma zuwa Kai kanama tazuwa, 

N"ace maka maigidan yatadasu tunda basubiyan kudin haya ka kuma  tambayeni cewa ina suka koma nace maka bansaniba! bansaniba!! Tunda ban sansuba, 

Amma kuma bakajiba shine yaukuma kasake zuwako? 

 Toh" yakake San nayi maka saboda Allah iye?


Shikam Abdul-jabbar tunda wannan saurayin yafara magana yayi mutuwar tsaye,  tareda zubamasa idanu tamkar yaga wata sabuwar halitta wace babil Adamuba  domin kuwa bai fahinci abunda saurayin yake fadaba,


Y Y K ya katseshi dacewa toh" Malam ya isahaka nan munji mun kuma gode Karka dokemu, domin naga kiris yarage kado  kemu saboda munzo gidanku Neman "Humaira KO?


To kasa ido kagani  daga yau daga Rana irin ta yau bazamu kuma zuwa Neman "Humaira gidan kuba insha Allahu, ballan Tana kasamu damar fadamana maganar DA taimaka dadi kaji KO?.


 Saurayin zai kumayin magana sai Y Y k Yace Jinan Malam don Allah kayi tafiyar NA nace munji kodole ne saika kasake maimai tawa iye?

Saurayi yatafi yana gunguni tareda cewa kada Allah yasa kujimana, kawai kunwani damun mutane dawata "Humaira Humaira sai kace wata yar gwal, ba "Humaira ba kodai Harawace kune kukasanta bamuba.


Abdul-jabbar yadawo DA dubanshi kanY Y K Wanda shima idonsa nakan Abdul-jabbar din,


D"akyar ya iyabude bakinsa Yace Nawa wai meke faruwa ne?

Saboda Ban fahimci abunda wannan  guy din yakefadaba, 


 Y Y K Yace mushiga daga cikin mota zanfada maka abunda  kefaruwa.

Baiyi musuba yabude mota daker ya'iyadaga kafafunsa yashiga saboda nauyin DA sukai masa, 


Y Y K Yasanar dashi duk abunda yafaru harzuwan dayake tayi ancewa batanan, yaci gaba dacewa ninasan Tana nan tadai kifito wane kawai zuwan kashe danyi shine akace Wanda akacemun wai ai "Humaira suntashi,

NA" girgiza kwarai da gaske domin kuwa bantaba tunani cewa gidan dasuke ciki nahaya neba, sai a wannan Rana nayi iya bincikena don nagane inda suka koma amma Allah baisana ganeba,


 Nayi tunanin nasanar dakai abunda kefaruwa.

To kuma sai natuna in harna nafada maka abunda kenan to kana iya shiga wani hali, domin kuwa nasan halinka sarai dasaka abu Cikin rai, don haka sai kawai nace Bari in barshi harka dawo sai musan abunyi.


T"urkashi babbar magana wai dansanda yaga gawar soja, tashin hankali Wanda ba'asamashi Rana,

To shine yafaru da Abdul-jabbar domin

 kuwa jiyayi kansa yana sarawa gawani daci dayaji bakinsa yayi,

Y Y k yadafa kafadarsa yace Nawa I hope kafahimci abunda nafada kuwa?

Ya kallesa DA idanuwansa dasuka kada sukai jajir kamar anwatsa masa barkono,


Y"ace lallai nayi zurfi Cikin SON abunda narasa, saudayawa RAI yakan kwadaitu dawani BURI wanda  yake ganin shine hanya daya TAK da rayuwa zata gudana Cikin kwanciyar hankali da NUTSUWA, amma sai Kaga Cikin Dan kankanin taki Mutum yarasa wannan abun to yaya kenan ZAIYI?


Y Y K Yace sai yayi hakuri yabarma Allah komai domin kuwa shike maganin kowani irin matsala a rayuwa,

Ya girgiza Kai Yace gaskiya ne yanzu shikenan narasa "Humaira maisanyina kenan? Yace a ah wayafa damaka cewa karasa ta?

Insha Allahu indai "Humaira rabon kace to zamusan inda suka koma, aishi bawa bayataba cire tsammani Daga Rahamar ubangiji,

Saboda haka nan abunda nakeso dakai yanzu shine ka kwantar DA hankalinka kacire komai a zuciyarka,


Don Allah kada kajama kanka wata cuta, dubi dai yanzu yanda kakoma sai kace Wanda ya shekara yana jinya, please kamai da komai ba komai ba kuma zamuci gabada binciken in da suka kuma dayardan Allah za muganta kajiko?

B"atare daya kalli Y Y K Yace muje kawai, 

Yace ok yanzu LUFHAT PHARMACY mukanufa don kasayi maganin KO?  Yace a ah gida zaka kaini, 


Yace bangane gida zankai kaba to shi maganin kumafa? Yace nafasa siya, Cikin matsananci  mamaki Yace  a ah nifa banganeba kanabufi baza kasha maganin ba kenan? Yace eh haka Na kenufi,


 Cikin bacin rai Y  Y K Yace wai mai yasa kake yin hakane? Kana nufin zaka zauna daciwo ajikin ka? shin wai anfadamaka SO" haukane?

Ko kuma Kai kadai ne mutumin dayafara soyayya a duniya dazaka wani rikicewa mutane,

Toh" Bari kaji ingaya maka kafin Kai dubunka sunyi dabasu samu abunda suke soba sukai hakuri toh" ballantana Kai, 


Tsaya nan ka kashe kanka abanza awofi "Tana can kilama tamanta dawani Abdul-jabbar, tasamu wani Kai kana nan kana tunanin banza DA wofi don hak!


Yadoka masa wani uban lhun daya sashi Yai shuru,  yace Yusuf kakaini gida inzaka kaini idan kuma baza kakainiba to sai nafita maka daga mota,


Y Y K yaja tsaki mtsww tareda cewa a ah tsaya don Allah Malam kar kafasa mun dodon kunne , yaja motar suka tafi yana Dada cewa oho dai Kai kasani niba abunda ya dameni,

 

Y Y K baigama yin parking ba Abdul-jabbar, yabude Marfin motar yafita yamaida marfin dakarfi yarufe jikake gaffff!!!


Y Y K yabi bayansa DA kallo daker yakedaga kafafunsa Yana  tafita yana hada hanya, yatabe baki tareda cewa Allah Yai maka sauki yaja motar shi Yai gaba.

Ta kofar baya yashiga daki batareda kowa yasan shigarsaba, yazube kangado jabar tamkar anzubar dakayan wanki, yadafe kansa sakamakon sarawar dayaji Yai masa,


Hakanan kuma yaji  kirjinsa yana harbawa DA Sauri DA Sauri, yasa hannu da Sauri yadafe kirjin tareda cewa washhhhh. Saikuma yaga dakin yana juya masa A"hankali yarufe idosa daga nan kuma baisake sanin inda yakeba.


To adai-dai wannan lokacin ne kuma  Humaira tadauki ruwa abokiti daniyar tayi  wanka, shigarta bayike dawuya sai kaji kwachauuuu!! 

Bokitin yakucche ruwan yazube,


 gaba daya jikinta yadauki Rawa yayinda gabanta kedakan uku-uku , 

 umma dake tsaye bakin fanfo tace Lafia meke faruwa?



💞LUFHAT CE💐

💞💞💐💐NU

💐💐💞N

💞💞SA

💐DA            💞

           Page16-19💐

                       💞

💐DA

💞💞SA

💐💐💞N

💞💞💐💐NU


               NA


💐 MEENAT💞 💞UMAR💐 FARUQ💞


  

Dedicated to my Family Allah yakara mana k'aunar juna Amin,


----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION 



PEN: THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------




only exquisite and whizkid writers are opportune to be writers






✍🏾






T"ana tsaye jikinta sai rawa yake yayin da kirjita yaci gaba da bugawa, 


 umma ta leka bayin tana cewa lafia?  Cikin rawar murya tace  ruuh wanh !! yaah zu beeeee!!!

Umma ta tsura Mata ido saka makon ganin datai jikinta  sairawa yakeyi, tace wai Humaira saunawa zanfada miki inzaki shiga bayi kidinga yin Add'du'a? 


Da sauri tace umma wallahi inayi ko yanzuma nayi  basan ya'akaiba kawai naji bokitin ya kubuche mun, 

Tace toh" Allah yakwauta ni miko mun bokitin nazubo miki wani ruwan, ta dauko Tamika Mata har A"lokacin jikinta rawa yake, ta rintse ido tareda dafa kirjinta aranta take fadin innalillahi'wa'inna'ilaihir'raju'un,


Umma tace gashi tabode ido da Sauri tace toh" tareda karban  ruwan, tana wanka tana maimaita Kalmar innalillahi acikin ranta,.


Umma tace toh"Abba "Humaira munga mota Allah yasa Albarka ya kuma kade tsautsayi da hasara, Yace to Amin kuma gobe insha zantafi Zaria yau yakamata natafi toh"amma naga yamma tayi, sannan kuma Malam Yace saidai nabari DA sassafe natafi, idan kuma nadawo mutafi yola akan maganar saukar daza'ayi domin kuwa Malam Yace dawuri zamu koma Chan yola din.

Tace yanzu duk agobe kakaje Zaria kuma kadawo katafi yola?  Yace insha Allahu duk a gobe za'ayi  ai Zaria  kusane saidai ko yola, KO shima aiba'amota zamu tafiba jirgi zamushiga in Allah ya yarda, tace to Allah ya yardan mana ya kuma kaimu goben lafia to Amin, ya mike tsaye tareda cewa Bari na fita waje gurin Malam tace toh"


D"a Sauri tashiga dakin fitowarta daga kwanka kenan, don haka da Sauri DA Sauri tagama shiryawa tana kokarin saka hijab. Umma tace  waishin wannan saurin duk nazuwa Ina ne? Ta kalle ta tareda cewa umma banace miki zanje gidan su HANAH da HALEEH bah,


 Tace yanzu da yamman nan zakije gida jansu?  Cikin sha'gwaba tace umma to aida gidan su Hanah dana Haleeh banisa, tace to Ai shikenan  saikiyi sauriki dawo tunda kinsan bason fitar yamma nikeyiba, to umma Ai bazan dadeba yanzu zakiga nadawo natafi toh" kidawo lafia ki gaishe da Hajiya Hafsatu da Mariya toh" zasuji ungo kudi mota, umma inadashi, to karadai tace toh" nagode tafice tareda cewa sai nadawo adawo lafia Allah yasa,


A ah budurwar kauye sai Ina kuma?   tace Allah Malam indai baka daina ce mun budurwar kauye ba to zance nafasa auran, Yace au toh"kice kinfasa   kigani yarinya idan ban hau buzunaba, saikinzo kina cewa don Allah Malam ka aureni yafadi Cikin zolaya yana dariya, tace wah nicezan rokeka saika aureni?  yace eh Saikin Rokeni, tace a haka zanrokeka Kai duk furfura sai kace narasa maisona? 


 Yace sosai ma kuwa yoh ke aibaki saniba ingaya miki irinmu masu furfura yan matan yanzu sukeso, saikiji suna cewa aini yan tsofaffun nan sun iya rukon aure Dan haka irinsu yansamu Na aura

Ta kyakyale da dariya tace Kayyah!


 Amma duk budurwar data auri tsoho kamar ka gaskiya taci baya,

T"abdijam nikam ina budurwa kamarta bazan auri tsoho ba, tab wane Mutum aini nan dakagan ni saurayi gal aleda Zan aura ba tsohoba irinka Kai duk furfura,  


Abba Yai gyarar murya da Sauri Humaira ta waiga Aikuwa sukai  four eyes dashi , da gudu taruga hanyar kofar gida domin kuwa bata luradashi agurin ba Sam, 


ya kwala Mata Kira Adda! Adda!! Adda!!!, tace na'am zonan, tazo tanarufe fuska da hijab saboda kunya Abba yaji a firarsu da Malam, 

Malam yace yar,nemakai, 


Abba Yace inazakije yanzu da yamma nan Cikin inda-inda tace um- umh dama- dama Malam yai dariya Yace zataje fadamusu kadawo, dariya Abba yayi shima Yace toh" shine za'aje yanzu DA yamma, why note dabaza abari har gobe ba? cikin shagwaba tace Abba please let me go I come back soon, Yace OK amma fakidawo dawuri, tace to tareda cewa Malam Dan tsoho bye saina dawo Yace Allah ya kiyaye tafice da sauri,


Malam Yai murmushi yace shakiyiya yau bazatayi karatun yamma ba kenan, Abba yace a ah waidama tanayin Karatu shine tafita unguwa da yamman nan? 


Yace eh ta nayi, toh" barina kirata tadawo yamike da Sauri, Malam ya dakatar dashi tareda cewa a ah kyale ta kawai aibata wasa da karatu, Bari ka gani bayan sallah isha'i zakaga tazo tauka kasan yanzu hadda takeyi tana kokari sosai, saidai yau kam baza'agane kantaba tunda kadawo to sai tafadama wayannan kawayan Nata, wadan da kullun suna tare sai kace Aluf da Lam sannan hankalinta zai kanta,


 Abba yakoma ya zauna Yai murmushi domin kuwa yaji dadin Abinda Malam yafada, tabbas yasani tanada kokari karatu tunbata Kai hakaba Yace to shikenan Malam tunda kace a kyaleta, sukaci gabada tattaunawa akan al'amuran duniya me cike da abun mamaki da al'ajabi.



A"kofar gidan su Hanah mai'adai-daita yasauketa bayan tabiyasa kudi, saita shiga cikin gidan tareda sallama Hajiya Hafsatu maihaifiyar Hanah ta amsa Mata dacewa maraba da Humaira tace yauwa sannu Hajiya inayini? Lafia qalau yasu "ummaki da "gwaggo Da "Malam? duk suna lafia sunce a gaisheki to madallah ina amsawa, yayanki" dai yana makaranta koh"?  tace eh yana can toh Allah yabada sa'a 

tace Amin,


Hajiya "Hanah tana nan kuwa? Tace ta nan Cikin   hausama kisameta yanzuta tashi nan wurin, tace to tareda hayewa sama.


A hankali ta lallaba tarufe Mata ido, tafara laluben KO wane amma bata ganeba Can sai tajawo hijab dinta takai hancinta D"a Sauri tace Humeeh tasakar Mata ido suka fada kangado suna kyalkyala dariya Humaira tace yah akai kika ganeni? Tace kamshinki kawai naji naganeki,


 Tazaro ido alamar mamaki hada wani kamshi nakeyi daban Wanda yasa'ake saurin ganeni dashi? Cikin zolaya Hanah tace.     "eh mana" (kasan cewar sarar dasuke fadakenan in sukai magana) kinsan special dinki yariga ya bataki da kamshinsa me shiga rai takai karshan maganar dayin dariya,


 Harara ta watsa mata tare da cewa banso iskanci zakifara KO? Cikin dariya kasa- kasa tace sorry me wasafa nake miki, Amma kinsan Allah bazancan wasa ba kamshinki yasa naganeki, tacigaba da cewa toh ya'akayine?  Naganki da yamman nan kuma nasandai bamuda buki yau ko? Domin dai jiya munje munyi karatu balle ince ko school zamutafi, don haka yanzu Ina muka dosa kuma?


 Tayi dariya tace gidan Doctor muka dosa  Hanah tace kin Rama kenan KO?  tace "eh mana" toh" ya kikaji?  tace very cool don haka indai gidan "D" nane am ready to go oya  tashi mutafi,


 Humaira tace  Toh" zakin mazallako wai da daga ciki rokon uban kwabo, inke kinshirya toh"mu bamu shiryaba yar gidan doctor, tace aini nayi zaton kunshirya ne danaji kince can muka dosa, toh" yar iska bamu shiryaba toh" wallahi gara kuyi kushirya inba hakaba kuma intafi nikadai , a haba dai kina iya Kai kanki kenan? Me zaihana tace eh nasanza ki'iya, yanzu kinsan me ne ne? 


 Tace sai kinfada, saka hijab mutafi gidan su Haleeh nazo muku D"a albishir maidadi, tace DA gaske?  tace Allah kuwa toh" tashi mutafi tasaka hijab suka fice,


Haleeh tace yana ganku yanzu badai karatu zamuje bako? Hanah tace a ah kinga wacce tace inzo muzo gurinki waitazo mana da albishir mai dadi, tace ah Haba dai? Allah kuwa toh" feso mana muji man ta special  tafada Tana Mata dariya  Humaira tace nagane abun'naku iskanci ne to nafasa fadin albishir din,


 Haleeh tace tuba mukeyi Addan "Abba A"utan "Umma beben "yah Himu ta Hanah DA Haleeh Dan fadamana kinji? Suka kyalkyale da  D"ariya tareda cewa "eh mana" tace albishirinku? sukace goro fari kalkal, 


Tace "Abba yadawo dazu wani irin ihu su kayi tareda rungumeta suna dariya, tace kadaku karyanifa kuyi ma umma ahasara, Hanah tace wayyo dadi jibi zamuyi Candy "Abba ya dawo yau kice zamu balle bishasha KO mai kikace? Haleeh tace kwarai kuwa da gaske tace kunsan abunda Abba Yace?


 Sukace saikin fada, cewa yayi idan jarabawar mutayi kyau to America zaikaini nayi karatu Na me kyau acan. Suka kuma saika ihu sukace wow ammafa zakifasa taro gaskiya Humeeh kin hadu wallahi , Abba ya birgeki sosai  tace nikuma tawani bangaran abunbai birgeniba, 


Hanah tazaro ido alamar mamaki tace ke koh" saboda menene? tace  saboda zanyi miss dinku dayawa fa kuma zamu koma yola dazama,  dasauri suka hada baki sukace yoh meh? 


tace yola , Cikin sanyin jiki sukace gaskiya zamuyi miss juna sosai amma kuma dasauki tunda akwai Waya mun dinga communicaty ,Halee tace saukinta kenan ma, tasake cewa kunsan Allah ni mamaki nake wai zamuyi candy Sainaga kamar munyi kanana ,Hanah tace me wallahi bamuyi kananaba gawasu nan basuko kaimuba sunayin candy, 


Humeeh tace ah basai mugama karatunmu da sauri ba Haleeh tace eh kumafa hakane, sukaci gaba da tattaunawa akan yanda candy zaya kasance,


Humeeh tace kubari natafi gida Cikin zolaya tace Haleeh   su O oh fatace muyi Sauri mukaita gidan doctor inba hakaba kuma she take herself to him"


 Haleeh tace au hakane?  Hanah tace eh dole naje gidan "D" dina kunsan inaji dashi  sukace  "eh mana" ta  "D D" tareda tafawa  tace  ni kadaice bawata sukai dariya tareda mikewa suka raka Humeeh ta hau adai-daita sahu, sannan kowa tanufi gida tunda tsakanisu banisa.



💞💐LUFHAT CE💞💐

💞💞💐💐"NU

💐💐💞N

💞💞SA

💐"DA             💞

             page20-24💐

                        💞

💞"DA

💐💐SA

💞💞💐N

💐💐💞💞"NU



               NA


💞MEENAT💐 💐UMAR💞 FARUQ💞



This page belong to charming boy Muhammad Bangee's yola, Hey  boy where are you? I have bee looking for you since kasan meh ?nayi miss  shirmenka  sosaifa 😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜missssSsss  boyyyyyyy onceeeee againnnnn.




-----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION



PEN: THE STRONGEST WEAPON

-----------------------------------------




only exquisite and whizkid writers are opportune to be writers






✍🏾






Da misalin 6:00 pm  na yamma suna zaune  kallo suke suna kuma Dan taba fira kadan kadan, sai Baba Lami tace Hajiya wai shin maigidana yadawo kuwa?  tace aibakidade tafita sai naji motsin shigarsa daki kodana leka haryayi bacci, nace to kila hada maganin bacci suka bashi to koshifa? aiyasamu yadan huta tunda kila achan basu samun lokacin bacci, 



Baba Lami tace yoh inazasu samu lokacin bacci wanna aiki nasu kullum suna tsaye kamar hakori, Ai yanzu zasusamu damar hutawa da kyau tunda 

aisungama KO?



Tace yoh inafa sukagama  sundai samu Hutu nadan wani lokacin lallai kam aisuna kokari sosai Mama ta tabe baki tace aiyaga zaya'iyane shiyasa yadau karma kansa wannan Aiki yaro sai shegiyar kafiya, kodayake ai barewa bata gudu danta Yai Rarrafe ko?  Baba Lami tace wannan magana haka take, toh" Ai shikenan Allah yakyau tai murmushi tace Hajiya kenan kedai kamar bakison wannan aiki na megidana,  to kuma Ai naga aikin nasu yanada kyau sosai, 

tace to Allah yabashi sa'a akan dukan abunda yasa gaba tace toh Ameen Addu'ar dayaka Mata kiringayi masa kenan A"matsayinki Na UWA, tace hmmm baba Lami kenan toh" ai kullum inayimasa toh" Allah ya amsa tace Ameen, hakanan suka cigaba dafira har'akakira sallah magrib suka tashi don suyi sallah.


Da misalin 10:30 pm 5nadare Suna Cikin kallo T.V atashar MBC 2 baba Lami hartafara hamma alamar tafara jin bacci, tace Hajiya  maigidana baizo yadauki abincinsa bafa kodai saina Kai masane? gashi hartafara gyangyadi, Tace toh" nima bansan abinda yahana sa zuwa yaci abincinba, baba Lami tace kila duk gajiyarce tahanasa zuwa toh barina tashi nakai masa can dakin nasai,



Assalamu'alaikum maigidana? shuru maigidana shuru babu asma tace a ah maigidana yau wani irin bacci ne haka, shin wai kamayi sallah kuwa?  ta kuma kiransa haryanzu shuru bai amsaba tace  a ah wannan bacci Na lafia ne kuwa? 


 Saita ajiye abincin takoma Cikin gida tana cewa Hajiya wanga bacci DA maigidana yakeyi yau nalafiya ne kuwa? Ina ta tadashi bai tashi ba  wanda  dakakira sa saudaya yatashi amma yau nakirashi yafi akirga bai tashi ba,  


Mama tace a toh"  kirabu dashi mana idan yagaji DA baccin yatashi, tace a ah Hajiya wannan bacci bana akyalesa bane domin ni nagama kamar baya motsi fa,


 Da sauri tace baya motsifa kikace? tace Allah Kuwa zomuje kigansa Cikin hanzari tamike jikinta haryana Rawa tanufi  dakinsa,

 

Tace Kai! Kai!! kai!! harsau uku tunda dama bakiran sunan sa takeyiba, wani irin bacci kakeyi haka ne yau?  ta bubbugasa akafa amma ko motsawa baiyiba tadafe kirji tare da cewa nashiga uku  baya motsi kodai ya Mutu ne? I tama baba Lami duk tarikice tace a ah Hajiya bai mutu ba KO kikira abokinsa "yusufa yazo akaisa asibiti, amma kafin nan barina debo ruwa azuba masa KO suma yayi? dasauri taje tadauko ruwa mesanyi acikin fridge suka yayyafa masa, 



Amma har alokacin kodan yatsansa bai motsaba, tace  Hajiya kira "yusufa  yazo akaisa asibiti da Sauri tace toh takoma Cikin gida tadauko wayarta jikinta sai rawa yakeyi, Da kyar tasamu Y Y K yana  zaune yana kallon labarai  saiyaji wayarsa tana ringing  kodaya daga saiyaga Ashe Mamace, 


Da Sauri yarage volume T.V ya amsa wayar Cikin ladabi haryana dukawa tamkar yana'agabanta, 



Yai sallama tare da cewa sannu mama inayini? Da Sauri tace lafia qalau don Allah Kai maza kazo Dan"uwanka bayada lafia, Zumbur yamike tare Da cewa ya salam!  mama gani nan zuwa yanzun nan,  


Koda ya isa gidan yatarar dasu tsaye chirko -chirko baba Lami sai kuka takeyi, I takam  mama karfihali kawai takeyi yayin da sai salati take tafamayi, aranta kuwa saifadi take Allah dai yasa bamutuwa yayiba,



Yana ganinsa yace lnnalillahi'wa'inna'ilaihir raju'u Allahumma'ajirni'fimusibati'wa'aKlifni'khairan minah,



Mama maiyasa meshi ne?  tace toh wallahi bamusa niba, baikuma tsayawa dogon bincike ba kawai yasun gumesa yafece sukabi bayan sa  yasashi mota yace mama kishiga mutafi tace      a ah baiyajeba kutafi tare Da baba Lami kawai, yace shiga muje baba Lami tace toh bari nadauko hijab, da Sauri yashiga mota yatayar sukanufi asibiti,



Koda suka isa asibiti Da Sauri akateresu, suka nufi emergency room dashi,

Doctor I S G ne akansa yanata kokarin ceto Rayuwarsa, ankwashi awoyi kafin doctor yasamu yafar fado KO shima saida  taimakon  oxygen numfashin sa ketafiya dai dai 

Doctor yazaro hand kacif daga Aljihun labcot dinsa yashare gumin daya tsatsufo  agoshinsa, 

Yaduba agogon hannun sa yaga karfe uku da rabi nadare ya girgiza Kai tare da kallon inda "Abdul-jabbar yake kwance lallai yadafe rabonda yaci karoda matsala irin ta "Abdul-jabbar.


Baba Lami tuntana kuka haryayi shuru bacci nemaya dauketa, shikam Y Y K bai'iya runtsawaba saboda baiga fitowar doctor ba,domin kuwa baisan awani hali amininsa yakeba.

Da Sauri doctor yafito yanufi office din,Cikin sauri Y Y K yabi bayan sa  zuwa office, yace doctor wai meyasami  Dan uwana ne? yace gaskiya Y Y K bazan boyema kaba datake yasan  Y Y K din,  Abokinka yakamu da ciwon zuciya ,

 Zumbur ya mike tare da cewa ciwon zuciya kacefa? yace kwarai da gaske domin kuwa hartafara kumbura,


Sannan DA alama

 abokin nan naka yabada taurin kai  saboda yazo nan nafada masa abunda kedamusa harda magunguna masu kyau narubuta masa yasiya yasha before ciwon Yai worst Amma baiyiba, I don't know why?


Shikam Y Y K mutuwar tsaye yayi ahankali ya zauna meye abunyi yanzu?   

Yace abinyi kenan mubari yadawo hayyacisa tukun Kaga sai'asan yaza'yi,



Yace some times "Abdul-jabbar yanada kafiya wallahi saida nacemasa muje  asai maganin Amma yace shi Sam a ah, 


Please doctor don girman Allah  katai makenu yanda Allah ya taimake ka,wallahi shikadai ne agurin maihaifiyarsa, karkabari yarasa rayuwarsa don Allah kaji? 



Doctor yace Y Y k  ka kwantar da hankalisa insha Allahu zaisamu lafia,

Kasan cewa darayuwa D"amutuwa  duk suna hannun Allah idan yazo saiya tashi idan kuma baiso hakaba toh" fabawanda ya'isa yatadashi kanaji ko? 



Y Y k ya kada Kai alamar gamsuwa,

D"domin shikam duk ya rikice yaja Dogon numfashi yace toh" shikenan ubangiji  yabasa lafia,  yace  to Ameen addu'ar daza aimasake nan.


Baba Lami baba Lami  Y Y K yakira sunannta  tai figigit tafara tare dacewa sannu yusufa ni har bacci yafada daukata, 


Toh"  ya jikin maigidan Nawa  dasuki daiko? Eh dasuki saidai doctor yamasa alluran bacci, insha Allahu zai farko normal tace toh Allah ya bashi lafia, yace Ameen mutafi nakaiki gida kiyi sallah tunda naga asuba takusa,

tace asubafa kace nadabo ?  Yace eh baba Lamin tunda Hudu darabi yanzu aikiga kuwa asuba takusa KO?


Tada gaKai Cikin tsananin mamaki yanzu  har sukai asuba,


Sun iske mama tsuru tsuru domin kuwa tunda sukatafi bata rintsaba, tana tarokon Allah yabasa lafia,


Yai Mata bayayin komai saidai yabiye Mata abinda kedamusa gudun karta daga hankalita, tace to shikenan Allah yabar zumunci, katafi gida Kaga iyalinka shikuma ubangijit yabasa lafia  Yace Ameen  idan nayi sallah zuwa karfe shida sainakoma tace tace toh  nagode kwarai DA gaske, bakomai mama aidani dashi duk dayane, toh ka gaishe dasu Jamila  Yace zasuji yafice daga gidan,


    WASHE GARI

D"amisalin 8:15 Am nasafe , Alh mahamud ne yafito Cikin shirinsa natafi ya Zaria, 

Sungama magana da Malam kenan yana kokarin bude mota saiga Humaira dagudu  tafito Cikin gida Cikin shirinta tsaf,


Malam ya kalleta  yace su budurwar kauye sai'ina kuma DA sassafan nan haka?  Tace Malam  kadainafa nibanaso ,Yai dariya Yace a ah nikam bazan dainaba,


T"ace to shikenan Cikin sha'gwaba  tace Abba nima zanije Zaria naga "yah Himu nadade bangasaba,


Malam Yai murmushi yace aukema Zaria kikeson kije,?  

Tace eh kaima zakajene? Yace a ah kedai kisamu atafida ke,tace aidani Abba zaune KO?  Cikin  wasa Yace a ah ni bazanje dakeba,


Tafara bugakafa Cikin sha'gwaba tace don Allah Abba katafi Dani nayi miss "yah Himu sosai, yamakale kafada alamar a ah tace please Abba kaji?


Yace toh zagaya kishiga mota tace yauwa Abba Na thanks ta kalli Malam tayi dariya sannan tace Kaga Abba Na zaya tafidani kaiko baza'a  tafida kaiba, yai dariya Yace basai nace afasa tafiyar dakeba tace Ai Abba Na bazaifasa tafiya Dani ba KO?


Yai murmushi batare Da Yace komai ba sukai sallama da Malam yaimusu fatan Allah yakiyaye hanya a dawo lafia  kuma  agaida masa da Abokinsan, Abba Yace zaiji insha Allahu yaja mota suka tafi.


💞💐LUFHAT Luv yours all FANS 💞💐

💞💞💐💐NU

💐💐💞N

💞💞SA

💐"DA.          💞

           Page25-28💐

                       💞

💐"DA

💞💞SA

💐💐💞N

💞💞💐💐NU




                 NA



💞MEENAT💐 💐UMAR💞 FARUQ💐



Wannan page nakune ADUK INDAKUKE AFADIN DUNIYA NAN,inafata gaisuwata zata iskeku 2006 graduated from GIRLS DAY SECONDARY SCHOOL kontagora Niger state, AMEENAN kuce  l'm really miss yours  LOVE  ALLLLLL💞💞💐💐💞💞💐💐💞💞💐💐💞💞💐💐💞💞💐💐💞💞💐💐💞💞💐




------------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION



PEN:THE STRONGEST WEAPON

------------------------------------------



only exquisite and whizkid writers are opportune to be writers




✍🏾





Tafiyar awa dayace takaisu garin Zaria Cikin  A.B.U  Abba yaifaki agefen wata bishiya me yawan ganye bayan yakashe motar, sai ya kalli gefenda "Humaira take baccinta kawai take kwasa ba abinda yadameta,


Dama" tun ahanya suna Cikin fira yaga tafara gyangyadi Yai murmushi tare da kada Kai Yace  Adda! Adda!!,


Ta bude ido ahakali tayi  mika tare da salati sai kuma tace washhh Abba nagaji,


Ya bude ido alamar mamaki Yace keh! Adda banason laziness saikace keki Kai driving dinmu?  


 Tace  Abba Allah idan mutum yadade zaune duk saiyaji yagaji,


Yai dariya Yace Adda Humaira tawa Haryanzu dai Ragwancin nan baira geba? 

Cikin sha'gwaba tace ummh Abba ah yakatseta dacewa Adda kenan, 


Yanzu dai kalli can kiga "gawani saurayi Can yaza shiga Hostel kirasa saimu basa sako yakira mana "Yah Himu dinko? 

Ta kalli Abba tare da cewa a ah Abba kakirasa awaya mana, ya girgiza Kai alamar   A ah, tace  why?     "Yace bcos I want to give him a surprise, ta kyalkyace da dariya tace yes Abba, barina kirasa tafada tare da fita daga motar. "Saurayin yace  ma Abba ina kwana?  Yace Lafia qalau ya sunan malamin ?  Saurayin Yai murmushi tare da cewa sunana saminu, Abba yace Malam saminu ya karatu?  Yace Alhamdullah, toh" masha'Allah, "dama don Allah munason ne kakira mana wanine a Hostal din nan idan kashiga.  

Saminu yace hala kuna tane man sa a waya  Baku samuba ko?  ya Yamutsa fuska tare da jan tsaki kadan mtsww Yace wlh matsalar net work ne, 

Abba Yai murmushi Yace bamu kirasa ba just we want to give him surprise, 


Saminu Yai dariya Yace ah  lallai zaku basa mamaki tunda baisan dazuwan kuba, toh" ya sunan sa? Humaira tafada masa Yace ok nagane sa yanzu zaku gansa in Sha Allahu,       Abba Yace toh" mun gode sosai, ya  Nufi  hostal ita kuma Humaira ta koma Cikin Mota ta zauna.



A" hostal saurayin nan me suna Saminu shine yake tafan ihun kiran "IBRAHIM MAHMOUD IBRAHIM YOLA.

Saida  saminu yakusa zowa dai dai bakin wata kofa An rubuta  Room 13 sannan Ya tsaya ya Kara kiran sunan.

"Yana kwance yana karatu saiyaji kamar Ana kiran sunan sa Yai shiru yana saurare tabbas shi din ake Kira don haka sai yai zumbur yamike yafito yayi tsaye abakin kofar Room dinsu,

A dai dai lokaci da Saminu ya iso

Suka hada ido sukai ma juna murmushi Yace ya akaine "saminu Naji kanata kiran sunana ne?

Yace"kanada baki Awaje,

Da Sauri yace suwane ne? yace wani ne shida wata yarinya, Yace OK saminu thanks bari naje nagani kila "Malam ne shida "Ashaty.


Tunda'ga nisa ta hango sa ya nufo gurinsu, da Sauri tafito daga motar tanufi gurinshi, yace oyoyo esha bebeh tare da Rungumeta aka fadarsa, ya kalleta yana murmushi I tama tanayi yace keda wane? 

Domin naga ba "Malam bane I hope dai ba Wannan "Abdul-jabbar din nan bane yadawo da munanan kalamansa na yaudara?


Ta bata rai sannan tace kai yah Himu ni' inaruwa "dashi Aini tun'tuni na manta dashi, yace eh dama Aini sonake  kimanta dashi" domin nagane shi din mayaudari ne, saboda haka nan bake bashi kinji KO?

(A ranta tace sorry yah Himu I can't forget him)


A fili kuma sai ta dan Taturo baki tare da cewa toh" aini dama narabu "dashi, yace yauwa my little sister  shiyasa nake Kara sonki saboda kina jin maganata,

Sukai dariya  tare da karasawa gurin motar. 


Ya juya baya"yana amsawa waya don haka ne yah Himu baigane shiba,

A hankali yajuyo dai dai lokacin da ya gama amsa wayar, yaje fata Aljihu yai murmushi i tama Humaira murmushi take.


  Shi"kam yah Himu mutuwar tsaye yayi saboda tsananin mamakin ganin Abban su,


Ya"runtse ido yabude ya kuma runtsewa yabude sannan ya kalli Humaira yace sister mafarki nake KO da gaske ne? 


Tai dariya tace yah Himu kenan you are  not a Dreaming oh Na reality fa,

Yace No! No!!No!!sister pinch me now saina tabbar l am dream  or not,

Dariya  tayi tare da kaima sa tsunkuli a hannun sa

Da Sauri yace yesss....lallai da gaske ne ba mafarki nake ba, sai kuma yasa hannun sa dai dai inda ta tsunkule sa Yace washhhh...

Gaskiya sister kin pinch nisosai fa,

Tai dariya tare Da cewa sorry yah Himu toh" aikai  ne kace Na tsunkule ka" Yai dariya tare da kallon inda

Abba yake tsaye yana murmushi, Abba yabude hannu tare dacewa  zonan baba Na nidin ne da gaske ba mafarki kake ba,

A hankali ya karasa gurin shi yafada kirjin sai tare da sauke ajiyar zuciya yace Abba meyasa katafi kabarmu tsawon wani lokacin ba kadawa garemuba?

Abba ya Dan bubbugi bayan sa kadan yace insha 'Allahu nadawo kenan bazan Kara tafia maitsawo irin haka nabar kuba kaji KO?  Yace toh" Abba.


Abba Yace Adda bude mota kidauko mana dadduma sai muzauna, tace toh

Ta ciro ta shinfida suka zazzauna.


Bayan sungaisa sai Abba yake tambayan sa ya karatu? Yace lafia lau, komai Na tafiya dai dai ko ? Yace eh Alhamdullah bah matsala, toh" ai haka nan a keso.

Sukaci gaba da hirarsu akan lamarin karatu Abba ya mika mishi key mota yace ka bude but akwai provisions Dana kawo maka da kuma tsarabar ka ta America, nace adebo maka sauran kuma sai kadawo.

Ya karbi key yana dariya yace nagode Abba yabude but din cike yake da kayan provisions, yace Abba duk  nawa ne  wannan  nikadai?  yace eh duk nakane KO sunyi kadan Ne akaro maka wasu?

Ya bude baki Cikin mamaki yai dariya sannan yace a ah ni sunyi Mani yawa, yace A ah basuyi yawaba tunda kanada friends sai kuyi amfani dashi duk.


Yace toh" mun gode sosai Allah yakara budi Yace ameen.

Humaira ta tayasa fitoda kayan a Cikin kayan ne yaga wata yar karamar cooler me kyau ya dauka yana juyata yace Abba wannan kumafa me ke Ciki?    Yace af harna manta sakone "daga "gwaggo tace akawo maka.


Yace Allah sarki "gwaggo kaka tawa nagode sosai ya zauna tare da bude cooler sai yaga soyayyen naman kaza da miyar tumatur, Yace Kai! tsohuwar nan ta'iya cin dadi fa ya yagi naman yakai baki ya tauna tare da lumshe ido sannan  yace Kai! wannan aisai yasa kunnan Mutum ya tsinke saboda dadi,


Humaira tana dariya tace yah Himu nima Dan bani inci  inji, Yace a ah nikam bazani bakiba tace  please yah Himu Kaga raina yabiya, Yace toh" ungo ya gutsuro Dan karami Yace kada kici dayawa Cikin kiyayi ciwon KO Abba?

Dariya yake  masu tace Dan wanga zaka bani? nikam bazan Ciba Yace Allah kici akwai dadifa bude baki inbaki, tabude yasa mata ta tauna tareda cewa ummh! ummh!! gaskiya akwai dadi toh" Dan karamun kadan, yace nakiya tace don Allah kaji my bros?

Ya harareta Cikin wasa Yace naki  wayon naki wato kicinye mun abina sannan kitafi kibarni Ko?  tace Ai bazan cinye ba, yace toh shikenan ya'aje sukaci gabada ci suna fira.


Sunyi nisa da cin naman sai ya kalli Abba Yace  abba idan yarinyar nan tacinye Mani nama toh" fa bazatabar school din nan ba saita biyani abina.

Abba yai murmushi Yace aizata biyaka ne shiyasa take taci ,yace toh" da dai yafi kam.


Can Yace af aina manta sister ya jaravawa?

Ta kalle sa tace aina zata bazaka tambaye niba ne shiyasa Na kyale ka, Yace sorry Allah murnan ganin Abba ne yasa namanta toh"yaya? 


Tace Alhamdullah gobe Nema ai zamu rubuta last paper, yace toh" Allah yabada sa'a tace Ameen.


Can kuma sai ya kalli Abba Cikin tsokana Yace Abba yarinyar nan tayi karama da yin candy, kamata yayi amaida ita J s s two,

Kadan yarage ta kware saboda jin abinda yah Himu yafada ,dariya yake mata sosai sannan ya mika mata eve water (dayake hada su Cikin provisions din)yace ungo kisha don naga kin kusan kwarewa toh" ni dawasa nake miki,Saidai tasha ruwan tukun sannan tace yauwa yanzu naji magana dakam banjiba.

Wane keson Allah yakai sa gaba sannan kuma yadawo baya? Aiba wanda yakeson haka KO

Abba? 


Yace eh tareda kallon agogon hannun sa lallai innabi tanaku" toh' KO yau bazani tafi yola ba, yah Himu Yace Abba tun yanzu zaku tafi?  Yace eh duba agogo  kagani, yaduba da Sauri yamike yace Abba 11:30am yanzu kuma inada test around 12:00pm 

Yace toh" aisai ka hanzarta katafi muma yanzu zamu tafi. yace toh" Ku "gaida su "umma da "Malam ita kuma "gwaggo kaKa ace mata nagode sosai sannan Ina gaida lta da kyau DA kyau waidaga ita bakari yakara she maganar dayin dariya suma dariyan sukai,

Abba Yace kaga gawasu" samari nan zuwa kace su tayaka daukan kayan yace toh" Abba Yace kafa maidai hankali akan karatu banda shiririta kajiko? yace toh" Abba insha'Allahu,

Samarin nan suka tayasa daukan kaya sukanufi Hostel su kuma suka shiga mota abba yaja suka tafi.

 

**********************

Yanzu 12:00pm narana amma harzuwa wannan lokacin "Abdul-jabbar baifar fadoba, hankalin Y Y K yatashi sosai yarasa abinda kemasa dadi Doctor yafada kafadar shi tareda cewa l am sorry to say bincikena tanuna Mani cewa "Abokinka yataba irin wannan ciwon

Sannan kuma yakai kusan awa biyar asume Wanda ta dalilin hakane yahaifar masa Da shiga koman Wanda bazance maka ga lokacin da zaya farfadoba,

Yana iya kaiwa gobe jibi one week two weeks three weeks Kai Harnan da one month  yana iya kaiwa batare da ya farfado ba Koma  yawuce fiyeda wayan kwana kin Dana lissafa maka, domin kuwa babu yanda baya zuwawa Mutum

Saboda haka saidai kawai muci gaba da yimasa addu'a Allah ya basa lafia.


Cikin tsananin tashin hankali Y Y K yadora hannu akai Yace yah salam!!!  Sai kuma yafita Da Sauri  daga office din,

    



  💞💐LUFHAT Ce Love friendssssss💞💐

💞💞💐💐NU

💐💐💞N

💞💞SA

💐DA           💞

          page29-32💐

                     💞

💐"DA

💞💞SA

💐💐💞N

💞💞💐💐NU


             NA


💐MEENAT💞 💞UMAR💐 FARUQ



edited by Zainuddeen zain


-----------------------------------------

PEN WRITERS ASSOCIATION



PEN: THE STRONGEST WEAPON

--------------------------------------------



only exquisite and whizkid writers are opportune to be writers





✍🏾






Tsaye yai abakin kofar office din tare da fitoda wayar sa daga Aljihu, yafara neman lambar "M.B  daya daga Cikin abokansu wato Muktar Bello,  don yasanar dashi abinda kefaruwa domin shikam yarasa abinyi gashi "Alh sa baya kasar, Kira daya M.B yadauki wayar Bayan sun  gaisa  yake sanar dashi cewa "Abdul-jabbar fa bayada lafia yanzu hakama suna asibiti saboda haka yazo yasa meshi,

Daga can M.b yace gashi nan zuwa yanzu insha'Allahu wani Asibiti ne?  Y Y K yafada mishi yace  gashi nan zuwa yace toh saikazo din,

Bayan yagama Waya da M.b sai kuma yafara neman number  dayan abokin nasu  (Wato "Abdul-ganiyu Delta boy kamar yanda suke kiran sa kasan cewarshi mutumi Niger delta)bayan sun gaisa yakefada masa rashin lafiyar "Abdul-jabbar.

Shikam delta boy tambaya yake meyasa "mesa kuma? jiyafa muka dawo lafia kalau koda yake tuncan naga "yana ramewa idan na tambaye sa me ke damunsa sai yace bakomai,


Nan Y Y K kesanar dashi Abinda "doctor yafada, Delta boy  yai salati tare da cewa lnsha'Allahu yana nan zuwa jibi Da sassafe Allah "yabashi lafia Y Y K yace toh" ameen sai kazo din sukai sallama yakashe wayar.


Yayi shuru yana tunanin ta yadda zai bulloma wannan lamarin ,

Ahaka M.b yasa mesa bayan sukara gaisawa sai Y Y K yajasa zuwa dakin da Aka kwantar Da   "Abdul-jabbar din, M.b ya tsorata daganin yanda "Abdul-jabbar yakoma Cikin lokaci kankani

M.b yace nifa ban san'ma yadawo ba?

Y Y K yace hmmm kaidai bari jiyafa "yadawo dasafe  nan yasanar dashi abinda "doctor yafada, M.b ya numfasa yace toh yanzu meye abinyi?

Y Y K yace abinyi kenan mu tsaya muga hukuncin ubangiji, M.b yace hakane toh Allah "yabashi lafia yace toh Ameen, 

Sukaci gaba da  tattaunawa akan ciwon "Abdul-jabbar din.



Yau asabar kuma a yau ne su "Humaira ke  graduated, don haka gabada basu samu nutsuwa ba saboda zirgazirgr dasuke tayi sai yanzu,


Zaune suke su uku Adakin "gwaggo  Hanah Haleeh da ita Humeeh kasan cewar Anan suka tsara zasuyi shirinsu tuda daganan gidan "Malam zuwa  school din banisa,

Sanye suke Cikin wayansu tsararrun dogayan Rigunan yadin materia ne pink colour yanada ratsin marun colour dinki  Rigar daga sama tadan matse kadan sai kuma daga kasa tabude sosai  gaskiya dinkin yai kyau sosai, "Aunty Habeeh ce ta dinka masu material "Aunty Habeeh ta kasance yaya ga Haleeh, 


Kai! yam'matan dai acan'acan abinsu gwanin sha'awa ko wacce tayi ruling da mayafi marun colour, fuskar nan "tasu koh hmmm tasha make up harta gaji sai zuba daddadan kamshi suke Kai!! yam'matan dai kam tubara kallah masha'Allah kamar kadaukesu ka gudu.



Yah Himu yadaga labulen dakin tare da cewa toh malamai sarakan kwalliya in kungama sai kufito mutafi, shima cikin shiri sa tsaf (kasan cewar yazo tunjiya Friday shida wani  friend din sa me suna "Idris Shehu Dan Zaria ne, yarako shine sunzo saboda grdt din idan angama su koma gobe lahadi kasan cewar "Humeeh ta damesa akan Dole sai yazo)


Ga badaya suka amsa da cewa mungama "yah Himu yace toh aisa kufito suka ce toh" gamu nan zuwa,


Da Sauri Humeeh tabi bayanshi tace yah Himu yace yap tare da juyowa ya kalleta yadai? tace wane zai kaimu school din?  ni yabata amsa, yah Himu yaushe ka'iya mota? yace yau tadan zaro ido kadan alamar mamaki tace yaufa kace?  Yace  Yesss kuma ka'iya sosai?  Ya harareta sannan ya dungure mata kai tareda cewa toh" malama idan zaku fito nakaiku toh" kufito saboda inason nadawo nakai Abba, idan kuma zaki tsaya dogon question" toh oya  bismillah, yafita yabarta nan tsaye itakam bin bayansa tayi da kallo Cikin mamaki  takama haba tare da cewa tabdi yanzu "yah Himu zayi driving dinmu? hmmm toh" Allah yakaimu Lafia  nima danake gefe nace to Ameen.


 Tace hey bebes kufito mutafi "yah Himu nachan yana jiranmu, sukace toh tare da mikewa tsaye KO wacce nakara kallon kanta amudubi taga inda beyiba ta gyara,

"Gwaggo dake tsaye tana kallonsu tai dariya tace kai yam'matan nan aiba sai kun sake duban kankuba kun hadu sosai, suka kyalkyace da dariya sukace " eh mana" sauran hadu warmu Da Allah Ko?  tace toh lallai sauran shikam,


 Amma dai yanzu kam wajan Hadu warku da samari yayi  dai dai,


Sukace ahhhh gwaggo tace eh wannan kalliya yau haka aisai ba samari, sukace Kai! gwaggo mudai kinga tabiyar mu,

Sukafita suna dariya itama dariya take.


Tafe suke Cikin motar "Abba parado jeep yah Himu ke driving dinsu ldris nagefen sa sukuma suna baya, fira suke shida ldris yayinda su Haleeh kesa baki jefi jefi itakam "Humeeh gum tayi Da baking ta domin kuwa gaba daya a tsorace take kodama ita din matsoraciya ce ta gaske, don haka take gani kamar "yah Himu zaije  yawatsar dasune kawai tunda  dai ita batasan ya'iya mota ba,


Saidai tasha mamaki lokacin da suka hau kan titi saboda yadda taga yana sarrafa sitiyar motar, domin kuwa kallo daya zakai masa ka tabbatar dacewa yadade da kwarewa atuki.


A hankali tai ajiyar zuciyar da harsaida yajita kasan cewar ta gefenshi take,

yai dariya tareda juyoda mudubi ta dai dai  saitinta dama yana kula da ita tunda suka shiga dayake yariga yasanta Sarkin tsoroce, yace yadai sister? ta kalleshi tareda turo baki Cikin sha'gwaba tace nothing,

Ya kyalkyace dariya dai dai lokacin da yake kokari shiga school din yace matsoraciyar yarinya kawai, ni narasa "inda kika samo wannan tsoro yarinya sai shegen tsoro sai kace farar kura, sai kace ba bafillataba,


Dai dai lokacin dayai parking su fito Hanah Da Haleeh sai dariya suke mata hada Idris,


Yah Himu ne yazo kusada ita saida yalalubi kunnanta sannan yadan murda kadan yace keh wai Afada miki fulani sunada tsoro ne?


Tace washhhh yah Himu you hot me fa,

Yai dariya tareda cewa sorry yadan rungumeta A kafada yace kina mamaki ne na'iya driving? "Idris ya koya mani tun lokacin danaje school farko farko gashi yanzu na'iya sosai,


Yace  bari mukoma mudauko " Abba tace toh" suka shiga mota sukatafi su kuma suka nufi inda inda za'a gudanar da programs.



A hanya Abba yace ma yah Himu  su tsaya wani shop complex yanason ya sayi Waya, Yace toh" "Abba nizaka saima Waya?


Abba yace no I want to buy to my "doughtes yace Abba toh" mu kumafa?  yace a ah,


Dasuka shiga shop din Abba yace Waya yakeso yasiya akawawo masa yazabi iPhone7 guda uku masu kyau, afada masa kudin yabiya,


Yah Himu yace Abba remains us Abb yace no! yah Himu yace why?  saboda you're  too  Young's to carry the phone,

Yai dariya yace Abba toh" idan mu kanana ne to sukumafa? Abba Yace ah "sukam ai big girls ne bakada yau suke candy bah,


Dariya suke sosai dagashi har ldris saboda jin abunda Abba yafada,


Shima Abban dariya yai cikin wasa Yace ko ba haka bane? ldris  Kai yakada yana dariya yace hakace Abba,yah Himu yace toh" shikenan tunda "su yan candy ansiya musu toh muma yan high sai asaya mana,


Yace a ah nakiya! yace please Abba buy us, Yace toh  kudauka,

Suma suka zabi manya manya masu kyau yabi kudi sutaka tafi.



Koda suka isa school din har anfar gudanar Da programs din don haka suma sukabi layi  A hankali Cikin tsari da nitsuwa ake tafiyar da komai har akagama, yayinda su Humeeh "suka karbi kyaututtuka masu yawa kasan cewar su dalibai masu hazaka da kuma tsafta.



Bayan agama ne suka koma gefen wata bishiya suna daukan photo hada Abba da kuma Aunty "Habeeh dayake tazo itama da kannan Hanah da kuma wayansu   kawayan su.


Bayan sun gama daukan photos sai Abba yabasu Waya yace ganasa kyautar nan aiko sukasa ihun murna tareda rungu meshi dariya yake yace toh yanzu idan Ku ka kada Abban naku Cikin mutanefa? 


Suka sake sa suna dariya tareda   tsugunnawa sukace Abba mun gode Allah yakara budi, yadafa kawunasu  Yace kutashi-kutashi Allah yaraya manaku yasa maku Albarka ya kuma Baku ilimi mai amfanin Al'umma suna dariya sukace Ameen Abban mu.


 Saida yah Himu yakai "Abba gida sannan yadawo ya kwashesu yakai su "Hanah da "Haleeh gida jansu sannan suka tafi gida


******************

Bayan kwana biyu da misalin 4:00pm su uku ne tsaye ajikin window dakin Da aka kwantar Da "Abdul-jabbar  Y Y K M.b Delta boy, saboda yanzu doctor ya Hana kowa shiga dakin saidai kowa yazo  tsaya ta window "ya gansa.


Delta boy Yace ni gaskiya ciwon "nasa yana bani tsoro yaufa satinsa daya kenan ahaka? watoma tunda nakoma gida haryanzu baya moving?


Y Y K yace kaidai bari one week  kenan Amma hattada dan yatsan sa bata working, hmmm kaidai lamarin saidai gyaran Allah kawai.

M.b yace ni wallahi "Mama kebani tausayi Acikin yan kwana kin'nan  duk tarame saboda tsabar zullumi Da fargaba Y Y K yace nima tausayi take bani sosai wallahi,


 Delta boy Yace Hmmm aidole atausaya Mata" domin kuwa shikadai ne mata gaba da baya kagako dole tayi fargaba da zullume,

Gashi kuma bata" fada masa kowa ne mahaifinsa ba, inaga harda tunnanin haka yasata zullumen halin dayake Cikin,


M.b yace hakane kumafa toh" yanzu dai mucigaba dayi masa" Addu'a kamar yadda muka saba Allah yabasa" Lafia sukace Ameen.


💐LUFHAT ce Luv Fanssss💞

💐💐💞💞NU

💞💞💐N

💐💐SA

💞DA            💞

           page33-35💐

                      💞

💐DA

💞💞SA

💐💐💞N

💞💞💐💐NU


             NA


💞MEENAT 💐U.  MAR 💐FARUQ💞




This page belong to All people of PEN WRITERS ASSOCIATION ✍🏾 ANA TARE  kugane GUYS irin Very tied din nan Faaaaaa!!!😀😀😀




edited by Zainuddeen  Zain



----------------------------------------

®PEN WRITERS -ASSOCIATION



PEN :THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------



only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers



✍🏾






Y Y K yace nifa Ina ganin harda san "yarinyar nan daya kwallafa  A zuciyar saha dashi keda munsa,


Delta boy yace hmmm tabbas harda shi domin kuwa nizan fada maka kaga "yanda yatada hankalisa saboda yakira number ta baijeba? yiyayi kamar wani zararre naita  lalla "shinsa inabashi hakuri akan cewa yabari mana harmu dawo gida tunda kadan yarege mukarasa amma ko "ya saurareni  sai abun yafara bani haushi ni kuma kawai saina kyale shi  tunda yaki ya saurareni Kai tun "yanabani haushi har yako mabani tausayi, Dana gane cewa bayin kasa bane Allah ne ya jarabeshi da San "Humaira Dan haka saina farayi mashi Addu'an Allah ya yaye mishi,


Ameen sukace Nan shima Y Y K kesanar dasu abinda yafaru tun kafin "sudawa har zuwanda sukai gidan su Humaira.


M.b yanisa yace gaskiya "Abdul-jabbar yana San yarinyar dayawa, kuma har yanzu bakuji inda "suka komaba?


Y Y K yace inafa muka sani  Delta boy yace inafa zasu sani kaidai bari kawai koda cewa akai za'aje "nemanta Toh ta'inama za'afara? tunda garin Kaduna ba kadan bane, hmmm kaidai Allah yai mana maganin dabazamu yiwa kan'muba shi kuma Allah yabashi lafia sukace Toh Ameen,

 Y Y K yace Mujenku sai zuwa anjima kuma sukace Toh.

Nasan dai me karatu yaso yasan wace wannan "Humaira da soyayyar ta keta wujujuwa da Abdul-jabbar hartana KO Karin Kai sa barzahu.

yakamata kam muji  KO,




WACECE HUMAIRA?

 Aishatul Humaira shine cikakken sunanta ta kasace ya ga Alh Mahamud Da Hajia Asma'u wadda  suke kirada Umma, su biyu ne agurin iyayensu  ita da yayanta lbrahim wato yah Himu,


"Alh Mahamud asalinshi mutumin Adamawa ne aikine yakawo shi garin kaduna inda yake aikin bank yana zaune A unguwar malali,

Alh Mahamud yahadu da  "Asma'u ne akan hanyar shi tazuwa aiki   Asma'u diyace ga Malam Garba me Almajirai, Cikin hukunci Allah soyayya me karfi tashiga tsakanin Mahamud DA Asma'u har Allah ya kaddara Aure tsakanisu, suna zaune Cikin aminci da yardan juna, inda  yaci gaba dazuwa aikinshi Cikin hakane,


 Allah ya'azurtasu da yara biyu wato lbrahim da Aishatul Humaira  lbrahim yaci sunan kakanshi ne nagurin Abba itama  taci sunan yayar Abba shiyasa "yake kiran ta Adda.


" su Humaira suntaso Cikin soda kaunar  iyayensu itada lbrahim wato "yah Himu Wanda itane ke kiran shi da yah Himu din,


Iyayansu Na matukar kaunar su musamman dasu kaga tunda gasu Allah bai Kara basu haihuwaba,


Don hakane "suka dauki so DA kauna suka Dora musu duk abunda Abba yamu Toh Na yah Himu ne da Humaira don haka Cikin gata suka tashi fache! fache!



Yah Himu yana aji biyar Na secondary ita kuma Humeeh tana jss two,


Kwatsem wani bakon lamari yasa mesu bank din da Abba yake aiki wasu makudan miliyoyi suka nace,


A lokacin kuma Abba shi ne manager Bank din don haka yashiga matsanaci tashin hankali, KO kuma nace sun shiga shida iyalinshi.


Wasa'wasa saida bank ta kwace duk wani Abuda ya mallakah hatta gidan da yake saidai suka kwance.


Kuma duk wannan abun "Alh Mahamud yana tsare a prison, "Abokin shi Alh Musa ke tsaye akan lamarin ko lokacin da akabasu notice cewa su tashi Alh Musa ne "yakama masu gidan haya a unguwar tudun wada suka koma chanda zama,


A haka "suka cigaba da Rayuwa cikin wani irin yanayi mara dadi,


Ana cikin haka akayen kema "Abban nasu zama agidan prison Na tsawon shekara biyu, saka makon makudan kudin da'aka biyoshi,


"Shikam bayada wayan kudi don haka dole ya Amince da hukunci da Alkali ya yanke  mishi Na zama gidan yari Cikin tsananin bakin ciki Da bacin rai.


Domin shikam yasan baici sisin kwabo acikin makudan kudin da suka salwanta ba, saidai kam yana zaton "mataima kinshi, koda yake ance zaton zunubi koda ya kasance gaskiya Amma dai kam yana zarginshi dasa hannun shi acikin lamarin,


Tunda "yanuna baya kaunarshi, tun lokacin Da akarbi matsayin shina manager akaba "Abban su Humaira,toh shikenan ya dauki karanta tsana yadore mishi


shiyasa Abba yayi tunnan KO shine toh kaidai wanene yake da sa hannu acikin wannan lamarin Toh yabarshi DA Allah.



A haka su "Humaira suke Rayuwar Cikin matsananci hali inda hartakai aka kiresu daga school din dasuke, tunda basu biyan kudi dayake su  private school baruwan su dazar time yayi Toh abasu kudi.


Dama "Alh Musa kedan taimaka musu toh shima iyalin shi sun'isheshi mata biyu dayara bakwai gashi shima karayar Arziki yasame shi, don hane maya Ko mai yakara jagulewa,


Dole badan sunaso ba suka koma wata government school tunda shi bawani kudi ake biyaba,

 

A haka har yah Himu  ya kammala S.S three din shi da taimakon Malam wato mahaifin Umman su dayake yah Himu yasamu result me kyau, Don haka Malam yasamar mishi Admission a A b u Zaria don yaci gabada karatun shi inda yake level one yanzu haka sunyi hune yana gida ita kuma Humeeh tana S.S two yanzu,


A yau ranace datake sance ranan aiki ga kowani ma'aikacin government Kai harda students wato yan makaranta, ranace wadda Malam bahaushe keyima kirari da cewa KO bature na tsoronki wato Monday.


" Wata yar kyakkyawar matashiyar buduurwace yar kimani shekara goma sha hudu zuwa sha biyar farace Itaba doguwaba ita kuma bagajera ba fuskarta Dan dai dai tana dauke Da manyan idanu Amma ba sosai ba, tanada Dogon hanci da Dan karamin baki Wanda idan tayi dariya kamar kada tarife bakin, badan komai ba saidan open teeth din datake dashi sama Da kasa wanda ya karama fuskarta kyau Da kwarjini, ga kirjinan Nata Kam hmmm! ba'acewa komai domin koh cike yake Da dukiyar Fulani zaka fahimci hakane ta yadda suka dago hijab dinta,


 Sanye take Da school uniform riga Da wando Da hijab, rigar da hijab din fararene shikuma wandon me ruwan kasane, Tara taya irin jakarnan da yammatan yanzu suke yiwa lakani da swaga bag ko kuma suce wankan gefe Humaira kenan yamma tan "Umma.


Kallo daya zakai ma kyakkyawar fuskarta kagane cewa da'alama yau bata jin zuwa school din, zakafahimci hakane daga ya nayi yanda take tafiya Ahankali tamkar bata son taka kasa,


A hankali take kokarin shiga kwarda zatafita Da ita bakin titin dazata hau adai dai ta sahu,


Toh kuma a wannan lokacin ne hanci wata mota kiran Honda civic yar karama new model takunno cikin tsautsayi kaji fachauuu daruwan kwataaaa!


Tunda ga kasanta har saman gaba daya school uniform din jikinta yabaci Da ruwan kwata, Allah yasota  bada  beauty fice din tabah a hankali tadago dakai don taga "waye  kedai wannan Aikai- akan?


Dai Dai lokacin da "yafito Cikin mota domin tuni yayi parking gefe yanufo  gurinta,


Ta tsura masa ido farine Dogone  kuma mikakke yanada tsayayyu kafada masu birgewa ma'abucin faffadan kirji da kakkauran jiki, sai kuma yadan Rankwafa kadan ta yadda zubin halittar shiya bada kirar wani Mutum mai tsararren tsayi mai ban sha'awa, 


 Kai kace wani bako ne daga karasar Lebanon, gawani saje daya aje wadda takarawa kyakkyawar fuskarshi me dauke da eye balls da Dogon hanci kyau da kwarjini, 


shekarun shi bazasu wuce Ashirin  da takwas zuwa da taraba yana sanye da Riga t-shart white and wandon jeams black. Abdul-jabbar Ahmed kenan

Mashi saurayi me jini ajika,


 Cikin lokaci kankani takare masa kallo Ahankali tadukar Da kanta kasa, A dai dai lokacin da yakarasa gurinta,

Cikin muryarsa me dadin saurare Yace eyya please  Am so sorry ban kula dakeba wallahi, ahankali tadaga Kai ta kallesa aiko suka hada ido at the same time jitai gabanta ya fadi shima Abdul-jabbar hakata kasance agaresa, Da sauri ta dukarda kanta kasa tareda cewa     it's ok,

Sannan tajuya da sauri

 tafara tafia,

Yayi Dan taki kadan ya isa gareta badon komai ba saidan yasake jin daddadan muryanta, ahankali ciki rada yace sorry once again,

Batare Da ta juyoba tace I say it's ok sannan tacigaba da tafiya ya tsurama bayanta ido duk Da cewa tana sanye da hijab hakan be hanashi hango kugunta yana motsawa ba,


Yana tsaye harta shiga  wani gida me dakali biyu  ahankali yasauke nauyayyan ajiyar zuciya sannan yajuya yanufi inda yai parking motar sa.


Itakam Humeeh kallo daya zakai mata kagane cewa kiris take jira tafashe da kuka,


Aikam tana shiga cikin zauren tafashe Da kuka Wanda kanajisa kasan Na sha'gwaba ne,

"Yah Himu da dakin shi yake cikin zauren yanaji kukanta yafito da Sauri haryana buga tuntube da bakin kofa,domin kuwa idan akwai abunda yatsana to baiwuce kukan Humeeh ba,


Lokaci guda yajero mata tambayoyi kamar haka meyasa meki? me'akai miki? kedaw! Maganar ta tsaya saka makon yadda yaganta, 

 

Da Sauri ya karasa gurinta tareda cewa kut! "wani  Dan renin Hankali ne yai miki wannan wulakanci?

Cikin sha'gwaba tace  "wani ne yanhhh aibai jira takara Saba ya shuri takalma  da sauri yai waje


Cikin zafin nama yah Himu yakara sa gurin  Abdul-jabbar dake ko Karin shiga mota sai yaji ance dakata Malam,


Da sauri yajuyo suka hada ido cikin daurewar fuska yah Himu yace haba don Allah Malam wannan wani irin abune haka meyasa idan kuna driving Baku kallon hanya da kyau ne?


Dubi yadda kabata mata school uniform yanzu shikenan Kai mata hasarar zuwa school yau,


Mtsww yaja tsaki sannan yaci gabada dacewa kudama ya yan masu kudin nan haka kuke some time sai kurika daukan yayan talaka abanza,


Abdul-jabbar dayake sauraran shi tunda yafara baice komaiba saida yaga yakai ayah sannan,

Yace Toh" kuyi hakuri bansan tana tahowo ba nikuma nariga nakawo shiyasa,

Yace toh idan bamuyi hakuri ba yaza muyi tunda kariga kagama, yajuya yanufi gida yana gunguni fada.


Shikam Abdul-jabbar bin bayan sayai da kallo harsaida yashiga gida,

 sannan ya bude mota yashiga yaja yai tafiyar  sa

Wannan shine silar haduwar Abdul-jabbar DA Humaira.





💐LUFHAT ce I Love all FANssss💞

💞💐💞💐 

       💐💞💐💞💞                     

          DA SANNU


        💞💐💞💐💐

           💞💐💞💞


             💐page36-40💞


         

     NA


💐MEENAT 💞UMAR FARUQ💐




Assalamu'alaikum

Masaoya wannan littafi kuyimun hakuri narashin ganin  posting din na jiya saboda banajin dadin jikina, Amma yanzu Alhamdullah. sannan kuyi hakuri  

Na chanja tsarin littafin hakan yafaru ne saboda wasu basugane sunan littafin ba, so dafatan hakan bamatsala NAGODE SOSAI.




Wannan page NA sadaukar DA shiga duk Wanda yagane SUNAN WANNAN LITTAFIN nagode kwarai dako karinku nagane sunan book din wato DA SANNU.





edited by Zainuddeen zain


----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION



PEN:THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------



only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers





✍🏾






Koda Humeeh tashiga cikin gida Umma tana  duke bakin fanfo tana wankin kayansu, 


saijin  sallamar Humeeh tayi" ta amsa tare da mikewa tsaye tace ke kuma lafiya ki kadawo  baki tsoron ki Makara?


Tajuya ta kalle ta ganin yadda take ne yasa tace A ah ya'akai kuma hakata faru? 


Cikin kukan Sha'gwaba tace bawani" ne yawatsa Mani ruwan kwata ba?


Umma tai murmushi tareda girgiza Kai tace Toh" shine kuma abun kuka?


Ta turo baki tace Umma kalli fa "yanda duk yabada Mani school uniform dina,



Umma tace hmmm "Humaira kenan "toh" yazakiyi da kaddarar Ubangiji?



Tasake turo baki kadan tace "toh" shikenan fa yau barani school ba,


Umma tadan ja tsaki  mtsww tareda cewa toh" sai meh? Dama yau bakiyi niyar zuwa makaranta ba ai ina kula dake tunda kika tashi,

Saboda haka sai kicire kayan Na wanke.



Dai dai lokacin da yah Himu ya shigo yana fada, Umma ta kallesa  tace Kai kuma fa Kai dawa ne?


Yace Umma nida wannan "guy din nan mana daya watsama  Humeeh ruwan kwata Dan renin hankali kawai, yai kwaf"


Umma data zuba masa ido saida yakai Aya, sannan  tace yanzu zuwa kayi kukai tashin hankali ko? banasan haka fa


Yace Umma nifa ba tashin hankali natafi mukayi ba, kawai da nafada masa" irin haka dasuke be dace ba ya kamata surika kula.



Ya kalli Humeeh yace tafi kitube kayan kikawo Na wanke maki kinji my sister?


Tace toh tanufi daki don ta tufe,


Shikuma yanufi wurin Umma yana cewa "Umma wanki ki kikeyi Ina daki baki kirani nayi makiba?


Tace eh  ai bansan kana nanba, yace Ina nan banfi taba, dai dai lokacin da ya tattare hannun Rikarsa yaduka yafara wankin.




Cikin nitsuwa yake driving zuciyar sa cike da tunani "Humeeh  Ahankali ya furta is beauty "she have a Sweet voice sai kuma yasaki lallausan Murmushi tareda Shafa suman kansa sannan yace ko meye  

sunan ta?


(Nikam dake gefe nace oho "kaji shi daga ganin Sarkin fawa sai meya tai zaki.?)

Chan kuma sai ya hade fuska sannan yai tsaki mtsww" saboda tuno kalaman "yah Himu,


Yace kai kaji "guy din nan fa?  Don yaga wannan motar shine hada wani cewa yayan masu kudi,? toh" nima Arzikinta naci akabani  Ni din'ma aidan talaka ne, yai kwaf."


"Yana tafe yana surutu harya karasa unguwar su Y.Y.K yai hon mai gadi "yabude masa get yashiga bayan sun gaisa da "baba maigadi sannan yakarasa ciki,


Bayan yayi parking sai yakashe "motar sannan yanufi cikin gida,


Yai sallama yashiga Y.Y.K suna zaune shida Jamila matar sa ya amsa tareda daga Kai ya kalle sa, 


Magani  yake ba "Jamila dayake tana dauke da tsohon ciki Haihuwa KO yau KO gobe."


Saida ya zauna a daya daga cikin kushin din falon sannan ya kalli "Jamila cikin sigar zolaya yace sannu tsohuwa!


Ta Dan harare sa kadan tace "wace tsohuwa?


Yace ah "kemana, tace koh dai Kaine tsohon ba?


Yai murmushi yace  ah haba

 dai ki kalle nifa da kyau yaro dallele Dani kice mani tsoho,


Tace tabdi lallai kam A haka kake kiran "kanka yaro hada wani dallele bayan kakusa zama baba,


Saida yai dariya sannan yace gaskiya kam toh barina Dena kiran kaina yaro  tunda yanzu Na kusa zama baba KO?


Tace a"toh da dai yafi kam,


Saidai gaskiya kidena  kirana tsoho domin ni aiba tsoho bane,


 Wanda zaya kwanke yammatan uku nan gaba shine za'akira da tsoho? yakai karshen maganar dayin dariya"


Tace oho Ashe babu dadi "ni aka kirani da tsohuwa?


Sannan ba "yammata uku zaka wanke ba ko goma ne ba abunda ya dame ni" kuma nima adena kirana tsohuwa,


Yace ah ke "kam ai tsohuwa ce ke bakiga yadda kike zama dakyar tashi dakyar ba,


 Sannan karki damu da

 "matan daza'a karo Asalima  ba'akanki fa zasu zaune ba"


 Harara ta watsa masa cikin wasa sannan tace dama ya za'ai "su zauna akaina saidai kam "su zauna kan Wanda "ya daukosu"


Dariya yai yace "toh shikenan tunda kan Wanda ya daukosu zasu zauna,


Itama dariya take tace   yasu "Mama da baba Lami?


Yace suna Lafia tace "toh madallah dai dai lokacin datake Ko Karin tashi dakyar,


Yace kin gani ba?

Ance ke tsohuwa ce kince "a ah,


 Tai murmushi tace kaidai kasani "Abdul-jabbar nikam nashiga daga cikin in kakoma ina gaidasu "mama.


murmushi yai  yace "toh" Uwan biyu zasuji azauna Lafia."


Y.Y.K dariya yake masu sannan ya "kalli Abdul-jabbar yace  Nawa kenan

Kadai  ya'iya zolayar my "Dear har kagaji,


"Toh ya akai ne"? naganka tunda sassafe I hope dai lafia ko kayi mafarkin My "Dear ta haihune? yakai karshen maganar sa da yin dariya"


Shima Abdul-jabbar dariya yai yace kaidai bari Nawa narasa yadda aikai yau nafito Tunda sassafe haka,


Saidai ga dukkan alama fitowar mai sa'ace domin ko nayi babbar tsintuwa,


Y.Y.k yace  babbar tsintuwa ta me kenan?


Nan "yabashi labarin   abunda yafaru tsakaninsa da "Humaira,


Yaci gabada dacewa Kai "Nawa gaskiya beben "ta hadu sosai wallahi ya Kai karshen maganar da yin murmushi.



Shikam Y.Y.K ido ya zubama "Abdul-jabbar saboda ganin yadda ya takarkare sai koda "yarinyar yake,


Hannu yasa ya girgiza Y.Y.k yace Nawa Ina ta magana Amma bakace komai ba,


Yai firgigi tareda cewa hmmm Nawa kaine kuwa?


Yace yes I am you Abdul-jabbar Amma me yasa kace ni ne kuwa?



Mamaki nake wai Kane ke koda mace hmmm Amma dai kam gaskiya this girl is Lucky  ko wacece domin ga dukkan alama ta tafi da lmanin ka koh? 


Dariya yai tareda shafa kyakkyawan sajen yace Kai nawa baka "ganta bane,


Shima dariya yake yace ai  zanso kam naganta ko wacece ita,


Yace saidai gaskiya bajin dadin yadda nabata mata school uniform ba" shikenan yau Na "hanata zuwa school kamar yadda yayanta yafada,


Y.Y.k yadan bubbuga kafadar sa tareda cewa kada kadamu

Anjima zamu je mukara "bata hakuri daga nan sai mu kafa gwamnatin mu ko?

Ya kai karshen maganar da yin dariya.


Shima Abdul-jabbar dariya yake,"


Hakan sukaci gabada firarsu har lokacin da Abdul-jabbar ya mike tareda cewa nizan tafi,


Shima Y.Y.K mikewa yai yace tunyanzu?


Yace eh zanbiya ta wurin "M .B daga Chan saina tafi gida,



Har wurin motar sa yaraka sa bayan yatafi sai shikuma yakoma cikin gida don yai shirin tafiya office.


**************


   Wanene Y.Y.K?


"Yusuf ya'u Na kaka Dane ga Alh "ya'u Na kaka da Matar sa daya Hajiya karima da yaran su uku


 Mata biyu Aunty "Naja'atu Da Aunty "Murjanatu sai  namiji daya shine "Yusuf matan duk sun girmi "Yusuf ko wace tana zaune gidan mijinta   lafia tare da yaranta"


Alh "ya'u Na kaka hamshaki mai kudi ne kuma dan kasuwa   yana zaune a unguwar sarki, yakasance Mutum ne mai tausayin talaka,


Dazaran ya kula kana bukatar taimako "Toh KO baka tambaye saba  zai tai makeka,


"Toh balle kaje ka tambaye sa to fa sai inda karfinsa yakare,


Wanda shine yadauki yauyin karatun "Abdul-jabbar tundaga primary secondary har zuwa N.D.A,


 yanzu haka ma "Abdul-jabbar yagama N.D.A din sa Zasu tafi America akwai wani kwas da zasuyi Na shekara daya, kuma Alh "ya'u Na kaka ne yadauki nauyin tafiyar",



A hankali  Abdul-jabbar yake  driving har ya isa gidansu dake unguwar  kurmin mashi,



Inda suke zaune shida mahaifiyarsa Hajiya "Aisha wanda shima Alh "ya'u na kaka ne ya mallaka masu kuma shine ya kaita makka,


"Toh wai duk sanadin Abotan dake tsakanin Yusuf DA Abdul-jabbar ne?

A ah shidin dai mai taimakone kawai  Toh madallah da kyakkyawar zuciya irin ta "Alh ya'u Na Kaka."



DA sallamar sa yashiga cikin gidan tana zaune afalo kallo take ta amsa masa sallamar tare da daga Kai ta kalle sa,


Dai dai lokacin daya zauna kan kafet tare da cewa ya Allahu, sannun "mama ya gida?


Tace yauwa sannu da zuwa, ina kaje ne tunda sassafe haka? Yace yace naje gidan Y.Y.k  tace aw "toh suna lafiya ? yace lafia kalau   sunce suna gaida ke, tace Ina amsawa,

Sun Dan taba fira kadan yamike tare da yace cewa Mama "baba Lami bata iso ba tukun ? tace eh wallah bata iso ba" yace toh Allah ya kawota Lafia tace Amin", ni Zan shiga Na kwana,

 tace Toh  shikenan.



Abdul-jabbar Sai juyi yake a gado shida ya tafi daniyar yai bacci Amma yakasa,tunanin "Humeeh ya addabi kwakwalwar sa,

Daya yarufe idon fuskarta yake gani tareda kyakkyawar surarta, Chan kuma kunnu wansa yana tuna masa daddadan  voice nata,


A hankali ya jawo filo ya matsesa a kirjin sa tareda rintse ido wani irin yanayi yakeji Wanda be taba jin irin

 Saba,


Dakyar! dakyar!! Abdul-jabbar ya gaya dare saboda tsabar tunanin "Humeeh burinsa kawai yasake gani beauty fice dinta tareda jin sweet voice Nata,


Bayan yai sallar magrib sai yai bude baki kasan cewa yana yin azumin Litinin Da Alhami",


Key motar sa kawai yadauka ya fita,

Ya kokarin shiga mota sai yaji wayar sa tana ringing, koda yaduba saiya ga "NAWA kamar yadda yai save, yai murmushi tareda dagawa,yace ya akai ne?


Daga Chan yace Lafia lau kana Ina ne? Yace gani nan zanzo wurinka, yace bana gida muna asibiti DA Sauri Abdul-jabbar yace Lafia meya faru?

My Dear ce zata haihu,

Kuma wani asibiti ne? Y.Y.K ya fada masa sunan asibiti yace OK gashi nan zuwa,


Don haka dole Abdul-jabbar ya hakura da maganar zuwa wurin Humeeh, ya nufi asibiti,



Koda ya isa asibiti Jamila ta haihu ta haifi yarta mace kyakkyawa DA ita tubara kalla masha'Allah,


Sai misalin karfe10:30pm nadare sannan Yakoma gida saida yashiga cikin gida yafadawa Mama cewa "Jamila ta haihu,


Mama tai murna sosan ta kumayi addu'ar Allah yaraya Bebe yace Amin tareda juyawa yanufi dakin sai.



**********

Washegari da misalin 2:30pm Abdul-jabbar ya isa gidan Y. Y.K ,


Bayan sun gaisa sai Abdul-jabbar yace Ina maijego? Y.Y.K yace tana ciki bacci take,


Y.Y.K yace ya akai ne nawa,?


Abdul-jabbar yace Dan safa kwata miliyon dinsa, yace gaskiya Nawa ina cikin wani yanayi fa,


Y.Y.K Idon yazaro alamar tsoro yace Nawa meya faru? Yace gaskiya tunanin yarinyar nan ya hanani sakat fa, dariya yake masa sosai,


 yayinda shi kuma ido yazuba masa sai kuma ya Dan hade fuska tareda cewa bansan fa iskaci wannan wani irin dariya ne haka?


Y.Y.K ya Dan tsaya dayin dariya yace toh aikai Nawa daganinka Ansan cewa you're a new come din Na,yanzu dai tashi mutafi yafada yana mikewa tsaye, shima Abdul-jabbar din mikewa yai suka fita






💞LUFHAT CE💐

💞💞💐💐               💐💐💞💞

            

  DA SANNU                   

💞💞💐💐

💐💐💞💞


                          💞Page41-45💐

                    



              NA



💐MEENAT 

💞UMAR FARUQ💐





edited by Zainuddeen zain


-----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION



PEN: THE STRONGEST WEAPON

-----------------------------------------



only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers




✍🏾





Tsaye suke  suna duban suga ta inda "yaro zaya bullo su'aikesa yakira masu "Humaira,

Y.Y.K ne ya hango wani yaro yanufosu sai yace yauwa gawani  yaro zaya biyo tanan  bari saimu aikesa yakirata,


Ya sunanta? Abdul-jabbar yai masa kallon nima bansa niba,


Dariya Y.Y.K yai a dai dai lokacin da yaron ya iso wurin su har zaya wuce su,

Da sauri Y.Y.K yace salamu'alaikum, tareda meka masa hannun shima yaro Hannun yamika masa tareda amsa"sallaman,


Dan Allah abokina kashiga gidan Chan kace ana sallama da "maigidan yace toh" yanufi gidan


Da Sauri Abdul-jabbar yamatso wurin Y.Y.K yace Kai Nawa maigidan fa kace?

Yace eh toh" tunda bakasan sunan sabuwar  budurwar takaba basai  muyi maigaba daya ba?


Yace Nawa banfa ganeba kamar ya maigaba daya?


Yace dadina dakai kenan wallahi sai Kai tayin abu kamar dan fari,


Yace toh ai shidin ne,  yai murmushi yace toh" sannu Sarkin yan wauta, abunda Nake nufi shine mufara kamun kafa da Babanta,


Yace da fatan kagane ai Dan fari gilashi? yakarasa maganar da yin dariya.

Shima Abdul-jabbar dariya yai yace eh nagane kanin mata,


 Ya watsa masa harara yace waikai baza kadena kirana kanin mata ba ko?


Dariya Abdul-jabbar yake sosai yace baza A denaba din, kaima baka  cemani Dan fari ba?


Yace toh"kai badan farin bane? yace ni ne,

Toh kaima ba kanin matan bane? ya langabe Kai tareda cewa toh" yazanyi tunda sun'rigani zuwa ni ne" dariya  sukai gaba daya tareda tafawa.


Dai dai lokacin da yaron yadawa yace ace "maigidan baya nan waisu wane ke nemansa? Kodaya kema naji ace wata tazo tagani Kusu wanene? tana nan zuwa.


Y.Y.K yace yauwa abokina mungode ya zaro naira Dari biyu Aljihu sa yami kama yaron,


Yaro yadan russuna tareda sa hannun biyu ya karba yace Nagode yajuya yatafi.


Tunda ga nesa  "Abdul-jabbar ya zuba   mata ido hankali take tafiya kamar bataso taka kasa sanye take da atamfa  brown   me ratsin ash  Riga da zani ne dinkin tasa hijab mai hannu Ashe colour,


 Ta isa wurin su tareda sallama "Y.Y.K ne ya amsa mata fuskarsa dauke da murmushi, tadan russuna kadan ta gaida su Y.Y.K ya amsa mata 


Shikam "Abdul-jabbar be amsa ba saidai ido  daya zuba "mata ganin yadda take komai cikin sanyi hakanan yasa yaji takara shiga cikin Ransa,

 

A hankali ya sauke ajiyar zuciya tareda maida hankalin sa wurin su,


Cikin Dan siririn muryarta mai dadin saurare tace kuke Neman maigidan Chan?


Yace eh mune saidai  ba "maigidan muke nema ba yar maigidan  muke nema"


Da sauri tace kalle sa  yai murmushi yace eh wurinki mukazo" ni sunana Yusuf kina iyakirana Y.Y.K shi kuma dan 'uwana sunan sa Abdul-jabbar,


 tace Lafiya dai KO? Yace Lafiya lau saidai bamu San sunan Malamar ba?


A hankali ta dukar dakai kasa tana murza zoben dake Dan yatsanta, 


Shikam "Abdul-jabbar ido ya zubama zarazaran yatsunta masu kyau da sha'awa sabada adon Jan lalle da bakin da akai masu,


Cikin sanyi tace sunana Aisha Amma Humaira ake kirana yace nice name toh malama Humaira ya "mutanan gida ya kuma school? Tace Lafiya Lau yace toh" madallah,


Yace Malama  Humaira nasan dai kingane wannan KO?

Ta kalli wurin da "Abdul-jabbar yake wanda shima din ita yake kallo,


 ido suka hada at the same time Abunda taji jiya shita karaji yau saboda haka saitai saurin dukar dakai kasa tareda cewa eh nagane sa,


Yace toh" dama munzo ne mu karabaki hakuri Akan abunda yafaru jiya don Allah a muna afuwa,

Sannan kuma idan ba damuwa munason kulla alaka tsakanin mu dake,

Wato Dan uwana ne yaji kin kwanta masa Arai tun lokacin daya ganki ma'ana yana sonki, saboda haka ne mukazo da kokon bararmu gareki dafatan za'a

 Amunta damu.?


Shuru tai ba tareda tace komai ba, Yace mlm Humaira kinyi shuru  bakice komai ba?


Tace toh ni mezan ce? yai dariya yace keko keda abuncewa, gaskiya bazan boye makiba dan'uwana yakamu da sonki lokaci daya don haka kinga dole zaiso yasan matsayinsa awurinki KO?


Tace toh kudan bani lokaci nai shawara, Yace kamar yaushe kenan? tace nanda sati biyu, Da sauri  yace two weeks fa ki kace!?


Ta kada Kai Wanda ita kanta bata San lokacin da tace  two weeks din ba, 

Shikam Abdul-jabbar cikin tsoron jin abunda tafada yasahi Kara zaro big eyes dinsa  waje, Y.Y.K yace haba Humaira sati biya ai yai yawa A yadda dan'uwana yakejinki aransa ai baza ya'iyayin sati biyu be gankiba,

Tace toh sati daya, Yace a ah inama dai laifin muzo gobe? ya fada yana mirgina kai, a ah ba gobe ba, toh" sai yaushe? tace jibi, yace beyi yawaba? tace a ah beyiba,


Yace toh shikenan ba komai hakama da akai mana mungode kwaraida gaske,

Tace  sai anjima Y.Y.K Yace  toh a gaida su "Umma da yayan mu yafada yana murmushi itama murmushi tai tace to zasuji tajuya ta tafi.


Abdul-jabbar yabi bayanta da kallo,


Y.Y.K ya zungure sa tareda cewa Kai wannan wani irin kallo ne haka? sai kace Wanda yawarke makanta

Wannan aisai kasa ta buga tuntube tafadi, tun dazu kake kallo ta da wannan kwala-kwalan idon naka kamar na mage kilama Shiya takasa sakin jiki tai magana, yakai karshen maganar dayin dariya.


Shima Abdul-jabbar dariya yake yace Amma dai Nawa da  sharri kake, yanzu saboda Allah idona ne kwala- kwala kamar Na mage?


Cikin zayala Yace eh koba haka sukeba? barima Allah yasa idan muka dawo jibin tace bakai mataba, saboda kafaye kato  sannan kuma idanun ka kwala-kwala.


Aikam me Abdul-jabbar zaiyi inba dariya ba hada rike ciki yadan tsaya dayin dariya yace ba Amin ba,aizata soni da yaddan  Allah kuma "DA SANNU" kuma zata gane irin kaunar danake mata.


Y.Y.K yace bani key kagani najamu kai kam  yau naga Happy yacika maka ciki so ba lallai bane ka'iya driving din'mu.


Yajefa masa key tareda cewa ai kaidin ne  Wallahi ko mutun beyi niyar dariya ba sai kasa sa,



Yai dariya yace Nawa kenan duk kawani rikicewa datace two weeks,yace aidole Na rikice ba kasan yadda nakejinta araina bane shiyasa.


Yace Hmmm ni mamaki kake bani ban taba zaton zaka mato akan san ya mace ba wallahi, a yadda naga mace bata gabanka kuma komai kyanta Amma sai gashi naga wannan kanata rawar jiki a kanta,


Koda yake gaskiya nayaba da "Humaira kyakkyawar ce gatada nutsuwa da alama tarbiya yaratsata, gata Da sanyin murya  kawai dai ka'iya zabe konace kayi dace saidai ace Allah ya tabbatar Da Alkhairi.



Abdul-jabbar dadi yaji aransa Yace amin,  Amma afili kuma sai yace Kai Nawa tun bata yai accept dinba tukun idan tace banyi mataba fa?



Yace Ah' haba dai wane ita santalelen saurayi kamar ka zatace bakai mata ba? Ai banga wannan macen ba tukun, haka sukaci gaba da tattaunawa akan "Humaira.


**************


Koda "Humaira tashiga gida da ta iske "Umma zaune akan tabarma ta, karasa kusada ita  ta zauna tareda cewa sannu Umma.


Ta amsa da yauwa sannu najiki shuru Lafiya dai KO?


Humaira tace Lafiya lau toh suwaye kene man "Abban Ku?


Takauda Kai gefe sannan tace aiba wurin "Abba suka zoba, 


Toh" wurin wasu kazo?  batare data kalli Umman  tace wai wurina sukazo,


Da saurii Umma tace  toh Lafiya dasukazo wurin ki?


Tace Mutumin nan ne fa najiya daya watsa mun kwata,


Oho toh mai kuma yakawosa? wai yazune yasake bani Hakuri,(ba tafada mata daya abunda ya kawo sunaba saboda tanajin kunya) 


Umma tace toh ke meki kace masu?   ta Dan tabe baki kadan tace ainace masu ba komai  na Hakura.


Umma tace ai haka yana Da kyau duk abunda mutun yai maka kayi hakuri  kada karikesa a zuciyar ka, saboda   Riko ba kyau ko zalintarka akai to kayi hakuri "DA SANNU" Allah yai maka sakayya.


Bayan kwana biyu.

************

Da misalin karfe 8:30 nadare Abdul-jabbar yai parking motar sa akofar gidan su "Humaira


Shika daya ne batare Da "Y.Y.K  yana Zane acikin mota be fitoba saidai yabude kofar motar ya fitoda kada daya waje dayar kuma tana daga ciki, hannun wansa duk suna kan  sitiyarin motar.


Wani yaro ne yazo ta kusada shi zai wuce da sauri yace salamu'alaikum abokina yakake?

Yaron yanarike da Allo ahannun sa Da Alama daka makaranta yake, ya Amsa salamar tareda tsayawa.


Abdul-jabbar yace abokina zaka tafi makaranta ne ko katasone? Yaro yace eh natasone, toh ya karatu? yace Lafia qalau toh" madallah, don Allah shiga gidan nan kace Abdul-jabbar yana sallama da "Humaira kaji? Yace toh.


Salama'alaikum wa'alaikassalamu, Umma ta amsa masa yace wai ana sallama Da "Humaira inji "Abdul-jabbar tace toh" gashi kuma bata ta tafi islamiyya Amma dai tabar sako tace idan yazo Abasa bari Na dauko maka adai dai lokacin da take shiga daki, jimawa kadan tafito hannun ta dauke da takarda tace ungo kakai masa yaron yakarba tareda cewa toh"


Koda yaron yafito yace masa ance ta tafi islamiyya Amma gashi tace idan kazo abaka yafada tareda mika masa takarda,


Abdul-jabbar ya karba yace nagode abokina ungo wannan yaciro kudi Daga ajihusa yamika masa yaron yarba yace nagode yatafi.


Shikam Abdul-jabbar bayan  yaron yatafi sai yakoma cikin mota ya zauna tareda bude  takarda yafara karatawa kamar haka.?





💐💞LUFHAT Luv your FANS ALL💞💐

💐💐💞💞           💞💞💐💐                                 

DA SANNU

💐💐💞💞

💞💞💐💐


                     💞Page46-50💐



              NA



💐MEENAT 💞UMAR FARUQ💐




edited by Zainuddeen zain



-----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION



PEN:THE STRONGEST WEAPON

-----------------------------------------



only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers




✍🏾





ABDUL-JABBAR

 Kana Lafiya ya gida da abokinka?  nayi tunani kuma Na Amince Allah ya tabbatar DA Alkhairi tsakanimu, saidai Na tsani abu biyu cin Amana da yaudara so please don't try to inter it our relationship between u and me please,

 daga "Aisha Mahmoud (Humaira).


Ya karanta takarda yafi akirga yai murmushi tareda girgiza Kai yace   "Humaira kenan  insha'Allahu bazaki taba samuna da daya daga cikin abunda kika fadaba saboda nima natsani cin Amana da yaudara, yajuya yashiga mota yatayar yatafi zuciyar sa cike fari ciki da kuma kaunar "Humaira ziryan Ahankali yake driving harya isa gida.


Washe gari da misalin 10:15am suna  zaune a karkashi bishiyar mangoro basu dade dafitowa break fast ba su uku ne "Humaira ce tareda best friends dinta "Haleema Abubakar da "Hannatu Umar,


"wayanda batada kamarsu, kamar yanda Humaira take batada rigima  suma haka suke, Toh" dama malam ba haushe yace sai hali yazo daya ake abota toh" haka ne yakasace tsakanin Humaira da kawayanta,(saidai wani Lokacin sunada tsokar fada especially Hanah) sunshaku da juna sosai  saboda tsananin shakuwarsu yasa tunbayan da "Humaira takoma government school,


 Sai suma suka matsawa "iyayansu da amaidasu government school din da aka maida "Humaira saboda bazasu iya cigabada zuwa school din batareda "Humaira ba kasan cewa dama tare suke achan private school din wannan shine dalilin dawo warsu wannan school din,


Kawancen nasu yasamo asaline tun suna primary school gashi yanzu suna secondary s s two,kuma iyayan suma sunsan da zaman  wannan   kawance nasu  mai tsafta wace ba gulma ba ha'inci duk dasun kasan ce su uku Amma hakan baisa suna munafurtan junansu ba, 


Kusan komai tare sukeyi ko abincin school matare sukeci Wanda suka tsaraayisa idan yau  "Humaira takawo gobe "Haleema takawo jibi kuma "Hannatu takawo, toh kamar yauma "Humaira ce takawo.


Wani kula ne  dan madai-dai ci mai kyau A gabansu soyayyen Dankalin Hausa ne da miyar tumatur(stew) aciki,

Hannah tace Humeeh      (kasan cewa haka suke kiran junansu Hannah; Humeeh; Haleeh;).


Gaskiya miyar dankalin nan is too sweet inji cewar Hannah, Haleeh tace Ai "Umma ta iya miya sosai wallahi Humeeh tai murmushi tace kudai kun cika santi wallahi sai kace yau kukafara cin girkin "Umma,


Haleeh tadan harare ta kadan cikin wasa tace toh" munji muncika santi din toh" ai miyar tayi dadin daza ai santi ne koh meh kikace ne Miss "D"?

("Doctor I S G saurayin Hanah ne da suhadu Asibitin sa  lokacin da Hajiya "Hafsat mahaifiyar Hannah batada Lafiya "Toh" Cikin Ikon Allah soyayya tashiga tsakanin Hanah da "Doctor I S G"  Wanda hartakai ga manya sunsan da soyayyan tasu yanzu hakama anajirane dasun gama school asha biki,Ita da  "D" din Nata.


Hannah tai dariya tareda daga babban yatsanta alamar jinjina tace godiya nake

kinsan tukuicin ki? 


 Haleeh tace A ah' saikin fada tace zance my "D"yai maki Allura talatin takara she maganar Da kanne mata ido daya,

Humeeh tace Wanda bature bai'iyaba,


Haleeh taro ido   tace wayyo Allah Na! yadai yimaki keda zaki zama matarsa,


 Humeeh tai dariya tace kinji tsorone?


 Haleeh tace ke ya bazanji tsoro! ba 30 injection wasa ne

tabdi badani ba wallah


Hannah tana dariya tace wai kuturun gada arama bah


Sukai dariya gaba dayansu tareda hada baki  sukace "eh mana",


Humeeh tace Hmmm kunsan mai yafaru? sukace sai kin fada"  tace ina mutumin nan daya watsa mun kwata shekaran jiya har banzo school ranan  bah?

(Kasan cewa tafada masu abunda yafaru tsakanin ta da "Abdul-jabbar)


Nan dai tasake basu Labarin zuwansu "Abdul-jabbar jiya gidansu tareda abokinsa Y Y k,


Sukam mamakin ta suke saboda yadda ta takarkare tanata koda mutumin da ta hadudashi jiya-jiya Hmmm lallai da Alama dai wannan mutumin yasamu babba matsayi azuciyarta.


Haleeh "ta zungurin Hanah suka hada ido sukai Dariya sannan  sukace eyeeeeeh lallai da Alama wannan guy din yasamu shiga Toh" ya sunansa? 

 

Humeeh tai fari da'ido sannan tace sunansa  Abdul-jabbar abokinsa kuma "Yusuf Amma yace Y Y K ake  kiransa,


Sukace "eh mana" gaba dayansu,  Humeeh tace Ku gaskiya guy din yahadu sosai,


Sukace ah"! haba dai ? tace  Allah Kuwa bakugan sabane bafa kyakkyawa  dashi ga hanci kamar karas shidin Ai special ne wallahi, sukace Au Allah ?  tace sosai makuwa, nan dai tafara wassafa masu kaman ninsa,


Hakanan sukaci gabada fira wadda Rabin firar duk ta "Abdul-jabbar ce har zuwa lokacin da aka buga komawa class sannan suka tashi suka nufi class dinsu.


*****************

Cikin lokaci kankani Soyayya mai  tsanani  tashiga tsakanin  "Abdul-jabbar da "Humaira  son junansu suke sosai hartakai daya baya iya yini batareda yaga daya ba  abun nasu gwanin sha'awa, idan kagansu sai karantse sun shekara tare, yanzu bafada tsakanisa da Yah Himu saidai mutunci.


Tun'wani Rana dayazo week ya iskosu 

Suna zaune akan dakali suna fira a lokacin ma tuni sundade dasha kuwa dajuna,


 sai ga yah Himu zaya shiga gida da sauri Abdul-jabbar yamike tsaye yai masa sallama tareda mikamsa Hunnu shima yah Himu hannun yamika masa suka gaisa fuskarta nan ba walwala sannan yashiga gida.


Daga zaure ya kwalama Humaira" Kira dasauri ta tashi tashiga zaure yana tsaye ransa abace yace ke me yakawo wanga guy din  nan

gurinki?

 

Cikin jin tsoro tace ayya ! yazo sake bani Hakuri ne,


Cikin hade fusta yace toh" sai me kuma?


Tai shiru kanta nakasa tana wasada yatsun hannunta batare da tace komai ba,


Yadaka mata tsawa  yace Ina magana kinyi mun shiru ko bakiji abunda nafada bane?


Cikin tsoro  da ha'gwaba tareda turo baki tace wayyo ! yace nefa yana sona, 


DA sauri yace what?

tace eh kuma fa yanada kirki sosai


Ido yah Himu yazaro

Cikin mamaki! yace keh Ashanty har yaushe kika sanshi daki kagane cewa yanada kirki?


Ta turo baki tace toh" ai yadade yana zuwa tunfa lokacin daka koma school 


Ido yasake zarowa yace yadade fa kikace?

Tace eh, sai ya sassauta murya Yace toh ke kina son sa?

Fuskarta tarufe datafin Hannun ta sannan tadaga Kai alama eh,

Yai shiru yana kallon ta kawai sai yaji tabasa tausayi ganin Cikin lokaci kankani takamu dason guy din, (aransa kam fadi yake Allah yasa ba'irin mayaudaran samarin nan bane) sai Yace toh" shikenan Amma fa kikula bana son Abunda zaya cuta makine shiyasa bakomai kije yana jiranki.


 tace toh yah Himu nagode.


***************

Ahankali yake driving yana sararon kira'ar sheikh Ahmed Sulaiman cikin suratu Kahf kasan cewar yau jumma'a (toh dama yasaba duk ranan jumma'a bayan ya karanta suratul kahf toh" sai kuma ya wuni yana sauraren kira'ar yana kuma bi)Abdul-jabbar kenan, cikin nutsuwa ya kalli agogon hannun sa yaga 5:00pm yai murmushi a dai dai lokacin dayake kokarin shiga layin gidan su "Humaira.


Karar Hon din sane ya tabbatar mata dacewa (specia dinta yazo kamar yanda take kiransa).

Lallausan murmushi tasaki tareda daukan Hijab dinta fari toh" dama already ashirye take tana sanye da jallabiya ne baka mai dogon hannu rigar tasama ta matse saikuma  tabude takasa saboda haka sai kawai ta sake kallon kanta a mirror ta gyara zaman hijab dinta sannan tafito daga dakin.


 ta kalli "Umma dake zaune akan tabarma tana tsintar shinkafa yar Hausa, Ahankali tace sannu Umma da Aiki?


Umma tadago dakai ta kalleta  tareda cewa yau sannu Umma tace sai Ina haka kuma?


Humaira cikin jin kunya tagukar da Kai kasa tana murza yatsunta ahankali tace um! um!! um!!! Da! Dam!!


Umma ta katseta dacewa dama "Abdul-jabbar ne yazo KO?

Humaira da kanta ke kasa tace eh,

Murmushi Umma tai sannan tace sai kindawo Amma fa ki kulada kanki sannan kada kidade kinji ko?  

Tace toh Umma tafita, girgiza Kai Umma tai tareda bin bayan ta da kallo, ita kam mamaki take yanda Humaira take son wannan yaro haka, wadda ko sauraren samari batayi Amma sai gashi ta saurari wannan,

Tace hmm toh Allah ya zaba mana abunda yafi zama Alkhairi.


Labewa tai abayan kofar zauren gidan ta kusurwar kofar take  hangen sa,


Zaune yake a kan dakali ya juyo bayan sa yana sanye da tsararriyar shadda fara kasan ba hula, gashin kansa sai kyalli yake gwanin sha'awa saida ta gama karemasa kallo sannan tafito tanufi gurinsa.


Kamshi turarenta yasanar dashi isowar ta Ahankali yadaga Kai ya kallo ta,


Hannuwan ta biyu tasa tarufe fuska cikin jin kunyarsa tace Assalamu'alaikum, my special one,


Ya Saki lallausan murmushi yace  wa'alaikassalamu my cool heart, yace barkada fitowa sarauniyar zuciya ta  ya nuna mata kusada shi alamar ta zauna,


bamusu ta zauna kusa dashi kadan,


Kamshin turaren sa Dana ta yahadu saboda haka sai yabada wani daddadan kamshi mai dadi,


Ahankali yace yaki ke" ya "Umma ta? 

Tace tana nan Lafiya lau toh" ya school din? Tace Alhamdullah yace yayi kyau,


Yace ko kunji motsin Yah "Himu? tace eh yana nan Lafiya Yace is good, toh" meye Labari?  tai  murmushi Cikin jin kunya tace umh! ba wani labari, shima  murmushi yai yace Ah haba dai? tace Allah kuwa, yace toh"bani labarin Hanah da Haleeh (yasan batada wani magana datawuce nasu Hanah DA Haleeh, wani abun kuma shine har yanzu basu hadu da "Hanah Da "Haleeh da Abdul-jabbar ba).


Aikam nan tashiga bashi labarin "Hanah Da "Haleeh.


Dariya yake sosai sakama konjin sunan Da "Hannah tasa ma wata senior   (saboda waita aiki Hanah tasawo mata yoghurt toh kadata je yoghurt din yakara shine tai ma Hanah bulala biyar wai aita tsaya wasane shiyasa ba tasawo mata  yoghurt din ba).


Toh" fa shikenan Hanah tasa mata suna wai mai tafiyar agwagwa,


Ya tsaya dayin dariya yace my cool Hanah bataji tsoro kada wata Rana tajita tasake yimata bulalar datafi wadda  tai mata abaya?


Tace oho mata nibasan Irin Hanah ba ita batada tsoro Sam,


Hakanan sukaci gabada firarsu Cikin soda kaunar juna Wanda Rabin firar duk a kan Haleeh da Hanah ( A hankali  yafa himmci cewa Hanah da Haleeh sunada matsayi mai girma a zuciyar ta) har misalin karfe shida na yamma.


Ya tashi yace ina zuwa yanufi motar sa jim kadan sai gashi yadawo hannun sa rike da wata firar leda saida ya zauna sannan yamika mata ledar,


Mamaki ne yakamasa saboda kin karban ledan datai ya kalleta yace A ah ungo mana,


Ahankali tasa hannun biyu ta karba tace na meye? batareda ya kalleta ba yace kiduba mana,


Koda "taduba sai taga kwalin Waya Tecno yace kiduba akwai Sim card aciki nasa number ta saida gaskiya banyarda kisaka number kowa acikin ba musamman ma ta namiji  saidai ta yah "Himu kawai sai kuma nasu "Hanah da "Haleeh,


Ya kalli agogon hannunsa yaga 60:30pm yamike tsaye tare da cewa zantafi  itama tamike tsaye tace nagode Allah yasaka da Alkhairi ina gaida "Mama da baba "Lami yace OK zasuji,


Saida taga tafiyar sa sannan tashiga gida zuciyar ta cike Da kaunar special dinta.





💐LUFHAT Luv your All FAN💞

💞💞💐💐                       💐💐💞💞

DA SANNU

💐💐💞💞

💞💞💐💐


                       Page46-50  



              NA



💐MEENAT 💞UMAR FARUQ💐




edited by Zainuddeen zain



-----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION



PEN:THE STRONGEST WEAPON

-----------------------------------------



only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers




✍🏾





ABDUL-JABBAR

 Kana Lafiya ya gida da abokinka?  nayi tunani kuma Na Amince Allah ya tabbatar DA Alkhairi tsakanimu, saidai Na tsani abu biyu cin Amana da yaudara so please don't try to inter it our relationship between u and me please,

 daga "Aisha Mahmoud (Humaira).


Ya karanta takarda yafi akirga yai murmushi tareda girgiza Kai yace   "Humaira kenan  insha'Allahu bazaki taba samuna da daya daga cikin abunda kika fadaba saboda nima natsani cin Amana da yaudara, yajuya yashiga mota yatayar yatafi zuciyar sa cike fari ciki da kuma kaunar "Humaira ziryan Ahankali yake driving harya isa gida.


Washe gari da misalin 10:15am suna  zaune a karkashi bishiyar mangoro basu dade dafitowa break fast ba su uku ne "Humaira ce tareda best friends dinta "Haleema Abubakar da "Hannatu Umar,


"wayanda batada kamarsu, kamar yanda Humaira take batada rigima  suma haka suke, Toh" dama malam ba haushe yace sai hali yazo daya ake abota toh" haka ne yakasace tsakanin Humaira da kawayanta,(saidai wani Lokacin sunada tsokar fada especially Hanah) sunshaku da juna sosai  saboda tsananin shakuwarsu yasa tunbayan da "Humaira takoma government school,


 Sai suma suka matsawa "iyayansu da amaidasu government school din da aka maida "Humaira saboda bazasu iya cigabada zuwa school din batareda "Humaira ba kasan cewa dama tare suke achan private school din wannan shine dalilin dawo warsu wannan school din,


Kawancen nasu yasamo asaline tun suna primary school gashi yanzu suna secondary s s two,kuma iyayan suma sunsan da zaman  wannan   kawance nasu  mai tsafta wace ba gulma ba ha'inci duk dasun kasan ce su uku Amma hakan baisa suna munafurtan junansu ba, 


Kusan komai tare sukeyi ko abincin school matare sukeci Wanda suka tsaraayisa idan yau  "Humaira takawo gobe "Haleema takawo jibi kuma "Hannatu takawo, toh kamar yauma "Humaira ce takawo.


Wani kula ne  dan madai-dai ci mai kyau A gabansu soyayyen Dankalin Hausa ne da miyar tumatur(stew) aciki,

Hannah tace Humeeh      (kasan cewa haka suke kiran junansu Hannah; Humeeh; Haleeh;).


Gaskiya miyar dankalin nan is too sweet inji cewar Hannah, Haleeh tace Ai "Umma ta iya miya sosai wallahi Humeeh tai murmushi tace kudai kun cika santi wallahi sai kace yau kukafara cin girkin "Umma,


Haleeh tadan harare ta kadan cikin wasa tace toh" munji muncika santi din toh" ai miyar tayi dadin daza ai santi ne koh meh kikace ne Miss "D"?

("Doctor I S G saurayin Hanah ne da suhadu Asibitin sa  lokacin da Hajiya "Hafsat mahaifiyar Hannah batada Lafiya "Toh" Cikin Ikon Allah soyayya tashiga tsakanin Hanah da "Doctor I S G"  Wanda hartakai ga manya sunsan da soyayyan tasu yanzu hakama anajirane dasun gama school asha biki,Ita da  "D" din Nata.


Hannah tai dariya tareda daga babban yatsanta alamar jinjina tace godiya nake

kinsan tukuicin ki? 


 Haleeh tace A ah' saikin fada tace zance my "D"yai maki Allura talatin takara she maganar Da kanne mata ido daya,

Humeeh tace Wanda bature bai'iyaba,


Haleeh taro ido   tace wayyo Allah Na! yadai yimaki keda zaki zama matarsa,


 Humeeh tai dariya tace kinji tsorone?


 Haleeh tace ke ya bazanji tsoro! ba 30 injection wasa ne

tabdi badani ba wallah


Hannah tana dariya tace wai kuturun gada arama bah


Sukai dariya gaba dayansu tareda hada baki  sukace "eh mana",


Humeeh tace Hmmm kunsan mai yafaru? sukace sai kin fada"  tace ina mutumin nan daya watsa mun kwata shekaran jiya har banzo school ranan  bah?

(Kasan cewa tafada masu abunda yafaru tsakanin ta da "Abdul-jabbar)


Nan dai tasake basu Labarin zuwansu "Abdul-jabbar jiya gidansu tareda abokinsa Y Y k,


Sukam mamakin ta suke saboda yadda ta takarkare tanata koda mutumin da ta hadudashi jiya-jiya Hmmm lallai da Alama dai wannan mutumin yasamu babba matsayi azuciyarta.


Haleeh "ta zungurin Hanah suka hada ido sukai Dariya sannan  sukace eyeeeeeh lallai da Alama wannan guy din yasamu shiga Toh" ya sunansa? 

 

Humeeh tai fari da'ido sannan tace sunansa  Abdul-jabbar abokinsa kuma "Yusuf Amma yace Y Y K ake  kiransa,


Sukace "eh mana" gaba dayansu,  Humeeh tace Ku gaskiya guy din yahadu sosai,


Sukace ah"! haba dai ? tace  Allah Kuwa bakugan sabane bafa kyakkyawa  dashi ga hanci kamar karas shidin Ai special ne wallahi, sukace Au Allah ?  tace sosai makuwa, nan dai tafara wassafa masu kaman ninsa,


Hakanan sukaci gabada fira wadda Rabin firar duk ta "Abdul-jabbar ce har zuwa lokacin da aka buga komawa class sannan suka tashi suka nufi class dinsu.


*****************

Cikin lokaci kankani Soyayya mai  tsanani  tashiga tsakanin  "Abdul-jabbar da "Humaira  son junansu suke sosai hartakai daya baya iya yini batareda yaga daya ba  abun nasu gwanin sha'awa, idan kagansu sai karantse sun shekara tare, yanzu bafada tsakanisa da Yah Himu saidai mutunci.


Tun'wani Rana dayazo week ya iskosu 

Suna zaune akan dakali suna fira a lokacin ma tuni sundade dasha kuwa dajuna,


 sai ga yah Himu zaya shiga gida da sauri Abdul-jabbar yamike tsaye yai masa sallama tareda mikamsa Hunnu shima yah Himu hannun yamika masa suka gaisa fuskarta nan ba walwala sannan yashiga gida.


Daga zaure ya kwalama Humaira" Kira dasauri ta tashi tashiga zaure yana tsaye ransa abace yace ke me yakawo wanga guy din  nan

gurinki?

 

Cikin jin tsoro tace eyya ! yazo sake bani Hakuri ne fa.


Cikin hade fusta yace toh" sai me kuma?


Tai shiru kanta nakasa tana wasada yatsun hannunta batare da tace komai ba,


Yadaka mata tsawa  yace Ina magana kinyi mun shiru ko bakiji abunda nafada bane?


Cikin tsoro  da ha'gwaba tareda turo baki tace wayyo ! yace nefa yana sona, 


DA sauri yace what?

tace eh kuma fa yanada kirki so sai


Ido yah Himu yazaro

Cikin mamaki! yace keh Ashanty har yaushe kika sanshi daki kagane cewa yanada kirki?


Ta turo baki tace toh" ai yadade yana zuwa tunfa lokacin daka koma school 


Ido yasake zarowa yace yadade fa kikace?

Tace eh, sai ya sassauta murya Yace toh ke kina son sa?

Fuskarta tarufe datafin Hannun ta sannan tadaga Kai alama eh,

Yai shiru yana kallon ta kawai sai yaji tabasa tausayi ganin Cikin lokaci kankani takamu dason guy din, (aransa kam fadi yake Allah yasa ba'irin mayaudaran samarin nan bane) sai Yace toh" shikenan Amma fa kikula bana son Abunda zaya cuta makine shiyasa bakomai kije yana jiranki.


 tace toh yah Himu nagode.


***************

Ahankali yake driving yana sararon kira'ar sheikh Ahmed Sulaiman cikin suratu Kahf kasan cewar yau jumma'a (toh dama yasaba duk ranan jumma'a bayan ya karanta suratul kahf toh" sai kuma ya wuni yana sauraren kira'ar yana kuma bi)Abdul-jabbar kenan, cikin nutsuwa ya kalli agogon hannun sa yaga 5:00pm yai murmushi a dai dai lokacin dayake kokarin shiga layin gidan su "Humaira.


Karar Hon din sane ya tabbatar mata dacewa (specia dinta yazo kamar yanda take kiransa).

Lallausan murmushi tasaki tareda daukan Hijab dinta fari toh" dama already ashirye take tana sanye da jallabiya ne baka mai dogon hannu rigar tasama ta matse saikuma  tabude takasa saboda haka sai kawai ta sake kallon kanta a mirror ta gyara zaman hijab dinta sannan tafito daga dakin.


 ta kalli "Umma dake zaune akan tabarma tana tsintar shinkafa yar Hausa, Ahankali tace sannu Umma da Aiki?


Umma tadago dakai ta kalleta  tareda cewa yau sannu Umma tace sai Ina haka kuma?


Humaira cikin jin kunya tagukar da Kai kasa tana murza yatsunta ahankali tace um! um!! um!!! Da! Dam!!


Umma ta katseta dacewa dama "Abdul-jabbar ne yazo KO?

Humaira da kanta ke kasa tace eh,

Murmushi Umma tai sannan tace sai kindawo Amma fa ki kulada kanki sannan kada kidade kinji ko?  

Tace toh Umma tafita, girgiza Kai Umma tai tareda bin bayan ta da kallo, ita kam mamaki take yanda Humaira take son wannan yaro haka, wadda ko sauraren samari batayi Amma sai gashi ta saurari wannan,

Tace hmm toh Allah ya zaba mana abunda yafi zama Alkhairi.


Labewa tai abayan kofar zauren gidan ta kusurwar kofar take  hangen sa,


Zaune yake a kan dakali ya juyo bayan sa yana sanye da tsararriyar shadda fara kasan ba hula, gashin kansa sai kyalli yake gwanin sha'awa saida ta gama karemasa kallo sannan tafito tanufi gurinsa.


Kamshi turarenta yasanar dashi isowar ta Ahankali yadaga Kai ya kallo ta,


Hannuwan ta biyu tasa tarufe fuska cikin jin kunyarsa tace Assalamu'alaikum, my special one,


Ya Saki lallausan murmushi yace  wa'alaikassalamu my cool heart, yace barkada fitowa sarauniyar zuciya ta  ya nuna mata kusada shi alamar ta zauna,


bamusu ta zauna kusa dashi kadan,


Kamshin turaren sa Dana ta yahadu saboda haka sai yabada wani daddadan kamshi mai dadi,


Ahankali yace yaki ke" ya "Umma ta? 

Tace tana nan Lafiya lau toh" ya school din? Tace Alhamdullah yace yayi kyau,


Yace ko kunji motsin Yah "Himu? tace eh yana nan Lafiya Yace is good, toh" meye Labari?  tai  murmushi Cikin jin kunya tace umh! ba wani labari, shima  murmushi yai yace Ah haba dai? tace Allah kuwa, yace toh"bani labarin Hanah da Haleeh (yasan batada wani magana datawuce nasu Hanah DA Haleeh, wani abun kuma shine har yanzu basu hadu da "Hanah Da "Haleeh da Abdul-jabbar ba).


Aikam nan tashiga bashi labarin "Hanah Da "Haleeh.


Dariya yake sosai sakama konjin sunan Da "Hannah tasa ma wata senior   (saboda waita aiki Hanah tasawo mata yoghurt toh kadata je yoghurt din yakara shine tai ma Hanah bulala biyar wai aita tsaya wasane shiyasa ba tasawo mata  yoghurt din ba).


Toh" fa shikenan Hanah tasa mata suna wai mai tafiyar agwagwa,


Ya tsaya dayin dariya yace my cool Hanah bataji tsoro kada wata Rana tajita tasake yimata bulalar datafi wadda  tai mata abaya?


Tace oho mata nibasan Irin Hanah ba ita batada tsoro Sam,


Hakanan sukaci gabada firarsu Cikin soda kaunar juna Wanda Rabin firar duk a kan Haleeh da Hanah ( A hankali  yafa himmci cewa Hanah da Haleeh sunada matsayi mai girma a zuciyar ta) har misalin karfe shida na yamma.


Ya tashi yace ina zuwa yanufi motar sa jim kadan sai gashi yadawo hannun sa rike da wata firar leda saida ya zauna sannan yamika mata ledar,


Mamaki ne yakamasa saboda kin karban ledan datai ya kalleta yace A ah ungo mana,


Ahankali tasa hannun biyu ta karba tace na meye? batareda ya kalleta ba yace kiduba mana,


Koda "taduba sai taga kwalin Waya Tecno yace kiduba akwai Sim card aciki nasa number ta saida gaskiya banyarda kisaka number kowa acikin ba musamman ma ta namiji  saidai ta yah "Himu kawai sai kuma nasu "Hanah da "Haleeh,


Ya kalli agogon hannunsa yaga 60:30pm yamike tsaye tare da cewa zantafi  itama tamike tsaye tace nagode Allah yasaka da Alkhairi ina gaida "Mama da baba "Lami yace OK zasuji,


Saida taga tafiyar sa sannan tashiga gida zuciyar ta cike Da kaunar special dinta....





💐LUFHAT Luv your All FAN💞

💐💐💞💞

💞💞💐💐

DA SANNU

💞💞💐💐

💐💐💞💞


            Page51-55



             NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

               OR

             (MEENAT)




edited by Zainuddeen zain



------------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION



PEN:THE STRONGEST WEAPON

------------------------------------------



only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers





✍🏾





Koda Humeeh tashiga gida ta iske Umma bakin murhu ta nayi masu girkin dare,

Dakin tashiga tacire hijab dinta tareda  ajiye wayar sannan tafito don ta taya Umma Aiki.

 

Bayan sallah magrib   suna zaune abinci sukeci akwano guda Humeeh itada Ummanta, bayan sungama ne sai Humeeh ta tattara kwanoni takai su kicin  ta'ajiye. bayan tadawo sai tashiga daki tadauko wayar da "Abdul-jabbar yabata  bayan ta zauna ne saita mikawa Umma wayar tareda yimata bayani....


Shuru Umma tai tareda jujjuwa wayar   sannan tace toh" Humaira nifa bana san karbe-kaben kayan samari, tsayama dai tukun na inafata dai ba rokon sa ki kayiba?


 Da sauri Humaira tace a ah Umma niban rokesa" ba, Umma tace ah toh" domin ni gaskiya  banason roko saboda yana zubarda kima da darajar  ya'mace a idon samari.

Allah Umma ni barokonsa naiba shi yabani dakansa,

Toh" shikenan yanzu abinda nakeso dake shine kibari yayan kin" yazo saimusan yadda za'ai kinji KO?


 Murmushi Humeeh tayi tace toh" Ummana yanda duk kikace haka za'ai,


 haka suka cigaba da  hira har aka kira sallar isha'i suka tafi yin sallah.



*****************

Koda yah Himu yazo week Umma tayi masa bayanin kan wayar Da "Abdul-jabbar yaba Humeeh, baice komai ba... saidai yace abata tayi amfani dashi saidai  takula dakainta tatsare mutuncinta.


Toh tunda ga wannan lokacin kuma sai soyayyar su itada "Abdul-jabbar yakara karfi,

 

Koda yaushe suna makale awaya KO Abdul-jabbar baige gidansu Humeeh toh" za'asha soyayya tawaya,

Sun shakuda juna sosai har sunajin idan daya yarasa daya tofa sai a slow,


Ah soyayya sukeyi kamar bagobe suna tsaka da Soyayyarsu kwatsan  sai wani lamari ya shiga masu.


Wata Rana Abdul-jabbar yaje gurin Humeeh bayan sun sha hirarsu Wanda aran nan hada Hanah akayi hirar kasan cewar sunzo, saida ita Haleeh ta tafi gida dawuri saboda Hajiyar ta tace takoma gida  dawuri zatayi mata aiki saboda haka sai bata dadeba ta tafi  don hakane ma bataga Abdul-jabbar din ba. sai Hanah ce kawai tagansa"

Suna cikin hira sai Hannah tace zata tafi gida bayan tafiyar "Hannah  da dan mituna kadan sai shima Abdul-jabbar yatafi,



Yana kulle kofar mota sai yaji wata murya abayansa tamkar ta mashaya tace ya kake? Bai juyaba saboda a tunanin sa ba dashi akeba,


Jiyayi ansake fadar ya kake? saboda haka sai yajuya don yaga wakeda wannan murya haka irin ta mayashaya,


Aikam yayi arbada wata yarinya tana sanye da wata Riga body hook da kuma minin siket kafarta sanye Da wani high shoe tarataya  kwankan gefe, kanta yaci uban atterch jiki shaya belicin yagaji ga farce zaro-zaro sun sha janfarce fuskar nanko tasha makeup ba kyan kallo. Amma ita kam agurin ta tahadu batada wani fasali sai kace sandar sunuka.


Bayan yakare mata kallo sai kuma yafara tunani aransa wannan kuma wacece haka?


Katse masa tunanin tayi dacewa baka ganeni bane?


Ya kalleta fuskarsa ayamutse yace inafa naganeki,

 keh' nibanma taba ganin ki ba sai yau,


Tace Lah kodai kamanta dani?  yace  eh toh' da alama Na manta dake kam.


Tayi wani yake wanshi dariya tace yoh nice fa Lariya,


Ya tabe baki tareda kauda kai gefe yace toh" Lariya  ta'ina kenan?


Dariya tasake yin tace Lah! Kai Abdul-jabbar haryanzu baka tunaniba ?


(Aransa yace ai mutanan kwarar ake tunawa ba'irin kuba), afilikuma cikin kosawa da maganar Yace Ayyah ban tunakiba?



Tace yoh nice" fa Lariya yar Hajiya "Jumma.


Yace oh! Allah sarki toh"sannu fa ya Hajiyar taki take?


Tace Lafiya lau  i tacema tace nazo nagaida Hajiya A'i,


Yace toh" Sannu da kokari ki gaisheta, yafada yana kokarin shiga cikin gida.


tace Abdul-jabbar yajuyo batare da ya" amsa, takarasa wurin sa har jikinta yana kokarin gogar nasa jikin.


Dasauri yaja baya domin kuwa wani irin Kari yaji tanayi, 


Dariya tayi tareda cewa Abdul-jabbar kanada kyau fa,  hannun ta mika  danufin shafo kyakkyawan  shajansa tace Inason irin wannan abun yanada kya!


Wani uban tsawa yadaka mata Wanda yasatai sauri sauke  hannun ta, harara ya watsa mata cikin takaici Yace keh! dalla gafara meye haka? 

Batace komai ba saidai ido data tsura masa. 


Harara yasake watsa mata tareada jan dogon tsaki mtsww.


 sannan ya juyawa yanufi gida cikin takaici domin gaba daya tabasa haushi,cikin rai sakuma yace dafa da wannan kazamin Hannun nata" zata tabani Kai! Amma da tacuceni, yayi kwaf dai-dai lokacin yake bude kofar dakin sa.


Wayarsa ce tayi kara dasauri yaduba sunan daya ganine yasa yai lallausan murmushi. bariyai saida ta katse sannan yakira tareda bude sifika A hankali ya lumshe ido yace my cool yakike?

Cikin zazzakar voice dinta tace Lafiya lau dama Inason naji yaka isa gida?


Yace Lafiya lau Na isa kingama yanzu Na shiga daki.

Tace toh ka huta lafiya ka kuma gaida "Mama da baba "Lami,

Yace ai bazan fadaba. dasuri tace why?

yace kullun fa cewa kike Na gaida su" ya sassauta murya yace please My cool kizo kidai dasu mana dakanki kinji?


A hankali tace nifa kunya nakeji Amma dai zanzo.

Da sauri yace yaushe zakizo?


 Tace zanzo  very soon Amma dai yanzu kace in gaida su.

 yace toh" zasuji tunda kin kizuwa nima kigaidamun da "Ummata tace toh" zataji, sanna sukai sallama ya kashe wayar tareda jefata saman gado sannan yanufi Cikin gida.



Tundaga zaure  Lariya take kukan Sangarta tana shiga Cikin gida  sai tafara jifa da jakarta da kuma takalmanta, sannan tayi zaman yan'bori a tsakar gida sai kuma tasaki wani kuka Mara dadin saurare.


Da sauri Mahaifiyarta Hajiya jumma tafito daga daki, hartana buga tun-tube da bakin kofa zani a hannun dankwali a hannun. 


 Da sauri tanufi gurin yartata tadafa kafadarta Cikin tashi  hankali tace Lariri ta maiyasa meki? mai akai maki ?

Taya mutsa fuska tareda tura hannun ta Cikin wannan danbanzan gashin dokin tana yamutawa  (nabakin tsofaffi )  sannan tace Hajiya ni aure nakeso.


Ajiyar Zuciya Hajiya Jumma tasauke, tace haba Lariri aini Na dauka wani abun akai maki.


 Sai kuma

 tawashe dafaffun hakoranta wai ita adole dariya take tace A ah abu mai sauki aini nan daki kagan'ni kullum fatana baiwuce naga auran kiba.


Taso zonan kafada Mani kinsamu Wanda kikesone?


Saman wani banci suka zauna Hajiya jumma ido ta tsurama yartata tana neman Karin bayani, Lariya tace eh nasamu.


Tace toh"- toh" wanene shi? tace Abdul ne, tace wani Abdul din? tace Abdul-jabbar Dan wajan Hajiya A'i.


Aikam tasake washe bakin tace A ah kice tuwona maina za'ai kenan KO? 

ta daga Kai  alamar eh, tace toh" shiyace yana sanki? tace eh Ai mun kwana biyu muna Soyayya bandai fada maki bane saboda inajin kunya.


Nikam saboda Tsabar mamakin jin Abunda Lariya tafada harsaida birona yakusa fadiwa kasa, DA sauri narike tareda tsura mata ido ganin yadda take kauda kai gefe ita adole kunyar takeji

         

Tabdi sunan wani waishi "zubairu(ah ita" kam wannan zubairace)

            

  Hajiya Jumma ta  washe baki tareada dukanta" kadan akafada tace yar'nema kunyar me? shakuru minki indai "Abdul-jabbar ne kamar kin auresa'  gobe zanje nasamu Hajiya A'i sai mutsara yadda za'ai kinji KO? tace toh"

   


Nasan dai mai karatu zayaso yasan WACECE Hajiya Jumma tare DA yarta LARIYA, Hajiya Jumma mutumiyar Buruku ce tanan Cikin garin Kaduna Hajiya Jumma macece mai zaman kanta saboda San abun duniya yasa tabaro garin iyayanta Buruku tadawo nan Cikin kaduna dazama.


Hajiya Jumma irin matan nan ne masu auren Mutum badan Allah ba saidan Abun hannun shi batada wani kyau, asalima bakace  sosai gata batada hanci saidai kam tanada dirin Allah yaimata Kira mai kyau. 


Wanda dashi take cutar duk Wanda yace yana sonta dazar kace kana sonta toh" shikenan  saitabi boka DA Malam ta aure ka bayan ta aure ka idan kanada iyali sai tarabaka DA iyalinka, sannan ta mallakeka ta kuma rabaka da Abunda ka mallaka daga karshe kuma taraba ka da rainka Hajiya Jumma kenan muguwar mace ce ta iya shiga bokaye da Malamai sosai 


A hakanan ta mallaki dukiya mai  tarin yawa tasayi gida tasayi adai-dai tasahu har guda uku   take bada haya ana kawo mata kudi,


 kuma tana zuwa kano saro kaya su atanfofi dasu lesissika dadai sauransu. 


don haka Cikin lokacin kankani tayi kudi hartaje makka inda acan'ne suka hadu da Hajiya A'i mahaifiyar Abdul-jabbar suka kulla aminta.


 bayan sun dawo makka ne sai Hajiya Jumma taci gabada kasuwancin ta inda Allah ya hadata dawani Mutum mai suna Labaran, yanuna yana santa wani abun mamaki shine itama Allah ya jarabe tada navigate sanshi cikin lokaci kankanidon haka ba'adauki wani lokaci ba aka saura masu aure.


Bayan kwana biyu da yin aure sai Labara yazoma Hajiya Jumma da Labarin cewa anche Lagos tafi kano saukin kaya, saboda haka takawo kudi yaje yaraso mata kaya acan aikam saikace wadda yaima asiri(dayake yafahimci cewa itadin gurin kudi batada sauki) 


aikon tawashi kudin ta tabashi harda sayarda adai-dai sahunta guda biyu  duk tahada kudin tabashi yatafi.


Aure da Albarka

Bayan tafiya Labaran da sati uku sai Hajiya Jumma tafamci cewa tanada Ciki, 

Saboda haka murna kamar ya kasheta.


 Tunda duk aure-auren datayi bata taba haihuwa ba sai wannan, saboda haka saita maida hankalin ta gurin kulada Cikin ta.


Har Cikin ta yakai wata hudu ba Labaran ba labarinsa,

(Hmmm Abunda Hajiya Jumma bata saniba shine Labaran rikakken Dan cacane kuma mane min matane,

 don haka koda yaje Legos Abunda yai tayi kenan da kudin.


Saida Cikin ta yakai wata biyar sannan sai gashi yadawo, dawasu yankaya wayanda KO Rabin-rabin kudin daya yaje dasu basu Kai ba.


Aikam sun kwashi yan'Kallo domin kuwa mutane ta tara masa tana taimashi masifa  akan sai   yafito mata da kudin ta tunda bai saro mata kayan ba, sai faman masifa take bata kodamu DA Cikin dake jikinta ba.


Shikam dayake tantirin Dan duniya ne sai ya kalalla meta dace mata aikayan yana siya yana sayar wane acan kuma anasamun riba sosai.


yanzu  hakama yasiya yabarma abokinsa yakula masa dashi. yanzu ma Abunda yasa yazo saboda yanata tunanin ta dakuma mafarkinta shiyasa yazo don yaganta shine acikin  kayan  yataho mata da wannan.


Aikom sai tashiga washe baki ita adole miji yadamu da'ita, bayan kwana biyu yakoma.


Besake dawowa ba harta haihu inda tasamu ya"mace mai Kama DA babanta tasamata suna LARIYA" tasha wahala sosai godiyan ta guda adai- dai sahun da'akeyi mata haya Ana kawo mata kudi.


Saidai Lariya tashe Kara biyar sannan Labaran yadawo batare dakomai ba DA gashi sai kayan jikinsa, duk yacinye mata dukiya.Hajiya Jumma taimasa tarba mai kyau kamar babu komai aranta abun yabashi mamaki sosai.


A wannan lokacin kuma tuni Hajiya Jumma tasangarta Lariya sosai

Ta dauki San duniya tadora akan Lariya tareda wani buri marar amfani tana kula da'ita sosai irin kulawan nan Wanda  bakomai acikin sa sai zallar rashin   tarbiyya.



Tunda ko makaranta taje idan tai badai-daiba akai mata fada sai Hajiya Jumma take har makaranta tai ta masifa wai saboda meza'a takurama yarta,


Su kam malamai dasu kagaji sai suka koreta a makaranta.

Hajiya Jumma tace yoh sai me don sun koreki yi zaman ki nima uwarki ai banyi karatu ba kuma gashi Ina rayuwa ta kamar kowa.



Bayan kwana biyu da dawowan Labaran sai Hajiya Jumma ta fahimci Labaran yana matukar kaunar yar tashi duk Abunda yasamo toh" Na Lariya, ne kuma har zuwa wannan lokacin batace masa komai ba akan dukiyar ta da yacinye.


Akwai wata Rana yadawo sai yakira Lariya bayan ta zauna sai yamika mata kunshin Laida Ashe tsirene aciki aikom sai tabude tafaraci,

tana Cikinci sai Hajiya Jumma ta kallesu sai tayi murmushi tace Laririta  zonan,

Aiko sai ta tashi yanufi gurinta,ta dorata acinyarta tare da daukar guda tasaka abakinta sannan ta kalli Labaran Wanda shima suyake kallo ita DA yarta ta.

Hajiya Jumma tahade girar sama da kasa ma'ana tabata fuska kamar bata tabayin dariya ba,

Cikin daga murya tace...?





💞Lufhat Ce💐

💞💞💐💐💐

💐💐💞💞💞

   DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


  page 56-60


           NA


💞AMEENAT UMAR💐FARUQ

          OR

     (MEENAT)



edited by Zainuddeen zain



------------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION



PEN:THE STRONGEST WEAPON

------------------------------------------



only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers




✍🏾




LABARAN! wai kana nufin dukiya ta dakaje kacinye kaci banza kenan? bai bata amsa tambayer taba, saidai jajayeb idosa daya tsurama ta yayida yaji kirjinsa yafara dakan Uku-uku, Ahankali yace Ashe ranan zatazo?


Nikam dake gefe nace tabdi Labaran ai dole wannan ranan tazo domin kuwa KO kudin Uwarka kacinye sai tayi maka magana toh" ballantana matarka.


Wani killer smile Hajiya Jumma tayi Wanda yasa kirjin Labaran ya cigaba da matsananci bugawa, domin tunda yake da ita bai taba ganin tayi irin wannan murmushi ba,

Saikuma yagata daure fuska tace nasan bakada amsar bani tunda kana ganin kacinye Mani kudi kaci banza kana nufin nadauki hakuri ko? tabdi 

Toh wallahi baka'isaba bazan dauki hakuri ba "Ai Hajiya Jumma ba'ai mata Abu tayefe Ina Labaran kayi kuskure idan har kayi tunani cewa zan yafe maka a ah, bana yafiya, kowa yaimani kankara toh" ni sainai masa Na itace yanzu kam nasan konace kabiyani kudi Na nasan baka dasu, saboda haka kaga wannan? tanuna Lariya dake kanciyarta sai cin nama take ba Abunda yada meta,

tace yarka ita ne madadin kudina da kacinye,

Cikin karfin hali yace aikema yarkice tunda ke keka haifeta, tayi dariya tace tabbas ya'tace saidai kabar tunani cewa Nina haifeta, saboda ninan daka ganni gurin KUDI banida mutunci saboda haka babu Abunda bazan iyayi ba indai akan kudi ne.

Cikin tsoro dajin kalamanta yace toh"Zaki siyar da'itane KO" me zakiyi da'ita?

Tai shewa tare da dariyar mugunta tace Allah nadawo inji Dan cirani Labaran Uban Lariya mai kakeci nabaka nazuba Bini Ahankali DA SANNU zakaga Abunda zanyi da yarta ka,


 Ta tashi tare da tajan Hannu Lariya suka nufi daki tabarshi nan cike da tsoro da kuma tunani Abunda zata'aikata da Lariya din.



SANNU ahankali rayuwa tai ta tafiya Lariya tazama cikakkiya Budurwa a wannan lokacin kuma tuni tazama tantiriya yar'iska bin maza take bihakki DA gaskiya Wanda hakan ya farune  Da taimakon Uwarta,

 Wanda Labaran yayi fada yayi zagi hada su duka Amma duk abanza.

(Allah yasa wake Amin).


Nikam nace toh"ai dama Kama titdina tidan duk abunda Kai sai Anyi maka

(Allah yasa


Sanadiyar hakane yasa Labaran kwantawa mummunan rashin Lafiya Wanda har saida yakai shi dabarin duniya,


ko" bayan mutuwar sa baisa Hajiya Jumma itada yarta Lariya sun saduda ba, saima Abunda yai gaba sai azo har gida adauki Lariya saitayi kwana DA kwanaki sannan, tadawo ma Hajiya Jumma da kudi sosai, shikam ciki gurin  zubar dashi tuni ta zama customer.

Wannan shine takai tattace tarihin Hajiya Jumma da yarta Lariya, 


 Yanzu gama yawace-yawacen ta aure takeso kuma ba wanda take so sai Abdul-jabbar, tabdijam toh" bari mugani  abun zayayuyu kuwa?


Washegari tun misalin karfe goma Na safe Hajiya Jumma ta isa gidan Hajiya A'i,da sallamar ta tashiga parlor Mama na zaune ta kallo  atashar MBC Bollywood, 


Sai jin sallama tayi Ahankali ta amsa tare da dagakai sai taga Hajiya jumma, hakanan kawai sai Mama ta tsinci kanta dajin faduwar gaba saka makon  ganin Hajiya jumma, Amma kuma sai bata nuna mata ba,


Saidai tace a a" yau Hajiya Jumma ce agidan namu? yayi dariya tace  kedai nice fa, dai-dai Lokacin data zauna

 Bayan sun gaisa sai Hajiya Jumma tace "ke dai kinganni tunda sassafe "KO?  Mama tayi murmushi tace "eh "ai jiyama Lariya tazo tai gaida ni aina gode Allah dai yabar zumunci,


Hajiya Jumma tayi murmushi tace "ai kedai bari gawani zumunci ma zaya kara kulluwa,

Mama tace toh" daga ina kuma?


Tace Hmm Ashe yaran nan Suna San junan su bamu saniba"?

Cikin rashin fahimta Mama tace wasu yara "kenan fa?

Dariya tayi tace Abdul-jabbar mana shida Lariya,

ita kam Mama jin maganar tayi tamkar Almara sai tace toh" lallai kam nibansani ba,


Ta washe baki tace "eh KO" nima bansaniba sai yau Ashe ma hada alkawarin aure sukai ma junansu", Mama tace toh" kice magana ta girma? 

Tace Hmmm kedai bari "ai abun yayi dadi kinga shikenan sai "ai tuwona maina,


Mama tace kinga nikuma banga alamar faruwar hakan ba,


Da sauri Haj jumma tace saboda me? yasa ki kace  haka Haj A'i?


Saboda tarbiyyarsu tasha ban-ban ke kanki kinsa cewa " "Lariya batada ce da shiba, ba wannan ba kinsani sarai cewa "Lariya batada tarbiyya duk kin bata yarinya Sam ba kiyi mata tarbiyyan kwarai, ba jifa jiya yadda tazo gidan nan  kamar ba diyar muslmai ba, gaskiya Yaron nan bazaya auri Lariya ba.


Ita kam Haj Jumma idan ranta yakai dubu toh"yabaci DA jin kalaman Mama,


 Sai ta kalleta rai abace tace Haj A'i yanzu Abunda zakice Mani kenan? tace " aike kinsa abunda nafada gaskiya ne,


Tace toh" "ai shikenan bakomai nagode nizan tafi tafada ranta bace tare da mikewa tsaye,


Itama" Mama mikewa tsaye tayi tareda cewa a a" har Zaki tafi kenan?

Tace Ummh dai-dai Lokacin da takai bakin kofar fita,


Mama tace toh"sai anjima ki" gaida gida, bayan ta" koma tazauna sai tace "ai "shikum zata shigo yasameni idan bayada ahankali ne toh" "ai nagani,


Duk yan'matan cikin garin nan yarasa wadda zayayi Soyayya da ita sai "Lariya, ko"me yagani ajikinta" daya birgesa Rashin tarbiyya? ko" kuma rashin Kamun kai? "oho masa.


Sai misalin karfe 11:15 Am sannan Abdul-jabbar yashiga cikin gida, yana sanye da Riga T.shat white da wandon jeans black hannun rige da key mata sai zuba kamshin yake,


Saida ya zauna ya Lankwashe kafafu sannan yace Mama Ina kwana?

Ta amsa rai bace da Lafiya lau,

idanu tsura mata domin yaga ranta kamar abace,

Saboda haka sai yace Mama meya faru naga kamar ranki yabaci?


Tace "ai ba Kama bane raina abace yake sosai, yanzu saboda Allah duk yan'matan garin nan karasa wadda zakai Soyayya sai "Lariya  

Kai KO" mekagani ajinta" daya birgeka?

 

Big eyes dinsa yazaro,Wanda har saida yasa taji faduwar gaba saka makon tuno mata wani Abunda idanun sa yayi, ga kuma wani irin kwarjini da sukai mata.


Don haka DA sauri takauda idonta daga barin kallon sa,


yace Mama "Lariya fa ki kace?  Cikin jin haushi tace wannan wani irin abune haka Ina tambayar "ka kana tambaya ta?

Ko" baka game "Lariya yar gurin Haj "Jumma ba?

ba harda alkawarin aure Kai mata ba?


Yace kiyi hakuri Mama nagane ta" jin abun'nayi kamar Almara, niko" me zaya birgeni ajikin "Lariya da zayasa nayi Soyayya DA ita,"har nayi mata alkawarin aure?


Hmmm Mama ke dagajin wannan Magana kinsan ba gaskiya ba ne,

Haba  dai tabdi

God for forbid nayi Soyayya da "Lariya har nai mata Alkawarin aure,


Yarinya DA batada kamun Kai kowa yatashi sai yakwashe ta, sai Dan banzan yawo wato

Yanzu tagama yawace-yawacen ta zatai aure sai nikuma nakwasa, tunda banida kowa KO"? toh" bawai hakan yana nufin nakai kaina ga halaka bane,

Yaja dogon tsaki mtsww

Kai amma dai yarinyar nan taraina ma kanta"hankali

Toh"nima ida baji dana ganta ba a kofar gida nan harna manta dawata "Lariya yai kwaf,


itakam mamaki abun yabata don haka,sai tace kana nufin kace Kai bakata ba zuwa gurinta ba?


Cikin takaici Yace haba Mama me zanjeyi gurinta? ke kanji kinsan bata dace Dani ba ,ya kuma Jan tsaki mtsww sannan yace Allah Maya hadani da'ita sai naci mutuncinta.


Tace a a" karabu dasu duk abinda suke nufi ya kare Kansu, ya mike tare da cewa nizan fita, tace toh" sai kadawo.


Shuru Mama tayi tana nazarin maganar da Haj "Jumma tazo mata dashi,

Jitayi gabanta yafadi saka makon tunawa da tayi kowacece Haj "Jumma,


Ahankali tafara tunani wani lokaci da "Haj Jumma tazo gidan ta bayan sun gaisa,  

Sai tace ke KO" Haj A'i meyasa bazaki auri Alh ya'u nakaka ba? gashi acikin Bari anata maganar yana sanki sosai,


Mama tace saboda bana ra'ayin aure,

Haj Jumma tace

Kinga idanice ke KO"? wallahi auransa zanyi, Mutum mai kudi irin "Alh ya'u nakaka tabdi "ai bazan barsaba, kinga idan kina tsoron matarsa ne toh" kisha kuruminki", ninan daki kagani nasan bokaye da malamai Kala-Kala saboda haka kizo muje nakai ki" gurin boka yan miki maganin ta",

ke" bama ita kadai ba har dashi" Alh ya'u Na kakan sai boka ya asirce mikisu, Ke koma kashesu" kikeso ayi boka zata iya.


Da sauri Haj A'i tace "a ah Haj Jumma kisafa kikace?


Tace eyi "yoh toh" meye? tace gaskiya nibana zan iya kashe mutum ba,shiko" harka Da boka Da malam ban iyasaba kuma banason Na iyashi har abada, bama haka ba ni aure ma baya gabana saboda hakanan mubar wannan maganan.


ajiyar zuciya tayi tareda dawowa daga dogon tunani datake,

tace toh" ni bansa Abunda "Haj Jumma take nufiba da tace "Lariya suna Soyayya DA wannan yaron ba toh" me hakan yake nufi?



Itako Haj Jumma rai abace ta isa gida Lariya ta tambaye ta yadda sukai da Haj "A'i ? nan tafada mata komai "aiko Lariya sai tasaki kukan sangarta tace itakam wallahi idan ba "Abdul-jabbar bazata auri kowa ba,


Haj Jumma tace kwantar da Hankalin ki indai "Abdul-jabbar ne sai kin aure sa kota halin kaka, badai Abunda Haj A'i tace Mani kenan ba? toh" sai tazo gidan nan daka farta taro keni ki auri danta, da alama ta tamanta KO" wacece Haj Jumma toh" Amma zantuna mata,

tashi kitafi abunki.



****************


Bayan kwana biyu

Abdul-jabbar ne zaune Shida Humeeh firarsu suke ta masoya, sai ya kalleta Cikin So da kauna Yace my cool idan muka tafi zanyi kewarki sosai fa.


DA sauri ta kallesa tace Ina kuma zaka tafi?  yace kin manta nafada miki cewa zamuje America yin wani cos? tace "eh natuna yaushe zaku tafi?  yace nanda three weeks,

tace Amma dai baza kodade ba KO"? ummh one year ne kawai, DA sauri tace shekara daya ne kawai? tafadi haka ne kamar zatai kuka.


Ahankali yace my cool idan akwai raida lafiya shekara daya a gurin Allah kamar yaune,

saboda haka karki damu very soon Zaki ga mundawo insha'Allahu,


Ke nimafa don tafiyar tazama dole ne, idan badan haka ba dasai nayi zamana muyita Soyayyar mu KO"? yakai karshen maganar sa dayi murmushi, 


itama murmushi tayi tare Da rufe fuskarta Da hannun alamar kunya, hakan sukaci gabada fira har tsawon wani lokaci sannan yatafi gida.



Mama ce keta faman safa da marwa a tsakiyar parlor, kallo daya zakai mata kafahimci cewa hankalin ta atashe yake,


Koda Abdul-jabbar yashiga ya isketa Cikin wannan halin,


Ya kalleta tare da cewa Mama Lafiya?

Cikin tashin hankali tace sonake yanzun nan Kai maza-maza katafi gidan "Haj Jumma kudai-daita juna kaida "Lariya,


DA karfi Abdul-jabbar yace eyeeee? 




💞Lufhat ce💐

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

   DA SANNU 

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   Page61-66


         NA


💞AMEENAT UMAR💐FARUQ

          OR

   (MEENAT)


edited by Zainuddeen zain


 ------------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN:THE

 STRONGEST WEAPON

------------------------------------------


only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers




✍🏾




Shidin ne" bayada Uba? Haj Jumma tade fuska tace "eh "shidin mana, yoh yanada ubane  idan kuma kince yana dashi toh" yana ina" Uban NASA"?


Mama tace haba Hajiya yazakice bayada Uba wallahi yanada uban sa kamar KO wani da dakikasani,



Tace Hmmm Haj A'i kenan inada labarin kifa kaf, tunda kikazo  garin nan yau kimani shekaru kusan talati Amma baki taba zuwa gida ba, 

sannan kuma wani dan'uwan ki be taba zuwa gurin ki ba kinga hakan yana nufin kinyi abun kunya ne, shiyasa ki kabaro garinku ki kadawo nan dazama KO?


Itakam Mama komai ya kwance mata saboda haka sai tarasa abunda zatace,

tabbas a Cikin ranta taji zafin kalaman Haj jumma musamman  Na San shegan ta mata DA datake shirin yi  saidai babu yadda zatai da'ita, 

ita dai yanzu burinta kawai  shine Haj Jumma ta amince yarta ta auri danta,


Ahankali tace Haj Jumma wallahi dukkan abunda kike fada ba haka bane,

 ni banyi abun kunyaba 

kuma bana tunanin "aikata sa a rayuwa ta,


kuma kamar yanda nafada miki abaya cewa shi ba shege bane toh"ba shege bane yanada uba,

Saboda haka mu daina wannan maganar,


Mufuskanci wannan maganar danazo muyin, nidan Don Allah Haj Jumma ki yarda da maganar auren yaran nan,


Wallahi idan ba auran nan akayi ba hankali Na bazai taba kwanciya ba,


Haj Jumma tace Hmmm Haj A'i manya  toh shikenan,

 Amma dai kije tukun Na sainayi shawara


Mama haba Haj jumma wani irin shawara kuma?


Tace  "eh idan mukai shawara da ita Laririn tawa kinga koda nan da kwana biyu ne ke" dawo  kiji abunda kenan,


Itakam Mama ba haka nan taso ba toh" Amma ya ta'iya dole ta tafi gida har zuwa bayan kwanan biyun,


ta mike tsaye tareda cewa

Toh"shikenan nagode Haj jumma nizan tafi toh" ki gaida gida toh" tafita,

yayin da Haj Jumma tabi bayanta

da harara a ranta tace Zaki gane naje gidanki" kinyi Mani walakanci saboda haka sai narama abunda kikai mani  domin nibana yafiya",


taja wani dogon tsaki mtswwwww sannan ta mike tashiga daki.



Washa gari da misali karfe 10:15 Am,

Zaune suke su uku suna break fast suna Dan fira kadan- kadan kamar yanda suka saba, Amma kuma sai sukaga yau Humeeh tayi shuru,


 Humeeh kam tunanin halin dataga special dinta jiya takeyi, itakam tunda take  dashi bata taba ganin sa Cikin wani yanayi irin najiya ba

Ahankali tayi ajiyar zuciya,


Haleeh ce tadan taba Hannah tareda yimata nuni da Humeeh, tambayan ta tayi da ido alamar meyasa mi Humeeh din? amsa tabata alamar itama bata sani ba,


Hannah ce tace Hey Miss special what is happen?

Haleeh tace yes tell us" meyasa meki ?


Murmushi tayi tace nothing, baki suka hada sukace Ahhhh!

Shine mukaga kinyi shuru?


Dataga sun dameta saita fada masu abunda yasa tai shuru

Suma shurun sukai,


can sai Haleeh tace kila kansa ke ciwon kamar yadda yafada maki,

Hakan nan sukaci gabada fira har lokacin komawa class yayi suka tashi sukanufi class.


*******************

Kwana biyu nan Mama tayishi ne Cikin matsananci wahala domin kuwa hankalin ta atashe yake natsuwarta ta gushe, hada wata yar ramewa tai tunanin ta yatsaya a guri daya shine Abdul-jabbar ya auri "Lariya yar gidan "Haj Jumma,


 shikasan Abdul-jabbar baya cikin nutsuwa badama yashiga cikin gida sai Mama tace masa kaje gidan su "Lariya kuwa? wani lokaci yace mata "eh wani lokaci kuma yace mata "a ah dayagane  idan yace mata "a ah sai tayi tafada, saboda haka saiya daina ce mata " a ah  idan ta tambaye sa sai yace mata "eh kawai.


Kamar yanzu ma yashiga Cikin gida Don yafada mata zai fita,yana sanye Cikin kananan kaya sai kamshi yake zubawa,


Bayan ya gaida ita kafin duk yace wani abu, sai tace zakaje gidansu "Lariya ne? yace "eh  tace toh" nima Ina nan zuwa saboda yaune mukai da ita zanje sai mutsara yadda auren zaya kasance,


Jiyai kirjinsa" ya buga ya kalleta" cikin tausayin kansa yace Mama Dan Allah kiyi Hakuri da maganar auren na da "yarinya nan Wallahi bana Santa,


Nafada miki Mama

Inada wacce nake So itama tana sona" kuma wallahi yar gidan mutunci ce, kinga yau saura sati biyu mutafi kinga Dana dawo sai "ai maganar aurenmu da Humai


Katse shi tai da cewa dalla rufe mani baki, ni"basan wata "Humaira ba "Lariya nasani, maganar aure kuwa idan kaga na barshi toh" bana numfashi ne "aini idan ba auren nan akai ba toh" hankalina bazaya taba kwantawa ba, saboda haka kawai katashi katafi nima gani nan zuwa

Haka yatashi jiki ba kwari yafita.


Shikam Abdul-jabbar daya fita

Bai tsaya ko'ina ba sai gidan "Alh ya'u Na kaka, domin  yasanar dashi abunda ke faruwa, saboda yasan "Alh ya'u Na kaka ne kadai mutumin da  "Mama take jin maganar sa", 


Ya yinda ita kuma tafito tanufi gidan Haj Jumma,


Da sallamar ta tashiga gidan yayinda Haj jumma ke zune a tsakar gida taji sallaman  Amma bata amsa mata ba, toh" itama Mama bata damu darashin amsa matan ba,


Kujera ta dauka ta zauna bayan sun gai sai  sannan Mama tace  Haj Jumma nazo ne akan maganar auren yaran nan, 


"aikam  nanta ke sai Haj Jumma ta daure fuskarta  tafara surfa masifa tana cewa "aidama nace sai narama walakanci daki Kai Mani lokacin da naje gidanki, 


kuma maganar aure tsakani danki da yata babu saboda ta tace bazata auri  Abdul-jabbar din ba tunda kince batada tarbiyya


  saboda haka sai kije kisamo masa mai tarbiyya ki aura masa,


Itakam Mama jikinta sai rawa yake saboda tsanani tashin hakali, 


tace Don Haj Jumma kitai makeni kirufa Mani aisiri wallahi idan ba auran nan akai ba hankalin bazaya taba kwanta waba, Oh Allah sarki Mama baiwai Allah,


 (Kai jama'a Allah Kai mana tsari da Aminai irin su Haj Jumma Amin)


 Saida Haj jumma ta tabbatar dacewa Mama ta galabaita sannan, tunda harda guntun hawayen tareda zube guywuyunta akasa  tana rokon ta akan ta aminci da auren yaran nan sannan,


Da karfi Haj Jumma tace Na amince Amma da sharadin?


Da sauri Mama tace na amince da KO" wani irin sharadi ne


Tace inason da daurin aure da komai karya wuce sati daya, Don wallahi idan ya wuce sati daya toh" saidai afasa,


Mama tace na amince, Haj Jumma ta mike tanufi daki tareda yima Mama dariyar mugunta, tace Oho nadai fada maki" dai dai lokacin da tashiga daki,



Mama ta mike tana cewa nagode sosai sai anjima.


Koda Mama tafita batai tunanin zuwa ko'ina ba sai gida "Alh ya'u Na kaka,


 domin tasan shine kadai ne mutumin" da zaya tsaya mata akan maganar aure nan Don haka direct cen tanufa.



Da sallamar ta tashiga parlor  zaune suke su uku, Alh ya'u Na kaka Y Y k Da Kuma Abdul-jabbar domin tun-tuni ya isa gidan,


Suka amsa sallaman tareda daga Kai suka kalleta, Alh ya'u Na kaka Dattijon kirki mai cikar kamala, 


Yace ah Haj A'isha ne sannu da zuwa, tace yauwa sannu Alh adai-dai lokacin data zauna a daya daga Cikin kushin din parlor,


Bayan sun gaisa ne sai Alh ya'u yace Haj A'isha dama KO" yanzu nake cewa Na Dabo" yaje ya daukoki"saboda Ina San magana dake",


Tayi murmushi tare da cewa Allah sarki nima dama nazone naiman wata alfarma,


Alh yace toh" Haj A'isha wani irin alfarma kenan fa?

Nan tafada masa abunda yake tafeda ita,


Shuru Alh ya'u yayi yana nazarin maganar ta, cen yanisa yace  Naji abunda ketafe dake Amma Haj A'isha meyasa like San Abdul-jabbar ya auri "yarinyar nan? Shin meyasa bazaki bari ya nemi yar gidan mutunci me tarbiyya yaura ba?


Tayi dariya tace Alh wannan ma "ai yar gidan mutunci ce "Lariya ce fa yar gurin Aminiyata ce "Haj Jumma,



Yace yanzu nidai abunda nake soda ke shine kiyi Hakuri abar maganar auren nan Don Allah kinji KO?


Aikam tuni jikinta ya dauki rawa tace Don Allah Alh ka taimaka mani wallahi idan ba auren nan akayi ba, bazani taba samun nutsuwa Da kwanciyar hankali ba a rayuwa ta,


Tanuna Abdul-jabbar tareda cewa wannan yaron Sam bayajin magana ta,


Tun-tuni nake masa maganar aure nan Amma yaki saurarena,

Wai "ace ka haifi yaro da Cikin ka kasayai maka abu sai yaki yimaka toh" "ashikenan, kawai sai tafashe da kuka,


Shikam Abdul-jabbar kirjinsa" ne yabuga yayinda jikinsa" yadauki rawa,


Da sauri yamatsa kusada kafarta cikin tsoro yace Mama kuka kike yimani?


Hannun sa yadora duk akai yace kaichona ni" Abdul-jabbar mahaifiyata kemani kuka? Wayyo Allah Na,


ya kalleta da idanusa dasuka kada sukayi jajir yace ki taimakeni Mama kidaina kukan nan, kinsa cewa kukanki" agareni babbar masifane? 


Cikin kuka tace toh" idan banyi kuka ba meka keson nayi? tunda bakajin magana ta,


Wani irin Yasu Abdul-jabbar ya hadiya mai daci sannan yace toh"Mama kidaina kukan hakanan,

 kifadi abunda kikeso nayi miki" koda hakan yana nufin  daukewar numfashi nane zanyi miki shi insha'Allahu,


Tashare hawayen dagefen zaninta tareda fece majina, sannan tace toh"aini dama "Lariya kawai nakeso ka aura,


 wallahi jinake idan har baka aure taba "Lariya ba zuciya ta bugawa zatai,


Da sauri Abdul-jabbar yace.....?





💞Lufhat ce💐

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page67-70


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)



Dan Allah kuyi hakuri narashin ganin posting din kwata biyu wallahi aikine yai mun yawa nagode,



----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN:THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------


only exquisite and whizkid writers are oppw to be pen writers.



✍🏾



Innalillahi'wa'inna'ilaihinraju'una, Mama Zuciyar ki bazata bugaba insha'Allahu badai "Lariya ki kesan Na aura ba?


 Da sauri tace "eh yace toh" Zan aure ta tace toh"Allah yai maka Albarka ya kare mani Kai yace Amin Mama,


Alh ya'u nakaka shida Y Y K kallon su" suke cike da tausayin su ,

Musamman ma Y Y K dayake tsanani tausaya ma Amin'ninsa akan wannan aure daba yada tsari,


Alh ya'u shuru yai nazarin yake aransa tabbas abun'nan Na Haj A'i akai sihiri Cikin sa,


Yai nauyayyan ajiyar zuciya yace Haj Aisha ki kwantar da hankalin ki, inda Abdul-jabbar ne zai auri "Laria take KO wa?

 

murmushi tayi tareda cewa "Lariya  ne sunanta yace toh" indai hakan shine farin Cikin ki toh" zaya aureta,


 Amma dai sai yadawo daga kos tunda saura sati biyu sutafi,kuma ba wani dadewa zasu yiba tunda duk bai wuce suyi shekara daya ba, 


 kinga dasun dawo sai "ai maganar auren KO?


DA sauri tace a ah Alh "ai mun'riga munsa rana nan da sati daya muke San "ayi bukin,


 Y Y k baisan lokacin da yace what ba?


Shikam Abdul-jabbar daya zaune tunda zu kamar butun-butumi jiyayi kirjinsa yaci gaba da matsananci bugawa,


Alh ya'u Na kaka kam yanzu takara tabbatar da zargin sa na cewa Haj A'isha akwai sihiri atareda "ita


Saboda hahabsai yace haba Haj A'isha wannan wani irin aure haka,


 daza'ace za'a yi shi nan da sati daya batare da anshirya komai ba?


tace "eh nidai don Allah Alh ka yaimaka mani nasan kanada halin yin mani wannan alfarma nan,


Yace Haj A'isha bawai Ina maganar cewa  banida halin yi maki bane,


Kuma bawai Ina alfahari bane,  Abdul-jabbar kadai ba idan sunkai Mutum Dari insha'Allahu inada abunda Zan aurar dasu Rana daya,


Ni Ina magana ne  akan gaggawar abun,kin gaggawa " "aikin shedan ne fa?


Kuka ta fashi dashi tace don Allah Alh Ka taimaka mani wlh bakaji yadda nake jibane aran'na,


Da suri Alh ya'u nakaka Yace a ah Haj A'isha kidai Na kukan nan,


Indai auren Abdul-jabbar da  wannan "yarinyar ne ki kwantar da hankalin ki insha'Allahu za'ai shi, yanzu ma Zan tafi ne mar masa auren ta" kinji KO"


tace toh" Na gode Allah yakara budi ta mike tareda cewa ni Zan tafi, 


yace toh" kijira su agurin Haj zasu zo sumai da ke gida, tace toh" adai- dai lokacin da tafita daga parlor,


Shuru parlor tsawon wani lokaci ba wanda yace komai,


Alh ya"u na ne ya mike ahankali yanufi gurin da Abdul-jabbar yake zaune kan"sa yadafa tareda cewa kiyi hakuri Abdul-jabbar kadauki wannan abun  a matsayin kaddara, 


saidai Ina gani kamar akwai sihiri ajikin "Haj A'isha' toh" kodai ma mene muciga ba dayi mata Addu'a insha'Allahu Komai zaiyi dai-dai ne kaji ko?


Ahankali yadaga Kai alamar "eh, sannan yace kuje kudau keta Ku kaita gida,


 yafadi haka ne dai- dai lokacin da yafita daga parlor,


Da sauri Y Y K ya matsa kusada Abdul-jabbar yafada kafadar sa" yace kayi hakuri Nawa komai yai farko toh" insha'Allahu zaiyi kashi ne kaji KO?


Shikam Abdul-jabbar sai Kai yaketa gyadawa sai kace kadan gare,


tsabar tashin hakalin daya ke ciki yasa shi, yakasa furta koda kalmar  a ne,

Y Y k yace tashi muje mukai ta,


Haka suka mike jiki ba kwari suka nufi hanyar fita,


***************

Cikin lokaci kankani baka fara shirin bukin Abdul-jabbar Da Lariya,

Wanda tuni Alh ya'u nakaka yadauki nauyin yin komai,

 

Abagaren Haj Jumma ma haka shiri takeyi sosai domin  taci buri wa bukin Lariya don haka da kare da biri duk ta gayyacesu,



Y Y k da M B suke tsaye akan sha'anin bukin shikam ango ko" ajikinsa domin KO ya dauki auren ne tamkar wasan yara,


Ana saura kwana uku bukin suna zaune su uku suna" fira sai Y Y K yace kai M B bari nakira Dalter boy na yafada masa, 

M B yace gaskiya ya kamata,


Shikam Abdul-ganiyyun wato dalter boy mamaki yake haryana tambayar Y Y K wai dama Abdul-jabbar yanada budurwar ne? 


shi kam Y Y k dariya yayi yace sai dai kazo tukun na,yace OK yana nan zuwa ana gobe daurin aure, yace toh" sai kazo sukai sallama.


 Abdul-jabbar sai faman masifa yake wa Y Y K wai akan wani dalili zayai tafadawa mutane wannan auren da bashi da tsari,


Yace malam idan kanaso ne  kaburge ni toh" ka tsaya aure Na da my cool yazo,


 Sannan kafadawa duk Wanda zaka fadawa Amma ba wannan auren ba,


 Wanda kai daganin sa kasan bana Allah da Añnabi bane abu haka ko"tsari babu yaja tsaki mtswwwww.


**************

Yaune aka daura Abdul-jabbar da Lariya da misalin karfe goma naran Asabar,


Kira'ar sheikh Ahmad Sulaiman ke tashi acikin motar,


Ahankali Dalter boy ke driving dinsu  Abdul-jabbar  yana kusa dashi, yayin da Y Y k da M B suke zaune abaya suna kan hanyar sune ta koma wa gida,

 

 Y Y k ne ya katse shuru da cewa cikin zolaya oh! shikenan yau wani yazama ango,

yakara she maganar dayin gwalo ga Abdul-jabbar,


Da sauri yace a ah ba ango ba ankwa Mtsww yaja tsaki,


Yace don Allah Dalter boy kabi hanyar cen muje naga my cool ko" zuciya ta nayi fari,


Bamusu Dalter boy yajuya kan motar tareda cewa wacece hakan kuma?

M B yace budurwar sa ce

Yace oh KO" "Humaira da Y Y K ya bani Labarin ta jiya?

M B yace ita fa kaidai, Yace "ai KO" zanso naganta,


Da sauri

Abdul-jabbar yace "ai ko zaka ganta very cute baby, 


Y Y yace kajishi saikace wata yar jaririn, ya bashi amsa dacewa "ai jariri yar,ce


da  kwatance da Abdul-jabbar yake ma dalter boy har suka karasa unguwar su "Humeeh.


Cikin zolaya Y Y k yace zumuje mufada mata" andauran aure ka ne da "Lariya?


Yace ban saniba Nawa bafa nason walakanci daka ke mun,


M B yace "au dama baifada mata" zayayi aure ba?


Y Y k inafa yafada mata" nayi nayi dashi yafada mata" Amma yaki fada mata",


Dalte boy yace "au haka ne toh" Ku kyalesa ni zanfada mata" yau din'nan,


Abdul-jabbar yace tunda kashe kwaya basai kafada mata" ba din ba, dalter boy yace "aiKo zaka gani,


dai-dai lokacin da Humeeh ta karasa gurinsu ,

Lokaci daya suka fito daga cikin mota,


 Cikin jin kunya Humeeh ta gaida su,

Suka amsa fuskarsu dauke da murmushi 

gogan'nata,


Abdul-jabbar ne yagaba tarda dalter boy Humeeh ta sake gaida shi, ya amsa tareda tambayan ta ya school? tace lafiya lau,


Shikam Dalter boy aransa sai yaba kyawau  Humeeh yake, 


yayinda yake mamaki abunda yasa "Mama tace sai Abdul-jabbar ya auri wannan yarinya mai Kama da one,


Maganar Humeeh ce ta katse masa tunanin sa" inda yaji tana cewa Ina zakuje yanzu KO" dama gurina kawai mukazo?


Dalter boy yace "eh dama munzo ne mufada miki,


DA sauri Abdul-jabbar yace....?





💐Lufhat ce💞

💞𷠽𷠽𷠽𴀽𴀊💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page76-80


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)


edited by Zainuddeen zain


----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN:THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------


only exquisite and whizkid writers are oppw to be pen writers.



✍🏾



Umma tana zaune ita kadai atsakar gida tana linkewa "Humeeh school uniform dints kasan cewar "Humeeh bata nan ta tafi islamiyya,


kawai sai taga anshigo mata gida bako sallama,

Ahankali tadaga Kai ta kalleta tace "a ah haba baiwar Allah yazaki shigo Mani gida haka bako sallama?,


Lariya datake sanye da wani matsiyaci dressing ta kalli Umma sama da kasa, ta yamutsa fuska tace sallama tabdi" aini ban sannan ya'akeyin taba, Umma gyada Kai tace tabbas naga alamar bakisan yadda akeyin taba,


Toh" bismillah ga wurin nan ki zauna tanuna mata shimfidar datake zaune akai,


Lariya tace zama? Umma tace eh, taja wani uban tsaki mtswwwww... tace "ah bashi yakawo niba Kuma, Umma tace toh' keh! ko" yarnan meya kawoki toh"?


Tace kinga Malama badon zance yakawo niba nazone infada miki kijawa yar iskar "yarki kune takiyayi "mijina,


Idan Kuma bata" kiyaye "shiba wlh sainai mata" mummunan illa,

Da sauri Umma tace  subhanallahi! Nidai ban haifi yar iskaba sannan kuma wanene "mijin naki?  tace "Abdul-jabbar idan bata fita harkar Saba tabbas saina nakasa mata rayuwa eheee!

 

tajuya danufin tafiya Da sauri Umma tace yi hakuri kinji indai "Humaira ce za tarabu da mijiki insha'Allahu kinji KO?  fiyuuuu tafice tana cewa oho indai bata rabuda shi" duk abunda yasa meta ita tazajo  makan ta domin ninan daki kagan'ni banida mutunci wlh DA SANNU Zan maida "yarki abun kwatance  eheeee,


Tun bayan fitar "Lariya  Umma take zaune shuru nazari take aranta tabbas wannan "yarinya duk inda tafito toh" ba gidan mutunci tafita ba,


Umma kam jitayi kirjinta yabuga  saka makon tuno kalaman "Lariya ga "yarta, ahankali tasaki sanyayyan ajiyar zuciya tareda cewa inda Abdul-jabbar ne toh" Humaira tabarsa tunda bashi kadai ne da namiji ba,



Cikin bacin rai Mama tace keh! Lariya nafa gaji da wannan abunda kikeyi mun haka, KO" agidan ku ankafada miki"haka ake zaman aure, "mijinki bayanan amma ke" kullum cikin yawon bin gari kike toh" wlh bazan cigaba da daukar wannan abun ba,


Lariya ta kalli Mama sama da kasa irin kallon nan Na walakanci mai dauke da harara sannan taja wani uban tsaki mtswwww...tace hmmm  wai bazaki cigaba da daukan wannan abunba, yoh Ina abun yake?   hmmmm "ai ba'ai komai ba toh" barima kiji in fada miki Haj A'i kike nema kowa? gwanda cigaba da  dauka  domin ninan dakika  ganin yanzu ne zanfara tsulamiki rashin mutunci badai kinci banida tarbiyya ba KO"?

toh" ko" zakiga zallar rashin tarbiyya damani bason wannan shegen "danki nake ba, dama wata muguwar sha'awar sace takamani toh" kuma dayake "shidin Dan bakin Cikine sai yaki yarda naji kalarsa, don haka ke kuma baki'isa ki hanani sha katawa ba eheeeee   tafice daga gida, 


ita kam Mama kuka tafashe dashi tareda cewa "Oh ni A'isha wannan wata irin matsiface haka waima ya'akai wannan yaron ya auri wannan "yarinyar ne marar mutunci,? Nikam nace toh,


 baba Lami ce tafito daga kitchen tace Haj Lafiya kike kuka?  Mama tace "aidole nayi kuka saboda Lamarin "yarinyar nan ya'isheni, ni basan ya "akai "ya auri wannan "yarin ba wlh,


itakam baba Lami hakuri kawai take bata, sannan tace "ah Haj aure kam  ke kikace dole sai maigida Na ya aure ta,

Mama ta face majina da gefen zaninta" tace toh" dole Kuma yarabuda itaba, domin  ni wlh bazan iyaba, haka kawai bakin Cikin Dana bai kasheni basai Na wata yar banza "aizan kirasa nafada masa yara bani da wannan marar tarbiyya   "yarinyar,


***************

Da misalin 9:00pm suna zaune Humeeh itada Umma fira suke kadan kadan sai Humeeh ta fahimci kamar wani abu nadamun Ummanta, don haka sai ta kalleta tace Umma  tunda nadawo daga islamiyya sainaga kamar wani abuna damunki KO"?


Umma tace Hmmm tabbas Ko" akwai abunda yake damuna, nan dai Umma tafada mata abuda yafaru  ta karashe maganar ta dacewa saboda haka kirabu mata da miji tunda ba "shi kadai bane dan namiji a duniya atoh" nibana San tashin hankali kinji KO?


Kai kawa Humeeh ta gyada domin kuwa takasa cewa komai asalima tunda Umma tafara magana kirjinta ke bugawa, aranta ko" fadi take Allah yasa ba "Abdul-jabbar dinta Umma ke magana akai ba,


Umma tace waiko kinji abunda nace kuwa? "eh Umma najiki saidai Ina ganin ba "Abdul-jabbar din'na bane shi "Abdul-jabbar din'na bayada mata  bai taba aure bafa shi,


Harara Umma ta watsa mata tace "au shi "Abdul-jabbar din'ne naki da yaushi yazama Naki ban saniba? Ciki Dan jin kunya Humeeh ta sunku yarda Kai kasa,

Umma ta cigaba dacewa ke kinsa waye namiji kuwa? idan yanada mata zaya fada miki ne KO"Kuma idan zaiyi auren sa yafada miki?


tabbas wannan "yarinyar  datazo gidan matar "sace Kuma abuda tafada lallai zata iya aikata shi don banga alamar digon mutunci a idanun "taba saboda haka idan Zaki rabu "mata da "mijinta toh" Kira budashi" idan Kuma bazaki rabuda "shiba toh" bismillah tana kaiwa nan, tashi ta shige daki tabar Humeeh zaune kamar anshu kata agurin,


Itakam Humeeh ido ta rintse sosai Ahankali tafurta Allah katadani daga wannan mummunan mafarkin  tsawon wani lokaci sannan tabude idanun tana nan inda take zaune hakane yasa tagane tabbas  ba mafarki takeba,


Ahankali tace haba my special meyasa zakai Mani haka? can Kuma saita mike kamar wadda aka tsikarama allura, daki tashiga Umma Na kallon ta  wayar ta dauko tafito waje ta kunna wayar tayi kasan cewar tundazu daza taje islamiyya take kashita number Abdul-jabbar tayi dialing



 Shikam Abdul-jabbar  suna zaune shida Dalter boy suna fira saiyaga calling din Mama, yana dauka saiji yai tafashe masada kuka da sauri ya mike tareda cewa ya Salam, Mama meyasa meki kike kuka Allah yasa bani ne sanadin zubar hawayen kiba?


Cikin sheshekar kuka tace toh" idan ba "Kai bane sanadi toh" waye? da 

 sauri yace oh kaicho na ni Abdul-jabbar shikenan nikuma zamana kenan sa mahaifinyata kuka? lallai kam banji dadin rayuwa ta ba,

kiyi hakuri Mama kifada Mani abuda nakeyi Wanda yasaki kike kuka nikuma insha'Allahu daga yau Na daina kinji?


tace toh" sonake kasaki "Lariya, idanu ya ritse aransa kuma fadi yake Allah kasa mafarkin dana keyine kullum yau zaya zama gaskiya,


Daga can Mama taca kajina kuwa? Dasauri yace "eh Mama meki kace?

tace cewa nai ka Saki Lariya, wani irin sanyine yaji yakwarara Cikin zuciyar sai, Amma don ya tabbatar da cewa da gaske takeyi, saiyai  gyaran murya tareda daure fuska kamar yana gabanta yace haba Mama yazakice nasaki "Lariya matata cefa kuma kinsa muna San juna, tace "au abuda zakace Mani kenan KO saboda baka san irin rashin mutunci datake mun bako? toh" wlh idan baka sake taba toh" saidai kanemi wata Uwar Amma bani ba,


DA sauri yace yi Hakuri Mamata "ai duk duniya nan ba wata Uwa dazanje nema bayan ke, indai "Lariya ce yanzu nan Zan saketa bama sai anjima ba Mama ina "Lariyan take? tace barina kirata Yanajin Mama tana kwalawa "Lariya kira "yajin Lariya na cewa Malama Lafiya ki ke mani irin wannan kira haka saikace kin warke makanta?


itadai Mama ba tace komai ba saida kawai tamika mata Waya, "Lariya ta yamutsa fuska tace meye zanyi da waya,? Mama tace anason ayi magana dake takar ba tareda cewa waye?  Cikin daka tsawa Abdul-jabbar Yace Uban ki ne Ashe bakida mutunci Maman tawa kike fadawa magana haka? 


toh" dama ita ce tasana aure ki" yanzu Kuma tace nasake ki saboda haka ki tattara komatsan kije nasakeki Saki biyu, tsaki tayi mtsww tace toh" donka sakeni saime? Dariya yayi yace sai narabuda jaraba, tsaki mtsww tasakeyi tareda jefawa Mama wayar ta akan ciya tace don kinsa yasake ni toh saime? Mama tace Saina rabuda bakar kadara, tafeta fuuuuu daga falon

Mama tace Allah yaraka taki gona,


baba Lami dake zaune tana sauraren duk abunda ake, batace komai ba sai yanzu  tace Hmmm nidama nasan DA SANNU  Allah zaya baiyana gaskiya, asauka lafiya dama shi duk abunda akayisa badan Allah ba toh" dama karshan sa kenan,



Da sauri Mama tadauki wayar tace Kai! yace na'am Mama yanzu shikenan hankalin ki ya kwanta? tace "eh Allah yai maka Albarka ya baka abunda kake nema na' alkhairi duniya da lahira kuma Allah yadawo daku Lafiya yace Ameen Mama ta, yace taba baba Lami su gaisa itakam baba Lami hada murnata tayasa narabuwa da "Lariya sukai sallama,


Shikam Abdul-jabbar jiyayi kamar ansauke masa wani katon dutse akai,

don haka yana gama Waya dasu Mama sai yai dialing din Humeeh kasan cewar yaji shigowar calling dinta lokacin dayake Waya da Mama,


A abangaren Humeeh kuwa tana takiran Abdul-jabbar acemata number busy, tana KO" karin sake yin dailing dinsa kenan sai gashi calling dinsa ya shigo,


Da sauri ta dauka tai sallama ya amsa tareda cewa sorry my cool naga kiranki lokaci Ina Waya da Mama ne, toh" yakike ya Umma ta? tace Lafiya lau yace gud than where is my Soyayya?

Shuru tai bata bashi amsa ba yayinda takeji sonshi yan ratsa jikinta,

A hankali tace tambayar ka" nake sanyi Kuma inasan don Allah "kafada Mani gaskiya banasan ka" boye Mani komai,


 Murmushi yayi har saida taji sautin sa akun'nanta ta rintsa ido, yace my cool ki tambaye ni KO" mene shi indai nasani zanfada miki gaskiya kinji?


tace OK Abdul-jabbar kanada MATA? Jiyayi kirjinsa" yabuga zaune yake Amma saboda tsabar razana dajin tambayan datai masa" saida "yamike tsaye, 

 tace ina nufin kataba AURE NE?

gaba daya Abdul-jabbar ya daburce Cikin Karfi hali yace.....?




💐Lufhat ce💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page81-85


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)


edited by Zainuddeen zain


----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN:THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------


only exquisite and whizkid writers are oppw to be pen writers.



✍🏾



Ah! Eh!  Da sauri Humeeh ta katsesa da cewa just amsa my question yes or no? Saida ya tattara natsuwar sannan yace "eh nataba aure Amma! 


da sauri ta katse sa  dacewa OK nagode kwarai DA abinda Kai Mani sai anjim, Da sauri Abdul-jabbar ya katse ta da cewa my cool ki saurareni, tace no I don't want to hearing anything from you, da sauri ta katse wayar,


 tabarsa yanata fadin Hello! hello!! hello!!! gaba daya Abdul-jabbar ya  birkice sai fadin yake pls my cool ki saurare ni mana sai faman neman line din "ta yake Amma  switch off,


itakam Humaira tana katse wayar sai ta tsugun'na tareda sakin wani irin kuka  Mara sauti fadi take meyasa zakai" Mani haka Kasan yadda nake sonka" kuwa? "my special Ina sonka dayawa shiyasa nake  matsananci KISHIN Ka" har Ina tunanin babu wata ya mace dazata rabeka sai ni" Ashe bansani ba tuni wata mace tadade da rabarka?


Wani kuka tasake Saki mai ban tausayi, daga can Umma ta kwala mata kira, da sauri ta amsa tareda mikewa tsaye tana goge hawaye,  


tace Umma gani' kallon ta Umma tayi tace meki keyi awaje? Ciki rawar murya tace bakomai  da sauri Umma tace kuka kikeyi? tace a ah, tace hmmm yaro man kaza yanzu saboda  Da namiji kike kuka? tun yanzu Zaki farasa damuwa da namiji a zuciyar ki? lallai kinada "aiki  dalla wuce kitafi ki kwanta, sum-sum tawuce ta kwanta.


A bangaren Abdul-jabbar kuwa abun ba'acewa komai, domin kuwa gaba daya ya birkice yatada hankalin sa" yatada Na Dalter boy" yakira Waya har yagaji Amma amsar dai guda ce wato switch off, kusan kwana yai yana abu daya, dayaga abun yanason birkita masa kwakwalwa sai kawai yaje ya dauro alwala, yafar gabatar da lafila tareda rokon All akan duk abinda yaza faru tsakanin sa da my Cool dinsa toh" Allah yasa yazo cikin sauki,  yanda yaga Rana haka yaga dare,


Itama Humeee hanne Ya kasance agareta yadda taga Rana haka taga dare ko kadain bata runtsa ba,don haka kids gariyawa sai ta tashi da matsananci Zazzabi mai zafi da kyar ta'iyayin sallar asuba sannan takoma ta kwanta


Tunda Umma taga takoma ta" kwanta tasan cewa yau ba Lafiya tunda bata saba komawa bacci ba idan tayi sallah,

 

Su Lariya kam sunzo da safe suka kwashi kayansu Amma fa "an rabu kare jini biri jini,  itakam Baba Lami sai basu Hakuri takeyi, 


inda Haj Jumma tace Haj A'i "ai zamu hadune wlh, da suri Mama tace insha'Allahu  Allah baya sake hadani dake ba daga nan duniya har  lahira muguwar Aminiya kawai,


Yayinda Baba Lami take fadin "ai duk abida ba'ayisa domin Allah ba toh" dama karshen sa kenan Allah dai Ya kyauta, nima nace Amin

Haka dai aka rabu bada dadi.


A yau jumma@

Wanda yayi dai-dai da kwana biyu kenan da zazzabi ya kwantar da Humeeh,   hankalin Umma yatashi sosai Ana cikin haka sai gaya Yah Himu yazo weekend kamar yadda yasaba,


Hankalin sa yatashi sosai da yadda ya ga Humeeh, Umma ke fada masa dalili zazzabin Nata "aikam yanata fada ya Kuma ce karta sake kiransa awaya dama shi bawai ya yarda da wannan Abdul-jabbar din bane,


Ana cikin wanna hali Kuma saiga notis anbasu sutashi gidan tunda wai basu biyan kudin haya, hankalisu yatashi sosai basuda gurin zuwa dole suka tattara suka koma gidan Malam mahaifin Umma, 


wanda bai sannan halin dasuke cikiba saida yagansu, aikam yayi fada kamar ya ari baki, musamman dayaga halin da Humeeh  take ciki nadai, Umma tayi ta ba shi Hakuri har ya Hakuri amma yace tarege wanna zurfin cikin Nata,


Wasa wasa saida Humeeh ta kwanta gadon Asibiti ahakadai akai tafama" har tasamu Lafiya taci gabada harko kinta" Amma fa son "Abdul-jabbar yana nan makale acikin zuciyarta,tawani bangane Kuma jin haushi sa take sosai akan abunda yai mata,


 Abdul-jabbar kuwa kullum yana cikin Neman line "Humeeh Amma shuru baya samu, Dalter boy yayi magana akan yayi hakuri harsu koma gida Amma yaki sauraren sa"  saboda haka sai ya  kyale sa,


wanna shine abinda ya faru da Abdul-jabbar Da Humeeh,  toh" wai Soyayyar Humaira ce ke  faman  wujujuwa  da Abdul-jabbar kodai akwai wani abun ne? toh bari mugani,



CIGAGAN LABARIN

------------------------------

Wurjan-jan yashi ga parlor tareda yin  sallama,

Alh ya'u nakaka Dattijon kirki mai cikar kamala, ya amsa Sallama tareda kallon Dan nasa"


Dayake ta faman zuba gumi kamar yahadiyi Karin kuna ma, sai duk yabashi tausayi gashi duk yarame yayi duhu, alamar dai tare suke yin jiya Da abokin'nasa,


Yasamu gurin ya zauna tareda cewa sannu, Baba,"


Batare daya amsa ba yace "any-anya nadabo ciwon nan Na "abokinka Ana samun cigaba kuwa?


yau kimanin sati hudu kenan fa Amma ace har yanzu "Mutum  baisan duniyar dayake ba, balle yasan Wanda ke kanshi ,


Nifa 'ni abin'nan yaki toh" fa Zan fita da "yaron, Germany tunda suna da kwararru likitoci,


 domin nidai tausayi mahaifiyar sa" yakaini makura  gaskiya,

DA sauri Y Y K yace...?



💐Lufhat ce💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page86-90


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)


edited by Zainuddeen zain


----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN:THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------


only exquisite and whizkid writers are oppw to be pen writers.



✍🏾



"Ansamu cigaba' 


Alh ya'u yace ta ina aka samu cigaba? "Mutum kashiga har kafito Amma bai sani ba,


Y  Y k yace daga asibiti nake yanzu shine nazo nafada maka cewa   "Abdul-jabbar din ya farfado, saidai haryanzu baiyi magana ba,


Sai "yanata wasu surutai alamar baya cikin hayyacinsa,

 Sannan Kuma yanata kiran Mama,


Shine nace toh" bari inzo nafada maka, abinda ke faruwa,

Alh yace toh" masha'allah Allah mun gode maka,


Yanzu abida nakeso dakai" shine Kai" maza- maza,

Kaje kataho Mani da "Haj A'isha,

Sai Ku iskemu can asibitin kaji KO"?

Yamike tareda cewa toh" yafita dasauri,



Asibiti Abdul-jabbar yana zauna ya jingina da filo, Alh ya'u yashiga dakin da sallama sa ya kalli Abdul-jabbar,


Yace sannu Abdul-jabbar yaya jikin naka,Ina fata kasamu Lafiya?


Bai amsa ba saidai ya zubawa Alh ya'u idanu, kamar bai taba ganin shi ba,

Ya sake tambayar sa still shuru ba amsa,


Sai ga Doctor I S G yashio dakin, yace sannu Alh kaga Abdul-jabbar ya farfado ko?


Alh yace kwarai nagansa", ya farfado saidai Kuma banji dadin ganinsa" hakaba gaskiya,


Doctor shiyasa nace kabari nafita dashi Germany, amma kace nabarsa ,


Yanzu haka zaya zauna babu magana,  hakanan zayayu kuwa doctor?


Doctor I S G yace a ah Alh insha'Allahu dazaran ya" warware zakaji yai magana,

 sannan Kuma yana bukatar ganin  "mahaifiyar sa" 


yace "eh natura nadabo ya daukota" docto yace OK shikenan,


Alh yayi shuru yana tunanin, abinda Doctor ya fada masa tun kwankin baya dasuka wuce,


Aransa yake fadin shiko "Abdul-jabbar meya keso haka, wanda yasaka shi acikin rai haryana baraza nan salwantar masa"da rayuwa?


Ahankali aka turo kofa aka shigo,

 Y Y K yana gaba Mama tabiya dashi abaya,


Wannan shine Karo nafarko Da Mama tazo asibitin, domin KO" da'akace tazo taga jikin Abdul-jabbar din sai tace "aibasai tazoba,


Tunda ga abokanan" sa nan suna zuwa, sannan Kuma ga "

Haj karima ga kuma "Baba lami kullun idan taje da safe sai dare take komawa gida,


Don haka ba dole sai tajeba, saboda haka bata taba zuwaba sai yau,


 Mama ta tsurama dan tilon dan'nata idanu tana kallon sa,

ta firgita kwarai daganin yadda ya koma,


A ranta take fadin ashe haka "yaron nan ya koma? tabbas duk abinda

 yasa meshi nice sila,


Domin kuwa naki fada masa" ko wane  mahaifinsa", sannan nasa shi ya auri "yarinyar da bayaso,


Alh ya'u nakaka' neya katse mata tunanin da takeyi", dacewa Haj A'isha  matsa kusa da dan'ki,


Yana bukatar ki kusa dashi, sannan Kuma "akwai abinda yakeso" Wanda muba musani ba, Amma babu mamaki ke kinsanshi,


Tunda kinzo don haka matsa gareshi KO" yaji sanyi aranshi,


Batayi musu ba ahankali ta matsa kusada gadon dayake, sai kallon ta yake kamar bai taba ganin taba,

ita din'ma shita ke kallon,


A hankali ta zauna a gefen gadon tace sannu ya jinkin ka?,

Haryanzu kallon ta yake batare Da yace komai ba,


Ta Kuma cewa meka keso yanzu? nan'ma babu amsa saidai hawaye daya wanke masa  fuska,


Jitayi ga banta yafadi aranta Kuma fadin take tabdijam, lallai abu yayi abu tunda harya keyin kuka, domin ba  karamin abu ne kesashi" kuka ba,


A hankali ya matso kusada ita ya kwantar da kansa akan ciyarta,  hakanan taji ta tsinci kanta da Dora hannun ta saman kamshi, ahankali tafara shafa masa" cukur kudeddan sumanshi irin Na fulanin asali,


Tace Na tambaye ka'  meka keso? baka bani amsa ba,

Koda yake nasan abinda ka keso, tana' maganar ne Amma idanun ta Na zubar da hawaye,


ta cigaba da cewa nasan kana" san kasan wanene mahaifinka KO?


Sannan kana san kasa dalilin da ya  rabu dashi KO?

toh"  zanfada maka komai,


Amma kafin nan inasan kayafe abinda nai maka,nasaka' dole ka aurin "Lariya wanda nidai basan ya akai haka tafaru Dani ba,


 Nasan Na kunta tamaka' a rayuwa saboda kayi hakuri, Na Kuma gode da biyayyar da Kai mun, 

Ina rokon Allah kaima yabaka mai yi maka biyayya fiye da yadda Kai Mani 


A yau zanfada maka KO" wanene mahaifinka' sannan Kuma zanfada maka dalilin daya rabani dashi, 

A hankali tace....?





don Allah kuyi hakuri DA wannan 



💐Lufhat ce💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page91-95


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)



edited by Zainuddeen zain




*Assalamu'alaikum, friends  dan Allah kuyi hakuri narashin gani post din Na akan lokacin abubuwan ne sai Ahankali nagode* 





----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN:THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------


only exquisite and whizkid writers are oppw to be pen writers.



✍🏾



Asalinmu mutanan" Adamawa ne kamar yadda kasani sunana A'ishatu, Amma ana kirana lndo, mahaifina Kuma sunan sa  Ibrahim amma ana kiransa Malam lro,

mukuma bappa muke kiranshi,

ita Kuma mahaifiya ta sunan ta Hajara Amma hajjo ake kiranta mukuma Inna muke kiranta,


Mu biyu iyayan mu suka haifa nida kanina Mahmud amma mado muke kiransa,


Mu fulanine gaba da baya masu zama a wannan ruggar zuwa waccan ruggar, a takai ce dai mu fulanin tashine,


Amma dai asalin ruggar mu idan muke zaune shine Husirin bombe,

nakance yar fari a gurin Inna ta' don haka take nuna Mani kunya Da  kawaici irin tamu ta Fulani, saboda haka ban faye sakin jikina da ita ba domin bata bani damar yin haka ba,


Idan ma kaga "tasaki jiki Dani toh" sai idan bappa" da Mado basanan, kamar wata rana basanan su tafi kiwo kasan cewar bappa" baya barina, natafi kiwo,

saidai yace Na zauna Na taya Inna "aikin gida kamar su tatsar nonon shanu, da Kuma dafa madara, da dai sauran aika-aikacen gida Wanda baza'a rasaba sai shi' kuma bappa da Mado su tafi kiwo,



A wannan lokacin kuwa munkai kimanin wata goma, rabanmu da ruggar mu, muna zaune nida Inna' Ina tankadan Karin tuwo ita Kuma tana kada zaren kadi (audiga),


Saina kalleta tareda jefa mata tambaya kamar haka, Inna meyasa bamu zama a ruggar mu saidai muje mudawo?

sai tace "aidaga bappan' kune yafi gaye ma haka shiyasa,

 saina Kuma cewa Inna kice ma bappan" idan muka koma kawai muyi Zan,mu a ruggar mu, karmu Kuma zuwa KO" wacce rugga,


Harara Na tayi tareda cewa toh" Sannu uwata sai kisani dole nafada masa",  tunda duk maganar Dana kemasa' bata isaba sataki daki ka kawo yanzu kam "ai zaiji sosai KO"? 

 Kin wani tasani agaba da tambaya sai kace wata  tsarar ki KO"? da sauri Na kalleta sai naga ta tsuke fuska tareda harara ta, 


toh" daganan nafahimci cewa firata tafara isarta, dama baka safai take zama Dani muke firar ba,

wani lokaci sai su bappa"da mado" basan nan KO" Kuma idan naganta cikin nishadi,


 toh" inda muke batawa da ita shine gurin tambaya, domin kuwa haka nake da dankaran tambaya kamar yar jarida,  toh" ita kuma bata san yawan tambaya don haka  dagan nan firar ke tsayawa domin kuwa tashi taka tabarni agurin, kamar lokacin danai mata wannan tambayar tashi tayi ta barni agurin,


Bin bayanta da kallo nai har saida tashiga daki sannan nayi ajiyar zuciya, domin kuwa mamakin Inna' take bani araina nace oni indo, wai Danna kasance yar' fari shikenan Kuma banida yanci daza "azauna Dani ayi fira?


Ina Cikin wanna tunani sai ga bappa shida mado sun dawo kiwo, nayi musu sannu da wowa tareda karban sandar hannun bappa Na agiye,

 yace Sannu Da gida nace yauwa,


tareda kawo masa ruwa atulo mai sanyi, ya karba yana cewa "an gaisheki' yace Ina ita lnnar tatu take bangan taba? nace tana daki, muna cikin magana saigata tafita tanayi masu Sannu, ya amsa tasamu guri ta zauna sai suka fara fira har aka kira sallar magriba,

bappa yai alwala shida mado suka tafi mallaci, nikuma mukai tama nida Inna,


*********

Bayan sati biyu da misalin karfe biyar Na yammacin ran alhamis, lokaci har mungama girkin dare nida inna bayan naci abinci sai nafita waje, Dan nisada bukkar mu kadan ta gefen wata bishiya na daura lilo,


Tunani ruggar mu kawai nakeyi Da Kuma kawayena, gaskiya a lokacin Na matsu mukoma ruggar mu,


Can nahango mado yana daga mani hannun yana dariya, nima nayi dariya tareda saukowa daga kan lilon,


A hanya muka hadu  muka Kuma yiwa juna dariya, na ce har kundawo kiwon?  yace tundazu muka dawo bappa yana Kiranki, nace lafiya dai KO"?  yace lafiya lau,


Muka jera muna tafiya muna fira sai Mado ya kalleni yace Adda Albishiri ki?, (kasan cewar haka yake kirana wato yaya kenan da fullanci), nayi murmushi tareda cewa goro madona Kuma fari tas- tas,


 Yace kinsan abokina nan Na bappa dayake bamu labarin raban dasuga juna tun suna kana nan?


Nace "eh bansan shiba Amma Kuma ban manta DA labarin sa ba,

Mado yace toh" yau mungan shi agurin kiwo, Kuma bappa yace masa" yadubi hanyar mu yau din nan zamu kawo masa ziyara,


Nace ahaba dai?  yace aradun, a dai- dai lokacin da muka karasa bukkar mu, muka isko bappa yana yiwa Inna bayani harnaji yana fadin sunan ruggar wato yolde kohe,


bayan na gaida bappa sai Na kalli Inna nace, nace Inna wata rugace yolde kohe Amma dai bamu taba zuwa can bako?

batare da takalle niba tace nima ban saniba, amma idan ki kayi hakuri "ai can zamu tafi yanzu KO?


Dajin haka Sai naja bakina natsuke  munshirya tsaf, muka fito zamu tafi sai bappa yace yana zuwa mujirasa kadan,


can sa gashi' yadawo yana cewa nafada wa "Malam jauro zamuje ruggar yolde kohe, yajimani motsin shanu tunda bazamu dawo yauba sai gobe,


"Malam jauro magocin mune, tunda muka sauka agurin sa" mike daukar karatun kasan cewar sa Malamin makaranta kallo,


haka muka Kama hanya da yamma nan, domin kuwa a lokacin rana tayija ta tafi yamma zatafadi, kunsan Fulani basuda tsoron dare, haka nan muka cigaba da tafiya, su bappa" suna gaba mu Kuma muna binsu abaya

munyi tafiya sosai,


Ta! ta!! ta!!! haka naji karan abu da sauri Na waiga bayana "aiko nai arangama dawani katon Mutum", bakikirin dashi' hannun shi yana rikeda wani abu, Wanda koba afada maniba  nasan bindiga ce"


gabana yafadi tsoro yakamani  domin kuwa ban taba ganin Mutum irin shiba, "azato nama KO" aljani ne


Sai naji yai magana Cikin kakkausar murya, yana cewa duk Wanda ya motsi koyai yankurin gudu  saina harbemashi Kai, Cikin firgici muka cukuikuye juna nida Mado, bappa Kuma yayi tsaye yayinda Inna ta boye bayan bappa, daga bayan mu Kuma mukaji wata murya mai Kama da irin wancan yace komotsai Mutum yai ka harbeshi,


 Muka Kuma rike juna nida mado, ashe su biyu ne 

Kuma kowan'ne hannun sa da bindiga, gudan yace kudi zaku bamu KO" muka she ku' yanzun nan,

bamusu bappa yafito da kudi Cikin aljihunsa ya mika masu da sauri gudan ya warce kudin yasa aljihun wandon,

 

Sannan ya kalli Inna yace ke Kuma fa? bamu kudi, Da sauri bappa yace "aisune duk Na baku' tsawa mutumin' ya bugawa bappa yace yimana shuru makaryaci


 keh! bamu kudi ? Jikinta yanarawa tace handin boni bani da kudi, yadaka mata tsawa tareda cewa karya kikeyi kina dasu, Cikin tsoro tace "aradu banidas,


Bai bari "taka rasaba yana karanta harbi agoshi, aikon take tafada kasa,

Cikin matsananci firgici muka saki juna nida Mado, muka nufi inda take kwance da sauri gudan yarike Mado,


 ni' kuma na karasa inda Inna take bappa Na kiran ta nima Ina kiran sunan ta'amma bata amsa kiranan kowa daga Cikin muba', da'alama ta amsa kiran Ubangijinmu,


Kuka nasaki domin kuwa tuni jini ya wanke mata' fuska, da sauri bappa ya dauki sandarsa yarafkawa dayan, ya Kuma rafka masa take yafadi sumamme,

 

Da gudan yaga haka saiya harbi bappa akafa, tuni bappa yafadi hannun sa rike da kafarsa dake zubar jini,


wani sabon kuka Na Kuma Saki, domin kuwa naga wayan nan mutanan suna kikarin nakasa mana rayuwa, shiko Mado yanata ihu mutumin nan yasake shi amma yaki yasake shi,

don haka sai Mado ya Kama hannun mutumin ya gantsara masa cizo, da sauri yasake shi da gudu "yataho muka hadu muka rungume Inna muna kuka hada bappa,


Domin kuwa mungane cewa Inna tarigamu gida gaskiya, da sauri mutumin  yabiyo Mado zai Kuma rikesa Ciki zafin nama bappa ya dauki sandarsa ya rafka masa akafa,

yafadi tareda rike sandar da hannun suka fara komawa da bappa, Ciki fullanci bappa yace mu tashi  mugudu

da sauri na kalleshi nace bappa Ina zamu tafi? tsawa yadaka mani yace nace kutafi KO?


Zumbur Na mike nafinciki hannun Mado nukanufi Cikin duhun daji da gudu,

gudu muke ba tsayawa munyi gudu sosai sannan muka tsaya agefen wata bishiya mai yawan ganye,


muka hada Kai nida Mado muna kuka sosai ba me lallashin wani, saida mukai mai isarmu tukun sannan mukai

shuru, can sainaji tsoro yaka mani tunani nafara yi kar wani Abu yasame mu Cikin dajin nan,


Don  haka sai Na Kuma Jan  hannun Mado" muka koma gurin su bappa, atunanina zamu iskosu koda muka isa gurin bamu iske kowaba , "aiko basan lokacin da Na Dora hannu akai Na kurma ihu kiran sunan "bappa da "Inna, shima Mado' kukan yakeyi  haka mukayi tsaye agurin muna tafan kuka, ga garin sai duhu yake karayi don haka sai Na Kuma fincikar hannun Mado,


Muka nausa Cikin dajin dagudu, gudu mukeyi batare da mun San ida muka dosaba Cikin ikon Allah sai gamu abaki titi,

nakali gabas da yamma kudu da arewa ba alamar mota KO" mashi balls keke,

Mukai tsaye Ciki jiran tsammani domin kuwa bamu Santa Ina mota KO mashin zaya bullo ba,


Can sai muka hango hasken fitilla mota daga gabas tanufo Inda muke tsaye, sai Kuma muka ga ta tsaya sai hasken fitillar ya dauke alamar ankashe,

sai Kuma mukaji shuru Na tsawan lokaci ba "akaraso inda muke ba, ni Kuma ganin haka sai naja a hannun Mado muka nufi gurin motar dagudu,


 saida mukai gudu sosai sannan muka iske motar ashe ma akori kurace,  bamu tsaya bata lokaci ba muka hau motar daba musan ida tadosa ba, mudai burin mu mubar wannan dajin, saida muka shiga muka zauna sannan ne muka fahimci ashe rake tadauko,


can sai mukaji anfisgi motar da karfi da sauri muka rike juna, Cikin tsoro domin kuwa ba mutaba shiga mota ba sai a wannan lokaci,

 Bansan KO" awa Nawa muka dauka muna tafiya ba,  saidai kam mun dauki lokaci mai tsawo muna tafiya,


Can saigamu aciki birni muna tabaza idanu muna kalle- kalle, ahaka yashiga wata anguwa ya tsaya DA alama salla zayayi  tunda munga mutane natayin alwala,


Sai bayan daya shiga masallaci ne sannan muka sauko daga motar, naja hannun Mado muka Fara tafiya ba tareda munsan inda zamu ba,


Tafiya mukeyi  batareda  mun hadu dako dabba ba balle ba bil'adamu, tsit gurin bakajin motsin  komai sai Na tafiyar mu, sai KO"bukun zuciyoyin mu domin kuwa tsoro yafara kama mu'


Ko"Kuma nace yakama mu' har,madai ni domin kuwa Allah yayini Da matsananci tsoro,


Saboda haka sai nakara sauri tareda Kuma damke hannun Mado, muka cigaba da tafiya  har muka isa wata anguwa wanda tafi inda muka baro kyau,


Domin kuwa manya- manyan gidajene masu dauke da manyan kofofi, sai Kuma manya- manyan fitilu dasuka haske anguwar, saika rantse DA Allah badare bane rana ce,


A kofar wasu gidaje masu kamada tagwaye kuma tsaya, domin kuwa komai nasu irin guda ne, hatta da fantin kofar irin guda ne wato kore, kowani kofar da karami da babba,


abakin karamar kofar muka zauna, kuka ne ya kwace wa Mama saida tayi mai isarta sannan taci gaba da cewa...?




💞Lufhat ce💐

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page91-95


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)



edited by Zainuddeen zain




*Assalamu'alaikum, friends  dan Allah kuyi hakuri narashin gani post din Na akan lokacin abubuwan ne sai Ahankali nagode* 





----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN:THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------


only exquisite and whizkid writers are oppw to be pen writers.



✍🏾



Asalinmu mutanan" Adamawa ne kamar yadda kasani sunana A'ishatu, Amma ana kirana lndo, mahaifina Kuma sunan sa  Ibrahim amma ana kiransa Malam lro,

mukuma bappa muke kiranshi,

ita Kuma mahaifiya ta sunan ta Hajara Amma hajjo ake kiranta mukuma Inna muke kiranta,


Mu biyu iyayan mu suka haifa nida kanina Mahmud amma mado muke kiransa,


Mu fulanine gaba da baya masu zama a wannan ruggar zuwa waccan ruggar, a takai ce dai mu fulanin tashine,


Amma dai asalin ruggar mu idan muke zaune shine Husirin bombe,

nakance yar fari a gurin Inna ta' don haka take nuna Mani kunya Da  kawaici irin tamu ta Fulani, saboda haka ban faye sakin jikina da ita ba domin bata bani damar yin haka ba,


Idan ma kaga "tasaki jiki Dani toh" sai idan bappa" da Mado basanan, kamar wata rana basanan su tafi kiwo kasan cewar bappa" baya barina, natafi kiwo,

saidai yace Na zauna Na taya Inna "aikin gida kamar su tatsar nonon shanu, da Kuma dafa madara, da dai sauran aika-aikacen gida Wanda baza'a rasaba sai shi' kuma bappa da Mado su tafi kiwo,



A wannan lokacin kuwa munkai kimanin wata goma, rabanmu da ruggar mu, muna zaune nida Inna' Ina tankadan Karin tuwo ita Kuma tana kada zaren kadi (audiga),


Saina kalleta tareda jefa mata tambaya kamar haka, Inna meyasa bamu zama a ruggar mu saidai muje mudawo?

sai tace "aidaga bappan' kune yafi gaye ma haka shiyasa,

 saina Kuma cewa Inna kice ma bappan" idan muka koma kawai muyi Zan,mu a ruggar mu, karmu Kuma zuwa KO" wacce rugga,


Harara Na tayi tareda cewa toh" Sannu uwata sai kisani dole nafada masa",  tunda duk maganar Dana kemasa' bata isaba sataki daki ka kawo yanzu kam "ai zaiji sosai KO"? 

 Kin wani tasani agaba da tambaya sai kace wata  tsarar ki KO"? da sauri Na kalleta sai naga ta tsuke fuska tareda harara ta, 


toh" daganan nafahimci cewa firata tafara isarta, dama baka safai take zama Dani muke firar ba,

wani lokaci sai su bappa"da mado" basan nan KO" Kuma idan naganta cikin nishadi,


 toh" inda muke batawa da ita shine gurin tambaya, domin kuwa haka nake da dankaran tambaya kamar yar jarida,  toh" ita kuma bata san yawan tambaya don haka  dagan nan firar ke tsayawa domin kuwa tashi taka tabarni agurin, kamar lokacin danai mata wannan tambayar tashi tayi ta barni agurin,


Bin bayanta da kallo nai har saida tashiga daki sannan nayi ajiyar zuciya, domin kuwa mamakin Inna' take bani araina nace oni indo, wai Danna kasance yar' fari shikenan Kuma banida yanci daza "azauna Dani ayi fira?


Ina Cikin wanna tunani sai ga bappa shida mado sun dawo kiwo, nayi musu sannu da wowa tareda karban sandar hannun bappa Na agiye,

 yace Sannu Da gida nace yauwa,


tareda kawo masa ruwa atulo mai sanyi, ya karba yana cewa "an gaisheki' yace Ina ita lnnar tatu take bangan taba? nace tana daki, muna cikin magana saigata tafita tanayi masu Sannu, ya amsa tasamu guri ta zauna sai suka fara fira har aka kira sallar magriba,

bappa yai alwala shida mado suka tafi mallaci, nikuma mukai tama nida Inna,


*********

Bayan sati biyu da misalin karfe biyar Na yammacin ran alhamis, lokaci har mungama girkin dare nida inna bayan naci abinci sai nafita waje, Dan nisada bukkar mu kadan ta gefen wata bishiya na daura lilo,


Tunani ruggar mu kawai nakeyi Da Kuma kawayena, gaskiya a lokacin Na matsu mukoma ruggar mu,


Can nahango mado yana daga mani hannun yana dariya, nima nayi dariya tareda saukowa daga kan lilon,


A hanya muka hadu  muka Kuma yiwa juna dariya, na ce har kundawo kiwon?  yace tundazu muka dawo bappa yana Kiranki, nace lafiya dai KO"?  yace lafiya lau,


Muka jera muna tafiya muna fira sai Mado ya kalleni yace Adda Albishiri ki?, (kasan cewar haka yake kirana wato yaya kenan da fullanci), nayi murmushi tareda cewa goro madona Kuma fari tas- tas,


 Yace kinsan abokina nan Na bappa dayake bamu labarin raban dasuga juna tun suna kana nan?


Nace "eh bansan shiba Amma Kuma ban manta DA labarin sa ba,

Mado yace toh" yau mungan shi agurin kiwo, Kuma bappa yace masa" yadubi hanyar mu yau din nan zamu kawo masa ziyara,


Nace ahaba dai?  yace aradun, a dai- dai lokacin da muka karasa bukkar mu, muka isko bappa yana yiwa Inna bayani harnaji yana fadin sunan ruggar wato yolde kohe,


bayan na gaida bappa sai Na kalli Inna nace, nace Inna wata rugace yolde kohe Amma dai bamu taba zuwa can bako?

batare da takalle niba tace nima ban saniba, amma idan ki kayi hakuri "ai can zamu tafi yanzu KO?


Dajin haka Sai naja bakina natsuke  munshirya tsaf, muka fito zamu tafi sai bappa yace yana zuwa mujirasa kadan,


can sa gashi' yadawo yana cewa nafada wa "Malam jauro zamuje ruggar yolde kohe, yajimani motsin shanu tunda bazamu dawo yauba sai gobe,


"Malam jauro magocin mune, tunda muka sauka agurin sa" mike daukar karatun kasan cewar sa Malamin makaranta kallo,


haka muka Kama hanya da yamma nan, domin kuwa a lokacin rana tayija ta tafi yamma zatafadi, kunsan Fulani basuda tsoron dare, haka nan muka cigaba da tafiya, su bappa" suna gaba mu Kuma muna binsu abaya

munyi tafiya sosai,


Ta! ta!! ta!!! haka naji karan abu da sauri Na waiga bayana "aiko nai arangama dawani katon Mutum", bakikirin dashi' hannun shi yana rikeda wani abu, Wanda koba afada maniba  nasan bindiga ce"


gabana yafadi tsoro yakamani  domin kuwa ban taba ganin Mutum irin shiba, "azato nama KO" aljani ne


Sai naji yai magana Cikin kakkausar murya, yana cewa duk Wanda ya motsi koyai yankurin gudu  saina harbemashi Kai, Cikin firgici muka cukuikuye juna nida Mado, bappa Kuma yayi tsaye yayinda Inna ta boye bayan bappa, daga bayan mu Kuma mukaji wata murya mai Kama da irin wancan yace komotsai Mutum yai ka harbeshi,


 Muka Kuma rike juna nida mado, ashe su biyu ne 

Kuma kowan'ne hannun sa da bindiga, gudan yace kudi zaku bamu KO" muka she ku' yanzun nan,

bamusu bappa yafito da kudi Cikin aljihunsa ya mika masu da sauri gudan ya warce kudin yasa aljihun wandon,

 

Sannan ya kalli Inna yace ke Kuma fa? bamu kudi, Da sauri bappa yace "aisune duk Na baku' tsawa mutumin' ya bugawa bappa yace yimana shuru makaryaci


 keh! bamu kudi ? Jikinta yanarawa tace handin boni bani da kudi, yadaka mata tsawa tareda cewa karya kikeyi kina dasu, Cikin tsoro tace "aradu banidas,


Bai bari "taka rasaba yana karanta harbi agoshi, aikon take tafada kasa,

Cikin matsananci firgici muka saki juna nida Mado, muka nufi inda take kwance da sauri gudan yarike Mado,


 ni' kuma na karasa inda Inna take bappa Na kiran ta nima Ina kiran sunan ta'amma bata amsa kiranan kowa daga Cikin muba', da'alama ta amsa kiran Ubangijinmu,


Kuka nasaki domin kuwa tuni jini ya wanke mata' fuska, da sauri bappa ya dauki sandarsa yarafkawa dayan, ya Kuma rafka masa take yafadi sumamme,

 

Da gudan yaga haka saiya harbi bappa akafa, tuni bappa yafadi hannun sa rike da kafarsa dake zubar jini,


wani sabon kuka Na Kuma Saki, domin kuwa naga wayan nan mutanan suna kikarin nakasa mana rayuwa, shiko Mado yanata ihu mutumin nan yasake shi amma yaki yasake shi,

don haka sai Mado ya Kama hannun mutumin ya gantsara masa cizo, da sauri yasake shi da gudu "yataho muka hadu muka rungume Inna muna kuka hada bappa,


Domin kuwa mungane cewa Inna tarigamu gida gaskiya, da sauri mutumin  yabiyo Mado zai Kuma rikesa Ciki zafin nama bappa ya dauki sandarsa ya rafka masa akafa,

yafadi tareda rike sandar da hannun suka fara komawa da bappa, Ciki fullanci bappa yace mu tashi  mugudu

da sauri na kalleshi nace bappa Ina zamu tafi? tsawa yadaka mani yace nace kutafi KO?


Zumbur Na mike nafinciki hannun Mado nukanufi Cikin duhun daji da gudu,

gudu muke ba tsayawa munyi gudu sosai sannan muka tsaya agefen wata bishiya mai yawan ganye,


muka hada Kai nida Mado muna kuka sosai ba me lallashin wani, saida mukai mai isarmu tukun sannan mukai

shuru, can sainaji tsoro yaka mani tunani nafara yi kar wani Abu yasame mu Cikin dajin nan,


Don  haka sai Na Kuma Jan  hannun Mado" muka koma gurin su bappa, atunanina zamu iskosu koda muka isa gurin bamu iske kowaba , "aiko basan lokacin da Na Dora hannu akai Na kurma ihu kiran sunan "bappa da "Inna, shima Mado' kukan yakeyi  haka mukayi tsaye agurin muna tafan kuka, ga garin sai duhu yake karayi don haka sai Na Kuma fincikar hannun Mado,


Muka nausa Cikin dajin dagudu, gudu mukeyi batare da mun San ida muka dosaba Cikin ikon Allah sai gamu abaki titi,

nakali gabas da yamma kudu da arewa ba alamar mota KO" mashi balls keke,

Mukai tsaye Ciki jiran tsammani domin kuwa bamu Santa Ina mota KO mashin zaya bullo ba,


Can sai muka hango hasken fitilla mota daga gabas tanufo Inda muke tsaye, sai Kuma muka ga ta tsaya sai hasken fitillar ya dauke alamar ankashe,

sai Kuma mukaji shuru Na tsawan lokaci ba "akaraso inda muke ba, ni Kuma ganin haka sai naja a hannun Mado muka nufi gurin motar dagudu,


 saida mukai gudu sosai sannan muka iske motar ashe ma akori kurace,  bamu tsaya bata lokaci ba muka hau motar daba musan ida tadosa ba, mudai burin mu mubar wannan dajin, saida muka shiga muka zauna sannan ne muka fahimci ashe rake tadauko,


can sai mukaji anfisgi motar da karfi da sauri muka rike juna, Cikin tsoro domin kuwa ba mutaba shiga mota ba sai a wannan lokaci,

 Bansan KO" awa Nawa muka dauka muna tafiya ba,  saidai kam mun dauki lokaci mai tsawo muna tafiya,


Can saigamu aciki birni muna tabaza idanu muna kalle- kalle, ahaka yashiga wata anguwa ya tsaya DA alama salla zayayi  tunda munga mutane natayin alwala,


Sai bayan daya shiga masallaci ne sannan muka sauko daga motar, naja hannun Mado muka Fara tafiya ba tareda munsan inda zamu ba,


Tafiya mukeyi  batareda  mun hadu dako dabba ba balle ba bil'adamu, tsit gurin bakajin motsin  komai sai Na tafiyar mu, sai KO"bukun zuciyoyin mu domin kuwa tsoro yafara kama mu'


Ko"Kuma nace yakama mu' har,madai ni domin kuwa Allah yayini Da matsananci tsoro,


Saboda haka sai nakara sauri tareda Kuma damke hannun Mado, muka cigaba da tafiya  har muka isa wata anguwa wanda tafi inda muka baro kyau,


Domin kuwa manya- manyan gidajene masu dauke da manyan kofofi, sai Kuma manya- manyan fitilu dasuka haske anguwar, saika rantse DA Allah badare bane rana ce,


A kofar wasu gidaje masu kamada tagwaye kuma tsaya, domin kuwa komai nasu irin guda ne, hatta da fantin kofar irin guda ne wato kore, kowani kofar da karami da babba,


abakin karamar kofar muka zauna, kuka ne ya kwace wa Mama saida tayi mai isarta sannan taci gaba da cewa...?




💞Lufhat ce💐

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page96-100


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)


Slm don Allah kuyi hakuri da rashin ganin posting din Na  akan lokaci, banida Lafiya ne kwana biyu shiyasa, Amma yanzu Alhamdullah nagode,




Wannan page nakane kai *DAYA*wato *ZAINUDDEEN JIBRIN ZAIN* Ina tayaka murna zagayowar ranan haihuwar ka, *ALLAH* yakara maka tsawon rai mai *ALBARKA*

*Happy* *Birthday* once again Dan 🕺🏻 *Zainunu*😜 *ALLAH* yakara shekara masu yawa muga diyanka da jikoki harda tattaba kunne, Ameee,  Yeeeeee 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼Dan *YARO*

Cut the *CAKE* 🔪🎂🎂🎂😀


   

----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN:THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------


only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.



✍🏾



"Mado  yace Adda inajin bacci, kallon sa nai Cikin tsananin mamaki na kalle sa wato shi har yaga gurin bacci,?


Arai na kuwa fadi nake Hodijam lallai yaro yarone "inbanda abin  Madon toh" mu har wani bacci zamuti yanzu, "wayanda suke Cikin wannan tashin hankali, narashin iyaye da rashin sanin takamai man inda zamu mado sa,


 Mado ne ya katse Mani zancen zucin danake, da yasake mai-mai tamani abinda yafada,


Kallon sa nai duk sainaji yabani tausayi, domin KO" dani dashi duk munyi wurjan-wurjan, ahankali Na mike kafa-funa nace ya kwana yayi bacci, nikuma sai najingina Da kofar sai Kuma nafara tunanin,  tayaya rayuwar mu zata kasance? taya kuma zamu fara  rayuwar ba tareda "Inna da bappa ba? 


Can Kuma saina tuna " ashefa "Inna tarigamu gidan gaskiya, bansan lokacin da Na fashe Da kuka ba da sauri Na toshe bakina saboda kadana tayar da Mado daga bacci, domin naga yana jin dadin baccin,


Hakana cigaba da kukana ina tunanin kila shima bappa" sun kashe sa,  can wata zuciya tace toh" insun kashe sa ina gawarsu" take shida Inna"? can Kuma naji wata zuciya tace kura sun cinye,


Da karfi Na Kuma sakin wani sabon kuka, nace shikenan munrasa Inna" da bappa" bamu da kowa" sai Allah, ni kadai nake ta faman surutu sai kace wata tababbiya, 

Shi KO" Mado yanata bacci sa ba bu abinda ya damesa',


************

 Bansan rana tayiba sannan Kuma banji karar bude kofa ba, hakalizika banji karar fitowar mota ba,domin kuwa nayi matukar nisa a tunani Wanda yahana Mani rintsawa,

Saidai naji da karfi ance "ku Lafiya me kukeyi anan gurin?


Nasan zakai mamakin yadda "akai mukejin hausa, tunda mu fulani ne kuma "arugga muke zama, sanna kuma bamu taba zuwa birniba maka  toh" ba abin mamaki ba,


Domin  kuwa min koyi Hausa ne abakin wani Mutum mai suna  mlm Mudi" da matarsa hassu," adalilin zaman daya kawosu ruggar mu toh" saboda haka agurin su muka koyi Hausa,


 Na daga Kai don naga me wannan maganar,

"aiko nai aranga da wani kyakkawan "Mutum acikin wata, zukekiyar mota baka wulik har sheki takeyi Saboda tsananin bakinta,


Da  sauri Na duki Mado Ina cewa tashi Kai ga aljaninan yazo yakama mu, domin KO" azatona ba Mutum bane Saboda kyawunsa ya muce tunanina,


wani tunani ne yafado Mani inda Malamin mu Na makarantan allo, yataba fada mana cewa mutanan boye sunada matukar kyau, don haka saina Kama hannun Mado narike tareda yin duk wata Addu'a datazo bakina,


Mado KO" dama tuni ya watseke daga baccin dayakeyi, sai mukayi tsaye tareda tsurama wannan Mutum idanu,


Sai yafito daga Cikin motar yanufo inda muke tsaye, da saurin muka jada baya sai yayi tsaye Cikin murya sa mai dadi, yace nace Lafiya me kuke nema anan gurin? da sauri nace bakomai , toh" wakuke nema acikin gidan, nan na Kuma cewa bakowa,


Jinai yace Peter sai gawani Mutum yafito yana KO" karin rufe kofa, sai bayan da yarufe kofar ne sannan yanufo inda muke tsaye, saiji suna wani irin yare shi ba fullanci ba shi Kuma ba Hausa ba, 


Domin KO" su kadai muka iya, Saboda haka sai kawai muka tsura masu idanu, tunda bamajin abinda sunke fadi, kallon mu yasake yi yace wai kudaga Ina ku" kafito? da sauri nace daga ruggar husiri bombe,


Yace' "Ina kika ce? Na Kuma mai-mai tawa, sai naga yai shuru can Kuma yace toh" Ina iyayan Ku! sai nasaki kuka mai karfin gaske tareda cewa "ankashe su, da karfi  yace suwane ne suka kashe su? Cikin kuka nace wasu mutane ne suka kwace kudin bappan" mu, suka harbeshi akafa sannan Kuma suka harbi Inna"


Da sauri naji yace innalillahi sannan yace kubiyoni, bamu tsaya bata lokaci ba muka bisa domin KO" mungane Mutum ne ba aljaniba, Cikin wannan gidan muka shiga gidan kato ne sosai gawasu shuke- shuke Na bishiyoyi, da Kuma fulawoyi masu kamshi farfajiyar gidan Kuma, wayansu duwatsune kanana-kanana masu ban sha'awa,


Munata kalle-kalle can sai idanun mu suka kallo mana, wayan su mutane manya-manya masu bakaken kaya, dakuma dogayen bindigogi a hannun su sunkai kimanin "Mutum goma sha biyar koma fiyeda haka,


Gashin duk sunyi saranda fuskokin nan babu annuri ko" kadan, da alama jirasuke abasu dama sukashe mutanan gari gaba daya, 


Wani irin ihu nasaki mai karfi tareda rungume Mado, da sauri ya waigo inda muke yace Lafiya,? Nace mu baza mu shiga wannan gidan ba yace Saboda me? nace masu irin wannan abin'ne suka kashi mana Inna" Da bappa" Na nuna mashi, mutanan nan,


Yace "aisu wayan nan bamasu kashin mutane ba ne, masu tsaron Lafiya Mutum ne, nace a ah mudai bazamu shiga ba, yayi yayi damu mu shiga nace a ah, dadai yagada gaske bazau shiga ba sainaga ya kallesu tareda irin wannan  yaren nadazu, duk sai naga sunjuya baya "a lokacin guda,


Sai yakalle mu yace toh" kuzo mu shiga babu abinda zasuyi maku, sai muka bishi munata waigen wayan mutanan har muka shiga ba tareda sunjuyo ba,


Wani guri muka shiga mai girman sosai da kujeru manya, sannan  Kuma ga  wasu irin abuda aka manna ajikin bango mai dauke da sunan Allah, kasan Kuma wani abune mai taushi domin kuwa jimukai kamar kafaunmu zasunutse aciki,


ga Kuma wani katon hoto "aman'ne "ajikin bango, kallo guda zakaima mutanan Cikin hoton ka tabbatar tagwayene, badon komai ba sai don tsananin kamar da sukai da juna,


Ya juyo ya kallemu yace kujirani anan inazuwa,ga guri nan kuzauna mukace toh", sai yabita wata kofa yashiga cikin,


Saida muka gama kalle kallon mu sannan muka nufi kujera Dani yar zama, "aimuna zama sai muka mike zumbur kamar 

wayanda suka zauna akan "allura,

Nida Mado sai muka tsurama juna idanu domin KO" munga "aniyar hadiyemu, 


Mado yace Adda "aradun Allah idan muka zauna zata hadiye mune,

Nace eh toh" kadamu zauna,

Don haka sai mukai tsaye cirko-cieko sai kace zakarun dasuka shafada suka gaji,


Can sai gashi yafito shida wata mata kyakkyawa mai cikar kamala, tana sanye da doguwar Riga baka ta Kuma lullube kanta tada mayafi baki, kasan cewar farace sai kayan sukai mata kyau, Dana kalleta' sainaga suna Kama da wannan mutumin  daya shigoda mu gidan,


Cikin sakin fuska ta kalle mu tace toh" baku zauna ba? Mado yace aradu "in muka zauna nan gurin yana hasiyemu, sainaga sun kalli juna sunyi murmushi, tace bazai hadiye kuba nace "a ah  tayi dariya tareda cewa toh" shikenan ku zauna anan tanu banana kasa,


Muka zauna sannan suma suka zauna,muna kallo bai hadiye Suba kamar yadda muka zato, araina nace kila Dan sun saba ne, ahankali tafara tambaya ta "Ina bata amsa kamar yadda naba wannan mutumin, Wanda nake kyauta ta zaton danta ne,


Sai naga ta kallesa tace kasan ruggar dasuka fadi yace baisani ba,

tace yanzu idan akasaku amota zaku iyagane ruggar taku?


Nace "aiba amota muje zuwaba akafa muke zuwa, KO" yanzu ma wani" mai motar rake mukabiyo yakawomu nan cikin birni Amma muba  mutaba zuwaba sai yau,


Sai ta girgiza kai tace ya sunan ki' nace lndo shi Kumaz Mado, tace indo A'isha kenan KO" nace "eh toh" shi kuma Mado fa? Nace Mahamud,


Tace masa kaje  ka Kira Mani lya Asabe yace toh", can saiga shi yadawo tareda wata yar dattijiyar mata sai matar tace Haj baki mukai, tace "eh wannan sunan ta A'isha shi Kuma sunan sa Mahamud,


Don Allah Inna Asabe akaita dakin anan nakusa danawa, tayi wanka akwai kaya wadurof abata tasa sannan abaya abinci tayi karin kumallo,

ta kalli mutumin nan tace Kai Kuma kai Mahamud dakin nan  Na hanyar boy's quarter, shima yai wanka akwai kaya a cikin wadurof  kabashi yasa sannan yazo yai Karin kumallo,


Tamike tana cewa Bari "inje nasami  general kila bazaya rasa sanin ruggar tasu ba, suka amsa da toh" dukkan su" Nina bi wannan mata Da akakira Inna Asabe, shi Kuma Mado yabi wannan mutumin da bansan sunan sa ba,


Gaskiya dakin ya kayatu matukar kayatuwa, "ainan nasaki baki Ina kallo dama gani yardaji Dan haka sai nakara zama yardaji sosai,


Tanuna Mani bayi nashiga nai wanka nafito tabani mai nashafa, sannan tabani kaya nasaka sannan muka koma falo, anan muka isko   Mado shima haryana shirya, aka bamu abinci banyan mun gama sai ga,


Hajiya tafito bayanta wani mutum yana biyeda ita kyakkyawa dashi managarci, mai cikar kwarjini yasamu guri ya zauna adaya daga Cikin kujerin falon, tace

Hajiya general kaga yaran nan Kai ya girgiza Cikin tausayi mu,


Sai yace gaskiya doctor bansan ruggar nan ba Amma insha'Allahu zansa abincika Mani,

 dajin haka sai kawai nasaki kuka "Ina fadin shikenan mun banu, ahankaki ta karaso gurin na tace haba A'isha yace maki kunbanu,?


Insha'Allahu za'a gane ruggar kinji " aiyace zaya sa "abinci ka ki  ba?

Nace "eh tace toh" kidaina kuka haka nace toh" tare da share hawayan, 


Wasa-wasa saida mukayi  satin uku agidan nan batare da angane ruggar mu ba, a lokacin Kuma idan kaganmu saika rantse da Allah bamu bane fulanin nan  yan daji, mun goge munyi kyau abinbu, 

Sai ranan damuka cika sati hudu sannan aka samu Wanda yadan ruggar mu, 


"aikam dadi kamar ya kashemu don murya, munsan dai KO" bakomai idan aka kaimu husiri bombe ruggar mu, akwai kannan bappa" da Kuma Na Inna"


Don haka sai mukayi ta murna muna hada kayan mu,Wanda mu kasan anbamu Hajiya natayi mana dariya,


Saida muka gama shiryawa  tsaf sannan muka fito afalo muka isko Hajiya,


Sai muka ajiye kayan mu muka zauna tareda tsurama Hajiya idanu, ta kallemu sai tayi dariya,


 tace karfe Tara darabi na dare zamubi hanyar ruggar husiri bombe? Nace "eh toh" aimu da daddare muke tafiya, sai tace...?





💞Lufha ce💐

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page96-100


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)


Slm don Allah kuyi hakuri da rashin ganin posting din Na  akan lokaci, banida Lafiya ne kwana biyu shiyasa, Amma yanzu Alhamdullah nagode,




Wannan page nakane kai *DAYA*wato *ZAINUDDEEN JIBRIN ZAIN* Ina tayaka murna zagayowar ranan haihuwar ka, *ALLAH* yakara maka tsawon rai mai *ALBARKA*

*Happy* *Birthday* once again Dan 🕺🏻 *Zainunu*😜 *ALLAH* yakara shekara masu yawa muga diyanka da jikoki harda tattaba kunne, Ameee,  Yeeeeee 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼Dan *YARO*

Cut the *CAKE* 🔪🎂🎂🎂😀


   

----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN:THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------


only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.



✍🏾



"Mado  yace Adda inajin bacci, kallon sa nai Cikin tsananin mamaki na kalle sa wato shi har yaga gurin bacci,?


Arai na kuwa fadi nake Hodijam lallai yaro yarone "inbanda abin  Madon toh" mu har wani bacci zamuti yanzu, "wayanda suke Cikin wannan tashin hankali, narashin iyaye da rashin sanin takamai man inda zamu mado sa,


 Mado ne ya katse Mani zancen zucin danake, da yasake mai-mai tamani abinda yafada,


Kallon sa nai duk sainaji yabani tausayi, domin KO" dani dashi duk munyi wurjan-wurjan, ahankali Na mike kafa-funa nace ya kwana yayi bacci, nikuma sai najingina Da kofar sai Kuma nafara tunanin,  tayaya rayuwar mu zata kasance? taya kuma zamu fara  rayuwar ba tareda "Inna da bappa ba? 


Can Kuma saina tuna " ashefa "Inna tarigamu gidan gaskiya, bansan lokacin da Na fashe Da kuka ba da sauri Na toshe bakina saboda kadana tayar da Mado daga bacci, domin naga yana jin dadin baccin,


Hakana cigaba da kukana ina tunanin kila shima bappa" sun kashe sa,  can wata zuciya tace toh" insun kashe sa ina gawarsu" take shida Inna"? can Kuma naji wata zuciya tace kura sun cinye,


Da karfi Na Kuma sakin wani sabon kuka, nace shikenan munrasa Inna" da bappa" bamu da kowa" sai Allah, ni kadai nake ta faman surutu sai kace wata tababbiya, 

Shi KO" Mado yanata bacci sa ba bu abinda ya damesa',


************

 Bansan rana tayiba sannan Kuma banji karar bude kofa ba, hakalizika banji karar fitowar mota ba,domin kuwa nayi matukar nisa a tunani Wanda yahana Mani rintsawa,

Saidai naji da karfi ance "ku Lafiya me kukeyi anan gurin?


Nasan zakai mamakin yadda "akai mukejin hausa, tunda mu fulani ne kuma "arugga muke zama, sanna kuma bamu taba zuwa birniba maka  toh" ba abin mamaki ba,


Domin  kuwa min koyi Hausa ne abakin wani Mutum mai suna  mlm Mudi" da matarsa hassu," adalilin zaman daya kawosu ruggar mu toh" saboda haka agurin su muka koyi Hausa,


 Na daga Kai don naga me wannan maganar,

"aiko nai aranga da wani kyakkawan "Mutum acikin wata, zukekiyar mota baka wulik har sheki takeyi Saboda tsananin bakinta,


Da  sauri Na duki Mado Ina cewa tashi Kai ga aljaninan yazo yakama mu, domin KO" azatona ba Mutum bane Saboda kyawunsa ya muce tunanina,


wani tunani ne yafado Mani inda Malamin mu Na makarantan allo, yataba fada mana cewa mutanan boye sunada matukar kyau, don haka saina Kama hannun Mado narike tareda yin duk wata Addu'a datazo bakina,


Mado KO" dama tuni ya watseke daga baccin dayakeyi, sai mukayi tsaye tareda tsurama wannan Mutum idanu,


Sai yafito daga Cikin motar yanufo inda muke tsaye, da saurin muka jada baya sai yayi tsaye Cikin murya sa mai dadi, yace nace Lafiya me kuke nema anan gurin? da sauri nace bakomai , toh" wakuke nema acikin gidan, nan na Kuma cewa bakowa,


Jinai yace Peter sai gawani Mutum yafito yana KO" karin rufe kofa, sai bayan da yarufe kofar ne sannan yanufo inda muke tsaye, saiji suna wani irin yare shi ba fullanci ba shi Kuma ba Hausa ba, 


Domin KO" su kadai muka iya, Saboda haka sai kawai muka tsura masu idanu, tunda bamajin abinda sunke fadi, kallon mu yasake yi yace wai kudaga Ina ku" kafito? da sauri nace daga ruggar husiri bombe,


Yace' "Ina kika ce? Na Kuma mai-mai tawa, sai naga yai shuru can Kuma yace toh" Ina iyayan Ku! sai nasaki kuka mai karfin gaske tareda cewa "ankashe su, da karfi  yace suwane ne suka kashe su? Cikin kuka nace wasu mutane ne suka kwace kudin bappan" mu, suka harbeshi akafa sannan Kuma suka harbi Inna"


Da sauri naji yace innalillahi sannan yace kubiyoni, bamu tsaya bata lokaci ba muka bisa domin KO" mungane Mutum ne ba aljaniba, Cikin wannan gidan muka shiga gidan kato ne sosai gawasu shuke- shuke Na bishiyoyi, da Kuma fulawoyi masu kamshi farfajiyar gidan Kuma, wayansu duwatsune kanana-kanana masu ban sha'awa,


Munata kalle-kalle can sai idanun mu suka kallo mana, wayan su mutane manya-manya masu bakaken kaya, dakuma dogayen bindigogi a hannun su sunkai kimanin "Mutum goma sha biyar koma fiyeda haka,


Gashin duk sunyi saranda fuskokin nan babu annuri ko" kadan, da alama jirasuke abasu dama sukashe mutanan gari gaba daya, 


Wani irin ihu nasaki mai karfi tareda rungume Mado, da sauri ya waigo inda muke yace Lafiya,? Nace mu baza mu shiga wannan gidan ba yace Saboda me? nace masu irin wannan abin'ne suka kashi mana Inna" Da bappa" Na nuna mashi, mutanan nan,


Yace "aisu wayan nan bamasu kashin mutane ba ne, masu tsaron Lafiya Mutum ne, nace a ah mudai bazamu shiga ba, yayi yayi damu mu shiga nace a ah, dadai yagada gaske bazau shiga ba sainaga ya kallesu tareda irin wannan  yaren nadazu, duk sai naga sunjuya baya "a lokacin guda,


Sai yakalle mu yace toh" kuzo mu shiga babu abinda zasuyi maku, sai muka bishi munata waigen wayan mutanan har muka shiga ba tareda sunjuyo ba,


Wani guri muka shiga mai girman sosai da kujeru manya, sannan  Kuma ga  wasu irin abuda aka manna ajikin bango mai dauke da sunan Allah, kasan Kuma wani abune mai taushi domin kuwa jimukai kamar kafaunmu zasunutse aciki,


ga Kuma wani katon hoto "aman'ne "ajikin bango, kallo guda zakaima mutanan Cikin hoton ka tabbatar tagwayene, badon komai ba sai don tsananin kamar da sukai da juna,


Ya juyo ya kallemu yace kujirani anan inazuwa,ga guri nan kuzauna mukace toh", sai yabita wata kofa yashiga cikin,


Saida muka gama kalle kallon mu sannan muka nufi kujera Dani yar zama, "aimuna zama sai muka mike zumbur kamar 

wayanda suka zauna akan "allura,

Nida Mado sai muka tsurama juna idanu domin KO" munga "aniyar hadiyemu, 


Mado yace Adda "aradun Allah idan muka zauna zata hadiye mune,

Nace eh toh" kadamu zauna,

Don haka sai mukai tsaye cirko-cieko sai kace zakarun dasuka shafada suka gaji,


Can sai gashi yafito shida wata mata kyakkyawa mai cikar kamala, tana sanye da doguwar Riga baka ta Kuma lullube kanta tada mayafi baki, kasan cewar farace sai kayan sukai mata kyau, Dana kalleta' sainaga suna Kama da wannan mutumin  daya shigoda mu gidan,


Cikin sakin fuska ta kalle mu tace toh" baku zauna ba? Mado yace aradu "in muka zauna nan gurin yana hasiyemu, sainaga sun kalli juna sunyi murmushi, tace bazai hadiye kuba nace "a ah  tayi dariya tareda cewa toh" shikenan ku zauna anan tanu banana kasa,


Muka zauna sannan suma suka zauna,muna kallo bai hadiye Suba kamar yadda muka zato, araina nace kila Dan sun saba ne, ahankali tafara tambaya ta "Ina bata amsa kamar yadda naba wannan mutumin, Wanda nake kyauta ta zaton danta ne,


Sai naga ta kallesa tace kasan ruggar dasuka fadi yace baisani ba,

tace yanzu idan akasaku amota zaku iyagane ruggar taku?


Nace "aiba amota muje zuwaba akafa muke zuwa, KO" yanzu ma wani" mai motar rake mukabiyo yakawomu nan cikin birni Amma muba  mutaba zuwaba sai yau,


Sai ta girgiza kai tace ya sunan ki' nace lndo shi Kumaz Mado, tace indo A'isha kenan KO" nace "eh toh" shi kuma Mado fa? Nace Mahamud,


Tace masa kaje  ka Kira Mani lya Asabe yace toh", can saiga shi yadawo tareda wata yar dattijiyar mata sai matar tace Haj baki mukai, tace "eh wannan sunan ta A'isha shi Kuma sunan sa Mahamud,


Don Allah Inna Asabe akaita dakin anan nakusa danawa, tayi wanka akwai kaya wadurof abata tasa sannan abaya abinci tayi karin kumallo,

ta kalli mutumin nan tace Kai Kuma kai Mahamud dakin nan  Na hanyar boy's quarter, shima yai wanka akwai kaya a cikin wadurof  kabashi yasa sannan yazo yai Karin kumallo,


Tamike tana cewa Bari "inje nasami  general kila bazaya rasa sanin ruggar tasu ba, suka amsa da toh" dukkan su" Nina bi wannan mata Da akakira Inna Asabe, shi Kuma Mado yabi wannan mutumin da bansan sunan sa ba,


Gaskiya dakin ya kayatu matukar kayatuwa, "ainan nasaki baki Ina kallo dama gani yardaji Dan haka sai nakara zama yardaji sosai,


Tanuna Mani bayi nashiga nai wanka nafito tabani mai nashafa, sannan tabani kaya nasaka sannan muka koma falo, anan muka isko   Mado shima haryana shirya, aka bamu abinci banyan mun gama sai ga,


Hajiya tafito bayanta wani mutum yana biyeda ita kyakkyawa dashi managarci, mai cikar kwarjini yasamu guri ya zauna adaya daga Cikin kujerin falon, tace

Hajiya general kaga yaran nan Kai ya girgiza Cikin tausayi mu,


Sai yace gaskiya doctor bansan ruggar nan ba Amma insha'Allahu zansa abincika Mani,

 dajin haka sai kawai nasaki kuka "Ina fadin shikenan mun banu, ahankaki ta karaso gurin na tace haba A'isha yace maki kunbanu,?


Insha'Allahu za'a gane ruggar kinji " aiyace zaya sa "abinci ka ki  ba?

Nace "eh tace toh" kidaina kuka haka nace toh" tare da share hawayan, 


Wasa-wasa saida mukayi  satin uku agidan nan batare da angane ruggar mu ba, a lokacin Kuma idan kaganmu saika rantse da Allah bamu bane fulanin nan  yan daji, mun goge munyi kyau abinbu, 

Sai ranan damuka cika sati hudu sannan aka samu Wanda yadan ruggar mu, 


"aikam dadi kamar ya kashemu don murya, munsan dai KO" bakomai idan aka kaimu husiri bombe ruggar mu, akwai kannan bappa" da Kuma Na Inna"


Don haka sai mukayi ta murna muna hada kayan mu,Wanda mu kasan anbamu Hajiya natayi mana dariya,


Saida muka gama shiryawa  tsaf sannan muka fito afalo muka isko Hajiya,


Sai muka ajiye kayan mu muka zauna tareda tsurama Hajiya idanu, ta kallemu sai tayi dariya,


 tace karfe Tara darabi na dare zamubi hanyar ruggar husiri bombe? Nace "eh toh" aimu da daddare muke tafiya, sai tace...?





💞Lufha ce💐

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page101-105


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)


edited by Zainuddeen zain


----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN:THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------


only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.



✍🏾



"A ah nikam bazanyi tafiyar dare ba, kunga yanzu abinda nakeso daku shine Ku kwashi kayan nan Ku maidasu daki, gobe da safe Ina Allah ya kaimu sai mufi dawuri,b


Kunga dama gobe  Lahadi ba "aiki sai mutafi harda, Magaji domin yace Mani yana hanyar dawowa gida, tunda shima nagane yakoyi tafiyar dare irin ku,


Ta kallemu tana murmushi taciga ba dacewa basai mutafi harda shi ba? Cikin zoyaya tace kodai kungaji DA Hajiyar takune, shine yasa ku kamatsu Ku tafi kubarni?

Na dukar dakai kasa tareda cewa "a ah, 


Tace toh" Ku mayar da kayan daki sai kuzo muyi fira, mukace toh' kowa yanufi daki don ya ajiye kayan,


Ni KO" arai Na tambaya nake wanene kuma Magaji? domin inajin wani lokaci Inna Asabe Na fadin Magajin gida Amma ban taba gani shi ba,


Sannan wani abin mamaki shine tun ranan da wannan "mutumin, yashiga damu wannan gidan haryau ban sake ganinsa ba,

Wata kila "Mado ya ganshi Amma nidai kam banganshi ba,


Muna kallon wani film nayaki Wanda nalura Hajiya Na matukar San kallo, da idan muna kallo tsoro mukeji amma damuka saba sai muka daina jin tsoro,



Muna kallo tana dan janmu dafira muna mayar mata,

Sai "akai sallama muka amsa tareda kallon maiyin sallama,


Zumbur namike tareda boyewa bayan Hajiya, Saboda tsananin tsoro domin kuwa saye yake da kaya irin na mutanan da muke kallon acikin 

harda wata yar karamar bindiga "asake akugun sa,


Da sauri nace SOJA kasan cewar Hajiya tafada mana sunan wayan damuke kallo acikin t.v,


Murmushi yai Wanda yakara mashi kyau da kwarjini yace Na'am,

Sai Na kalli Hajiya Cikin sanyin jiki nace "au Hajiya itama SOJA takeyi? tace "eh a hankali Na zauna tareda fashewa da kuka,


Da sauri Hajiya tada fani tace A'isha Lafiya meya faru? Nace itama tana kashin mutane tunda gatan da bindiga, shikenan muna zata kashe mu KO?


Zama yayi dirshan yana dariya saina daina kuka Na tsaye kallon sa, yanada kyau kwarai da gaske sai Kuma dariya shi takara masa kwarjini,


Dana kalli Hajiya sainaga tana murmushi, sai nace Hajiya "ai itama tana kashin mutane KO?

tace "a ah sai mace toh" me takeyi dawan nan bindiga? 


Saiya tsaya dayin dariya sannan yazaro yar bindigar, da saurayi Na matsa kusada Hajiya, sai ya Kuma yin dariya sannan yace kinga wannan ko ? Nace "eh yace toh" da irinta ake kashe mutanan nan dasuka tareku "ahanya,


Da sauri nace yauwa irin su zakirika kashe wa tunda, din azzalumai ne masu raba yaya da iyayansu nafada kamar zanyin kuka,


Hajiya tace banasan kukan nan daki keyi share hawayen nan, da sauri Na share domin Na fahimci Hajiya Na san mu  ya maida bindigar "agurin zamanta


 Sannan ya gaida Hajiya sai nida Mado muka gaidashi, Sai naji tana tambaya sa  "ina Aina'u"?,

Sainaga ya yamutsa fuska sannan yace tareda "ita muka fito tace' Na sauke ta agidan gwaggo Rakiya,

tace" tana gaidake' wai sai gobe zata zota gaida Ku,


itama ta amsa fuska bafara'a tace toh" aishikenan, Amma dai kotazo gobe bazata iskoni ba,tunda asamu wanda ya san  ruggar su A'isha,


Yace masha'allah yanzu gobe-gobe zasu tafi, tace "eh suda sukace da yau zasu tafi ni nace su bari sai gobe, 


Ya kalleni' yace "au da tafiya zakuyi ba tareda muyi sallama ba? nace " a ah dama "ai Hajiya tace abari sai Magaji yadawo, sannan mutafi gobe,

gashi kaima kadawo ba sai atafi harda Kai ba


Sai naga sunyi murmushi yace toh" Allah ya kaimu goben Lafiya, nace Amin, saidai  tunani  nakeyi  araina wacece Aina'u,? kaina nake tambaya wanda nasani banida amsarta, gadai masu bani amsar nan,saidai kuma kash! bazan iya tambayar suba domin kuwa sudin mutane ne masu girma wayan da kokaso tambayar su" abu kwarjini su da haibarsu bazata barka ka tambaye su" abuba, sundan taba fira kadan sannan yai mata sallama ya tafi,


 *********

  Washe gari da misalin karfe takwas na safiyar Lahadi,  bayan mungama karya kumallo, muna tsaye afalo nida Mado muna rikeda kayan mu, Hajiya muke jira tafito,


 Sai gasu itada maigidan ta Wanda take kirasa Da general, suka kalli juna sukai dariya, saina gaida su shima Mado ya gaida su, suka amsa fuskarsu cike da fara'a,


Cikin zolaya yace doctor  "aini har "Ina cewa mun samu yaya,tayi murmushi tace wlh nima Da haka nace saidai

 Kuma naga yayan, sai sauri suke sugudu subar uwartasu KO" A'isha?


Nace "a ah Hajiya "aiko muntafi zamu dinga zuwa muna ganin ki ko Mado? yace " eh, ta kalli maigidanta tace kaji abinda "sukace KO? yace naji  ta kuma cewa kunyi Alkawari  zakudiga zuwa? nace "eh tace  toh  shikenan  Allah yasa  kutashi mutafi,


 Muna zaune acikin mota ni' da Hajiya da Mado muna abayan, Shi Kuma Soja (nikan soja nake kiransa tunda bansan sunan sa ba)yana zaune agurin maituki da alama shi zaya kaimu , sai kuma Mutumin dazaya rakamu akusa da Soja mai suna Malam Habu,


Har Soja' zaya tada mota sainai saurin cewa Hajiya gashi har za'a tafi ita "Magaji batazo ba?


Murmushi tayi tace A'isha kenan toh "ai shine' yaza jamu zuwa ruggar taku,


Da sauri Na kalli Soja sai naga shima'  yana kallo Na', mai hade Da murmushi yace yanzu ke' da har Zaku tafi ba tareda kinsan 'suna Na ba?

 Dai-dai lokacin da maigadi" yabude mana kofa muka fito muka dauki hanya,


Da sauri nace "a ah toh" aike nasan sunan ki Soja mana ko"?


Yace "a ah ni basuna na Soja ba Soja sunan "aikina ne, amma ni suna Na AHMED su Hajiya ne suke kirana' Magaji, kema Zaki iya kirana Magaji KO" ki kirani Ahamed dina,


Ahankali Na gukar da kaina kasa cikin jin nauyinsa' nace toh" kiyi hakuri ni bansan sunanki kenan ba,

Sannan Kuma kiyi hakuri bazan iya kiran sunan kiba,


Da sauri naji yace Saboda me? Kaina' nakasa  Nace shaboda sunan ki yanada girma saidai zani cigaba da kiran ki SOJA,


Yace toh" shikenan Amma dai kidaina kirana mace,"aikece mace Amma ni' "aina mijine ko"? Nace toh" Hajiya itada mlm Habu sai dariya suke yimana, harda shima Sojan dariya yake,


Can Kuma sai kaji motar "anyi shuru yayinda Soja yaketa sharara gudu akan titi, tum muna tafiya akan titi har mukafara tafiya cikin Dani, yayida mlm Habu yake muna masa' hanya munyi tafiya mai tsawon sosai, Wanda har saidai Hajiya tace mlm Habu' Amma dai ruggar akwai nisa? yace sosai ma kuwa, tace toh" Allah yakaimu Lafiya, yace amin. ahaka har Allah yasa muka isa ruggar husiri bombe Lafiya.


bayan yai fakin sai muka firfito daga motar, kallo guda naima ruggar araina Nace ayya wannan mlm Habun yasan ruggar mu kuwa?

  

Domin kuwa banga bukko kinmu ba wanda suke sunkai guda goma sha,toh" amma kuma yanzu bukka guda nagani kol,


Mlm Habu ne ya katse Mani zancan zucin danake, jinai yace naga ruggar tasake mun ne amma dai bari Na tambayi mutumin can,

dayake alwala suka nufi gurin shida Soja, mu kuma sai mukatsa jiransu.


Shikam Mado yakasa hakuri saida yace Adda amma dai wannan ba ruggar mu bane KO"?

Jikina asanyaye Nace Mado nan ne, bakaga "inda ku keyin gardo gardo ba kaida su jauro ba, 

Yace' eh Adda nan ne toh "Inasu Kawu dasu jauro hadasu Dija kawayanki,' kum...

Yayi shuru Saboda ganin su Soja sun dawo, gabana yafadi saka makon ganin fuskokin su ba bara'a,


Hajiya tace yadai mlm Habu meya faru ne? ya girgiza Kai yace wai  "a tun lokacin da yanfashi suka kashe  matarsa, sai yan'uwana suka dawo dashi wannan ruggar don suyi jinyarsa,


 Kasan cewar sun harbesa" akafa toh" bayan kwana biyu Kuma, sai suka tashi gaba daya daga wannan ruggar, Kuma mun tambaye shi KO" yasan "inda suka koma yace shi wallahi baisan "inda suka koma ba,


Kuka nasaki "Ina fadin mu kam mu shiga uku  shikenan banida kowa, da sauri Hajiya ta rungumeni tace  "akul  nasa kejin wannan Kalmar tafito daga bakin ki',


Sannan Kuma kiyi maza ki gaggauta yin istigifari, domin KO" kin sabi ALLAH,

ta Kuma cewa shin ke kika halicci  kanji?  Nace "a ah  Waya halicce ki' Nace ALLAH, tace yauwa toh" aiduk Wanda yakeda ALLAH toh" "aiyana da kowa,


Saboda haka share hawayen ki' domin  nagane cewa kudin amanace ALLAH ya bani, don haka nikuma zanrike amana Kuma "Ina rokon  Ubangijinmu, yata yani riko, 


Saboda haka kwantar da hankalin ki' nizan rike Ku tamkar yayan Dana haifada da cikina, sai "a lokacin naji hankali ya kwanta,


Ta' kalli Soja tace maidamu gida, yace toh"  Amma Hajiya da mun tsaya munyi sallah tunda naga lokaci yayi, tace' "eh yaja mata muyi kar mutafi da ita akai, tunda bamusan lokacin da zamu isa gida ba.


Bayan munyi sallah "agidan wannan mutumin sannan muka Kama hanyar komawa gida,

sai kusan sallar magrib sannan muka isa gida.


 Bayan munyi sallah munci abinci muna zaune afalo muna kallo, saiga general yafito ya zauna kusada Hajiya tace sannu da fitowa yace yauwa,sannan  muka gaida shi ya amsa tareda cewa A'isha nace na'am yace Doctor tayi Mani bayani komai, Saboda haka Ku kwantar da hankalin Ku" Ku dauka cewa nan gidaku ne kinji KO? Nace toh"


Cikin wasa yace Doctor "ashe maganta tazama gaskiya danace mun samu yaya? yakara sa maganar dayin dariya itama dariya tayi tace takam zama, yace toh" Allah yata yamu riko tace amin,


***********


Bayan kwana biyu da misalin karfe goma nasafiyar litini "Ina zaune afalo nikada "Ina kallo kasan cewar Hajiya" ta tafi gurin "aiki  Mado" Kuma yafita, Inna " Asabe Kuma tan kichin tana "akinta, Saboda haka sai Na kasance ni' kadai,


Azahiri "inkagani zakace "eh kallo nake, toh" Amma Kuma ba kallon nakeyi ba domin kuwa nayi nisa "atunani,Wanda ba lallai bane nafahimci "abinda akeyi a" T.V


Don haka banji shigo warsa ba ballan tana "insan zaman sa, saidai kawai naga mutun zaune kusada ni' KO" Kuma Nace naji kamshin turaren sa'


Da sauri Na waiga Sojane ya tsura Mani idanu, nadukar DA kaina kasa Nace "Ina kwana? bai "amsa ba saidai yayi Dan guntu tsaki mtsww.... da sauri na dagoda Kai Na kallesa,


Batare da ya kalleni ba yace "inacan office  jikina yabani cewa kina nan kina "aikin tunani, narasa "abinda yasa haryanzu kin kasa sakin jikin ki' damu, kiduba kiga Mahamud tuni yasaki jikinsa yanata harkokin sa ba'abinda yada mesa,


Yace A'isha Nace na'am, ko" har yanzu baki yarda samu bane kina ganin kamar zamu cuceku ne? da sauri Nace "a ah,


Yace toh" meyasa bazaki Zaki jikin ki' kiyi harkokin ki' kamar yanda kowa yakeyi ba,?  bance komai ba sai ya girgiza Kai tareda mikewa,

 Yaje ya dauko wanna babban Hoton dayake manne "ajikin bango,

sannan yadawo ya zauna ya kalleni yace....?




💐Lufhat ce💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page101-105


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)


edited by Zainuddeen zain


----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN:THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------


only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.



✍🏾



"A ah nikam bazanyi tafiyar dare ba, kunga yanzu abinda nakeso daku shine Ku kwashi kayan nan Ku maidasu daki, gobe da safe Ina Allah ya kaimu sai mufi dawuri,b


Kunga dama gobe  Lahadi ba "aiki sai mutafi harda, Magaji domin yace Mani yana hanyar dawowa gida, tunda shima nagane yakoyi tafiyar dare irin ku,


Ta kallemu tana murmushi taciga ba dacewa basai mutafi harda shi ba? Cikin zoyaya tace kodai kungaji DA Hajiyar takune, shine yasa ku kamatsu Ku tafi kubarni?

Na dukar dakai kasa tareda cewa "a ah, 


Tace toh" Ku mayar da kayan daki sai kuzo muyi fira, mukace toh' kowa yanufi daki don ya ajiye kayan,


Ni KO" arai Na tambaya nake wanene kuma Magaji? domin inajin wani lokaci Inna Asabe Na fadin Magajin gida Amma ban taba gani shi ba,


Sannan wani abin mamaki shine tun ranan da wannan "mutumin, yashiga damu wannan gidan haryau ban sake ganinsa ba,

Wata kila "Mado ya ganshi Amma nidai kam banganshi ba,


Muna kallon wani film nayaki Wanda nalura Hajiya Na matukar San kallo, da idan muna kallo tsoro mukeji amma damuka saba sai muka daina jin tsoro,



Muna kallo tana dan janmu dafira muna mayar mata,

Sai "akai sallama muka amsa tareda kallon maiyin sallama,


Zumbur namike tareda boyewa bayan Hajiya, Saboda tsananin tsoro domin kuwa saye yake da kaya irin na mutanan da muke kallon acikin 

harda wata yar karamar bindiga "asake akugun sa,


Da sauri nace SOJA kasan cewar Hajiya tafada mana sunan wayan damuke kallo acikin t.v,


Murmushi yai Wanda yakara mashi kyau da kwarjini yace Na'am,

Sai Na kalli Hajiya Cikin sanyin jiki nace "au Hajiya itama SOJA takeyi? tace "eh a hankali Na zauna tareda fashewa da kuka,


Da sauri Hajiya tada fani tace A'isha Lafiya meya faru? Nace itama tana kashin mutane tunda gatan da bindiga, shikenan muna zata kashe mu KO?


Zama yayi dirshan yana dariya saina daina kuka Na tsaye kallon sa, yanada kyau kwarai da gaske sai Kuma dariya shi takara masa kwarjini,


Dana kalli Hajiya sainaga tana murmushi, sai nace Hajiya "ai itama tana kashin mutane KO?

tace "a ah sai mace toh" me takeyi dawan nan bindiga? 


Saiya tsaya dayin dariya sannan yazaro yar bindigar, da saurayi Na matsa kusada Hajiya, sai ya Kuma yin dariya sannan yace kinga wannan ko ? Nace "eh yace toh" da irinta ake kashe mutanan nan dasuka tareku "ahanya,


Da sauri nace yauwa irin su zakirika kashe wa tunda, din azzalumai ne masu raba yaya da iyayansu nafada kamar zanyin kuka,


Hajiya tace banasan kukan nan daki keyi share hawayen nan, da sauri Na share domin Na fahimci Hajiya Na san mu  ya maida bindigar "agurin zamanta


 Sannan ya gaida Hajiya sai nida Mado muka gaidashi, Sai naji tana tambaya sa  "ina Aina'u"?,

Sainaga ya yamutsa fuska sannan yace tareda "ita muka fito tace' Na sauke ta agidan gwaggo Rakiya,

tace" tana gaidake' wai sai gobe zata zota gaida Ku,


itama ta amsa fuska bafara'a tace toh" aishikenan, Amma dai kotazo gobe bazata iskoni ba,tunda asamu wanda ya san  ruggar su A'isha,


Yace masha'allah yanzu gobe-gobe zasu tafi, tace "eh suda sukace da yau zasu tafi ni nace su bari sai gobe, 


Ya kalleni' yace "au da tafiya zakuyi ba tareda muyi sallama ba? nace " a ah dama "ai Hajiya tace abari sai Magaji yadawo, sannan mutafi gobe,

gashi kaima kadawo ba sai atafi harda Kai ba


Sai naga sunyi murmushi yace toh" Allah ya kaimu goben Lafiya, nace Amin, saidai  tunani  nakeyi  araina wacece Aina'u,? kaina nake tambaya wanda nasani banida amsarta, gadai masu bani amsar nan,saidai kuma kash! bazan iya tambayar suba domin kuwa sudin mutane ne masu girma wayan da kokaso tambayar su" abu kwarjini su da haibarsu bazata barka ka tambaye su" abuba, sundan taba fira kadan sannan yai mata sallama ya tafi,


 *********

  Washe gari da misalin karfe takwas na safiyar Lahadi,  bayan mungama karya kumallo, muna tsaye afalo nida Mado muna rikeda kayan mu, Hajiya muke jira tafito,


 Sai gasu itada maigidan ta Wanda take kirasa Da general, suka kalli juna sukai dariya, saina gaida su shima Mado ya gaida su, suka amsa fuskarsu cike da fara'a,


Cikin zolaya yace doctor  "aini har "Ina cewa mun samu yaya,tayi murmushi tace wlh nima Da haka nace saidai

 Kuma naga yayan, sai sauri suke sugudu subar uwartasu KO" A'isha?


Nace "a ah Hajiya "aiko muntafi zamu dinga zuwa muna ganin ki ko Mado? yace " eh, ta kalli maigidanta tace kaji abinda "sukace KO? yace naji  ta kuma cewa kunyi Alkawari  zakudiga zuwa? nace "eh tace  toh  shikenan  Allah yasa  kutashi mutafi,


 Muna zaune acikin mota ni' da Hajiya da Mado muna abayan, Shi Kuma Soja (nikan soja nake kiransa tunda bansan sunan sa ba)yana zaune agurin maituki da alama shi zaya kaimu , sai kuma Mutumin dazaya rakamu akusa da Soja mai suna Malam Habu,


Har Soja' zaya tada mota sainai saurin cewa Hajiya gashi har za'a tafi ita "Magaji batazo ba?


Murmushi tayi tace A'isha kenan toh "ai shine' yaza jamu zuwa ruggar taku,


Da sauri Na kalli Soja sai naga shima'  yana kallo Na', mai hade Da murmushi yace yanzu ke' da har Zaku tafi ba tareda kinsan 'suna Na ba?

 Dai-dai lokacin da maigadi" yabude mana kofa muka fito muka dauki hanya,


Da sauri nace "a ah toh" aike nasan sunan ki Soja mana ko"?


Yace "a ah ni basuna na Soja ba Soja sunan "aikina ne, amma ni suna Na AHMED su Hajiya ne suke kirana' Magaji, kema Zaki iya kirana Magaji KO" ki kirani Ahamed dina,


Ahankali Na gukar da kaina kasa cikin jin nauyinsa' nace toh" kiyi hakuri ni bansan sunanki kenan ba,

Sannan Kuma kiyi hakuri bazan iya kiran sunan kiba,


Da sauri naji yace Saboda me? Kaina' nakasa  Nace shaboda sunan ki yanada girma saidai zani cigaba da kiran ki SOJA,


Yace toh" shikenan Amma dai kidaina kirana mace,"aikece mace Amma ni' "aina mijine ko"? Nace toh" Hajiya itada mlm Habu sai dariya suke yimana, harda shima Sojan dariya yake,


Can Kuma sai kaji motar "anyi shuru yayinda Soja yaketa sharara gudu akan titi, tum muna tafiya akan titi har mukafara tafiya cikin Dani, yayida mlm Habu yake muna masa' hanya munyi tafiya mai tsawon sosai, Wanda har saidai Hajiya tace mlm Habu' Amma dai ruggar akwai nisa? yace sosai ma kuwa, tace toh" Allah yakaimu Lafiya, yace amin. ahaka har Allah yasa muka isa ruggar husiri bombe Lafiya.


bayan yai fakin sai muka firfito daga motar, kallo guda naima ruggar araina Nace ayya wannan mlm Habun yasan ruggar mu kuwa?

  

Domin kuwa banga bukko kinmu ba wanda suke sunkai guda goma sha,toh" amma kuma yanzu bukka guda nagani kol,


Mlm Habu ne ya katse Mani zancan zucin danake, jinai yace naga ruggar tasake mun ne amma dai bari Na tambayi mutumin can,

dayake alwala suka nufi gurin shida Soja, mu kuma sai mukatsa jiransu.


Shikam Mado yakasa hakuri saida yace Adda amma dai wannan ba ruggar mu bane KO"?

Jikina asanyaye Nace Mado nan ne, bakaga "inda ku keyin gardo gardo ba kaida su jauro ba, 

Yace' eh Adda nan ne toh "Inasu Kawu dasu jauro hadasu Dija kawayanki,' kum...

Yayi shuru Saboda ganin su Soja sun dawo, gabana yafadi saka makon ganin fuskokin su ba bara'a,


Hajiya tace yadai mlm Habu meya faru ne? ya girgiza Kai yace wai  "a tun lokacin da yanfashi suka kashe  matarsa, sai yan'uwana suka dawo dashi wannan ruggar don suyi jinyarsa,


 Kasan cewar sun harbesa" akafa toh" bayan kwana biyu Kuma, sai suka tashi gaba daya daga wannan ruggar, Kuma mun tambaye shi KO" yasan "inda suka koma yace shi wallahi baisan "inda suka koma ba,


Kuka nasaki "Ina fadin mu kam mu shiga uku  shikenan banida kowa, da sauri Hajiya ta rungumeni tace  "akul  nasa kejin wannan Kalmar tafito daga bakin ki',


Sannan Kuma kiyi maza ki gaggauta yin istigifari, domin KO" kin sabi ALLAH,

ta Kuma cewa shin ke kika halicci  kanji?  Nace "a ah  Waya halicce ki' Nace ALLAH, tace yauwa toh" aiduk Wanda yakeda ALLAH toh" "aiyana da kowa,


Saboda haka share hawayen ki' domin  nagane cewa kudin amanace ALLAH ya bani, don haka nikuma zanrike amana Kuma "Ina rokon  Ubangijinmu, yata yani riko, 


Saboda haka kwantar da hankalin ki' nizan rike Ku tamkar yayan Dana haifada da cikina, sai "a lokacin naji hankali ya kwanta,


Ta' kalli Soja tace maidamu gida, yace toh"  Amma Hajiya da mun tsaya munyi sallah tunda naga lokaci yayi, tace' "eh yaja mata muyi kar mutafi da ita akai, tunda bamusan lokacin da zamu isa gida ba.


Bayan munyi sallah "agidan wannan mutumin sannan muka Kama hanyar komawa gida,

sai kusan sallar magrib sannan muka isa gida.


 Bayan munyi sallah munci abinci muna zaune afalo muna kallo, saiga general yafito ya zauna kusada Hajiya tace sannu da fitowa yace yauwa,sannan  muka gaida shi ya amsa tareda cewa A'isha nace na'am yace Doctor tayi Mani bayani komai, Saboda haka Ku kwantar da hankalin Ku" Ku dauka cewa nan gidaku ne kinji KO? Nace toh"


Cikin wasa yace Doctor "ashe maganta tazama gaskiya danace mun samu yaya? yakara sa maganar dayin dariya itama dariya tayi tace takam zama, yace toh" Allah yata yamu riko tace amin,


***********


Bayan kwana biyu da misalin karfe goma nasafiyar litini "Ina zaune afalo nikada "Ina kallo kasan cewar Hajiya" ta tafi gurin "aiki  Mado" Kuma yafita, Inna " Asabe Kuma tan kichin tana "akinta, Saboda haka sai Na kasance ni' kadai,


Azahiri "inkagani zakace "eh kallo nake, toh" Amma Kuma ba kallon nakeyi ba domin kuwa nayi nisa "atunani,Wanda ba lallai bane nafahimci "abinda akeyi a" T.V


Don haka banji shigo warsa ba ballan tana "insan zaman sa, saidai kawai naga mutun zaune kusada ni' KO" Kuma Nace naji kamshin turaren sa'


Da sauri Na waiga Sojane ya tsura Mani idanu, nadukar DA kaina kasa Nace "Ina kwana? bai "amsa ba saidai yayi Dan guntu tsaki mtsww.... da sauri na dagoda Kai Na kallesa,


Batare da ya kalleni ba yace "inacan office  jikina yabani cewa kina nan kina "aikin tunani, narasa "abinda yasa haryanzu kin kasa sakin jikin ki' damu, kiduba kiga Mahamud tuni yasaki jikinsa yanata harkokin sa ba'abinda yada mesa,


Yace A'isha Nace na'am, ko" har yanzu baki yarda samu bane kina ganin kamar zamu cuceku ne? da sauri Nace "a ah,


Yace toh" meyasa bazaki Zaki jikin ki' kiyi harkokin ki' kamar yanda kowa yakeyi ba,?  bance komai ba sai ya girgiza Kai tareda mikewa,

 Yaje ya dauko wanna babban Hoton dayake manne "ajikin bango,

sannan yadawo ya zauna ya kalleni yace....?




💐Lufhat ce💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page106-1010


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)




----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN:THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------


only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.



✍🏾



Yanzu idan "aka tambaye ki  "mutanan cikin Hotan nan, dawa sukai Kama meza kice? Da sauri Nace tagwaye,


Yai murmushi yace hakane tagwaye nesu," wannan shine babba general ABDUL-JALAL" kenan shene mai gidan nan  sai muna kiransa baba general,


Wannan Kuma shine karami engineer  ABDULl-JABBAR" kenan, shine kuma baba engr muke  kiransa,


Gidan sane na kusa da wannan "aikin gashi KO"? Nace "eh, yace su uku ne iyayansu" suka haifa  da kanwarsu wacce takasan ce' Gambon su' mai suna goggo "Rakiya,


Kuma dukkan iyayansu" sun rasu da sauri Na kallesa yace "eh kwarai da gaske sun rasu ba wanda yarage daga ya"ya sai abokan arziki,


Kinga mahaifinsu "Alh Ahmed Dan kwangila, tsohon Dan kwangilane Kuma ma'aikacin gwamnati ne, yarasu ne " asana diyar hatsarin jirgin sama, daga London zuwa gida Najeriya, kasan cewar yana taba kasuwancin "acan ,


Mutuwar sa" ta taba iyayansa DA Kuma matarsa kasan cewar sun shakuda shi sosai,  hakana sukayi hakuri suka rungumi mahaifiyar su" saidai Kuma kash!, ALLAH maiyadda yasa a lokacin da yaga dama, bayan  mutuwar mahaifinsu" da shekara guda sai ALLAH yaima  Hajiya Hajara rasuwa, wato mahaifiyar su" sun  girgiza kwarai da gaske da rashin iyayansu" dasu kayi "a kusan lokacin guda,


Hakan su kayi hakuri suka rungumi junansu', suka Kuma rike maraicinsu domin sun'san iyayansu" sunyi masu nisa,


Bawani mai taimakon su sai ALLAH suka cigaba da gudanar da harkokin su" har suka kammala karatun su", suka cigaba Da kulada dukiyar da mahaifinsu" yabari ,

ga Kuma "aikinsu dasu keyi sukai "auransu a lokaci guda,


Saida ALLAH bai ba Baba gen haihuwa ba, shikam Baba engr ALLAH yabasa domin "a lokacin shekaransu" goma shabiyar  dayin "aure  ya"yansa biyar duk yanmata,

"Baba engr yana tausayama dan'uwansa" da rashin haihuwar DA ALLAH bai basaba,


Don haka sai yabashi babbar yarsa wadda taci sunan mahaifiyar su' wato Hajara Amma sai anakiran ta da "Uwa baba gen yaji dadin abinda dan'uwansa yai masa, don haka sai suka dauki son duniya suka dorawa Adda "Uwa,


Kwatsam sai ga Hajiya Binta tasamu Ciki wato matar Baba gen, kenan zokiga murna agurin wayan bayin ALLAH, cikin yana wata biyar suka tafi Saudiyya,  saida ta haihu sannan suka dawo tahaifi DA namiji, akasa masa suna AHMED wato sunan mahaifinsu"


"Baba engr ne yasa masa wannan suna  domin kuwa yace shine MAGAJIN gida, DA saurin Na kallesa sai naga shima niyake kallo, yai murmushi yace "eh dalilin dayasa akekirana magaji kenan, 


Amma fa "anan gida ne kawai suke kirana da Magaji, awaje kam Ahmed dina "ake kirana,

Tun "inajariri "baba engr yake sawa anakai nasani', har nai wayo nake zuwa da kaina Saboda haka nafi sabawa dashi, 


Yanayi Mani duk abinda nakeso KO" kadan bayasan bacin raina, yadda nake ganin "Baba gen acikin kakin SOJA shine yake bani sha'awa, sai nacewa "Baba engr nima SOJA  zanyi sai yayi dariya yace Magiji kenan toh", kadage da karatu saikaga kazama Soja,


Dan haka saina dage da karatu wanda rabinayi sane akasar waje, har Na kammala tafito Soja, bayan nafara "aikine sai Baba engr yace' saura aure sainace masa niban samu yarinyar da nakeso ba, sai yace "aisu yanke shawara zasu hadamu aure nida " "Aina'u yar gurin goggo "Rakiya,


Duk dacewa bana Santa, hakan baisa nayimasa" musu ba domin kuwa bazan iya jayyada shiba, sai kawai Na amsa masa da toh" ba'adauki wani lokaci mai tsawon ba akai auran mu,


Yau shekara daya kenan da wata biyar dayin auren mu, yaushe zakuje gidana keda Mahamud? koda yake haryanzu bakisaki jikin kiba balle Hajiya tasa drive yakai ku,


Yace A'isha don Allah kisaki jikin ki kinga kamar ranan da babu "aiki sai nazo nakaiku gidan "Adda Uwa da "Adda murja "Adda Safiya  "Adda Sa'adatu" da Kuma gidan Jamila autar "Baba engr ita ba adade dayin auren ta ba, azaku jeko?


Yafada 'yana murmushi nima murmushi nayi tareda sun kuyar Da

 kaina kasa Nace "eh, yace yauwa A'isha haka nakeso,

Dai-dai lokacin da yamayar da hoton gurin zaman sa,


Mado ne yashigo da sauri yana cewa Adda zoki gani, nace mezan gani? yace zodai muje kigani, tareda Soja muka fita koda muka fita sai mukaga yara" suna sayeda wani irin kaya, duk da dai bansan ko kayan meye ba, amma dai ga dukkan alama kayan makaranta,


Lallai kuwa wai kayan makaranta Boko ne, Mado yace Hamman Soja nima inasan irin wannan kayan, yai murmushi yace ashe kana San kazama Dan makaranta Boko kenan? 


yace "eh yana so, sai Ya kalleni yace kefa A'isha kina so? Nace "eh, yace toh" Ku bari sai gobe insha'Allahu saina Kai Ku mukace toh"

Koda Hajiya da baba  gen suka dawo muka fada musu sunyi murna sosai,


**************

 Washe gari tun karfe bakwai Soja yazo yadaukemu muka isa makaranta,

 Ciki lokacin kadan aka gama komai wani sati  muka fara zuwa makaranta boko,

Dama tuni muna zuwa makaranta  allo,


Saida gabaya nafahimci cewa ashe awan can lokaci karatun Boko sai Dan wane' dawane keyin sa, hakan mukaci gabada zuwa makaranta Boko, data data allo Cikin nutsuwa Da kwanciyar hankali,


Saboda haka Cikin lokacin kankani muka rikida muka zama zuriyan Alh Ahmed Dan kwangila, idan kaganmu sai karantse da Allah Cewa mu yayan "Baba gen ne, Saboda yadda muka saje da su "Adda Uwa,


Muna yima kowa biyayya, haka zalika muna bin kowa sauda kafa, Saboda 

Bamuda matsala da kowa kaf zuriyan  nan kowan yana sanmu, idan kacire Mutum biyu wato "goggo Rakiya da yarta' "Aina'u  sunan kam nasara abida mukai masu ba basu sanmu,

tsakanin mu dasu sai zagi da hantara ga "goggo Rakiya irin mutanan nan ne masifaffu,


Daga ita har "yarta gashi nikuma Allah yasaka mun tsoron su"shiko "Mado baya tsoron su' KO" kadan, yayinda Na lura ita Kuma Aina'u tana shakkar "Mado sosai, don KO" idan yana gida kota zo batayi Mani rashin mutunci Wanda sai takula "Hajiya bata kusa sannan takeyi mun,


Cikin haka har muka gama mataki nafarko karatun Boko, munajiran mutafi mataki nagaba sai kuma samari suka fara neman aure na domin KO" nazama budurwa tunda a lokacin shekara ta goma sha hudu,


Shikam "Hamman Soja baya so "Ina kula samari saiyai tafada idan yazo yasameni Ina fira, aciki samarin Nawa yafijin haushi Abubakar Saboda yaga nafi kula shi,


**************

Akwai wata rana yazo sai ya iskemu muna fira, sai yace nashiga gida bace komai ba Na nufi cikin gida nabar su' nan tsaye shida "Abubakar,


"lna daga daki naji yace wa Hajiya wai tadaina barina "Ina fita yin firada samari  barkatai harda mawan "Abubakar din wallahi Hajiya ni haushi sa nakeji, Hajiya tace "ah samari kam "ai dole takulasu' tunda ba'ajiye ta zamuyi "agida muna kallon taba dole gidan wani zata,


 "aima tunda naga tafi kula shi Abubakar din zan fadawa gen yace masa ya turo iyayansa, da karfi naji yace haba Hajiya "ai gida bai koshi ba baza'akai waje bako"?  (sai tayi kamar bata fahimci abinda yake nufi ba) 


Sai tace kamar ya gida bai KO shiba? sai yace Hajiya wallahi nadade nima "lna San "A'isha don Allah ki yardan mun Na aureta, tace "a ah nibazan yardan maka ba har sai tace tana sanka, Saboda haka sai kaje kanemi so dayar danta.


Niko "lnajin haka saida gabana yafadi "araina ko" fadi nake ni A'isha Hamman Soja keso? "Ina cikin wannan zancen zucin sai naga Hamman Soja yashigo dakina,

"aiko sai naji gabana Ya cigaba Da faduwa,


Zama yayi kusada ni kadan yace A'isha nasan kinji maganar da mukai da Hajiya KO"? Nace "eh yace toh" meki kace? shuru nai bance komai ba, yace A'isha wallahi "Ina sanki Kuma "Ina san Na aure ki, kema kina sona? 


nai shuru domin jinai kunya duk tarufe ni, yasake cewa don haka A'isha kina so na Zaki aureni,? Kai nadaga alamar "eh  ko" da bana san Hamman Soja, bazan iya cewa "a ah ba balle "Ina San sa, kodan halaccin dasukai mana a rayuwa,

 

 "ako gaba daya zuriyan "Alh Ahmed Dan kwangila sunyi murna da jin haka, idan kadauki mutun biyu wato goggo "Rakiya DA yarta "Aina'u,

Oho! Ba wanda kula

 lamarin su, don haka Cikin lokaci  kankani  "Baba engr yasa ranan auren wata biyu,


Wanda tundaga ranan nafara fuskantar kalubale a rayuwa ta daga gurin "goggo Rakiya DA "Aina'u 


haka naci gabada fuskarta  abubuwa kala-kal daga gurinsu" Wanda sai sun tabbatar da Hajiya bata nan sannan sai suzo suyi Mani zagi ta Uwa ta Uba,


tsoron su" yashige ni sosai da Kuma gargadin su", dauke cewa duk ranan dana kuskura nafadawa "Hajiya sai sunyi Mani dukan tsiya don haka bantaba tunani fada mata ba,


Ana saura sati biyu auren, a wannan lokacin Kuma tuni Mado "aikai shi karatu can kasar waje, wai bazaya dawoba sai yagama karatun sa duka, 


Don sai nakasan ce' ni kadai "a gida "Ina zaune a falo "Ina kallo, kasan cewar aranan "Hajiya  taje unguwa, sai kawai naji saukar duka "abaya na,

tareda cewa yauwa gashegiyar nan'


Zumbur namike goggo Rakiya nagani "itada Aina'u, jinayi gabana yafadi yayinda suka Hauni da zagi da dunguri,


Cin mutunci su" kayi mani nakarshe Kuma suka ce Mani muddun nayarda Na AURI "SOJA sai sun kasheni fuuu....

Suka fice daga falon...



Tab turkashi babban magana,







💞Lufhat CE💐

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page116-120


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)



*😭KULLU'NAFSI'ZA'EKATUL'MAUT*😭

*DUKKAN RAI* saita dandani *DACIN* *MUTUWA*

Wannan page din NASA daukar dashi ga yayata *HAJIYA LARAI GODABE  wadda tarigamu gidan *GASKIYA* Ina rokon *ALLAH* yaji kanta da *RAHAMA* yasa Aljanan'nar *FIDDAUSI* makomar ta tarada yan' uwa *MUSLIMAN* baki daya Amin, 😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭

*WE MISS YOU MORE AUNTY LARAI* Allah yajikan kida *RAHAMAR SA* 

    

*DAN ALLAH KUYI MATA ADDU'A*

Please Don  Allah Ina rokon  Duk Wanda 

Karanta wannan page din nan yaima *AUNTY NA HAJIYA LARAI GODABE ADDU'A*

----------------------------------------

®PEN WRITERS ASSOCIATION


PEN:THE STRONGEST WEAPON

----------------------------------------


only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.



✍🏾


"Meh ?  "eh Nace  masa  duk dacewa ban fahimci "abinda yake nufi da hakan ba, amma dai tunani na yabani cewa farin ciki ne yasa shi yace haka, don haka sai nima naji farin cikin yaka Mani, duk dacewa "Ina danjin faduwar gaba kadan, Saidai Kash! "Ashe bansa niba farin cikin nai  shine zaizama mani bakin ciki mara musaltuwa arayuwata zuwa gaba bansa niba...


Domin kuwa wani irin harara yai Mani Wanda yasa, naji gabata ya cigaba da matsananci bugawan dayake yi, yace toh"  wannan takardan kam ba naki bane, 

Na zaro idanu Ciki tsoro tareda cewa  eye! ? da sauri nakarbi takardan "a hannun sa nace' nawane mana ga sunana nan "an'rubuta A'isha Ahmed,


Yace' "eh sunanki nagani A'isha Ahmed, saidai Wanda ya baki takardan baisan "aikinsa bako...? Cikin matsananci kosawa dajin zancen Hamman Soja, wayan  dasuke kokari tarwatsa Mani kwakwalwa,

Nace masa "Hajiya ce fa ta tadu bani' Kuma itane tayi rubuta Kuma ma "aikasan "aikin tane tadade tanayi ballan tana "ace bata iyab.... 


Da daga murya yakatseni dacewa ke! rufe Mani baki, "aikam da sauri nayi shuru, yace kinsan abinda takardan ta kunsa kuwa? DA saurin Nace "eh Ciki "akace "ina dauke dashi, yace "eh hakane wato ke' din kina dauke da cikin kenan KO? Nace masa "eh "ai wannan watan daya kare banga "al'adata ba Kuma kasan farkon wata nake gani, gashi wannan harya kwanan sa" hudu amma ban gani ba, kaga kenan "Ina' dauke dashi KO?  Wani wawan tsawa Hamman Soja yadoka Mani, tareda cewa Ke! banasan maganar banza DA wofi kinji KO"


"An fada maki Ciki "abun  wasa ne da kike kokarin kiyi wasa dashi? Kodaya ke' naga "alama Nema kikeyi kiyi Mani wasa da hankali, "inba haka ba "a "Ina kike da Ciki eye? yakarasa fada Cikin daga murya, Cikin matsananci tsoro Nace  wallahi "Ina dashi nafada tareda kallon sa' gabana ne ya cigaba DA matsananci bugawa  lokacin danaga idanun shi sun can a Kala daga fari zuwa JA,


Sainaga yafito  mani SOJA SAK Don haka sai naji tsoro yasake kamani, sai ya girgiza Kai tareda watsa Mani JAJAYEN idanu sa masu bani TSORO, yace lallai A'isha baki Cikin  hankalin ki dan'naga alama bakisan "abinda kike fadaba, kodai CIWON KI' yatashi ne? nace wallahi "Ina Cikin hankali Na Kuma bawani ciwon danakeji ajikina "idan ba zazzabin Cikin nan ba, kaduba kagani da gaskene Hamman Soja wallahi "Ina DA ciki,


Dakarfi yace "indai harda gaske ne "kina' da Ciki toh" tabbas dashi kika zo, amma kam ba'agidan nan kika same shiba, Domin kuwa ni' bana haihuwa Dan haka taya za'ai kisamu Ciki tareda ni'?

Jinai gabana yayi mummunan faduwa harsaida naji "antar Ciki Na yakada dajin kalaman Hamman Soja, bangama fita  daga cikin wannan tashin hankali ba,  Hamman Soja yasake sakani "cikin wani,


Domin kuwa cewa yayi' barina kawo maki takardan dasuke nuna cewa' nidin bazan taba haihuwa ba, Saboda nasamu matsala tun lokacin Da nayi hatsari, da sauri yanufi dakin shi,


Can  sai gashi yafito hannun sa' rikeda takardu, yana zuwa girina sai watsa matani takardan "ajikin tareda cewa gashi nan Kiduba kigani DA kyau saida naga likitoci har mutun uku  Kuma sun tabbatar Mani da cewa bazan taba Haihuwa ba Saboda kwayoyin Na sun mutu,


Toh" tayaya zakice Mani wai kinada ciki, yanada kyau kije kinemi Wanda yakeda Cikin nan, amma bani ba ransa "abace yafita,

"Ahankali nabi  bayan sa DA kallo har yashiga Cikin daki, sannan  nadawo da kallo Na kan takardan tareda  dauka "Ina dubawa,


Tabbas rubutun "irin guda ne,  wato hakan yana nufi da gaske Hamman Soja bazaya taba haihuwa ba...? Idanu na rinte fatana wannan abun yazama mafarki, rokona kuma shine ALLAH yatasheni daga wannan nauyayyan baccin mai dauke da mummunan mafarki, Saidai ba mafarki nakeyi ba domin kuwa "Ina bude idanu Na takardun magani, "Ahankali nasa hannuna nakwashe su' sai kallon su nake daya bayan daya, naima takardun kallon da ni kaina bansan "iya "adadin sa ba,


Yayin da gabana yaci gabada faduwa  zuciyata kuwa wani irin matsnanci harbawa takeyi, "araina Kuma fadin nake Na shiga uku ni A'isha mene yake shirin faruwa Dani...? "Ahankali Na mike Hannun na dauke da takardun JIKINA "asanyaye,  Na nufi dakin Hamman Soja domin Na Kai masa,  saidai ga Bamako na ko" da na'isa kofar dakin kod nasa hannun natura kofar sai najita GAM,


Kirjina najiya Kuma bugawa yayinda kaina yasara  "Ahankali naja nafara zuwa bakin table dakin dayake tsakiyar falon, Na'aje mashi takardu domin nasan idan yafito zaya ganinsu,

Na nufi dakina ba tareda "Ina ganin hanya ba domin kuwa wani irin duhu nake gani, rabona dashiga tashi hankali irin haka tun lokacin da, yan'fashi sukai sanadin rabamu da iyayen mu'


"Ahankali Na kwanta "agado yayinda wani  matsananci zazzabi yarufe ni, da kyar nasha magani Na koma na kwanta,yadda naga rana haka naga dare domin kuwa ko" bacci ya kaura cewa iduna,


*******************

Washegari tunda nai sallah "asubu nashiga kicin Nawa Hamman Soja abun Karin kumallo, kamar yadda nasa ba duk ranan danake da girki, saidai wani abun mamaki shine koda naje dakin sa Don nagaida shin "in, Kuma fada masa ga Karin kumallo shi" saina "iske har yafita, JIKINA "asanyaye najuya DA nufin nakoma dakina, tsaye nayi turus saka makon ganin Adda Aina'u tsaye abakin kofar dakina,


Tana doka mani wani irin murmushi Wanda narasa gane kona mene?... , cikin faduwan gaba Nace mata "Ina kwana? tace lafiya lau mai CIKI, sai Kuma ta fasheda dariya Wanda kana jin sa kasan ta mugun ta ce', 


Saida tayi mai "isarta sannan tsaya tace su"ciki manya ke' yanzu kina nufin ciki gareki?..., tab lallai taya ki ke tunani samun ciki da mutumin da bazaya taba haihuwa ba?..., toh" bari kiji "nafada maki muddun kika yarda kika  haihu  "agidan nan toh" KO" DA SANNU...Zaki gane kin tabka babban kuskuren "arayuwan ki', domin kuwa kisani cewa duk "Abinda kika Haifa "agidan nan toh" KO" dashi da shege basuda bambanci,


Saboda "Hamman Magaji bazaya taba daukar miki shege ko" shegiya ba "ehee, don haka gwanda kisan yadda Zaki yi DA wannan cikin , ta harareni sama da kasa ta watsar sannan taja tsaki mtsww...., tareda tureni tawuce.


 Da" sauri nadafa bango badan  haka ba dana fadi, gaba daya maganganun ta" sun Kuma birkita Mani kwakwalwa,

yayin da gabana ya cigaba da faduwa DA kyar Na "iyajan kafa zuwa daki,


Koda nashiga dak... kukane yakwa cewa Mama' mai tsuma zuciyan mai sauraro gaba daya dakin sunyi tsit suna sauraran Mama' tareda tausayi ta     Y Y k shima kukan  yake na tausayin ta,' saida tayi kuka sosai sannan taci gabada Shafa kam Abdul-jabbar Wanda shima kukan yakeyi, Na tausayi mahaifiyar sa,


taci gabada da cewa" kuka nayi sosai dana shiga daki, Na tausayin kaina da " abida Zan Haifa, tun baizo duniya ba "anfara shegan tasa?... nikam nasan shi ba shege bane tabbas "Hamman Soja shine UBAN shi  tunda ni' dai bantaba tarayya dawani DA namiji "idan ba Hamman Soja ba, 


 Shikenan Kuma tundaga wannan lokaci, nake fuskarta matsaloli Kala Kala banayin bacci kullum da  zazzabin nake kwana, dashi nake tashi gashi bana "iyacin "abinci sosai saboda laulayin ciki, kullum "ina cikin daki duk narame nayi baki "Hamman Soja kuwa dama tuni yadaina kulani, bana ganisa Kuma bana sanin lokacin fitarsa" haka kum banasanin dawowar sa" 


"Wani abin mamaki Kuma shine ban taba fadawa kowa halin danake ciki ba, "idan "Hajiya takirani ta tambaye ni' yanake "ina shan magani kuwa?... saidai nace mata "eh kawai, "a haka  har Ciki Na yakai wata biyar "a lokacin Kuma rabona  da Hamman Soja harna manta rana, 


Ran wata Lahadi da bazan taba manta da ita ba "arayuwa ta, nafito daki kenan sainaji telephone nakara saina dauka, gabana ne yafadi saka makon jin murya Hamman Soja,


"A hanka Nace "Ina yini bai amsa cikin fada yace A'isha wai zaman meki keyi "agidana har yanzu  dauke DA wanna cikin Daba Nawa ba?...

 toh" Bari kinji nafada miki karki kuskura nadawo nasa meki gidan nan  kina dauke DA wannan cikin, Saboda haka duk yadda zakiyi da shi kiyi dashi kinji  nagaya miki, Domin ni bazan dauki abinda bana waba zanyi magana kenan sainaji ta katse,


Don haka sai namayar Da telephone din na'jiye, yayin da"idanu Na sai tsiyayar hawaye suke jiki "asanyaye Na nufi daki,kayan jikina nacire nasa wasu tareda daukan wasu kudi  da wasu yan kayana guda biyu, sannan nafito, yahuza drive nagani zaune yana ganina sai yataso,


Bayan mun gaisa saiya tambaye ni' ta "Inazaya  kaini'?.... saina ce' masa " "asibiti zaya Kaine, yace toh" kodaya kaini "asibiti sai yace zaya jirani nagama ne?.. sai Nace "a ah yatafi  sai "anjima yadawo ya daukeni yace toh", "Ina gani yawuce, sai kawai nafita daga 

"asibi ,


domin banajin Zan' iya  fadawa "Hajiya komai toh" mizan ce mata?... Saboda haka "koda na fita asibitin motar haya Na hau sai nace yakai ni'  tasha, yace toh" sai kallon gari nake tunda bana fita koda muka "isa nabi yashi kudinshi sai naji "Ana fadin Kaduna mutun daya, basan kaduna ban taba zuwa ba, amma kawai sai nashiga  mota nan da "akace  kuduna ba'dauki wani lokaci ba motar ta tashi zuwa Kaduna.



"tafiya sosai mukayi tunda sai daddare muka "isa, Kaduna fasinja suna tafita amma ni' "Ina zaune ban fita ba saboda nayi nisa "a tunani sai jinai mai mota yace?....






💞Lufhat Ce💐

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page121-125


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)



*WANNAN page*

*GARGADI NE GA MASU SATAR FAHIMTAR WASU SU MAYAR TA SU*

*Hmmm Abun DA  mamaki gaskiya  NI BAN TABA tunani SATAR FAHIMTAR KOWA Ba hmmm dazan fada maka/ maki TUNLOKACI DANA KE RUBUTA WANNAN LITTAFI SAI KAYI MAMAKI saboda haka WALAHI duk wacce KO Wanda  I mean MACE' KO NAMIJI" ta Ya JUYA Mani LITTAFI NA azuwan SHIYA RUBUTA TO BANYA FEBA! BANYA FEBA!! BANYA FEBA!!!*


----------------------------------------

*®PEN WRITERS ASSOCIATION*


*PEN:THE STRONGEST WEAPON*

----------------------------------------


only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.



✍🏾



"Haba Baiwar ALLAH wannan wani irin "abune haka tun dazu muka "iso mutane duk sun fita  "amma ke' baki fito ba  KO" bakisan dare yayi bane? 

"Ahankali Nace kayi hakuri sannan  nafito, gefe nakoma Na  tsaya sainaji tsoro yaka mani ' Saboda ganin  tashar  ba buwasu  mutane sosai, sai kadan kadan, shikam drive tuni yaja motar sa" yatafi,


"Ahankali nakoma jikin wata runfa nazauna tsawon wani lokaci, sainaga mutanan sunata tafiya " saida Na tabbatar mutane sungama tafiya, dare yayi sosai, saina shinfida zani Na, na kwanta duk Dana sai dacewa ba baccin zanyi ba, saboda dama nasaba sai kusan sallah "asuba bacci mai nauyi yake dauka ta,


  "A hankali nabude "idanu na saka makon Jinda nai "ana  bubbu gamani kafa, tareda cewa ke! baiwar Allah lafiya ki kazo nan Ciki tasha kika kwanta,?...


 "A hankali na juyawa dan'naga mai magana, wata dattijiyar mata nagani tareda mutane ne dayawa suna kallon Na, Da sauri natashi nazauna matar ne tace baiwar Allah lafiya meya same ki'?....


Kuka kawai nafashe dashi batare da nace" mata komai ba, da sauri tace'  "subhanallahi! mai yafaru taso! taso!! takama hannuna muka shiga shagon dake cikin wanna runfar,


Babu wani tarkace  "acikin shagon daga bancina nazama ne sai table "inda "ake dora abinci, "abanci ta zaunar Dani  sannan "itama ta zauna, sannan tace yishuru kinji ya'ta share hawayen ki fada Mani meya faru dake?


"Ahankali nafada mata "abinda yafaru ban boye komai ba, tayi shuru Na Dan wani lokaci tana nazari, can tace tabbas "ayanda nafa himci labarin ki'  lallai akwai sihiri "aciki tareda sharrin kishiya, sannan mijin ki baiyi kwakkwar bincike "akan cikin  kiba,


Saidai karki damu "DA SANNU"  Allah zai bayyanar da gaskiya, saboda haka yanzu "abida nakeso dake shine kikwan tarda hankali ki' kinga ba'asan mai juna biyu" tana yawan tunani dasa damuwa "aranta tashi muge nakai ki' gidana kiyi wanka ciki Abinci kinji ko?

Nace toh" tareda mikewa muka fito,


Bayan mun fitone sai naji tana kiran maryam, saiga  wata  yarinya yar kimani shekara goma , tafito daga dayan shagon dayake kusa Da "inda mukafi to, hannun ta rige da tsintiya da "alama shara zatayi,

tace gani' matar tace yauwa kikula sosai bari nakai wannan gida yanzu zan dawo, Maryam tace toh" 


taxi muka shiga tace masa' sabangari zaya kaimu, yace toh' "adai-dai wani Dan matsakaicin gida aka saukemu bayan tafiya shi" kudi, sai muka shiga gidan yana dauke da dakuna uku,da kuma kicin da bayi tsakar gidan yana da fadi kadan, ga wasu manya-manyan tukwane Dana hango "acikin kicin din,


Daya daga cikin dakin muka shiga yana dauke da, gado biyu da Kuma tarkacen kaya tace bari Na kai miki ruwa kiyi wanka, Nace toh"


Bayan nayi wakan da ruwan zafi, tunda "a lokacin (hunturu ne) wato sanyi takawo Mani abinci, naci, sai take fada Mani sunan ta Hajiya Hafsatu amma Hajiya Magajiya ake kiranta', sannan   gidan nan nata ne' "itada yarta, da mijinta  yarasu aka raba gado aka bata sai tasiya, tana Kuma yin abinci takaiwa tasha, bayan tagama fada Mani sai tace toh" nahau gado Na kwanta nahuta "ita zata koma Tasha gurin sana'arta Nace sai tadawo ALLAH ya bada sa'a tace' Ameen tareda fita,


Haka naci gabada zama agidan Hajiya Magajiya, cikin kwanciyar hankali tana kula Dani sosai  bata barina nayi "aikin wahala, saidai Dan motsa jiki kawai, ranan wata litini natashi Dana kuda Hajiya takira mai taxi yakaimu "asibiti,


 Ciki "ikon Allah Na haifeka lafiya bayan "angama komai, "aka salla memu muka dawo gida, nikam ba "abida zancewa Hajiya saidai nace Allah yajikan ta', da rahama yasa Aljannar Fiddausi ce mako marta, domin tayi mani abubuwa dayawa arayuwa, bayan kwana biyu saita tambaye ni"wani suna nakeso asakama?,nafada mata akai maka huduba dashi, komai "ita ce tai mani kayan sawata DA naka da ragon suna duk itace' tayi da sati yaza gayo "akai suna,


Bayan suna saita cigaba da kula mu ni' dakai, da dafarko Da "Madona kake kama "amma daga baya saika rikida ka koma "Hamman Soja, kamar yanda"akace jarirai rikida suke" toh" haka yake,


 domin kuwa rikida ka keyi naban mamaki, kullum kaman'nika sake fitowa yake Dana "Hamman Soja komai naka irin Na shine', hattada kunban kafarka irin nashi ne, hankali ya kwanta ganin yadda kayi Kama Da "Hamman Soja Wanda KO makaho yalalibeka yasan kaidin DAN SANE", "ahaka dai Na cigaba da goyonka harna yayeka,


 lokacin da ka shekara hudu Hajiya tasaka "a makaranta islamiyya data boko "awanna lokacim Kuma tadade tanayi Mani maganar komawa gida, "amma saina ce' mata "a ah, bazani kowa ba wani lokaci idan tayi maganar komawa gida saina farayi kuka, dan'haka sai ta kyaleni tunda taga bana so",


 ************

Ranan Wata  jumma'a daga makaranta aka kawo ka', baka da lafiya hankali mu yatashi sosai muka tafi "asibiti, bayan  Likita yaduba ka' yace kana fama da ciwon zuciya, dan haka sai "aguji bata maka rai,nikam mamaki nayi tareda tambayar kaine cewa dama yara suna ciwon zuciya,?


"Ahaka dai mukai jinyarka' har kaji sauki, saidai Kuma tun bayan Da kaji saukin sai Na kula dawani bakon "al'amari daga gareka, shine sai ka zauna kayi shuru "abin Nada muna'

Duk da cewa dama Kai din bamai yawan magana bane,


 "Amma Kuma wannan din yayi yawa sosai, ran saina tambaye ka mai kakeso sai kace Mani bakomai, can Kuma sai kace Mani Mama "ina BABA NA? gabana yafadi tareda jin wani irin tashin hankali, "amma  Kuma sai ban bari kagane ba,


 murmushi nayi Nace babanka bayanan, sai bakace komai toh" shikenan kuma

tundaga wannan lokacin sai ka cigaba da tambaya ta, "amsar daya ce nake baka shi BABAN Ka bayanan, ran sai kace yaushe baban ka zaya dawo? shuru Nai "Ina tunani "abida zanba ka? saboda karka cigaba da tambaya ta, sai Nace maka ba "Ai BABAN Ka yace bazaya dawowa ba,


toh" fa shikenan sai kadaina tambaya Na, duk da cewa bakasan BABAN ka ba Amma Ina ganin SON shi akwayar idanu ka, 


Kanada shekara bakwa, ALLAH yaima Hajiya rasuwa,  saka makon rashin lafiyar kwana biyu, nayi kuka sosai bayan tayi kwana arba'in,  hankali Na yatashi lokacin da yan' uwanta "sukazo, Dan asiyar Da gidan, su" Kuma tafida "Maryam za'ai mata aure can garinsu sokoto,


Haka kuwa akai bayan ansiyar dagida, sai suka tafi da maryam, amma kafin su tafi saida Maryam takama mini gidan haya tabiya kudi, sannan Kuma tabani wasu kudin tace' narike,


A haka Na cigaba Da kula da Kai' gashi Allah yasa maka san karatu "aranka',  Dan haka nasha wahala sosai gurin Neman kudin Da zakai karatu, ba abinda banyi ba nasiyar wa kosai, waina, wankau, aikatau, harda surfe da daka duk nayi, kai komai nasamu yinake, don kawai naga na'inganta rayuwar ka, nafara samun saukine lokacin da karfinka yakawo, sai kafar dako da Na baro, Wanda nasan duk baka manta da hakan ba,


 Har lokacin DA ALLAH ya hadamu DA Alh ya'u Na Kaka, yatallafi rayuwan mu" wannan shine abinda yafaru arayuwa ta da Kuma Kai, takarashe maganar tareda share hawaye.


"Tabbas Abdul-jabbar bai manta wahalar dasu kasha ba shida Mama, Ahankali Abdul-jabbar yakejin wani irin tausayi Mama na ratsashi, tareda Sonta da Kaunar ta yana ratsa jini da bargon shi, yayinda yakejin wani iri.  haushi babansa" musamman daya kasance mutun Mara BINCIKE, "acikin lamari sa domin inda yayi bincike tabbas da Mama bata shiga wani haliba,  "ahankali ya dagoda kansa, ya kalli Mama  fuskarsa shabe-shabe Da hawaye, hannun yasa yana share mata hawayen fuskarta tareda cewa, kiyi hakuri Mama na kidaina Kuka tabbas "anzalin ceki tareda yimaki mummunan fahimta, saidai kisani DA SANNU gaskiya zatayi halinta, kinji KO?

tace haka ne musamman ma "akan mahaifiyaka" Wanda "Naji LABARIN cewa yanzu shine Governor Adamaw! da sauri yace " a ah! a ah!! a ah!!! Mama basonjin koshi" wanene yanzu, tunda yace niba Dansa bane toh" shikenan, nima shi" ba babana bane' kece MAMA Na Kuma kece BABA na, dakarfi yake fadar maganar Wanda kanaji kasan baya cikin hayyacinsa, yace

 saboda haka abinda nakeso shine   kidaina kuka, saboda bana san ganin hawayenki kinji, sannan "ina Son duk Wanda ya kyautata maki a rayuwa, saidai kam Na tsani Wanda duk ya cuta maki,  Mama ina Sonki! "Ina Sonki!! Ina Sonki!!! Mama Na!!!!!!! 


A hankali jikinsa yasaki,  saka makon alluran bacci da Doctor  I s g yai masa, aikam cikin lokaci kankani  nauyayyan bacci ya dauke sa, da sauri  Y Y k yazo yadaga kasan daga kafar Mama, yayin da  Doctor yai sauri jawo filo suka dorasa tareda gyaramasa kwanciyar,


Alh ya'u nakaka ya suke nauyayyan ajiyar zuciya, yace kiyi hakuri Hajiya A'isha kisani kowani bawa DA irin jarabawar da Allah keyi masa, Amma idan yayi Hakuri toh" "DA SANNU" zayaga kyakkyawa saka mako, yamaida dubansa ga Doctor yace Doctor Ina fata babu  wani sauran matsala tareda Abdul-jabbar din KO?.... yace eh Alh bakomai darazan yasamu isassaa bacci toh insha Allahu sai tashi normal,  saidai game DA ciwon zuciyansa sai andinga yin taka tsantsan da gudun bacin ransa, Alh yace toh " shikenan ALLAH yabashi lafiya gada suka "amsa DA Ameen, yace nadabo kamaida Hajiya A'isha gida yace to, "alokaci guda suka fita daga dakin gaba dayansu.


**************

Abdul-jabbar yaji sauki sosai,jikinsa yamarje yakara wani irin kyau idan kagashi baka taba cewa shine yai wannan rashin lafiya, sai wani Kuma shine tun bayanda "Mama tabashi labarin ta,


Shikenan Kuma sai yake jin haushi mutane Abinda bayayi da toh" shiyakeyi yanzu wato fada, abu kadan sai yafara, yayinda yake ba Mama kulawa ta musamman fiye da tunani mai karatu, data motsa sai yace Mama mekike son, hakan itama tace kula dashi sosai musamman dataji abida likita yafada dan haka batasan "abida zaya bata masa rai,


Ranan wata laraba Abdul-jabbar yafito zayaje gida su Y Y K dakuma yawan da yasaba Na Neman Humaira *nikam Nace  tabdi Humeeh kam tana yola*

yana sanye da t shat baka da wandon jims fari kalkal, hannun sa rike Da key" mota tareda wayar sa,' sai kamshi yake zubawa cikin  nutsuwa yake tafiya  har ya isa bakin mota, zaya bude motar kenan sai yaji wayarsa Na Kara koda yaduba saiyaga sunan Dalter boy, yana dauka sainaji DA karfi yace?.....




💐Lufha Ce💞

💐💐💞💞💞 💞💞💞💐💐 

    DA SANNU

💐💐💐💞💞            💞💞💞💐💐


  page126-130


             NA


💞AMEENAT 💐UMAR 💐FARUQ

       (MEENAT)


------------------------------

-------     


*®PEN WRITERS ASSOCIATION*


*PEN:THE STRONGEST WEAPON*

--------------------------------------


*only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers*



✍🏽



"Meh kace? sai kuma yacire wayar da sauri  daga kunsan shi', sannan yakara volume din wayar, don yaji maganar da kyau, yace banji da kyau ba fa meh kace? Delter boy yace Dan "iska nasan kaji, kanaso ne nasake maimai tawa, toh" nace ne" "anyi posting din mu yola nan da two months zamu tafi,


Cikin karaji Abdul-jabbar yalallayo wani Uban ashar yakwada wa Delter boy,  tareda cewa Kai! Uban wanene yai posting dina Wannan garin?  Delter boy yace a ah to menene "aiba Shame bane, Dan "anyi posting dinmu Adamawa inace garin kune? 


Cikin masifa Abdul-jabbar yace toh" nibana San wannan gari kaji KO"? Cikin mamaki Delter boy yece toh" ikon Allah tunda nake bantaba jin Wanda yake gudun garinsa ba saikai' 


yace "eh naji Dalla malam kafada mun Uban wanene yace ayi posting dina wannan garin? cikin jin haushi Delter boy yace Ubana ne, Dan iska tunda idan zasuyi posting din suna tambayan Mutum ne, Kuma wlh saikaje yola nan saboda haka kazauna cikin shiri nan Da wata biyu zamu tafi , yana kainan yakashe wayarsa kit!!!


Abdul-jabbar kam ranshi yabaci fadi yakeyi Don me za'ai posting dinsa wannan garin daya tsana,awani gefen Kuma yafijin  haushi Delter boy *nikam nace Toh" aibashi yace ai posting dinka can ba*


Cikin bacin rai Abdul-jabbar yajuya yakoma cikin gida, don "ayanda yakejin bacin rai bazaya "iya driving ba,

Mama kam gaban tane yafadi saka makon gani shi datayi a hargitse,  saboda yanzu batason abinda zaya bata masa rai, shiyasa ma take taka tsantsan DA abinda "Doctor yace',

 don bata son tarasa Dan tilon DANTA


Da sauri tace meya faru? cikin bacin rai yace mama wai "arasa inda za'ai posting Dina sai YOLA? "Ajiyar zuciya tayi "aranta tace Masha'allah Anzo gurin, lokacin Dana kejira yazo kenan?

Kallon sa tayi tareda cewa zonan,

"Ahankali yazo kusa Da "ita yazauna tareda kwantar Da kansa saman cinyar ta,domin yanzu ya sangarce dayin haka, yayin "ita Kuma saita Dora hannun ta saman kanshi, tana shafa lallausan sumanshi irin na fulanin asali,


tace kwantar DA hankalin ka, aiko" bakaje Adamawa Dan kowa ba kaje Dan Dan'uwana, KO" kamanta dashi' ne?, yace "a ah tace Saboda haka kadaina bata ranka kafa Doctor yace ba'asan kana bata ranka, Saboda bacin ranka tashin ciwon kan Kuma kaga ciwon ka,' ciwone mai hatsari tashin sa komai Na iya faruwa, 


Wanda tasanadin haka "Ana "iyarasa ran Mutum KO" kana san' narasa kane?, da sauri yace a ah tace toh" kadai bata ranka kaji KO"? yace toh" saboda haka kar kadamu kataje kayi "aikinka, kawai kaji ko"?


 yace toh" Mama "amma dai gaskiya "idan naje "iyakata barikin daza'a "ajiyemu (nasojoji) kawai, tace "ah baza katafi gurin "Mado na ba? shi kadai nefa dan'uwana, "a duniya,


 yace toh" gurin sa"kawai zanje ni' baruwana dakowa, tunda basa sanki' toh nima banasan su" ,yakara she maganar Cikin jin haushi, tace "ah suna sona mana "Hajiya tana sona' "Baba genr Da "Baba engr Da su Adda "Uwa duk suna" sona',


 yanajin tana tafadan sunayen mutane "amma baiji tafadi sunan "Baban sa da na wannan "Adda Aina'u ba, wato haka yana nufin sune mutanan dasuka fi kuntata mata arayuwa kenan ko?, Mtsww yaja tsaki, "ahankali shiyasa yake jin haushi su" duk dacewa yanajin kaunar "Baban shi acikin zuciyarsa, Amma hakan bai hanashi jin'hau shin abinda ya "aika tawa Mama shin ba,  "Ahankali ya mike tareda cewa Mama Bari natafi gidan Y Y k,  tace toh" yaushe ne tafiyar naku"?  

yace nan da wata biyu ne tace toh " ALLAH yakai mu Lafiya, yace Amin tareda fita

    

*******************

            YOLA

Wani katafare gida Na hango awata hadadde yar unguwa me suna KAREWA GRA ginin gidan upstear ne anyi mashi paint ashes and White colour,


"Tana kwance awani tanfareren gado tana sanye da wani sleeping gown milk colour ce, Rigar tanada dan sirin hannun batada tsawon sosai domin KO iyakarta kwauri, Humaira kenan mutanan YOLA.


 A hankali tafurta sorry "yah Himu I can't forget "Him bcos l Love "him so much  "where are you my special?....,

Chan kuma saita fashe da kuka me ban tausayi, sai kuma tafara surutai barkatai tankar zararriya, "acikin surutu natane take cewa "yah Himu yace waikai mayaudari ne? Ni' Kuma zuciya ta taki yarda dacewa "kaidin mayaudari, ne Amma kuma meyasa kai Mani haka? Why are you doing this to me  (meyasa!!)why!! (meyasa!!)why!!! "Abdul-jabbarrrrrrr?


Haka tacigaba da kuka dakuma surutai har tsawon wani lokaci, saida tayi mai'sarta tukun sannan ta mike Ahankali tanufi (toilet) bayi,


Ko" a toilet dinma tana wanka tana kuka kadan kadan, "ahaka harta gama tadauro towel tafito, agaban mirror ta tsaya tana kallon kanta saida taka rema kanta kallo tukun, sannan tafara Shafa mai kamar bataso harda tagama, tabude wedrof tadauko Riga da siket na'atamfa tanada ratsi ja da fari ajinta, bayan tasane sai tayafa Dan karami mayafi fari, sannan tasa wani flat shoe  fari sannan tanufi waje "A hankali take taka steps din tamkar bataso.

  

Ta "kuntane yasa Umma datake falo tana kallo T.v tadaga Kai ta kalleta,  


Sannan tadubi agogon dake manne "afalon yanuna 1:00pm, sannan tamaida dubanta kan Humeeh data zauna kusada ita, fiska ba walwala tace Umma Ina kwana?


Umma tace dayake yanzu kika tashi kam dole kice Ina kwana, kalli "agogo yanzu kafe Nawa?


"A hankali ta kalla tareda dukar dakai kasa sannan tace karfe daya Na Rana,


Umma tace ace" tunda kikai sallar asuba sai yanzu kike fitowa haba "Humaira, nalura dake duk kwana kin nan haka kike, wai me ke damunki ne?


Me makon taba "Umma Amsar tambayar  datai mata sai kawai tafashe da kuka,


Umma kam baki tasaki tana kallon ta Cikin matsanancin mamaki tace a ah lafia?


Cikin kuka tace "Umma nima bansan "abunda keda munaba saidai banajin dadi araina,


Umma tai murmushi tace shikenan kuma Dan bakijin dadi aranki saiki zauna kina kuka?...Haba autata, matso kiji,


 "A hankali Humeeh tamatsa tareda kwantar da kanta akafadar "Umma,

Umma tasa hannu tana Shafa bayanta tace'  idan Mutum yatsici kamshi Cikin wani yanayi dabai sabajiba toh" addu'a yakama tayayi ba kuka ba habah,sai kace ba matar "Malam?... ba tafadi tana murmushi.


 itama Humeeh murmushi, tayi tareda turo baki tace toh" Umma "ai "inayi, tace yauwa toh kikara "DA SANNU" komai zaiyi dai dai ne kinjiko? tace  Toh" Umma Ina "Abba Na?..., tace Abbanki kam tundazu yafita tunda yayi zaman jiranki baki fitoba, baki ta turo kadan tace toh" Umma shine baki tadani ba?.... baki Umma ta tabe tareda cewa taya Zan tadake" bayan 'kinsan "Abbanki yace "adaina tadake idan kina bacci, abari harsai kin tashi dakanki " Saboda  ciwon Kain nan naki nafama, murmushi tayi tareda cewa toh Umma yaushe yace zai dawo?,,,, tace "a ah ni bai fada Mani ba, yanzu dai kitashi kaje kicin kidebo abinci Ciki. toh" tace tareda mikewa tanufi kicin.


***********

*DA MISALIN KARFE 12:30PM*

Yana zaune akatafarin office  dinsa" gaba daya attention (hankali) dinsa, yanaga wani babban photo dayake manne ajikin bango, wato irin window size din nan duba guda zakai wa photo kane cewa bana yanzu bane, irin photo nan ne nada  wato fari da baki, photo akalla zaikai kimani shekara ashirin da takwas zuwa talatin, macece ajikin photo tana sanye da kayan Fulani hannun reke da kwarya tana dariya,


"Ahankali aka turo kofar office din aka shiga tareda sallama, duba guda zakaiwa mai sallama kagane cewa shi security guard ne (maigadi) "aciki ya "amsa sallamar ba tareda yajuya ba, yace Jabeer sonawa zanfada maka cewa bana San damuwa?....

idan wani Abune aje gurin Dept mana KO" dole saini?


Ahankali Wanda akakira da Jabeer ya russuna tareda cewa, Allah ya huci zuciyar  excellecy" bawani Abu bane, damai wani  Mutum ne yake son ganin 

ka, toh kuma "ace masa yatafi sai anjima yadawo yace "a ah shi yanzu yake san ganin ka,


Cikin daga murya yace wanene shi?...., Jabeer yace "eh toh ranka yadake bansan shi ba,

Saidai yace "ace Alh Mahmoud wai idan baka gane ba "ace maka MADO n! da 

sauri yajuyo yace *what*?... (Meh) MADO kace yace?...


 Jabeer cikin jin tsoro yace "eh ranka yadade haka yace,'

Da sauri yace OK" jeka shigo dashi yanzun nan, da sauri Jabeer yace toh" tareda fita,


"A hankali aka tura kafar  Da sallama  aka shiga, ya'amsa sallama tareda   zuba masa idanu shima Wanda yashiga kallon sa yake, Ciki sanyi murya yace Mahmoud Ashe Zan sake gani. Ka?... wato hankan yana nufi "DA SANNU" ALLAH zaya baiya nar mun da A'ISHA ta kamar yanda ALLAH ya baiyanar dakai,


"A Hankali Yace kana nufin kace mani har yanzu ba' asan inda Adda A'isha Na take ba kenan?....

 Cikin sanyin murya yace  have a sit first, bamusu yasamu kujera guda ya zauna, yana duban sa Wanda shidin ma duban nasayeke,  

A hankali excellancy

Yace?......






💐LUFHA CE💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page131-35


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)




----------------------------------------

*®PEN WRITERS ASSOCIATION*


*PEN:THE STRONGEST WEAPON*

----------------------------------------


*only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers.*



✍🏾




"Mene ne yasa tun bayan, da kadawo "aka fada maka abinda yafaru tsakanin Nada "A'isha shine ka tafi, tsawon shekaru masu yawa baka dawowa ba sai yau,


 "Anya Mahamud abinda kayi ka   kyauta mana kenan,?...kako San   "irin tashin hankali da "aka shiga lokaci da "aka nemeka ba'agan kaba?...., muna Cikin jima min rashin A'isha sai Kai kuma katafi, Shin meyasa baka yarda da kaddara ba?.. meyasa bakayi tunani cewa duk abinda yasami bawa  da sanin UBANGIJI ba?..., Mahmoud ba baka kyauta ba, Sam, "ahankali yadukar da kai cikin nadama, yace kayi hakuri Hamman Soja, nazauna nayi tunani nage cewa haka danayi sam kyauta ba, shiyasa nakasa tunkarar "Baba gen Da "Hajiya domin "Ina matukar jin kunyarsu, 


wani "irin kaya tattace  murmushi yayi yace tsawon shekaru masu yawa, nake san naji wannan "sunan musamman daga bakin wacce "tasa mun sunan' Amma banji ba saiyau, Hmmmm...


 ya ALLAH Kaine masani abinda yake boye DA baiyane ya UBANGIJINMU "ina rokonka'  ka" banyanar mana da wannan baiwa taka "A'isha,  tareda abida ta Haifa,"ahankali yace Ameen tareda kwantawa sosai a "irin kujerar nan mai juyawa, idanu yarufe tareda.....jin wani irin kauranar ta yana ratsashi.


     *TUNA BAYA*

***********""""********

"Tun Lokacin da  Hamman Soja sukai magana da A'isha bai saike kiran taba, "asalima bai dawo gidan ba, saida yayi wata daya sannan  yadawo kuma bai isake A'isha agidan ba wani abin mamaki kuma shine Sam baidamu ba, don "a tunanin sa' gida taje domin yasan batada gurin zuwa daya wuce can, 


" Tunda A'isha tabar gidan "Aina'u takecin karanta babu babbaka,gida yazama Nata sai yadda taso takeyi KO" dayake tace dama gidanta ne', "akacin Amanarta' Dan haka nema yasa taci alwashin cewa duk Wanda yashiga  hurumin ta toh"  "DA SANNU" zata fitarda  dashi,


********

"A bangaran Hajiya kam hankalin ta yafara tashi,Saboda takira telephone din gidan su A'isha saidai Aina'u ce" ke' dagawa, kuma idan ta tambaye ta "Ina "A'isha sai tace mata "aitana bacci,

toh" itakuma Hajiya Saboda ganin tana dauke da juna biyu

Shiyasa bata cewa "atashe da "ita toh ganin cewa cikin ta yashiga wata Na biyu, 


ya kamata tafara zuwa "ana dubata "itada "abinda ke ciki ta, saidan kuma da  gabaya "idan ta kira telephone din ba'a dauka, toh shine   kuma "abin yafara bata tsoro,  gashi  shima Magajin kota kira shi bata sabu.


Tana zaune afalo tana tunanin A'isha, sai ga Hamman Soja yashiga da sallama, ajiyar zuciya tayi tareda amsa sallama saida yazauna nesa da'ita kadan sannan yagaida ita, bayan ta amsa sai take tambayar sa ya'u shi yadawo?...


yace dazu, tace yasu A'isha da Aina'u ?.... yai shuerun sannan yace lafiya lau, nan dai tafar yimasa Malabar A'isha har tana cewa yaka mata 

tafara zuwa "ana 

dubata "inafata dai cikin baya bata" wahala sosai, kasan cikin fari wani saiyai tabashi matsala Saboda rashin sabo,


shikam Hamman Soja gaban sane yake faduwa, saka makon jin abinda Hajiya take fadi, "ahankali yadago dakai yace batana nan ba?.. cikin rashin fahimar abinda yake nufi, tace wakenan fa?...cikin daure fuska yace ita Aishan mana gaskiya Hajiya A'isha bata kyauta Mani ba ni Sam basan haka take ba,


Da sauri tace me "A'isha tayi maka sannan Kuma tana "Ina,?... Don niba tazo nan ba,asalima rabona da ita tunda taje asibiti Na dubata nace tanada juna biyu, Kuma nakira telephone din gidan Kuma sai "Aina'u ce ke dau sai tace mun tana bacci

nan data fada mashi, 


Mtsww yaja tsaki yace yafi "mata dama nace", karta kuskura nadawo Na isaketa agidan nan,

Da sauri Hajiya ta mike  tareda cewa me kake nufi da hakan?... Cikin bacin rai Yace Hajiya wannan cikin dayake jikin Aisha banawa bane', alima ni bazan tabaq haihuwa ba tunda nasamu matsala lokacin, danai hatsari saboda haka shiyasa nace taje tanemi wan...


Da sauri Hajiya tadafe kirji tareda cewa Na shiga uku ni FATIMA, kace Ciki dake jikin A'isha banaka bane toh" nawaye?.... sannan Kuma bazaka taba haihuwa ba meyasa meka,?....

Yace "eh sabo...maganar ta tsaya saka makon gani Hajiya tafadi Sumammiya...


 Da gudu Baba gen ya karasa gurinta'wanda dama tuni yafito daga daki yana tsaye yana sauraran su, daga kanta Baba gen yayi tadora akafar shi yayinda yakata fadin Subhanallahi, Hajiya gabada hankalin sa yatashi ganin KO" motsi batayi,


Da sauri Hamman Soja zaya gurinta,wani mahaukacin tsawa Baba gen yadaka masa, tareda cewa kana zuwa gurin nan  zanyi shooting din ka Da wanna bindigan  najikin ka,' (nace tab lallai ran tsohon soja ya baci) yace zaka bani ruwa KO sai nayi mugun Saba maka, da saurin Hamman Soja yadauko ruwa, baba gen ya yayyafa mata, wani irin ajiyar zuciya tayi tareda bude idanun, da sauri ta tashi ta dubi Baba gen cikin gigita,


 Tace general mafarki nakeyi KO" da gaske ne abinda yaron nan yafada?... Cikin bacin rai tareda duban Hamman Soja Wanda ya dukar da Kai kasa, yace ba mafarki kikeyi ba Docter yakori matarsa daga gidan shi, Saboda yana zargin cewa cikin jikinta bana shiba ne, saboda  wai baza taba haihuwa ba,


Cikin daka tsawa Baba gen yace' Dan Ubanka,' waye yace maka bazaka taba haihuwa ba?... 

Da saurin yace naje gurin Likita har sau uku, shine yafada min,Hajiya kam kuka tasaki mai ban tausayi, cikin tashin hakali take fadi  shikenan yanzu baza ka taba haihuwa ba....?

yace "eh Baba ger Yace toh Maine ne hujjar ka?.. yace takardun suna nan, 

Shuru Baba gen yayi yana nazari, 


 Cikin kuka natashin hankali tace toh yanzu Ina A'isha ta tafi,?....yace niban saniba, tace oh" ni Fatima KO Ina A'isha ta shi ga?..


oho  yafada aran shi koma dai inataje ita' tasani, nikam  bazan iya zama Da itaba tana cin amanata ba, 


Cikin kuka Hajiya tace "a yadda nayima A'isha tarbiyya Sam bazata iya aikata wanna mummunan Aikin ba, haba Magaji zina da aure fa kake nufi?...., general nikam banyarda da "abinda wannan yaron yafada ba, kilama karya yakeyi,


Da sauriyace' ba karya nakeyi ba takardun suna nan, Baba gen yace' jeka dauko Mani takardu nagani toh" yace tareda mikewa yafita.


Cikin minti talatin sai gashi yadawo  koda Baba gen yaduba takardun, jikinsa yai sanyi yayinda wani irin zufa ke karyo masa,

 Da sauri Hajiya ta karba itama taduba, wani sabon kuka tasaki tana fadin,


 shikenan mu kuma  haka ALLAH ya kaddara mana, Kai guda muka Haifa Kai kuma bazaka taba haihuwa ba ikon sai ALLAH, toh meyasa ka kori A'isha meyasa baka kawo Mani ita ba nikam, Dana taya ta rungumar kaddara,

 Koda yake dama kila kana Neman hayyar dazaya rabuda ita, haka Hajiya taciga da fada tareda surutai, Wanda kai daga jikasan bata Cikin hayyacinta,

Yayin DA Baba gen meta faman  lallashinta Wanda shima karfin hali kawai yake.


***************

Cikin lokacin kankani magana takarade family cewa "A'isha tabace' sannan Kuma Hamman Soja bazaya taba haihuwa ba,


 hankalin zuriyan Alh Ahmed Dan kwangila yatashi sosai, dajin cewa Magajin family baya haihuba, Cikin lokaci kankani aka baza Neman A'isha tareda abinda ke Cikin ta, saida  kome kama Da ita basu gani ba balle ita kanta toh" ballanta Na su saran ganin abinda ke Cikin ta,


Tun "ana saran ganin A'isha har "aka fidda rai, yayinda kwana ki suka tafi tareda satittika da watan'ni shekaru, sunja Sosai yayinda Hamman Soja yaci gabada gudarar Da "aikin sa, ganin shekaru sun tafi sunja amma har awannan lokaci, Hamman Soja da Aina'u shuru ba  haihuwar, saboda haka nan sai su Baba gen suka yanke shawara cewa" Hamman Soja yasaki  Aina'u sai ta "auri wani KO" ALLAH yasa tasamu rabonta, tunda shi bazai haihuwa duk dacewa basu debe tsammani ba daga RAHAMAR ungijiba  "aikam Aina'u ta tuma kasa tace ita "abarta da mijinta zata zauna dashi "a haka, don haka sai "aka kyale ta,  saidai Kuma hakan yabata daman yin  abidan duk tagadama takeyi,  sannan   duk "abinda tace dashi Hamman Soja yake "aiki ,


itakam Hajiya idanu tasa musu yanzu tsakanin tada Hamman Soja sai gaisuwa, yayin kullum Addu'a takeyi ALLAH ya tsare A'isha aduk inda take tareda abinda ke jikinta, don tanaji ajikin ta cewa wannan cikin najikin Aisha Na halal ne yayinda shikuma 

Hamman Soja take rokon ALLAH ya yaye masa "abinda keda mashi, domin tabbas kwai wani abun da'akai masa wanda yake damusa Amma KO" meyene "DA SANNU" Allah zaibaiya narai dashi,


Kwatsam Aina'u tace Hamman Soja ya ajiye aiki wai tunda yasamu kudi yafara business, aikam baiyi shawara dakowa ba ya ajiye aiki, yafa business, ranada Baba gen yaji yaimasa fada sosai Baba engr yace' ya kyale shi dama shi yace yanasan Soja toh Dan yanzu yace bayayi aiba dole,


Don haka sai yaci gabada da Business dinsa  din sa, kwatsam, wata rana sai ya hadu dawata yarinya yar wani tsohon kwamishi Na ilimi Na nan  Yola, sunanta  Maryam yanu yansan ta DA aure itama haka, yafada mata baya haihuwa tace "eh zata aure sa haka saboda tana son shi,


"Aiko ba "adauki lokaci ba "akai bikin duk da rashin sanda Aina'u tanuna, wanda  saida aka Kai ruwa Rana tukun na, watan Amarya Maryam biya da tarewa sai tafara rashin lafiya zazzabi sosai a lokacin tuni Hajiya tadaina aiki, don haka Hamman Soja ya dauki Maryam dakan shi yakata asibiti, bayan Doctor ya dubata tareda yan tambayoyi ya tabbatar musu da cewa Maryam tana dauke da Ciki Na wata daya da sari biyu,


 Da sauri Hamman Soja yace Sam Maryam batada Ciki Doctor, ya kalleni shi yace haba yallabai kamar yabata daciki?... nifa nadu bata, Kuma  kaganni Na Kai kusan shekaru goma sha biyar Ina aikin balle kace KO" ban iyaba ne 


itakam Maryam hankalin ta yatashi, yayinda Hamman Soja ya kurawa Doctor idanu tabbas baza taba mantawa da wanannan fuskaba,  yace eh haka ne "ainata bazuwa gurin ka shekarun baya dasuka wuce, kadubani' Ka kuma  tabbatar Mani dacewa bazan Baba haihuwa ba, ka Kuma hadani da wasu Doctors suka  dubani suma Kuma sunka tabbatar Mani dacewa bazan haihuwa, toh yanzu kuma ya'akai matata tasamu ciki?...,


Wani irin faduwa gaban Doctor yayi yayinda yaji  zufana karyo masa "ahankali yace?...




💐Lufha ce💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page141-145


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)



----------------------------------------

*®PEN WRITERS ASSOCIATION*


*PEN:THE STRONGEST WEAPON*

----------------------------------------


 _only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen_



✍🏾



Lokacin danayi wani zazzabi tareda wani irin ciwon ciki mai tsanani,  ga kuma jini yana tazuba mani  saina shirya  natafi asibiti saboda naga Likita, 


don "atunani Na ciki nasamu yake rawa, don haka saidai kashhh Ashe ba haka bane, bayan likita yadubani don harda sikainin yace' najena yi bayan nakwo masa takardan sikaini din,


Sai yace Mani banida ciki "asalima mahaifata talalaci tayi guntu-guntu bazata iya daukar daba, saka makon sham magunguna barka tai dankeyi,


Yanzu haka masai yayi Mani aiki yacire domin batada amfani, "idan ba "acire ta ba toh" zantayin zubar jini ne, hankali Na yatashi sosai sai nace masa  toh" zanje nayi shawara da mijina  zandawo yace Mani toh", nikuma atunani Na bazan dawoba,


Sai abun mamaki tundaga wannan lokacin jini yake tazubo mani sosai, dole muka tafi nida gwaggo don "acire Mani mahaifa, tunda duk abinda yake faruwa ba wanda yasani dagani sai ita, Kuma "a lokacin Hamman Magaji yana can gurin aiki sa, don haka mukai tayin komai batareda yasani ba,


Bayan Doctor yacire mani mahaifa yace Mani shikenan banza taba haihuwa ba, muka dawo gida toh" tundaga ran muka fara shirya yadda zamuyi, tunda "a lokacin ansaka ranan auren Hamman Magaji da A'isha, bamu samu mafitaba saida "ana gobe sauri aure.


Sai muka shirya muka tafi Wani kauye, mukaje gurin wani mugun  boka bayan mun fada masa, bukatar mu, yace karmu damu dai mubiya kudin aiki, basai anbarta da Lafiya sannan zata samu Cikin ta haihuba.


Toh shine ran da'aka kaita akuma dawo Da ita ba Lafiya, Wanda tadauki tsawon lokacin tana fama  darashin Lafiya, bayan taji sauki ta tare saina fara tunanin yadda Zan hanata samun Cikin, nadauki alwashin cewa tunda bazan haihuba toh" itama bazan taba Bari tahaihuba,


Nayi ta tunani yadda zansamu mafita amma ban samu ba, watan "A'isha biyu da tareda sai nafahimci cewa tasamu ciki, saboda haka shine nai amfani da lokacin da Hamman Magaji yai hatsari, sai nacewa Hamman Magaji yakamata yaje yafara ganin Doctor saboda matsalan rashin haihuwar,


 Wani abin mamaki shine baiyi mani musuba, sai yace mani toh" yauwa zayaje amma saita fara biyawa tagida tukun Na sannan yaje asibiti, yana fita, sai nikuma nashirya nadauki bindigar Hamman Magaji naje guri Doctor nace masa baya idan yazo tafada masa cewa bazaya taba haihuwa ba,


 Toh Kuma bayan nayi nasara yakori A'isha, na kuma jegurin boka nace yayimata asirin da bazata dawo ba, sannan Kuma muka ce mashi muna San yaima Hamman Magaji asirin dazamu mallakesa,


Bayan yayi mani aiki sai yace toh" saidai muddun muka Bari Hamman Magaji, yai aure har yayi tarayya da matar har tasamu ciki, toh" daganan asirin zaya karye, mukace' ba matsala mu'a tunanin mu tunda baya haihuwa aiba zaya taba yin aure ba,


Kwatsam sai naji Hamman Magaji zaiyi aure, naso nahana amma hankan baiyu ba, tun bayan DA Maryam ta tare Saina fara tunanin, yadda Zan hanata samun ciki, Ashe bansani ba tuni tasamu ciki.


Wannan shine abinda na'aikata don Allah Baba engr kuyi hakuri, kace kar Hamman Magaji yasakeni' son shine yasa na'aikata haka saboda bana San wata ta haihu dashi yazo yana fifitata akaina, takarshe maganar tada sheshshekar kuka.


Hamman Soja ya harareta tareda cewa karya ki ke' munafuka bakya sona, asalima kedin makiyiya tace Kuma Saki "ainariga nayi shi, (kasan cewa lokackn dayai sakin batasani ba)saboda ni bazan Kara zama da azzaluma macuciya irin ki ba,


yayinda falon yakaure da surutu yan'iwa sai Allah wadai da halin irin ta sukeyi, dama dayansu sunajin haushin ta tunda kirikiri saita hana Hamman Magaji yai musu Alkhairi,

Baba general da Hajiya Binta kam Kala basuce ba,


 Baba engr ne yace ya isa haka

Cikin bacin rai yafara fada sosai, yace nasan duk abinda Aina'u takeyi dasa hannun ki, Rakiya Kuma baki kyautawa kanki ba "ace yarki zakisa "amugun hanya da za'a cuci Dan dan'uwanki, tareda baiwar Allah "A'isha mai tayi muku haka dakuka rabata da mijinta, kunata kulla mugun aiki bawanda yasani toh" aigashi nan dayake batada Hakkiku "DA SANNU" Allah ya bayyana Ku,


Cikin bacin rai Baba general yace aidama duk abinda Mutum yake aikata wa aboye sharri ko hairan toh" fa DA SANN wata rana Allah zaya baiyya nashi mutane kowa yaganshi, ALLAH ya shirya Ku, sannan yatashi bar falon.


Baba engr yabi bayan shida kallo tabbas yasan ran dan'uwansa ya baci, ahankali itama Hajiya tabi bayan mijinta,


 Sai falon yaitsit, shima Baba engr ransa yabaci sosai, sai yadubi gwaggo Rakiya data dukar dakai kasa, yace Rakiya ki dauki Aina'u kutafin gida domin Magaji yariga yasake ta Saki biyu,


 zatayi magana   yace banasan jinkomai, kawai kidauke ta kutafi duk shawarar damuka yanke zanfada maki, yace ku kuma kowa wacce ta tashi tatafi gida saboda haka sai ko" yatafi gida,


************* 

Saida Aina'u ta kai wata viyar sannan takoma gidan Hamman Magaji, koshi saida Baba engr yanuna mashi bacin rai tukun, Amma dayace shi Sam bazaya baida "ita ba,


Kulawa sosai Hamman Soja yakeba Maryam, har Cikin ta ya'isa haihuwa ta haifi diya Mace, ranan suna taci suna Hajiya Saratu matar Baba engr, fadin shagalin da'akayi ranan suna ban baki ne saidai mai karatu yasani shagali 'akayi bana wasa ba,


A haka yaci gabada kulada Maryam da AMA haka suke kiran ta, tare Kuma da son A'isha Wanda yakasa boyeshi "agaban kowa nuna  begenta yake, Wanda har hakan yafara damun Maryam, musamman dataga duk yabi falon su yaman'na photo A'isha saboda haka sai tafara nuna kishi, 


Yayinda shi kuma tuni yaja mata burki dacewa tabari, baiyi matar dazata fi A'isha azuciyar shi ba, tasani cewa Aina'u hadasu akayi A'isha kuwa itace macen daya fara so", saboda haka "amatsayin tada ban'ne "a zuciyar shi,


Saboda haka idan har tana son farin Cikin sa toh" taso A'isha, batada yadda zatayi don haka dole tabi "abinda yace' amma kasan zuciyar ta tanajin haushi A'isha,


Amah nada shekara daya Maryam tasake haihuwar diya Mace, akasa mata A'isha Wanda Hajiya ce tace asa mata A'ishan ta, "aikam Hamman Magaji kamar yayi hauka don farinciki, yayinda yadauki so yadora akan Little esha wacce yake kirada Honey, itama shekarar tadaya Maryam tasake haihuwar diya Mace, sai "akasa mata Fatima wato sunan Hajiya kenan sai suna kiranta Zarah mama


Toh" Kuma tundaga kan Zarah mama Hajiya Maryam bata sake haihuwa ba, saboda haka sai suka cigaba da kulada yaransu, tareda yi musu tarbiyya mai kyau,


Aina'u kam da'ita da banza agidan Hamman Magaji duk daya, kilama har gara banza yafita daraja, domin kuwa kwata-kwata yafita harkarta baya shiga sha'anin ta,


 bakin ciki ya isheta don haka sai ta iske shi daki tace itaka tagaji da'bakin cikin dayake mata saboda haka ya 

bata takardan Saki,

ba musu ya rubuta Saki daya yabata,

yace gashi nan rabuwarki Dani shine Abu mafi sauki garayuwai ki.



 shukaru sunja  arziki ya bunkasa ga Hamman Magaji, yayinda kaunar A'isha ke karuwa "azuciyar shi saboda haka ya dukufa Addu'a Allah ya baiyyana A'isha tareda abinda tahaifa.


********"******

Kamar wasa,Abokan  Hamman Magaji sukace yafito "takarar gwamna, aikam yafito, da lokacin zabe yayi Cikin sa'a yalashe zabe "inda yahaye kujerar gwamnan jahar Adamawa yola, yayinda yazama gwamna mai adalci wannan kenan.


A hankali ya sauke ajiyar zuciya tareda bude idanun shi ya zubawa Alh Mahamud, yace?.... 





💐Lufhat Ce 💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page136-140


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)


edited by Zainuddeen zain


----------------------------------------

*®PEN WRITERS ASSOCIATION*


*PEN:THE STRONGEST WEAPON*

----------------------------------------


_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pe writers_





✍🏾



"eh  tabbas "anyi haka  shekarun baya dasuka wuce nafada maka, saidai kasani' nima bada San raina na rubuta  maka, cewa bazaka taba haihuwa ba, tilasta Mani "akayi, da sauri Hamman Soja yace  ban fahimce kaba waye ya tilasta maka ka' rubuta Mani bazan taba haihuwa ba?... yafadi haka yayinda yakejin wani irin matsananci faduwar gaba,


Doctor yace shekurun baya dasuka wuce, "Ina zaune "a office din Na sai ga wata tashigo bako sallama, saidai kawai tanuna Mani bindiga, mamaki yakamani tareda tsoro Cikin karfin hali nace baiwar Allah Lafiya?...


tace Lafiya lau "aiki takeso nayi "mata "idan kuma bazanyi ba, toh" zata kasheni tafita batareda kowa yasani ba, Dan yanzu ma ba wanda yaga sanda tashigo,


"Idan Kuma kana ganin, bazan iya kashe' kaba toh" "aizan "iya kulla maka sharrin da Harka mutu bazaka manta dashiba,


 Tabbas zata iya "aikata abinda tafada domin naga fuskarta" ba "imani, don haka Cikin faduwar gaba nace wani irin Aiki kenan fa?... 


 Sai tace Mani wani mutun" zayazo nadu bashi,' "idan nadu bashi nafada masa cewa bazaya taba haihuwa ba, sannan Kuma nayi masa" hayyar zuwa gurin wasu "Doctor's din "idan yaje "suma sufada masa cewa bazaya taba haihuwa ba,

 

Banida yadda zanyi don haka sai nace mata toh" sannan tafita tareda cewa sai nado, batafi minti talatin da fitaba sai gaka kashe go,


Don Allah Kayi' hakuri wallah koda  nadubaka, lafiyar ka kalau ba abida yasame ka, saidai narasa abida yasa wannan matar tace nafada maka haka kagafarc.....Hamman Soja ne yakatse shi ta hanyar daga masa hannun, 


gaba daya jikin sa rawayake yayinda yakejin kafafunshi kamar baza su'iya daukar saba, don haka sai yadafa table din Doctor tareda dukar da kashi kasa, domin kuwa wani irin nauyi yaji yai masa,Wanda tunda yake bai tabajin nauyi irin wannan ba,


Cikin tashin hankali yadaga Kai ya watsawa ma Doctor jajayan idanun sa,  yace kana nufin "a wannan lokaci duk macen danayi tarayya da ita zata iya samun ciki?...., Doctor yace sosa kuwa tunda lafiyar ka kalau, saidai idan itace batada Lafiya,


Wani irin Kara Hamman Soja yayi tareda faduwa kasa Sumamme, ihu Maryam tayi Cikin matsananci tashin hankali, taduka tana jijjiga shi tana kiran  sunan shi Amma baitashi ba, hannun ta Dora akai ta tace Na shiga uku shikenan Doctor ka kashe Mani mijina,


Doctor da shima jikinsa rawa yake da sauri, yazo ya taba Hamman Soja yaji bai mutuba sumadai yayi, yace kiyi hakuri ba  mutuwa yayi ba sumace Ina zuwa ruwa ya dauko, yayyafa mashi, can saiya farfado da sauri ya mike tareda rike kwalar rigan Doctor, Cikin tashi hakali yace yasunan matar?...


Cikin matsananci tsoro yace bansan suna ta ba, Amma dai bazan taba matawa Da kaman'nin ta, Farace tanada kina ba sann... Hamman Soja ne yakatse shi da cewa nagode  kasan cewar yagane wadda yake nufi, sannan yakama hannun Maryam wacce keta faman kuka suka fita da sauri daga office din.



Tun bayan fitar Hamman Soja DA Maryam, hankali Aina'u yatashi don haka saita kasa zaune takasa tsaye, sai faman safa DA marwa takeyi "atsakiyar falo, sai tunanin take tareda tambayar kanta "Ina Hamman Soja sukaje shida Maryam,

Kasan cewar tana bacci suka tafi,

 

 tana Cikin wannan halin sai kawai taji sallama Maryam, dauri tajuya tana kallon su gabanta ne yafadi saka makon gani Hamman Soja, yanufe ta fuskashi ba'an'nuri don haka da sauri tajuya zata nufi daki,yayinda Hamman Soja yafinciko tada karfi  ya yarda ita kasa timmm sai kace kayan wanki sannan yajata kiiiii yanufi dakinshi da ita,


wata irin katuwar bulala yadauko irin tasuce ta SOJOJi, aikam tuni idanun Aina'u suka fito waje saboda tsoro zatai magana kenan, saitaji saukar bulala dukan ta yake  DA iyakacin karfi sa' "itako sai ihu takeyi tana fadin menayi maka?....Magaji,   yana dukanta yana fadin "au tambaya ta kike abinda kikai Mani ko?....Hmmm "DA SANNU"  idan  jikinki yaci duka Zaki ba kanki amsar tambayar ki',


Maryam kam tana tsaye abakin kofar dakin  sai kuka takeyi, takasa shiga kasan cewar itakam tana bala'in tsoron bulala, Amma dai sai faman bashi  hakuri takeyi, cikin tsoro tace Ahmed kar kayi kisan Kai fa! yace Maryam "aiyau rai kadan zan ragewa yar iska, "idan Kuma nayi Na sarar rabata daran' nata toh" shikenan ta huna, nima nahuta domin idan muka cigaba da rayuwa tare toh" tabbas zan dauwama Cikin bakin Cikin abinda ta'aikata Mani yayinda, ita Kuma zata gwanmaci gara muguwar ta da bakin cikin dazan guma mata arayuwa, duk wannan maganar yanayin tane ya dukan Aina'u wadda tuni tagala baita, jikinta kuwa duk yafarfashe abu ga farar mace harjini nafita,


Itakam Maryam tuni takara tsorata ganin jini yafita ajikin Aina'u, hakan ne yasa take ganin da gaske Hamman Soja kisan Kai zayayi, 


don haka da sauri taje takira layin  gidan Baba engr ciki sa'a shida kansa' Baba engr yada wayar, aikam tana kuka tana fada masa abinda kefaruwa, Cikin tashin hankali yace toh" gashi nan zuwa shida Hajiya Saratu matar shi,


Cikin abinda baifi miti talatin ba suka iso gidan, dai-dai lokacin da Hamman Soja yace nasake ki Saki daya Aina'u Nasake ki Saki biyu nas.... DA sauri Baba engr yace Kul! kana karasa fada sainayi mummunan Saba maka, ashe bakada hankali Magaji?.....,


Da sauri yasaki bulalan yaje yafada jikin Baba engr yasaki wani irin kuka maiban tausayi, kuka yakeyi sai kace karamin yaro "ahankali Baba engr ya zauna dashi, yayinda yake Shafa masa baya yana cewa ya'isa haka.


Yace haba Magaji "idan rai yabaci "aibai kamata hankali ya gushe ba,  kanasan kayi kisan kaine?.... sannan ya kalli Hajiya Saratu yace dake DA Maryam ku kama Aina'u kuje mukai ta asibiti, tace toh" dakyar suka iyafita da ita saboda nauyi tunda KO" motsi batayi, 


Sanna ya dubi Hamman Soja yace Magaji meya faru ne haka?...Cikin kuka yace Baba Aina'u ta cuce rayuwa ta' ta ha'inceni taraba nida matata A'isha, don haka ni ba'abunda zance mata saidai Na bartada ALLAH "DA SANNU"  kuma zata gane kurenta, Baba engr yace fada mun abinda tayi maka?....


Nan yafada mashi abinda Doctor yafada masu, rai Baba engr sosai yace tashi mutafi bamu Hamman Soja tashi suka fita,


A can asibiti Kuma da taimakon ALLAH dana likitoci Aina'u tafarar fado, yayinda Maryam taci gabada kula da ita harta jisauki Wanda bada San rain Hamman Soja haken tafaru ba, saidan tirsasawar da Baba engr yai mashi.


Gaba daya family an'hadu gidan Baba gen, Baba engr yadubi Aina'u yace Aina'u menene dalilin daya sakika ce sai Doctor ya rubuta wa Magaji cewa bazaya taba haihuwa?...

Cikin kukan nadama tace.?..


 



💐Lufhat ce💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page146-150


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)




----------------------------------------

*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*


*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*

----------------------------------------


~Don Allah kuyi hakuri narashin ganin posting Dina akan lokaci~ 



_*only exquisite and whizkid writers are opportune to be pe writers*_ .





✍🏾




Mahamud "Ina son ganin A'isha tareda "abinda tahaifa narokesu" gafara saboda, nasan nine silar shigan su duk wani kunci dasuka fuskanta arayuwa, saidai kashhh! ban San "inda zangansu" ba, don ALLAH katayani Addu'a Allah ya bayyana su "a duk "inda suke Afadin duniya nan, wlh Mahamud "Ina matukar bukatar su" kusada ni.


A" hankali yece Hamman Soja ka kwantar DA hankalin Ka, insha'Allahu " DA SANNU " ALLAH zaya baiyyanar  dasu," kullum  Addu'ar Dana keyi kenan Kuma inajin "Ajikina da yarda Allah sun kusa baiyana garemu.


Yace Hmmm! Mahamud na tabka babban kuskure   "Arayuwata  Wanda gashin nan har yanzu "Ina Da nasani  yisa,  Mahamud  meyasa ban saurari A'isha ba lokacin da take fadin Hamman Soja ka saurareni ba?..., meyasa bankasan ce Cikin mutane masu  _"BINCIKE"_?.... ba, farin Cikina guda "idan Na tuna cewa ban furta kalmar _SAKI"_ga A'isha ba,


Yace Hmmm! Mahamud kokasan cewa duk abinda yafaru dasa hannun Aina'u, Dasauri  Abba Yace kamar ya?...nan yafada masa abinda yafaru, Cikin takaici 

Abba yace "aikanta tayiwa,


"A hakali ya sauke Ajiyar zuciya tareda Mikewa yazo kusada Shi, kafadar shi yadafa yace Kayi hakuri Mahamud nine Silar rabaka Da yar'uwarka, Wanda ta dalilin haka ne yasa katafi kabarmu tsawon shekaru, baka dawoba sai yau daka zama babban Mutum,

Yafada yana murmushi,


Shima Murmushi yai yace Kai Hamman Soja, yace Allah you're a big Man nasan dai by now kanada iyali KO?...,

Yace eh inada Mata daya Asma'u" da yara biyu Baba na "Ibrahim da "Adda A'isha Yace masha'allah naji dadi da kasa A'isha Allah ya Albarkacesu"

Yace Ameen.


Toh yanzu kabani Labarin bayan rabuwa, murmushi yai yace "ai lokacin dana barnan Kaduna  natafi, nan dai yabashi labari "abubuwa dasuka faru dashi,"agarin Kaduna  da masu" dadi da marasa dadi,


Nan dai Hamman Magaji ya jajanta mashi  marasa dadi, yayinda yai mashi farin Ciki ga masu dadi,  yace toh" yanzu "Ina iyalin Ka suna can Kaduna nan ne?...,yace "a ah tareda su nazo saidai shi Baba Na "lbrahim yana can  Abu Zaria yace ita Kuma A'isha tagama Secondary school din ta, yace madallah Ashe dai yaran Nawa Sungirma?..   Murmushi yai yace bafa wani babba bane  saurin girma ne kawai _he just nineteen years go to twenty_ ita kuma A'isha _yanzu tashiga fiftieth years_ kasan yaran yanzu saikace "Ana zuba masu taki saboda saurin girma, Murmushi yai  yace haka fa yanzu fa "Amah itama _fifteen years_ My "Esha Honey _fouteen_ itakuma "Zarah Mama _thiree teen_  kasan cewar basu dawani tseyarya tsakanin su" sosai, toh" kajiba toh" Allah dai yaraya manasu" yace toh Ameen , toh" yanzu "Ina su "A'isha da "Mamanta kace tare Ku kazo KO"?...., 


"Eh "ai  gidana yana nan "a Karewa GRA watan'mu  daya kenan da tarewa agidan, da sauri  Yace _one month_kana garin nan Amma bakaje family House ba haba Mahamud toh' kana "Ina?...., yace  "aikamar yau muka tare toh" Kuma washe gari sai natafi America kasan cewar Ina gudanar da Business "acan toh" shine fa sai jiya nadawo, yace "OK


" Ashe muna tare kenan, kasan nimafa Business din nakeyi, shine fa su ALH NASIR JIMETA(abokinsa ne) sukasa nafito takarar gwamna, toh sai   gashi kuma Cikin lkon ALLAH nazama Governor of Adamawa state, Abunfa

 very Surpersi wai l'm a Governor  Hmmm l can't believe saida nagan'ni a office din nan sannan fa nayarda.


 yace Masha'allah A"iba "a Mamaki Da hukunci UBANGIJI  kasan  Mulki nashine kuma sai wanda yagadama yake ba, Addu'armu dai shine Allah yatayaka riko ya Kuma baka lkon" yimana Adalci, yace Ameen, yakai karshen maganar dayin dariya, shima dariyar yace toh" Ameen, 


Sannan Ciki Zoyala yace' yanzu tashi mutafi family House, Ka karbi bulala gurin Baba general da Hajiya Kai harda Baba engr, shima sai yatsala maka nashi bulalan saboda tafiya dakayi kabar su', tsawon shekaru kaga daka can sai mutafi gidana kaga iyalina,


Dai-dai lokacin da suka fita office din Hannun su rike da juna suna dariya.


**********

Wani Kyakkyawan Dattijo nagani zaune "Akan lallausan kushin, yana karanta Jarinda idanusa man'ne Da _medicate glass_ Baba general kenan dottijon kirki managarci mai   cikar kamala, Sallaman da'akayine yasa shi dagoda Kai,

tareda amsa sallama Cikin Matsananci Mamaki Yace Mahamud Kai ne?....Yace nine Baba.


Dai-dai lokacin da naga wata kyakkyawar Dattijiyar tana saukowa daga _steps_Hajiya Binta kenan, yayi danaji tana fadin "a ah wanake gani haka kamar Mahamud ?....,


"A dai-dai lokacin Da ta zauna, sukuma suka zauna "akasan kafet,

Tace general shin gizon da idanuna suka sabayi munne, kodai da gaske ne Mahamud Din'mu ne yau "agabana ?...

Murmushi Baba general yayi Yace Doctor tabbas Mahamud din'mu ne, sai kawai tafashe da kuka tace ashe zan sake ganinka Haba Mahamud me yasa kayi mana haka?...,

"Ahankali yamatso kusada ita cikin matsananci  tausayita, yayinda yaji wani irin haushin kashi yaka mashi waima  meyasa yatafi ya barsu?...,


 Sai shima yafara kukan yana cewa kuyi hakuri Hajiya

nasan ban kyauta ba,  amma insha'Allahu bazan sake ba kinji?...Baba  General yace "a ah Doctor farinciki zakiyi kin gansa "araye Kuma  Lafiya lau, Amma bawai kixauna kina Kuka ba, "Ahankali tasa hannu tashare hawaye shima yashare nashi,


Bayansu nutsu sai Kuma "a kafara gaisuwar yaushe gamo, toh" dagan nain kuma sai ya basu labari kamar yanda yaba Hamman Soja,

Baba general yace toh" _Alhamdullah_ ALLAH mungode maka, dama shi duk abida kaga yasamu BAWA toh" dama can rubutacce "Al'amarine daga ALLAH,


Ya UBANGIJINMU don tsarkin Mulkinka Ka "idan har A'isha tanareye itada abinda ta haifa toh" ka baiyyana mana da dasu" kamar yanda Ka baiyyana mana Mahamud 

 Dukkan su suka "amsa Da Ameen.


**********

Wani hadaddan folane mai dauke da kayan more rayuwa, wasu _3 beautiful flowers girls_nagani dukkan su suna sanye  Cikin kayan _sports_, da "alama sun dawo daga motsa jikine. duk da cewa sunyi kama da juna domin idan kagansu zakace ko Hassana Da Husaina Da Gambo ne toh" biyu sunfi dakyar tsawon, babban Cikin su tana rike da Waya da " alama chatting takeyi, mai bimata Kuma ear piece ne makale akunnen ta tan,karamar Kuma tana t.v game, gaba daya hankalin su yatafi ga abida sukeyi, gaskiya yamma ta kyakkyawai ne sai kace yayan larabawa.


Can sai karamar ta "Ajiye remote din ta  mike tana tsalle tareda fadi yeeeeehhh! "Dad is back, babban ta Dan harareta tace  dalla yiwa mutane shuru me karya Dad ne zaya dawo ya zu?.... Ganin suna magana ne yasa  tacire earpiece din "A hankali ta kalle su tace _what's happen?...._karamar tace Dad is back, dasauri tace ur liar "Dad ne zaya dawo yanzu?...tace Allah l'm not a liar, ku tsaya kuji karar jiniya mana, "aikam  tana rufe bakinta sai sukajiyo karar jiniya,


Da sauri sukaje gurin _Window_dakin suka leka, dai-dai lokacin da motoci kimanin guda goma suke shigowa harabar gidan, wasuma har sunfa Rayin _parking_ "aikam Da gudu suka sheka, don suyo mashi" oyoyo   har suna rigerigen shiga babban falo,


Dai-dai lokacin da yashiga falon da Sallama shi, da gudu sukaje suka rungume shi suna murna sukace barkada dawowa Dad, Cikin farin yace yauwa _My lovely Daughters yakuke ?_ suka ce Lafiya lau,

Dad yau meyasa ka dawo dawuri?...

yace "Ina tareda bako ne,


Shikam Abba kallon su yake cike da sha'awa "aranshi Kuma yace oh! Da yanzu wannan yaran diyan Adda A'isha ne, oh! ALLAH mai lko", gaisuwar sune takatsa mashi Zan can zucin dayake, ya Amsa fuskar shi cike da fara'.


Bayan sun zauna sai Dad yace  Mahamud this is my Doughters, yana Nuna su shi yace wannan itace Saratu Amah, sai Kuma A'isha My Honey esha and  last born Fatima Zarah Mama, Abba yace masha'allah ALLAH yara yasu yasa musu Albarka    yace Yace Ameen,


Dad ya kalli _beautiful Daughters dinsa_ Yace kunsan wannan?... yanuna Abba dayake ta Murmushi, Amah tayi shuru tana tunani itama Zarah Mama haka tayi, "Itakam esha datake can makale jikin Dad kamar zata shige Cikin babban rigarsa, dayake "itadin Sarkin son jiki ce kamar Mage,


"A hankali tace Dad yayi kamada Na cikin picture din can, daka ke bamu labari harma kace sunan shi Uncle Mahamud,

Dad yace yes My Honey shine, da sauri Amah tace Lah  Dad Allah bangane shiba, dariya sukeyi shida Abba Dad Yace toh" shine, Yace Zarah Mama jeki kira "Mom dinku tazo yau munada babban bako agidan mu,

 tace toh" tareda mikewa tanufi Ciki.


        

      *KADUNA*

*BAYAN WATA  DAYA*

**********************

Kamar koda yaushe yana zaune "a office dinsa' kanshi "aduke sai faman rubutu yake Doctor  I S G kenan,  A hankali Abdul-jabbar yaturo kofar yashiga bakinsa "adauke da sallama, 


"A hankalin yadaga Kai ya kalleshi suka hada idanu sukai wa Juna Murmushi, biron hannun shi ya'ajiye yana cewa ni wannan _patient_ din Nawa koda yaushe "amakare yake zuwa _Check up why?_ yace saboda banasan na isko kada mutane sosai  dai-dai lokacin da yazauna, nasan _by this time_ karage duba _patient_


 Shiyasa nake zuwa wannan lokacin, Doctor I S G yace hakane fa Kuma "aikai kyauta mun aikin ne yake yawa "inada maka abinfa sai "a Slow Abdul-jabbar yace "aikuna kokari Sosai wlh Yace toh yaza'ayi,


Bayan Doctor yagama duba shi yace abokina munkusa cin nasara "akan ciwon nakafa, Bakin Abdul-jabbar yadan tabe kadan tareda cewa toh" Allah yasa yace Ameen, sun Dan taba fira kadan sannan Abdul-jabbar ya mike yana cewa toh" nizan tafi, shima Doctor din mikewa yayi yace OK" toh" muje nataka maka, harsun Kai bakin kofar fita office din,


 Sai Doctor yace  af "aina manta barina baka naka _I.V_ dai-dai lokacin daya ke mika masa katin yace gashi kaga nahuta zuwa kasan saura _one week ne fa_ 

Abdul-jabbar yakarba yace?...







💐Lufhat Ce💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page151-155


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)




----------------------------------------

*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*


*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*

----------------------------------------



~*Don Allah kuyi Mani Hakuri narashin ganin posting Dina akan lokaci*~




*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers._*



✍🏾




Haba Doctor yanzu Saboda ALLAH yau saura _one week_ bikinka sannan zakayi "invited din'na,?... toh" yanzu dabanzo Check up din bafa?...  Doctor

 Yace yi hakuri "Aiyukane suyin mun yawa shiyasa, 


 Dama yanzu danatashi daga office zantafi nakai maku kaga hada manasu Y Y K shida M.B, Cikin zolaya  Abdul-jabbar yace toh" nidai bazan zoba, Da sauri Doctor ya rungumo kafadar sa tareda cewa yi hakuri taimaka mun kazo Don ALLAH kaji?..yakarshi maganar yana langabe kai irin nayara din'nan,


 Dariya Sukayi gaba daya tareda tafawa Abdul-jabbar yace karka damu Doctor zanzo insha'Allahu, nima saura _two weeks "intafi Yola kasan can sukai posting Dina,_ kaga bayan bukinka da _one week_ Zan tafi  yace masha'allah toh ALLAH yakaima narai Lafiya, 


Yace Ameen nagode, yace kai habadai "Ana tare nima nagode Allah ya bar zumunci ya kuma bayyana mana da "Humaira, Da sauri Abdul-jabbar yace ya'akai kasan zancan Humaira?... yace karkadamu "Ai yanzu mun zama daya, naji komai "agurinsu Y Y K mu cigaba da Addu'a Allah zaisa kaganta "indai tana garin nan,  yace nagoda Doctor kawo nasu Y Y K nakai masu, yadauko yana cewa yauwa my _My friend_kaga kahutar sheni dai-dai lokacin da yamika Abdul-jabbar l .V card din, 

Har bakin Motarsa yara kashi sannan yakoma office dinsa.



*********

Hannah DA Haleeh ne Zaune afaton gidan su  Hannah, kasan cewar sufara shirye shiryen bikin Hannah din, yayinda  ta keta faman kiran wayar Humeeh, sai kara take Amma bata dagaba,  Haleeh tace "Ah toh" wai "Ina "ta'ajiye wayar ne haka?...  kasan cewar takirata yafi sau goma sha biyar, Don haka Cikin Haushi Hannah  tace oh mata ace _Handset_ita tamaida Nata _Roomset_ Domin daga jin wayar nan "adaki tabar ta,



Da sauri Humeeh ta daga wayar da harta kusa katsewa, daga can Hannah zata farayi mata masifa ta katseta dacewa _Sorry My Hannah ta D D bada kanji asare kije gida kice ma Hajiya yafadi_dariya Hannah tayi tace Kai _My Humeeh kin kashe bakin dazanyi maki masifa kenan KO?..._ tace "ah wace ni DA kashe wannan baki naki wannan aikin "aisai Darling Doctor din.


Tace "aibazai iyaba tace Hmmm yarinya "aibaza ki'iya ganewa ba tukun sai kinje, dariya Hannah tayi tace nida kyaleni, yanzu Saboda ALLAH "Ina kika "ajiyar Waya tundazu nake ta faman Kiranki Amma _no respond?..._ tace kedai bari "Ina kicin "Ina tanaya "Umma aikine, tace "OK shiyasa, toh" ya kike  _where is my Haleeh_?... Haleeh tace _hello My Humeeh l'm here, (dayake Hannah tabude volume din) yakike?..._ tace Lafiya lau ya kuke ya Kuma shirye-shiryen?... sukace Lafiya lau, Hannah tace yaushe zakijo? 


Tace Ranan _Friday_ Da sauri Hannah tace wani irin Friday Kuma?..abinda za'afara events gobe, tace abinda yasa nace Friday Saboda shirye-shiryen School kinsa ranan Monday zanfara zuwa School din,


 (kasan cewar Malam yasoke maganar zuwa School America din  Shiyasa Abba yanema mata, "Admission "a American University dakenan cikin Yola) Hannah tace "eh hakane Kuma fa "aini walh naji dadi da da "Malam ya yahana tafiyar nan,


 Da yanzu fa badake za'ai bukin nan  ba, Humeeh tace kedai Bari dama inata tunani taya zanfara Rayuwa ba tareda "Ummata ba, tace toh" yar gidan "Umma "aigwara kifara koyo tunda "idan ba School akwai aure, tace hakane Kuma fa ke! "aidana tuna zaya rabani Da "Umma sai naji gabana yafadi _My Hannah yaki keji yanzu Don ALLAH? Dariya tayi tace My Humeeh kyaleni yanzu pls kizo jibi mana?,...tace au baza kifada mani ba?...tace zan fada maki Amma sai kinzo zakizo jibin?... tace toh" bari "Abba ya shigo saina fada mashi najima yana cewa zaya tafi Kaduna jibi sai mutaho tare shikenan ko?...,  sukace  "eh Mana" ta  Special_da sauri tace sai "anjiman ku tareda katse wayar.



***********

Masha'allah _Dinner ya kayatar_Amarya Hannah Da Angonta Doctor Ibrahim saimuce ALLAH yabada Zaman Lafiya, _Alhamdullah! Alhamdullah!! Alhamdullah!!!_injicewar Humeeh data ke kokari rufe taro da Addu'a, gabanta ne yafadi yayinda ta hango Abdul-jabbar Zaune yana Cikin wani dakakken Shadda _Sky blue yasa hula mai ratsi blue,_ya goge yayi  kyau abinshi kamar bashene yaiwann tashin Lafiya ba, ita Humeeh gani tayi kamar yakara kiba, da sauri tarufe taron Da Addu'a tabar gurin,


Zumbur Abdul-jabbar ya mike sai kace antsira masa "Allura, Ku tsawa yafara yi Cikin mutane da sauri Y Y k ya bishi yana cewa Nawa me yafaru?... batareda ya kalleni shi ba yace _My Cool_ ce gatacen zata fita Da Sauri Y Y K yajawo shi daga cikin mutane, yana cewa Haba Nawa wannan wani irin "Abune haka pls kanutu kadawo hayyacinka mana,


Tun' dazu fa nake maka magana Amma kana can kana tafaman tunani, toh" waima Ta'ina kaga Humaira?....da Sauri Abdul-jabbar yace naganta" tacan tabi  pls Nawa kasa keni naje gareta karta sake kubce cemani,


Shikam Y Y K sai sake rike shi yake yana cewa ni bazan sake kana, Saboda bansan inda zakaje ba Don naga alama baka Cikin Hayyacinka,


 Abdul-jabbar yarasa yadda zayayi, Y Y K yasake shi Amma yakiya, Don hakane yaji wani irin bacin rai yaziyarce shi, Saboda haka sai ya tattaro gabada karfinsa ya ture Y Y K "aikam yatafi taka-taka zaifadi sai yai saurin dafe wata bishiya dake kusa dashi,


Cikin matsananci Mamaki Y Y K yadaga Kai ya kalli Abdul-jabbar, Wanda yake faman huci saikace kumurcin maciji, Cikin bacin rai yace Dalla gafara Malan wannan wani irin abune haka?... duk kabi karirrikeni saikace wani Mahaukaci, nace kasa keni  gashi nan harta" tafi Saboda tsabar iskanci da walakanci irina ka, yakai karshen maganar dayin wani irin tsaki mtswwwww, yana gyara rigarsa adai-dai lokaci da M.B yakara so gurunsu,


Shikam Y Y K cikin matsanacin "al'ajabi yabude baki da hanci yana kallon Abdul-jabbar, yayinda ya hango wani irin matsananci bacin rai "afuskar shi Wanda tunda yake dashi bai taba gani irin shi ba.


M B yace kai Amma dai gaskiya ana Kama duniya, yanzun nan nagawa Kamar Humaira, Da sauri Abdul-jabbar yarike mashi hannun tareda cewa  "itace ba Kama bace kagani wlh KO"?.. Nawa nafada maka _l see My Cool_ Amma kace wai _l'm not ln My Sense,_ pls muje Karta tafi banaso narasa "ta "akaro Na biyu Ina Sonta" sosai, gaba daya Abdul-jabbar ya birkice masu saijan hannun M.B yake,


M.B yace Pls Abdul-jabbar Ka nutsu Kama fa nace kaga banida tabbacin itace" KO ba ita bace, Da sauri yace wlh itace _see her ln my eyes_

Yace toh" mutafinku muduba kila itace' da sauri Abdul-jabbar yace "eh, Sai kutsewa suke Cikin mutane suna duban Humaira har mutane sun Fara watsewa Amma KO mai kanada "ita basu ganiba,


Cikin bacin rai Abdul-jabbar yace saida nafada mashi Naganta" Amma yaki yarda, "Ahankali Y Y k yakarasa gurin shi saboda wani irin tausayin shine yaji ya kamashi, "aran kuwa fadi ya Kai ALLAH yaraba muda *MASIFAR SO*  rungume shi yayi yace kayi hakuri, banyi zaton da gaske kaganta" ba Amma Ka kwantar Da Hankali Ka idan tana ciki garin nan "DA SANNU" Allah yaza bayyanar Da ita,


M.B yadafa kafadar shi yace haka ne Ka kwantar Da hankalin ka insha'allahu zamu ganta", Amma kafin nan _why not_ mu tambayi "Ango shikuma ya tambayar mana "Amarya kila kawarta ce'KO?,...da sauri Abdul-jabbar yace "eh hakane mukarasa.



Doctor ya Dan hararesu Cikin sigar wasa yace saboda Allah sai yanzu kuke zuwa?...Y Y K yace "a ah tundazu mukazo saboda jama'a sunyi yawane shiyasa bamuyi maka magana ba, yace OK Shikam Abdul-jabbar wani sanyi ne yaziyarci zuciyansa saboda gani KO" wacece "Amarya hakan ya tabbatar masa Da cewa _you Cool dinsa tana nan gurin_.... nadai suka gaggaisa yayinda "Ango yagaba tardasu gurin Amarya Hannah, tagaida Y Y k Da M.B Amma sai taki gaida Abdul-jabbar "asalima hararan shita tareda Jan tsaki mtswwwww! sannan ta kauda kai  tanuna irin bama ta San kallon sa.


Mamaki ne yakama "Ango kai bashi kadai ba harda Su Y Y K, Shikam Abdul-jabbar Jikinsa ne yai sanyi ganin yadda Hannah tayi masa, Da sauri Ango ya kallesu yace?.....






💐Lufhat Ce💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page156-160


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)



----------------------------------------

*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*


*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*

----------------------------------------


~dafatan  readers zasuyi Mani afuwa narashin ganin posting Dina akan lokaci~


*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_.*




✍🏾




"Kuyi hakuri Don ALLAH "Ina zuwa Hannun Hannah yaja suka yufi bayan wata mota, suka tsaya hannun shi yaka dai-dai gefen Cikin ta ya _pinch ce ta  sosai yanda zataji zafi,_ "aikam taji domin kuwa kara tasaki mai hadeda Shagwaba, tafada jikinshi yariketa sannan yadago da'ita yadan tureta kadan ya kalle ta Cikin bacin rai yace My D "abokina nefa tun yanzu irin kalar tarban dazaki ringayiwa abokanai Na kenan?


Meyai maki baki gaida shiba" sannan kika masa wannan _bad look_? baki ta turo tareda zuba masa fararan "idanunta, sannan tace tabdi shi wannan mayaudarin ne abokinka?... lallai kam bakayi abokin kwarai ba.


"Idanu yazaro Cikin Mamaki yace ke! "Inaki kasan shi?... sannan kuma yaudarai meyayi maki?....,tace ah! ba Abdul-jabbar bane? Da sauri ya matso kusa da'ita yarike mata hannun da karfi, da sauri tadaga kai takalle shi gaban tane yafadi, saboda yadda taga idanun shi sunyi jajir lokaci daya alamar kishi karara "afuskar sa, sai abunya bata dariya Amma saita gintse gudun kartasha Mari lol,


yace "eh shine fada Mani inda kika sanshi?...,

Tace shine" fa saurayin My "Humeeh Wanda ya yaudareta, wani irin sanyayyan "ajiyar zuciya yayi tareda sakin hannun ta, dariya tasaki  hararanta yayi Cikin sigar Soyayya yace _what are you laugh?.._ tana rurrufe baki tace nothing,


Tsaki yayi mtswwwww tareda cewa Allah My D kinrai nani fa, Amma kwanan nan zanyi maganin wannan bakin meyiwa mutane tsiwa, 


Ya kalle ta yace fada mani yaudarain meyaiwa Humeeh?...., nan Hannah tafada Masa komai, yace wai yanzu dama Humeeh ce yarinyar da My friend yake nema acikin garin nan?....tace nema kuma toh" neman me yake mata "OK nagane yana Neman "tane yajidadin Kara yaudaranta KO?...,


Hararar tayati tareda cewa ban sani ba, Allah idan kika sake fadar Kalmar yaudaran saina bige maki baki, waiku mata meyasa tunani Ku kusan duk daya ne?...., keda "indakin San halinda Abdul-jabbar yashiga akan Son Humaira da kowani kikaji yakira shi da mayaudari sai "inda karfinki yakara,  mutumin da Har COMA yashiga kusan wata daya yayi batareda yasan "inda yake ba, ga ciwon zuciya dake damushi yanzu haka  yanazuwa gurina _Check up_, "idanu ta zaro tareda cewa what?... yace yes nine Doctor shi, kuma duk "a dalilin Sonta" Amma sai faman kiransa" mayaudari kike'

Nan yafada mata duk abinda yasani dakuma 

Wanda Y Y K yafada masa,

Toh yaudaran meyayi mata?....


Jikin Hannah yai sanyi dajin "abida Doctor yafada,   tadan tabe baki tace Hmmm toh" aida saiyafata mata gaskiya, "Amma meyena boye mata toh" aigashi nan "DA SANNU" Allah ya baiyyana gaskiya,  yace "eh toh" nan kam bai kyauta ba yanada kyau duk "abinda mutun zayayi "arayuwa toh" kafadi gaskiya, toh" "Ai mashi" afuwa yanzu mutafi kigaida shi"sannan kibashi hakuri, Don gaskiya banji dadin "abinda kikai mashi ba, sannan kikira masa Humaira tace toh"



 Doctor yace kuyi hakuri Don Allah munbar Ku tsaye, Y Y k yace "ah bakomai Hannah tace Abdul-jabbar "Inayini yajiki "Ashe kayi rashin Lafiya?.... da saurin Yace " eh Lafiya lau Hannah jiki aiyayi sauki ya jama'a?.... tace Lafiya lau toh" Allah yasanya Alkhairi yabada zaman Lafiya, 


Tace' Amin mun gode fa Don Allah kafayi hakuri dazu nayi maka mummunan fahimta,  dariya yayi  yace Lah bakomai "ai rashin sanine,  


Tace kaga "Humeeh kuwa?....da Sauri yace "eh naga kamar "itace" tayi Closed prayer KO?... tace "eh itace yace toh" yanzu kuma banganta, tace "OK Bari nakirata "awaya yace toh"


"Abun mamaki kuwa shine Hannah sai kiran number Humaira take Amma is Switch off,  ta kalli Abdul-jabbar wanda shima ita yake kallo tace' kaga wai wayar Nata akashe yake,


Amma Bari nakira "Haleeh kila suna tare, tana kokarin kiranta" sai ta hangota zuwa gurin su" Don haka sai tace yauwa gatanan mazuwa,


Assalamu'alaikum sannun Ku, shine abinda Haleeh tace' suka amsa, tace Miss D D kokin ganar Mani Humeeh?... l have be looking for her "Amma bangan taba, nakira wayar ta wai "akashe take"  Hannah tace nimafa "ita nake nema ainayi zaton KO kuna tarene"?... tace "a ah tace toh" Ina Humeeh tashiga ne?..., toh" KO ta tafi gida ne?… Haleeh tace Anya kuwa?...toh" idan KO" ta tafi toh" KO tabbas  "Aleeyu ne yatafi kaita gida, domin inajin yana cewa "idan antashi shizaya maida ita gida,


Dammm! Abdul-jabbar yaji kirjinsa yabuga, wani irin kishine yaturni kesa" nan DA nan idanun sa sukaru fe, Don haka Cikin zafin nama yafin ciki hannun Haleeh yace wanene "Aleeyu neye hadinta" dashi?....ina yakai Mani My Cool?... Cikin tsoro tareda zaro ido tace "ah Saurayinta ne" mana, Kai kumafa waye?... dakake kokarin tsinka Mani Hannu,



_Pls readers  kar kumanta Haleeh bata taba ganin Abdul-jabbar_


Yace pls  Sorry call me Abdul-jabbar. da sauri ta nunashi da yatsa tana cewa Oho" dama Kaine' ka, yaudari my besty "Humeeh saida kadasa Sonka "acikin zuciyar ta sannan kagudu kabarta", saboda tsabar yaudara shine  yanzu ka kuma  dawowa toh" kasani cewa yanzu  My besty "Humeeh tafi karfin ka domin tasamu me" Sonta da gaskiya Wanda yafik.....


shuru tayi saka makon wani irin Uban tsawa da Abdul-jabbar yadaka mata,  Cikin matsananci bacin rai yace' karyane babu wanda yafini "SONTA" kum....  yakasa karasa wa, saboda jindayai Zuciyar shi tanai masa zafi, da saurin yasa hannun shi dai-dai saiti zuciyar shi yace wahhhhhhh!


Yayi da Hannah taja Haleeh gefe tana cewa gaba Haleeh meye haka?... bashi Da lafiya fa, nan dai tafada mata komai jikinta yai Sanyi, "ahankali tajuya tana kallon shi saitaji yabata tausayi su" Doctor ta hango suna mashi magana da "alama suna lallashin sane'


"Ahankali suka karasa gurin su" nandai "aka fahimci juna tareda bajuna hakuri, sannan suka kwashi jiki zuwa gidan su Hannah "Amarya Dan suna kyauta ta zaton Humeeh tana can.


**********************


"Abinda yafaru kuwa shine Lokacin Da "Humeeh tagama " Addu'a jikinta yana tarawa tabar  harabar Hotel, saboda kar Abdul-jabbar yaganta Don haka tana fita sai ta tare "adai-dai tahau Sai gidan malam,

Bayan tabiya me adai-dai kusan kudin sanna 



Sai tanufi cikin gida "A zaure ta iske Malam shida Abba suna fira, Malam yace "a ah su budurwar Kauye yan biki mashaya gara, "ai yanzu nake cewa Abban ki yatafi kawai yabarki', idan  kun gama bikin sai kiringa taya matana Aiki,


Tace wani?.... tab... kafata kafar Abba na, Bari ma kagani nashiga Nai Sallama da yar tsohuwar 

matar taka, tareda dauko kayana nazo mutafi KO" Abbana....? shidai Abba baice komai Sai dariya dayake yi, Cikin wasa Malam yace aisaikin sati biyu anan tukun na, tace me?... aibazan iya sati biyu banga "Umma ta ba tafada tana dariya shima dariya yake yace ja'ira sannan tashiga Cikin gida.


**********

Zaune suke' Cikin kayatattacen falon gidan  Hannah dayaji kayan more rayuwa, _(tunda dama  anriga ana kai ta daga can aka tafi Dinner)_ Abdul-jabbar Y Y K, M B  Doctor S I G Haleeh and Hannah,  ga badaya hankalin su atashe yake especially Abdul-jabbar, tunanin Su "Ina wannan Aleeyun yakai "Humeeh?....


Kasan cewar suje gidansu Hannah hada gidansu Haleeh amma bata can, sannan har Lokacin wayar ta "Akashe gashi  tun karfe takwas har yanzu karfe goma darabi nadare, Hannah tace toh" wai Ina My "Humeeh tashiga ne?... 


Haleeh tace' kashhhh! ai mun matan kodai tana gidan Malam ne?...Hannah tace' tabbas tana can da sauri Abdul-jabbar yace "Ina ne?... tace gidan kakanta Doctor yace  lallai kuwa toh" mujenku can gidan ko?... Abdul-jabbar yace eh muje, Doctor yace My D kubarimu muje KO?,... tace toh" .


Har zasu fita sai Wayar Hannah tayi Kara, kodata duba saita ga sunan Humeeh" da sauri tace Lah!... Kunga taka kira, da Sauri suka dawo, Wayar tadauka tareda bude Volume din yaka sance duk sunajin  magana kenan.


Saidai Hannah shuru tayi ba tareda tace' komai ba, daga can "Humeeh tasaki kayatattacen Murmushin Da harsada saurin shi yafito ta cikin wayar,

Yayinda Abdul-jabbar yaji Wani irin yarrrrrr!  "ajikinshi "Aranshi KO fadi yake yaushe rabonda yaji wannan tsadaddan Murmushi.


Sannan Cikin siririyar muryarta mai dadi tace _Sorry My Hannah I know  U angry with me ba,?_... Hannah tace haba My Humeeh "aikema kinsan dole nayi fushi kin kosan irin tashin hankalin damuka shiga, saboda rashin ganin ki'?...tace toh kuyi  nan "Ina my Haleeh?.. tace gatan kusa dani tanajinki,


Hannah tace toh" munyi  Amma dai yanzu where are you?... Dariya Humeeh tayi me sauti, sannan tace am ln my "Umma bed  What?.... shine abinda Hannah DA Haleeh suka fada "alokaci guda, da Sauri Hannah tace kina nufin yola?...tace yap...tace pls my Humeeh talk true fa?... tace  Allah kuwa gani nan "akan gadon "Ummana, "inata juye-juye saboda kewar Kuta dameni, Hannah tace Amma meyasa zakiyi mana haka?.., tace shiyasa nace kuyi hakuri, bansan yadda zanyi na fada maku ba ne, tunda saida Abba yariga yayi bokin jirgin sannan yakira yace idan mun gama nataho mutafi.


Pls kiyi hakuri kinji My besty kicewa my Haleeh itama tayi Hakuri, Allah har nayi miss dinkufa Haleeh tace muma muyi miss dinki. Hannah tace toh" yanzu  kice  Ina gaida "Abba DA "Umma sannan kifada mana Address dinku, DA Sauri Humeeh tace Zaku zone?.. tace "eh tace toh" kibari idan kunzo sai muzonida driver mu dauke Ku' Hannah tace kedai fada mana saboda zuwan bazata zamuyi maki',


Tace "au hakane? sukace "eh mana" tace toh" shikenan rubuta nandai tafada, Haleeh ta rubuta sukai tace toh " wai yaushe zakuzo keda kike "Amarya?... tace kedai baruwankin, tace "au hakane?... sukace "eh mana" sannan sukai Sallama. ta kashe wayar. tareda kallon Abdul-jabbar tace my Haleeh bashi Address din, idan harda gaske yana Son  our "Humeeh toh" yasa meta Yola Kome kikace?...


 Haleeh tace kwarai DA gaske, dai-dai Lokacin da tamika masa takardan medauke DA Address din,

Ya karba fuskarta shi cikeda  farinciki yace?...






💐Lufhat💞💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page161-165


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)



----------------------------------------

*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*



*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*

----------------------------------------


*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_*.




✍🏾




"Insha'Allahu zani Yola Saboda Na tabbatar maku dacewa Son "My Cool "acikin jinina yake, yanzu saura Number ta zakubani saidai don ALLAH kar kufada mata, komai gameda Address dinta dakuma number tada kuka bani, Saboda "Inason ne nai mata zuwan bazata. So dama  nest week zamu tafi kasan cewar Chan "akai posting din'mu, So kunga da yardan Allah zuwa Yola bama kawa KO?.. Me kukace friend's dai-dai lokacin daya ke kallon su Y Y K fuskarsa cike tada farin Ciki da an'nashuwa,


Suka hada baki gaba daya sukace" yesssss "angon A'isha Humaira,  tareda tafawa sukai dariya harda shi yace in ALLAH yayarda, very soon zakusha bikin kamar yadda  mukasha Na Doctor yau. Sukace Allah yasa Ameen suka amsa gaba DAYA. nan dai Hannah tabashi number Humeeh sannan sukayi Addu'a Allah yaba Amarya da Ango zaman lafiya da zuri'a tagari, sannan sukai musu Sallama zasu  tafi  sai Haleeh tace ummh Bari nazo kusaukeni gida. 


DA sauri Hannah tarike ta tareda fata fuska tace haba my Haleeh ki kwana "anan mana? "Idanu Haleeh ta zaro tace kwana kuma my?... Hannah. suma baki suka hada guri fadin kwana kuma?...


Cikin shagwaba Hannah tace "eh tunda dare yayi basai takwana ba gobe ta tafi KO? My D D tafada tana kallon Doctor Wanda yaketa watsa mata harara cikin gatse yace mata "eh dariya tayi tace yau shikenan kinga my D D yace "eh ki kwana nan,


Su Abdul-jabbar kam suma dariya suke najin wannan "Almara DA Hannah takeyi, itama Haleeh "abin dariya ya bata.  tace toh" zomu koma sai My D D yaraka su KO?...tafadi tana Jan hannun Haleeh, da Sauri Kuma Ciki daure fuska Doctor yace ke! Haleema wuce muje su' sauke ki "agida,


Tace toh" Hannah kam rike Haleeh tayi sosai tana cewa haba my D D bakace ta kwana ba?...

 Doctor Bai saurare taba yace wuce mutafi yafada yana kallon Haleeh, saida Kuma takasa tafiya Saboda rikentan da Hannah tayi.


Kallon Hannah yayi tareda cewa my D  saketa sutafi, kafada tama kale tareda rungume Haleeh sai Kuma tasaki kuka, tana cewa pls my Haleeh Karki tafi kinji?... "itama Haleeh rungumeta tayi sai kuma tafashe da kuka, sukam

Su Abdul-jabbar  shuru sukai suna kallon cikin Mamaki. Yayinda sukuma suke kuka sosai narabo dajuna, Wanda sunsan "inbadan aure ba toh",sunsan babu abinda zaya rabasu saidai mutuwa tunda wani lokacin taresuke kwana, KO" gidan su' Hannah KO" gidan su Haleeh, toh" sai gashi yau zasu kwana da ban Da ban.


Ganin cewa da gaske kuka suke sosai sunki sakin juna, sai Kuma suka basu Abdul-jabbar tausayi. Ahankali Doctor ya isa gurinsu cikin sigar lallashi yace haba  _Lovely friends_kukan mekuke?... 


OK" nagane kuna kukan rabuwa da junane KO?...da Sauri suka daga Kai alamar "eh yace toh" "anfada Ku "idan daya "yayi aure shikenan "an'rabu?...

toh" ba'arabu ba "ai wannan lokacin ne zaku Kara dankon zuminci ku, bawai Ku tsaya kuna kuka kamar  irin little-little childrens din'nan ba.


 Kuba kusan cewa yanzu they're bigs girls ba?... cikin zolaya yace bani wayarki nakira Humaira ko dariya tayi maku


Cikin shagwaba Hannah tace gashi, yace "au nakira  tadin?... tace "eh.   nan danan yayi Dialling number Humeeh tareda sa Wayar "ahandsfree, saiko tadaga, saidai cikin sheshshakar kuka zukaji tace Hello waye?...kasan cewar bata tsaya duba waba, cikin matsananci Mamaki Doctor yace Humeeh tace na'am yace meyasa meki naji kamar kina kuka ko?..


_*Allah sarki Humeeh" tana can tana kuka mai kunshe da Abu biyu", daya kewar su Hannah da Haleeh daya Kuma na SON Abdul-jabbar, wanda ganishi yatayar mata da tsohon mikin dake zuciyar ta. domin kuwa jitayi SON Abdul-jabbar yadawo mata sabo fil "ayanda takeji yanzuma haryafi Nada saidai tunawa datayi cewa yanzu Abdul-jabbar banata bane yasa take kukan tausayin kanta*._


"Don haka cikin cikin kukan Shagwaba tace ummh! I Miss my Hannah and Haleeh I lot.

 

Dariya ce takwace wa Doctor shidasu Abdul-jabbar, da sauri Humeeh tace waye Kai?... yace l am Doctor Ibrahim "Angon Hannatun Humeeh DA Haleeh, hakane?... Tace eh, yace ayya

 No wonder ashe kema kina can kina kukan'ne, shiyasa suma suke nan sunayi.

"ALLAH sarki three heart's in one place,


Toh ku "Inbanda "abunku ai "idan kaji kewar dan'uwanka bazama zakayi kana kuka ba, just dauki Waya kakira shi saikaji lafiyarsa' Shima sai yaji taka za'a

Ko?....

Bahaka bane friends suka ce" hakane.

 

Yayinda sukaji tausayinsu" yaka masu"  tawani bangaren kuma kawancansu yana birgesu. Haleeh tace Doctor "Ina Hannah DA Haleeh yace gasunan sai kuka suke faman yi,

Humeeh tace My Hannah,

Cikin Shagwaba Hannah tace Na'ma

toh" my Humeeh Shinefa yace my Haleeh ta tafi ba,


 yace toh" ai abinda yasa nace ta tafi Saboda kinga gida ba'asan zata kwana ba shiyasa,


Humeeh tace pls Doctor kabari my Haleeh ta kwana mana?...kaga saita taya my Hannah hira. yace Humeeh bai Kamata  Haleeh ta kwana ba tunda gida ba'asan zata kwana ba, kinga kwanan ta anan  zaya'iyazama damuwa "azo ana nemanta "amma kunsame ?.. girgiza Kai sukayi alamar "a ah yace l promise yours gobe dakaina Zanje har gidana dauko maki Haleeh tazo tawuni maki hardare, wani "abinda Mamaki shine DA Sauri suka hada baki harda Humeeh, sukace  da gaske?... yace insha'allahu


Dariya sukayi gaba dayan su" tareda cewa "eh mana", nandan Doctor cikin hikima irin ta maza ya lallashesu", sannan suka tafi "akasauke Haleeh gida sannan Y Y k yakai M B gida yakai Kuma Abdul-jabbar sannan shima yanufi gida, dayake da motar shi Y Y k din  sukaje gurin Dinner.


*American university Yola*

*****************

Da misalin karfe goma Na safe, Humeeh ce' zaune saman wani dotse "akarkashin wata bishiyar fulawa, sanye take cikin rigada siket na'atamfa  mairuwan toka, tanada ratsin ja tasaka hijab shima ja.

tana rataye da jaka mairuwan toka shima takalmin kalarshi kenan.


 fuskarta bawani kwalliya saidai powder kawai data Shafa, sai Kuma  man baki kadan  data shafa alebenta. Gaskiya dress din yai mata kyau musamman data man'na wani Dan siririn glass "afuskarta. 


Wasu littafiai naga tana dubawa, can Kuma sai naga tabude Jakarta tafito da wayarta, Dailling Number Hannah naga tayi tareda bude hands free din wayar sannan ta ajiyeta "akan littafai.

Daga can Hannah tadauka tareda yin Sallama, cikin zalaya Humeeh ta amsa dacewa Amarya  kinsha mai yamike?


Dan tsaki mtsww! tayi tareda cewa nasha mai kona sha wahala,

Dariya Humeeh tayi, yayinda Hannah tace "au dariya ma kike Mani?... tace toh" kedince' wlh "inbanda abinki meya hada Amarya Da shan wahala?... Wadda akace' yar'sha galice "ita komai a kasamu ita "akaba ta karashe maganar tana dariya. tsaki  mtsww tayi tace "aiko meye idan kikayi "aure zakisani yar'rainin sense kawai.


 DA Sauri tace wani?... tab.. nikam bazanyi aure nabar Umma taba. tace "au Allah?... tace ummh, (Murmushi tayi data tuna cewa Abdul-jabbar yana nan zuwa gareta Wanda Kuma tabbas da maganar aure zaije) Dan haka sai tace toh "ashikena saiki zauna kiyi tayiwa "Umma gadin daki, 

tace "aidama yarinya kobaki fadaba, tace toh "Aisaiki tattake nidai yakike?.. 


Tace lafiya lau toh" ya school din?... tace lafiya toh" Allah ya bada sa'a Ameen, nan dai suka Dan  taba fira sannan ta kashe wayar, yayinda tacigaba DA duba littafai.


Assalamu'alaikum shine Abunda taji amfada cikin wata siririyar murya,

A hankali ta "amsa tareda daga Kai ta kalli maiyin Sallamar wata budurwar tagani yar kimani shekara goma sha biyar, kyakkyawa tana sanye da "Abaya baka.

 tayaye kanta da mayafin abayar fuskarta tasha kwalliya, yayinda ta man'nawa idonta irin glass din'nan DA "akekira no respect.


Cikin yar siririr murya tace Don Allah zan'iya zama nan wurin?...tana Nina kusada Humeeh, yayinda Humeeh tace Lah! bakomai kizauna mana. tace OK ta zauna tareda cewa thanks, Humeeh tace no problem. Can sai tace sunana *SARAH "AHMED ABDUL-JABBAR* kefe?...,wani irin yarrrrrr! Humeeh taji "ajikinta saka makon jin sunan "Abdul-jabbar, Murmushi tayi sannan tace *A'ISHA "MAHAMUD IBRAHIM,* tace OK wani department kike?.. tace Medicine. Da sauri tace Wow! nice to meet you wlh, dai-dai lokacin datake mika mata hannu tace nima can nake.


"Itama hannun ta mika mata tana dariya tace Allah sarki, tace kinga nifa banyi copying times table ba koda yake  "ance sai 12:00 mukeda lecturer  KO?... Humeeh tace "eh hakane toh" ganawa basai kiyi copy din ba,  tace "OK toh" nagode takarba tana rubutawa. bayan tagama sai kuma sukafara fira kamar sun dade dasanin juna, har zuwa Lokacin lecture yayi suka nufi Class din.



*BAYAN  SATI DAYA*

*****************

Da misalin karfe 2:30 pm Humeeh ce" kwance tana Waya da Sarah sabuwar kawarta. kasan cewar yau tun  2:00pm suka tashi daga school. Dan haka take hutawar ta'abinta, wadda Kuma "acikin sati dayan nan sun shaku sosai dajuna itada SARAH "idan kagansu" sai karantse dama can tare suke" wanda har tasan "Haleeh DA "Hannah kasan cewar Humeeh tabata Labarin su harsun gaisa "AWaya"


Hira suke tazu bawa kamar bayanzu suka rabu makaranta ba, Sarah ce' keyiwa Humeeh korafi cewa ya kamata tazo gidansu. Kasan cewar "ita Sarah taje gidansu" Humeeh har sau biyu, dariya Humeeh tayi sannan cikin zolaya tace 

Sorry my Saratutu aizanzo.


_(Dayake tasan bata son akirata Saratu saidai_*SARAH*)


Da sauri  tace Kut! Amma dai my Humeeh kinci abinci hada wani Saratutu KO?... kuma kinsa I don't like it faaa! Cikin dariya tace Sorry nadaina. tace "OK toh" fada Mani yaushe zakizo?... kinga sisters Dina sun'matsu suganki.


Tace Ummh! dama "Abunda yasa kikaga banzo ba saboda "Abba baya nan ne shiyasa toh" Amma kinsan me?.. tace "a ah saikin fada, tace "Abba  yadawo da sauri  tace da gaske yaushe?... tace Allah koda nadawo gida Na iske shi' dama shizan fada miki, So kinga gobe zanzo insha'Allahu. tace toh Allah ya kaimu tace Ameen, "Ina gaida "Umma shima "Abba ina gaida shida dawowa sukai Sallama.



Tana cikin chatting Da  mutanan ta "Hannah da "Haleeh sai bacci ya kwashi ta, cikin baccin taji Wayar Na Kara, dauka tayi tasa "akun'ne batareda taduba ba. cikin murya bacci tace Assalamu'alaikum,


Zumbur naga tamike tamkar wadda "aka tsikarawa Allura tareda zaro beauty eyes dinta waje cikin hada kalmomi naji tana cewa?...






💐Lufhat Ce💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page166-170


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)


----------------------------------------

*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*


*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*

----------------------------------------



_*Pls masoya wannan littafin kuyi Mani afuwa narashin ganin posting Dina, akan lokaci. abubuwa wanne sai a slowly Amma insha'Allahu komai zayazo normal nagode.*_






*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_.*



✍🏾




"W..a..n..e..ne..?.. Sai Kuma naga tasauke wayar tareda tsura wa number idanu, yayinda jikinta  yaketa rawa "a handsfreen tasa wayar, da'alama tanaso ne' ta tabbatar da gaske muryar shi" din'ne, KO kuwa kunnan tane yake mata gizo kamar yanda yasaba.


 Saidai ga Mamakin ta saitaji Cikin Zazzakar muryarshi dabaza ta taba mantawa da'ita ba,  yace Hello my Cool kenan, nasan kinajina sannan kuma kamar yadda *SONKI da KAUNAR KI' kE DA KOMAI NAKI*bazaya taba gushewa acikin Kwakwalwa taba, toh" kema nasan haka *KOMAI NAWA* bazaya taba gushewa acikin Kwakwalwarki ba.


 Domin *SO DAYA NE* saboda haka gani "A harabar gidanku, kizo kiyi Mani jagora domin kinsan bai dace Na shiga gidan mutane, batareda *IZINI* ba so l am wanting for *U my Cool*" sannan yakashe wayar.


"Idanu nagata  tsurama wayar tabbas shine jitayi kirjinta yaci gaba da bugawa, saka  makon tunawa datayi yace' yana harabar gidan. don haka da  sauri tamike tareda jawo mayafin "abayarta dama shike jikinta Dan haka saita yafashi,


 Tareda shuran flat shoes dinta tasaka sannan tafito waje, da sauri take saukowa daga matattakalar benan, Da sauri tawuce Umma dake zaune "afalo, yayinda Umma tabi bayan ta Da kallo Cikin mamakin "aranta tace toh "ina kuma wannan lafiya "inazata haka Da sauri?..


Humeeh kam tana fita Sai tafara waige-waige aikam saita  hango shi, tsaye ya jingina ajikin wata dan kareriyar mota ya rungume hannu akirji, yana sanye da uniform din,su" na SOJOJI.


_*Kut shine abinda nace saka makon ganin ABDUL-JABBAR turkashi toh faaaa*!_


Tsaye tayi Chak! tana kallon shi fuskarta cike da mamaki, yayinda shima yake kallon ta yana takowa "Ahankali Cikin tafiyar kasaita, irin Nasu" na Sojojin masuji da'isa da takama.


Sai Murmushi yake sakar mata ganin yakusa isketa yasa tafara tafiya, "ahankali da baya da ba yayinda shikuma yake binta ahankali-"Ahakali, 


Harsuka isa bakin kofar falon tadaga kafa daniyar zata shiga falon kenan, Saita tafisuuuuu! zata fadi tabaya.


Cikin Zafin nama irin Na SOJOJI  yarike mata hannun, tareda tallabo  kugunta. yayinda hannun ta guda Cikin nashi hannun, gudan Kuma  tadafa kafadar shi yaza mana  suna jiyo bugun zuciyar su tareda jin'numfashi 

Juna.


Kallon juna suke sosai yayinda kamshin turaransa yahadu danata, Sai yabada wani irin ni'imantaccen kamshi mai dadin gaske, yayinda sukaji wani irin kasala yaka masu "alokaci guda.


"A hankali yakai bakin sa gurin kun'nanta Cikin rada yace wayace maki ana tafiya da baya da baya bakisan hakan bayada kyau Ummh?..



"Itakam Umma dataji Humeeh shiru bata shigoba, Saita tashi tanufo hanyar waje don taga KO lafiya,

Saidai abinda tahango talabulen yasata tsayawa, kasan cewar labulen falon irin  mai ragan'nan ne 

Don haka da sauri tace Humaira...


Cikin tsoro tareda rawar murya Humeeh tace N..a.n.a na'am Um..mah gani, "Ahankali Abdul-jabbar yadaga ta yayinda yaketa sakar mata lallausan Murmushin sa mai kashe mata jiki.


Da sauri tajuya tanufi Cikin falon jikinta Sai rawa yake, bin bayanta yayi yana dariya  bakinsa dauke da Sallama yashiga cikin falo, Umma ta amsa yayinda ya tsugun'na  har kasa yace sannu Umma "Inayini da fatan munsa meku lafiya?.. cikin jin kunya tace lafiya ya Aiki yakuma mutane nan gida?...yace lafiya, tace toh" madallah sannan tanufi kitchen kasan cewar dama tana girkin'ne,


Humeeh tana ganin "Umma tanufi kitchen Sai ita Kuma tanufi dakinta, yayin da Abdul-jabbar yabi bayanta da kallo, da dan gudu-gudu take taka steps din tana shiga dakin tarufo kofa. tareda  jingina bayanta "a kofar idanun ta rufe, sai sauke nufashi take sai kace wacce tayi gudun tsere.


"A hankali Abdul-jabbar yamike' daga tsugun'nin,yayinda yatura hannun wanshi dukka biyu 'acikin aljihun, tunani yake arashi kuma fadi yake meyasa my "Cool ta tafi kodai batayi farin Cikin ganinsa bane?...


Zama yayi "a daya  daga Cikin kushindin falon yafara kallon t.v, kusan 30 mints shuru ba Humeeh ba dalilin ta. Yayinda kallo daya zakaiwa Abdul-jabbar ka' fahimci cewa kallon kawai yake ba tareda yana fahimtar abinda "akeyi acikin t.v ba.


Domin kusan duk hankalin sa yanaga hanyar da Humeeh tabi, yayinda jafi-jafi yana kallon agogon hannun shi ki'la yanada wani uzirine.


Umma ce' tafito daga kitchen zata hausama sai taga Abdul-jabbar zaune shikadai. Kallon sa tayi tace "a ah Kai kadai ne ina ita "Humaira take'? Cikin jin kunya tareda Sosa Kai yace "eh tunda tashiga Ciki bata fitoba,


Tace" a ah toh" inazuwa, yace toh" dai-dai Lokacin datake hawa steps din.


"Abangaren Humeeh kuwa bayan tagama tsayuwa, saita koma gefen gado ta zauna tareda zuba Uban tagumi, sai kace wadda akayiwa mutuwa.


Sai kuma tafara tambayar kanta take Waya ba Abdul-jabbar number ta?.. sannan Kuma Waya fada mashi cewan tadawo Yola bayan haka Kuma me yazo yi gurinta?...


_domin batayi tunanin cewa Hannah KO Haleeh zasu bashi no taba_ 


Toh Waya bashi no ta?..toh kodai wanene tabbas agurin bikin Hannah yasamu toh" kodai Doc... turo kofar Umma ne' yakatse mata tunani.


'Da sauri tamike tana kallon Umma, itama Umman kallon ta take', cikin mamakin domin taga tsoro karara 'afuskar ta. saboda haka sai tace "a ah waike yau  Lafiyar ki' kalau kuwa?...  Humeeh tace Lafiya lau. 


Umma Tace toh" Lafiya lau kike shine  kika bar "mututum, shikadai "afalo ko' ruwa baki'kai masaba. baki ta turo tareda cewa Umma *ABDUL-JABBAR* nefa.. Da sauri Umma tace' "Abdul-jabbar fakikace'?.. tace "eh Umma shine, tace "ikon Allah nikam 'aiban'ma ganeshi" ba dama nan garin yake aiki?. 


Humeeh tace "Oho niban saniba, toh" yanzu Kuma meya zoyi gurin ki?. toh" waima Waya fadamasa mundawo nan garin?.


 tace Umma nimafa "abinda nake tunayi kenan, kawai nidai yakira ni yace wai "infito gashi nan "aharabar gidan mu, toh" shinefa kikaga nafita da sauri toh" Kuma kodanaje sai kawai naganshi'. 


Umma tace toh" aisai kije kiji da meyazo Kuma, tace Umma nidai gaskiya ba.. Umma ta katse ta dacewa wuce kitafi nace' kije kiji da meyazo, hakan Humeeh tawuce' tana gun-guni.


_Nikam nace um-umhum su Humeeh anaso ana kawai market (kasuwa)_


Kitchen tanufa tire Da Cup tadauka, tareda bude fridge taciro lemon juice  da ever water masu sanyi, tajera "afarantin sannan tanufi gurinsa fuskarta ba walwala

yayinda kirjinta keta dukan uku-uku.


"A hankali tayi sallama Cikin yar siririyar murya ta, idanunshi na'akanta ya amsa sallaman, a hankali tajawo Dan karamin table gabanshi tadora faranti, sannan takoma nesada shi kadan ta zauna.


Batareda ta kalleshi' ba tace inawuni, shuru bai amsa ba tasake cewa inawuni nan ma shuru bai amsa ba, Dan haka sai tajuyo dasaurin do taga meyasa yaki amsa bai suwarta.


Caraf suka hada idanu dashi' tsawon yan mintoci suna kallon juna, can sai ta kauda Kai gefe tace bismillah kasha ruwa.


Cikin sanyin yace pls ataimaka azuba mani, "ahankali ta tashi tajeta zuba mashi Lemon juice din ta miki masa batareda ta kalle shiba,yayinda shi Kuma idanu shi suna kanta. 


Bayan tamika mashi saita komawa ta zauna, yayinda taketa cika tana batsewa fuskar nan nata babu walwala, ganin hakane yasa gaba daya Abdul-jabbar yadaburce yarasa  ta iyazai fara..


Har yagama shan lemon idanu shi nakanta' yayinda ita Kuma KO kallon inda yake batayi ba.


Wata dabarace tafado mashi wayar shi naga yaciro, yayi dailling number Mama tareda sata a handsfreen, yayi Sallama Mata amsa yace Mama nakira wayar ki' dazu Amma baki dagaba Lafiya?.. 


Tace" eh Lafiya lau bana kusada wayar ne,"ainagani toh" Kuma Dana kirana sai ban sameka ba, yace

Kila "inata gurin da ba

Network. tace Oho"  toh" yanzu ankaiku gurin daza kuyi "aiki?.. yace eh ankaimu Gibson jalo Barrack,  shuru tayi batace' komai ba, (da'alama ta tuna wani abune)  yace hello Mama  naji kinyi shuru l hope dai Lafiya?..


 Tace' a ah bakomai nadai tuna wani "Abune,' Da sauri yace' inafata dai abinda kika tuna baisa kinji ranki yabaci ba?.. kinsa bana

san bacin ranki yanasa naji duk hankali Na yatashi.


Tace a ah bakomai don haka ka kwantar DA hankalika, ALLAH  yabada sa'an abuda "akaje nema, yace Ameen tace yaushe zakaje kidansu takwara ta?..


_*kasan cewar tasan DA maganar zuwa wansa gurin Humaira*_


Yace Mama gani "agidansu"My Cool, tace masha'allah kasa mesu lafiya?..

yace Lafiya  lau suke", saidai kinsan wani abu?.. tace "a ah sai kafada yace' Mama My Cool tana fushi dani sosai ko" magana batayi maniba, saboda hakane yasa narasa ta "ina zanfara bata Hakuri. Kingani ma hada hararana takeyi pls Mama kiyi wani abun kinji?

Yakara she maganar cikeda shagwaba.


Cikin Mamaki jin 'abunda yafada Humeeh take kallon shi, yayinda shidin'ma idanun sa suna "akanta yana sakar mata Murmushi, aranta kuma take fadin ji yadda yake' magana kamar wani karamin yaro.


Murmushi Mama tayi har saida sauti shi yafito tacikin wayar, (Allah sarki Mama yanzu kam  tuni  tasaba da shangartar Abdul-jabbar, domin kuwa tun bayada yaji sauki shikenan sai  yake zuba mata shagwaba "iya san ranshi yayinda ita Kuma take biye mashi)


Tace toh" yanzu kaba takwarar tawa wayar,yace toh" tareda mikawa Humeeh wayar, idon shi cikin Nata takarba, yayinda take sakar masa' harara Wanda narasa gane kona meye..


"A hankali tace Mama 'inayi, Tace Lafiya lau takwarata ya "Ummanki' da yayanki" ya kuma karatu?..tace duk Lafiya  lau, tace toh" madallah. nan dai Mama tafada mata duk Abunda yafaru, tun daga yanda akai "aurenshi Da Lariya har zuwa rashin Lafiyar dayayi. 


Takara da cewa don ALLAH kiyi Hakuri kinji takwarata, duk wannan abun da yafaru nice' natilasta mashi Wanda ni kaina bansan yadda akai hakan tafaru ba


 Saidaga baya nagane cewa harda makircin Haj Jumma, kinga dayake "abun ba Saboda ALLAH akayi shiba sai gashi "DA SANNU" Allah yawarware komai.


Don haka "inasan kimance Da duk "abunda yafaru "abaya, domin nasan dake dashi kuna SON junanku" saboda haka Ku manta da baya Kufuskanci gaba,  Allah ya tabbatar Da Alkhairi tsakanin ku'

Kinji KO"?.. 


tace toh" Mama Insha'Allahu komai yawuce, tace toh" nagode ALLAH yaimuku Albarka

tace' ameen sai anjima sannan tamika mashi wayar.


Yakarba tareda cewa Mama "Ina SONKI' sosai ga kewarki tada meni dayawa, dariya tayi tace Kai kam shiriri tarka tayi yawa, daga jiya zuwa yau shine kayi kewata dayawa?..


 Yace' Allah kuwa Mama sainaji kamar nashekara bana kusa dake", shiyasa nake rokon Allah yabarni da Mamanta, Murmushi tayi tace' ka kulada kanka sannan Karin ga shan maganin ka'

"Akan lokaci, saboda nasan halinka sarai baka San shan magani.


Yace zanyi yadda kikace insha'allahu kice" ina gaida Baba Lami Tace toh" sai anjima ka gaida abokinka yace toh tareda kashe wayar.


Ya kalli Humeeh itama shi take kallo, sannan tace' kaci *DARAJAR* Mama,  Amma badan hakaba hmmm?... Yace ainasan dayau sunana SORRY KO?.. Kilama KO wannan ruwan da juice Umma ce' tasa kika kawo Mani Ko?..


 Bata bashi amsa ba saidai tace' Waya baka number Wayata, Waya fada maka mun dawo nan Yola than Waya baka Address Dina?..


Murmushi yayi yace duk wannan questions din ni kadai?.. Kai tadaga alamar "eh, yace "aikam yanzu kuwa zanbaki "amsar tambayar ki'.

Nan dai yafada mata duk abunda yafaru, harda gani ta dayayi yakara da cewa Dr I S g

"Abokina ne Kuma shine Dr na.


Murmushi tayi tace'

Nima ainagan ka, idanu yazaro Cikin Mamaki yace' shine kika kyaleni?.. tace' toh" mezance' maka?.. yace hmm My cool "inda kinsan halin Dana shiga adalilin SONKI' dabaki guje maniba.


Tace toh" aikain...da sauri ya katseta dacewa Shhhh! don't say anything, just we do what Mama say.

Aikam Cikin lokaci kankani suka balle Da firar Soyayya, tareda tambayar bayan rabuwa nan dai kowa yafadi wa Dan uwansa, halin da yashiga dalilin rashin dan'uwan sa.


 Sun'nutsun sosai acikin firar Soyayya harbasu" San lokaci yajasosai ba, saidai kawai sukaji "ana kiran sallar La'asar

Kallon juna sukai suna dariya.


Ya mike tareda kallon agogon hannun shi yace", kinga har lokaci yaja bansaniba bari natafi kar'anemeni 


Itama tamike tareda cewa toh" ya kalleta Cikin So da kauna yace' Kai my Cool  bako cewa sai anjima KO sai yaushe?.. kodai kindai SO Na sosai ne?..


Fuska tarufe da hannun ta tace' ah nikam aibanki kazauna muyita firaba, ya matsa kusada ita kadan yace' da gaske My Cool?. kaita daga alamar eh.


Murmushi yayi yayinda yakejin Sonta yan karuwa acikin Zuciyar shi, yace nima zanso haka saidai yanayi aikin'mune sai a Slow, amma karki damu insha'Allahu "DA SANNU" 

zamu kasance  tare, har abada kedai kiyi mana Addu'a kinji me SANYI TA?.. 


tace toh" insha'Allahu zanyi. yace' yauwa toh"muje kirakani,

Har gurin mata tarakashi sannan takoma Cikin gida,

Zuciyar ta cike DA farin Ciki yaugata ga Special dinta.


Umma ta kalleta tace' sai yanzu yatafi?. Cikin farin Ciki tace' "eh yatafi yace" yana gaida ke' tace' "Ina 'amsawa toh" meke tafedashi kuma?..


Nan tafada mata duk yanda sukai harda wayan Da sukai Da Mama, tace' Umma Bari naje nayi sallah,

batajira amsar Umma ba tanufi hanyar toilet.


Yayinda Umma tabi bayan "tada kallo tace Hmmm yaro" mankaza, Humaira ainasan haryanzu kinsan Yaron nan toh" Allah ya tabbatar Da Alkhairi tsakanin nace' 

Toh Ameen.



Dai-dai lokacin da Abdul-jabbar yake kokari fitadaga harabar gidan, toh" Kuma alokaci ne Abba ya kun'no hancin motar shi.


Da sauri Abdul-jabbar yasauke glass din motar shi, domin KO Ba'a fada masaba yasan cewa Abban' su" Humeeh Saboda Kama daya  hango.


Shima Abba  yasauke glass din motar yayi tareda tsurama Abdul-jabbar idanu, Cikin ladabi ya gaida Abba ya'amsa tareda cewa?..




💐Lufhat Ce💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page178-182


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)



*GAREKI MASOYIYAR "DA SANNU"*

*Wannan page naki ne ke kadai kiyi yadda kikeso dashi, MY HABITY SALMA USMAN gital group novel, inayi dake kamar yadda kikeyi Dani NAGODE SOSAI DA KAUNARKI AGARENI ALLAH YABAR ZUMINCI "DA SANNU" ALLAH ZAYA HADA FUSKOKIN MU LOVE U SO MUCH*💋💋💋



----------------------------------------

*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*


*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*

----------------------------------------


*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_.*



✍🏾




Wanene wannan?. SARAH tayi Murmushi  tareda cewa Lah my besty shinefa "Daddy mu,


Tace sorry My besty ban fada maki koni wacece bako?. toh kamar yadda kika sani sunana SARAH AHMED ABDUL-JABBAR, 


wayan nan najikin picture din sune' mahaifana wannan itace Mom dina Hajiya Maryam, wannan mahaifina Kuma shine governor jahar nan ayanzu dai nice babba agidan nan sai kan'nan Na gasunan,

wannan itace Esha baby wannan Kuma Zarah Mama,


 SARAH tayi dariya tace besty I hope kin gamsu, Cikin karfin hali Humeeh tace "eh Amma kinsan ban taba sanin cewa Dad dinku shine governor jahar nan ba?


Idanu SARAH tarazo Cikin mamaki tace Kai besty kina Cikin garin Yola kice bakisan governor kuba?.. Humeeh tace Allah ban sanshi ba saiyau dana ganshi ahoton, kinsan nafada maki bamu Dade Da dawowa nan garin ba,


SARAH tace' eh haka nefa, nan dai suka  Esha baby da  Zarah Mama suka gaida ita, dagan kuma suka nufi danning don cin Delusions din Da aka hadawa Humeeh,


Bayan su gama sai suka koma falo suka baje kolin fira, yayinda rabin ahankali ta yana kan wannan hoton, suna cikin fira sai Mom tafito Humeeh ta gaida ita harta tambaye ta ya Umman ta da Abban ta tace Lafiya lau suke,

 Sai bayan tayi sallah azahar sannan tayi shirin tafiya gida, 


Mom tayi mata kwatar abaya da turaruka DA mansha fawa masu asalin kyau da tsada, ta Kuma bata wasu turare da lifaya takaiwa Ummanta, tace toh  ta godiya.


Har gurin mota suka rakata saida sukaga fitarsu sannan suka koma Cikin gida. 


"A cikin mota kam Humeeh Sai tunani take tareda mamakin hoton datagani agidan su "Sarah, Wanda Sarah tace shine Daddy su"


Caf  aida badan  da "Sarah tace' Daddy su ba tabbas datace' shidin  Special dinta ne,


Hakadai take ta tunani DA Kuma mamaki, can dai wata zuciya tace toh waike mamakin mekike shin kin manta dacewa "anakama?


Da karfi tace' "eh hakane Kuma fa,

har saida Bala drive yajuyo yace ranki yadade kina magana ne? dasauri tace' a ah,


A ranta kuwa take fadino "Oh ni A'isha tunda nake aduniya bantaba ganin Kama irin haka ba, irin wannan kama haka sai kace irin identical twins, haka take tasake sake harsuka isa gida.


Suna shiga motar su Abdul-jabbar tana shigowa, Bayan Bala drive yayi parking sannan tafito tanufi cikin gida Cikin nutsuwa take takawa, har takusan shiga falon sataji ance Aminci Allah ya tabbata ga mai sanyin ZUCIYA ta.


Ahankali tajuyo suka hada idanu tareda sakarwa juna Murmushi, yauma sanye yake da kakinsu Na SOJOJI, ahankali yakaraso gurinta saikuma yadan hade fuska yace' yawo kigaje ko?


Kai ta girgiza alamar "a ah, yace toh' idan bayawo kikaje ba toh Ina kikaje saida ta turo Dan mitsitsin bakinta sannan tace Kai Special gidansu my besty Sarah fanaje shine naje yawo?


Dariya tabashi ganin yadda ta turo Dan bakin hada wani bata fuska, sai yace toh" shine Kuma hada su fushi?   bakin takara turowa tareda cewa toh" bakai bane kace naje yawo,


Yace toh' yi hakuri aibasan gidan su new besty mu kikaje ba, Kuma ni aiwasa mana nakeyi nasan my Cool bazata ringa zuwa yawoba, kodan kar wasu surinka kalle Mani beautiful face dinta KO? toh" Dan Saki fuskar mana yafadi yana Murmushi, itama Murmushi tayi Wanda har saida wushiryar ta tabaiyyana.


 A dai dai lokacin da Dalter boy yakaraso kasan cewar taresu kazo, nan dai  tashiga gaba suka bita abaya zuwa falo   Bayan sun zazzauna sannan suka gaisa,


Abdul-jabbar yace Abba fa?.. tace' yafita yece OK aikilan kafin mutafi yadawo tace "eh Ina sa ran haka insha'allahu,

Dalter boy yace wa  Abdul-jabbar shi Sam bagane Humaira ba wai yaga takara kyau da kiba, ita kam kunya yaka mata, don haka ta tashi tareda cewa tana zuwa tanufi sama.


Bayan tafita sai Dalter boy ya kalli Abdul-jabbar yace J boy, dama suma Humaira mutanan Yola ne kamar ka?..  Kafada yadaga yace I think KO" Kuma aiki yakawo Abbansu nan ba,


Dalter boy yace may be haka ne KO, aiki ya kwoshi KO Kuma "asalin kararsu kenan, dai-dai lokacin da Humeeh tadawo itada Umma,


Da sauri suka sauka daga kan kushin suka tsuguna suka gaida Umma, ta amsa fuskarta sake har tana tambayar su ya Aiki?. sukace' Lafiya lau tace toh madallah sannan ta koma sama,


Yayin Da Humeeh tashiga jera masu Delusion's din data shirya masa, bayan ta zuzzu bamasu', sai ta mike zata tafi da sauri Abdul-jabbar yace inazaki Kuma?


Cikin jin kunya tace Zan shiga daga cikine har kugama, yace "ah 'ai idan baki kusa Dani abincin bazaya tafiba, amma Idan ina kallon beautiful face dinki sai nakusan ciyen wannan garar batareda nasani ba KO bahaka ba?.. Dalter boy?.. yace ummh  dai-dai lokacin daya Cika bakin sa, da farfesun kayan ciki daya sha kayan yaji sai kamshi katashi.


Yace yauwa toh kinji so come and sit here yanuna mata kusada shi, kasan cewar a three site suka zauna Dan haka sai ta zauna dan'nisa dashi kadan,


Sunacin abinci suna zuba santi daga  Abdul-jabbar din har Dalter boy, tana tayimusu dariya harsuka gama sannan ta kwashe kayan takai kicin,

 

Bayan tadawo sannan Kuma suka cigaba da fira harda Dalter boy din, sundan taba fira sannan Dalter boy ya kalli agogon hannun sa, sannan yamike


 yace' 

J boy yakamata mutafi haka nan yanzu fa 3:40Pm kasan akwai aiki agaban mu, Humaira mun gode sai kuma gani Na biyu tace nikeda godiya, sai anjima yace OK sannan yafita yabarsu.


Abdul-jabbar yace my Cool gashi har yanzu Abba baidawo ba gashi Kuma muza mutafi Saboda akwai Abunda zamuyi tace toh shikenan, yace ba damuwa kinfa San yace' yana San magana dani..


Tace "eh haka yace so kutafi kawai idan yadawo sai nafada mashi kazo, yace toh' idan yadawo kitambayar mani shi lokacin dayake gida ya free sainazo KO?

tace toh" shikenan.


 Suna tafiya zata rakashi, tace' af my Special aina mata nafada maka, yace" me kenan fa?.. tace yau agidan su my besty Sarah kasan mena gani?.. yace "a ah saikin 'fada, my Cool, 


Tace wlh Daddy su my besty kamar kudaya dashi, jiyayi gabansa yafadi amma saiya basar yace' ah habadai?


Da sauri tace ALLAH  dakai dashi kamar irin  identical twins din'nan saida shi yafika kiba kadan, yace ikon Allah, tace ai inata mamaki harnace kilama Dan' uwanka ne shi? yace' a ah bansan shiba nida nake bako agarin, ke Kama ce ba kawai, tace haka nefa,Kuma fa shine governor garin nan, 


Yace ALLAH sarki dai-dai Lokacin Da suka isa gurin motar, saida taga tafiyar su sannan takoma Cikin gida.


Daga yadda yake Driving zaka fahimci gaba daya ransa abace yake, Saboda wani irin mugun gudu yakeyi akan titin kamar zaya tashi sama,


Ganin hakane yasa

Dalter boy yawaiga ya kalleshi tareda cewa  master duk wannan gudun dakakeyi iyakarmu fa Gibson barrack,


Juyowa yayin shima ya watsa mashi idanun sa dasuka kada sunayi jajir, yace I know sannan yamaida hakalinsa ga driving, Cikin bacin rai yace' kajiko  yanada mata dayara hakan yana nufin wato gaba daya yamanta damu",

 yashafemu "ababin RAYUWAR SA" Saboda baya kaunarmu ko? saidai kuma "DA SANNU" zayayi NADAMAR  "Abunda ya'aikata agaremu,


Dalter boy yace' master nifa ban fahimce kaba domin gaba daya maganar  adunkule kayita, don haka bansan inda kado saba, batareda daya kalleshi ba yace' aiba zaka gane ba ahaka harsuka isa barrack din.


*************

Yau Monday don haka  Humeeh yau sai 4:00pm  zasu dada makaranta  Saboda sunada lectures kuma zasuyi practical, zaune suke itada Sarah fitiwarsu kenan daga masallaci sunyi sallah azahar,


Sarah tace Kai! Kai!! kai!!! besty tashi mutafi ga mutunki nan Chan ya iso, muyi sauri kafin yashiga kinsan shiba sauki, Humeeh tace hakane fa dai-dai lokacin da suka nufi cikin holl din'da zasuyi lecture din,


 Sarah tace I hopo kinyi switch off din phone naki? Kinsan shi Dan ka'idane, Humeeh tace tundazu, dai-dai lokacin da suka shige cikin holl din.


Abdul-jabbar ne agaban Abba kasan cewar sunyi wayada Humeeh tace" masa Abba yana gida don hakane yaje,


Tun bayan dasuka gaisa da Abba kanshi ke kasa Saboda wani irin kunyar Abba yakeji, shikam Abba kallon Abdul-jabbar yake yayinda yake mamakin irin wannan Kama komai irin guda haka, hatta da kunbar hannun irin dayane.


Saida yagama  nazarin sannan yace samari ya sunanka kace'?...Cikin jin nauyi yace Abdul-jabbar, "ance daga Kaduna akaturoka nan kayi kos KO? yace "eh,


Abba yace "Ok shin  wanene mahaifinka  "a Kaduna?.. Abdul-jabbar jiyayi gabana yafadi yayinda yaji nutsuwar shi tana Neman kubce masa,


 Shi Sam baiyi tsammani wannan tambayar Abba zayayi masa ba, saida ya tattara natsuwarsa sannan yaba Abba amsa da cewa?..




💐Lufhat Ce💞

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page183-187


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)


----------------------------------------

*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*


*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*

----------------------------------------


*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_.*



✍🏾




"Alh ya'u nakaka shine mahaifina, kuri Abba yayiwa Abdul-jabbar da idanu yana kallon shi cikin matsananci mamaki, yace' kace' sunan ka Abdul-jabbar KO?.


Cikin jin nauyi yace "eh Abba sunana kenan, Abba yace toh" Abdul-jabbar "Inaso kafada Mani ainihin gaskiya wanene mahaifinka  "a cikin Kaduna?..


"A hankali Abdul-jabbar yasake cewa Alh ya'u nakaka shine mahaifina, Abba yace bashi bane mahaifika, gaban Abdul-jabbar ne yafadi yayi da yaji zufa tana karyomasa kai yadukar batareda yace' komai ba, Abba yace nasan Alh ya'u nakaka dan'shi daya ne Yusuf, Amma meyasa zakayi mani karya Abdul-jabbar?.


Cikin sanyi murya  yace Abba kayi hakuri wlh duk fadin Kaduna banida Ubanda yawuce Alh ya'u nakaka domin shi nasani,


Abba yace OK" toh" wacece Mahaifiyar ka?.. yace sunanta Hajiya A'isha, yace' bata fada maka  ko wanene mahaifin kaba?.. Da sauri yadago dakai yakalli Abba Wanda shima din kallon shi yake, dukar dakai kasa yayi batareda cewa komai ba,


 Abba yace shin Abdul-jabbar baka San "mahaifinka bane?.., sannan Kuma "mahaifiyar ka' bata fadamaka kowane shiba?.., Cikin karfin hali Abdul-jabbar yace Abba tafada mani saidai banasan nasan shi dama can bansan shiba don haka ko yanzu ma banasan nasanshi 


Shuru Abba yayi domin yanzu kam zargin dayakeyi akanshi yazama gaskiya, dama Abba tun ranan farko daya ga Abdul-jabbar yagane kosha waye, jiyayi wani irin Sanshi tareda matsananci tausayi shi, yaka mashi,


"A hankali Abba yace Abdul-jabbar meyasa baka San kasan shi waishin  bakasan cewa kowani Da' da' uba yake adoba?.. shi bakasan cewa duk matsayin mutun duk mulkinsa dazan akace yau bashida UBA toh"  darajarshi fa ragewa take a gurin mutane ,


Shin meyasa bakanan kasa kowaney mahaifinka?

"A hankali Abdul-jabbar yabude baki daniyar yayi magana, saikuma yakasa saka makon wani irin zafi dayaji ZUCIYAR shi nayi,

Kai yadago tareda yazubawa Abba idanu shi dasuka kada sukayi jajir,


Sai Kuma yasaki kuka tamkar karamin yaro kamar kuma ba SOJA ba, SOJAN ma wanda yake sanye uniform ajikinsa kuka yake mai ban tausayi, Wanda kanajinshi kasan 'andade "anasan ayishi ba'asamu damaba sai wannan lokaci,


Cikin kuku yace Abba tunban San kainaba nake san ganinshi, ZUCIYATA tarayu da KAUNAR shi saboda tunani nasan shi harsaida nakamuda CIWON ZUCIYA, wanda haryanzu inashan magani, Amma meyasa shi baya sona meyasa tun Ina cikin mahaifiya ta yatsaneni? 


Abba shiyasa nima yanzu bana San ganin shi tunda shima baya sona, pls Abba Ina son Humaira kar kace bazaka bani auren ta ba Saboda naka sance banida mahaifi sai Uban riko,


"Ahankali Abba tadaga hannu sama yanatafan kwarara Addu'a, saida yayi Addu'a sosan sannan yasauke hannu tareda karasa dafadin ALLAH Kaine maji rokon bayinka ALLAH mun gode maka daka amsa Addu'a mu,

  

Cikin sanyi murya yace zonan kusa dani Abdul-jabbar "aikam da sassarfa Abdul-jabbar yakarasa gurin sa, Abba yace haba SOJA sukutun yake kuka haka kamar MACE ayya kuwa SOJAN NE?.. Kai SOJAN NEFA tunda gashinan harda kakinsu Ajikin shi,


Cikin zalaya Abba yaci gaba da cewa

Kai Kuma fa shi din JARUMI NE KO sunan shi kawai abun kallo ne, toh" koya manta da hakan ne"?.hmm Lallai nasan "DA SANNU" zaya gane cewa shinefa

 ABDUL-JABBAR jikan "ABDUL-JABBAR Da "ABDUL-JALAL Daga "AHMED DA A'ISHA" Addan MAHAMUD Angon "AISHA HUMAIRA insha'allahu,


Cikin mamaki   Abdul-jabbar yasaki bakida hanci yana kallon Abba, dayake tafaman doka masa murmushi, cikin rada Abba yace kayi sauri kashare hawayen nan kafin Humaira tazo tagani,


tace tafasa auran tunda kaidin RAggo ne kana sanye da kakin SOJA amma kana kuka kamar mace, Abba yakarashe maganar tareda rike haba,


Da sauri yashare hawayen tareda yin murmushi  sannan ya dagoda Kai yatsurawa Abba idanu, shisai yanzu ma yagano kamar DA sukeyi DA Mama wani irin dadine yaji yaratsashi,


"Ahankali Abdul-jabbar yace KAWU NA Mahamud Abba yace na'am ABDUL-JABBAR da sauri yamike ya rungume Abba shima rungume shi yayi cikin tsananin farin cikin Abdul-jabbar yace Abba ya'aikai kaganeni?..


Abba yace' haba Abdul-jabber "ai tun ranan farko danaganka gane cewa Kaidin jinina ne, balle kuma ko makaho yalalubaka zaya gane kokai Dan  waye, baki Abdul-jabber  yaturo kamar karamin yaro yace Abba toh" nidin Dan waye?..


 Dariya Abba yayi yace' Abdul-jabbar kenan "ai kobaka taba sanin shiba nasan kaji Labarin shi gurin Maman ka Kuma aikaji dazu nafadi sunan shi akirarin danai maka KO?.. 


yace Abba toh nikam bashi bane "Babana, DA sauri yace kul naji kasake jin kalman nan tafito daga bakin ka, toh" idan bashi bane "Babanka toh" wanene Baban Ka?.. cikin sanyin murya yace' Abba toh" Ai shidin ne baya SONA  Abba yace Waya fada maka baya son ko?.


 Nan dai Abba yafada masa duk "abinda yafaru Wanda "Aina'u ce duk keda sahannu 'afaruwar komai, jiyayi SON mahaifinsa yasake kamashi amma fa duk da hakanan yanajin Dan haushin Sa kadan, narashin BIN CIKEN da baiyi ba kawai ya yanke hukunci.


Abba ya kalli Abdul-jabbar yace toh" yanzu fada mani Address "inda Adda ta take dama yau zantafi  Kaduna Saboda wasu kayana dasuka fito tacan, Saboda haka yau agidan Adda ta Zan sauka insha'allahu, 


dariya Abdul-jabbar yayi yace Abba Ka tsaya mana nakara ganinka da kyau,

Shima dariya yayi yace "a ah aikai kagan'ni Adda ta yarage tagani, naganta Kuma yaudin nan zamu haduda izinin Allah,


Yamike yana cewa Bari nakira Umman taku kugaisa KO?... Abdul-jabbar yace toh" Abba yana gaba Umma tabiye da shi'abaya, tana fadin ikon Allah Ashema shin din Dan gida ne nan dai suka gaisa Da Umma, yayida Abdul-jabbar yasaki jikin shi da sun har suka danyi fira kadan,


Sannan yace zaya koma gurin aiki Abba yace toh" shikenan, shima kamar yadda yafada masa insha'Allahu idan ma yasamu yadda yakeso zaya taho da Addan, yace toh" shikenan sai yadawo nan dai sukai Sallama yatafi.


Yau sai karfe 4:00Pm su Humeeh suka tashi daga school don haka agajiye ta isa gida, koda taleka dakin Umma tana Sallah don haka itama sai tashiga wanka tayi sallah sannan tanufi kichin don wata irin yinwa takeji,


Saida taci abinci tayi nak sannan tanufi dakin Umma tana cewa sannu da gida Ummata, tace yauwa ake za'ayiwa sannu sai yanzu kuka tashi? Tace' Hmm kedai Umma sai yanzu fa, toh" Sannun Ku' yauwa Umma Ina Abba Na?


Abbanki kam yana Kaduna da sauri Tace' Kaduna Kuma? Umma Lafiya tace' Lafiya lau nan dai tafada mata komai gameda Abdul-jabbar, cikin mamaki tace Umma yanzu Abdul-jabbar Dan Uwanane?.. tace' najini kuwa,


Wani irin dadi taji yaratsata da sauri ta tashi tanufi dakin ta, yayinda Umma tabi bayan ta DA kallo tana murmushi, koda ta isa daki wayar ta taciro ajaka takunna wadda ta kasheta tun lokacin da zasu shiga lecture,


Kiran Abdul-jabbar ne first Da yafara shigowa dariya tayi Sannan tadaga tareda sa wayar a handsfreen, jinai yace' haba my cool wannan wani irin "abune haka yaza'ai ki kashi waya tun dazu inata faman nema layinki wai switch off Lafiya?..


tace ah Malam aikai Zan tambaya Lafiya kakirani sai faman yimani ihu kakeyi, alhalin ni bansan komai wanene ba Kai wannan number warron number ce', don niban mataba ganinta ba sai yau Saboda haka sai anjim, 


Da sauri yakatse tada cewa ke! Ninefa Abdul-jabbar  fuska tayamutse kamar yana ganinta tace' waye Kuma haka nan?.. jitayi Ciki sarkewar murya yace' Special dinki nefa, harza tace Oho sai tafasa sai Kuma ta kyalkyace da dariya,


"Ahankali yasake ajiyar zuciya tareda cewa haba my Cool wannan aisaikisa ZUCIYAR ta tarwatse, ke bakisan haryanzu akwai sauran gyanbo acikinta ba?.. cikin dariya tace Sorry my Special one banyi niyar bata maka rai ba,


tace kasa meye yace a ah saikin fada tace' wannan shine karona farka arayuwata danai wasada abokin wasana, yace "OK toh" ni abokin wasanki ne? tace "eh mana, yace eyyee lallai ma yarinyar nan waya fada maki?.. tace' ah tun yaushe naji komai, yace haka ne Abunda kikaji, Kai no wonder nafaye Son ki dayawa Ashe kedin jininace,


Tace toh" ainima "inason kadayawa harfada zazzabi saida nayi,

yace Hmmm Son Danake yimuku kedai Daddy yayi yawa sosai tunda har saida ya haifarmani DA ciwon ZUCIYA,


tace toh" Amma meyasa danace ko kasan Daddy su my besty sai kace Kai baka sanshi ba, yace toh" mezan ce maki my Cool bakisan Abunda mutumin nan yai mana bane shiyasa,


Da sauri tace kodai meyayi maka shi din dai ne mahaifinka  

Don haka Ka gyara kalaman ka, so fadin munanan kalamai ga iyaye badabi'abace me kyau ga mutumin kirki irin ka, shi lamari duniya DA kagani idan Mutum yabi ahankali toh" "DA SANNU" Allah zaya warware masa komai,


Nan dai tayi tamasa magana gani masu ratsa zuciya Wanda yaji kaunarta takarashiga aranshi, Daga nan Kuma sai sukacigaba da tsokanar junansu me cikeda  Soyayya.


*Kaduna*

*************

Alh ya'u nakaka ya kalli Abba bayan sun gama gaisawa sai yace" bawan Allah ban bangane kaba fa, Abba yai murmushi tareda cewa ainasan baka ganeni ba Amma dai aikasan Haj A'isha  Mahaifiyar Abdul-jabbar KO?

Cikin mamaki yace'




💞Lufhat Ce💐

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page188-192


Second to the last

page

          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)


_*Slm Masoya wannan littafin kuyi hakuri da sunan shi za yakare Ina nufin "DA SANNU" zamuga karshen shi Lafiya Dani daku insha'Allahu nagode sosai da kawar Ku*._



----------------------------------------

*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*


*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*

----------------------------------------


*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_.*



✍🏾




"Niko nasan ta inafata dai lafiya?.. Abba yace'l lafiya lau, sunana Alh Mahamud ni mutumin  Yola ne "amma na taba zama agarin nan idan tabayin  manager Bank a G T ada, amma yanzu banayi nakoma can Yola,


kuma ni kanine "agurin Hajiya "A'isha mundade muna Neman ta, Allah baisa mungan taba sai yaune cikin gudurar ubangiji mukasamu Labarin inda take agurin danta, Abdul-jabbar toh" shine nazo natafi da ita idan bada muwa?..


Tunda Abba yafara magana Alh ya'u nakaka yake Murmushi farin ciki najin wannan daddadan labari, yace ikon Allah dama duk abunda kaga yayi farko toh" idan akayi hakuri  "DA SANNU" za'aga karshen shi,


Abba yace'wannan haka yake nan dai Abba yabashi labari "abunda yafito da Mama gida, Alh ya'u yace kai wasu matan sai "ahankali kaji irin wannan makirci haka, kai Allah kayi mana tsari da shaidanun mata, ameen


 Abba yace Ameen nan dai shima Alh ya'un yabashi Labarin tun lokacin daya hadu dasu har zuwa yanzu, Abba yaita godiya Alh ya'u yace bakomai aiyiwa kai sannan yakira Hajiya karima matar shi suka gaisa,


Bayan komai yalafa sai Alh ya'u yakira Y Y K awaya yace' masa yajeya dauko masa "Mama yakawo ta nan gidan shi yanasan ganin da, Y Y k yace' toh".


Dagan suka cigaba cigaba da fira har lokacin da Y Y k shida Mama suka iso da Sallama suka shiga falon, bayan  sun gaisa sai Mama tace" Alh gani yusufa yace kana son ganina nace toh" Allah yasa Lafiya?..


Yace" lafiya lau dama wannan bawan ALLAH ne yazo gurin ki, yafada yananu namata inda Abba yake zaune yana tafaman doka Murmushi, kuri tayi mashi da idanu tabbas baza taba manta wa da wannan kyakkyawa Murmushi ga fuskar dan'uwanta duk dadai yanzu  yazama babban Mutum. 


da sauri ta tanufi inda yake dai-dai shima yataso Hannun shi tareke tareda cewa wannan MADO name, yace" nine ADDA rungume juna sukayi suna farin cikin ganin juna, Mama kam harda kuka tayi najin dadin ganin dan'uwanta, yace' Adda na ashe Zan sake ganin ki?..


Tace mado Na gashi Allah ya hada mu yace' haka ne toh" Allah mungode maka, tace Allah "abun godiya kallon shi take cike da mamaki tace madona kazama babban Mutum, 


dariya yayi yace' Addana kenan niko sainaga kamar bake kika haifi wannan santalelen saurayin nan Abdul-jabbar ba,

tace hmmm kana nandai yadda nasanka da tsokana  bakasan yanzu kagirma bako?..


Dariya yayi tareda sake rike Hannun ta yace" a ah idan Ina kusadake nidin yarone harma dai idan kince MADO na,  yakara she magana yana dariya itama dariyar takeyi, nan dai sukan taba fira yaushe gamo sannan Abba yace yanason yatafida Mama gidan Malam su gaisa.


Alh ya'u yace idan bada muwa shima zayaje sugai sa, Abba yace badamuwa, nandai suka dunguma sai   gidan Malam, bayan "angama gaggaiwa sai Abba yaiwa Mlm bayanin komai tareda nunamasa Mama,


Sosai Mlm yayi Fari Ciki tareda sawa Alh ya'u nakaka Albarka dagan kuma sai aka ajiye maganar lafiya Yola gobe insha'Allahu.


   ********""""*********

Washe gari karfe goma nasafe jirgin su yatashi zuwa Yola, Abba Alh ya'u nakaka Mlm Hajiya karima  gwaggo da Y Y k, Abba da Alh ya'u nakaka sune suka dauki nauyin lafiyar , dan Kari kaji masu abida abunsu kurada kallabin kitse,


_*To mukan saidai muce "asauka Lafiya*._


💐💐💞💞💐💐

Sun isa Yola lafiya Abba ne yakira bala direba yazo yadauke su, direct gidan Baba gen yace" bala yakaisu, bayan yasauke su sai yace yaje yadauko Umma da Humeeh kasan cewar yau basuda lecture,


Labari Abdul-jabbar dan"uwanta kuwa ne tuni ta fadawa mutanan ta, watoh Hannah da Haleeh

Sarah kuwa tace sai sun hadu gidan baba gen,


*GIDAN BABA GENR*

 Baba gen da Hajiya Binta suna zaune a tamfareren falonsu" suna fira sai jin Sallama sukai,


Abba yana rikeda hannun Mama suka shiga falon ahankali ya karasa gurinsu gaba daya dashida Mama suka tsugunna gabansu, yayinda sukuma kallon sukawai suke fukarsu cikeda mamaki, Abba yace' Baba Hajiya yau ga Adda A'isha Allah ya baiyyana mana ita,


Da sauri Baba gen yace Masha'allah Allah mungode maka, yayinda ita kuma  Hajiya Binta ta rungume ta tareda sakin kukan farin Cikin tana cewa Allah nagode maka,  daka baiyyana Mani Amanar daka bani dama "ance mahakurci mawadaci, gashi damukayi hakuri muka barwa Allah komai gashi "DA SANNU" Allah ya baiyyana ta.


Nan dai akai ta farin Ciki harda Baba engr  da Matarsa kasan cewar Baba gen yace akira shi, sai da

 komai yalafa  sannan Abba yagabatar da Alh ya'u nakaka da matar sa tareda dan shi Yusuf, sune suka taimakawa Mama tareda danta Abdul-jabbar, sannan yagatarda Malam Garba da gwaggo sune sarakan shi.


Aikam nan su Baba engr sukai tazuba godiya tareda samashi Albarka, Alh ya'u wlh bakomai ai anzama daya,  bayan komai yalafa sai matar Baba engr tace' A'isha toh" Inashi maigidan nawa banga shiba?..


shuru tayi tareda dukarda kai kasa  Saboda kunya irin ta fulani, Abba yayi dariya tareda cewa Hajiya aikam Santalelen maigida yana nan  SOJA amma sai kin bada toshi Zaki ganshi, tace au haka ne?.. Cikin wasa yace' "eh Saboda haka kawo nikuma  yanzu naje nataho dashi.


Da sauri Baba engr yace Masha'allah Mahamud yimaza kaje kataho Mani da ABOKINA, Abba yace toh" yayinda matar Baba engr ta sake cewa yauwa jeka tahodashi, idan naga yayi Mani kagasai nabada toshi dakyau idan kuma baiyimaniba sai akai kasuwa, tafada tana dariya gabadaya falonma  dariya akayi, yayinda Abba yamike tanufi hanyar fita yana cewa sosai kuwa zayayi maki kilama kibar Baba engr ki dauke shi.


Yana fita sai gasu Humeeh sun iso key ya amsa Hannun bala direban yace' su shiga Ciki zayaje yatahoda Abdul-jabbar, sukace toh tareda shiga Cikin gidan.


Abba bai tsaya ko'inaba sai Gibson barrack, bai samu matsalaba gurin tahowada Abdul-jabbar, suna tafiya suna fira yayinda Abdul-jabbar kejansu Abba kuma yana gefen shi yayinda Dalter boy yake baya kasan cewar harda shi.


Abba yana fadawa Abdul-jabbar cewa?.. tareda su "Alh ya'u nakaka suka zo, harda abokin shi "Y Y K, Abdul-jabbar yaji dadin cewa harda Y Y k akazo, yace Abba duk family sun hadune?..


Basu naduba tukun amma zasu hadun idan ka'isa, yace shi kam nasan yazo KO?.. Abba yace waye shikuma?...baki yaturo tareda cewa shi din mana Daddy su" bata rai Abba yayi yace ayya Abdul-jabbar yanzu Daddy nakane shi Ku.a Daddy wasu, Ai kafin yazama Daddy wasu" Daddy ka yafara zama, yace' Abba toh" aisu" yakeso nibaya sona shiyasa nace sh....


Kasa karasa wa yayi saka makon kallon Da Abba ya watsa masa tareda cewa baza kadaina bako?.. da sauri yace' yi hakuri Abba na daina, kyale shi Abba yayi baice komai, can sai yace Abba kafada Mani yadda "Baba gen da "Baba eng suka banbanta,


 Saboda "Mama tace mun "sunyi Kama dajuna sosai wai harkaya irin daya suke sakawa, Saboda tsananin kamar su bakowa yake gane su ba, haryanzu mada suka tsufa kaya iri daya suke sakawa.?..


Gaskiya nikuma sona ke nagane su", dakaina batareda "annuna munsu ba.

Dariya Abba yayi tareda cewa?...




💞Lufhat ce💐

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞

  DA SANNU

💞💞💞💐💐

💐💐💐💞💞


   page193-200


          END


          NA


💞AMEENAT UMAR💐 FARUQ

         OR

       (MEENAT)


Alhamdullah!

Alhamdullah!!

Alhamdullah!!!  nagode ALLAH daya bani ikon fara littafin nan lafiya, ya kuma bani ikon gamashi lafiya Allah kabani Ladan Abunda Na rubuta,tareda wayanda suka karanta inda kumanayi kuskure kayafe Mani, tareda wayanda suka karanta Ameen.


----------------------------------------

*_®PEN WRITERS ASSOCIATION_*


*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*

----------------------------------------


*_only exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_.*



✍🏾



"Tabbas har yanzu ma kaya iri daya su" kesawa, don haka Bari nafada maka yadda zaka gane su  kaga "Baba gen baya dariya saidai yanada yawan murmushi, kuma bayada yawan magana,


Shikuma Baba engr yanada magana sosai sannan yanada yawan dariya, nan dai Abba yai tafada mashi yadda suke har suka isa gidan da taimakon Abba tunda baisa gida ba.


Abdul-jabbar yanata Mamaki wannan tangamemen gida haka kusan unguwa guda, haka dai suka shiga Cikin gidan security kuwa gasu nan birjek, bai tashi tsinkewa ba saida suka shiga tamfatsetsen falon dayaji kayan more rayuwa wai ran kashi aljannar duniya kenan.


Cike falon yake Da mutane kasan cewar bayan tafiyar Abba sai Baba engr yasa Waya, yana takiran ya'ya'da jikoki suzo akwai family mitin Saboda haka falon cike yake wasu mabasu isoba tukun,


Abun Mamaki shine saida Baba engr yagama kiran kowa Sannan yakira Daddy, yace yazo shida iyalinsa yanason ganin su yanzu-yanzu.


Shikam Abdul-jabbar gaba daya daburcewa yayi Saboda ganin yawan mutane haka, gashi kuma duk ahankalin su' yana gurinshi.


gurin Y Y k yanufa ya zauna tareda cewa Kai Nawa irin wannan kollo "aisaina buga tuntube nafadi, kallesu fa duk nikadai suke kallo,  Cikin rada yace' ka kallesu" da kyau mana meka gani acikin kwayar idanun su?...


"Ahankali ya kalle su" ba'abunda yagani akwayar idanunsu" sai zallar kaunarshi gawani lallausan Murmushi dayake tashi "a fuskokinsu", jikin shi ne yai sanyi "aranshi kuwa fadi yake duk wayannan di yan'uwana ne?.. Oh ashe ni Abdul-jabbar dandangine haka, jiyayi wani irin kaunarsu yadarsu a zuciyar shi Cikin kan-kai lokaci.


"Ahankali yamaida kallon shi gasu" Baba engr aikam sai yaga Baba gen yanata Murmushi fuskarsa cikeda farinciki naganin wannan santalele Saurayi wai jikansa ne, kuma magajin shi kai aidole yai farinciki tareda godiya da wannan kyauta da Allah yabasu.


 Shima Baba engr dayake amsa waya Murmushi yake tareda yiwa Abdul-jabbar nuni da hannu alamar yazo garesu', "aikam da sauri Abdul-jabbar yatashi jikin shi har yana rawa yanufi gurinsu domin jin kaunar su yakeyi har cikin jininshi, tsakiyarsu yazauna ya kalli Baba gen haryanzu Murmushi yake sai ya kalli Baba engr shima Murmushi yake amma sai yamika wa Abdul-jabbar hannun shi yakama ya kalli Baba gen  shima hannun yamika masa yakama yahada hannu Baba engr dan baba gen ya rungume "akirjinshi wani irin kaunar su yaji har cikin jinshi.


 Sai kuma yasaki kuka Wanda Ina kyauta ta zaton nafarinciki ne, dai-dai lokacin da Baba engr yagama amsa wayar tareda dora hannushi guda saman kafadar Abdul-jabbar Sannan Cikin zoyala yace kai "ashema wannan SOJAN raggo ne ban saniba, Cikin kuka yace "eh din "aikam gabada ya falon "akasa dariya, juyawa yayi yakalli Baba gen Cikin kuka me kunshe da farin Ciki yace toh Kai kuma baba gen mekace?.. Cikin Murmushi yace toh" ni mezan ce' tunda Na gashi magajin Nawa raggo ne, yace' au haka neko?..  to shikenan dama bakusanmu shiyasa Ku kabarmu munata faman shan wahala badan Allah yasa Baban abokin Na yataimake muba dashikenan hakaza kubarmu mukare rayuwar mu acikin wahala nida mama Na KO?... 


da sauri suka rungume shi suna cewa kayi hakuri duk abunda kaga yasamu bawa toh dama can Allah yatsara hakan sai yasa meshi kuma wani lokaci jaraba mutun ubangiji yakeyi idan ka kwantar Da hankalin ka saikaga "DA SANNU kacinye jarabawar kuma dakace bamusan ka waya  fada maka bama  sonka?.. Baba engr yace' kalli can ahankali yadaga Kai yakalli tulin jama'ar dake falon Cikin sanyi murya yace' nagansu, yace toh dukkan sun masoyan Kane wasu" mabasu zoba tukun saboda haka duk muna sonka, yace nima Ina sonku.


Nan Dai Baba engr yayi tafada masa irin yadda suke sanshi daga nan kuma yakira Adda Uwa yace tayita nuna masa kowa da kuma yadda suke", "ahankali Abdul-jabbar yagane kowa yawancinsu duk abokan wasa shine aikam sunata zolayar shi bayan komai yalafa sai yakoma kusada Y Y k yanzu. dai-dai lokacin da Daddy yashiga falon da Sallama iyalansa nabiye dashi, gurin su baba yanufa yazube tareda gaidasu suma iyalain shi haka sukayi, Sarah ce itada Esha baby da Zarah Mama suka nufi kusada Humeeh suka zauna Sarah  cikin rada tace ke! my besty lafiya naga all family here?..


tace Lafiya lau za'yi mitin ne tace OK dai-dai lokacin da idanun ta yasauka akan Abdul-jabbar, Cikin tsoro tace' my besty waye wancan din mai kamada Daddy mu?.. Esha baby tace' eh fa, Cikin rada tace you brother Abdul-jabbar da sauri tace' don Allah?.. tace Allah kuwa aikam da sauri suka tashi dukkan su Esha baby da Zarah Mama suka nufi guri Abdul-jabbar suka bufe gaban shi tareda Kama hannun shi sukace da gaske Kai  Hamman mune?.. inaka shiga munata son ganin ka amma bamu ganka bai sai kuma suka fashe da kuka sukace  Hamman mu muna sonka. 


kallon su yake yayinda yaji kaunar su" takamashi rungume su yayi shima kukan yake yace, nima inasanku sosai inata neman inda yan'uwana suke amma bansan inda suke ba sai yau Allah yahadani rabin jikina Ina sonku sosai, Sarah tace pls Hamman karka sake tafiya kabarmu kaji?.. yace "a ah ba'inda zayi Ina nan tareda Ku duk dacewa Daddy Ku baya sona, Cikin tsoro esha tace kai! Hamman mu Waya fada maka cewar Dadd'mu baya sonka?..Cikin Dan jin haushi yace ba shine yakori Mama Na tun'ina Cikin Ciki kinga hakan yana nufi baya son muke nanko?.. Kai take girgizawa alamar a ah.


dai-dai lokacin da Daddy yakaraso gurinsu ya zauna idanu suka hada shida Abdul-jabbar Daddy jiyayi son Dan'nashi yana ratsashi shima Abdul-jabbar din haka yaji kaunar Daddy yana shi garshi, Abdul-jabbar ne yakauda Kai gefe hannun Daddy yasa yajujo da fuskar shi tareda cewa my Son baka son ganina ne?...Cikin kuka yace' Daddy toh' aikaine bakas....bai bari ya karasa ba yajawo shi ya rungume shi yana kuka tareda cewa Ina Sonka my son kuyafe Mani abunda nayi maku duk sharri makirci Aina'une, nan dai Daddy yabashi hakuri tareda zuwa gurin mama itama yabata hakuri tace bakomai dama haka Allah yatsara hakan sai yafaru,

harda Aina'uma tabasu hakuri sai kukan nadama takeyi, gatadai Cikin dauka amma duk tare me ta lalace, nikam nace alhakine.


Bayan komai yalafa sai Mlm yayitayi nasiha mai kashe jiki musamman ma "akan mata dabasu San zama da kishiyoyin su Lafiya,

har Mlm zaya rufe taronda Addu'a sai Daddy yace yanane man alfarma da amayar da  auren shi da A'isha aikam bawani bata lokaci mlm yafadi sadaki Daddy yabayar aka daura aure,


bayan "angama daurin auren sai Abdul-jabbar yace Daddy wani abunake so kayi Mani...yace fadi abunda ka keso indai baifi karfina toh" zanyi maka shi ko mene ne?... yace aure nakeso dariya akayi falon Daddy yace Abu me sauki fadi komata Nawa nakeso, yace biyu ne gasu can yanuna inda Hajiyar Baba gen Da Hajiyar Baba engr, dariya akasakeyi yayinda Daddy yakama kun'nan shi yace my Son iyayan Nawa zaka aura?.. yace ahhhh Daddy wasa nake sudin aitsofine kaga wanda nakeso can yanuna inda Humeeh take zaune aikam da sauri taboye fuskarta "abayan Sarah,


Daddy yace Kai  masha'allah "aikam ba'abar gurinba saida da "akasa ranan bukin Abdul-jabbar da Humeeh wata daya, sannan Mlm yarufe taro DA Addu'a

Washegari tunda safe jirgin su mlm yatashi zuwa Kaduna.


💐💐💐

Bayan kwana biyu Mama tare agidan Daddy "aranan ne kuma Daddy yahada gagarumar walima na farin cikin baiyyanar Danshi, walimar kam manyamayan mutane sun halatta sosai "ankuma gama lafiya inda Abdul-jabbar yasamu kyau gudu ka sosai.


Haka rayuwa yaitatafiya Abdul-jabbar da Mama basuda sauran matsala yanzu duk yasan gidajen yan'uwansa yana kuma cigaba da aikin sa, Soyayya kuma shida Humeeh sai abunda yai gaba, "akwana antashi bawuya "agurin Allah gashi yausauran sati daya bukinsu.


Su Sarah "ankasa zaune "ankasa tsaye bukin nasu da kawa da yaya yaune suka fara event, zaune suke afalon gidan Baba gen kasan cewar nan za'a sa Amarya lalle Humeeh Sarah Esha Zarah da kuma, Haleeh da Hannah dayake duk sunzo saikuma sauran wasu yammata daga Cikin family din fira suke tayi irin na'amare.


"A yaune dubun mutane suka shaida  auren ABDUL-JABBAR AHMED ABDUL-JABBAR DA amaryarshi A'ISHA HUMAIRA MAHAMUD, masha'allah Allah yabada zaman Lafiya.


"Anhada lafiyayyan dinner awani kayatacce gurin mesuna komesment dinar tahadu iyakar haduwa angoda Amarya sunyi kyau harsun gaji, abokan angodana Amarya ma sunyi kyau sosai kasan cewar sunyi ankonsu mai asalin kyau, haka nandai aka gama dinner lafiya.


Zaune suke sai faman shakiyanci suke irin na kawayan "amarya saijin Sallama angon'nai sukaji "aikam sai sukayi shuru, Humeeh kam da sauri tarufe fukada mayafi Bayan sun shigo "angaisa akataba Dan barkwanci Sannan M B yayimusu nasiha Y Y k yai Addu'a Sannan sukayi masu Sallam


"aikam da sauri Humeeh tarike Hannah da Haleeh sai tafara kuka wai karsu tafi suma kukan suke, Doctor S I g ne yakallesu yai dariya yace wato tarihi zaya maimaita kanshi kenan KO?.. kallon shi Haleeh tayi tareda turo baki Dalter boy yace a ah Barau sunyi kukan rabuwa kasa yanzu idan suka rabu kafin su gajuna sai andade..


Abdul-jabbar yace' eh fa haka ne Nan dai Sukai talallashi su har sukayi shuru sannan sukayi masu Sallama suka tafi, suka bar Amarya da Ango don yace bazaya rakasu ba tunda suna dayawa, suma sukace "eh sunyafe yazauna yaci amarcisa.


_*toh" ainima barin Amarya DA Ango zanyi suci amarcisu lafiya*_


**********

"DA SANNU" rayuwa tacigabada tafiya Abdul-jabbar yagama kos dinshi Cikin sa'a kuma su kabar shi nan Yola din don haka Soyayyar su sukeyi shida Humeeh, yayida itama tacigaba dazuwa makaranta abunta.


*********

*BAYAN WATA TARA*

Humeeh ce" nahango sanye da doguwar rigar shadda me ruwan toka, dinkin aikin wutane gaskiya shaddan yamata kyau sosai idanba kasanta ba toh" balallai bane kallo guda kagane ta, kasan cewar tayi kiba tabude saka makon Cikin da take dauke dashi.


 "ahankali take saukowa daga bene da koma "ace kyar Da kyar, kasan cewar cikin yashiga watan haihu steps biyu ta taka zata ta kana uku kenan, saiga Abdul-jabbar yashigo sanyeda uniform din SOJOJI,

da sauri najiyace tsaya daganan aikam cak tatsaya dasassarfa yahau benan yace bakijiko?..my Cool.


Baki ta turo tareda cewa toh" nina ganijene yace' toh" basai kikiraniba?..tace toh" Sorry, daukanta yayi cak yasauke takasa tareda Doratasaman kushin yafara manmatsa mata kafafunta dasuka dan kunbura.


Can saitaji matar yaya daure dakuma ba harda kunkuru da sauri tace Innalillahi, yace mene?.dai-dai lokacin da taji wani irin ciwo aikam tuni tasaki kuka tareda cewa wayyo Umma,Cikin tsoro yace me yafaru tace marata da sauri ya dauke ta sai mota "asibiti Cikin ikon Allah tahaifi tagwaye duk mata, kyakkyawai dasu masu kamada Babansu"


Zokaga murna gurin Abdul-jabbar nanda nan yafarakiran mutane yanafada musu Cikin lokaci kankani akacika asibiti.


***********

Rana yara sukaci sunan su" wato Hassana DA Hussaina, suna yakayatu mature kayatuwa mutanan ta sunzo Hannah da goyon danta, namiji Haleeh kuma da Cikin tana "aure wani laccara haka nan akaci suna akawatse taro lafiya alamar megego da yaranta toh" mu masaimuce ALLAH yaraya HASSANA DA HUSSAINA.



_Masha'allah_


Anan 


Nakawo karshen wannan littafi me suna DA SANNU.

kuskuren DA nayi ALLAH kayafe Mani.




💐Lufhat ce💐


adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *