Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Wednesday, January 20, 2021

RAYUWAR-WASU HAUSA NOVELS

adsense here

RAYUWAR-WASU HAUSA NOVELS

 [3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


```NA........ ✍🏼```

*UⓂmiey Xeey Abakson*



*Assalamu Alaikum  wa rahmatullahi wa barakatuh.... I'm  back again💃🏻,  Banyi wannan novel  din dancin zarafin wani ko wata ba.. Idan yazo daidai da halinki to ki gyara...*


       _•••°°°Devoted  to......°°°•••._

*Miss Zarah Mansur😍*

     ```I'M  PROUD OF YOU MY DEAR... I LOVE YOU SO MUCH sweety, KODA DUKA LITTAFIN SUNANKI ZAN AMBATO BAN BIYAKI BA```


    *❣Bilkisu bk* wannan page din nakine ke kadai,  I'm truely blessed  to have you in my life,  Ina matukar farin cikin dawowarki...Allah ya Kara maki lafiya Sweet heart 😍



*PAGE 1➖5*


Wata yarinyace da bazata wuce shekaru shabakwai da haihuwa ba zaune a daki tayi tagumi se kuka takeyi, hankada labular dakin da taji anyine yasa tai saurin dag'o kanta, ido hudu sukai da wata mata wacce ake Kira da Inna. 

        Inna harararta tayi tace" ke Dan ubanki bazaki fito kimun wanke wanken bane ko ni kike jira nai miki? Yarinyar nan mai suna husna ta mik'e tace" inna kiyi hakuri yanzun nan zan fito, karma ki fito nidai na fita kuma Kafin na dawo ki tabbatar kin gyaramun ko ina a cewar" inna..


Inna na ficewa husna ta sake wani irin kuka me ratsa zuciya tace" kaico na, na shiga uku,  yanzu haka rayuwata Zata kasance kullun cikin bakin ciki! Ta zurfafa a tinani taba ba shine mafita ba hakanan ta tashi tai abun da inna ta umurceta tayi, tana cikin yine sai ga wata yarinya ta shugo da sallama cikin natsuwa tace" yaya husna    ai da kin bari idan na dawo sai nayi, husna ta kalleta tace" uhm Kedai khadija Kije ki cire uniform dinki Dan inna ta shugo taganki anan kinsan bazataji dadi ba, khadija ta tabe baki tace" to shikkenan husnah, khadija tayi daki itakam husna taci gaba da aikin da takeyi, 


        Khadija na daki after  ta cire kayan makaranta ta zauna itama tace" wai me yasa inna take hakane?  Kenan yanzu wasu idan basu suka haifeka ba sesui ta ba mutun wahala abun da babu kyau..khadija taga bazata iya zama ita kam ba tuni ta fito tasama husna hannu suka cigaba da aikin tare,  suna cikin yin sharar tsakar gidan ne inna ta dawo taga khadija wani ashar ta zuba sannan tace" ke husna bance ke kadai zaki aikin ba Dan me naga khadija nayi kuma?  Tayo kanta da gudu ta fara duka, khadija na cewa" Dan Allah inna ki mata hakuri wallahi ni nace zan tayata ba ita tace" nazo ba... Inna bata saurareta taci gaba da dukan asma'u (husna) seda ta gaba mata ligis sannan ta waigo kan khadija tace" in k'ara ganinki kina wani abu a gidan nan nasan me zan miki, 

    Khdijat tace" inna kiyi hakuri ni macene dole nayi aikin cikin gida, inna tai mata wani irin mugun kallo tace" _bazakiyiba tunda ubanki ai Kasa hakura yayi Kafin na haifoki yaje ya samo mana mugun iri, Mayyar yarinya_ *karku manta da wannan kalmar na samo husna* agaba zasuji ya akai aka samo husna har tazo gidan...


Husna na dok'e duk abun duniya ya isheta ga kuma maganar da inna tayi wai itace mugun iri, wani ajiyar zuciya tayi tace" a zuciyarta wallahi baba na dawowa ita dole ma tabar gidan nan.,  inna da khadija kam daki suka shige inna ta ciro Dan tsiran data siyo taci ta mik'a ma khadija tace" ungo kice,  khadia ita Sam abun da mahaifiyarta takeyi bata kyautawa, shuru kawai tayi tace to inna na gode amma ina na HUSNA?  wani harara da inna tai mata yasa da sauri ta sa tsiran a baki tanaci ne amma bawai don ranta yaso ba.. 


          Husna kuwa ta gama aikinta tsab ta sama waje ta zauna a tsakar gida cikinta se Kiran churuma yakeyi, iyayanta ta tuno ko suna raye ko suna mace Allah kadai yasani..addua tai musu taji gaba dayama yunwar ya tafi.. Tana zaune ne Sega baban khadija ya shugo da sauri yace" asma'ul husna yana ganki a waje ko basanan ne? Inna najin muryar mijinta ta fito tace" kasan husna bameson hayaniya bane nayi nayi da ita ta shugo wai iska take ji, Husna duk mamaki ya kmata yanzu yanzu makirar matarnan har ta shirya Zance, Baba yace" ok to shikkenan aka wuce wajen....



Haka rayuwar husna ya kasance kullun cikin bakin cikin Gashi batasan kowa nataba, kotayi yunkirin guduwa sai tace" inta tafi yanzu inama Zata dosa tunda ba kowa ta sanine, nan ne dai yazammata wajibi ta zauna da dadi ko ba dadi.. 







*Kuci gaba da biyoni*

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


```NA........ ✍🏼```

*UⓂmiey Xeey Abakson*


       _•••°°°Devoted  to......°°°•••._

*Miss Zarah Mansur😍*


Dedicated  this page to you my love, my twieny,  my happiness, my jinin jiki my everything *EMNOOR AHMERD DON* bby ki huta domin kina tashe a hrt din ummiey Xeey😍



*PAGE 5➖10*


*TOSHEN LABARIN*

Asma'u (Husna) dalilin zuwanta gidan baba (kabir) 

        mahaifin asma'u (husna) Alhaji aminu Dan garin kano a wata unguwa kurna, Yanada mata guda daya maryam sunyi auran soyayya har Allah ya azurtasu da yarinya guda daya asma'u ana ce mata husna, sun bata cikakkiyar kulawa da tarbiya daidai gwargwado har takai 10years lokacin ta fara girma, Ananan Ananan se wata rana Alhaji aminu da matarsa maryam suka yanke shawarar kawo ziyara garin kaduna, suna cikin tafiyane Alhaji  aminu yaga gittawar wani shanu kan kace meye nan take sukai hatsari, subhanallah, 

      Ashe shanun nan ba shanu bane na yan cultism ne (yan shan jini) ne, suna hatsarin mutane suka taro kan kace meye Wanda suka haifar da hatsarin har sun dauke asma'u sunyi gaba.. Mutane kam duk ba Wanda ya lura, kowa ta ceto ran Alhaji Aminu da maryam akeyi, direct asibiti aka nufa dasu dan cikinsu ba Wanda yake hayyacinsa, seda  kusan sati daya sukace" ai akwai wata yarinya batafi 10 years ba, yar suce, Asibitin ya dauka ba'aga yarinya ba,  wanda suka kawosu sukace basuga ko wace yarinya ba,  nan Ciwo ta dawo musu sabuwa na rashin yarsu Husna da sukai,  da yake masu tawakkaline hakanan suka hakura  amma kullun suna zullumin ko zasu ganta, kuma kullun cikin rokan Allah suke kuma aka tayasu da addua Allah yasa a ganta


Wanda  kuma suka sace husna, antafi da ita gidan yankai kai amma Allah be basu ikon aiwatar da abun da sukai niyya ba, ogan ne yace" karsui mata komai yarinyar tana da kyau yace" a kawota dakinshi, nan aka kawota da yake mahaifiyar ta tana Dan koya mata addu'o'i tana shiga dakin sukai Ido hudu da ogan,  addua tayi yace" ga waje ta zauna,  ta zauna batabar fadin _innalillahi wa inna ilaihi rajiun ba da hasbunallahu wa ni'eemal wakeel_ shi kanshi yasan yarinyar ta fi karfinshi Dan ajikinshi shima yaji.. Dan tabbas addu'a ba karya bane,  Kasa komai shi ma yayi yace" akawo mata abinci,  aka kawo husna ta kafe ita fa batajin yunwa, nan aka kawo mata abun sha nan ma tace" bazata sha ba... ogan yaji yarinyar tamai Dan ko ba komai she's damn beauty  *tanada kyau* ya kalle asma'u da hausarshi da bata fitowa sosai yace" mene sunanki? Ta kyallale da dariya tace" ba haka ake fada ba menene sunanki akecewa" ogan yai mamaki matuka yanda yarinyar take magana, yace" yes tell me tace" sunanan Asmau ana cemun husna" yace huzna? Tace" a a husna,  yace" ok na rik'e,  ita sam tama manta da halin da take seta tino da mahaifiyarta ta fara kuka tana cewa mamana,  mamana, tunda ta fara Kiran sunan mamanta ogan yaji gaba daya hankalinshi ba'akwanceba,  nan take ya Kira wasu mutane wai a kaita wani dakin!  Nan sukazo suka dauketa suka kaita dakin da ogan yace"


Bayan sun kaitane suka dawo wajen ogan sukace" Oga munyi abun da kace muyi yanzu me kkeso ai ma yarinyar?  Ogan yace" no please  don't  do any bad thing to her,  ko ajiyemun ita ina son yarinyar nan, sunyi mamaki sosai yanda yarinyar  ta shiga ran Oga GATA ba budurwaba balle sui tinanin wani abu, daya daga cikinsu yace" Oga Kodai zakai keeping dinta ne har ta girma se ka dinga amfani da ita?  Shiiii Oga yace" kar ka sakemun irin wannanar maganar,  intact  ni kaina bansan mezayi da ita ba just yarinyar tamun ne,  

    Sukace okay nan ya ciro kudi  ya basu yace" duk wani kaya na wasa Dana sawa da su sweet duk kuje ku siyo mata please... Sukace" angama Oga, suka tafi kasuwa yi mata siyayya

     Itakam husna ganin dakin duk ta bi ta rude tace" na shiga uku, taga wani blanket Me kyau a kan gado taje ta taba  taji mutun, wani ihu ta saka wacce ke baccin itama ta farka suka fara ihu duka..jin ihun da Oga yayine ya fito ya shiga dakin ya gansu,  tsaki yayi" yace" ok daki daya aka hadaku? Ok ku zauna kunji ba abun da zai faru daku, yai ficewarsa,  

     Dayar da yake tafi husna wayau da shekaru tace" kema satoki akai ko?  Husna ta daga kai tace" eh kema haka?  Dukansu dai eh ne amsarsu,  nan suka fara kuka dayar me suna khairat tace" ki dena kuka ni na kusan 1 year anan abun da nakeso dake shine  kita addua Allah yabamu ikon fita daga nan gidan,  ai kin iya addua ko?  Husna ta daga kai tace" eh tace to shikkenan dukansu suka shiga innalillahi  wa inna  ilaihi rajiun.. Suna zaune Sega Wanda oga ya aika dinnan sun kawo mata kayan da ogan ya aikesu





Ummiey Xeey

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


```NA........ ✍🏼```

*UⓂmiey Xeey Abakson*



       _•••°°°Devoted  to......°°°•••._

*Miss Zarah Mansur😍*


Dedicated  to all my fans # I love  you wujiga wujiga❣



*PAGE 10➖15*

Suna zaune ne Sega Wanda Oga ya aika dinnan suka kawo mata kayan da ogan ya aikesu, suna ajiyewa suka fita,  khairat ce" ta bude kayan tai tsaki tace" ta Allah ba nakaba itadai husna bin khairat da ido kawai takeyi


     Bayan sati daya Alhaji aminu da matarsa har har sunji sauki sun koma gida,  amma tamkar marasa lafiya saboda an rabasu da farin cikinsu,  inama ana saida da a kasuwa da sunje sun siya,  asma'u  ita kadai ce farin cikinsu Gashi yanzu bata a gidan! Kowanninsu kana gani kasan ba cikin kwanciyar hankali suke ba, amma to ya zasui?  Hakanan suka hakura! 


      Bangaren su Husna kuma satin ta daya a gidan, kullun da dare sai Oga yazo ya zaunar dasu ita da khairat sui ta hira, Yau ma kamar kullun suna cikin daki sai ga ogan nan ya shugo ya samesu zaune sunyi shuru ya kalla khairat yace" akwai abun da kuke bukatane?  Khairat tai banza da shi, Husna ce me karfin hali tace" eh munaso muje gidan iyayan mune, Ogan a fusata ya kalleta a zuciyarshi yace" badan ina son yarinyar nan ba da sai ta sani cikin daren nan, yana tinanin zuci ne ta kara da cewa Kaji please ka kaimu wajen iyayanmu, kallonta yayi yace" bazaki zauna da niba a nan gidan?  Kada kai tayi alamar a'a sannan ta fasa kuka nidai ka kaimu wajen su mamanmu, Bacin rai yaji a fusace ya Kira ma'ai katanshi yace" wa ennan yaran sunaso su Tona mana asiri kui maza ku fitar dasu a nan gidan, nan take suka buga ma khairat da husna kai dukannsu tsintar kansu sukai a waje


Khairat ta ganta a wani daji da gudu take ta tafiya ga dare yayi har Allah yasa ta fito cikin gari ta sama wasu mutane tace su temaketa, nan ta basu labarin halin data shiga sukace Insha Allah zasu temaka mata har taje gidan iyayanta.... 


     Ita kuma Husna koda ta tsinta kanta a waje ga dare yayi, tama rasa ina zataje, kuka taketayi me Susa zuciya,  wani Babban tifa ta samu a bakin titi ta shiga karkashin tifan (motor kwasan yashi) ta cire zaninta ta kwanta ta lulluba abun tausayi, bacci takeyi me dadin gaske dan Allah ya temaketa tabar gidan mugun mutumin nan... 


     Gari ya fara wayewa masu Motor tifa sunzo zasu dauka motarsu su wuce wajen aiki, sai daya daga cikinsu yace" kamar nunfashi nakeji ko? Dayar yace" wani irin nunfashi kuwa,  dayan yace" wlhi kuwa mudai duba, aiko suna cikin haske haske suka hasko husna a karkashin motar, Allah sarki dayan yace" haskata da sukai Husna ta tashi firgigit, tana dan Allah kar ku yankani kuyi hakuri,  daya daga cikinsu ya daka mata tsawa yace" ance miki mu yan yan kan kaine? 

       HUSNA  a rude tace" kuyi hakuri, ta fito sumi sumi duk ta zama abun tausayi, dayan yace" Meya kawoki nan wajen?


Kuka sosai takeyi nan ta basu labarin komai, sun tausaya mata matuka sannan sukace Allah ya raba na gari da mugu tace" Ameen,  dayan yace" yanzu ya za'ai kenan? Daya yace ai mu kaita wajen me unguwa kawai dan mu bamusan ya zamui da ita ba,  kuma kaga bedace ba sam mu riketa a hannunmu... 

    Haka ko akai suka Kama hannun husna sai gidan me unguwa


Sallama sukai sanan suka  shiga wajenshi,  nan suka sanar dashi ga abun da yake faruwa, Me unguwa beyi Kasa a gwiwaba ya tambayeta tace" tabbas hakane ya k'ara umurtan ta data bada labarin da kanta,  tsab ta fada.  


       "mamaki ya kamashi, nan aka baza a radio duk Wanda yarshi ta bace" yazo ko itace,  kowa yazo yace ba yarshi bace, Anyi cigiya har an gaji, har Allah yasa Baba Kabir mijin inna yazo ya roka alfarma a bashi ita duk da beda hali sosai amma Insha Allah zai kula da ita kuma duk randa aka ga iyayanta zai bada ita dan be taba haihuwa ba a rayuwarshi

     Me unguwa da sauran mutane sukace to shikkenan  Allah ya tayashi riko yace" ameen



*_To kinji dalilin  zuwan husna gidan baba Kabir kenan_*














Xeexeeee✍🏼

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


*FA'IZA ANFA* ina tayaki murnar KAMMALA littafinki me suna *D'AN FASHI*  Allah ya Kara basira dear faxeey sai munjiki a book dinki na gaba


*PAGE 15➖20*


_CIGABAN LABARIN_

baba yai shigewarsa daki, Inna ne ta leko ta ga Husna still tana tsakar gida,  wani harara tai mata tace" yar matsiyata kawai, maganar nan ba karamin sosa ma husna zuciya yayiba amma seta share dan she can do nothing to her


Baba ne ya kwalla ma husna Kira, tazo cikin natsuwa yace" tun rannar banji Kin karamun maganar makarantar ba ko bazaki koma bane?  Susa kai tayi tanaso tace wani abu amma tsoron inna take ji dan tace ba makarantar da Zata koma, sedai yarta ce khadija zatai makaranta,

    Baba ya kara magana yace" inajinki,  zatai magana kenan Sega inna ta shugo tace to me kuma take ce maka? Baba Kabir dariya yayi yace" ba abun da muke cewa maganar makaranta mukeyi! 

      

         Inna taba baki tayi" tace to yan Boko, yanzu wannan katuwar yarinyarce zakace Zata koma boko ai tunda tayi js3 ta gama makaranta kuwa, salon taje ta dakko mana abun magana!  

      Maganar  ta batawa malan kabir rai yace" Kinga a kullun kidinga wa mutun kyakkyawan zato wannan wace irin magana kikeyi haka?  Nan Inna ta fara sababi wai ba Dama ta fada gaskiya akan wannan yar yarinyar har malan zaizo yana fada mata magana, nan ta shiga kuka kuma tace" nasan a rina wai an sace zanin mahaukaciya ni nasan kafison ta akan Khadijat, tunda Gashi tun Kafin mu sama khadijan ai kaje ka Kasa hakuri ka samu wannan shegiyar yarinyar,  sannan ta fita,  Da yake Malan yasan halin nata, Allah ya kyauta yace" ita ko Husna  na tsugunne tace" dan Allah baba ina neman alfarma

     Yace" to inajinki, kabarni na bar gidan nan bazan iya zama ba a cewar Husna, baba kallonta yayi yace" Husna kiyi hakuri Inanan tare dake kidena damuwa da halin wannar matar kinajina ko?  Husna  to kawai tace dan tasan bazata iya ma baba musu  ba.. Mikewa  tayi ta koma tsakar gida abun tausayi


Yamma nayi ta shiga daki tasa uniform dinta na islamiya tai tafiyarta,  tana zuwa ta hadu da kawarta me suna Zainab, Zainab tace" naganki wani iri menene?  Husna  tace" wlhi ki bari kawai duniyar nan ta isheni, banjin dadin komai!  Zainab tace" husna kiyi hakuri duk tsanani yana tare Da sauki, kici gaba da addua kawai kinji! husna tai murmushi tace" sai yasa nakeson kasancewa dake kullun sai kin farantamun rai Zainab tace" Lol ba komai mu biya karatu Kafin malan ya shugo


                   °°°°°°°°°°°°°°°

Bangaren Iyayan husnah kuwa duk tinaninsu yanzu kusan 4years husna ta mutu, har Allah ya k'ara  basu wata yarinya suka maida sunan sunan husna,


ana ce mata husna karama..cikin ikon Allah yarinyar tsab husna babbancinsu kadan ne husna babba farace while  husna karama kuma baka,  har sun cire ri gaba daya kullun sedai suita mata Addua.... Wannan kenan


                   ➖➖➖➖➖➖➖

Bayan Husna  ta dawo daga islamiyane, tana shiga ko zama batai ba Gashi ta gaji,  inna tace to malama ga kayan miyanan sai kije ki jajjaga ki daura wa mutane girki kuma kafin magrib kin gama, wani takaici Husna taji tace" hmm Wannan matar bazata barni na huta bane hakan,  kullun aiki, bakomai Allah ka sakmun, nan na cire kaya tai maza tazo tai abun da inna tace...


Bayan ta gama ne tayi sallah tai azkar dinta tana zaune akan sallaya, sallamar wani yaro sukaji wai ance" Husna tazo, karaf a kunnan inna,  fitowa tayi tace" kaje kace mai tace bazata zoba, yaro ya fita yaje ya sanar da abun da aka cemai, 


      Inna kuwa binta da kallo tayi tace" to yar iska,  ba sai kince yazoba aurar dake zamui mu huta,  tun yanzu kin fara Kiran maza suzo miki ko?

 

      Gaban husnah ne ya fadi tace"






Ummiey Xeey

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*



*​PAGE 20➖25*


Gaban Husnah ne ya fadi tace" wallahi inna ni bansan waye yazo ba,  inna takai mata duka tace" rufemun baki yar banzan yarinya, tun kina karamar ki zaki lalace, itadai khadija tana daki tanajin abun da mahaifiyarta takeyi amma ba yanda ta iya shuru tayi dan bata da ikon da zatai mata magana.. 

      Husnah ta kara bude baki tace" kiyi hakuri inna,  ana cikin hakane sai ga baba kabiru ya shugo ya sama Inna a gaban Husna yasan masifar ta takeyi, 


       Baba matsowa kusa da su yayi yace" lafiya kuwa?  Inna ta waigo cikin huce tace" ina lafiya anan wannan yar banzan yarinyar nan zataja mana abun magana yanzu wani ya kamota a waje wai ya ganta da wani suna iskanci... Gaban baba ne ya fadi yace" Anya kuwa?  Husna tace" wallahi baba ba gaskiya bane tun dazu inanan wajen, nan danan inna ta fara salati wai yarinya  ta kulla mata sharri wai tayi karya kenan! 

     Baba shima yasan ba gaskiya bane Yace" kedai wallahi kiji tsoron Allah, tun randa yarinyar nan tazo gidan nan kke nuna mata kiyayya karara,  haba


Maganar da baba yayi kamar ya kunna ta, Nan inna ta fara sababi wai ai dama ita tasan haka Zata faru, akan wannar yarinyar ze karyata ta, masifa take sosai ita kam husna in banda tsoro da gabanta nata fadi ba abun da yakeyi, tun da take bata taba ganin mace mai masifa da mugunta kamar inna ba,  se masifar ta take, baba yace" Husna  ta tashi ta shiga cikin daki shima yai wucewarsa daki,  har ya shiga dakin kuma seya kwalla Husna Kira,  yace" kome inna zatai mata kar ta ji haushi, haka *rayuwar wasu* yake,  akwai su da mugunta Dan Allah karta dama kanta, To tace" sannan ta mike ta tafi dakin baccinsu ita da khadija....


Tana shiga gado ta fada ta fara kuka sosai,  tace oh ni Husna haka rayuwata Zata kasance?  *Rayuwar wasu* gwanin sha'awa amma banda ni kukai tayi sosai khadija nata bata hakuri, Husna  tace" ni bake kikai mun komai ba wallahi badan baba ba guduwa zanyi inje in karace rayuwata a wani wajen...Khadija ta rungumeta tace" dan Allah aunty kar ki tafi ki barmu,  kiyi hakuri komai yai farko zaiyi karshe itama inna Allah ya dawo da ita kan hanya.. Husnah  kawai jinta takeyi azuciyarta tace kayya,  Anya kuwa?

     Da tinani barkatai tai bacci,  batai bacci me tsayi ba ta tashi ta fara nafilan dare, Sai da tai addu'o'i sosai sannan ta koma bacci shima  bata dade ba aka Kira asuba..


Bayan tayi sallahr asuba ne tana zaune wasu zafafan hawaye suka zubo mata, iyayanta ta tuna Gashi abun takaici kwata kwata ta manta inda suka, addu'a tai musu gari na waye wa ta tashi ta fara aikin data saba tun safe. Wanke wanke tayi sannan ta dauka Dan kamun Da sukesha ta ta dama bayan ta gamane ta dakko littafi tana karatun abun Da aka koya musu a islamiya 

    Koda inna ta hangeta zaune hararar ta tayi dai dai da lokacin da baba yazo zai fita


Kallon husna yayi yace"





*Kuci gaba da biyoni*




   

                Ummiey  Xeey

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


     *Dedicated  to Umar M SHARIFF  fans*❣


*​PAGE 25➖30*


"Baba kallon Husnah yayi yace" yar baba karatu akeyi ne?  "Eh tace sannan ta kara da cewa" dazu nazo gaisheka bakanan ina kwana baba" "amsawa yayi da lafiya lau ma'u, Allah dai yayi albarka kinji? Tace" Ameen sai ka dawo yai ficewarsa


       Innace na zaune a daki duk haushin as'mau ya isheta sallamar makwabciyarta taji, Inna ce ta fito dauke da farin ciki a tare da ita tace" marhaban lale, makwabciyarta tace" kaman zan wuce Ashe Kinanan! Inna tace" eh wallahi shugo daga ciki mana, tace" toh

           Bayan sun gaisane makwabciyarta tace" Naga su asma'au har an girma har yanzu dai ba labarin iyayanta? 

  Inna ta taba baki tace" gatanan dai ni wallahi aminiya bason yarinyar nan nake ba fa, da akwai inda zan kaita wallahi da nakai, makwabciyarta tace" to me zai hana ki amfani da ita wajen neman kudi? Tunda dai Kinga ba juya komai kikeyiba ki dinga daura mata talla ko ko ki turata gidan aiki tane nemo maki kudi


Inna ta washe baki taji labari me dadi tace" Allah ko aminiya? Kinga shikkenan Allah yasa a k'ara saceta kota hadu da ajalinta Kinga shikkenan na rabu da ala kakai, dadan haushinma malan duk yabi ya damu da ita kome takeso nan danan yake mata mu kuma oho..   Makwabciyar ta tace tabdijam adaidai ma kenan dan nikam banga amfanin zamanta agidan nan ba, in banda halin wasu yaushe dan waje zai fi dan gida?  Gaskiya ki gagauta turata aikin ko tallan shawarace fa!  Inna tace ai wannan shawarar yayi sosai aminiya  na gode amma kai naji dadin zuwanki,  makwabciyar tace" bakomai ai Muna tare ni zan tafi duk abun da kika yanke shine dai dai.... Inna tace to nagode har bakin kota ta rakata 


               °°°°°°°°°°°°°°°°


Bayan kwana biyu, malan kabir da inna suna zaune suna hira, inna tace" Malan ina neman wani abu a wajenka,  malan yana cin goro yace" ina jinki, inna tace" Dan Allah husnah ne naga tun da ba boko Zata koma ba me zai hana ta dinga zuwa wanke wanke haka? Malan zaro Ido yayi yace" gaskiya ban yardaba bada yawuna ba, duk kokarin da nakeyi bakya gani?  Har sai kin tura ta aiki?  In abun dadine ki tura yarki mana.. Inna tace" ai kaga khadija yarinyace, Malan yace haka ma husna  yarinyace! 

    _Itadai husna tana daki tana jinsu, taso baba ya yarda dan a ganinta haka ne samun saukin ta_


      K'in yarda Da malan yayi, inna tashi tayi fuuuu sai cikin daki tace" to Wallahi se taje aikinnan,  shidai malan bece mata komai ba,  mamakin halayar matarshi yakeyi


      *Washe Gari*

Inna ce ta Kira khadija  tace  taje ta Kira mata saude (makwabciyarta) to khadija tace sannan ta fita,  tana zuwa ta sanar da sakon da mamanta ta aiko ta,  Saude tace" ok ki jirani mu tafi,  basui minti ukuba se ga sunan sun dawo..


Suna shuguwa, inna ta aika Khadija Dan bataso tasan maganar da zasu tattauna, lokacin itama husna an aiketa 

       Inna ce ta fara magana tace" malan yaqi amincewa fa!   Saude tace" sai kikace mai mene?  Inna tace" cewa nayi sai taje, saude tace" kash ai da bakimai musu ba amma hakan ma bata baci ba,  yanzu  abun Da zamui shine, dama akwai wani gida da ake neman me aiki ance in kawo yarinya kuma sukeso, gobe se mu kai husna,  amma ko da wasa kar ki bari malan ya sani, inyaso koda wata rana ya tambaya ina take sai kice tana zuwa islamiyar safe ne tunda dama aikin 9 zuwa daya 1pm sukeso


      "Inna shewa tayi tace" kai amma naji dadi sosai sosai,  saude tace" bakomai bari na tafi goben ma hadu!





*Ummiey Xeey*

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


         Where  is my *Aishan Umma*... Your page  is here.  Tnx for your love  & support Allah ya barmunke 💋


*​PAGE 30➖35*


Saude tace" bakomai bari na tafi goben ma hadu,  tana fita Inna ta Kira HUSNA take sanar da ita in Allah ya kaimu gobe za'a kaita wajen aiki, wani dadi husna  taji kamar tai tsalle dan hutu yanzu yazo mata, zaman kadaic yanzu ya Kare dan ko yushe tasan Zata kasance cikin busy, shurun da tayine Inna tace" bakya sone?  Ai se kinje shi, Husnah tace" to Inna Allah yakaimu, A wulakance inna tace Ameen, Ta Kara  da cewa" dan haka ki Shirya fes,  ga 30 nan kije ki siyo omo ki dan wanke kayanki masu datti, AMSA husna tayi tace to"


Allah Sarki husna, Fitowa tayi taje siyo omo, se dadi takeji dan at least  ko ba komai Zata huta kuma zataji me dadi dan haka tai maza ta siyo omon tazo ta fara wanki,  tana gamawa aka Kira salla tai shirya ta tafi islamiya. 

    koda taje islamiya ta hadu Da zainab kawarta take bata labarin  ansamo mata aiki,  zainab ma Murna sosai ta tayata,  sannan tace" amma sa sai kinyi hakuri, kinsan *RAYUWAR WASU* akwai wulakanci a ciki,  balle ma suga kana musu aiki, nufina kana kasansu,  Husnah murmushi tayi,  tace" Zainab ai wannan da sauki a wajena  akan wahalar da nakesha Wajen inna...   

        Zainab  tace" Hakane gaskiya, amma ki kula da kanki kinji, Allah ya temakemu, Husna tace" Ameen,


Suna cikin hirar *RAYUWAR WASU* yanda rayuwar  kowa daban, wasu tausayi, wasu mugaye, Malan ya shugo musu karatu dan haka suka ajiye hirar, suka maida hankalinsu kan karatu ahaka har aka tashi... Zainab  tayi gida  itama husna tayi gida

      Koda taje gida  taga inna faram faram tayi mamaki sosai dan wannan ne karo na farko datai mata dariya, sannu da gida tai ma inna sannan ta wuce ta cire uniform, ta fito ta amsa jajjagen da inna takeyi, tana gamawa ta daura abinci

       Da daddare Khadija suna kwance  da Husna, husna  tace" gobefa zan tafi gidan aiki,  zare Ido khadija tayi tace" gidan aiki kuma?  Ba baba ya hanaba?  Husna tai dariya tace" duk da haka Nikam gwanda na tafi ko na huta,, 

     Khadija bataji dadin maganar ba data duba kuma taga Gaskiyane,  tace" to aunty husna Allah ya temaka husna tace" *Ameen* kowo yai baccinsa

      

_Washe gari_

Husna ta tashi kamar lokacin data saba tashi, tai aikace aikacen Da zatai, tai wanka ta shirya,  malan kabir na fita, Inna da kanta taje ta Kira saude akan sun shirya, saude  tace" to muje gidan Muja mata kunne! 


        Tafiyar minti 3 Sega saude da inna sun shugo,  daki suka nufa sannan husna ta bisu, ba kwalliya tai ba amma tayi kyau sosai, nan ta zauna suka fara mata kashedi kamar haka, kome aka bara kar taci ta bari ta kawo gidan tace to, kuma kudin aikinta na wata ba ita za'a dinga ba ba inna da kanta zataje ta amso,  tace" shima  to, sannan kuma banda kwalliya da yawa dan kar dan gidan yace" yana sonta,  tace" to shima  taji, sannan suka tashi suka tafi gidan hajiyar


Suna fitowa keke napep suka tare, sukace a kaisu ung GRA yace" okay

     Tafiya minti kadan sukai, suka isa, Fitowar da Husna zatai taga gidan mekyau, Alhamdulillah  tace" a zuciyarta, su inna da saude suna tafe itadai tana binsu a baya har suka isa wani kofa,  saude ce ta bubbuga akace yes suwaye?  Saude tace" mune, wata yar karamar yarinya  tazo ta bude musu, hajiya Farida tana ganinsu ta sake musu murmushi tace" sannunku da zuwa,  Sukace" yauwa hajiya sannan suka sama waje suka zauna


Bayan sun gaisa, Husna karema dakin kallo tayi tsaf, Saude ce tace" hajiya ga yarinyar nan sunanta Asma'u amma ana ce mata husna, hajiya Farida tace" Masha Allah,  kun mata bayanin komai ko?  Aikin Karfe tara zuwa 1 na ranane, Saude tace" eh mun mata, hajiya Farida tace" yauwa wanke wanke ne  da wankin toilet da share share se wankin yara,  Husna  ta dago kanta cikin natsuwa tace" angama hajiya Insha Allah,  hajiya Farida taji dadi sosai yanda yarinyar ta ansa dan ansha kawo mata yara amma sam basuda kunya

    

Hajiya Farida  tace"









*Kash I'm tired mu hadu gobe*











*Ummiey Xeey*

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


*Dedicated  to zauren uⓂmiey xeey.. Loves you plenty 😍*


*PAGE 41➖42*


Hakadai rayuwar Husna ya kasance kullun sedaje gidan aikinta,  yanzu kusan one month amma har yau baba beson tana zuwa aikiba

     Yau ne ta shirya tsab Zata tafi, Tayi kyau sosai skin dinta ta fara murjewa da kyau dan ba karamin dadin take kwasha a gidan nan


    Tafiya take har ta sama napep tace akaita GRA ung rimi, suka daidai ta da me napep, suna isa ta ciro kudi ta bashi tai shigewarta gidan,  koda taje yau hajiya batanan tana office, wani iri taji a tsorace dai tai aikinta, tana kitchen ne tana goge goge, Usman ya shugo, yace ta dan samai ruwan wanka a kettle idan yayi zafi takai mai dakinshi a cikin bukiti, kamar zata ce" bazata  kai ba kuma dai ta kyaleshi, yana yin zafi ta dauka ruwan takai side  dinshi, setaji kamar muryan wata a cikin dakin, seta fara tinanin Anya ma ba mace bane a dakin?  Wata zuciya kuma tace" ko wa ka gani kamai kyayyawar zato,  seta share itakam taje tai abun a zatai,  tana gamawa tunda hajiya batanan ranar tun 12 ta koma ma gida


*Washe gari*

       Haka ranar ta ta sake komawa gidan still hajiya  batanan,  ta tafi wajen  aiki, tana shiga ta dakko kayan ameerah ta fara wankewa,  jin muryar Usman tayi yace" ga boxer's  dina nan ki wankemun kinji,  dagowa tayi a fusace tace" nifa abunda kkemun ya fara isanka,  badon kai aka kawo ni nan gidan ba, binta da Ido yayi yace" yar kauye kin sama waje, idan baki wankemun ba sena bata maki rai, wawiya kawai, abun ya kuluta tace" ni ba wawiya bace,  wani mari ya sakar mata seda taje kasa,  rike kumatunta tayi se kuka takeyi tace" on ni Husna,  Ina ganin rayuwa kala kala,  

     Usman  dariyar mugunta yai mata yace" yar banza kawai nasan maganinki,


Yajuya ya tafi, kuka tayi sosai taga ba sarki se Allah,  jika boxer's  din tayi tana gama wankin ameerah ta wankemai tas, a zuciyarta tace" wlhi mugunta ba kyau ne da duk sai na barbada barkono a ciki, tagama ta shanya taje tai sauran ayyukan, kafin ta gama kayan sun bushe, ta kwaso takai ma ameera daki tasa a wardrobe Kafin me guga yazo


Sannan ta kwashe nashi  takai mai daki,Tana shiga ta same Umsan a kan gado, binta da wani irin kallo yayi da ni kaina bansan wani irin kallo bane wannan, yace" banza ba'a koya miki sallama bane?  Yi hakuri tace" sannan yace duk randa ya sata abu tai mai musu wallahi seya bala'in bata mata rai, to tace" ta mik'a mai boxer's  din, tana mik'a mai ya bude su yace" kin ma raina ma kanki wawau, boxers dina sababbi amma ji yanda kika dafar mun dasu ya watsu mata,  yace" maza ki tashi ki kara wankemun su

    Shidai mus'ab yana daki yaji hayaniya yace boss  wai meye ne?  Nan usman yace" kaya na bata ta wankemu ta k'ara  samun datti a ciki, mus'ab bushewa da dariya yace" tab lalle ma bakisan waye ya Usman bane maza tashi kije ki sake wankemai, Usman yace" help me tell her my bros,  ji tai kamar ta kwalla ihu, badab tanajin dadi a gidan ba yau kam da tace" tabar aikin gidan nan,  hakanan ta tashi jikinta ba kwari taje ta sake wankemai ta shanya, Gashi time din tafiyarta yayi amma tana tsoron tafiya saboda Usman,  hakanan ta hakura ta jira har suka bushe sannan ta kwashe ta kai mai ya duba yace" kinci sa'a yarinya Da yau kinsan babbancin ruwa Da kalanzir, batace komai  ba ta mike tai tafiyarta  gida CIKE da bakin ciki,  ko Ina kaje ba dadi, tirr da *Rayuwar  wasu*


Tana isa gidansu,  baba ta  gani, a kofar gida, Allah yasa bega sanda ta sauka a napep dinba, sallama tayi mai,  yace" ha'a daga Ina husnah, tace" innace ta aikine baba,  yace ok, Allah dai yai miki albarka yar nan tace" Ameen tai shigewarta gida..... 















Ummiey Xeey

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


Dedicated  this page to my dear *ASY KHALEEL* You mean so much to me❤


*​PAGE 35➖40*


Hajiya Farida tace" Masha Allah,  gaskiya  yarinyar ta shiga raina, husna smiling  tayi a mind dinta tace wlhi nima hajiyar nan tamun da akama bazatai muguntaba. inna najin haka wani bakin ciki taji tace" inama y'ata na kawo ko Allah yasa tayi dace dan Dan gidan ya aureta..! 

      Nan dai Suketa hira,  su saude sukace zasu tafi hajiya Farida ta dakko  kudi masu yawa ta basu, Sunyi mamakin kudin sosai dan kusan 10k ne basuzata zasu samu ba, Sukaima hajiyar  godiya sosai, sannan  ta rakosu har bakin gate suka wuce,   

      Hajiya Farida na dawowa, ta iske husna inda suka barta, Ce mata tayi" kije ki cire hijab  muje na nunnana maki wajen Da zaki dinga aiki, ki sake jikinki dani kome kkeso ki sanar dani kinji, to tace" sannan ta mike ta bi bayan hajiyar


         Side din maza ta fara nuna mata tace" wannan dakin Usman ne shine babban Dana, yagama karatunshi a Egypt, shekarunshi 27, wannan kuma na mus'ab ne second  born  dina yanzu he's just 25years, Zaki dinga zuwa kina wanke musu toilet  da sharan daki,  Okay tace" sanan ta kaita chan bayan wajen wanke wankensu, Ta nuna mata tace" nan muke wanke wanke, Husna  tace" to hajiya Insha Allah, haka ta nuna mata ko Ina na gidan, sannan suka dawo pallow.. Sune zaune Sega Ameera, ta fito itace wacce ta bude musu kofa dasuka shugo,  tace" wannan ne autata yanzu ta gama secondary  school, Masha Allah tace" sannan ta mike tace" hajiya ba aikine?  Hajiya Farida dariya tayi tace" yanzu dai babu, husna tace" ok, Tana zaune a kasa, suna kallon TV... Sallamar Usman da mus'ab sukaji, 

      _Usman  da mus'ab ya da kanine amma kuma duk inda zasuje tare suke zuwa ko wanninsu beda aboki inda ban uwanshi ba idan ka gansu kamar twin's_


Yanayin usman shi irin black beauty ne,  beda tsayi  sosai yanada eyes Masha Allah, jikinshi dan dai dai


Hajiya Farida ce" ta Amsa sallamar suka shugo suka sama waje suka zauna!  Mus'ab ne ya kai idonshi kan Husna yace" mum who is this?  Hajiya farida tace" me aikine muka samu,  sanan usman ya kalleta  tsab yace *hmmmm* ko me ya ayyana a mind dinshi Ohon mai a gaba zamuji

       Gaishesu tayi suka amsa suka bita da wani irin kallon yar kauye..


Mus'ab ne yace" bari naje side  dinmu nagaji mum, Usman yace" wait for me mu jera tare, haka suka fito daga dakin mum itadai Husna binsu da kallo tayi,  

 

Sun isa part dinsu  Usman ya wani tintsire da dariya yace" bros mun sama yar aiki da gani zatai aiki sosai,  Mus'ab shima dariya YAYI yace" ato aikuwa zatasha aiki, ni yarinyar se aslow bawai tamun sosai bane,  Usman yace" tab Ina ruwana ai indai zatai aiki banda matsala da ita yana magana ya shige dakinshi ya fada kan gado

Koda ya fada kan gado, phone dinshi ya dauko naga yai dialing Wani suna ansa _HONEY_ Ringing  biyu ta dauka tace" heeelloooo Honey!  Wani nunfashi yaja yace" kai na a wuya Ina baki hakuri,  dayan bangaren tace" uhm how's you kai fa dama kirkinka kadan ne! Yace" hmm nasani 

Tace" to how far 

Yace" lfy lau kawai dai nakira kine mu gaisa,  tace" aiko nagode tnx tai katse waya, Suna gama waya tsaki yaja yace" *this girl kamar bata gane me nake nufi ba* ajiye wayar yayi baccinshi yasha,  shi kuma mus'ab yan shiga daki wanka ya shiga yasa karamar riga da gajeron wando ya fara chatting 😀


Husna na zaune hajiya ta kawo mata wani hadadden ferfesun Kaji lolz.  Naga wasu har sun fara hadiye miyau,  hade da shinkafa da miya ae zobo yaji kayan kamshi, tagode tace" a zuciyarta  kam taji dadi sosai dan yaushe rabon da taci irin wannan abinci,  tun randa aka kaita gidan *Oga* hamdala tayi a mind dinta,  sannan tai bismillah ta fara ci


     Cin abincinta take a tsanake, har ta gama ta kwashe kayan zuwa wajen wanke wanke, ta gama aikin da zatai musu sannan gajiya ta bata 100 tahau napep ta koma gidan da lokacin tashinta yayi, ta AMSA tai mata sallama sai gobe... 


       Koda ta koma gida ta tarar da yan wanke wanke,  batace komai ba ta Kama tayi kokcin islamiya nayi ta tafi









Ummiey Xeey

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*



Where  is Aisha A Muhd💋 your page is here... Kiyi yanda kikeso wannan page din nakine *ke kadai*


*PAGE 43➖44*


"Baba yace Allah dai yai miki albarka wannan yar" Ameen tace" sannan tai shigewarta gidan, tana shiga Allah yasa inna

 batanan dan haka tai sauri ta sa uniform din islamiya dan tayi latti, fitowa tai baba yai mata saita dawo. 

   Yau ma kamar kullun husna na zaune da aminiyarta Zainab take bata labarin wahalan da Usman yake bata kullun seyace tamai kaza tayi kaza, tana gama fada ta fashe da kuka" Zainab ce" haba Husna ai inda sabo kin saba kedai kiyi hakuri, Allah zai saka miki, kuma kici gaba Da addua Allah dai ya kawo mana chanjin rayuwa me kyau, Husna taji dadin maganarta tace" Ameen,  dan haka  Zainab  tace" to ki dena kuka dan Allah,  Allah na sane da komai Husna tace" hakane,  ranar dai Zainab  ta kwantar ma husna da hankali sosai


*Bayan kwana biyu*

    husna ce" a gidan aikinta yau tagama aikin da sauri,  tana zaune suna hira da hajiya farida, Usman ne ya shugo, yace ma husna  ta kawo mai abinci, tace to,  zata tashi ta nufa kitchen  yace" ba yanzuba dan anjuma irin 12:30 tace to,  

  Hajiya farida na jinsu tace" Usman kenan sarkin son girma, husna tace" uhm, kuma cikin ikon Allah kokadan Husna bata taba nunawa hajiya farida muguntar da usman ke mata ba. 


       12:30 nayi kwata kwata shi Usman yama manta sunyi da husna zata kawo mai abinci, yana daki shi da honey hajiya farida sam batasan abunda danta ke aikatawa ba kuma ko alama daya bata ganiba, Husna  ce ta mik'e  ta shiga kitchen  taji dai gabanta na fadi amma se ta share, abincin Usman  ta dauka ta nufa part  dinshi, murda abun kofar Da zatai kenan taga Usman da wata a a kwance suna iskanci,  ai sake foodflask din abincin tayi hade da kwalla wanni irin ihu, nan danan suka dawo hayyacinsu, Usman najin muryar hajiya tana Husna Meya farune? Kafin ta Iso yai maza yace Budurwan nan ta shige toilet ya kwashe kayanta yasa a wardrobe, ya zira jallabiya,  ya iso kusa da Husna wacce ta ke duk'e a kasa ta rike kai, saiga hajiya farida! 

          Tace" mai ya farune?  Cikin muryar shi na rashin gaskiya yace tuntube tayi, hajiya farida tace" ka fadamun gaskiya nasanka da masifa halan tsawa kai mata ko?  A'a yace" itadai husna na duke tanajin karya kiri_kiri


Hajiya farida ne ta Kama hannun husna ta mikar da ita sukai pallow, jikin husna ba inda be rawa, tunda take bata taba ganin abun da ya firgita taba kamar usman data gani, Usman kuma su hajiya da husna na tafiya wani  zufa yaji ya zubomai ta ko Ina,  da sauri ya jefa ma budurwan nan kayanta yace" maza ta saka,  itama jikinta na rawa ta saka yai maza ya bude mata kofar baya ta samu ta fice, koda ta fita hankakinshi be kwanta ba dan tsoro yakeji Husna zata iya fadawa hajiyarsu ko dan muguntar da yake mata


Gaban shi ne keta fadi Dan tsoron abun Da zai biyo baya yakeyi.. 


     Itakam hajiya Farida se tambayar  husna takeyi Meya faru, Husna tace":Tsawa yai mun na firgita, hajiya farida tace" ni nasani kiyi hakuri kinji,  nasan halinshi sarai, karki damu, husna tace" to hajiya itama dai karyan tayi  dan bazata iya Fadan abun da tagani... 


        Seda ta sarara bugun zuciyarta  yadan ragu,  sannan tace zata tafi!  Hajiya tace to shikkenan sai goben kinji ki gaida su  mamanki,  Sun fito kenan Sega  Usman,  wani harara hajiyarshi ta sake mai shi duk tinaninshi husna ta sanar da ita abunda ya faru! 

       

Daki ta Shugo ya biyota ta banka mai harara tace wuce ka bani waje katon banza..... Jin gabanshi yayi dassss ya fadi




       






Ku ci gaba Da biyoni hope  Kuna enjoying 



*For comment  Only*

08164640126










*Ummiey Xeey*

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


Dedicated  to *Meelat, & real khady* loves  you irin Sosai  dinnan 


*PAGE 45➖46*


Usman Jin gabanshi yayi ya fadi gham, Cije labe yayi yace Yarinyar nan zata sani yai wucewarsa daki ya goge kayan da husnan ta zubur, zama yayi a daki maganar hajiyarsu se maimaita ta yakeyi _wuce  ka bani wajen katon banza_  ji yayi ya kara tsanar husna,   

        Ita kam husna tun data koma gidan se kallon abun takeyi, kenan ba shakka ranar data kawo mai ruwan zafi tabbas muryar macen taji a dakin, abun se yawo a zuciyarta  yakeyi,  taba idan ma ta damu ita zata sha wahala seta share


      Shikam Usman kwata kwata da daddaren ranar kasa zuwa bangaren hajiyarsu yayi, Duk ya kusa safiya tayi yaga Husna  ya tambayeta ko ta fadama hajiyar ne

    Aiko Washe gari tana zuwa tun kafin ta Shugo gate ya tareta yace" ke zonan ya wani murtuke fuska, zuwa tayi yace" husna Kin fadama hajiya abunda ya farune?  Eh tace nafada sai mai?  Gabanshi yace gham,  shikkenan  na shiga uku,  ji yayi kamar ya kai mata duka dan haushi, kallon zaki sani yai mata,  sannan yace" wuce zamu hadu ai.. Gidan ta Shige  abunta


Tana shiga taga hajiya ta gaisheta, sannan ta fara aikin gabanta har ta gama,  


Usman na kofar gida hajiya ta kirashi a waya lokacin husna na zaune tace" kana inane?  Yace" gashinan a kofar gida  tace" ka shugo Ina son ganinka, gaban shine  ya fara dukan uku uku yace" shikkenan  yau karyata ta kare, wallahi yarinyar  nan zata sani, tazo ta sama gindin zama har da munafunshi ko, shi duk a tinanin shi Husna da gaske take ta fada mata, kuma maganar da yai mata yanasha ta kara zuwa ta sanar da hajiya ne.. 

         Shuguwa yayi da sallama yayi ya sama waje ya zauna a kasa,  hajiya tace" usman kai abun da kai ya dace kenan?  Kana babba!  Ji yai kamar yai fitsari a wando dan tsoro da kunya, kasa motsi ma yayi zufa ya fara zubumai, Hajiya ta jarau da cewa badakai nake magana ba? Me yasa bakajine? 

   Dago kanshi yayi idonshi yai ja,  yace" Dan Allah hajiya ki gafarceni, tace"rufemun baki kawai,  duk me aikin da ka kawo gidan nan sabida masifarka da da Shouting dinka sukesa subar gidan nan yanzu me Husna tai maka?  Wani sanyi a ranshi yaji kamar yai tsalle ya gane Ashe HUSNA bata fada gaskiya abun da yafaru ba

     Dago kai yayi yace" hajiya kiyi hakuri na miki alkawarin bazan sake ba,  yana kai maganar suka hada Ido da Husna, 


    Hajiya  tace" to shikkenan  kadai chanza for good Kaji?  Yace" ok hajiya ya mike ya shiga  daki CIKE da farin ciki yace" gaskiya yarinyar  nan tayi


Tun daga lokacin yaji yana sonta amma kuma bazai iya auranta ba saboda ya wuce da class  dinta sosai


        Zata tafine, shima daidai time din da ya dakko matarshi,  yace shugo in kaiki gida,  tace" a a,  Hajiya tace" Kaji dai husna ki shiga mana meye a ciki, zata shiga sit din baya ya juyo yace ni ba driver  dinki bane ki shugo gaba... Mtsww tayi, ta shugo gidan gaba suna tafiya ya kalleta yace" yanzu nasan zakiji a zuciyarki cewa InaSonki ko?  Allah ya kyauta tace" yace" good yarinya  kinsan gaskiya,  barama kiji dai dalilin da yasa nace zan fita har na ce ki shugo na rage maki hanya, Binshi  da Ido tayi ita sam kwata kwata be burgeta


Yace.....

          Ya soma magana tana kallon  bakinshi ta mirrow (madubi) yace" wallahi da kin kuskura kin fada ma hajiya wani magana,  da sai kin bar gidan nan kota tsiya kota arziki, tsaki tayi" yace kibi a hankal yarinya  kinsan dai da Wanda kike tare,  nan danan se tsoro yazo mata bata kara cewa komai ba


Se Surutanshi yakeyi itakam ko qala bata ceba,  har akazo dai dai layinsu,  tace" inka sama waje  ya kalleta  yace" meye  wani inka sama waje sai kace wani  driver dinki ai se kice akwai nan.. Ita dai duk ta kosa ta sauka tace  nan ne, yai parking  amma yaki bude kofar

       














Ummiey Xeey

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


```Dedicated  to my Bilkisu Bk & khady fresh.. Inaso ku sani Kuna da babban matsayi a hrt dina💋```


*PAGE 47➖48*


Ya kalleta yace" meye wani in ka sama waje sai kace wani driver dinki? Ai se kice akwai nan!  Ita kam husna duk ta kosa ta sauka tace"  to akwai nan


    Wani irin parking yayi, ta murda kofar zata fita taga Ashe ya kulle,  ce mai tayi dan Allah ka bude, yanda tai maganar ya shigeshi sosai har tsakiyar kanshi, binta DA Ido yayi shi kwata kwata ma ya manta me tace, Kara  magana tayi "tace Dan Allah ka bude mun kofar na fita,  A zuciyarshi Wow yace" kai wannan  yarinyar ta hadu ta ko Ina sedai kash bazan iya soyayya da itaba


Bude mata kofar yayi,  tai sauri ta sauka ta fada wani lungu,  dan tsoro takeji kar wani ya ganta yai mata mummunar fassara ko kuma akai gulma wajen inna ace wani mai mota ya kawota!


Tana tafiya se sake sake takeyi a zuciyarta  tace" Allah dai ya raba na gari DA mugu ameen


*USMAN*  bayan ya koma gidane ya hadu da abokinshi kuma kaninshi,  Mus'ab yake tambayarshi daga Ina yake haka da tsakar ranar ne!  Usman yace" aww yarinyar nan nakai gida, Mus'ab yace badai husna ba,  eh usman yace" mus'ab ne ya zare Ido yace don't  tell me you fall in love  with her Kodai yaudararta zakai?  

        Wani nunfashi Usman  yaja yace" ganinan  dai I like the girl  but tamun local da yawa, abokaina ai se sun mun dariya, sanin kankane yan mata ke biyoni amma aga na bige da soyayya da wannan?  Mus'ab dariya yayi sosai,  harda rike ciki yace" kai Allah dai yasa mu dace Usman  yace Ameen


°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

_Bayan Shekara daya, Usman gaba daya yasama Husna Ido,  kome takeyi idonshi kirr na kanta, zuciyarshi kam ta kamu da sonta..._


Inna ne zaune da Husna suna yar hiransu,  balle taga wata yakusan zuwa karshe, itadai burin inna kudi,  kudi,  kallon  Husna  tayi dakyau,  taga kyanta kara yawa yakeyi, tayi bul bul tayi fresh, da alama hutu ya zauna mata, Wani bakin ciki taji tace" aranta lalle ma har husna ta fini kyan jiki, mikewa tayi, ta dakko gyale fuuu ta fita se gidan Saude, Saude na ganinta tace" mutumiyar ya akai ne?  Nan inna ta zayyane mata komai,  Saude tace" kwantar da hankalinki,  meyai zafi? Ae se a chanza ko?  Inna kwashewa da dariya tayi tace" sai yasa nake sonki,  saude  tace uhmmmm


Sati, shekaru natayi,  kullun Son Husna na karuwa a zuciyar Usman, yau husna tazo aikinta ta gama da sauri, Usman ya shugo dakin Hajiyarsu  yaga husna zaune, kallo daya yai mata ya ga yarinyar fa k'ara  kyau takeyi,  ga dukiyar fulaninta sunyi girma,  nan danan shaidan ya fara mai huduba, Karfin hali yayi ya fita dan sab za'a iya samun matsala


    Daki ya shiga gabanshi ya fara dukan uku uku... To fa, Wata zuciya tace" ka fada mata mana wqta zuciya  kuma tace" Kaji tsoran Allah, Toilet  ya shiga ya watsa ruwa,  sannan ya kwanta,  yana kwance  kamar ance ya Leka window, husna ya hango tana kwashe shanya, kayan da tasa sun dan matseta, boobs dintane ya fito sosai duk da ba wasu manyan nan bane amma ya mata kyau sosai, kura idonshi yai akanta, yaga idan ya ci gaba da kallonta bazai iya  controlling  kanshi ba dan haka ya fada gado ya rungume pillow... Yana ganin siffar Husna

Kara matse pillow yayi a chest dinshi, nace to fa Aiki yaga maza.. 

    Ita kam husna basan ma me akeyiba wai kunu awani gida,  tana gamawa ta sako hijab dinta tayo gida, Sallamar da zatai kenan inna taci karo da ita a tsakar gida,  wani harara tai mata Husna tace" to ni kuma me nayi?  Sannu da gida tai ma inna wani harara ta kara balla mata, Shuru husna tayi ta sama waje ta zauna, ta fara tinanin abubuwa da dama, shurun da inna taga tayi a tinaninta saurayi take tinani, wani mari inna ta sake mata hade da cewa dan ubanki wato SOYAYYA kike YI KO?  


















Ummiey Xeey

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


```​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​```

*​​UⓂmiey Xeey Abakson​​*


*FB PAGE*    

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/​​


*EMNOOR AHMAD DON* Missing you badly 😭


*PAGE 49➖50*


Shurun da inna taga tayi a tinaninta saurayi take tinani, wani mari inna ta sake mata hade da cewa" dan ubanki wato SOYAYYA kike YI KO"?   

    Husna  ta fara KUKA tace" wallahi inna ba wani soyayya da nakeyi,  dawa zanyi?  Inna ta dakko bulala tai mata dukan tsiya tace" dan ubanki ni kike tambaya ko, Husna se kuka takeyi, seda inna tai mata ligis sannan ta koma daki,  Ita kawai inna haushin husna takeyi,  Dan harsashen da takeyi  ba gaskiya bane! 


Husna daki aa shiga taci kuka sosai,  tace" Ya Allah ka sakamun,  Allah ka kawomun mafita, ni na gaji da wannan wahalar, tagama kukanta ta kwanta a dan karamar katifanta, abun tausayi.. A yan kwanakin nan dai husna bawai zaman dadi takeyi a gidan nan ba,  kuma ko taje gidan Aiki,  shima Usman  yai ta kallonta duk tabi ta tsargu,


Haka dai RAYUWAR husna ya kasance yau dadi gobe bakin ciki,  ita kwata kwata batajin dadin rayuwarta, Sedai tai ta addua, Allah ya kawo mata mafita.. 


Kamar wasa husna na zaune yau ma kamar kullun hajiya batanan, ta gama aikinta ta dakko wata rigan shan iska dan lokacin zafine, taga ba kowa a gidan,  tasa dan batai tinanin ma Usman nanan ba! 

         Tana zaune se Usman ya shugo dakin, wani irin kunya taji, kuma idan tace zata tashi ta dakko hijab kunyar zatai yawa dan tsab usman zeta kalleta, ba yanda ta iya hakanan ta zauna, usman ya gama abinda zaiyi ya fita yana lura  da ita, 

      Seda ya shiga daki wata zuciyar tace" kai wallahi banzane,  ga yarinya available  kai abun Da zakai da ita amma kaqi,  nan Take ya kwalla mata Kira yace ta kawo mai Apple juice din dake cikin fridge, "To tace" ta TASHI ta dakko hijab dinta tayi dakin tana shiga ta shugunna tace" Gashi,  mikewa yayi ya kulle kufa,  ya kalleshi tace" Usman  me kke nufi? 

     "Abunda zuciyarki ta fada miki shi nake nufi a cewar usman" gabantane ya fadi Sosai tace" na shiga uku na lalace,  Wuka ya dakko mata yace" wallahi idan kikaimun ihu,  sai na yankaki ba Wanda ya sani! 

    Husna tsugunnawa tayi a gabanshi ta fara kuka ya toshe mata baki,  tana Dan Allah kar kai wannan mugun aiki dani, Kaji tausayina,  Rungumeta yayi tana tureshi,  yace" Ina sonki ne Husna,  wallahi sonki ne ya jefani zan aikata wannan abun dake, 


Kara rok'anshi sosai takeyi amma Ina banza da ita tayi,  turata gado yayi,  tun tana ihu har na dena jin ihunta,  seda Usman yaci ma burinsa sannan ya kyaketa,  Husna kuka sosai tayi,  ta samu dakyar ta fito a dakin lokacin still ba kowa a gidan, ruwan zafi taje ta saka ta gaggasa jikinta Dan kar a gane zuciyarta cike Da bakin ciki,


Ta gama shiryawa kenan zata tafi Sega hajiya farida ya shugo, kallo daya tai mata tasan something is wrong,  Hajiya farida ne tace" Husna Meya faru, kikai kuka ji yanda idonki duk ya kumbura, Nan Husna tai maza tace" hajiya yau dakyar nai aikin nan kaina ne keta ciwo,  Hajiya tace" ayyah sannu Allah ya kara sauki, Husna  tace" Ameen hajiya ta dakko magani ta bata tasha,  husna zata tafi kenan Hajiya tace" bari ba Kira Usman ko mus'ab duk wanda yake gida ya kaiki,  Husna  tasan Usman ne ke gida gabanta ne ya fadi dan kar suje hanya yai mata na biyu, tana zaune Hajiya ta Kira Uaman  yace" gashinan zuwa,  manyan kaya yasa kamar bashiba, yana zuwa Hajiya tace" ka kaita gida bata da lfiyane, To Usman yace" amma shi kanshi yasan abun da yai be daceba


Fita yayi husna na binshi a baya, taji kamar tace" bazata jeba Dan dai kar hajiya ta gane wani abune, hakanan  ta shiga Motar, Usman ya fara driving, suna tafe ba wanda yacema kowa komai, Husna idonta se zubar da kwalla take, tana ganin inda zai bi ya sadasu da gidan  su taga be beba,  ya bi wata hanyar a zuciyarta  tace" Shikkenan  yau sai Allah,  Ina kuma zaije da ni duk wanda yai mun be isheka bane?  Tana maganar ne amma sam batasan ya fito fili ba.. 

      Shuru yayi da alama ta batashi tausayi,  yace" Dan Allah Husna kiyi hakuri,  wallahi sharrin shaidan ne kuma Dan Allah Ina rokanki karki sanar da kowa ki rikemun alkawari,  bawai nayi wannan abun da in bata miki rai bane,  wallahi Sonki ne ne ya hanani sukuni har shaidn yaci galaba akaina kiyi hkuri Dan Allah,  banza dashi tayi idonta se zubda hawaye yakeyi... 















Ummiey  Xeey

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


*PAGE 55➖56*


"Nan take Take Malan ya rubuta mata saki daya abun da bai tabi yi mata kenan ba" sanan ya mik'a mata

      Inna bawai ta iya karatu bane, yar ta khadija ta Kira tace dubamun me babanki ya rubuta,  Zare Ido khadija tayi tace" ya sakeki saki daya, Khadija runguma m amanta tayi se kuka tare sukeyi,  inna tace" yau na shiga uku,  Ina zani tsofai tsofai dani,  wallahi ba inda zanje,  baba najinsu yai banza dasu tuni yaje wajen me ung ya sanar dashi yar da suka bashi ga abun da ya faru nan! 


        "Ita kam Husna koda ta fito tafiya take dai dai wani bakin titi tana tafiya Sega Wasu Samari su Biyu Manya a kalla zasukai 32years cikin Wani babban mota kana gani kasan motor  manyan yarane (big boys) ta yanko titin kenan tana tafiya hankalinta  gaba daya be jikinta, su kuma Gasu sun danno Motar da karfi wani wawan birki suka ja,  ji kake _kiiiiyy_ mufeed ne da yake driving yai sauri ya tsaya suka fito tare da farouk da yake zaune dayan bangaren

     Farouk ne ya kalleta cikin tausayawa yace" Baiwar Allah Ina zaki haka baki ganine?  Bin su tai da kallo seta tuna ranar da aka saceta,  ta gansu guys din masu kyau tace a ranta ya Allah kasa ba dasu na sake haduwa ba,  jin shurun da sukai  batai magana bane Mufeed yace" aboki kamar bata magana fa,  kasa tai da kanta tama rasa me zatace masu, Farouk  ne yace" nima naga alama,  yanda bata maganar nan idan zamu temaka mata ya zamui kenan? Wuya zamusha Kawai,  Mufeed  yai tsaki yace gaskiyane,  mu shiga mu wuce kawai Allah dai ya tsareta daga sharrin  mugaye Suka juya suka nufa motarsu, kararaf Sukaji Tace" Ameen wai gowa sukai Abun ya basu mamaki!


Farouk yace" ikon Allah dama kina iya magana tun dazu Muna magana kikai banza damu?  Kuka ta saki tace" inayi Dan Allah ku temaka mun Dan Allah,  Farko Sunji tsoro dan a zamanin nan ba kowa zaka gani ka temaka mai ba...,  Farouk  yace" zamu temaka maki,  mufeed shidai Binsu da Ido yayi, Farouk  yace" mufeed bakace komai ba!  Agogon Hannunshi ya kalla yaga 10:00 ya kusa yace kasan munada aiki a office ko,  just ta fada mata tsakaninta da Allah ita mutun ce kar muje ku dakkowa kanmu,  HUSNA  tace" Wallahi Ni mutun ce,  Okay yace sannan yace mata ta biyosu in badamuwa Insha Allah zasu temaketa, tace to nagode, bude sit din baya tayi ta sama waje ta zauna,  mufeed  ya fara driving be tsaya ko inaba Se babban court  din dake katsina, suna shiga suka sama parking  space sukai, Farouk  da mufeed har sun fito 


     tace" musu Dan Allah yunwa nakeji, Mufeed  ya kalleta yace" ok zaka KAWO maki abinci yanzun nan kuma kar ki sake ki fita daga Motar nan kinajina ko? "Eh tace"  ba' ai minti 5 ba Sega wata mata dagani ma'ai kaciyar wajen ne irin masu saida abinci nan ta KAWO mata abinci lafiyayye ta amsa, ta fara ci, a zuciyarta  tana cewa oh ni husna rabona dacin wannan abincin tun Ina gidan Su Hajiya farida nan ta fara cin abinci  har ta gama Sannan tadan takura kadan tayi bacci a sit din bayan Motor

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°


Shi kuma Usman kwanciyar da yayi ba sai zazzafan zazzabi ya kamashi ba,  kan kace meye jikinshi ya fara rawa sai yunkirin Amai yakeyi,


Gabanshi se dukan uku uku yakeyi, Su hajiya farida da mus'ab da autarta suna zaune a pallow se jamamin rashin husna sukeyi, hajiya farida ne tace" jeki dubamun yayanki a daki, ya kan nashi, tana shiga taga halin da yake ciki da gudu ta fado kan Mamanta tace" mummy Uncle Usman  zai mutu,  da sauri dukansu suka nufa dakin,  yanda suka Ganshi sunyi mamaki sosai,  nan take hajiya ta Kira abbansu da yake be gari yace ga doctor  Abubakar nan zaizo dubashi ya jikin nashi?  Hajiya tace da sauki, Yace" Allah ya Kara sauki tace" Ameen 









Ummiey Xeey

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


*PAGE 51➖52*


Shuru yayi da alama ya batashi tausayi,  yace" Dan Allah Husna kiyi hakuri,  wallahi sharrin shaidan ne kuma Dan Allah Ina rokanki karki sanar da kowa ki rikemun alkawari,  bawai nayi wannan abun da in bata miki rai bane,  wallahi Sonki ne ne ya hanani sukuni har shaidn yaci galaba akaina kiyi hkuri Dan Allah,  banza dashi tayi idonta se zubda hawaye yakeyi,


Shurun da tayi, yasa yaci gaba da driving  har ya kawota kofar gidansu, Allah yasa ba kowa ta sakko tai maza ta shige  gidan, tana shiga Nan ba ba kowa a tsakar gidan inna batanan, Daki ta shige tasa kanta a kasar pillow tai kuka ma'ishinta,  idonta suka kara kumbura, duk lokacin data tino da abun setai ta hawaye,


Washe gari inna taga duk tabi ta chanza tai wani iri,  tace" wai meke damunkine? Husna tace" Inna kaina ne keta ciwo tun jiya,  Sannu tace" mata amma a zuciyarta Allah ya k'ara inna tace"


      Kwanan HUSNA  Uku ahaka bataje aikiba,  Duk Usman yabi ya damu dan ko yasan tabbas ta dalilinshine yasa Bata zoba, Musamman zai kintsa yaje layinsu ko Zai ganta amma Ina ko me Kama da ita be taba ganiba, Washe gari har Kwana 4 hajiya bataga Husna na ba, kintsawa tayi taje gidan,  ta sama Husna a wani daki a kwance duk ta dan rame, tai mata sannu da jiki har ta dan bata kudi Husna tace" tagode sannan hajiyar ta tafi! 

     Bangaren Usman  kuma hankakinshi ba karamin tASHI shima yai ba dan be ganin husna,  shima ya dan rame yayi duhu abunka da mara gaskiya

    

Tun daga ranar Husna bata Kara zuwa gidan ba,  hajiya tasha zuwa ta tambayeta ko dai an mata wani abun ne sai tace" a a ita ta gajine kawai, ahaka Har Hajiya ta hakura!


Usman kuma yayi kuka Sosai, Gashi bazai iya zuwa gidan yace" ta fito ba dan yasan ba zuwa zatai ba.. Amma kullun addua yake Allah yasa wata rana su hadu


   *Bayan wata daya* 

Inna na lura da Husna sab, kallonta takeyi dan gaba daya ta chanza, se laulayi husna takeyi,  ta rasa yanda zatai, itada ba zama da hijab takeyiba ba amma yanzu kullun cikin hajib da zubar da miyau,

       ""Yau Inna na zaune a tsakar gida Sega Husna ta fito da gudu tana kakakin amai, salati inna tayi tace" yau me zangani ba makawa wannan yar ciki gareta, Sa6a hijab dinta tayi se gidan Saude, Tana zuwa aikuwq tai sa'a Saude nanan tace" zo ki tayani gani! Saude da gulma, ta biyota suna  shiga gidan suka  ganta se kakarin Amai take irin na masu laulayin nan,  Salati itama Saude tayi tace" tab a wannan gidan.?  Ke Dan ubanki wayai miki ciki,  gabantane ya fadi russs,  ta mik'e daidai  da shuguwar Baba kabir


Baba kabir najin hayaniya,  yaje wajen yace waye ba lafiya? Inna tai wani dariyar mugunta tace" husna ce ta dakko mana abun magana!  Ciki gareta, baba kasa tsayawa yayi yace" CI me?  inna tace" Ciki mana,  ai ga irintanan,  ita yar so ko?  Yar da tafi yqr cikinka ai GATA gaka nidai bazata zauna a gidan nan ba wallahi, dama abun da inna take nema kenan, nan ta fara sababi, Kan kace meye unguwa ya dauka Husna tayi ciki


        Baba daki ya shiga ya Kira Husna wayai miki?  Sedai tai ta kuka ba AMSA,  ranar kwarai baba yai mata fada sosai,  abun ya bashi mamaki matuka,  a ranar Husna ba wani bacci tai ba, cikin darene ta tashi ta fara tinanin guduwa a gidan Dan ko ta zauna bawai zaman dai zatai ba, Harhada  kayanta tayi, duk ta kosa asuba tayi........ 














Ummiey Xeey

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


```Dedicated this page to```

Biebie Dee🌸

Mar°Ahmad

Ruqeey Ce

        I love you guys😍


*PAGE 53➖54*


Cikin darene Husna ta tashi ta fara tinanin guduwa, dan tasan muddin ta zauna a gidan nan to tabbas ba zaman dadi zatai ba, habaici ma kadai zai ta ta kusan mutuwa dan inna bawai sonta takeyiba, 


     Harhada kayanta tayi duk ta kosa asuba tayi,se kallon agogo takeyi amma Ina gani take kamar ba tafiya yakeyiba, Kiran sallar farko taji wani irin dadi, fitowa tayi tai alwala tai raka'atanil fijr ba ita ta mike akan Sallayar ba har se da ta idar da asuba, Khadija  ta tayar tace kije ki alwala ki sallah, lokacin baba shima ya fita, tana ganin khadija ta Shiga bandaki ta tattara inata inata tasamu ta fito waje, koda Khadija ta dawo dakin bataga Husna ba,  bata damuba dan tasan Husna  intaga dama tun asuba take tashi ta fara aikace aikace sai yasama bata damuba. khadija  na idar da Sallah ta koma  bacci  abunta


Ita kam Husnah tana fitowa,  rasa inda Zataje tayi,  ga se zubar da miyau  takeyi,  ga yunwa tanaji daka ganta seta baka tausayi,  tafiya takeyi amma sam batasan Ina zata tafi ba tace Oh yanzu *RAYUWAR  WASU* Haka take, zuciyarta  tace kema ba gashinan ba yanda rayuwarki ta kasance,  wani zafafan hawaye suka zubo mata tace " ya Allah ka dubani kasa Alheri ne wannan tafiyar. 


    Gari ya waye rasss baba yaji shuru husna batazo ta gaisheba, a tinaninshi Fadan da yai matane yasa batazoba,  aiken khadija  yayi yace taje ta kiramai Husna, Khadija  tace" baba wlhi nima ita nake nema tun da asuba ban gantaba,  nan take baba yaji gabanshi ya fadi Gham! Yace" me kikace?  Tace tun da asuba baba nima nake ta nemanta,  Inasha ma tana aikin cikin gidane na tashi banji motsinta ko kadan ba, baba Inna ya kwalla na Kira yace" gashinan ae Kinsa asma'u ta gudu ko ke abu me kyau ne haka?  Ko akwai wanda ya wuce kaddarane?  Nan Inna ta fara masira tace" to ni Ina ruwana,  ni na aiketa tai cikin?  Ko da tai ai bani na koretaba,  Baba Yace" kece mana jiya fa inaji kikace badai ta zauna a nan gidan ba, Wallahi  idan bakije kin nemo taba ranki zai mugun baci,  mtssw tace"sannan ta dauka hijab, ta fito, koda ta fito,  koda ta fito bata wuce ko Ina ba se gidan hajiya farida, a tinaninta ko nan zata

     "Inna na shiga ta samesu duka a pillow tai sallama  dagani sunsan hankakinta ba kwance ba,  tace" Husna tazo nan gidan tun asuba bamu ganta, hajiya farida tace" kai Wallahi Husna batazo ba wani abun ne ya faru?  inna bata tsaya ce musu komai ba ta juya, *Usman* kuma ana cewa ba aga Husna ba wani mummunar faduwa gabanshi yayi,  a zuciyarshi  yace *NINE SILA* innalillahi, nan take ya nema natsuwarshi ya rasa,  har hajiya farida  ta lura dashi tace" Usman Meya farune?  Yace" wallahi wani irin ciwon kai naji yanzun nan,  tace" ayyah Sorry je kasha magani ka huta, Nan sun shiga jimamin to Ina Husna zataje? 

         

Mikewa yayi tana tafiya wani duhu duhu yake gani,  daki ya shiga ya kulle ya fara wani irin kuka, se Alokacin ya Kara nadaba yasan tabbas abunda daya aikata ba abu me kyau bane,  dadin dadawa ma yasa tabar gida,  cusa kanshi a cikin pillow  yayi yaci gaba da kuka Sosai seda yai ma'ishi sannan yadanyi shuru bawai dena kukar yayi ba....

     Koda ya dan tsagaita da kukan,  innalillahi yaketa fada, waata zuciyar tace ka tashi ka fita ko Zaka ganta kabata hakuri  akan abun dakai mata,  har ya mike  ya dauka mukulli,  wata Zuciya kuma tace" yo inka fita kanada tabbacin Inda zaka gantane? Dawowa yayi ya fada kan gado luuuuu... 

               *************


Inna kuwa tafiya take tama rasa Ina zata sa kanta Dan tana komawa baba yace Ina Husna tace" bata gantaba to ba karamin bacin rai zata taddaba,  taci nemanta har ta gaji ba yanda ta iya dawowa gida tayi,  

   Tana shuguwa baba wani irin kallo yai mata alamar Ina Husnah? ita kanta Tasan itace silar barin Husna gidan. Kuka ta fara tace" Mlan duk inda zanje ko Zan ganta Wallahi ban ganta ba.. 

     Nan take malan ranshi ya baci ya rubuta mata saki daya.. Abun da bai taba yi mata kenan ba












Ummiey Xeey

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


*PAGE 57➖58*


Usman ne kwance su hajiya na kanshi, Karar knocking din kofa sukaji, Mus'ab ne yaje ya bude kofar, yana budewa doctor ya gani ya mai iso har cikin dakin, Nan doctor  ya fara aikinshi ya mai gwaje gwaje, har ya gano BP dinshi ya dan hau, nan yasamai ruwa yamai duk abun da zai mai yace" zai tafi idan akwai wata matsalar akirashi "Su Hajiya sukace to shikkenan mungode"

    Da fitar dashi,  hajiya taga jikinshi da dan sauki take tambayarshi me ya faru har BP dinahu yayi high, "usman ce wa yayi ba bakomai hajiya, Tace" hmm naji dai amma ban yardaba bari dai naje na daura mana girki mus'ab ka kula dashi Ina zuwa,  tai ficewarta, 


Da fitar tane" mus'ab ya kalle bro dinshi yace" yaya kasan dai baka da aboki kama ni ko? Kuma damuwarka tawace ko?  Usman "eh yace amma kwata kwata be so mus'ab ya fara wannan maganar ba yasan inda ya dosa,  Gashi Usman din ba yanda zayi dole ya fadamai gaskiya, 

   Musa'ab yace to Dan Allah meke damunka? 

Usman  ya fara magana idonshi cike da kwalla yace" nayi babban laifi, na aikata HARAM, wallahi nine sanadiyar barin Husna gidansu, Mus'ab ya sake baki yace" ammm banganeba, 


Usman mikewa yayi daga kwaciyar da yake yace" nayi taping  din Husna, dalilin da yasa ta dena zuwa nan kenan kuma nasan ma ba zata a gidan su zatai ba kagani duk na naja yana kaiwa karshe ya fasa kuka

     "Innalillahi wainna ilaihi rajiun mus'ab yace hade da fadin why Yaya Usman  me yaja ka aikata haka?


Usman  yace" hmm kabari kawai tsautsayi da sharrin shaidan,  nan Usman ya sanar dashi tun farkon abun da ya fara hadasu na ganin shi da tai da wata tun daga lokacin shima yaji yana sonta,  Wani nunfashi mus'ab yaja yace to shikkenan yanzu dai aikin gama ya gama, Sekai  ta Istighfari kuma dan Allah kar ka sake,  ita kuma Insha Allah zamu bazama nemanta se inda karfinmu ya kare!  Usman  yaji dadi har cikin ransa yace" to nagode nan dai Suketa hirarsu har hajiya ta dawo taga jikin bashi ma da sauki,  a ka samakai abinci yaci har drip  din ya kare amma ka ganinshi kasan akwai damuwa cikin Ranshi,


Hakadai ranar wunin usman ya kasance duk a takure yai wani iri


••••••••••••••••••••••••••••••••••••••

Bangaren Su Mufeed kuwa bayan sun shiga court (kotu) ha sun gama judging wani case suka fito dashi da Farouk suga shiga cikin Motar zasu wuce kaduna,  su sun ma manta kwata kwata akwai wata Husna  a cikin Motar 

    Farouk  ne ya kalleta yace" kalle,  se sharar baccin ta takeyi,  muffed  yace" oh yanzu ya zamui da itane?  Farouk  yace" why not ka wuce  da ita part dinka tunda ba kowa? Ni kaga akwai matsala?  Mufeed yace" Allah ko? /Farouk  yace yes gaskiyar kenan kaga se idan muka gama bincike akanta se musan abun da zamui,  Mufeed  yace" hakane, Allah yai man jagora sukace Ameen,  Mufeed  yaja mota suka wuce


Suna tafiyane Husna ta farka daga bacci, abunka da mai ciki ta fara tara miyar a baki, Farouk ne ya waigo yace lafiya?  Se yunkirin amai take kan kace meye tayi amai a Motar,  Mufeed kam be dena driving  ba yana kallonta  ta mirror  a zuciyarshi  yace" hala ma irin yaran nan ne da basajin magana,  taje tayi ciki dan *RAYUWAR WASU*  haka take, Farouk  na ya kalle abokinshi ya juya harshe da turanci  yace" _like she's pregnance_ Mufeed  ya daga gira yace" _hmmm that's  what am thinking,_ but koda yake duk wani bayani yana wajenta,  muje kawai.... Suna tafe suna hirarsu har suka isa Ung dosa inda Mufeed  yake kenan!

[3/27, 11:13 AM] UⓂMIEY XEEY😍: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂

WANNAN PAGE DIN nakane Alone.. *HAYATU BABA ZUBAIRU✍🏼* Wishing an amazing day and many great things to come to youuuu.. 

   *HAPPY BIRTHDAY TO YOU*

*/ღ˚ •。* ❤ ˚ ˚✰˚ ˛★* 。 ღ˛° 。* °*❤

🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂


*PAGE 59➖60*


Yana shiga ya sama parking space yayi, Farouk  yace" kalle har yanzu ba bacci takeyi ya zamui kenan, "Mufeed ne ya dan bubbugata yace tashi" afirgece ta tashi ta fara waige waige shap tama manta a inda take, Farouk  ne yace" ki fito mana jin kafarta tai nauyi dakyar dai ta samu ta sakko suna tafe tana binsu a baya,  

       Wani dan madaidaicin falow taga sunshiga, Mufeed ne ya zauna se Farouk shima dan haka itama ta zauna, se tinati takeyi a zuciyar ta Allah dai yasa ba yan iska bane, kardai ace sun yaudareta ta biyusu sui abun da zasui da ita Dan tasan wasu mazan haka suke,  shuru  tayi, Farouk  yace" to Alhamdulillah, yanzu dai abunda mukeso dake shine  ki sanar damu, dan kinsan zamanki anan bazaiyuba ko?  Eh tace" tana shirin yin kuka dan gaba daya ji tai ta tsana rayuwarta, farkon wanda sukafara salwantar mata da rayuwa shine yan yankan kan nan da suka dauketa da yanzu tana tare da iyayenta

   "Mufeed ne yace munajinki ba kuka zaki mana ba kuma tsakaninki da Allah mukeso Insha Allah zamu temaka miki,  nan ta fara kuka tana sanar dasu duk abun da ya faro ds ita, tun daga ran da iyayenta sukai accident aka saceta, ta samo ta kubuta tazo gidan Malan kabir, Inna bata sonta, har Dai Allah yasa aka neman mata aiki Daganan ne Wannan iftila'in ya sameta, nan Inna ta fara bala'i wai badai gidanta ba to a tinani na idan ba gidan na bari ba ba samun kwanciyar  hankali zanyiba, shine na gudu har Allah yasa na hadu daku,  Bata boye masu komai ba ta fada.... Wani irin tausayi Farouk yaji tana bashi,  Mufeed  kam kasa komai yayi ya kalleta yace" ke inkinsan karya kike mana ki fada mana gaskiya Dan mudinnan da kike gani lawyers  ne,  kar mu yanke hukunci yazo ba haka bane, kuma idan. Mukai finding  out mukaga karyane wallahi zaki fuskanci hukunci... Husna kuka takeyi sosai tace wallahi maganar nan da nafada muku ba karya bane, Wani munfashi Mufeed yaja... Yace" zaki iya kaimu gidan da kika fito?  Akwai abun da zamui ne, tace" eh Zan kaiku yace" ok... Zamui magana akai anjuma, yanzu ga wannan dakin,  ya nuna mata wani room yace" kome kike bukata akwai a ciki, idan kuma wani abu kike so ki dinga sanar dani... To tace


Ta tashi ta shiga dakin  fadawa akan gado tayi ta fara kuka mecin rai,  tace" oh ni rayuwata haka zata kare?  Farouk ne ya leko, yace" ki dena kuka Insha Allah zamu tsaya miki... 


              ********************

Bangaren su Usman kuwa har yanzu be dawo normal ba duk lokacin da ya tina shine sikar barin husna gidan bejin dadi*


     Washe gari kamar yanda yai alkawarin zaije nemanta, tun wuri ya tashi shi da mus'ab brother shi sukai wa mamansu karya akan zasukai ziyarane, tace" to adai kula da hanya kuma Karku dade, to kawai sukace suka mik'a Hanya, tafiya  suke duk lungu da sako da sunga dandazon mutane sai sun Leka, ko wata mace sukaga tana tafiya sai sun bita har gabanta dan gizo suke musu sesuga tamkar HUSNA... sunyi yawo ba iyaka, basu gantaba,  hakan ba karamin daga mai hankali yayi ba


Sungaji da nema basuganta, they have no option hakanan suka dawo gida,  koda shigarsu gida hajiya taga Usma wani iri take tambayarshi me ya faru!  Cemata yayi kawai kanshi ke ciwo!  Tace yasha magani ya kwanta,




[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


*Thank you all masoyana.. Nagode sosai da Addu'a.. Nasama sauki Alhamdulillah.. Allah dai yabar so da kauna... I love you plenty*❤❤


       *•••AISHAN UMMA TA•••*

  _Ina Tayaki murnar kammala littafinki me suna *MEELA_ADEEL* kinyi kokari sosai... Allah ya Kara basira sweet mamma na_

❤❤❤❤❤❤❤❤❤❤❤


   

*PAGE 61➖62*


_Washe Gari_ hakanan usman ya tashi da matsanancin ciwon kai shi komai ma bemai dadi.. Gashi yanzu shikkenan bazai sake ganin husna ba! Hakanan ya tashi ya dauro alwala yazo tai Sallah, ya roka Allah, Allah ya Kara shiryashi, Kuma Allah yasa duk inda Husna take tana hannu na gari


Yana idar da adduan.. Kwanciya yayi akan sallayar,  Sega Mus'ab ya shugo, ganin yanayin da yake mus'ab ya tausaya mai matuka... Ya dafashi Yace" bro Sekace ba jiya doctor yazo ya dubakaba?  Kana tinani da yawa idan Hajiya ta gano kaine silar barin Husna gidan kasan ranka zai baci... Just be strong  plz kamanta da komai


Wani kirkikar murmushi Usman yayi Wanda beyi niyya ba yace ok dear bro..nan Mus'ab yace hmm you see since morning bakaci komai ba kalle breakfast dinkafa! Zanci usman yace" mus'ab yace better ooo!! 

  

     Bangeren su Mufeed kuwa Tun jiya bayan fitarsu da farouk kasuwa sukaje suka dan siyowa Husna kaya, da duk Wani Abu dai da 'ya mace take bukata suka kawo mata, tayi farin ciki sosai. A mind dinta taji dadi tace' oh watakilama da ko gidan iyayena nake  bazan sama haka ba


       Bayan kwana biyune Mufeed na fallow yana zaune ita kuma husna tana Bed room Wani Irin ihu me firgitar da mutun yaji Husna tayi,  da gudu ya leko dakin me zai gani? Jini yagani yana kwarara a kafarta... Subhanallah yace" da Sauri ya isa gunta yana Sannu,  Sannu baiwar Allah.. Saboda Wani Irin juyo da cikinta ke yi kasa amsamai tayi, daukarta yayi yayo waje da ita yana shirin Sata a cikin mota kenan Sega Hajiya mahaifiyarshi ta window ta hangoshi, ta Kara kallonshi rik'e da husna a hannu ga jini na biyo kafanta, Ihu ta sake hade da fadin INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUN tace" jin Muryan mamanshi yayi kafin yasa husna a mota har mahaifiyarshi ta fito tace" mufeed mezangani yau?  ta fasa kuka... Nan itama ta fadi kasa sumammiya... 


              °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

Bangeren Su ainihin iyayan Husna kowa su sun sadakar ma GABA daya husna bata a duniya.. Dan kullun Addu'an Allah yajikanta da rahama suke.. Allah sarki..

     Bangaren Malan kabir kuwa Rayuwa yamai kunci, kullun ya tino da halin matarshi sai yayi tir dashi,  Irin matan nan ne na yayansu sune yaya, 'yayan Wasu kuma oho, Wani kwalla ke shirin zobomai, ya dake, dan kullun harsashenshi zai ga husna.. Addu'a yayi yace ya Allah kasa tana hannu nagari.. Ameen 

          

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

Mufeed na tsaye yaga mahaifiyarshi ta fadi, nan hankalinshi yai matukar tashi, dakyar ya samu yasata a Mota itama, Be wuce da su ko inaba sai asibiti,  Ana zuwa Kowanne aka bashi dakin Da zai kwanta.. 

    Ana shiga da husna aka dubata aka sanar da Mufeed cikin dake jikintane ya bare.. Alhamdulillah a zuciyarshi yace" Sannan ya Kira Babban aminshi yake sanar dashi ga abun dake faruwa ba... Nan take ya sanar da matarshi yace please ta daure ta hada mai ruwan zafi da abinci yanzu zasukai asibiti

    

         Ummi ce matar farouk ta tambaya waye ba lafiya?  Yace my dear please idan munje kya gani, ta lura yana cikin damuwa that's why amsar daya bata taja bakinta tai shuru taje tai abun da ya umurceta, ba'ai 40mins ba ta gama duk abun Da zata, tace" mai nagama mutafi ko? 

    Ok yace" ya dakko key suka nufa asibitin

    

Suna shiga suka ga mufeed a reception yana zaune alamar shima be kwanciyar hankali,  tasowa yayi ya karaso inda Suka suka gaisa yace' muje ko!  Dakin mummy suka fara zuwa sukaga bata farkaba dan haka suka wuce inda Husna take, tana kwance suka shuga, Inda take suka gaisheta da jiki, tace" Alhamdulillah,  Ummi matar farouk Tun shuguwarta taga yarinya kyakkyawa ta fara tambayar kanta shin waneni wannan kuma? Meya hadasu da wannan?  Gata dai badai Irin wayayyun nan ba amma gaskiya she's damn beauty, nunfashi taja tace baiwar Allah sannu?  Husna ta daga kai a mind dinga tace" tabbas ko ba a fadamun ba wannan matar farouk ce dan na Tina randa suka dakkoni,  farouk yace" ba yanda za'ai na kaita gidana saboda inada mata!! 


    Sunyi kusan 30mins A dakin Farouk  yace" ummi matarsa ta koma gida zaizo.. Bataso haka ba dan ba yanda zatai ne yasa tace" ok.. Taso ta zauna yaji kwakwaf wannan kuma waye? Dan haka tai tafiyarta amma zuciyarta dam yake da tambayoyi













*Ummiey Xeey*

[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


*Dedicated  to Muhammd lawal❤... Nagode sosai da son book dinnan da kake*


*PAGE 63➖64*


Ummi tafiyarta tayi amma zuciyarta cike yake dam da tambayoyi.. 

     Bayan ta tatafine, farouk ya sake kallon Husna yace" sannu tace" yauwa. Sannan ya maido kallonshi kan Mufeed yace" kaima sannu da kokari!  Zai amsa kenan Sega wata nurse ta shugo tacewa Mufeed mahaifiyarka na Kira, Husna najin haka gabantane ya fadi gham tace" yau kashina ya bushe

     

  "Kallon Husna yayi yace mata Muna zuwa" daga kai kawai tayi


Su Mufeed suna shiga yaga ran mahaifiyarshi a bace yace" sannu hajiya, kin amsawa tayi,  farouk ne ya gaisheta Sannan yace mata ya jiki? Ta amsa da dasauki, Sannan hajiya mum din Mufeed tace" Mufeed yanzu abun maganan, daka dakkomun kenan KO?  Wato mace ka kawo Daki kana abun dakaga dama KO? Sai yasa yasa yan kwanakin nan na rasa gane kanka, to Yau ALLAH ya Tona maka asiri

    Ba Mufeed ba hatta Farouk seda ya girgiza akan maganar hajiya, hawaye Mufeed ya fara, Farouk ne yai karfin hali yace" Wallahi hajiya ba hakabane, Rufemun baki tace" Sannan ta Kara da cewa kai me yasa baka kaita dakinkaba,  AI kaga kanada mata, dukkansu shuru sukai kamar Wanda ruwa ya cinyesu, hajiya tace" *only Son* wuce kubani waje ka matukar bani mamaki... 


A fusace Su farouk suka fito dakin,  Mufeed ne ya dake hannunshi a bango yace" ya salam yanzu wazai fuskanceni? Na shiga ban daukaba bata fidda barawo, farouk yace" hakane kayi hakuri, Allah na tare damu kuma zai bayyanar da gaskiya insha Allah... Wani Nunfashi Mufeed yaja irin ran maza ya baci sosai... 


     Ita kuma hajiya bayan fitar Su Mufeed, waya ta daga tai calling din Alhaji mahaifin mufeed, yana Abuja..  yaji muryanta somehow yake tambaya lafiya kuwa?  Cikin shesshekin kuka take cewa" Ina asibitine Alhaji,  baban mufeed yace" meke faruwa? 

   Hajiya tace" Wannan Dan ne ya dakko mana magana! 

   Alhaji yace" too badai akan aikinshi bane KO? Hajiya tace" wata yai ma ciki!! Ci what?  Alhaji ya fada, Sannan yace ganinan zuwa komun dare

Ok tace" ta katse waya! 


       Bangaren Husna kuwa tun fitowar Su mufeed se addu'a takeyi Allah yasa ba maganarta akeyiba, Wata zuciya tace" kinama yaudarar kankine kinsan tabbas za'ai maganarki tana cikin tinani ne Sega Farouk  ya shugo dakin,  yaganta cikin wani yanayi yace meyafarune? Tace" Dan Allah nagode da taimakon da kukai nun amma Dan Allah wannar maganar Sirrine tsakanina dakai, karka bari abokinka yaji,  yace" ok inajinki

Husna tace" Dan Allah Zan gudu!! Zare ido yayi yace" mene? 

"Ta Kara cewa Zan gudu"

Ganin Mufeed kawai sukai a ward (dakin)


Basusan duk hirar da sukeyiba Mufeed naji, Daka mata tsawa yayi yace" You're very Stupid!!  A wannan yanayin da kike cikene zakice zaki gudu? Well you're free to go, kenan duk labarin da kika bamu karyane?  Kuka ta fara tace" Dan Allah kayi hakuri naga ta dalilinane mahaifiyarka ta kwanta a sibitin nan! Kuma wlhi labarin da na fada muku ba karya bane, mufeed ne ya kalleta, yace" yace" ahhh you don't have to worry,  mu mukace zamu temaka miki,  Kuma insha Allah,  Allah zai temakemu gaba daya.. Duk da dai batasan meye ya fada duka ba, amma hankakinta yadan kwanta tace" nagode. Farouk ne yace bakomai,  mufeed kam Ko A be Kara cewa ba!  Hakanan dai sukai spending kusan 30mins a dakin Sannan Suka fita, koda Suka fita, magrib tayi,  sallah farouk yayi Sannan tai musu sallama ya tafi wajen amaryanshi Ummi


Yana shiga ummi ta tare mijinta da hug, tamai sannu Da zuwa ya gajiya?  Yace" Alhamdulillah, Sannan ta hadamai ruwan wanka, yaje yayi,  after ya gama wankan ne yayo alwala time din ankira sallah isha'i,  ya gaji be samu yaje masjid ba Dan haka yayi a gida, yana idarwa ya matarshi ta kawo mai lafiyayyan jallof shinkafa da wake yaji manja ga kifi se kamshi abincin yakeyi, 

   "Ya kalleta cikin shaukin So yace" sweethrt kullun fa bana gajiya da wannan abincin naki, 

"Ummi tace Allah KO"

Farouk yace" yes dear 

Ummi tai smiling tace okay lemme feed you.. Shima smiling  din yayi yace da KO naji dadi yanda na gajin nan


Tana feeding dinshi suna hira seda tacika main ciki fam Sannan yace" sweet hrt Alhamdulillah I'm ok, 

Ummi tace" Masha Allah

Sannan ta tattara kwanukan wajen takai kitchen tadawo Suka fara hirar masoya

    Anan ne take tambayarshi wai wannan wacece dazu dasukaje gaisheta a hospital wannan tar budurwan!  Dan hade rai yayi yace" *YAR AMANA CE* tace" yar amana like how?  Yace yanda kikaji ankawo mana itane aka wani case ne Ok tace" Dan tasan irin aikinsu na lawyers









Ummiey Xeey

[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


_Dedicated to my sweet heart, my sweet cocumber, my chocolatey my Everything_ *REAL KHADY* you mean so much to meeee💪🏼💯


*PAGE 65➖66*


Farouk ne ya kalle matarsa ciki da tsantsar so, amma wani bangaren na heart dinshi kuma yana tino halin da Mufeed yake ciki, 

  Ummi ganin Farouk be cikin hayyacinsane tace" Sweet heart muje ka kwanta ko? OK Yace mata muje suka Shiga daki....


Bangaren Husna kuwa tana kan gado ga azaban cikinta na ciwo ga tinanin yanda rayuwarta ya kasance, kuka takeyi sosai a yayin da shi kuma mufeed se yawo yakeyi a cikin asibiti.


Around 10pm ne Alhaji Baban mufeed ya shugo asibitin..yana zuwa yaci karo da mufeed a reception wani harara ya balla mai sannan Yace" INA aka kai mahaifiyarka? Jikin mufeed na rawa ya shiga gaba babanshi na binshi a baya har suka Isa dakin da'aka kwantar da mahaifiyarshi


Da azama Alhaji ya Isa kusa da ita yana hajiya ya jikin naki? Da sauki tace" 

  Mufeed ne ya kalla babanshi dama be gaisheshiba Yace" daddy, you're highly welcome,INA wuni, kallon da dad dinshi kadai ma da yai mai yasan me zai fito bakinshi.. _I don't need your greetings!_ dad said" wani iri mufeed yaji a mind dinshi, Mahaifiyarshi ce tace" hmmmmm!


    Sannan ya kalle matarshi Yace" hajiya meya faru? Nan ta bashi labarin komai, tana tsayene ta window kawai taga ya dakko wannan budurwar yarinya  duk jini na binta, Innalillahi wa inna ilaihi rajiun dad Yace" sannan ya kalle mufeed Yace" Ashe kai mutumin banzane? Kenan karatun Dana turaka kasar waje Allah Kadai yasan ta'asan da kayi, dama hausawa sunce "kwana 99 na barawo, rana daya name kaya, Yau Allah ya tona asirinka


Zaiyi magana kenan! Babanshi ya daka mai tsawa Yace" don't say anything wuce ka bani waje, mufeed cikin bacin rai ya fito daga dakin zai wuce kenan Husna ta hangeshi fuskarnan ba annuri da alama iyayanshi suka bata mai rai kuma tasan duk saboda ita ne..cikintane ya d'ura ruwa a mind dinta tace" yau na Shiga uku,nasan wannan mutumin sai yadau hukunci yanda aka batamai rai!

  

      Shi kuma mufeed yana fita rasama Inda zaije yayi mota ya shiga ta saka karatun qur'ani sannan yadan sama natsuwa


Bangaren Iyayan mufeed kuma bayan mufeed din y fita, Alhaji ya kalle matar Yace" Hajiya saboda Allah kina mene har haka ta faru? Saida nace ban yarda ya koma part dinnan ba har se randa yai aure saboda irin haka yanzu ga shinan!

    Hajiya hankalinta gaba daya be jikinta tace" to Alhaji ya xanyi, Ko da a part din nawa yake lokacin da zai kawota ba Sani zanyiba, Alhaji Yace" kai Allah dai ya kyauta...Kodai dama ya taba miki maganar zaiyi aurene baki fadamunba? Hajiya tace" wallahi a'a kasan dai ko an mai ma maganar sai Yace" shi ba yanzu ba..


Oo oo ohh Alhaji Yace" Allah dai ya kara tsare mana zuri'an mu saboda Yayan Yanzu wasu da yawa ka haifesune baka Haifa halinsuba...Dan *RAYUWAR WASU* sedai muce Allah ya shirya..hajiya tace" Ameen


    *Washe gariii*

Tun wuri matar Farouk ta tashi ta sa ruwa a flask, Farouk ya shirya yayo asibiti, A waje ya sama mufeed duk yai wani iri yake tambayarshi meya faru?

    Mufeed Yace" kasan matsalar ai duk kan Husnan nan ne daga temako? Farouk dafa kafadar mufeed yayi Yace" kayi hakuri everything will be ok..

"Insha Allah mufeed Yace" sannan suka wuce dakin Su mum

    Suna shiga Farouk da mufeed suka gaishesu, amma suka amsa na Farouk sukaqi amsa na mufeed, kamar yai kuka amma ya daure

   Dakin yayi shuru na yan mintina sannan Baban mufeed Yace" Look Farouk inaso na tambayeka wani abu 

Ok Yace" Sannan dad yace,.........!



Kuci gaba fa kasancewa dani....











Ummiey Xeey

[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​*


*FB PAGE..* 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


        _​•••°°°Devoted  to......°°°•••_

*​​Miss Zarah Mansur😍​​*


```Find a heart that will love you at your worst and arms that will hold you at your weakest.```


*PAGE 67➖68*


Baban mufeed ne Yace" look Farouk, I want to ask you something

     Natsuwa Farouk yayi Yace" ok Daddy, shidai mufeed na zaune a gafe


Dad zai fara magana kenan hajiya tace" Alhaji ka dakata kawai wannan case din bananan bane Kar inji abun dazai kara dagamun hankali!


 Toooo Alhaji Yace" amma dai naso nayi magana, Gaban mufeed ne Yace" gham Amma wani bangaren na heart dinshi Yace" to tunda bakai kai ba meya dameka...

            Su mufeed ne suka fito, Farouk Yace" aboki karfa ka damu, kasan bakai kai ba wlhi ko a kunbanka, kabi ka damu ka hana kanka sukunu, Hmm mufeed Yace" kasan iyayanmu irin wannan bawai dauka da sauki sukeyiba..duk da bani nai ba walhi aka matsamun zance nine.

     Smile Farouk yayi Yace" karka fara laifin da bakai ma kace kai kayi, 

Mufeed Yace" to ya sukeso inyi? 

Farouk Yace" ka tsaya kan gaskiyarka ni zan wuce may sai zuwa anjuma..Ok Mufeed Yace ya rakashi har bakin mota sannan ya dawo..


Abubuwa dai birjik a mind din mufeed, ko aiki be cika zuwa ba kullun yana cikin damuwa abun tausayi..


        *Bayan Kwana biyu*

HUSNA taji sauki Alhamdulillah, itama haka mahaifiyar Mufeed taji sauki, Har an sallamesu amma basu tafi gida ba, mufeed na jiran Farouk, ba'ai minti 15 ba se ga Farouk yazo, nan ya gaishe dasu hajiya da Alhaji, 


Ita Kam husna tunda taji an sallamesu, ta ayyana a ranta insha Allah yau seta gudu, tunda tasan yau karyanta ya kare, Dan tasan ko Me zatai hajiya ba barin ta ta koma gidan zatai ba...to wai ma idan ta koma dakin wa zata zauna? Da wannan tininin na barta


Shi kuma mufeed da Farouk dama sun yanke shawarar idan suka kai Su mummy gida zasu dawo dole Su saman ma Husna waje Su kwato mata yancinta


HUSNA CE se leken Su mufeed take a dakin da aka kwantar da Mahaifiyarshi, Suna shirin fitowane Husta ta shugo dakin ta tsugunna

Hajiya, Alhaji, farouk fa mufeed kowa yayi mamakin ganinta, Alhajine Yace" wannan fa daga ina? Hajiya ta juyar dakai tace" itace yarinyar da nake maka magana ai, Wanda mufeed ya.....! 

Ohh Alhaji Yace" suna shirin fita kenan Husna cikin muryar tausayi tace" _Dan Allah Alhaji kuyi hakuri, d'an ku mufeed kwata kwata beda laifi, wallahi temakona sukayi, dashi da Farouk, nazone na baku hakuri akan Zargin da kukewa mufeed ba haka bane na rantse harga Allah_ 

su Alhaji da hajiya sororo sukai a dakin, Hajiya tama rasa me zatace" too too too tace, 

Zuciyan mufeed kam fari kal atleast zargin da sukemai Susan ba haka bane, Alhaji kuwa Bin Husna da ido yayi, Bayan Husna ta gama maganar ta kenan tace" to Mufeed da Farouk nagode, Ni na tafi sai wata rana, Yanda kuka temakeni Allah ya temakeku, tai mikewarta ta fice...


Mufeed kamar ya kamo gefen hijab dinta Yace" karta tafi amma ina ba dama! Hakanan yana gani ta fita.

     Dad ne Yace" to Mu tafi ko? Hajiya tace" eh me zamu jira, Nan Mufeed yaje ya tada mota, Farouk na dayan bangaren, Mum da dad kuma suna sit din baya Suka zauna...nan take ba bata lokaci mufeed ya fara driving.. 

    Tun fitar Husna hankalin kowa ya tashi balle mufeed, Ita kanta Mummy da Taga husna hankalinta yadan tashi, suna tafiyane amma Hajiya a ranta tana cewa Ya Allah kasa naga wannan yarinyar, 

Aiko mufeed na driving yasha kwana kenan! Sega Husna ta koma da baya da gudu saura kiris ya kabeta, Innalilahi Yace" yaja burki kiiiiii..

    

       Hajiya da hankakinta yafi kowa tashi tace" mufeed yayane? Shuru yayi fitowar da hajiya da Alhaji zasui kenan sukaga  Husna a doke a wajen tana cewa Dan Allah Ku kasheni, Ku kasheni na huta..nan take hajiya da Alhajin sukaji tausayinta.  Se a lokacin suma sukaji yanda yaronsu yaji 

Daya ganta, dole duk wani mai tausayi yaga Husna ya tausaya mata,


Hajiyane ta kama hannunta tace" kizo muje kinji, kamar Husna bazata bita ba hakana ta shiga motar Suka wuce gida...zuciyar Mufeed yai fari,











Ummiey Xeey

[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​​*


*​FB PAGE..*​ 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


          _•••°°°Devoted  to......°°°•••​_

*​​​Miss Zarah Mansur😍*


_Wannan page din sadaukarwa ce gareku manyan mata_

*Ruqeey ce*

*Mamin nasreen*

*Amina Ibrahim &*

*Mummy's frnd*

Ina yinku irin sosai dinnan💋💋


*PAGE 69➖70*


"Mufeed driving yakeyi amma gaba daya hankalinshi be tare dashi,

       "Husna kam tunda ta shiga motor in banda kuka ba abun da takeyi, hajiyane da Alhaji duke ta bata hakuri, akan tayi shuru, Husna kam a mind dinta tana cewa" kaico na naga rayuwa Kala Kala taci  gaba da kukanta 


      Mufeed kam tinanin Husna yake tayi, yanda take shan wahala a rayuwa, Har ya wuce gidansu bema sani ba,  Alhaji ne yace" d'an nan lafiyar ka qalau kuwa?  Se a lokacin mufeed ya dawo daga dogon tinanin da yakeyi, yace" afuwan ya seta kan motar zuwa cikin gidan! 


      Suna isa kowa yaje yayi alwala yai sallah Sannan aka tare a fallow, itadai Husna tana gefe tana jiran taga abun dazai faru, Hajiyane tace" baiwar Allah, Meye babban dalilin barinki gida Har wannan abubuwan Meya faruwa dake? 

  

"Husna ce cikin kuka sosai ta soma basu labarin abun da ya faru da Ita tun daga kan accident din da iyayanta sukai, aka saceta, Har Allah yasa Malan kabiru ya Dakkota zuwa gidanshi, daganan matarshi bata sonta, anan ne aka neman mun aiki,  duk kudina na karshen wata seta amshe, Har Tsautsayi ya fadamun yaron gidan yamun ciki, to tun daganan tsangwama da habaici matar malan kabiru kullun takemun, wai badai a gidanta, ni kuma ina ganin guduwana shine sauki, to Anna ne na fito da sassafe ina jin jiri ga amai ga yunwa inaji Har Allah yasa na hadu da wa ennan bayin Allah Suka temakamun ta nuna *mufeed da farouk* shine ya kawoni dakinshi,  amma koda Nazo ko sau daya be tabama kwana dakinba,  sedai ya shiga mota ya kwana.. Har nai miscarriage (bari) to anan ne kika ganmu, ta gama fada kenan ta fashe da kuka ta tashi tace" nagode sosai da karamcin da kukai mun ni zan tafi Sai wata rana..,. Gaba daya dakin sun matukar tausaya mata Valle Alhaji da hajiya dan wannan ne karo na farko da Suka fara jin tarihin rayuwarta,  Hajiyane ta rungumeta tace" ba inda zakike,  munyi miki alkawarin zamu temaka miki


Ita Husna kuwa fisge jikinta tayi a jikin hajiya ta ruga da guda zata bude kofa, da Sauri Su mufeed Suka mik'e ya daka mata tsawa "yace Idan kika kuskura kika fita ko?  Hmm

     

"Tsawar da mufeed yai matane yasa ta dakata dan Ita gaba daya tsoron Shi takeji, kowa a tsaye ya kalleta yace" wuce Ki zauna, jikinta a sanyaye ta dawo ta zauna Su kam kallon ikon Allah kawai sukeyi, Nan take hajiya taji kaunar yarinyar a ranta, dan haka Suka yanke shawarar zata zauna a gidan, amma kuma Mufeed  yace" Sai ya dau babban mataki akan *inna matar malan kabiru* dan tana daya daga Wanda Suka jefa Husna cikin tashin hankali 


   Dan haka aka bata Daki,  Mufeed yaje ya dakko mata yan kayayyakin da yai saimata, Farouk kuma suna zaune matarshi ummi ta kirashi yace" gashinan zuwa! 


Dan haka Alhaji da hajiya Suka shiga Daki, Husna ma haka ta shiga dakin da aka bata,  Mufeed kuma ya raka farouk yana dawowa ya wuce part dinshi yai wanka ya kwanta a gado, tinanin Husna kawai ya fadomai, Ji yake yana mugun Sonta,  kuma yana tausayinta,  yanzu kenan da hannun bata gari ta fada shikkenan haka rayuwarta zata kasance a wulakance, Mufeed kam na kwance besan sanda yace" *I love you my  Husna ba* 


Farouk kuma yana shiga gida matarshi Ummi taci kwalliya kana ganinta kasan Beloved husband dinta take jira.. Yana shiga sukai 4eyes dashi wani sanyi taji a mind dinta da salon tafiyarta ta karaso inda yake tace" welcome sweet heart,  ya rungumeta sukai Daki! 



Bangaren Su hajiya kuma, Koda Suka shiga Daki da Alhaji, kowa shuru yayi na dan mintuna, Alhaji yace" ikon Allah *rayuwar Wasu* fa haka yake! 


Hajiya ma tace" uhm gaskiya na tabbatar da rayuwar Wasu haka yake,  yanzu fa da mun barta ta tafi Allah kadai yasan Wanda zai temaketa yanda zamanin nan ba kowa keda tsoron Allah ba


"Alhaji yace Ki bari kawai zamusan yanda za'ai a sata makaranta kawai dan zamanta bazai yuwa hakanan ba, Hajiya tace" Allah ya temakemu yace"ameen









Ummiey Xeey

[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​​*


*​FB PAGE..*​ 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


          _•••°°°Devoted  to......°°°•••​_

*​​​Miss Zarah Mansur😍*


```Keep smiling😊, b’coz life is a beautiful thing and there’s so much to smile about.```


*PAGE 71➖72*


Husna kuwa

   Tun da ta shiga dakin samun waje tayi ta zauna,  se tinanin guduwa ya fado mata a ranta tace" yanzu da na gudu ina Zan nufa?  Alhamdulillah tace" Sannan ta tashi ta shiga toilet tai wanka tai alwala,  ta ziro duguwar rigan da Mufeed ya siyo mata, da tasa yai mata das a jiki kamar dama dan Ita akayi


      Around 8:30 ne Su Hajiya da Alhaji da Mufeed suna zaune kan dinning suna cin abinci, hajiya taga ba Husna, kwalla mata Kira tayi akan yazo Su zauna suci abinci, Husna ta fito tama manta ba dankwali akanta ga gashi yazubo mata ta leko tace"

 Hajiya a a dakin ma ya isheni, bari dai Nazo na eba, ta fito ta eba hankalin mufeed gaba daya yana kanta yaga ta yi kyau ne,  kasa ckn abincin yayi seda Alhaji yai gyaran murya sannan Mufeed ya gane abun da yayi,  Alhajine yace" murya a kasa baka da kunya ko?  Sosa kai mufeed yayi yace" uhm no dad, Hajiya tace" meyake faruwane?  Alhaji yace" ba ruwanki nida yaronane,  tace uhm AI kunfi kusa... 


Husna kuwa, tana daki, fara cin abinci tayi taji dadi sosai, ta cinye sab, Ita robonta dataci abinci me dadin gaske haka tun tana gidan aiki, gashi ta na so ta Karo hakanan ta hakura tace" uhm ba gidan ubana bane.. Allah sarki


Su Alhaji sun gama cin abinci kenan daidai lokacin da Husna ta fito,  taga hajiya na kokarin kwashe kwanuka tace" hajiya Ki barshi, kafin hajiya ta fara magana Har Husna ta kwashe takai kitchen, da taga kitchen din irin yayi Baja Baja ta tsaya gyarawa daganan ta fara wanke wanke, hajiya taji shuru ta leko taga Husna na wanke wanke Sa mata albarka tayi, kuma taji dadi sosai,  Husna tace" bakomai,  a zuciyarta tana cewa tab AI wannan aikin me saukine a wajena


Seda ta gama komai Sannan ta fito ta samesu a pallow tace" saida safenku, Ji Mufeed yake kamar yace Ki tsaya dan dama saboda Ita ne ya tsaya a pallow din, gashi tace" saida safe.. 


Misalin 9:30 ne mufeed ya shiga dakinshi dan bacci ina,  bacci ya gagara se juyi yake yana tuno kamamnin Husna yanda yaganta dazu,  kamar wani mahaukaci ya tashi ta fara yin yanda tayi dazu, Shi kanshi abun ya bashi dariya, dan haka ya dawo ya kwanta dakyar bacci yai awon gaba dashi,  koda yai baccin ma nan ma ba tsira yayi ba mafarkin Husna yakeyi barkatai wai gashinan suna park,  suna shan iska,  ko kuma suna hira 


Su hajiya kuma bayan fitar Mufeed suma Daki shuka shiga, hajiya seyabawa da hankalin Husna takeyi,  Alhaji yace" gaskiyane abunda baka saniba baka saniba da Har munfara zargin ko danmu tarbiyarshi ya lalace Ashe ba haka bane,  Allah dai ya kara tsare kullihi musulmi,  Ameen, 


Sannan Alhaji yace" ya batun maganar makarantar ta?  Hajiya tace" banko mai magana ba se gobe, Alhaji yace ok barshima Zan mai da kaina hajiya tace ok


*Washe gari*

saboda Monday ne da hajiya ta tashi da wuri dan hadawa maigidanta da Mufeed breakfast dan Kar sui latti, tana kitchen taji tafiyar mutun waigawar da zatai taga Husna tace" kafin tai magana Har Husna ta tshugunna ta gaisheta ta amsa,  Sannan tace" hajiya me za'ai?  Ki kawo kawai nayi kije ki huta, Hajiya tace" kai yar nan AI da kin barshi ma nayi just arish Zan soya se yar miya se kayan tea,  Husna tace" karki damu hajiya nayi aikin da yafi wannan ki kawo wlhi,  

   Hajiya tace" kai amma nagode bari na koma Daki nai ida azkhar dama bangama ba,  kan kace meye Husna har ta harhada komai ya kasance ready akan dinning,


Sannan taje ta sanar da hajiya, kara dai shimata albarka tayi,  Husna na shiga Daki Mufeed  yaga abinci akan dinning, ya zauna kenan Sega hajiya da Alhaji suma sun fito Suka zauna gaba daya sukai having breakfast dinsu,  Mufeed  kam cewa yayi" kai Hajiya gaskiya irin wannan zaki dinga mana dasafe, yayi dadi sosai,  yana magana yana lashe hannu


    Hajiya tace" to sannunka bani nayiba, Husna ce" zare ido yayi yace kai!!!  Yanaso yayi comment amma ba dama saboda mahaifinshi nanan dan haka yai shuru, amma dai be dena santin abincin ba... 



Bayan sun gamane Mufeed Har ya dauka jaka zai fita dad dinshi yace" yanason magana dashi, Ok yace"

   Wannan dad ya fara magana kamar haka!  Mufeed in kasama lokaci inaso ke nemo ma Husna makarantar Boko da islamiya, 


 gaban Mufeed yaji yace" gham





Kuci gaba da kasancewa dani






Ummiey Xeey

[4/11, 8:41 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *RAYUWAR WASU​​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​​*


*​FB PAGE..*​ 

https://www.facebook.com/Ummiey-Xeey-Fans-485709968267150/


          _•••°°°Devoted  to......°°°•••​_

*​​​Miss Zarah Mansur😍*



*PAGE 73➖74*


Gaban mufeed ne yaji yace" gham, shuru yayi nadan lukuta, dad dinshi na lura dashi yace" anything wrong? 

   Girgiza kai Mufeed yayi yace" a a amma dai dad da da da.... 


Be karasa maganar ba dad dinshi yace" my wish is your command, so kake ta zauna ba arabi ba boko? A a mufeed yace" sannan yace" zanyi kokari a duba insha Allah,  smile dad dinshi yayi yace" Allah ya tsare Sai ka dawo,  Mufeed yace" Ameen Dad


Koda Mufeed ya fito da tinanin maganar babanshi ya tafi wajen aiki, maganar se yawo yake mai, Har abokinshi Farouk yake tambayar"

Wai ina Husna ne?  Nan Mufeed yace" I'm in love with her, kuma wallahi I want to marry her!! 

 

Zare ido farouk yayi yace" you most be joking, 

"I'm serious Mufeed yace" farouk yace babban magana, yau Mufeed  kaine da maganar aure??


Mufeed yace" kwarai kuwa, nine,  Suprise farouk yace"

Mufeed yace" meye abun mamaki, ni ba mutun bane ko dama ance bazanyi aure bane?  Farouk ya fara magana yana murmushi yace" woo wane ni, abun da mamakine kai da ban tabaji ma kana maganar aureba duk yan matan da suke kawo kansu gareka baka sauraran kowa,  se yau rana tsaka kace ma Husna zaka aura,  AI akwai mamaki, 


  Shuru Mufeed yayi yace" uhm nima haka kawai fa naji jarinyar tamun, kuma naji ina san ta kasance matata, very good farouk  yace" sannan yace Su hajiya sun sani ne kuwa?  A a Mufeed yace" Dad ne fa wai na nemo mata school ni kuma yanda take da kyan nan da hankali yaushe Zan bari taje chan wani ya ganta yace yana so,  dariya hahaha farouk yayi sannan yace maza an shugo gari, ka manta lokaci da nace yarinyar nan tanada kyau,  kace ba wani kyau da take dashi se yanzu ka gani kenan ko?  Mufeed cikin burin kunya yace" eh naji dai,  yanzu kaban shawara, 


Farouk yace" shawara guda dayace kawai ka nemo mata islamiya inyaso boko din ko tana gidan ka se kai, good idea Mufeed yace sannan kowa ya ci gaba da harkokinshi Har Suka tashi daga office din


****************************

Koda Mufeed ya dawo nan ma Ganin Husna yayi tare da mahaifiyarshi suna kitchen suna abinci,  kayan da tasa yai wani mugun mata kyau, idon Mufeed kyar akanta duk husna taji wani iri a daddafe dai ta samu Suka kammala, shikam mufeed fallow ya dawo

husna ta fito daga kitchen kenan, taci karo Mufeed a pallow again, wani kallon I love you ya jefo mata tajita duk wani iri


   Daki ta shiga tace" ya salam meke shirin faruwane haka?  Me wannan guy din yake nufi,


Shikam Mufeed be ki kullun ya dinga ganinta ba,  a zuciyarshi Har cewa yake inama ace time din Dana dawo daga malesia ne da Idan na kura mata ido se Allah,  hakanan ya karace zaman Shi a pallow din husna kam taqi fitowa


A yan kwanankin nan husna Sam bata yarda da da irin kallon da yake mata ba,  a zuciyarta tana tsoron Kar abun daya faru fa Ita ya sake faruwa da Ita dan haka kwata kwata da taji motsinshi seta boye


Da dadarene husna na juye ruwa a bucket tana kitchen zatai wanka, Shi Mufeed yana sha mum dinshine a kitchen ne dan haka ya shiga kai tsaye,  yana shiga sukai ido hudu da husna, ajiye kettle din tayi jikinta na rawa tace" dan Allah kayi hakuri,  Shi abun dariya ya bashi yace" meya faru?  Tace inajin tsoro ne,  Smile yayi yace karki wani ji Tsoro *HUSNA ina sonki kuma Zan aureki* sake baki tayi tace" wane ni kafi karfina, jin tafiyar mummy yayi, ya daga mata gira yai ficewarshi, itakam Husna tsayawa tayi abun na bata mamaki


Chan taji hajiya nama Mufeed  magana tace" Ya maganar kamarantar?  Mufeed karya yayi, yace" na mata magana! Nace zuwa jibi laraba kenan ta kintsa nakaita, Masha Allah hajiya tace"


Husna da take tsaye a kitchen abun mamaki ya bata ko yaushe Mufeed yai mata magana oho,  dan haka ta dauka ruwan zafinta takai Daki, tayi wankarta


Bayan tayi wankanta ta dauro alwala tazo tai sallahn magrib tanajin hayaniyar Su Mufeed da Hajiya a pallow taqi fitowa,  shikam Mufeed duk haushi yabi ya isheshi, ganin husna bata fito ba, yai wa mum sallama, itama tanajin ya fita ta fito tai joining Hajiya Suka fara kallon Arewa 24 ana wani film 


Bayan Mufeed ya shiga dakinshi, ya lalubo wayarshi yaji babu Ashe ya manta dashi dakin Hajiya, dan haka ya dawo,  zai dauka yaci karo da kyayyawan yarinyar da yakeson gani a ko yaushe,  dan haka daga daukar waya ya bige da kallo shima...se satar kallon husna yake 






*Team Mufeed*😍

[4/15, 2:29 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *​RAYUWAR WASU​​​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​​​*


*​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​​* 

    _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_


*FB Page* 

https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/



        ​  _•••°°°Devoted  to......°°°•••​​_

*​​​​Miss Zarah Mansur😍​*


*Where is Maryam Aliyu A* mar'ahmad your page is here, I love you so much💋💋💋


*PAGE 75➖76*


Kallo Sukeyi amma idon mufeed na kan husna, Ji tai ta kasa zama a pallow din dan haka tace hajiya saida safe, maganar datai mufeed kam ya bashi haushi, Hajiya tace" har zaki kwanta?

Eh tace ta tashi tai wucewart daki, tana shiga gado ta fada, tafara tinanin wai shin me yaya mufeed yake nufi ne haka? Da wannan tinanin tai bacci


Bangaren mufeed shi kuma tun time din d husna ta shiga daki ji yai kamar ya bita too faa, Dan be gama ganin kyakkyawan fuskarnan ta ta ba...yana zaune wata zuciyar tace" what are you waiting for? Wanda kazo Dan ita ta tafi daki kai me kke jira? Phone dinshi ya dauka yai wa mamanshi seda safe, Itama hajiya da taga kowa ya tafi bacci kashe kayan wutar dakin tai itama taje ta kwanta


Mufeed tun da ya shiga daki kasa samun natsuwa yayi, Kwanciya yayi Amma ina kasa bacci yayi, Dan haka ya mik'e yama rasa me zaiyi, rarumu waya yayi zaiyi dialing numbern farouk ya tuna fa yana chan tare da matarshi, kuma beso ya takuramai dan haka ya kyaleshi, hakanan ya kwanta besan ma sanda bacci yai awon gaba dashi ba, a cikin baccinshine yai mafarkin wai gashinan shi da husna akan dining tana feeding dinshi, smiling yayi, be wani Dade a baccin ba ya farka, a ganshi a gado wani tsaki yaja, dole ya sake addua yai bacci


*Washe gari*

Kamar kullun husna ta saba tashi da wuri kasan cewar weekend ne, kitchen ta fito tana so ta hada musu break fast, motsi hajiya taji ta fito, husna CE ta gaisheta, hajiya tace" bakya gajiyane? Da kinje kin kwanta se 10 tunda yau ba aiki, mufeed ba fita Zaiyi ba, Ok tace" ta koma daki tai kwanciyarta


Misalin 10am din hajiya da taji shuru bata fito ba dan haka ita da kanta ta Shiga kitchen ta hada komai na breakfast, sannan tazo ta jera kan dining, tana cikin jerawane, Sega Husna ta fito tace" laa hajiya badai kin gama ba?


Hajiya murmushi tayi, tace" aiko na gama kinga kema kin huta ko? Husna tace uhm Amma ba haka nasoba, hajiya tace" bakomai, je kiyi wanka kizo muci abinci, toh tace" ta juya tai daki


Tana Shiga dakin kamar an jefo mufeed, yana ganin abinci a Jere a dining ya nufa ya zauna, Hajiya ta fito kenan tace" har ka tashi kenan? Sosa kai yayi yace" eh wlhi ina kwana hajya?

Lafiya lau ta amsa sun fara hira kenan Sega Husna ta fito cikin wani atamfa Riga fa siket yayi mata kyau sosai, Dosowa wajen tayi cike da faduwar Gaba, Tasa waje ta zauna itama, hajiya ta kyalleta tace" kinyi kyau, duk'ar da kanta kasa tayi ta fara wasa da yan yatsunta, 


Mufeed kam dam tun da yaga ta fito dama idonshi na kanta, mind dinshi yace" kai masha Allah, ahaka suna dan Fira har suka gama, zai fita kenan ya juyo yace" Husna, anjuma ki shirya zan kaiki makarantar islamiya ai miki registration, Toh tace"


Mufeed na fita, gidan abokinshi farouk, ya wuce, nan ya sameshi da matarshi se hiran masoya sukeyi abun ya burgeshi...


Farouk yace" abokina ya akai ne? Yace" walhi Alhamdulillah, akan dai maganar rannan ne


Farouk yace wato kananan kan bakarka ko? Mufeed  yace kai ma ka sani ae, itadai ummi na jinsu bata ce musu komai ba,


Sun taba hira sosai wajen yanda zasu bulluwa wannan al'amarin, farouk ya bashi kafin gwiwa sosai, sannan yamai fatan alheri sukai sallama ya dawo gida


Misalin 4:pm, Husna ta shirya, tana zaune Sega mufeed yace" mu tafi ko malama? Daga kai tayi sannan sukai waa mama sallama tace Allah ya tsare


Sun fito harabar gidan, mufeed ya tada mota yace" Bismillah ki shugo mana, Bude back site tayi, yace" no Husna ki shugo gaba mana?


Uhm tace" sannan ta bude front sit zauna








*Ummie Xeey*

[4/15, 2:29 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *​RAYUWAR WASU​​​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​​​*


*​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​​* 

    _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_


*FB Page* 

https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/



        ​  _•••°°°Devoted  to......°°°•••​​_

*​​​​Miss Zarah Mansur😍​*


_Woooo where are you ♻exclusive ladies... The whole page is for you guyz, inajin dadin zama daku Allah ya kara hada kawunanmu_ *#ONE LOVE*💘💘


*PAGE 77➖78*


Husna ce tace" uhm sannan ta bude front sit ta zauna

Mufeed kam kallonta yayi yai smiling sannan ya tada motar ya fita a harabar gidan!


Suna cikin tafiyane kafin su karasa school ne yace" Husna nace ina sonki baki cemun komai ba? Itadai shuru tamai har suka isa makarantar


Nan ya fito akai mata komai sannan aka bata class akace no need ta koma gida, ta zauna kawai tayi karatu, Ok mufeed yace" da zai tafine ya kirata yai mata nasiha akan ta maida hankali, kuma ta san d frnds din da zatai Hulda, infact shi beso ma ta kula kowa, Yace" ya tafi sai ya dawo daukarta, Tace Ok Allah ya kaimu,


Husna na shiga Aji, taga duk yan yarane ma ba wasu manya sosai, dan haka taje kusa da wata yar babba kamarta a zauna, nan dai suka gaisa tace" sunanta Husna, kawar kuma tace" Sunanta Khadeeja...


Khadeja irin wayayyun yaran nan ne, itama boarding school aka kaita har ss2 ta gudu sai yasa batai islamiya da wuriba, 


Nan dai suka fara karatu har aka tashi, Yau dinnan da haduwa amma Jinin Khadija da husna ya hadu sosai..


Misalin 6pm aka tashi, Khadija da husna suna tafe har bakin gate, khadija tai gida husna kuma ta tsaya jiran mufeed, magana taji from no where akace" Zo mu tafi ko? Firgita tayi, sannan daga baya ta gane muryan waye, sannu da zuwa tace" shikam bece komai ba illa binta da ido da yai, gaba daya shi mufeed yarinyar na burgeshine,


Husna ce taga kallon ya isa haka tace" yaya mufeed mu tafi gida kaga Kar hajiya tayi fada"


Ok yace" sannan yace wlhi kullun ina son kasancewa dake, itadai uhm tace ta bude mota sannan shima ya shiga, koda ya shiga  ba Wanda yacewa kowa komai har suka isa gida, suna shiga hajiya tace" oyoyo y'ata sannu da dawowa 


"Husna yauwa tace" sannan ta shiga daki Dan ajiye takardu, mufeed ne yace" ni ba'acemun ba, hajiya dan hararanshi tayi, sannan yace" uhm bari na je dai nai alwala time din magrib ya kusa, hajiya tace" atoh, bayan mufeed ya fita a dakin, Husna ta fito ta Dan kakkama ma hajiya aikacen aikacen gidan suka kammala kafin magrib, kowa yai sallah sannan sukaci abinci 10pm nayi kowa yai bacci Dan sun gaji


Mufeed kam daya Shiga daki, kiran abokinshi yayi, yake sanar mai da cewa ya furta mata yana sonta!! Farouk yace" me tace? Mufeed yace" shuru tayi, Farouk yace very good yanzu kawai ka sanar dasu hajiya, Ok mufeed yace sannan sukai sallama


Washe gari kamar kullun husna ta tashi tai duk abun da zatai kafin lokacin islamiya,

Time nayi Sega mufeed, ya shugo yace" ki sameni wajen mota, ok tace" yai ficewarshi, yana zaune Sega husna ta fito, nan take ya dauko wayarshi ya kashe mata hoto, ita duk bata saniba


Takowa tayi har wajen motar sannan ta shiga, taga kamar yadin uniform din ta akan screen din wayarshi, Amma bata gani dakyau ba Dan batasan waye ba kuma bazata Iya tambayarshi waye ba sai yasa ta basar


Haka suke ta tafiya, har suka isa, tana zuwa bakin gate taci karo da kawarta, khadija, kiranta tayi, ta tsaya suka jera tare, 


Khadijane tace" wannan yayankine? Gaskiya yanada kyau, husna ji tai wani kulolo ya tsaya mata a zuciya yana da kyau? To me wannan yarinyar take nufine?


Haka dai suka shiga Aji, Amma yanayin husna daka ganta kasan abu na damunta, khadijace tace" menene yar uwa? Karyan dole husna tayi tace" iyayena nake tinawa! Wani kallo khadija tai mata irin bata gane me take cewa ba, khadija tace" wanchan ba yayanki bane? Girgiza kai tayi tana hawaye tace" a a! Khadija abun ya bata mamaki tace" Amma naga kuna kama, meye dangartakarki dashi???

 

Husna ta fara kuka tace" nasan zaki rikemun amana bari na baki tarihin rayuwata, khadija ta gyara zama tace" inajinki....


"Nan Husna ta fara cewa"









.

Ummiey Xeey

[4/15, 2:29 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *​RAYUWAR WASU​​​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​​​*


*​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​​* 

    _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_


*FB Page* 

https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/



        ​  _•••°°°Devoted  to......°°°•••​​_

*​​​​Miss Zarah Mansur😍​*


*Emnoor Ahmad don* I miss you like crazy......😭😭


*PAGE 79➖80*


"Husna ce ta fara kuka tace" nasan zaki rikemun amanata, Khadija tace" insha Allah, 

Husna tace to bara na baki tarihin rayuwata, khadija ta gyara zama tace" inajinki


Nan husna cikin shesshekin kuka ta fara magana tace" kinga wannan dinnan d kike gani shi ya cece rayuwata da yanzu bansan Inda nake ba a rayuwata, Farkon labarina ya farane tun ranar da zamu kawowa yan uwanmu ziyara daga kano zuwa Kaduna, anan mukai accident, kinsan mutane ba tsoron Allah, ganin iyayena da sukai, ba cikin hayyacinsuba, wasu yan yankan kai suka saceni, Nan khadija ta zare ido, tace Allah sarki, daganan Allah yasa ogansu jinina ya hadu dashi, kullun seya kawoun kayan dadi naki ci, da yake ina addua Allah bai basu sa'a akaina ba hakanan aka fito da ni daga wannan gidan, daganan aka kaini gidan me unguwa na hadu da wani malan kabiru yace zai daukeni, indai takaice miki labarin banji dadin zamn gidan nan ba, Anan ne takaini gun aiki, na hadu da yaron matan, yai mun fyade, A'uzubillah Khadija tace" lalle kam ta fada a zuciyarta kaidai kaga mutun bakasan wahalan da yake sha ba


Husna taci gaba d cewa to tun daga ranar da inna matar mlm kabiru, ta lura ina da ciki, zagi, tsangwam ba wanda banshaba, karshe kawai na yanke hukuncin guduwa dan ta hakane zan sama sauki


"Ina cikin tafiya ni kaina bansan ina zanjeba ga jiri, ga yunwa ga amai, kinsan ciki se ahankali, kawai Allah ya jefo su yaya mufeed da Farouk Nan Suka temakeni, har mufeed ya kaini gidansu, anan ne cikin ya bare, yazo zai kaini asibiti kenan mamanshi ta ganshi, Toofaa khadija tace" lalle kin ga *RAYUWA* 


hmmm haka dai ta bata labarin yanda akai komai, har shuguwarta islamiyar nan, Amma bata sanar da ita cewa mufeed na sonta ba kinjii dai labarina tan gamawa ta fashe da kuka


"Khadija tace Wallahi kinban tausayi, Amma ki godewa Allah ma da kika fado hannu na gari, yanzu dai ki dena kuka komai zaizo karshe, dakyar dai husna tai shuru, ita kuma khadija ta fara bata labarin rayuwarta


"Tace nidai sunana Khadija ina zaune d iyayena lfy lau, gaskiya ba abun daya faru dani, intact dai Alhamdulillah komai daidai, kema karki damu, Allah na tare dake, ki manta da komai ki rike Allah, Zakiga komai naki naci gaba..Su kuma Su mufeed Allah ya Saka musu da alheri....tace" Ameen


Ranar dai ba wani karatun kirki sukai ba, har aka tashi, ko wanninsu ya tafi gida da daukin amininshi, Husna kam ta sama kawa har ta kosa gobe tayi



Hakadai rayuwarsu ta kasance kullun cikin zumudin juna suke, daka kalla husna kasan Alhamdulillah yanzu damuwa ta Dan ragun mata duk saboda friend, at least ta sama abokiyar hira duk da  a school kadai suke haduwa


Shikam mufeed kullun kara sonta yake, idan yananan Saturday & Sunday kullun yaje dakkota yaganta da babban aminiyartau se yaji kishi, a mind dinshi yana inama dashi ake wannan hiran!


Yaune sun tashi, yazo daukanta yaganta dai da babban kawarta, kamar yace" ke Kar ki sake mata magana Dan shi mufeed bameson yaga Wanda yakeso tana Hulda d mutune bane, hakanan dai ya hakura har yana hararar khadija saboda kishi,


Yace" husna shiga muje....Khadija tace" Bestie sai gobe, husna tace" ok bestie byeee


Mufeed na jinsu yace a zuciyarshi" zakuci kaniyarku da bestie dinnan...lol


Murtuke fuska yayi yace" waye wannan daga zuwa ko 1month bakiyiba zaki fara jajiban kawaye anan ne ake chanzawa mutun ra'ayi, itadai batace komai se surutanshi yake irin ran maza ya baci dinnan


Suna Isa gida, Mufeed yaga Car (Mota) din babanshi, yaji dadi sosai, Dan dama be gari kwana biyu, yanzu mufeed Nada damar dazai sanar d mahifishi abun dake ranshi, Dan haka yai parking suka shiga tare


Suna shiga suka tarar da alhaji da hajjya a falo, nan suka gaishesu, husna tai daki mufeed kuma ya tsaya gun dad dinshi


Suna hira, Magrib yayi babanshi yace" zuwa anjuma yanason magana d mufeed yazo ya sameshi, Ok mufeed yace"


Misalin 9:pm mufeed ya shiga dakin babanshi da sallama, ya sameshi d hajiya suna hira


Alhaji ya kalle mufeed yace" wato duk abun Dana tsara seka chanzako? Ba harda boko nace kasa Husna ba, dan me bakai abun Dana saka kaba yanzu kusan 2moths


Budan bakin Mufeed yace" dad I'm sorry dalilin da yasa bansata boko ba ina son aurantane!!!


Hajiya da Alhaji suka zare ido sukace mene???






Dan jin cigaban labarin sai kuci gaba da biyoni








Ummiey Xeey

[4/19, 3:22 PM] Ummi Abubakar😃: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *​RAYUWAR WASU​​​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​​​*


*​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​​* 

    _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_


*FB Page* 

https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/



        ​  _•••°°°Devoted  to......°°°•••​​_

*​​​​Miss Zarah Mansur😍​*



Wooo where are you *Safiyya A Yunus😍* _your page is here...Naga Book masha Allah, Allah ya kara Basira dear_



*PAGE 81➖82*


Budan bakin mufeed yace" dad I'm sorry dalilin da yasa ban kaita boko ba inason aurantane!!!


Hajiya da Alhaji suka zare ido sukace mene???


"Mufeed ne yakara kaskantar da murya yace" ina son aurantane, hajiya dai tai shuru, Alhaji kuma yace" Mara kunya har zaka duba idonmu kace zaka aureta To Sam ban yardaba, dad ya mike yabar dakin!!


Hajiya tai sororo a zaune shima mufeed kasa motsi yayi, Hajiyane tai karfin Hali ta mike tabi Alhaji, 


Bed room dinshi ta bishi, taga ya zauna yayi tagumi, hajiya ne tace" haba Alhaji, meye dalilin da yasa bazaka amincewa d'an mu ba?


Alhaji cikin fushi yace" haba Matata taya za'ai na amince mai? Bayan bebi umurnina ba, ni bama haka ba, nafiso ya sama yarinya me asali, duk da nasan ta fada mana iya gaskiyanta be zama lalle gaskiya bane, Hajiya tace" hakane Amma Dan Allah kayi hakuri, 


Suna cikin magana kenan Sega mufeed ya shugo idonshi yayi jajur gab yake da zubar da kwalla, yazo ya tsugunna gabansu yana basu hakuri akan su amincemai ya aura Husna


Alhaji Sam yai kamar bemasan mufeed na magana ba, "mufeed ne ya kara da cewa dan Allah abba kayi hakuri, se a lokacin dad ya kalle mufeed yace" na Riga na fada maka kuma bazan chanza ra'ayina ba...ka tashi ka fita ka bai waje


Allah sarki uwa, Abun da alhaji yai wa mufeed Sam bataji dadi ba, Dandai ba yanda zatai ne, "mufeed ne ya mik'e yaji kafafunshi sun mai nauyi, dakyar ya fito yazo wucewa ta pallow kenan yaga Husna.... I'm a loser ya fada a mind dinshi, yana fita wasu zafafan hawaye suka zobomai, dakyar dai ya karasa daki, koda ya shiga daki nan danan yaji duniyar gaba daya batamai dadi, yanzu abun da yake burin samu shikkenan bazai samu ba, ji yai kanshi ya fara ciwo, kwanciya yayi a gado, abun tausayi be dade ba bacci yai awon gaba dashi...


Hajiya kuma se ba alhaji hakuri takeyi tunda shi da kanshi ya nuna yanaso yayi hakuri kawai, inyaso sa bishi da addua"


Alhaji yace shima fa sam karma ta sake mai maganar auransu dan bayuwuwa zaiyiba dan haka taja bakinta tai shuru.


Mufeeed kam Dama tun da ya shiga daki yai bacci bashi ya farkaba se 3 na dare, yana tashi ya duba yaga 3 toilet ya shiga ya dauro alwala yazo yana fadawa Allah bukatunshi, bashi ya koma bacci ba har seda akai sallar asba'i


Bangaren su hajiya kuwa an kammala kayan break fast, har 11 shuru mufeed baizoba, Alhaji shima yadan damu yasan dalilin qin zuwanshi Amma ya basar, Hajiyane tace" naji wannan yaron shuru bari dai na je nadubashi ko lafiya, Alhaji binta da kallo yayi kamar yace kar taje amma shima yanason sanin wani hali danshi ke ciki


Hajiya ne ta tashi ta tafi part dinshi ta murda kofan taji a kulle, buga kofar sosai tayi, shi kuma mufeed cikin bacci yaji kamar ana knocking kofa, dakyar dai ya tashi, yaje ya bude yaga ashe hajiyarshi, 


Kallo daya tai mai ta gane mufeed beda lfy, dan idonshi yayi ja, kuma irin beda kuzari haka, Son meke damunka tace"


Girgizakai yayi, alamun ba komai, hajiya tace" I can't believe this, taba jikinshi tayi taji zafi *ramm* subhanallah tace" hade da cewa sannu Son, yauwa yace, "tace bari naje na fadawa babanka baka da lfiya,"

Har ta juya zata tafi ya kamo hannunta yace" mum please don't tell him na gwammace na mutu tunda dad yace bazan aura Husna ba


Hajiya ne tace" you're mad kar in karajin wannan maganar a bakinka, mahaifinkane, ka dade kana mai biyayya kar Dan yace bazaka aura husna ba ka qi mai biyayya, Mufeed shuru yayi, sannan hajiya ta fita!!


Koda ta fita da rawar jiki ta isa gun alhaji tana cewa" Alhaji kazo son beda lafiy, Alhaji smiling yayi a mind dinshi Dan yasan musabbabin rashin lafiyarsa, be bar wajenba seda ya kira doctor dinsu yace" maza yazo akwai Patient a gida, doctor yace ok!


Bayan Alhaji ya gama waya da doctor ne ya kalle hajiya yace" muji in ganshi, itadai Husna na gidan Amma batasan wainar da ake toyawaba, tagadai mufeed be fito ba tana sha ma aikine ya rikeshi


Hajiya na tafe Alhaji na biye da ita har suka isa dakin mufeed, a kwance suka taddashi ya rike kai, abun yaba Alhaji dariya, a mind dinshi yace" yaro yaso Aure, Dan Alhaji irin iyayen nan ne Wanda suke friendly da yayansu,  kusa dashi Alhaji yazo ya dafashi, yace ya jikin?


Mufeed cikin wani irin murya Wanda kanaji kasan Abu na damunshi yace" dasauki dad, 


Babanshi dariya yayi, Sannan yace"Allah ya kara sauki, mufeed yace Ameen, suna zaune daga doctor ya kira Alhaji yana sanar dashi ya iso...










Ummiey xeey

[4/19, 3:23 PM] Ummi Abubakar😃: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *​RAYUWAR WASU​​​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​​​*


*​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​​* 

    _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_


*FB Page* 

https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/


        ​  _•••°°°Devoted  to......°°°•••​​_

*​​​​Miss Zarah Mansur😍​*


_Respect people’s feelings. Even if it does not mean anything to you, it could mean everything to them._


*PAGE 83➖84*


Babanshi dariya yayi, Sannan yace" Allah ya kara sauki, mufeed yace Ameen, suna zaune sega doctor ya kira Alhaji yana sanar dashi ya iso...


Alhaji yace" okay sannan ya mik'e ya fita yamai iso har cikin dakin mufeed, Nan doctor ya fara gwaje gwajenshi, har ya gwada BP dinshi yaga yayi high sosai,


Doctor din was shocked daya gani, yace" Amma Alhaji meke damun yaron nan haka cikin lokacin kadan jininshi yahau sosai, gaban Alhaji ne yace gham!! Hajiya a mind dinta kuma tace Subhanallah,


"Alhaji yace doctor please kayi duk abun da zakai, Dr yace ok insha Allah, Amma fa gaskiya in akwai wani abun da yakeso a bashi Dan BP din nashi ya sauka in ba haka ba kuma akwai matsala, Insha Allah Alhaji yace" nan dai doctor yamai duk abun daya kamata, yace zuwa anjuma in drip din ya kare a kirashi ok sukace sannan yar tafiyarshi,


Hajiya tace" mu tafi ko Alhaji ya huta, Jikin Alhaji a sanyaye yace" ok


"Suna fita mufeed ya raromu wayarshi ya kira abokinshi, yake sanar dashi ga yanda sukai da dad, Farouk beji ddi ba shima Sam Amma yace" yayi hakuri gashinan zuwa inyaso se Su tatauna, Ok yace"


Hajiya kuma suna komawa part dinsu taga Husna har ta daura sanwar rana, tace" kekam baki hutawa, husna tace" ae gwanda na rage miki aikin kafin na tafi islamiya, hajiya dai tace" aiko nagode, tanajin son yarinyar har cikin ranta...sannan hajiya tace" yayankifa beda lafiya!!


Gaban husna na yai mugun fadi, hajiya na shigewa daki tai maza ta dakko hijab dinta tai dakin mufeed da gudu, tana zuwa bakin kokar kuma taji kunya ta kasa shiga


Minti daya, biyu uku, taga dai ba sarki sai Allah ta murda kofar, tana shiga da sallama sukai 4eyes Dashi, wani murmushi ya sakar mata aranshi har yaji wani sanyi, itakam duk kunya yabi ya isheta, karasowa tayi a kunyace ta sama waje ta zauna ta gaisheshi, sannan tacemai ya jiki? Yace" Alhamdulillah, sannan tace" kamaci abinci kuwa?

A'a yace" 

"tace bari naje dakkoma sannu, 

Shidai binta da ido kawai yakeyi, Dan komai tayi kara birgeshi da sonta shiga jinin jikinshi yakeyi,


Aiko mik'ewa tayi taje ta dakkomai break fast dinshi, dawowar da zatai kenan, taga farouk a cikin dakin, nan kunyarta ya karu, a sanyaye ta gaisheshi, sannan tace" yaya mufeed gashi, ita Sam bata daukeshi saurayiba, Dan tun temakon da sukai mata wani girmama na musamman take basu, bayan ta ajiye abinci, tace" yaya gashi kaci, Abun ya burge farouk yanda yaga tana kula dashi sosai, 


Farouk ya tafa hannu yace" masha Allah, amaryan mu ashe dai kinason abokin nawa!!

 

Ji tai maganar ya mata banbarakwai, nan take taji wani iri tana so ta fice, mufeed yace" ya zaki tafi bayan bazan Iya ci in baki kusaba? Kunya taji sosai ta rufe ido da Sauri ta fice, abun dariya ya basu sosai, sukace Husna akwai kunya!!


Bayan fitar tane, Nan mufeed ya kwashe labarin komai yanda sukai da Alhaji ya sanar da farouk, 

Farouk" yace karka damu, zamui magana da Alhaji, nan dai suka gama hira 


     Ummi matar Farouk kam ta kira, se kira take, wai tana missing dinshi, abun burge mufeed ykeyi, hardai ya gaji ya amsa wayar yace" gashinan dawowa ba cinyeshi zanyiba, Nan dai taji kunya tacemai ya jiki!! Misalin 6pm farouk ya koma gida


Ita kuma husna tana dawowa gida daga islamiya bata wuce ko inaba se dakin mufeed, tana shiga taga drip din da aka samai yama kare,


Tana kokarin cirewa kenan, mufeed yace wait baki iyaba, tace Allah na Iya, ai lokacin dana kwanta a asibiti naga yanda akeyi, yace ok shikkenan ciremun nagani, tana kicikicin ciremai drip din kenan Sega Alhaji da hajiya sun shugo,  husna ta tsorata, Su hajiya da Alhaji abun mamaki ya basu, wato dama wa ennan yaran soyayya sukeyi ko? 


Tana cirewa, Hajiya tace" sannan, dasauri husna ta fice, Alhaji kuwa kasa cewa komai yayi


Kuci gaba da biyoni








Ummiey Xeey

[4/19, 4:13 PM] Ummi Abubakar😃: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *​RAYUWAR WASU​​​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​​​*


*​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​​* 

    _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_


*FB Page* 

https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/



        ​  _•••°°°Devoted  to......°°°•••​​_

*​​​​Miss Zarah Mansur😍​*


*Aisha a muhd😍 & Aishan umma😍* woooo uwayen dakina...Halinku na gari ya biku a duk Inda kuke..Gaskiya ina sonku har cikin raina...Allah ya kara daukaka.... *I love you*



*PAGE 85__86*


"Husna na gama ciremai drip din, "hajiya ta kalleta tace sannu"


Da sauri husna ta fice, Alhaji kuma kasa cewa komai yayi,....Mufeed ne yace sannunku hajiya!!


Alhaji kallonshi yayi yace" banace bazaka aureta? Danme zaka dinga inviting dinta har cikin dakinka? Kai soyayya dadi ko?


Mufeed kwata kwata beji dadin magar abbanshiba, ba yanda ya iya, "Sorry  daddy yace" sannan suka sama waje suka zauna


Hajiyane ta kalle d'anta cike da tausayi "tace son how are you feeling now? "Alhamdulillah mufeed yace" 

Tace" Allah ya kara sauki yace Ameen...suna zaune doctor ya kira, yake tambayar ya jikin nashi, yasan dai by now drip din ya kare ko?


Alhaji yace" Alhamdulillah, eh ya kare, mumma ciremai basai kazoba, Doctor yace" To Alhamdulillah adai kula da jikinshi kuma ya dinga shan magungunanshi, Alhaji yace Okay!!


Suna dakin aka kira magrib, Dan haka Alhaji ya fita yaje yai sallah, hajiya kuma tace" ok inanan koda ka dawo, Dan haka yana fita itama alwal tayi tazo ta sallahn ta, bayan ta idar ne tazo kusa da mufeed ta shafa kumatunshi, tace" nasan kana tare da damuwa Amma insha Allah zan maka kokari kaji?


Mufeed ne ya kalle mamanshi wasu zafafan hawaye suka zubomai, yace" Dan Allah mummy ki temakemi wlhi idan na rasa husna akwai matsala, Hajiyarshi ta matukar tausayamai Dan tasan radadin so, tace" karya damu, suna cikin hirane Alhaji ya dawo, nan suka zauna har 10pm ganin jikinshi da saukine yasa suka koma part dinsu...

                   **********

Haka dai rayuwar mufeed ya kasance daga kanshi kasan something is wrong with him...be da wani kwanciyar hankali 


Duk ya rame yau kusan 2weeks kenan,


Yana zaune yaji wani mugun son husna se shigrshi yake, mik'ewa yayi ya nufa dakin babanshi, yai sa'a hajiya itama tana wajen, zube musu a kasa yayi ya fara kuka Dan Allah abbanshi yai hakuri, kamar bemasan yana yiba, Dan haka ya rike kafan babanshi yana kuka, har abun yaba hajiya haushi ta daka mai tsawa tace" kai kayi hakuri tunda ya riga ya yanke hukunci, nima kaina banga aibun husna ba...Alhaji inma kana tinanin husna shiiyace" to ba haka bane!!


Alhaji yana jinsu, bece musu komai ba, mufeed ne ya mik'e yace" nasan ku kuka haifeni, kunada ikon ku juyani yanda ya kamata, Amma abba tunda na nuna ina son husna Ku amince mun mana


Babanshi cikin zafin rai yace" ban amince maka... Mufeed gaba daya jin kalaman babanshi ya rude, ya mik'e ya fita, Ashe koda ya fitan ba daki ya wuce be waje yake shirin fita, Chan *buba* _ya kwalla wa su hajiya da alhaji kira, yace" Hajiya lafiya kuwa? Ga mufeed nan zai fita kuma da alama ba cikin hayyacinsa yakeba_ kan kace meye, Hajiya da Alhaji da gudu suka fito, Hajiya taje ta kamoshi, she fisge fisge yake, Dakyar dai suka kamoshi, suka shugo dashi daki


Hankalin Alhaji yai matukar tashi yanda yaga mufeed cikin kankanin lokacin ya chanza, har kwakwalwarshi tana shirin birkicewa... 


Mufeed kam se kubarni na fita, Ku barni na fita yake ta maimaitawa, nan aka samai karatun al'qurani, sannan Alhaji ya kira abokinshi farouk yai maza yazo,


Da'aka samai karatun Alhamdulillah yadan fara dawowa hankalinshi, nan ake ta tofamai addu'o sannan ya dan dawo normal, Amma, Husna na shugowa dakin kuwa komai ya rikice, mik'ewa yayi yazo daf da ita kuma sai ya koma ya zauna....


Itadai husna da gudu ta fita, cos batasan wainar da ake toyawaba...


Hajiya hankalinta ya tashi, farouk saboda yasan komai yace" Dan Allah, Alhaji kuyi hakuri Ku auramai husnan mana, kaga da yanda hankakinshi yake nema ya gushe........





Lol.....bara muga ko Alhaji zai yarda ko a'a....kuci gaba da kasancewa dani







Ummiey Xeey

[4/20, 12:43 AM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *​​RAYUWAR WASU​​​​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​​​​*


*​​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM*​​​ 

    _​[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]​_


​FB Page​ 

https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/


        ​  _​•••°°°Devoted  to......°°°•••​​​_

*​​​​​Miss Zarah Mansur😍​​*


Shout out to *Zauren UⓂmiey Xeey...* _Gaskiya inajin dadin yanda kuke son wannan littafin nawa...Allah yabar kauna yan uwa...zan rayu daku, zan mutu da Ku Abadan da ni daku zamu zauna_


*PAGE 87➖88*


"Farouk yace m sorry daddy, duk d bansan dalilin da yasa kace mufeed bazai aura husna ba, Amma ya kamata ka duba, kaga fa yanda yake shan wahala!


Wani nunfashi Alhaji yaja...yace" to shikkenan, na amince ya aureta, Zumbur mufeed ya tashi yana kallon babanshi, gani yake kamar a mafarki,  mufeed besan time din, Daya mik'e ba yaje gaban dad dinshi yana nagode Abba.. Hajiya gaba daya abun tausayi ya bata yanda mufeed yake Abu..


Alhaji shima kanshi mamaki abun ya bashi...tabbas kalma daya ka furtawa mutun zai Iya sanadin wargazar da farin cikin mutun, haka zalika kalma daya zata Iya sa mutun farin ciki na har abada.... *Take note readers* 


Bayan dakin yadau shuru na wasu mintinane, Farouk ya kalla mufeed ya sakar mai murmushi, hajiya tace" bara Mu baka waje qila zaku zanta,


Alhaji yace" NO ki zamanki ai komai dake za'ai, kan kace meye hankalin mufeed Alhamdulillah ya dawo, chest dinshi ya dena bugawan nan


Alhaji nan sukai magana an yanke auran nan da sati biyu, Komai Alhaji zai ma mufeed, bangaren wasu kaya kuma hajiya zatai wa mufeed... Atakaice dai auran gata za'ai musu


Sun gama tattaunawa...Mufeed da farouk suka wuce part din shi, nan fa suka fara shirye shiryen yanda abun zai kankama


Mufeed yaji dadi sosai...da ya tuno Husna se yace" a zuciyarshi she's mine, se yai smiling


Bangaren Su Alhaji kuma tun fitar Su mufeed, hajiya taje ta kira husna, tazo cikin ladabi da biyayya ta zube a kasa, Hajiyane ta fara magana kamar haka

"Husna kiyi hakuri mun zarce wani hukunci ba tare da kinsani ba..duk da muna zargin ko hakan ne, bamu sani ba, Zamu aura miki Mufeed, please kiyi hakuri!! 


Da sauri husna ta dago kai ta kallesu, tana son cewa wani Abu Amma ta kasa, "Alhaji yace in akwai magana kiyi, 

Husna cikin murya me sanyi tace" ah ah ba komai, nagode da komai da kukaimun, Kun sharemun hawaye Sosai, Allah ya saka muku d gidan Aljannah, "sukace Ameen"


Alhaji matuka yaji dadin yanda Husna keda tarbiya, shima kanshi yaji yana sonta. 


"Sukace  Shikkenan, Ta tashi ta tafi daki, tana shiga Alhamdulillah tace" a zuciyarta Dan ita gani take inba mufeed dinba waye zai aureta? Ranar dai wuni tai Dan murna gashi ba islamiya bare taje taba kawarta labari


***********************

Farouk yana shiga gida, matarshi Ummie, taga se fa'a yakeyi, itama smiling tayi, "tace yau kuma me gida dame akazo mana?

 Farouk kara yalwata murmushin shi yayi yace" dear wife mu shiga daki dai ko, nan ta kama hannunshi sukai daki suka baje a pallow, Nan ya soma bata labarin ina wannan yarinyar? Wanda mukaje hospital dubata?


Ummiey tace" eh na ganeta, Nan farouk ya gaya mata komai mufeed zai aureta, ansa bikin nan da sati biyu, Har zuciyarta taji dadi, Tace" to Alhamdulillah insha Allah kuwa gobe zanje, tun yanzu mu fara sabawa, 


Farouk yace" dadai yafi kam....nan suka ci gaba da hirarsu.. 


Ummie ce zaune, se tinanin Husna take, a zuciyar ta tace Allah sarki, Yanzuma irin yan gyran amaren nan da ake ba samu zatai ba, Wani tausayin husna taji, Kome ta tuno naji tace" Allah ya kaimu gobe



*Washe gari*

Tun Wuri Ummi ta tashi tai duk abun da zatai, misalin 10.am ta gama komai Dan haka farouk ya kaita gidan Su mufeed, ya kira husna yace" ga matar shinan, ya kawota ta gaishesu Su saba...lol husna ta gane Ummi, ita ta kawo mata ruwan zafi time din suna asabiti, Dan haka t rufe ido wai ita kunya...


Ummi ce ta kama mata hannu sukai daki, nan suka kara gaisawa...Ummi ce t fara magana kamar haka" amarya bakya laifi, yanzu wani shirye shirye kikeyi?


Husna tace" ba komai, Ummi tai murmushi tace" nayi tinanin haka, nan ta bude yar jakarta ta dakko mata wasu kayan mata, dan gyarab jiki, duk ta nuna mata yanda zatai amfani dasu, kuma insha Allah zatai kokari kusan kullun ta dinga zuwa, dan komai ya kammala cikin tsari...Husna tace" kai ammafa nagode, nagode, bansan me zancemiki, 


Ummi tace" bakomai ai muna tare, nan husna ta fito da wani number tace" ta kira mata ita kawartace a islamiya, aiki ba musu ummi ta amsa ta kirat, nan husna suka fara hira, tace" ansa mun rana fa nan da sati biyu, Khadija tace" haba? Dawaye?

Husna tce" yayana mana

Khadija tace" to Masha Allah, yimun kwatancen gidanku Nazo, aiko tayi,


Bayan sun gama wayar ba'ai 30 mins ba Sega khadija ta shugo, nan fa suka hadu su 2 seba husna yan shawarwari suke yanda zata gyara jikinta, da yake sun dan fita wayewa...aikuwa taji dadi sosai nan take ta fara amfani da wasu.......kai mata


Gaskiya husna taji dadin  haduwa dasu, misalin 12 Ne, Khadija tace"  zata tafi, sukai mata godiya sosai...


Husna lol..tun randa aka ce mata zata aura mufeed wani kunyarshi takeji, around 5pm ne Suna zaune da Ummi sega mufeed da farouk sun shugo, kirari farouk ya fara mata wani kunya duk yabi ya ishe husna, Mufeed kam kunyarnan da takeji wani kara sonta yakeyi, 


Amaryata yace" Dan kunya husna batasan lokacin da Ta bude baki cikin muryanta me sanyi tace _Dan Allah yaya ka dena_ abun dariya ya basu dukansu, farouk yace bara mu barki haka, My wifey taso mu tafi ko?


Ummi ok tace" sannan ta fara shiri, suka wuce gida....



Da daddarene..kowa ya hallara a pallow







Danci gaban labarin sai Ku biyoni









Ummiey Xeey

[4/22, 12:08 PM] Xeeexeeetah: ❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣

                 *​RAYUWAR WASU​​​​​*

❄❣❄❣❄❣❄❣❄❣❄


​​​​​​​​​NA........ ✍🏼​​​​​​​​​

*​​​​​UⓂmiey Xeey Abakson​​​​​*


*​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​​* 

    _[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_


*FB Page* 

https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/



        ​  _•••°°°Devoted  to......°°°•••​​_

*​​​​Miss Zarah Mansur😍​*


```Dedicated to duk me suna asma'u yau takwarar ku tana birthday....```

*24___04___2018*


*Hip hip hip hurray🎈🎈🎈*


*EMNOOR AHMAD DON*


_May this day be the beginning of another beautiful year for you. May there be pleasant surprises, loads of joy and infinite happiness. Wish you a very happy birthday._


🎈🎈🎈🎈🎈🎈🎈🎈🎈🎈

_Zan rayu dake, zan mutu dake, Abadan dani dake zamu zauna....har Aljannah insha Allah_

🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂

_It's your day baby.....have fun... Stay bless....Allah ya albarkaci rayuwarki sweet heart_

*HAPPY BIRTHDAY ONCE AGAIN*



*PAGE 89__90*



Da daddarane kowa ya hallara a pallow, suna kallon T.V mufeed ne ya mik'e yace" dad bari naje na kwanta akwai aiki gobe okay yace" Amma yana lura dashi like sun ta kuramai ne yaso dagashi sai husna, da Alhaji ya lura haka har mufeed ya fita ya kirashi, yace ya zauna, Alhaji ya kalla Hajiya yace" muje ciki ina son magana dake...Ran mufeed ba karamin fari yayi ba,...dan dad dinshi mutun ne me lura sosai


Dasu hajiya suka shiga daki, Alhaji yace" bafa wata magana bane, kawai naga kar mushiga hakkin yaron nan ne kuma naga alama yanaso yai magana da husna sai yasa nai dubaran haka, "Hajiya tace aikuwa ka kyauta nan suka ci gaba da hirarsu yanda bikin zai kasance


Bangaren mufeed kuwa, tun dayaga Anbasu waje matsowa kusa da husna yayi, itakam se matsawa takeyi, A ranshi yace" kita matsawa akwai ranar da zan kamaki ae, ganin taki zama kusa dashi yasa ya kyaleta, nan ya fara mata irin hira, haka Amma bawai ta sake jikinta bane...ita duk tsoro takeji wai Kar Alhaji Su fito Su samesu haka, that's why bata sake jikiba, Sun dan yi hira dai har yake tambayanta me take bukata itadai tace" bakomai, hakanan yaga kamar tana tsoronsa ya kyaleta yace" saida safe...ta tashi ta kulle part dinsu, ta tsaya ta window se hangenshi takeyi, har ya juya ya dawo ya manta key dinshi, still tana wajen, ta tsunduma kogin soyayya, knocking din kofa taji da sauri ta bude.


Abun ne ya bashi mamaki wai ya akai yana knocking ta bude, Husna kallonshi take tayi ita duk duniya ba Wanda takeso yake burgeta kamar shi, har ya dauka key dinshi idonta na kanshi, abun yama mufeed dadi at least yanzu ya gane tana sonshi, Zai tafine ya matso kusa da ita daf, ya hura mata iska a fuskar ta, nan ta dawo daga dogon tinanin da take, ya kalleta yace" jeki kwanta, ta bude baki ta fara magana cikin yanayin Irin soyayyan nan ya kamata tace" ina jirane ka fita na kulle.


Yai murmushi yace" a a muje na rakaki daki ki kwanta kawai, kamo hannunta yayi, har kofar room dinta ya kaita yace oya shiga dakin, good nyt my baby, ita kasa cewa komai tayi, daki ta shiga ta fada tinanin mufeed kawai takeyi, 


Yana ganin ta shiga, ya kira Hajiya yace" good night,


Tace" ok har ka wuce dakine? Yace" a a ina Pallow, tace okay se gata ta sakko daga upstairs, tace" akwai maganar dama da nakeso muyi, a inane kakeso Ku zauna? Anan gidan ko kuma zaka gaggauta karashe ginin Kane?


Mufeed yace" a a mamma anan ne inyaso daga baya semi koma chan tace okay, Tunda dare beyiba ka kira masu gyara, tun yanzu Suzo gobe, inyaso insunzo se asiyo duk abun da za'a bukata agyara maka part din, ok yace yai mata sallama


Yana shiga ya kira masu aiki, akan suzo gobe akwai yan gyare gyaren da za'ai sukace ok Allah ya kaimu,


Washe gari Monday tun 6 ya tashi, yai wanka beyi break fast ba, cos ya Dade beje wajen aiki ba, yai wa iyayanshi sallama zai tafi se Friday zaidawo, se leke yakeyi ko zaiga husna amma ina, itama tanajin muryanshi kamar ta fito, ta kasa dan jiya daya rike mata hannu kunyarshi takeji, da yaga bai ganta ba yai wucewarsa gidansu farouk, cos tare zasu tafi, yana shiga yaga farouk na break fast nan shima ya zauna, har farouk namai tsiya wai gauro...ummiey nata dariya tace" ai dai ya kusa samun mata dai ko? 


Mufeed yace" yauwa fadamai dai, suna ci suna barkwanci har suka gama suka nufa wajen aiki...


***********************

Masu aiki kam sunzo, da yake dad Nanan shi ya basu komai, ba wani gyara ma bane me yawa, penti ne kawai akayi, a duka dakunan, Masha Allah yayi kyau


*Bayan kwana biyu*

Dad gaba daya sunje sunma mufeed siyayyan komai, daga kan atamfa, less komai dai da ake sawa a akwati, bayan sunyi siyayyan basu wuce ko ina ba se gidan kanin babanshi Alhaji zubair da yake rafin zuwa a Kaduna a chan aka ajiye komai 



Bangaren Su mufeed kuwa kwanan Su biyu, baiji muryan Husna ba, Ya kalle farouk yace" kai gaskiya farouk kana kokari sosai, wlhi kwana biyu da banga husna ba duk na gigice, Farouk yai dariya sosai, yace" tun baka aureta ba? Idan ka aureta kumafa?, " mufeed yace ai ba zuwa ko INA... Farouk yai daria sosai yace" lalle damafa Ku irinku da bakwa labarin budurwa idan kukayi se Ku nuna kunfi kowa Iya love, mufeed ya dariya yace" eh din nidai bari na kira.....



Hope kuna enjoying.... Love you alL

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *