Shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wato Hausa Novels Blog a kyauta wanda muke kawo muku littatafai daga marubuta daban daban. dandalin hausa novels | dandalin hausa novels| hausa novels facebook | completed hausa novels on wattpad| hausa novels wattpad | hausa novels pdf | hausa novels world | hausa novels documents | dandalin littafin hausa | duniyar hausa novels | dandalin littafan hausa | home of hausa novels facebook | hausa novels world | littafin hausa zalla

Thursday, December 2, 2021

FATU A BIRNI COMPLETE HAUSA NOVEL

adsense here

FATU A BIRNI COMPLETE HAUSA NOVEL

 [1:58PM, 5/4/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

 

01

CIKIN TASHA:

Mutanen dake fitowa daga cikin bus din ne na hango wata matashiyar budurwa, wacce inka lura da yadda take waige waige tana zare idanu zaka tabbatar yaune farkon shigowanta garin Gombe, "Gombawa diban fari, ba'a kwana daku ba an tashi daku"😜 Itama FATU haka ya ksance da ita don ynxu misalin karfe 7:20 na safe. Matsawa gefe tayi ta tsaya inda bbu mutane sosai ta cigaba da dube dubenta. Can nesa ta hango wata mai sayar da kosai da dankali a cikin tashan. Nufanta tayi da sauri cikinta na bada wani sauti qululululu don rabon da taci abinci tun jiya da rana sai fura kadan da kakanta ya bata da dare. Sauri take yi har ta isa, sallama tayiwa mata mai sayar da kosai, matar ta amsa, fatu tace a bata kosai da dankali na dari, matar ta sa mata a leda ta miqa mata, kudi ta ciro 500 daga cikin jakarta ta miqawa matar, aka bata canji, gurin wasu yara masu sayarda pure water taje gefe kadan da mai sayar da kosan. Ta sayi guda biu. Anan ta fara tunanin a ina zata zauna taci,  don har masu shaguna sun fara budewa. Bakin wani shago taje inda bbu mutane ta zauna, juya baya tayi yanda baxa a ganta ba ta fara cin kosan tana korawa da pure water. Sauri sauri har ta gama. Alhamdulillah ta furta, sannan ta wanke hannunta ta goge bakinta da zumbulelen hijabinta. Minti biyu da haka ta miqe hade da karkade jikinta ta dauki jakanta ta rataya ta cikin hijabi. Wajen tashar ta fito tana tunani barkatai a cikin zuciyarta. Kuuuuuuuuuuu sai timm. Innalillahi abunta matar dake cikin motar ta fada cikin kidimewa. Kafin ta fito har an fara taruwa akan fatu, tana fitowa tayi kan yarinyar da saurinta tana su taimaka mata su saka ta cikin motar ta. Wasu mata yan sharan titi ne suka taimaka mata suka sata a mota yayin da matar ta shiga driver seat ta cilla kan titi sai hospital.

[2:25PM, 5/4/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

 

02

Hospital:

Tana isa asibiti ta shiga sai gata ta fito da nurses biu hade da gadon tura mara lafiya. Suka ciccibi fatu suka daura akan gadon sukayi ciki da ita cikin sauri. Emergency aka shigar da ita, bayan 15 minutes wata doctor ta fito da sauri matar ta tare ta, tace "ya patient din? Doc tace "da sauqi don bata buge sosai ba, tsoritan da tayi ne yasa ta suma, sai kurjewa da tayi a kafa. Ynxu za'a kaita dakin hutawa zata farka nan da 4-5 hours. Don tana bukatar hutu. Tana gama fadan hka tayi gaba abinta yyinta wata nurse da gangaro fatu a kan gadon marasa lfyn ta kaita dakin hutu matar ba biye da ita. Ta kai minti biu tsaye a kanta sannan ta juya ta koma mota, yaronta dan kimanin 7 yrs yace 'mum ina wanda kika bugen? Sai a sannan ta tuna ashe tare suke, school zata kaishi da yake yau monday tana sauri kar y makara, shine hatsarin ya faru. Shafa kanshi tayi tace 'farouq tana ciki an bata gado, muje in kaika school.

Acan school tayiwa teachers bayanin abunda ya faru don yara sun dde da shiga class. Komawa gida tayi wanda a lokacin 9 da yan mintuna. Ta samu dija mai aiki tana goge a palour, 'sannu da dawowa hajia' hajia ta amsa tace 'kiyi abinci da mutum 1 za'a kai asibiti, na buge wata yarinya a hanya. Bata farfado ba balle in san gidansu, na duba jakanta banga tana da phone ba ko ID card. Cikin jimami dija tace "to hajia Allah ya kiyaye na gaba, taji ciwo sosai ne? Hajia ta mata bayanin da Doc ta mata sannan ta haura sama tana tunanin yarinyar game da tambayoyi cike a kanta wanda bbu wanda zai bata amsan sai yarinyar. Don daga ganin shigar da tayi zaka gane yar kauye ce, amma cikin jakarta kudi dari biyar biyar sabbi wanda yawansu zai kai 25k, kuma jakan nata irin na yara masu zuwa makaranta ne, sai kaya kala uku. Ni kaina mmn Fa'iz sai da zare😳. Duk answers na gurin fatu wacce har ynxu tana gadon asibiti bata san duniyar da take cikiba.

 

Taku Maman Fa'iz👯

[11:44AM, 5/5/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

 

03

Fatu bata farka sai 12:23. A hankali take bude idonta har ta fara gani rass. Juyo da kanta tayi gefe inda taji muryan mace na mata sannu, kyakkyawar mata ce mai dan jiki kadan wanda da alama ta danbmanyanta,  "Ya jiki ta qara cewa da fatu, a hankali ta furta da sauqi.  Sannan ta fara qoqarin tashi, matar tayi hanxarin taimaka mata ta zauna. Tace "ki dan huta sai kici abinci. Bari in hada miki tea. Tea ta hada mata mai kauri tasha kadan tayi hamdala. Sannan matar tace meye sunanki, kuma a ina iyayenki suke? "Suna na fateema ana cemin fatu, dangina suna kauye mai suna Garin Modibbo dake karkashin qaramar hukumar Akko. Matar tace "sunana hajia kulsum, nice na buge ki da mota ina sauri zan kai dana makaranta. Kiyi hakuri. Hope yanxu bakya jin ciwo? Daga kai fatu tayi, hajia kulsum tace "gurin wa kika zo nan garin? Ina son in kaiki in bada hakuri. Saurin girgiza kai tayi kanta na qasa tace "a'a hajia hakama ya isa, ba sai kinje ba, nagode. Hajia  kulsum ta tashi ta deba mata abinci da kyar fatu taci rabin plate tace ta koshi tasha ruwa. Hajia na lura da yanayinta, yarinyar tana cikin damuwa. "Hajia ina son zuwa bandaki" hajia kulsum ta taimaka mata taje bandaki, kama ruwa tayi sannan tayi alwala ta fito. Zama ta qara yi  a kan gadon, shiru sukayi na dan lokaci sannan aka fara kiraye kirayen sallah. Sukayi sallah, sannan Doc ta shigo ta duba fatu, ta mata questions game da yadda take ji. Doc ta juya gurin hajia kulsum tace "zaku iya tafiya gida, shes gud now" ta fita. Hajia ta fita taje ta biya kudi ta dawo tace mu tafi. Sun fito harabar hospital dinne fatu tace "hajia ko kun tsinci jakata" hajia tace "eehh, yana gidana manta wa nayi ban dauko miki ba. Amma muje  sai ki karba. Mota suka shiga suka tafi. Unguwar GRA suka shiga, ita dai fatu in banda kalle kalle bbu abunda takeyi, wani layi suka shiga wanda yafi ko ina haduwa don gidaje 20 suna kallon juna sai titi a shimfide a tsakiyarsu. Gaskiya fadin tsaruwar houses din ma bata lokaci ne. Nidai mmn fa'iz nace kamar a turai. Fatu kuma tace Aljannar duniya. A cikin jerin gidajen wata mota hadaddiya ta fito ta hau kan titi, hakan yyi daidai da juyowar fatu wacce take kalle kalle tun shigar ta unguwar mutumin da ta gani a cikin motar shiya sata daskarewa, bakinta a bude tana nuna shi da yatsa, har yazo ya wuce baima san tanayi ba don waya ma yakeyi yana murmushi. Horn hajia tayi a bakin gate din gidanta wanda yake kallon gidan da mutumin ya fito. Aka wangale gate ta kusa hancin motar har ta samu parking space tayi. Sai a sannan ta lura da fatu wacce idanunta na tsiyayar hawaye tana nuna glass da yatsa, fatu" ta kira sunanta amma bata amsa ba, dafa kafadarta tayi ta juyo a firgice sannan ta fashe da matsanancin kuka wanda yasa hajia cikin wasi wasi. Anya yarinyar nan ba aljanu gareta ba? Ace yarinya da ita ta fito daga garinsu ba kowa tare da ita, kuma ba'a mata komai ba tana kuka tana nuna glass. Whats wrong with her? Kodai auren dole za'a mata ta gudu? Ko ko ko?

 

Maman Fa'iz👯

[9:05PM, 5/7/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

 

04

Fitowa hajia tayi daga motar ta zagayo inda fatu take, bude murfin kofan tayi ta kamo hannun fatu suka shigo cikin gida ta zaunar sa ita kan kujera a palour. Fatu ta cigaba da kukanta. "Dija dija" dija ta fito dga kitchen ta ce "gani hajia" hajia tace "taimaka min da ruwa pls" komawa kitchen tayi ta fito da tray an daura swan water da cup. Ta ajiye ta koma tana tunanin wace yarinya ce haka hajia ta samu? Daga kafada tayi tace hala yar aiki ce. Hajia ta tsiyayi ruwa ta miqa ma fatu wacce kukanta ya tsaya sai sheshsheka takeyi tace "kisha ruwa" ba musu ta karba ta sha, tayi ajiyar zuciya. Hajia ta numfasa ta fara magana "fatu a yanda na lura da yanayinki kina cikin matsala, kuma kinyi yarinya a barki ki fito daga kauyenku ke kadai ba tare da wani dan uwanki ba. Tambaya nake son miki, ki fadi tsakaninki da Allah, gurin waye kika zo anan garin? Fatu da tunda hajia ta fara magana kanta na qasa tace "gurin dan'uwa na nazo"  " a ina yake?  Fatu tace "na manta sunan unguwan amma yana cikin jakata. "Farouq farouq hajia ta kira shi yana room dinshi yana buga game, tun 12:30 y dawo daga skul. "Gani mummy" "jeka room dina ka dauko min wani skul bag akan bedside drower. Yace "to, amm mummy wannan ba itace ta mutu dazu ba? A cikin motarki. Hajia tayi daria tace a'a suma tayi not mutuwa, now get d bag. Ya juya da gudu ya dauko ya miqawa hajia ita kuma ta miqawa fatu, gurin fatu yaje da take kallonsa tun farkon shigowarsa. Yace daxu mum ta bugeki, kinji ciwone? Tace "a'a tana murmushi, amma kin suma ko? Tace ehh. Zai qara wata tambayar hajia ta katse shi tace " farouq jeka fara shirin islamiyya. In ka dawo she wll answer all ur questions. Ya haura sama da gudu yana cewa to mummy kar ta tafi, ta jirani fa.

Aljihun gefe na skul bag din fatu ta bude ta ciro wani pic hade da guntun paper ta miqawa hajia kulsum. Mamakine ya bayyana qarara a fuskar hajia data kalli pic din, paper ta bude ta qara gaskata abunda ta gani. Ba komai ta gani ba illa pic din sultan gefenshi kuma fatu ce, a kauye aka dauki pic din,don ga irin bukkan rumbun nan da ake ajiye amfanin gona. A cikin paper kuma adress na gidansu sultan ne,  wato gida mai kallon gidanta.

Hajia ta dubi fatu tace "wannan dan'uwanki ne? Fatu tace ehhh, "ya dangantakar ku take? Fatu ta numfasa tace hajia zan fada miki ko zaki taimaka min in shiga cikin gidan, don naga kamar sai da mota ake shiga irin gidajenku.

☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆

 

ASALIN LABARIN

Taku

Maman Fa'iz👯👯

[4:57PM, 5/8/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻          

Na Mrs Aslam Haidar

 

05

ASALIN LABARIN

    Kamar yadda na fada miki sunana fatima. Dangin mahaifina yan asalin garin modibbo ne, fulanine usul. Dangin mahaifiya ta kuma yan dukku ne, suma fulani.    

Kaka na mallam Aminu malami ne sosae wanda yake koyarda almajirai da manya, yana da matarsa binta wacce tun auren saurayi da budurwa suke tare, auren dangi aka hadasu. Yayansu biyar amma biyu ba rai, uku ne suka rayu har girma, goggo innani itace babba, sai sama'ila da kaninshi jamilu sune suka rasu, sai babana mamuda da kaninshi muntari. Tun kafin a haifi muntari goggo innani tayi aure. Tun tasowan babana Allah y yishi mai kokari ta fannin karatu da neman na kanshi, baiyi boko ba amma yyi arabi sosae. Tun yana saurayi ya fara kasuwanci, inda yake bin kasuwannin kauyuka yana sayar da busheshen kubewa. In damina tazo kuma ya taya bbanshi noma. A yawonsa na bin kauyuka ya hadu da mamata a Dukku, tazo siyan kubewa ya ganta yace yana so, itama ta nuna ra'ayin hakan, bai bata lokaci ba ya samu babanta ya masa bayanin inda ya fito da sana'ar sa kuma yaga diyarsa yana so. Babanta yayi murna da jin haka, don akoyaushe addu'arsa bai wuce Rahmatu ta samu miji tayi aure ba, don tun tana karama mahaifiyarta ta rasu anan zamanta ya dawo gurin kishiyar mamanta, ba irin duka zagi da wahala rahmatu bata dandana ba, babanta kuma bashi da bakin magana kamar an asirce shi. Bukatarsa kullum ta samu miji tayi aure ko zata huta. Ya sami yayansa da maganan inda yaqi amincewa, wai tunda gida bai koshi ba baza a bawa bare ba. Kuma ai zatayi nisa da gida. Shi a sonsa a hada ta aure da dansa wanda duk garin bbu wanda baisan yana dauke dauke ba, bashi da takamaimen sana'a. Babanta ya nuna rashin amincewarsa shima, a haka suka tashi ba tare da tsayayyem magana ba. Babana kuma yana komawa gida ya sanar da iyayenshi inda sukayi murna da fatan alkhairi.

Sati daya da maganan babana ya koma dukku don jin amsarsa, Inda ya tafi da kakana wato malam Aminu. mallam sirajo (baban mamana) ya musu iso yasa aka shimfida musu tabarma a zaure, fura da nono aka kawo musu hade da ruwa suka sha sukayi hamdala, sannan aka fara magana. Yayan babana na aka kira yazo, koda aka koro masa bayani yace shi sam bai san zancen ba, fada yakeyi sosai ta inda yake shiga ba tanan yake fitaba, wai sai da baki suka zo sannan za'a kirashi, kuma sai da sirajo ya amince? To me  zaice? Ai yarsa ce yayi abunda yaga dama. Don anga danshi bashida abun hannu amma da mai kudi yazo shine xa'a bata? Karshe ma cewa yayi bbu ruwansa akanta yayi tafiyarsa. Zuciyar fulani ta tashi na mallam sirajo ya cewa mallam Aminu a yau za'a daura auren, karshen iko kenan. A ranar aka daura auren a masallacin garin bayan an idar da sallahn azahar. Sai shigowa da akayi da goro da cingam cikin gida yara na cewa an daura auren rahmatu da mamuda. Da farko ta aza wasane sai da taga inna haule (kishiyar mamanta) na watso mata kayanta waje tana cewa ta hada ta kulle yau zata tafi gidan mijinta. Tana hawaye tana hada kayanta inna haule bata daina masifa ba da yake bakinta daya da su yayan mallam sirajo da matarsa. Wasu na cewa bakin cikinsu ne ya kashe maman rahmatun. Babanta ya mata nasiha ya miqa amanarta gurin kakana. Tana kuka yana hawaye suka rabu. Basu dawo ba sai bayan isha. Kakata tana jiran isowansu sai kawai taga har da amaryan aka taho. Bayan sun huta sunci abinci mallam Amenu yake sanar da ita komai. Ta jinjina lamarin inda ta tausayawa mamata. Dakin babana aka gyara musu inda ya siyo mata duk kayan daki da ake sayawa amarya na wannan lokacin.

 

Hajia kulsum ta numfasa tace fatu ki tsaya anan. Lokacin sallar la'asar yayi. Dakin hajia suka shiga anan ta nuna mata yanda zatayi amfani da toilet din taa barta a ciki ta sauko kasa tana kiran farouq yazo driver ya kaishi islamiyah time yayi. Bayan ta shigo daki ne ta samu fatu har tayi alwala ta fito, sallaya ta miqa mata ta nuna alkiblah sannan ta shiga toilet din don gabatar da alwala. Fatu sake baki tayi tana kallon duniya tun a toilet din take kauyanci taba nan taba can da kyar ta yi alwalan ta fito, a dakin ma sai da taga kamar hajia zata fito ne ta tada kabbara.

 

Taku

Maman Fa'iz👯👯

[12:26PM, 5/10/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

 

06

Sunyi sallah inda fatu taci gaba da labarinta..

   Zaman lafiya akeyi tsakanin mamata da surkunanta, abu daya ya ke damun mahaifiyata rashin haihuwa. Duk lokacin da goggo innani tazo sai ta samu bakar magana ta yaba mata, nan ma kakata na mata fada. Ta shekara biyu ne ta shirya zuwa ganin gida. Tana isa ta tarar babanta ba lafiya sosai sai dai a kwantar a tayar, tayi kukan halin da yake ciki shi kuma yayi murnar ganinta, don tayi kyau tayi kiba. Ta bawa kowa tsarabar sa bbu wanda ta manta, bayan kwana biu tace a kaishi asibiti, mallam jauro (yayan babanta) yace ba za'a kaishi ba, ai rubutu da maganin gargajiyan da ta raina shi ya kawo shi har yau, yayi ta mita. Satin ta uku tana jinyarsa Allah ya amshi abunsa. Tayi kuka sosai bbu wanda bai tausaya mata ba. Bayan sadakan arba'insa akace azo ayi rabiyan gado, aka raba da yake ita mace ce bata tashi da komai ba sai budurwar akuya. Tun suna bata abinci har rannan mallam jauro yace shi ya gaji da ciyar da ita, hala wani mugun abun tayi acan mijin ya korota shine zata zo tace wai tazo ganin gida, ai wata biun ya cika mijin baizo ba, tana kuka tana bashi hakuri amma ko a jikinsa, hasalima inna haule da matarsa ce suke zugashi, a cewarsu zata cinyesu in suna bata abinci, Akuyarta ta sayar take cin abinci. Ranar sai ga babana ya zo inda ya tarar da rasuwan surikinsa, ya musu ta'aziyya yace zai dauki matarsa su tafi. Budan bakin mallam jauro cewa yayi kar rahmatu ta sake zuwa garin don wanda ya hada ya raba, (kuji rashin tunani da imani) in kuma tazo ta nemi inda zata sauka badai gidansa ba. Mamata tayi kuka kamar ranta zai fita haka babana ya jata suka tafi. Anan yake tambayanta yan'uwan mahaifiyarta. Tace fulani masu yawo ne, sunzo dukku babanta  mallam sirajo ya ga  mahaifiyar ta wacce ta taba aure a cikin yan'uwansu amma zaman baiyi dadi ba, 'yarsu daya suka rabu da mijin, aka daura musu aure, bayan wata 2 sauran kuma suka kara gaba. Daga nan basu kara yowa ta dukku ba. Sun dawo gida ta samu muntari yayi amarya.  Shekararsu 9 Allah bai basu haihuwa ba, inda amarya asabe ta haifi 'yaya 4, goggo innani ta hada kai da asaben muntari suna kuntata wa mamata kakata na tsawatar musu. Ana haka har ta samu cikina sunyi murna sosai amma cikin yazo da laulayi ta wahala sosai inda tana haihuwata tace ga garinku. Babana yayi kukan rashin matarsa mai hakuri da juriya ga sanin dattako. Ran suna naci sunan kakata (mamar babana) wato Fatima inda ake ce mini fatu. Na taso cikin kulawan mutum uku, kakannina da babana. Don yanzu kawu muntari ya fara bin hudubar su goggo innani wai an fi sona akan yayansu. Na yi primary anan kauyen mu. Inda duk garinmu bbu wanda ya kaini kokari, sannan na shiga secondry ina jss 2 babana ya hadu da accident akan hanyarshi ta zuwa kasuwanci. Bamu da labari sai gawarsa da aka kawo. Fadin irin tashin hankalin da muka shiga ma bata lokaci ne. Nayi kuka har na rasa inda zan tsoma raina. Anan nake tunanin kodai gaskiansu goggo asabe cewa dangin mu akwai mayu masu cinye duk wanda suka rabe su. Kakata kuma tun daga lokacin ta fara kananun rashin lafiya. Na cigaba da karatuna inda kakana ya jajirce sai na gama secondry skul, duk sa'annina sunyi aure daga mai 'ya'ya biu sai mai uku. Na kuma faranta masa nayi candy daga nan kuma samari suka min caaa! Don duk wanda yazo gurina kakana kance mishi sai na gama karatu. A cikinsu kuwa harda dan kawu muntari da dan goggo innani. Ni kuma wallahi duk cikinsu bbu wanda nake so.

Rannan ina bacci da dare naji ana shafani, bude idon da zanyi naga babangida dan kawu muntari ne. Zan yi ihu ya toshe bakina, na takarkare na dankara mushi cizo sannan nayi ihu. Mutanen gida suka fito ana haskawa. Fitowa nayi da gudu cikin gida ina haki, kaka yace "mene fatu me ya sameki? Nace "babangida ne ya shiga dakina kuma yana tabani" na fada ina matsar kwalla wanda har lokacin jikina bai daina rawa ba. Inna asabe ta cabe "munafuka, sharri zaki yiwa yayan naki? Me zaiyi da ke jiki kamar na aljanu" kaka ya dakatar da ita yace "ina babangidan? Ya ce gani nan, "kaji abunda fatu  tace? Yace "wallahi karya take min, na fito zaga bayan gida ne naji kamar nishin mutum a daki, nayi zaton batada lafiya ne da na haskata sai naga mafarki takeyi tana wannan nishin. Shine na bugi hannunta tana tashi tasa ihu. Salallamai goggo asabe tasa wai nayiwa danta sharri. Shi kuma ya fita zaure inda dakinsu yake yana mita wai dama ba'a sonsu a gidan. Ni kuma sai rantse rantse nake, kakanina da kawu muntari sun yarda don zai aikata. Kakatace ta jawoni dakinta na karasa kwana anan. Daga ranan na dawo dakinta kwana. Sati da faruwar lamarin kakata ta tashi da matsanancin ciwon kai da zazzabi ga jiri da yake dibanta, anyi magani na gida har asibiti aka je inda suka ce jininta ne yahau sosai.

[12:42PM, 5/10/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

 

07

Inda sukace jininta ne ya hau sosai, bata jima a asibitin ba ta koma ga mahaliccinta. Damuwa goma da ashirin.

 

Anan fatu ta fara hawaye, hajia kulsum cikin tausayawa ta miqa mata tissue paper ta goge fuskarta sannan taci gaba.

Na shaku da kakata sosai, a matsayin mahaifiya na dauke ta. Bana jin rasuwar mahaifiyata kamar nata. Bayan rasuwan kakatace zamana ya dawo gurin goggo asabe, nine wankinta dana 'yayanta da yake duk maza ne sai autar ta zainab yar shekara 4. Shara, wanke wanke da girki ya zama daily work dina, duka zagi da tsangwama kuma har na saba dasu. Duk abunda yake faruwa kakana bai sani ba, da yake baya zaman gida yana can masallaci tare da tsofi irinsa suna karatu. Idan ya ganni ina kuka sai yayita lallashina da inyi hakuri komai zai wuce inyi ta musu addu'a, Tunaninshi mutuwar iyayena yake damuna, bai san harda wahalan da nakesha yanxu bane. Kwatsam ranar wata friday bayan an dawo daga sallahn juma'a goggo ta sameni da duka wai ban gama abincin rana da wuri ba, na tsaya wasa, tace "shegiyar yarinya da ido kamar na mujiya ki gama abincin sannan kixo kiyi wanki, kuma wallahi kika kai la'asar sai naci uwarki. Ta aza mini rankwashi a kaina wanda ya sani sakin wani wahalallen qara, "kina jina ina miki magana kina daga min kai kamar wata kadangaruwa don ubanki" da sauri nace "goggo kiyi hakuri" na cigaba da sheshshekar kuka, na tashi da sauri na fada kitchen. Kakana ne ya shigo da sallamarsa ta amsa tana muzurai, Allah yasa baiji abunda tayiwa fatu ba, don batayi tsammaninsa yanzu ba, baya dawowa a wannan lokacin. Ya shige dakinsa ya jima sannan ya kwala min kira, ina sauri zanje ta yafuto ni, naje, murde min kunne tayi tace "saura ki fada masa wani abu sai na ballaki, bulaliya kawai" ta sake ni hade hankada ni har ina cin tuntube na shiga dakin kakana. Cewa yayi inje inyi wanka zan rakashi unguwa. Na fito na fada mata ta harareni tayi kitchen. Da sauri na watsa ruwa na fito, kaya nasa da hijabi na cewa kakana na shirya muka fita. Maimakon naga mun shiga gari sai naga munyi hanyar gona. A cikin gonarshi a karkashin wata bishiyar dorawa muka zauna. Yace "fatu me asabe take miki a gida? Don yau naji wasu maganganu sabanin hankalina" ban yi jayayyaba na fada mishi komai. Idonshi yayi jawur yace " mahaifiyarki rahmatu amanace a gurina haka kema amanace, bazan bari ta maida ke baiwa ba insha Allah zan nema miki mijin aure kwanan nan inda zaki sami yancinki. Nayi farin ciki da haka sosai. Yayita bani baki hade da nasiha sai yamma liss muka koma gida. Muna zuwa yace in shimfida mishi tabarma a kofar dakinshi ya zauna. Daga ranar ya dawo wuni a gida yana waje tare da mutane, zai aika a kirani sau goma shi ma zai shiga gida sau goma. Abun yana damun goggo asabe sai dai bbu yanda ta iya. Na murmure na fara samun kwanciyan hankali, kaka ya sama min miji dan ladanin garinmu. Hafizu yarone mai hankali da nutsuwa, ga karatun addini baiyi boko ba amma yana da sana'arsa ta dinki, Yana samu ba laifi. Kaka yace "ga zabina wato hafizu dan ladan, idan kin amince inje in sami babansa muyi magana" gaskia bana jin sonshi a raina amma hankali da nitsuwarshi sun kwanta min. Nace "kaka duk wanda ka zaba shine zabina, fatana Allah yasa in samu zaman lafiya da kwanciyar hankali" kaka yaji dadin furucina yace "Allah ya miki albarka uwargidana" daria nayi nace "Ameen tsoho na" carbinsa ya dauka da niyyan min dukan wasa nayi saurin shigewa gida ina daria shima yana daria. Daga kan da zaiyi ya hango wata mota tana tahowa ta layin unguwanmu ga yara rudududu suna binta da gudu, parking tayi a jikin katangar gidanmu. Samari biyu ne suka fito suka nufo kakana da har yanzu yake zaune a kofar gida bai motsa ba. Kallo ya dawo kansu aka manta da mota. Sun fi kama da turawa ko aljanu.

 

Taku a kullum

 

Maman fa'iz👯👯

[9:27AM, 5/18/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

08

 

Sallama sukayi ya amsa, kana ya dubi yaran da sukayi dandazo suna kallon samarin yace su tafi wasan su, kan kace me kowa ya watse don basu da rashin kunya. daya daga cikin samarin  yace

"Don Allah baba nan ne gidan mallam mahmudu? Duk'ar da kai kaka yayi sannan yace "ehh" still wanda yayi tambaya na farkon yace "gurinshi muka zo shi da matarshi, daga gombe muke" kaka yayi dan jimm sannan yace "Allah ya musu rasuwa dukansu" "sun rasu" saurayi na biyu ya fada cikin firgici, sannan ya nemi guri ya tsuguna yana "innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Allah ya jikanku".

Saurayi na farkon ya dubi kaka da tarin damuwa a fuskarsa yace "Allah ya jikansu yasa sun huta" "Amin Amin" kaka ya furta yana goge hawayen da ya zubo mishi ba shiri. Saurayi na tsugunne yace "jameel mu tafi" ya miqe jikinshi a sanyaye ya nufi mota. Kaka ne yace "zaku tafi baku sanar dani alakar ku ba" jameel yace "wancan abokina nane, sunanshi sultan, matar mallam mamudu wato aunty rahmatu qanwar mamanshi ce, uwarsu daya. "Allahu Akbar Alhamdulillah" kaka ya fada cikin tsananin mamaki don baiyi tsammanin za'a ga dangin mahaifiyar rahmatu ba cikin ruwan sanyi haka. "ai akwai rabo tsakaninsu sun sami 'ya mace fatu, tana nan, ni mahaifin mahmudu ne" farinciki ne kwance a fuskar kaka yana murmushi. Jameel ne ya kwalawa sultan kira ya fito daga mota still jikinshi a sanyaye, jameel yace "akwai cousin dinka fatu, 'yar aunty rahmatun ce" cikin doki yace "ina take? Yana kallon zauren gidan. Kaka yace "tana ciki, amma in bazaku damu ba ina son magana daku.

Tabarma kaka ya shimfida musu a zaure suka zauna, shiga gida yayi ya sameni  tsakar gida ina karanta wani  littafi, yace "uwargida ki samin ruwa a kofi nayi baki" nace "to". Miqa mishi kofin nayi ya karba ya wuce cikin zauren. Bayan sun qara gaisawa ne kaka ya fara basu labarin mamata har zuwa kaina, bai rage komai ba harda wahalan da nake sha gurin asabe idan taga kaka baya nan. Kaka ya qarasa magananshi da cewa "idan baza ka damu ba kai sultanu ka auri qanwarka zata fi jin dadi cikin ku, nasan dana fadi na mutu fatu bata da gata sai Allah, don wadannan ba riqeta da gaskia zasuyi ba" kaka ya cigaba da maganarsa duk akan sultan ya aureni ya taimaka min. Kan sultan ne yadau zafi yayi dana sanin nemo su, gaskia bazata sabu ba. Shiru yayi kansa a qasa ko motsi mai kyau bayayi, ya bude baki zaiyi magana kenan Jameel yayi caraf yace "hakan yayi kyau, Allah ya tabbatar da alheri" Amin. Kallon mamaki sultan yake bin jameel dashi don ya wargaza mishi plan, wata dabara ce tazo mishi in akayi sa'a zai fita.

Yace "mallam zamu koma gida sai daga baya inshaAllah magabata su zo. Kaka yace "mutum bai san ranar mutuwanshi ba, watakila bazan kai zuwa gobe ba har zuwa lokacin da zaka turo magabatanka, kamar yadda na fada maka nine ke riqe da fatu, ayau nabar dunia zasu iya aura mata wanda ransu yake so, inda zata cigaba da shan wahala. Nafi aminta dakai shiyasa nake so ayau a daura muku aure, "Shikenan" abunda sultan ya iya fadi kenan don tsohon ya cika kwarjini bazai iya mishi musu ba.

 

An daura aurena da sultan a masallaci bayan an idar da sallah. Inda kaka ya zame min waliyyi liman kuma waliyyin sultan. (Tarihi ya maimaita kansa). Gida suka dawo inda kaka yace ya tafi dani, amma sultan yace zai tafi wani course na wata biyu inya dawo zaizo ya daukeni, kaka bai kawo komai ransa ba ya yarda. Shiga cikin gida yayi ya barsu a zaure inda ya aika in kai musu abinci don ranar ni nayi girki. Har lokacin banida labari don kawu muntari yayi tafiya, asabe kuma taje ganin gida. 'yayansu kuma ba zuwa masallaci suke ba. Na fita na kai musu, durkusawa har kasa nayi na gaishesu mutum daya ne ya amsa yana min murmushi, amma dayan ko dago kai baiyi ba. Mai murmushin yace "me sunanki" nace "fatu" yace "masha Allah abokina yayi sa'ar mata" fita nayi ina mamakin maganarsa, to a ina hafizu ya sami abokai yan birni haka.

Shiga na keda wuya kaka ya kirani dakinsa, da farko nasiha ya fara min kan ya bani labarin abunda ya faru. Babu abinda na iyacewa illah hawaye da ya dinga bin fuskata, na rasa hawayen menene, ta wani gurin ina farincikin samun dangin mamata, while ta wani gurin ina tausayawa kaina don wanda aka aura min ko kallona bai yi ba. Na dade a dakin kaka sanna ya fita dubo bakinshi ko sun gama cin abinci. Ya fita ya samu jameel yaci amma sultan ko ruwa bai sha ba, jameel ne yake cewa wai sultan din azumi yakeyi.

Kaka ya musu iso cikin gida aka shimfida musu tabarma ta bayan dakunan mu gurin akwai bishiiya gefenta kuma rumbun ajiye abinci ne. Kaka ya wuce yana cewa bari ya kira fatun. Gefen su kadan na zauna akan wani dutse na sunkuyar dakai ina wasa da yatsuna. Mijin nawa dai har yanzu kansa na kasa bazaka game yanayin da yake ciki ba. Jameel ne ya fara magana.

[9:28AM, 5/18/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

 

09

 

Jameel ne ya fara magana "Amaryanmu kina lafiya" nace "lafiya kalau" ya kara cewa "sai kika ji an daura aure babu wani taro babu al'adu irinsu zance, bayarwa, kayan aure da sauransu. "Uhmm" na iya cewa. "Komai da kika gani muqaddari ne daga Allah, wannan aure naku insha Allah baza kuyi dana sani ba. Ya cigaba da maganan shi inda yake nuna mana mu riqe junan mu cikin amana duk da ba auren soyayya bane, ya karasa magananshi cikin nasiha. Duk abunda yake cewa sultan bai ce uffan ba, don wayarsa ya dauka yana dannawa. Mikewa yayi sannan yace "bari in barku kuyi magana, kar in takuraku da yawa" ya fada cikin tsokana. Mun fi minti biyar b wanda yayi magana can yace "kinyi makaranta? Nace "ehh" "ina kika tsaya" "secondry" yace "shekarunki nawa? Nace "17" sai lokacin ya dago kai ya kalleni 4 d first time nayi saurin sunkuyar da kaina. Can ya kara cewa "kin taba shiga birni" nace "Aa'aa" yace cikin bata rai "kin min yarinta da yawa, kuma karatunki baiyi zurfi ba, bana jin zan iya rayuwa da irinki" dai dai nan jameel ya dawo yace "times up, kar muyi yamma a hanya" hope kun daidata? Ya fada yana murmushi. Babu wanda ya kula shi don ni ina kokarin mayar da hawayen da yake son zubo min ne, jameel ne yace in matso kusa da sultan zai daukemu hoto. Shiru nayi sai da ya kara maimaitawa na taso na tsaya nesa dashi, turo sultan yayi gurina wanda yake aika masa harara ta ko'ina, baya yayi yace mu dago fuskokin mu, still kowa kansa na qasa, yace to bari in kira kaka, may be zaku fi jin  magiyarsa. Saurin dago da kanmu mukayi yace "smile" sannan ya daukemu a hoto. Abun mamaki yana daukan hoton wani abu ya fito daga cikin camera, ya kara daukan mu abun ya qara fitowa. Miqa min na farkon yayi na karba ban duba ba. Sultan har ya fita waje, ciro kati yayi daga aljihunshi ya bani, yace "wannan shine address na gidansu sultan, abokina yana da wuyar sha'ani amma in kika yi hakuri komai zaiyi karshe, ki ajiye address din don bamusan gaba me zata haifar ba" ya karashe maganarsa cikin tausayawa. Nace "Nagode Allah ya kiyaye hanya" shima fitan yayi inda ya iske kaka da sultan suna hira kamar bashi ne yake bata rai dazu ba. Tafiya sukayi kaka ya shigo cikin gida yana mai farincikin fatu tayi sa'ar miji. Ni kuma tun tafiyan jameel na nade tabarman na shige dakina ina kuka mai tsuma zuciya, daa kaka yasan wa ya aura min da bazaiyi farin ciki ba. Kiran da kaka yake min yasa nayi saurin goge fuskata na fita ina murmushi yace in sameshi a dakinsa. A dakinsa na samu guri na zauna ya miqo min kudi yace "sadakin ki ne dubu ashirin" nace ya dauka ni bana so, yace ai hakkina ne maza in karba. Na karba na wuce dakina na cigaba da kukana har bacci ya daukeni. Bugun kafa na naji anayi na tashi ya firgice goggo asabe na gani tsaye a kaina fuskar nan a tamke, tace "wani jita-jita nake ji a gari wai an daura miki aure hka ne? Nace "ehh" nan ta fara masifa ai dama dangin mu haka suke sai sunga mai kudi suke aura, ga babangida yana sona amma kaka ya hana shi. Allah yasa mijin nawa ma dan yankan kai ne, kallonta nayi ido cikin ido nace "ba kudin shi muka bi ba, sultan dan'uwana ne, mahaifiyarsa addar mamata ce" cikin mamaki tace 'eeeyeee' nace  "kwarai" fita tayi daga dakin tana jin bakin cikin auren, don yadda aka fada musu mijin nawa dan birni ne kuma ga kudi akace da mota irin ta sarkin Kumo yazo. Sadakina na boye don nasan ko ita ki 'yayanta wani zai biyo dare. An koma baya don goggo asabe tana ganin kaka ya fita zata fara cin zalina, girki kuma da shara wanke wanke nice keyi da kaka yayi maganan a rage min koda daya  ne cewa tayi horar dani takeyi, gidan wani zanje don haka ya kamata in saba da aiki, kaka kuwa ya yarda da magananta.  Bayan wata da daurin aure na wani mutum yazo da envelope ya bani yace aikoshi akayi daga gombe. Na aza wasika ce amma sai naga kudi ne 30k. Kakana na kaiwa yayi godia yana cewa sultan bai mance dani ba tunda har yana kokarin sauke wasu hakkina. Bayan wata daya muna tsammaninshi sai muka ga dan aikan rannan. Yace sultan yace a fada mana zai qara yin wata uku. Kowanne karshen wata sai dan aiken yazo da envelope kudine a ciki wataran 50k watarana 30k. Koyaushe aka kawo zanyi tsammanin akwai wasiqar sultan a ciki amma babu. Har wata 3 ya wuce babu labarinsa daga nan su goggo asabe suka fara habaici "ai nasan za'a rina, hala kakaba mishi ita akayi, yoo dama me zaiyi da kucakar yarinyar nan; shi dan birni. A haka zakiyi ta zama har ki tsufe, dama kudi kuke so to ai gashi ana turo muku" idan ta fara maganganun nan nakan shiga daki inyi ta kuka ina kallon hoton da jameel ya dauke mu.

[10:09AM, 5/18/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

 

10

 

Idan na gaji inyi alwala inyi sallah in kai kukana gurin Allah.

Sati daya daya wuce na cika shekara daya da aure, a cikin shekaran kuma dan aika yana kan zuwa kowanne month. Idan muka tambayeshi labarin sultan sai yace bai dawo bane. Hankalin kaka ya fara tashi ya fara dana sanin daura auren, akwai lokacin da ya kirani ya ke cemin ko zamuje kotu a raba auren? Nace mishi a'a, don nasan gwanda zamana da igiyar sultan akaina akan in zama bazawara hankalin kaka zai fi tashi. A ranar da zan cika shekara da aure muke tsammanin zuwan dan aika, a ranar na shirya plan dina don sanin matsayina. Yawanci bayan azahar dan aika yake kawo kudi, kaka na samu a kofar gida karfe 12:30 nace zan shiga jeji debo ganyen lalle, yace in aika yara mana, nace ina son zuwa da kaina ne, bai kawo komai a ransa ba ya mini izini. Already na gama shiri na fito, hanya kawai na yanka na shiga jeji inda nan ne hanyar shigowa cikin gari. Sai da na debo ganyen lallen na fito bakin hanya na tsaya a gindin bishiya ina jiran dan aika.

Nafi minti 30 na hangoshi yana tahowa kamar kullum a kan machine dinshi. Fitowa nayi ina tafiya nayi kamar ban ganshi ba, yazo dab dani na juya ya ganni ya ce ahh fatu me kikeyi anan? Yana kokarin tsayar da machine din, nace laa nazo tsinkar ganyen lalle ne yanxuma gida na nufa. Yace in hau ya isar dani, nace a'a nagode. Yace to ga aikan tunda na hadu dake a hanya, ki gaishe min da mallam Ameenu. Na karba nayi godia ya juya ya koma. Sai dana tabbatar yayi nisa sannan na bude envelope din, yau ma kamar kullum kudine babu wasiqa. Na fito da yar takarda daga cikin ledan da tun fitowana daga gida yana cikin hijabi na, hade da dan kunu a farar leda takardan na tura cikin envelope din na shapa kunu na liqe kamar ba'a budeba nayi hanyar gida ina mai farin cikin hukuncin dana yanke.

 

Jama'a menene fatu ta rubuta? 😳😳😳😳

Ina mai bawa masoya hakuri na rashin jina kwana biyu, phone dina ne ya samu matsala.

Luv u ol

 

Taku a kullum

Maman Fa'iz👯👯

[1:33PM, 5/19/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

11

Dawowa na gida na iske kaka na yana masallaci, don haka kai tsaye dakina na fada na ajiye kayan na fito nayi alwala nayi sallah. Ina idar wa naji kakana ya dawo, goggo asabe ta kirani in kai mishi abinci, naje na karba, har zan juya ta kirani na jiyo, "amm fatu yau ba'a kawo miki saqo bane, wallahi rance nake so ki bani na dubu uku, masifaffiyar goggon kin nan innani na ara a gurinta, don tsiya jiya har da aiko sadiqa tayi tamin rashin mutunci" nan ta fara matsar kwalla, kar ki manta hajia duk randa aka aiko kudi rabashi akeyi duk abunda aka bani ita ke amshe wa da wayo, wani tace zata biya bashi wani kuma tace zata karbo min maganin bakin mutane, Wani kashin na abincin gida, don wani abincin da muke ci ba'a cinsa a gidan maigari, kinga kamar taliya da dan waken fulawa, wallahi wataran harda macaro  muke ci (inji jawaheer😂😂). Hajia tace "Macaroni kike nufi? Fatu tace "ehh, sauran a ajiye saboda bukatun yau da kullum. Nace "an kawo in kaka ya bani zan kawo miki" na fita a zuciyana ina cewa anji kanku. Dakina na fara bi na dauko envelope din na wuce dakin kaka. A daki na iske shi yana kishingide, na masa sallama ya amsa, ajiye abincin na miqa mishi saqon nace a hanya na hadu dashi ya bani. Ya karba jikinshi a sanyaye yace zai kirani anjima. Ina fita naga goggo asabe a kofar dakinta tana jirana, sai da na isa tace ina kudin? Nace " sai yaci abinci sannan zai bani. Shiga dakinta tayi bata kulani ba ni kuma nayi shigewata daki ina jiran kiran kaka don karanta wasiqa. Bayan Minti sha biyar lamido dan goggo asabe ya zo ya kirani hijabi nasa na fita. Shiga nayi na samu guri na zauna nace "kaka gani" yace "takarda na gani a cikin kudin Allah yasa ba abunda nake zato bane, ya fada yana mai girgixa kai cikin damuwa. Nace "ba komai kaka Allah ya zaba mana mafi alkairi. Yace "ameen" hade da mikomin paper. "Hajia kinsan abunda na rubuta? Hajia tace "a'aa" fatu tacigaba "rubuta ban hakuri nayi na jimawan da sultan yayi bai zo ba, hakan ya samu asali ne ga riqeshin da akayi a kasar wajen, kuma kaka ya bari inzo gombe gidansu yana so yayi wa mamarsa suprise"

[10:17PM, 5/19/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

12

Tunda na fara kaka murmushi yakeyi cikin jindadi, har bansan lokacin da hawaye ya zubo min ba, na share ba tareda ya gani ba. Sai dana gama yace " fatu Allah ya amsa addu'a na, kullum burina mijinki yazo ya dauke ki, ayau Allah ya nuna min ranar" kwalla taff a idon kaka na farinciki. Hajia nayi dana sanin rubuta wannan wasiqar don bawai inason zuwa gurin sultan don ya karbe ni a matsayin matarsa bane, a'a don ya sauwaqe min ne nima in samu dai dai ni in aura. Kuma hakan zaisa kaka ya samu kwanciyar hankali. To amma tsananin farincikin dana hango shimfide fuskarsa sai tausayinsa ya kamani, ban kyauta masa ba. Kaka yace in shirya gobe in tafi. Kuka na fara Nace a'a sai shi sultan din yazo, zanyi ta zama da igiyarsa a kaina har ranar da Allah ya kawo shi. Ban taba yiwa kaka musu ba sai ranar. Bai ce min komai ba har na tashi na tafi dakina na cigaba da kukana, ina tausayin kaina da kaka. Da kawu muntari ya dawo aka fada masa abunda mijina ya rubuta shima ya bada goyon baya in tafi, goggo asabe kuwa hankalinta ne ya tashi don bata son taga abu mai kyau ya rabe ni. Ana gobe zan taho  na fara shirin tafiya gombe don inje ayita ta qare, na kasance koyaushe ina tunani da addu'ar Allah yasa zuwana ya kasance alkhairi. Hajia har abinci nake kasa ci, ace an daura mini aure yau shekara amma mijin bai ko waiwayeni ba. Abunda kaka ya fada min ne ya girgiza ni, wai da kawu muntari zanyi tafiyan!!! Tirkashi😳😳

Nace masa ai a wasiqar sultan yace inzo ni daya, na nuna masa tunda nayi karatun boko ai bazan bata ba koda a kano ne😜, Kaka ya amince. Da dare kasa cin abinci nayi don ina da tabbacin in naje sultan zai sake ni kamar yadda zan bukata. Da kyar kaka yasa na sha fura da daddare a dakinsa, mun kusan kai karfe goma yana min nasiha gameda inda zan koma wato gidan mijina, jinshi kawai nake yi ina mai tausaya mana.

Tun da asuba na gama shiri kaka yana dawowa daga masallaci naje na gaishe shi, ya miqo min 15k wai in riqe zai min amfani a can din. 5 din saman na dauka nace zai ishe ni, ya qara min nasiha ya bani addu'o'I. A lokacin gari ya fara haske, machine din abokin baba ne mukaji yana diri a kofar gida. Har daki na sami goggo asabe na Mata sallama, duk 'yan gida aka fito domin ganin tafiyana. Ban dauki komai ba sai 'yar jakana na skull da kudin sadakina 20k sai kayana kala 3 don nasan ba jimawa zanyi ba. Kudin kuma bashi kayanshi zanyi. Na haye machine din ina hawaye haka muka kama hanya suna daga min hannu. 6:22 muka iso kumo, direct tasha muka isa ya sakani a motar gombe, shi ya biyamin kudin motan ma, yayi tafiyarsa don anan kumon yake aiki. Bakwai saura motar mu ta tashi mune bamu shigo garin gombe ba sai 7:30. Anan na sauka na sayi abinci, fitowana kuwa tsautsayi ya afka dani. Wannan shine takaitaccen tarihina.

 

Shiru sukayi kowa da abunda yake sakawa a ransa, farouq ne ya dawo yana mummy oyoyo, hajia ta shafa kanshi tace "Ka dawo" yace "ehh, yauwa mummy kika ce dama baza ta tafi ba, to yanzu in mata questions din? Hajia tace "gata a gabanka ai" zuwa gurin fatu yayi yace "dama tambaya daya ya rage, ina ne gidanku? Kai tsaye fatu tace "a kauyen kumo, ka taba zuwa kumo? Yace "aa'aa" tace "kana kama min da wani sunan shi jameel" yayi caraf yace " ya jameel yayi aure rannan ya tafi da matarsa south africa wai yana aiki, amma naji dady na cewa ya kusa dawowa" kafin ya qara bude baki hajia ta katse shi tace "aje a canja kaya ayi shirin zuwa sallah magrib" ba musu ya haura sama da gudu. Hajia ta juyo ta kalli fatu da kanta na qasa tace " jameel dana ne yana da kanne 4, mahmud ne mai binsa sai khadija da Aisha da autana umar farouq. Mahmud yana karatu a cyprus lawyer ne, insha Allah nan da 4 months zai kammala ya dawo gida. Khadija da Aisha sunyi aure inda khadija ke Abuja Aisha ke kano. Jameel abokin sultan ne tun suna yara, daa ba'a unguwan nan muke ba, muna jeka da fari ne, Allah cikin ikonsa ya budawa mahaifansu inda suka sayi fili anan GRA, In kin lura yanayin ginin gidajen iri daya ne amma kowanne da design dinshi. Skul daya sukayi tun daga primary har sec, inda a university kowa da zabinsa, don sultan fita waje yayi ya karanci Business ad, while jameel yana gwags karantan likita. Alhamdulillah sun kammala with flying colors. 8months da suka wuce jameel yayi aure ya tafi da matarsa south africa akan karatunsa. Mahaifiyar sultan qawatace sosai, hakama dads dinsu suke abokai.

Kiran sallah da aka fara ya tsayar da hajia, sai da aka idar tacewa fatu ta isa daki tayi sallah, ita kuma hajia ta nufi kitchen don duba me aka girka.

 

 

 Nima na fita daga gidan don inje in daura nawa sanwar kar oga ya dawo babu abinci, kunsan bature yace "Hungry man is an Angry man"🏃🏽🏃🏽🏃🏽🏃🏽🏃🏽

Taku a kullum

Maman Fa'iz👯👯

[12:32PM, 5/22/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

13

Sun idar da sallah suka ci abinci, dija mai aiki ta tattare gurin fatu ta taya ta suka kai kitchen ta fito palour, farouq sai zuba surutu yakeyi fatu tana biye mishi har aka kira sallan isha ya tafi mosque suma suka tashi don yin sallah. Bayan sun idar da sallah ne suka dawo palour hajia ke tambayar fatu "sultan din bai baku number wayarshi ba? Fatu tace "hajia ai address din ma ya jameel ne ya bani bashi ba" kuma ni ban taba yin waya bama, to da waye zanyi? Ta karasa tana daria. "Babangida da kawu muntari ne kadai masu waya a gidanmu sai goggo asabe da ta taba siya tayi wata hudu ba'a kirata ba shine ta sayar😂😂. Murmushi hajia tayi tace "to yanxu fatu ya za'ayi ki tunkari sultan har kice ya sauwaqe miki? Fatu tayi dan jimm sannan tace "hajia tunda innar tawa qawarki ce sai ki fada mata ita tayi mishi magana" hajia tace "ke bakya dokin ganin innar taki ce"? Fatu tace "hajia inaga abunda sultan ya mini itama shi zata min, mahaifiyata suka zo nema bani ba, kinga ko baza su damu dani ba, nima kuma bazan tura kaina cikinsu ba" Haajia tace "fatu mahaifiyar sultan zata so ki sosai, don tun muna jeka da fari ta je dukku gurin mamanta wato kakarki, sunje aka ce musu ta rasu, 'yarta rahmatu kuma tayi aure a wani gari. Hajia sadiya (maman sultan) ba yanda ba tayi su fada mata sunan garin ba amma suka ce sun manta, zuwanta na biyu bana mantawa bamu dade da dawowa nan gidan ba ta qara zuwa, wannan karon  Cewa sukayi karta qara zuwa gurinsu, don basu hada dangi da ita ba, wacce suka hadan ma sun yafe ta. Duk maganganun nan daga bakin yayan kakan ki yake fitowa, wai sunan shi mal jauro, ina mamakin yanda akayi sultan ya nemo ku". Fatu tayi shiru tana tunanin ya auntyn ta hajia sadiya zata karbeta, taji dadin jin ance tana son su. Hajia ta cigaba da cewa "ni a nawa shawaran ki zauna anan har lokacin da kike tunanin zaki iya samunshi ki masa magana, batun hajia sadiya kuma baza ta taba yarda sultan ya sake ki ba, don haka ki zauna anan ki fara makaranta har zuwa lokacin da naga ya dace ki tunkareshi. Fatu tayi shiru tana tunanin maganan hajia, hala in taje gurinshi yanzu yace bazai saketa ba ya korata kauye, amma in ta zama 'YAR BIRNI bazai wulakanta ta ba zai bata abunda take nema cikin salama tunda yasan tana da ilimi.

[12:43PM, 5/22/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar 

14

Da wannan tunanin tace "hajia na amince in har zaki yarda ki dauke ni, wanke wanke da shara ko girki zan dinga yi? Hajia tace "ban gane ba" fatu tace "kince zan zauna anan inyi karatu to kuma banida kudi kuma ai bazan zauna hakanan ba tareda ina muku aiki ba" murmushi hajia tayi sannan tace "ni babu abunda zaki min, kudin makaranta kuma nice zan biya, dake dasu jameel duk daya na dauke ku" fatu harda hawayen farinciki tana kwararawa hajia kulsum addu'a sai da ta dakatar da ita. Fatu tace "hajia to kakana fa? Don yace in sanar dasu in na isa" hajia tace "karki damu nasan abunyi" farouq ne ya shigo da sallaman shi ya nemi guri kusa da fatu ya zauna hajia tace " farouq a ina ka zauna tun tafiyanka sallah isha? Yanzu gashi har 8:42" yace "mummy gurin baba mai gadi na tsaya, yana bani labarin sojoji ne, kinsan ina son zama soja" hajia tace "kai kam da son soja, shima mal amadu da yake biye maka kana sa shi surutu" daria sukayi dukansu, farouq yaje ya dauko home work dinshi ya kaiwa fatu wai ta tayashi. Yanda take nuna mai komai dalla dallah yasa hajia cikin mamaki, don ta english take masa bayanin wanda in bai gane ba sai ta masa da hausa, sun gama ya dauki bag dinshi ya musu sai da safe ya wuce dakinshi. Hajia ta dubi fatu wacce tafiyan farouq bai mata dadi ba, don har ta fara takura kana tace "fatu kince a kauyenku kikayi primary, to sec fa? Fatu tace " a garin kumo nayi scndry skul dina, abokin babana ne wanda ya kawo ni tasha yake zuwa da sassafe ya kaini, in an tashi ni kuma in hau acaba ya mayar dani kauye, anan na fara tun daga jss1 har nayi waec da neco, na samu kyautuka da dama ranar speech and prize giving day din mu. After months result ya fito na samu both waec and neco, sai dai banyi jamb a shekarar ba. Bayan aure na ne nayi jamb ina tunanin in sultan ya yarda sai inyi university dina. To da yake bai zo ba sai abun ya mulmulce" hajia tace "kinci jamb dinne? Fatu tace "eeh naci, ina da 220 points" hajia tace "ahh lalle kinyi kokari, last year ne kikayi ko this year? Fatu tace "nayi last year kuma nayi this year" hajia tace "ashe bazamu sha wahalan sama miki admission ba, yanzu dare yayi muje ki kwanta ki huta, gobe in Allah ya kaimu zamu qarasa magana" kashe komai na wuta sukayi suka haura sama hajia ta kaita wani daki kusa da na farouq, daki ne madaidaici da toilet dinshi a ciki, komai na dakin pink nd white ne, gadon Mai dan girma, sai wardrobe dinshi da mirrow duka pink, can gefe kuma gurin karatu ne desk da chair white, labulayen pink nd white sai paint na dakin sky blue mai oily sai sheqi yakeyi. Sana'ar dai fatu ta sake yi wato sake baki, hajia tace "nan dakin aisha ne yanzu kuma ya dawo naki" fatu tace "hajia duka wannan, nikam ko da mai aikin ki zan dinga kwana" hajia tace "a'a anan zaki zauna na fada miki bana son kina banbanta kanki dasu farouq, duk daya kuke, ki saki jikinki tamkar nan ne gidanku, abunda nake bukata daga gareki kenan in har zan samu" fatu tayi saurin riqo hannun hajia tace "kinfi karfin bukatar abu a gurina sai dai ki bani umarni, insha Allah zaki sameni mai miki biyayya, wallahi ban taba tsammanin akwai masu kudi da son jama'a irinku ba hajia. Nagode Allah ya biyaki da Aljannah ya kuma raya miki 'yayanki" "Ameen Ameen" hajia ta fada sannan ta mata sai da safe ta wuce dakinta, rufe kofar fatu tayi ta ajiye jakanta a gado, ta hau kan gadon tana daddannawa, can ta miqe ta shiga toilet din sai da ta gama qare masa kallo tana daria sannan ta fito ta cire hijabinta ta bude jakanta ta dauko soso da sabulu hade da brush da tootpaste ta ajiye a gefe. Cire kayanta tayi ta dauki Wani extra zani da alama na wankanta ne tasa ta shiga wanka, bata dade ba ta fito ta sane jikinta ta shafa mai, tazo daukan wani kaya ne taga wasu night wears riga da wando orange colour masu laushi akan gadon, taga kuma an saka bedsheet an lailaye gadon wahoho fatu tace "Alhamdulillah" tasa kayan ta jera kayanta kala uku a cikin wadrobe din jakan ma tasa shi a ciki wanda akwai kudinta a ciki. Ta kashe wuta ta haye kan gadon tayi addua ta rufe idonta tana tunani har bacci ya dauketa.

 

Taku a kullum

 

Maman Fa'iz👯👯

[10:15PM, 5/27/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

15

 

Bangaren hajia kuwa wautan fatu take gani, ace miji kamar sultan kaso rabuwa dashi? Ita dai bazata bari hakan ta faru ba shiyasa take son fatun tayi karatu ta kuma waye yanda shi sultan bazai so koda kuda ya gifta tsakaninsu ba. Duk da sultan bai kyauta ba amma ba taga laifin shi sosai ba don rayuwar turai yayi, ya saba ganin mata masu class da wayewa zai so matar sa ta kasance kamar su.

Don haka hajia tayiwa kanta alkawarin kai fatu gidan sultan cikin so da kaunar junansu.

 

Tun asuba fatu ta tashi tayi sallah ta dan jima tana addu'o'inta sannan ta shafa. Ta kusan minti 30 a zaune tana tunanin ko ta fita ne ta taya mutanen gidan aiki ko ta zauna ne oho. A haka har gari ya fara haske Knocking kofarta taji anayi da sauri ta tashi ta bude. Hajia ta gani ta durkusa har kasa ta gaisheta, hajia ta amsa tana murmushi tace "ya kwanan baqunta" fatu tace "Alhamdulillah" hajia ta miqo mata wata doguwar riga tace "idan kinyi wanka ki saka, sai ki sauqo kasa breakfast ni zan je in shirya farouq zuwa skul" fatu ta karba tayi godia ta ajiye kan gado Sannan tayi hanyar fita daga dakin hajia tace "ina zaki je" fatu tace "zanje in shirya farouq dinne" bata jira me hajia zata ce ba ta fita ta shiga dakin farouq don kusa da nata yake, tattausan murmushi hajia tayi sannan itama ta fice zuwa dakinta. Fatu tana shiga dakin ta samu shi baccinshi ma yakeyi, a hankali da wayo ta tashe shi ya shiga wanka bayan ta hada mishi ruwan wankan. Da ya fito ta tsane mishi jikinshi ta shafa mishi mai hade da sanya mishi uniform dinshi, gurin sa neck tie ne suka kai ruwa rana, don daga ita har farouq din babu wanda ya iya. Daria yake ta mata yace "mummy ta iya, muje ta saka min" daukan skul bag dinshi tayi suka sauqo zuwa palour anan suka sami hajia tana rufe lunch box din farouq. Tace "iyee har kun gama ne?" Cikin daria farouq yake bata labarin yanda fatu ta rinqa kokawa da neck tie wai bata iya ba, hajia ta dara kadan ta kirashi tana saka masa duk fatu tana gani. Dinning hajia ta kaishi aka hada mishi tea ga hadedden indomie dinshi a gefe, cikin nitsuwa ya cinye ba tareda ya bata kayansa ba, kana ya tashi yace "mum yau ma kece zaki kaini skul" hajia tace "noo, driver zai kaika, jiya ma don yayi asubancin tafiya garinsu ne" Farouq ya hade rai hajia na lallashinshi don kar ya makara. Fatu ce ta jawo shi jikinta ta rada masa magana a kunne,  duk iya gulma na banji me ta fada masa ba, kawai naga suna daria ta riqo hannunshi tace "muje in raka ka mota" hajia da ta tsaya kallonsu tace "ohh wariya za'a min kenan? Farouq yayi saurin hugging dinta tace "a'a mummy kema zan fada miki in na dawo, bye" har mota fatu ta rakashi ya shiga suna dagawa juna hannu, baba maigadi ne ya bude gate suka fita, yana kokarin rufe gate din fatu ta kalleshi da kyau.

O M G 😳 mai kawo mata aika ne. Da gudu ta koma palour shi bai ma ganta ba.

 

Taku a kullum

 

Maman Fai'iz👯👯

[10:26AM, 5/28/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

16

 

A guje fatu ta shigo palour, hajia dake qoqarin haurawa sama ta dakata tace "lafiya fatu? Fatu tace "mummy wallahi mal usman na gani, mai kawo min saqo din nan, yana tura gate" hajia tace "mal usman ne yake kai miki saqo dama? No wonder kowanne month yakance zaije kumo kai saqo, kuma ban taba tambayarshi ba, da yake shi dan garin kumon ne" fatu dai bata ce komai ba sai zare eyes da take yi. Hajia tace "karki damu, nasan abun yi, kije ki shirya ki sauqo muyi breakfast" fatu tace "to" kana ta miqe ta haura zuwa dakinta.

Hajia kuma hijabinta ta saka ta nufi bakin gate gurin mal usman. Yana ganinta ya taso da sauri har yana duqawa ya gaishe ta, ta amsa masa cikin fara'a kana tace "mal usman saqo da kake kaiwa kumo gurin waye kake kaiwa" mal usman yace "gurin wata yarinya da kakanta ne, shekara kenan ina kaiwa, inaga na taimako ne ko kuma yar uwarsu yallabai sultanun ne" harda abunda ba'a tambayeshi ba ya fada. Hajia ta nisa tace "Yarinyar tana nan gidana amma shi sultan bai sani ba, idan ya baka saqon next month ka kai can garin modibbon, idan kakan ya tambayeka labarin fatu kace tana nan lafiya kalau, kar ka nuna masa ba'a gidan su sultan din take ba, zaka min wannan alfarmar? Kai tsaye mal usman yace "hajia duk yanda kika ce haka za'ayi" hajia tace "nagode kuma shima sultan din kar ka nuna mishi komai" hajia ta fada sannan ta shige cikin gida. Shi kuma ya koma bakin aikinsa don ta daure masa kai, amma dai yasan duk rintsi hajia baza ta taba cutan wani ba, kuma in ba kwanan nan ba basu san cewa Iyalai biyun ba dangin juna bane.

Sake curtain din window fatu tayi bayan taga hajia ta koma palour tayi ajiyar zuciya ta fada toilet tana mai addu'an Allah yasa mal usman ya bada hadin kai.

[10:44AM, 5/28/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

17

 

Wankanta ta tsala ta fito ta shafa mai da dan pop powder dinta na 100, sai kwallinta data sawa idonta, ta lakuti vaseline ta shafawa lips dinta. Doguwar rigan da hajia ta bata ta saka black ne mai adon sky blue a gaban rigan, kana ta dauki gyalensa shima sky blue ta yane kanta Wahoho jama'a sai yau na qarewa fatu kallo. Fara ce amma ba tass ba, tana da matsakaicin tsayi, figure 8 ce don rigan anyi shaping dinta, idanunta ba manya bane kuma ba kanana ba, tana da dogon hanci ba laifi, bakinta dan tsurut kamar bakin bottle, tana da gashin gira dai dai, fuskarta mai yawan murmushi. Itama kallon kanta ta tsaya yi a jikin mirrow tana smilling, sannan ta nufi kofa ta fita. Tun daga kan steps hajia ta ganta a ranta tace "masha Allah" don sultan yayi sa'ar mata, ga kyau ga ilimi both arabi da boko ga nutsuwa ga kuma ladabi da biyayya. Fatu ta iso ta dan duqa tace "mummy sannu da aiki" har ranta hajia taji dadin yanda fatu ta saki jikinta tana kiranta da mummy. Dinning suka nufa fatu tayi serving dinsu indomie da dankali da kwai sai tea. Suna ci suna hira duk akan yanda skul din fatu zai kasance. Bayan sun gama ne hajia tace zata yi bacci kadan kana ta haura sama. Fatu ta tattare gurin ta kai kitchen ta samu dija na wanke wanke,;ta tayata suka qarisa cikin tadi da raha, suka gyara kitchen din. Anan ne dija take tambayar fatu dangantakarta da hajia fatu tace "zan fada miki amma ba yanzu ba" dija tayi daria tace "to Allah ya kaimu ranar" fatu tace ameen ta haura sama itama ko zata runtsa.

 

Taku a kullum

 

Maman Fa'iz👯👯

[12:16PM, 5/28/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

18

 

Shigan fatu daki ta kwanta a gado tana tunanin rayuwarta, ita kanta mamakin yanda ta sake a gidan takeyi, amma da ta tuna da yanda hajia ta karramata sai take ganin ko me hajia tace tayi zatayi in dai bai kauce shari'a ba.  Duba agogo tayi 8:34, kakanta ne ya fado mata a rai, yanzu haka yana can yana kewanta, Allah sarki, hawaye ne ya fara sintiri a beautifull face dinta idonta a rufe, a haka har bacci ya dauketa.

11:00 ta farka, bandaki ta shiga ta kama ruwa sannan ta sauqo palour, babu kowa sai kamshin girki da yake tashi a kitchen, ta shiga kitchen din ta samu dija tana girka abincin rana, fatu ta mata sannu da aiki ta kama sunayi tare. Fatu tace "maman isya (dija) mummy bata fito bane? Dija tace "ta fito dazu ta fadi abinda za'a girka" Fried rice wanda yaji hanta da kayan lambu sukayi sai coslow, fatu tace "akwai zobo ne?" Dija ta kawo mata, tace "mman isya a ina zan samu bawon abarba? Dija tace "sai dai a aika habu driver ya karbo, akwai masu sayar da fruits a bakin hanya" dija ta fita ta bawa habu driver aika, minti goma ya dawo da bawon abarba mai yawa, fatu ta karba ta daura akan wuta tasa ginger, kanunfari da zobon, suka ci gaba da hiransu suna gyara inda suka bata har zobon yayi, ta sauke dija ta tace shi a wani bokitin roba ya dan huce suka sa sugar sukayi blending cucumber suka saka. Dija ne ta fara tabawa tace "zuwaiiitt kenan, hajia zata ji dadin wannan zobo dama bata cika son na kwalin nan ba" fatu tayi murmushi itama ta taba tabbas yayi dadi don bata taba yi ba, time din da take secondary tayi food and nutrition to anan ta dan iya wasu girke girken sai dai ba kowanne ta gwada saboda yanayin gidansu. Freezer suka kai don yayi sanyi da wuri, barin dija tayi a kitchen Din ta fito palour, hakan yayi dai dai da shigowan farouq 12:40 da sauri ta rungumeshi tana masa oyoyo, peck ya mata a kumatu tayi murmushi itama ta masa duk suka sa daria, wa yaga FATU A BIRNI har an fara wayewa😜. Duk abunda sukeyi hajia na kallonsu tana jindadin shakuwarsu na kwana 1. Da gudu yaje gurin hajia itama ya mata peck ta masa oyoyo.

[9:56PM, 6/3/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

19

 

Hajia tace yaje yayi wanka ya sauqo yin lunch, fatu ta riqe hannunsa suka tafi dakinsa tana tambayarshi labarin skul. Yayi wanka fatu ta wuce dakinta don gabatar da sallah, shima farouq wucewa mosque yayi. Bayan ya dawo ne suka hallara a dinning don cin abinci, suna kan ci fatu ta dauko musu zobo, ta tsiyayawa kowa kana ta zauna. Farouq ne ya fara tabawa yace "mummy wannan Ribena ne? Mummy tace " kamar zobo ne lemme taste it" hajia ta dan kurba tace "natural" kana ta kira dija tazo "haba dija, dama kin iya irin wannan zobon amma baki taba mana ba? Dija tace "hajia bani bane fa, fatu ce tayi" nan hajia ta maida dubanta ga fatu wacce cin abincinta take hankali kwance, tace "fateema a ina kika koyi wannan zobon? Fatu tace "mummy a skul ne, nayi food nd nut ai" fatu ta fada mata yanda sukayi. hajia tayi smile tace "zaki koya min nima, gashi babu wani flavour ko color, komai natural sai qarin lafiya ba abun cutarwa" duk sukayi daria, in banyi qarya ba kowa yasha zobo cup 5😜.

 

Kwanci tashi ba wuya a gurin Allah, yau fatu ta cika 3 weeks a gidan, tayi fresh tayi kyau abunta, hajia tana nuna mata gata ba qarya, don kaya kala kala naga fatu na sawa ita da tazo da kala 3, shoes and bags ma gasu nan kamar na wata yar gwamna, make up kuwa takanas hajia ta kaita PRETTY AYSHA PALOUR ta koya mata kwalliya na zamani.

 

Sanye take cikin wani swiss lace mai pink nd blue, tayi simple make up amma tayi matuqar kyau, kayan sun amshe ta kamar ka sace ka gudu, gyalenta ta dauka ta yafa a kafada ta fito palour ta samu hajia na kallo manara tv. "Sannu da hutawa mummy" hajia ta juyo tace "yauwa yar mummy, gurin mal usman zaki je kice kafin ya wuce kumo ina son ganinsa" fatu tace "to mummy" ta fita daga palourn ta nufi bakin gate. Turuss ta tsaya ganin sultan na magana da mal usman din. Rabon da ta ganshi tun ranar shigowanta gombe. Zuciyarta ne yake dukan uku uku, kar fa ya ganeta ya korata kauye ko kuma yaci mutuncinta, wayyo Allah! A zuciyarta tana ina ma bata fito yanzu ba. Yana gama maganansa ya miqa wa mal usman envelope yana cewa "bari in gaisa da mummy" juyowan da zaiyi yayi arba da ita, dumm gabansa ya fadi, "tsarki ya tabbata ga Allah da ya tsara wannan halitta" sultan ya fada a zuciyarsa yana mai qarewa fatu kallo ita ma din shi take kallo, sunfi 1 min a haka, fatu ce tayi qarfin halin fara tafiya ta nufi gurinsa.

 

Taku a kullum

Maman Fa'iz👯👯

[9:27PM, 6/4/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

20

 

Tafiya take yi a hankali zuwa gurinsa don ita duk a tunaninta ya ganeta, tazo dab dashi ya aika mata da murmushi yace "sannu yan mata" tsayawa tayi cakk, a ranta tace ashe bai ganeta ba, don haka ta fuske tace "sannunka" kana ta cigaba da tafiyanta zuwa gurin mal usman. Ta gaishe shi tace "mummy tace tana son ganinka kafin ka tafi" yace "to" kana yayi qasa da muryansa yace "fatu yallabai ya ganeki kuwa? (Mal usman gulma😂) shiru tayi tana kallon gefe, sannan tace "ka manta abunda hajia tace ne? Duqawa yayi kamar me neman gafara yace cikin karamin murya "ahh yi hakuri, wallahi mantawa nayi fateema, bakin nawa ne ba sakata" murmushi tayi tace "ba komai" wuce wa tazo ta sake yi ta gaban sultan wanda tun tafiyanta gurin mal usman ya tsaya ya zuba musu ido, sai dai bai san me suke cewa ba. Tana shiga palour ta isar wa hajia saqonta tayi saurin haurawa sama, hakan yayi dai dai da shigowan sultan ya zuba ma bayanta ido, sai yake ganin duk duniya babu wanda hawan step ya masa kyau irin wannan babe din. Sai da ta shige ya juyo da kallonsa palourn ganin idon👀 mummy qurrr a kansa yasa yaji kunya. Daya daga cikin kujeran ya samu ya zauna yace "sannu mummy" tace "kaima sannunka" dariya yayi don duk a tsarge yake kamashi da mummy tayi yana kalla mata baquwa. Suka gaisa, mummy ke jajensa tace "wato don jameel baya nan shine ko kafanka ba'a gani ko" murmushi yayi yana sosa qeya yace "wallahi mummy ban zauna bane, last wik ma dawowana daga china, kuma nazo farouq yace kina bacci" hajia tace "ba komai in abokin naka ya dawo ai zamu na ganinka, Kaga shikam yayi iyali, kai kuma naga alama so kake azumin nan a fara kada maka gangan tuzuru" daria yayi sosai yace "mummy ki shirya bayan sallah zakuyi bikina, na samu mata sai dai bamu daidaita ba" Mummy ta kallesa tace "a ina" sultan yace "kin santa ma mummy, ki tayani addu'a kawai" da jin haka mummy ta gane fateeman ta yake nufi, sai ta fuske tace "nidai ban gane wacece ba, Allah ya baka sa'a" ganin bai samu fuska ba yasa ya maida kallonshi kan tv, yafi kusan 30 mins xaune da hajia suna hira sai dai ko kadan bata kawo masa tadin baquwarta ba, fatu kuwa qin fitowa tayi. Ya gaji da jiran fitowan ta yayiwa hajia sallama ya fita.

 

Taku a kullum

 

Maman Fa'iz👯👯

[10:36PM, 6/5/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

21

 

Sultan na fita ya hadu da farouq ya dawo daga skul, tafawa sukayi yace "big boy, ka dawo? Ya skul" yace "lafiya kalau, yau muka yi games, mukayi gudu muna waqan soldiers" sultan yace "Ai ana ganinka anga sojaa, give me five" suka qara tafawa, kana sultan yace "amm sojaa, nikam wacece baquwar mummyn nan? Farouq yace "anty fateema ce, tazo karatu ne" da yake hajia ta gargade shi kan duk wanda ya tambayeshi fateema ya fadi haka nan. Yace "ok good boy, maza in ka shiga gida kace ina gaisheta" yace to. "Fateema" sunan ta mai dadi, murmushi yyi ya shafi face dinsa kana ya dan bugi kirjinsa saitin heart dinsa, (ko me hakan ke nufi oho😜) fita yayi daga gidan, a bakin gate ya hango mal ahmadu yazo karban mal usman guard tunda zaije aika. Suka gaisa ya wuce gidansu.

Dawowan farouq yasa fatu sauqowa kasa ta masa oyoyo, yace "bro sultan yace yana gaisheki" kallon mummy tayi taga hankalinta na kan tv don haka tace "yaushe" yace "yanzu na hadu dashi a bakin gate, kin ganeshi? Shine wanda nake baki labarin ya kawo min tsaraba zuwansa china, muje in qara nuna miki tsaraban" fatu tace "awww yanzu na tuna, kaje kayi wanka kayi sallah sai muci abinci, akwai labarin da zan baka" ya tafi dakinsa. Mal usman ne ya shigo ya gaishe da hajia ya tsaya a bakin kofa, hajia tace "sultan ya baka aika ne? Yace "ehh" tace "ka bawa fateema ta dubamin, miqa ma fatu yayi ta bude kudi ne dai har yanzu, har zata rufe taga wata karamar paper da dauka ta miqa wa hajia. Hajia tace "a'a letter dinki ne" rufe envelope din tayi ta bawa mal usman yasa a aljihu. Hajia tace wa fatu shikenan kije dakinki. Ta wuce. Hajia tace "mal usman kamar yadda na fada maka fateema tana nan amma kakanta bai sani ba, haka sultan, inaso a dauka a gidansu sultan take, kakanta kan iya tambayarka fatu, kace masa tana lafiya, kuma a baka takardun karatun ta duka, sultan zai saka ta a makaranta" da saurinsa yace "hajia an gama" kudi ta bashi ya karba yana godia kana ya fita.

Fatu kuwa tana shiga dakinta ta fada kan gado tana tariyo yanda sultan ya mata murmushi, karo na biyu kenan da taga smillin dinshi. Ya qara mata kyau da kwarjini, dazu tayi matuqar yin qoqarin ganin bata kwapsa ba balle ya ganota. Papern tayi saurin budewa, ta fara karantawa

 

Hii

 

""Ki cewa mal Ameenu na gaishe shi, ki kuma bashi hakurin rashin ganina, may be bayan sallah zanzo""

 

Samun kanta tayi tana nanata wasiqar, duk da ba ita akayiwa ba amma taji dadin sa. Murmushi naga ya subuce a fuskarta can kuma ta fara hawaye, tana tausayin kanta, yanzu zata rabu da mijinta, duk da ba sonshi takeyi ba amma zata so ta zauna da dan'uwanta. Kuma taga yana mata murmushi. Wata zuciya tace fateema yake yiwa ba fatu ba. Kar ma kisa shi a ranki, a duk lokacin da ya gano kece fatu bazai qara kulaki ba. Wasu zafafan hawaye ne suka qara gangaro mata tayi saurin gogewa, farouq ne ya shigo dakinta wai ta sauko yin lunch, goge fuskarta tayi suka fita tare da yake tana fashin sallah.

 

Acan garin modibbo kuwa mal usman ya kai saqo kamar kullum. Mal aminu ke tambayarsa? Ina uwargidan nawa, da fatan tana lafiya? Mal usman yace "tana lafiya kalau, tace a gaisheka ma. Kuma a bata takardun makarantar ta zata cigaba da karatu. Cikin jin dadi kaka ya dauko komai da komai ya bashi, da yake duk takardun nata a gurin kaka yake.

Bayan mal usman ya dawo ya bawa hajia, nan da nan tasa a nema wa fatu admission a GSU cikin qanqanin lokaci aka sama mata, aka gama komai ta fara zuwa lectures.

 

 

Anan zamu tsaya a FATU A BIRNI insha Allah bayan sallah zamu cigaba.

Kuyi hakuri na rashin post da wuri hakan ya samo asaline na rashin charge.

FATU NA MUKU HAPPY RAMADAN🍉🍏🍎🍐🍊🍉

Allah ya bamu ladan dake cikin wannan wata ta Ramadan. Ameeen

[3:15PM, 7/11/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

22

 

Kwanaki sun shude yau watan fatu biyar da barin garinsu tayi nisa a karatunta kuma tana fahimta, qawarta daya sunanta itama ma fatima. Qawancen su ya samu asali ne ranan wata monday fatu tayi latti sosai gashi har an shiga  lecture kuma lecturer baya barin a shiga, fatu sai safa da marwa takeyi a bakin hall din, fatima da take ciki ta hango ta sai ta bata tausayi, don tana lura da fatu, irin dodging lecture da students sukeyi ita sam bata yi ga kokari kamar me! Tana cikin tunaninta taji an jefe ta da abu; dumm gabanta ya fadi don tasan lalle yau zai korata waje, maimakon taji ance yi waje sai taji yace "Me kike kallo a waje? Bata san lokacin da tace "qawata ce" "u can join her" abunda ya fada kenan. Zare ido ta fara yi tace "sir bata da lafiya ne, ko dazu she called me tace bazata samu zuwa ba, so ganinta da nayi ne ya ban mamaki" sai da yayi dan jimm sannan ya mawa fatu hannu da take waje ta sake baki tana kallon ikon Allah. (Sana'ar ta ne dama sake baki😂). Sai da ta shigo yace "get well dear" tana in ina tace "thank you sir" guri ta samu ta zauna aka cigaba da lecture. Bayan ya fita ne ta samu fatima ta miqa mata hannu hade da sallama ta amsa hade da shaking hannunta. Fatu tace "amma kin taimakeni nagode sosai, gashi ya bamu light akan abunda zai fito a exams. Fatima tayi murmushi tace "ai kuwa, me sunanki? Fatu ta amsa "Fateema Mahmud" tayi carab tace "sunan mu daya amma ana kira na xahra levels" fatu tace "I like it" xahra tace "tnks namesey"

Haka qawancen su ya cigaba cikin aminci. Suna ziyaran junansu lokaci lokaci, hajia ta yaba da hankalin xahra shiyasa take barin fatu tana ziyartar ta. Bangaren sultan kuma soyayyar fateema ta gama narkewa a zuciyansa, sukan gaisa amma daga nan yake tsayawa, dan gaisuwan da yake yawan shigowan ma ya rage, don akwai ranar da yazo fatu tana ganinshi ta haura sama, yazo ya zauna suka gaisa da mummy, hajia tace "nikam sai kora min 'ya kakeyi, da ta ganka sai ta tafi" yayi murmushi yace "afuwa mummy" Haka suka cigaba da hiransu har yake tambayanta daddy tace yana Abuja, don shi bai cika zama a gida ba, lokacin zuwan fatu ma baya gida, da ya dawo hajia ta bashi labarin ta bai yi comment akai ba, illa cewa da yayi Allah ya taimaka. Yasa hajia ta kira masa ita ya mata questions akan rayuwarta ta bashi amsa,  kana ya mata nasiha yace ta dauki gidan kamar gidansu, kuma ta maida hankali akan karatu.

Yau shirye shirye akeyi a gidan don tarban manyan baki, mahmud ne zai dawo daga cyprus sai jameel da matarsa suma zasu dawo daga south Africa. Hajia ta kasa zaune ko tsaye haka fatu, duk wani shiri da girke girke an kammala sai isowan su kadai ake jira, karfe 2 na rana sukayi waya sun sauqo, nan da nan hajia ta aika driver a dauko su, farouq yaso a je tarbansu hajia tace nooo. Bayan tafiyan driver fatu tace wa hajia zata je tayi wanka kafin su dawo, hajia tace to. Fatu ansha aiki, tana shiga daki tace bari ta dan miqe a gado kadan, bata san lokacin da bacci ya kwashe ta ba.

Jameel sun dawo cikin dokin ganin gida, hajia tayi murnan ganinsu harda kwallanta, farouq murna kamar ranar ne sallah. Bayan an gama gaishe gaishe aka nufi dinning cin abinci, amaryan jameel, lubna mai dauke da qaramin ciki tafi kowa kwasan girki, sai santi take zubawa, mahmud da yake qanin mijinta yana ta tsokananta kota kulashi, mummy dai dadi ya hanata magana. Can hajia tace "mahmud kai kuma maimakon kana gama karatunka kayo gida shine ka biya can south africa ko, wato ko missin din gida baka yi?  Riqe hannunta yayi yace "wlh mummy jameel ne ya dameni wai in biya can tunda suma sun kusa dawowa wa, mummy 3 wiks kawai nayi a can din fa" ya qarasa maganarsa cikin shagwaba, daria sukayi lubna tace "ji shi kamar wani yaro" "yaro nake tunda ban kusa ajiye baby ba" mahmud ya bata amsan da ya saka ta kunya, don haka tayi shiru. Murmushi Jameel yace "mummy nafi son mu dawo rana daya ne thats why nace ya biya can, nd he enjoyed staying there" hajia tace "Alhamdulillah tunda kun dawo lafiya all, sai shirye shirye walima da party na taya murna, in da next 1 week" murmushin jindadi mahmud yayi yace "thanks mum, Allah ya biyaku dawainiyan da kukeyi akan mu" dukansu suka amsa da Ameen.

Bayan kammala cin abinci kowa ya nufi part dinshi, jameel ya dauki matarsa suka tafi gidansu da yake basu da nisa da gidan iyayen nashi.

[3:19PM, 7/11/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

23

 

Fatu bata farka ba sai bayan la'asar, kallon agogo tayi ta saka salati ta shige bathroom. Wanka tayo da alwala ta bada farali kana tasa kaya hade da light make up. Palour ta fito taji shiru tace ba dai har sun kammala ba. Kitchen ta shiga ta samu dija na aikin girkin dare ta tsaya tambayanta hajia dasu jameel, dija tace "ai tun dazu su lubna suka tafi, mahmud kuma inaga ya shiga cikin gari. Fatu tace "mmn isya yanda kika san an mini duka haka nake jin jikina dazu, ina shiga daki kawai na kwanta in huta ashe bacci ya kwashe ni" Dija tace "kinyi kokari ai" fita daga kitchen din tayi dakin hajia, sai da ta knockin tayi sallama aka amsa ta shiga. Hajia ta samu zaune a bakin gado tana waya da aunty sadiya (maman sultan). Kujera na dressin mirrow taja ta zauna Sai da hajia tayi hangin fatu tace "mummy ya gajiyan yau? Hajia tayi mrmshi tace "ai ke za'a cewa ya gajiyan yau, kikayi ta bacci abunki" daria fatu tayi tace "Allah mummy nima bansan tym din da bacci ya debe ni ba, kuma farouq ma ko yazo ya tasheni" mummy tace "ni nace ya barki ki huta. Ki dauki wancan jakan ki kaiwa hajia sadia tsaraban su ne, naki kuma sai kin dawo ki gani" fatu tace "tooo" daukan jakan tayi ta fito, room dinta ta shiga ta dauko hijabi iya gwuiwa tasa ta fito.

A palour ta tarar da qanwarsa Amrah tana danne danne a waya, zata kai 13 yrs, "anty fateema oyoyo" amrah tace da fatu yayinda take zuwa gurinta ta karbi ledan hannunta suka zauna, fatu tace "washhh, Ina mammi" amrah tace "tana dakinta, bari in kirata" bata jima da shiga ba suka fito tare, hajia sadia na cewa "amrah bi kitchen ki daukowa fateema ruwa" zama tayi akan kujera fuskarta dauke da murmushi tace "sannunki da zuwa fateeman mummy" murmushin fatu ma takeyi amma fuskarta a qasa, ta zamo daga kan kujeran ta gaisheta kana ta koma ta zauna. "Mummy ne tace in kawo muku tsarabanku" ta fada yayin da take miqawa hajia ledan. Amrah ta kawo wa fatu ruwa ta tsiyaya mata ta koma kusa da hajia sadia ta zauna tana cewa "mammi ina nawa" hajia sadia tace "gashi nan, kinga na kowa Anyi wrapping dinshi da suna" ta karba tace "anty fateema kice nagode sosai" fatu tace "to amrah" amrah ta wuce dakinta don ganin tsarabanta. Fatu ta miqe tace "mammi sai anjima" hajia sadia tace "daga zuwa? Ko ruwa baki sha ba" fatu tace "mammi na sha" sultan ne ya shigo a dai dai inda hajia sadia ke cewa "ki gaishe min da mummyn naki" sultan yace "muje in raka ki" saurin dago da kanta tayi ganin ita yake kallo yasa ta fara tafiya tana cewa "to mammi" hajia sadia kuma ta koma ciki tana jindadi, don tun ba yau ba take son sultan da fateema, don yarinyar ta mata, ga nitsuwa da hankali, har cikin ranta take son fatu. A bakin gate ya cim mata, wani sauri takeyi bata son wani abu ya hada su, gudun kar ta kopsa ya ganeta. Sultan yace "madam ba haka tafiyanki yake ba" dolenta ta fara tafiya yanda ta saba, hakan ya bashi daman jerawa da ita. "Ina wuni" fatu tace dashi, yace "lafiya kalau fateey, kina lafiya" a gajarce tace "lafiya" dai dai nan suka iso bakin gate ta shige abunta, shi kuma ya juya ya fara tafiya, tana shiga taga bai biyota ba, sai taga sam bata kyauta ba, ko godia babu, leqawa tayi tace "hey" ya juyo ta sakar masa murmushin da ya saka shi jin sansanyar iska na bin jinin jikinshi. Yace "yess" tace "thanks" bata jira amsar sa ba ta shige. Samun kansa yayi da tsayawa a gurin yana doka uban murmushi da yasa hakoransa shan iska yana kallon kofar, yafi 5mins a gurin wucewar wata mota ce ta sa shi dawowa hayyacinsa ya koma gidansu. Ita kuma tana shiga a farfajiyan gidan ta hadu da mahmud zaune a irin kujerun shan iska nan yana karanta newspaper tazo ta gurinshi tace "sannu da hutawa" ya sauqe jaridan yace "yauwa" tayi wucewarta. A ranshi yace wacece wannan? May be dangin su sultan ce don tana kama dasu, amma dai ta hadu ba laifi, tashi yayi ya shiga cikin gidan shima, mummy ne ta fara ganinshi tace "mahmud har ka dawo? Yace "ehh" ya nemi guri ya zauna. Fatu tace "mummy shine ya mahmud? Mummy tace "shine" fatu ta gaishe shi ta masa sannu da dawowa ya amsa. Tace "na hadu dashi a waje ban zata shi bane ai" mummy tace "ayya, kina bacci suka dawo shiyasa" mahmud yace "mummy banganeta ba" mummy tace "yar uwarku ce daga bauchi tazo karatu ne" tana fadan haka ta tashi ta shige kitchen. Kallon fatu yayi yace "a gidan wa kike a bauchin, don ban taba ganinki ba duk zuwa na" shiru tayi ta rasa me zata ce can ta qakalo murmushi ta ce "ko na fada ma baza ka gane ba" zai qara magana mummy ta fito da basket a hannun ta tace "fateema ko zaki kai abincin gidan jameel? Ta nan sai ki musu sannu da dawowa" da dokin ta tace "ai kuwa mummy" "amma ki jira yanzu farouq zai dawo daga islamiyya sai ku tafi tare driver ya kai ku" yamma liss farouq ya dawo driver ya kaisu gidan jameel da amarya lubna.

 

Afuwan fans, sai yau Allah yayi na turo FATU A BIRNI. Ba jan ranku nayi ba, lokaci ne ban samu ba. Barka Da Sallah. Allah ya maimaita mana. Ameen

 

Taku a kullum

Maman Fa'iz👯👯

[9:14PM, 7/13/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

24

Gefen sultan kuma yana komawa gida ya wuce dakinsa ya kwanta yana tunanin fateema, wayarshi ce ta katse masa tunaninsa, ganin number jameel yasa shi miqewa tare da amsa wayar "ka shigo ne?........ ok bari in fito. A haraban gidan ya ga jameel bayan sun gaisa ne kai tsaye suka shige cikin palourn gidan, mammi ce kadai zaune tana rubutu a wani memo, sallaman da sukayi yasa ta cire tabarau idonta "lale marhabin da mutanen S Africa" zama sukayi, bayan sun gaisa da mammi ne suka fito haraban gidan, sultan yace "dude yau ma tazo gidan nan wallahi, har rakata bakin gidanku nayi" ya fada yana shafa sajensa daya kwanta luff a fuskar sa, jameel dai kallon mamaki yake binshi dashi, tunda suke sultan bai taba cewa yana son wata ba, shi har ya fara tunanin ko yana da matsala ne, mata sunsha warce kansu a gurinshi amma ko kallonsu baya yi, amma akan wata wai fateema ya gama rudewa. Koyaushe sukayi waya sai sultan yayi maganar ta, jameel yana so yaga  wacece fateeyn nan da take qoqarin zautar masa aboki. "Wai dama haka love din yake? Da ita nake bacci da ita nake tashi, jameel na rasa yadda zanyi" Jameel da ya tsaya kallonshi sai yanzu ya samu bakin magana "why not ka tunkareta? Ajiyar zuciya mai qarfi sultan ya sauke yace "I cant! Tana min kwarjini da yawa, to me zan ce mata ma? Kuma I asked farouq bata riqe waya nd tura wasiqa ka gane yayi yawa" Jameel yace "amma ka taba sanin tana da saurayi? Sultan yace "ko a skul bata kula kowa qawarta ma daya ce, a gida ma babu wanda yake zuwa mata, all I know shine ita TAWA CE! "Bravo alaika" jameel ya fada yana tafa masa, "ka iya yanda zakayi ka samu details akanta amma baka san yanda zakayi ka mata magana ba" sultan yace "kai dai ka taimakeni" "yanzu dai muje gidana ma qarasa maganar acan" shiga cars dinsu sukayi suka fita.

Gidan jameel ya hadu shima ba laifi, dai dai zaman mace daya. Driver na ajiyesu farouq ya fito da gudu ya shige cikin gidan, fatu ma ta fito tacewa mal habu ya jirasu yanzu zasu fito. Tana shiga motocin su jameel suka shigo. Bayan sun fito ne jameel yake tambayan mal habu ko aika ne ya kawo, yace masa ya kawo farouq da fateema ne, sultan dake gefe yayiwa jameel ido, jameel yace "ok kaje zan dawo dasu anjima" ba musu habu ya tafi. Su kuma suka tsaya anan suka cigaba da maganansu. Farouq a daki ya tarar da lubna tana gyara cikin wardrobe dinta, tace "farouq yaushe kazo" yace "yanzun nan, ni da anty fateema ne" tace waye kuma anty fateema" yayinda ta riqo hannunshi suka fito palour inda fatu tayi wa kanta masauqi a daya daga cikin kujerun da suka qawata palour.

Sannu da zuwa lubna tayi wa fatu tace bari in dauko miki ruwa, fatu tace "a'a nagode, ban jima da sha ba" suka gaisa anan lubna tace "sai dai ban ganeki ba" farouq yace "nace miki sunanta anty fateema kuma tazo karatu ne gurin mummy" daria sukayi lubna tace "to uban yan surutu, kai na tambaya? Bai kulata ba don ya danno tashan cartoon. Maida hankalinta tayi kan fatu tace "ke yar uwarsu ce kenan, kamar na taba ganinki, daga bauchi kike ko? Fatu tace "ehh, mummy tace a kawo muku abinci, kun dawo lafiya? "Lafiya kalau" lubna ta bata amsa. Fatu ta kalli farouq tace "my sojaa lets go" ba musu ya miqe yace "bye anty lubna, kuma sai na fadawa mummy kince nine uban yan surutu" zaro ido lubna tayi tace "kaji dashi" fita yayi zuwa inda sukayi parking amma wayam ba mota, sai motoci biu da ya gani, zai juya ya koma ya hango sultan da jameel da bayan cars din. Gurinsu ya nufa dai dai nan su fatu suka fito suma. Fatu tana ganin ba motan su tace "ba dai mal habu tafiya yayi ya barmu ba? Sai dana ce ya jiramu fa" ta karisa maganan kamar zatayi kuka. "DJ" lubna ta kwalawa jameel kira suka taho dukansu sultan n Nna cewa "oyoyo uwargida, don yanzu kin tsufa wata sabuwa zamu kawo" lubna ta harareshi na wasa tace "hurul ain kenan? Suna can suna jiransa insha Allah" gaisawa sukayi tsakaninsu fatu na gefe riqe da hannun farouq tana wasa dashi, can tace "ya jameel sannu da dawowa" yace "yauwa, fateema ko? Tace "ehh" gaisawa sukayi tace sai anjiman ku. Da sauri sultan yace "ina zaki je" bata kalle shi ba taja hannun farouq tace "gida" jameel yace "ni nacewa mal habu ya tafi zan maida ku in munyi sallah" ba yanda ta iya dole ta koma, su kuma suka wuce masallaci da farouq. Lubna taja fatu dakinta sukayi sallah, sai tadi sukeyi kamar sun jima da sanin juna, anan ta tayata qarisa gyaran wardrobe din, suka share dakin duk da kafin su dawo an share da gyara ko ina na gidan. Su sultan basu dawo ba sai bayan sunyi sallah isha. A palour suka tarar da su lubna da fatu suna ta tadinsu, sallama sukayi suka shigo, Lubna tace "ba dai har anyi sallah isha ba? Jameel ya zauna kusa da ita yace "ina zaki sani tunda kin samu abokiar hira" lubna ne ta canja tasha zuwa cartoon wa farouq tace  "fateema ki shiga daki kiyi sallah, bari inyi serving dinsu abinci" shigan fatu keda wuya suma suka wuce kan dinning jameel yace "mutumina ka tafi da yawa fa, irin wannan kallon haka" cike da tsokana ya karasa maganar. Lubna tace "ba dai fateema yake kallo ba? Sultan yace "dadina dake yawan tambaya, ni kawai ki tayani campaign" Jameel yace "ni dai kaman na taba ganinta a bauchi, amma inaga mahmud zai fi saninta don ya fini shiga ziyara, ko hutu yazo sai yaje bauchi ya zaga dangi" nan dai sukayi ta tattaunawa har suka samu solution, fitowan fatu yasa sukayi shiru, ganin haka ta gane maganarta sukeyi kawai ta wayance ta zauna kusa da farouq. Bata dade da zama ba suka kammala jameel yace "muje ko fateey" sun fito haraban gidan jameel yace "ohh ashee ba mai da yawa a mota na, pls sultan ka sauqesu mana" sai da yayi dan jimm kana yace "ok" jameel ya tura farouq baya, lubna kuma ta budewa fatu gaba tace "ki zauna a gaba ke" ba musu ta shiga, lubna ta miqo mata leda tace "ga tsaraba ba yawa" godia fatu tayi sultan yaja su suka tafi.

 

Taku a kullum

Maman Fa'iz👯👯

[10:40PM, 7/16/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

25

 

Tun shiganta motan kamshin jikinsu ya gauraya ya bada wani ni'imantaccen scent mai kwantar da hankali, ga a'c ya sanyaya ko ina. Ba sultan kadai ba har fatu taso inama suyi ta zama haka har abada *what? Fatu ar u in love?* tsohuwar cool music na celin dion mai taken _TITANIC_ ya saka musu (in d nyt in my dreams I see u, I feel u....) yana bi a hankali, fatu da ta gama narkewa ta juya kanta gurin window tana jin kalaman waqar har cikin zuciyarta yana ratsa ta. Maimakon taga anyi hanyar gida sai ya biya wani guri, basu tsaya a ko"ina ba sai katafaren gurin sayar da phones. Ya juya zaiyiwa farouq magana yaga yayi bacci. Fatu ta juyo tace "baka ce zaka yi branching ba, srry mun takuraka" yace "no wahala, abu zan saya kuma gashi farouq yayi bacci banida dan rakiya, muje ki rakani" tace "no, in kai alone ne zaka fi sauri" Yace "noo, to ki biyani rakiyan dana miki dazu" yanda yyi maganar kamar yaro yasa fatu daria tace "muje to". Suka shiga tana binshi a baya,  yace "pls ki tayani zabe, amrah nake son sayawa waya" tasan dai amrah nada waya koda yake abunka da masu shi, tara wayoyi a hannu qaramin aikinsu ne. Iphone latest ta nuna tace "wannan yayi" Yace "irin nawa" tace "sai kuyi anko" yace "hakan za'ayi" Qaramin Nokia ya qara dauka ya biya kudinsu, anan ya qara sayan sim cards 2 dfffrnt layi suka fita. Har komawansu mota farouq na baccinsa, basu zame ko ina ba sai *eman* ya saya musu ice cream da snacks, daga nan suka yoo gida wajen tara saura. Har cikin gidan ya shiga yayi parking suka fito daga motan, fatu na qoqarin daukan farouq yace "lemme help" ba musu ta matsa masa ya dauke sa suka shige gidan, a palour ya kwantar dashi mummy kuma da alama tana dakinta, Fatu tace "thanks" yace kinyi mantuwa a mota, tace "ni? Ok tsaraban da anty lubna ta bani" fita sukayi ya bude motar ya dauko ledojin da sukayi shoppin ya miqa mata, tace "wannan ne nawa" ta karba yace "dan tsaya pls" tayi juyi irin ta gajin nan, yace "srry" bude ledan wayoyin yayi ya saka musu layi duk tana tsaye ya kunna ya miqa mata, yace "bari in gwada kira" ita duk bata dauka wani abu ba ta karba, wayarshi ya ciro sak irin na hannunta ya kira sai ga numbern shi ya bayyana a screen din, miqa mishi tayi tace "yayi" yace "kip it, naki ne" cikin zaro ido tace "what? Noo kayi hakuri.... kafin ta qara magana ya rufe motarsa yayi reverse tana tsaye har aka wangale masa gate ya fita, ta jima kana ta koma gida jiki a sanyaye, a palour ta tarar har mummy ta shigar da farouq dakinsa, tana sauqowa qasa, fatu tace "mummy mun dawo" hajia tace "sai yanzu kenan? Jameel din ne yadawo daku? Fatu tace "a'a amm.... yayan amrah ne" sarai hajia tasan sultan ne ya dawo dasu don tana ganin shigowarsu duka, tace "bari in duba kullin masan nan, gobe da safe dadynku zai sauqo yace shi yake sha'awa" har hajia ta dubo ta fito fatu na tsaye a gun, hajia tace "auu baki haura bane? Kaman zatayi kuka tace "mummy wayoyi ya bani fa" da fara'a hajia tace "a ina" fatu ta labarta mata komai, hajia taga wayoyin tace "amma sunyi kyau Allah ya amfana" fatu da mamaki ya gama lullubeta tace "mummy gobe zan mayar masa dai ko? bata fuska hajia tayi tace "maganar gaskia fateema ki nemi soyayyar mijinki, abunda zan iya fada miki kenan, kibi komai a hankali da nutsuwa" har zata juya fatu tace "mummy ga tsaraba anty lubna ta bani" mummy ta gani tayi Allah ya amfana tayi upstairs. Zama jugum fatu tayi tana aukin tunani, ita ta rasa a wani yanayi take, shin tana son mijinta ne ko bata sonshi? Kodai kawai son yan'uwantaka ne? Amma deep inside her heart tana jin bazata iya rayuwa babu shi ba. Da taga tunani bazai fishhe ta ba tace "Allah ka shige min gaba" tashi tayi ta dauki roban ice cream daya da snack iya wanda zata ci sauran tasa a fridge, kashe wuta tayi ta kulle kofa tayi dakinta, bayan ta gama ci ne tayi wanka ta fito taga leda akan mirrow nata, murmushi tayi tace tsaraban mummy ne. Ta duba takalma ne yan ubansu guda uku kowanne da jakansa, na lubna kuma turaruka ne da cosmetics, adana su tayi ta kwanta. Qarar wayanta ne yasa ta tashi zaune a tsorice (sabon shiga😂🤓) a hankali tasa hannu ta dauka, number ta gani wanda tasan na sultan ne tace "hello" can gefe akace "hii" shiru ya biyo baya, can a gefe yace "sultan ne ya gajia? Tace "lafiya, nagode fa Allah ya saka" har cikin ranshi yaji dadin addu'anta yace "ameen, sai da safe, karki shanye ice cream din ki ragewa farouq nashi" daria dukansu sukayi kana sukayi hanging, daga ita har shi da murmushi a fuskarsu bacci ya dauke su. Hmm _lovebirds_😍

 

 

Maman Fa'izz👯👯

[7:41PM, 7/17/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

26

 

Yau kimanin wata biu da sati biu kenan da haduwan sultan da fatu a a gidan jameel, shakuwa mai tsanani ya shiga tsakaninsu, wanda yawanci in sultan na qasar shi yake kaita school, waya kuma kowanne dare sai sunyi b4 bacci, no love jst qanwa da yaya. Chattin babu wanda fatu batayi da taimakon qawarta xahra levels. fatu har sunyi exams na second semester suna hutu. Yau saturday sunyi da levels zasu je saloon, Karfe 11 na safe tana gidansu levels daga nan suka rankaya gurin saloon din da yake ba nisa tsakaninsu.

 

A gidan jameel naga sultan da abokin nashi a palour suna magana, jameel yace "its time ka furtawa fateema cewa kana sonta, don kun saba wanda nasan lokacin da kuka dauka kuna tare itama ta fara sonka" sosa kai sultan yayi yace "kana ganin ta fara sona? "Kwarai insha Allah" Jameel ya bashi amsa. Sunkuyar da kai sultan yayi kana ya dago yana kallon gefe. Muryan jameel yaji yace "FATU FA?? Da sauri sultan ya juyo da kanshi gurin jameel zuciyarsa na dukan uku uku, don shi ya manta ma da wata fatu, yau kimanin wata uku kenan ko aika da yake mata ya daina, fateema ta mantar dashi cewa yana da mata ajiyayya. Jameel ya qura masa ido yana jiran yaji mai zai ce, shi dai fatu ta masa tun ranan har yanxu kuma yana tausaya mata a matsayinta na marainiya abar tausayi, "baka yi magana ba" jameel yace dashi, sultan da har yanzu bai gama saita kanshi ba yace "ni fateema nake so, bani da ra'ayin zama da mata biu kuma. Inaga its time itama da zan furta mata abunda ya dace da ita" jameel zaiyi magana sultan yace "jameel u knw yanda aka hada auren, sam babu yarda ta. I cnt live with her" Shiru jameel yayi, sultan sai da ji hankalinshi ya dawo jikinshi ya dauki wayarsa yayi dialing numbern fatu.

Bayan an gama musu suka rankayo gida. Fatu ne da xahra ke hira kan sultan levels na cewa "wallahi qawa har yanzu ina mamakin wai sultan mijinki ne amma kuma bai ganeki ba, kuma wai he's in love with new fateema" murmushin daya fi kuka ciwo fatu tayi tace "labarin rayuwata kamar a movie, bansan nan gaba ya zaya kasance ba, zan rabu dashi ne ko zamu kasance a inuwa daya a matsayin mata da miji, levels ki tayani addu'a kawai. Allah ne kadai abun dogaro na" siririn hawaye ta goge hakan yayi dai dai da ringing din da wayarta ya fara "dan halal, yaqi ambato" cewar fatu yayin da murmushi ya bayyana a fuskarta, xahra ta bita da kallon tausayi. "Assalam alaika yayan fateey" "wa'alaiku mussalam qanwata, ya kike? Tace "lafiya lau, ya aiki? Yace "da godia, jiya kince zaki je saloon kinje ne? Tace "ehh, yanzu muka dawo ina gidansu levels ne" Yace "ok, in baza ki damuba anjima da yamma inason ganinki" tace "ok yayana, zaka zo gidane? Yace "noo, mu hadu a gidan jameel" sukayi sallama sukayi hanging. Fatu ta kalli levels tace "I gotta go, zanyi wa mummy kunun aya nd sultan yana son ganina" levels kada kai tayi kawai ta rakata haraban gidansu tasa drivernsu ya maida fatu gida.

Sultan na ajiye waya yace "jameel insha Allah nan da 1 week zamu je Garin Modibbo gurin FATU"

 

Maman Fateey👯👯

[9:44PM, 7/18/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

27

 

Jameel yace "I am sorry to say bazan iya raka ka ba, I cnt face da dattijo" yana gama fadan haka ya fice daga palourn, sultan ya bi bayansa amma yana fita jameel already yaja motarsa ya bar gidan, shima ya fita.

Lubna dake kitchen ta fito jiki a sanyaye da alama taji duk hiransu, jameel ya bata labarin fatu tun ba yau ba, haka kawai itama take kaunar sultan da fatu, ko ba komai 'yar uwarsa ce, marainiya mai neman taimako, kuma a yanda taji jameel ya fada fatun tayi karatu har zuwa secondary, so why not ya maida ta skul in educated wife din yake so, tunani barkatai lubna tayi akan fatu, tana tausayawa yarinyar. Tashi tayi ta shige dakin jameel ta bude drawer da yake ajiye pictures, da kyar ta samo pic din sultan da matarsa fatu. *WHAT*? naji ta furta da karfi hade da miqewa tsaye harta manta cikin 6months da yake jikinta.

 

Fatu na isa gida tayiwa mummy kunun aya tasa mata a fridge, fitowanta daga kitchen din yayi dai dai da shigowan mummy gidan, fatu tace "sannu da dawowa mummy" tace "yauwa fateema" fatu tace "farouq daya dawo daga skul yace zai biki gidan mammi, yaje ne" hajia tace "dan rigima yaje, ynxuma na barsu zasu je unguwa da amrah ne" fatu tace "ayya, nima inason zuwa gidan anty lubna anjima" mummy tace "Allah ya kaimu" fatu tace "Ameen, na gama kunun ayan, yana fridge" da murmushi a fuskar hajia tace "nagode 'yata Allah ya miki albarka" "Ameen mummy" fatu tace ta bar mummy a palour ta shige dakinta don tadan huta zuwa yamma, ko meyasa sultan yake nemanta oho. Wayarta ta dauka don tayi chattin amma sai taga missed calls din lubna 4, da sauri ta kirata don ita ta dauka ma ba lafiya ne. Ringing daya biyu ta dauka tace "Hello fateema kina gidana ne? Tace "ina gida, naga missed calls dinki ne, lafiya kam? Lubna tace "sai alkhairi, don Allah ina son ganinki yanzu yanzu" fatu tace "ai anjima ina zuwa da yamma" lubna tace "a'a its urgent pls ko minti biyar karki qara" fatu tace "to pls bari inyi wanka" "ohhh fateema kiyi hakuri ki dauko kayan da zakisa in kinzo kiyi anan" fatu tace "to gani nan zuwa" kashe wayan tayi zuciyarta na dukan uku uku. Anya ba ganeta sultan da jameel sukayi ba? Saisaita kanta tayi ta dauki abubuwan da take bukata taje dakin mummy tace "mummy bari inje yanxu anty lubna ta kirani" mummy tace "to shykenan Allah ya kiyaye hanya, ki dauka mata kunun ayan nan naga itama tana so" murmushi fatu tayi tace "to mummy" bayan ta dauka ne ta fita mal habu ya drivin dinta sai gidan jameel.

 

Maman Fateey👯👯

[9:45PM, 7/19/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

28

 

Sultan na fita gidansu ya nufa, kai tsaye room dinsa ya nufa ya zauna akan daya daga cikin kujerun da suke room din. Shi gabadaya jin haushin fatu yakeyi, ta bata mishi plan din rayuwarsa, gashi akanta har sun sami matsala da abokinshi wanda tun suna yara rabon da hakan ya faru, shi fa bazai iya ba, never!! Zai saketa ya kawota gurin mammi ya kuma gargadeta tayi kipp da bakinta. Laifinshi ne ma daya qarfafa bincike wajen nemo innar tashi. Tunani ya fara shekara biyu da suka wuce yana tare da mammin shi a dakinta suna hira lokaci daya tayi shiru yace "mammi lafiya" tace "tunanin 'yar uwata nakeyi, ko ya take? A ina take? ita kadai ce 'yar uwata da muke uwa daya, sai kannena da muke uba daya, shekarana 6 a lokacin aurensu ya mutu, ba yanda ba'ayiba a maida auren abun ya faskara, a haka aka barsu amma kuma ana tare don rabuwansu bai raba zumuncin dake tsakanin babanta da babanshi wanda suke yan uwan juna ba. Ina shekara 7 muka je dukku anan wani da ake cewa mal sirajo ya ganta yace yana so, a lokacin yana da mata da 'yayansa 4, da kyar aka bashi aurenta don ma tace itama tana sonshi ne, saboda bakin cikin hakan dangin mu suka tattara suka bar garin a cewarsu ta zabi bare akan dan'uwanta, duk da shi din ma bafulatanin ne, amma wai su fulanin yawo ne. Na sha kuka dana rabu da ita, bamu wuce ko ina ba sai yola dama can ne asalin garin mu, anan muka zauna har babana ya fara shiga birni yana kasuwanci anan yaga yara na zuwa skul ya saka ni, har Allah ya buda masa sosai yayi aure, kamar yanda ka sani kannena biu, rufa'I da musa. Mahaifinka shima auren dangi aka hada ni dashi, a can na haifeku duka muka dawo nan gombe lokacin ina goyon amrah. Na tashi cikin dangi amma ina kewar mahaifiyata Muna dawowa gombe na je dukku ganin mahaifiyata amma aka ce ta rasu, kanwata kuma tayi aure, nayi nayi su fada min inda tayi auren amma suka ce sun manta, sultan ina kaunar naga wani tsatso daga mahaifiyata" kwallan daya taru a idonta ne ya saurin zubowa ta share. Tun daga wannan lokacin sultan ya qudura aniyar nemowa mahaifiyarsa 'yar uwarta, yaje sau daya shima suka fada masa haka, zuwansa na biyu shigan dare yayi da wasu soldiers da yayi hayansu, tsoro sosai suka bawa mal jauro wanda ya fadi inda take aure har da sunan mijin nata. Yanzu a dalilin haka ya jawo wa kanshi damuwa.

[11:06PM, 7/20/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

29

 

Fatu na isa gidan jameel ta shiga gabanta na dukan uku uku, a palour ta tarar da lubna na zaune "kin iso? Tace da ita, sai da ta zauna tukun tace "ehh, Allah yasa lafiya" hoton ta ajiye akan cinyar fatu wanda lokaci qanqane dan walwalar da yake fuskarta ya bace ya koma matsanancin damuwa, ido ta kurawa hoton kamar yau taba kallon irinsa, lubna da ta kafe ta da ido tana nazarinta tace "explain please" hawaye naga yana zarya a kumatun fatu tana girgiza kai tace "its over, d charade" lubna ta matso kusa da ita ta dafa kafadunta tace "its not over yet, yanxu aka fara, trust me" tiryan tiryan fatu ta fara bata labarin har zuwanta gombe da yanda hajia ta taimaketa ta sakata a skul ta maida ita *FATUN BIRNI* ta kuma dauketa tamkar 'yar cikinta da ta haifa. Ajiyar zuciya lubna tayi tace "one last question, do u love sultan" dago idonta tayi da sukayi dan jaa don kuka tace "anty lubna......a life without sultan, even an immortal life would be empty, I wish to stay on earth with him" murmushi mai bayyana 32 lubna tayi tace "kamar yanda na fada miki its not over, to hakan ne" magana suka fara wanda nayi nayi inji amma fateey na ta dameni da kuka, naga dai lubna na zazzago magana yayinda fatu ke ta maida hankali 100% tana ji, can naji tace "he'll love her too" fatu da ta kasa boye farincikinta ta ruqunqume lubna tana daria kamar ance yau za'a kaita gidan sultan. Sai da suka natsa tace "anty lubna tnx alot Allah ya bar mini ke" "Ameen" ta bata amsa tana murmushi. Kiran sallah la'asar yasa suka farga dat its time. Lubna ta shiga bandakinta ta hadawa fatu ruwa a bathtub turarukan wanka naga ta diga a ciki, tayi alwala ta fito, ta bawa fatu towel ta shiga bathroom din yayinda ita kuma ta fara sallah. 15mins ta dauka tana dirja jikinta kamar yau aka haifeta😉 kana tayi alwala ta fito, zani da hijab lubna ta bata tasa tayi sallah, daga nan ta feshe jikinta da body spray ta shafa humra da kulacca duk na lubna, nan da nan dakin ya dau asirtaccen kamshin da komin gulmanka bazaka gane me da me aka hada ba. Wani swiss lace red nd black naga lubna ta dauko ta bawa fatu ta saka, fatu tace "na taho da kayana fa" "ban taba saka shiba, ko DJ bai san da zaman shiba, jst ki saka" ba musu ta karba ta saka, kamar a jikinta aka dinka, figure 8 dinta ya fito tarr, zaunar da ita lubna tayi akan kujera ta fara tsara mata make up, dauri ta kafa mata wanda yasa gashinta ya fito ta tsakiya ya kwanta a bayanta, Qara feshe ta tayi da wani turare mai sanyin kamshi, tace "done! Kallon kanta tayi a mirrow, ita kanta tasan tayi kyau bana wasa ba, kamar wata amaryan da za'aje dinner, qaran phone dinta ya katse kallon qurilla da take yiwa kanta, sultan nagani a screen din, dauka tayi ta kashe murya tace "Hello" sultan da yake kusa da motarsa yayin saurin dafawa don yanda muryan ya kashe masa jijiyoyin jikinsa, "hey" ya fada a sanyaye, ya cigaba "gani zan fito yanzu, kina gida ne in biya mu tafi tare? Sai data ja aji tace "nop, ina gidan yanzu haka" yace "ok gani zuwa" ya kashe wayan. Tsayawa nayi na qare masa kallo yau, dogo ne amma ba can ba, kuma da alama yana motsa jiki, fuskarsa irin na fulani sak, dogon fuska, manyan idanuwa, dogon hanci da bakinsa dan daidai, ga saje daya zagaye fuskar da quarter million suka qara qawata shi, gashin kansa kamar na fulani Aww ashe fulanin ne, black ga santsi a kwance. Fatar jikinsa Brownie ne kuma ba chocolate ba, daka ganshi kasan hutu da kudi sun zauna hade da kwanciyar hankali. Half jumfa ne a jikinsa na dakakkiyar shadda mai launin blue, takalmin shi da agogon shi black, ya hadu ne iya haduwa Dan Fulanin. Motarsa ya shige sai gidan jameel.

 

Maman Fateey👯👯

[10:38PM, 7/22/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

30

 

Fatu ta kalli lubna tace "he's on his way" jinjina kai lubna tayi ta fara magana "ki kula kiyi duk abunda ya dace, zan fita in nemo mijina nima" daria suka sanya dukansu, hijabi ta sanya ta fice a gidan a yar qaramar motarta, a waje ta hadu da sultan sukayi gaisuwan light ta harba titi shi kuma ya shige gidan maigadi ya rufe gate.

Da sallamansa ya shigo falon fatu data bashi keya ta juyo a kasalance ta amsa sallaman, daskarewa yayi a gurin yayinda ita kuma take jefanshi da malalacin murmushi tace "ka shigo mana" samun kanshi yayi da bin umarninta, a 1sitter ya zauna yayinda ita kuma take 2sitter suna fuskantar juna, bai taba ganinta haka ba gyale ko hijab ba sai yau,  manyan idanunshi sexy ya zuba mata kamar yau ya taba kallonta, kunya ce ta rufe ta ta dago ido tace "kai yayana wannan kallon" bai sani ba bakinshi ya furta "u luk gorgeous" "tnx" ta furta mishi. Tashi tayi tace "mutanen gidan basa nan bari in dauko maka ruwa" a hankali take tafiya wanda ya bawa sultan daman kare ma bayanta kallo, tana shigewa kitchen ya jijjiga kanshi yace "control sultan, control" saisaita kanshi yayi ya gyara zama yana tunanin ta ina zai fara mata magana, bai gama shawara ba ta fito da tire a hannunta ruwa ne da cups sai juice, nan dinma kura mata ido yayi har ta iso ta jawo centre table kusa dashi ta ajiye kana ta sunkuyo yanda dole ya shaqi kamshin jikinta, tace "wanne za'a zuba maka? Sultan da ya lula shaqar kamshinta ya kuma shagala da kallon kirjinta yace "na'am" sarai tasan abunda yake kallo amma ta nuna bata ganeba cikin ranta kuma tace ka kalla halalinka ne. Miqewa tayi tsaye ta qara maimaita masa tambayar da sauri yace "juice" don yasan dole ta tsaya shaking dinsa kafin ta zuba masa hakan kuma na nufin shaking din abunda yake son kallo Murmushi tayi ta dauki juice din ta shaking dinsa daga tsaye ta sunkuya tana saka masa a cup, tana gama sawa ta koma gurin zamanta shi kuma ji yayi inama tayita tsiyaya masa har gobe, kodai yace ta saka mishi ruwa ne? "Control sultan" ya fada a sanyaye ya dauki kofin yasha kadan ya ajiye. "As u said kana son ganina" fatu tace dashi yayinda take harde  kafuwanta, yace "ehh" tace "gani to".

 

Maman Fateey👯👯

[10:38PM, 7/22/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

31

 

Sunanta ya kira "Fateema" tsikar jikinta ne ya tashi tace "na'am" yace "magana ce tafe dani very important" yayi shiru tace "ehen i'm ol ears" yace "fateey tun ranar da na fara ganinki nake jinki cikin raina _love at first sight_ da tunaninki nake kwana dashi nake tashi, nayi amfani da lokacin da muka dauka tare don mu shaqu nd to knw more about each other" fatu da tun daya fara magana kanta na qasa naga murmushi ya subuce a fuskarta, "fateey" ya kira sunanta a hnkali, dago idanunta tayi suka sarqe cikin nashi "I'm really madly deeply in love with you fateema" Da sauri ta sauqe kwayar idonta yayinda wani siririn hawaye ya biyo kuncinta, na rasa gane na farinciki ne ko ko! Shiru tayi, zufa ne ya fara keto masa ba dai tana da wanda take so ba! "Fateema ko kinada wanda kike so ne? Ya fada cikin tashin hankali. Kada mishi kai tayi alamar a'a. "Bakya so na ne? Talk to me fateema, idan bakya sona zan iya jiran har lokacin da kikaji kin fara sona, shirunki kan iya sa jinina ya hau pls talk to me" ya qarasa maganar yana dafe kanshi da yaji yana barazanar tsagewa. Lura da yanayinsa yasa tace "Ina buqatar time nayi tunani" yace "zuwa yaushe? Tace "ko nan da 2 weeks" yaqe yyi 'wanda masu iya magana suka ce mugun kuka' yace "kiyi hakuri na baki 5 hours, zan kiraki anjima in d nyt" zatayi magana ya tari numfashinta yace "kiji tausayina please" ya langabar da kai kaman qaramin yaro dolenta yasa tace "to Allah ya kaimu" yace "Ameen matata" daria tayi tace "tun kafin inyi tunanin? Kana gaggawa" shima darian yayi ya mance ciwon kan daya fara damunshi dazu yace "I knw tunaninki zai kasance positively" daga nan suka bige da hira yana sako maganan soyayyarshi tana basarwa. Kiran sallan da aka fara ne yayi daidai da shigowan lubna da jameel sai darawa sukeyi, ganin fatu ta sultan yasa sukayi kasaqe suna kallonsu, sultan tadi yayi tadi ya dawo 2sitter inda fatu take sai hiransu suke. Gyaran muryan jameel yasa suka farga yace "sannunku" fatu tayi saurin daukan gyalenta ta yane jikinta sultan kuma ya miqe yace "ai sai muje sallah ko, tunda kaji ana kira" bai kula darian da jameel ke mishi ba ya fita daga falon shima jameel ya bishi suka wuce masallaci yana tsokanarshi wai akan yarinya ya dawo parrot.

Suna fita lubna tace "mutumiyata ya akayi" labarin yanda akayi fatu ta bata duka. Kallon sama lubna tayi tana murmushi tace "sai nan da 4 days zamuyi move din mu na biyu" fatu tace "na fara tsoro anty lubna, anya bazai..... "noo insha Allah babu abunda zai faru sai alkhairi, mu hada da addu'a" Daga nan suka shiga daki sukayi sallah suka girka simple abinci mara nauyi, ana kiran isha sukayi sallah bayan sun idar ne su sultan suka dawo. Lubna tasa fatu ta qara gyara fuskarta sai dai wannan karon da gyalenta suka fito falo, abinci suka fara ci wanda fatu duk a takure take yayinda lubna, Jameel da sultan ko a jikinsu, suna qare cin abincin Jameel da lubna suka rako su bakin mota, inka gansu sai sun burge ka, a gaba ta zauna suka tafi.

Suna isowa gida tana kokarin budewa ya sa lock tayi tayi ta bude ta kasa, kallonshi tayi ya zuba mata sexy eyes dinshi yana murmushi,  anan ta gane shi yasa lock, da shagwaba tace "amma ka wahalar dani, Allah na dauka yaqi buduwa ne" kwaikwayanta yayi yace "ai ban gaji da kallonki bane" daria tayi tace "kai ko? Bude mata yayi yace "sai na kiraki, kar kiyi bacci" "ok" tace yayinda ta fita ta maida marfin motar, daga mishi hannu tayi alamar bye amma bawan Allah yaqi tafiya, har cikin zuciyarta take jinjina irin son da sultan ke yiwa fateema. "Allah ka barmin mijina" ta furta a hankali ta shige cikin gida, shima sai daya ga kulewarta yayi ajiyan zuciya yace "Allah ka taimakeni" kana ya wuce gidansu.

 

Maman Fateey👯👯

[4:05PM, 7/26/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

32

 

Fatu na shiga gida ta samu farouq na kallo ya mata oyoyo tace "har yanzu bakayi bacci ba? Yace "yau saturday,  remember? Ba skul gobe" tace "yess hakane, ina mummy? Yace "tana falon daddy" tace "ok, bari in shiga in watsa ruwa".

Wanka tayi ta sa sleeping dress ta dora hijab kana ta fito palour, ganin mahmud a zaune kusa da farouq wanda har yayi bacci yasa kirjinta dukan uku uku! Tun dawowan shi yake tsare ta da tambayoyi yana so yasan daga cikin wani gida take a familyn nasu, answers da take bashi basa gamsar dashi kuma akwai alamun rashin gaskia a tattare a ita, _real lawyer_ 😄. Rufin asirinta daya shine after walima na gama karatunshi ya fara aiki a abuja, ba kowanne weekend yake dawowa ba, duk randa ya dawo kuma bata bari su zauna su kadai, in kuma suka zauna zai fara tambayoyi, in mummy na kusa sai tace "mamuda nan fa ba kotu bane da zaka dame yarinya da questions, distant relative ce baza ka ganeta ba" To yau kam qaryanta ya qare tunda ba mummy mai rufe bakinsa. Murmushi ta qaqalo tace "ahh mutan abuja sauqar yaushe" murmushin shima yayi yace "dazu da yamma, kina fita na shigo, naje gidan jameel din ma na samu kuna maganarku ke da matarsa, so bana son katse muku sai na tsaya, da naji bamai qarewa bane yasa na tafi" cikinta ne ya bada sautin qulululu... kirjinta na bugawa da sauri da sauri tace "m..me..me.. kaji? Murmushin cin nasara yayi ya qara narkewa a cikin kujeran yace "abunda kuka gama magana akai" Shiru tayi fuskarta na qasa tace "can u kip a secret?" bai motsa daga kwanciyar ba yace "yess, amma ina son details" briefly ta fada masa abunda ya dace, ta qarisa maganar da cewa "promise me babu wanda zaka fada wa" daria yayi yace "ni banida gulma, bincike na iya" daria sukayi dukansu hkan yayi daidai da shigowan mummy tana cewa "oya farouq kallon ya isa haka kaje ka kwanta" ganin su fatu yasa ta yin shiru Tace "fateema kin dawo? Fatu tace "eeh mummy, anty lubna tace a gaisheki kuma tana godia da kunun aya" da murmushi a fuskar hajia tace "madallah, mahmud dauki farouq ka kaishi dakinsa" Mahmud na haurawa tace "fateema akwai matsala ne? Naga mahmuda yana damunki da tambayoyi" murmushi fatu tayi tace "babu komai mummy, munyi magana dashi" hakan yayi daidai da dawowan mahmud mummy tace "to asuba ta gari, fateema ki locking kofa ki kashe wuta, na tafi" suka mata sai da safe ta wuce side din daddy.

5mins ya qara shima ya mata sai da safe, kopa ta kulle ta kashe wuta ta wuce dakinta. Tana hawa gado ta lalubo wayarta ta kira xahra "badai kinyi bacci ba? Fatu tace da ita xahra wacce da alama tayi nisa da baccinta tace "8:30 ma ina kan gado" fatu tace "ok dama labari zan baki amma tunda kin fara bacci sai da safe" da sauri xahra ta miqe zaune harda kunne bedside lamp tace "bani in sha, wallahi na tashi" daria sosai fatu tayi tace "shegen son labari"

 

Maman Fateey👯👯

[9:37PM, 7/26/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

33

 

Labarta mata yanda akayi duka tayi. Shiruu xahra tayi can tace "anya wannan plan din babu hatsari a ciki, kar garin neman gira a rasa ido fa" itama fatun shiru tayi xahra ce tace "are you there? "Yess" fatu ta bata amsa ta cigaba da cewa "insha Allah ba matsala, ki tayani da addu'a, Allah ya zaba mana mafi alkhairi" "Ameen" xahra tace suka cigaba da tattaunawa daga baya sukayi hanging.

Missed calls din sultan ta gani kusan goma a screen din wayarta tace yaushe ya kirani? (Har yanzu dai sabin shiga ne) Wani kiran ne ya qara shigowa ta dauka tace "hello" bai amsa ba ya watso mata tambaya "da waye kike waya? Ina kiranki ana cewa call waiting" murmushi tayi kaman yana kusa da ita tace "levels ne fa, ka koma lafiya? Shima murmushin yayi yace "lafiya lau, ya maganar mu? Tace "wacce kenan? Shiru yayi kaman bazaiyi magana ba, a kalla babes sun kai goma shima yana musu irin tambayan nan cikin jin kai, amma reshe ya juye da mujiya yau shi ake yiwa! "Answer na dazu, u said zakiyi tunani" fatu tace "ok, na tuna" yace "ina jinki" shiru tayi yayinda shi kuma ya qagu yaji matsayinsa a gurinta, gani yakeyi in ya rasa fateema duk matar da ya aura baza ta samu soyayyar da yake yiwa fateema ba. Sunanta ya kira "fateey, kinyi shiru" sai da ta dauki 5seconds kana tace "yess, Allah ya zaba mana mafi alkhairi" farinciki fal a fuskarsa yace "u mean kin amince? Tace "yeah". Hira suka yi cikin wayewa da natsuwa, sai da sukayi 30mins yace "ya kamata in barki haka kiyi bacci, amma ban gaji da jin sweet voice naki ba" qanqame wayar tayi a kunnenta tana lumshe ido ta qara qasa da murya tace "okay, gud nyt" yace "nyt dear, karki manta kiyi addu'an bacci" tace "ok tnx" sallama sukayi. Suna kashe wayan fatu ta tashi ta dauko pic dinsu tare da kudin sadakinta ta qura musu ido, kuka ne ya kwace mata tayi mai isarta har bacci ya dauketa. Sultan kuma yana ajiye wayan yace "saura fatu" murmushi yayi ya fara danne dannen laptop akan business dinshi. Yau kimanin 4days da fara soyayyarsu, in kaga yanda suke love sai ka aza sun shekara, wani zazzafan soyayya sultan yake nunawa fatu, yayinda itama take nuna masa bata da kowa like him. Haka da yamma zaizo ya dauketa suje yawon shaqatawa su sha hiransu ya dawo da ita, ga shopping niki niki. Wata rana kuma a gidan jameel zasu yi hiran, sai dare ya dawo da ita, nan ma sai an qara bata time kafin ta shiga gida. *love kenan* Mummy ta lura da hakan ta kira fatu tace "meke faruwa tsakaninki da sultan? Cikin jin kunya tace "wai mummy sona yakeyi" murmushi mummy tayi tace "kefa? Kina sonshi? Rufe fuska fatu tayi hakan yasa mummy ta gano answer dinta, "Alhamdulillah" mummy ta furta a hankali, tace "kin fada mishi matsayinki a gurinshi? Da sauri fatu tace "a'a mummy ba yanzu ba, kuma zan fada mishi da kaina in lokaci yayi" mummy taso ta gane wani abu amma ta basar a cewarta tunda suna son junansu shykenan. Ranar da suka cika 5 days suka hadu a gidan jameel. Hiransu sukeyi gwanin ban sha'awa, lubna ne ta fito da pics ta rarraba musu suna kallo, na daria suyi daria, na a bada labari a labarta, caraf a cikin pics din dake hannun fatu taga hotonsu itada sultan, turo baki tayi tace "honey wacece kusa da kai haka? Ta wani manne maka! Ta qarisa maganan tana miqawa lubna pic din, lubna na karba tace "laa fatu ce, uwargidan sultan" sultan da tunda fatu ta fara magana notinan kanshi ya sunce, ji yakeyi kaman ya rusa ihu, shikam fatu ta cuce shi, a 'yan kwanakin da yayi da fateema ya lura tana da kishi, yanzu in tasan fatu matarsa ce ya zaiyi. "Innalillahi" yayinda fatu ta miqe tsaye tana dafe kirji "lubna matarsa fa kika ce".......

 

Maman Fateey👯👯

[10:51AM, 7/31/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

34

 

Fatu ta juyo da kallonta gurin sultan tace "matarka? Pls kace wasa ne" bai dago ya kalleta ba zuciyarsa na tafarfasa, ya dafe kanshi yayi shiru, lubna ta miqe tayi daki dama jameel yana gurin aiki. "alama ya nuna gaskia ne kenan, ya Allah" juyi tayi ta cigaba "ashe yaudarata kakeyi? Na dauka kai mutumin kirki ne ashe ba haka ba ne, why me sultan? Jin muryanta kaman tana kuka yasa ya dago da kanshi, hawaye ne ke sintiri a fuskarta, ji yyi bazai iya ganin su suna zuba ba, kamo hannunta yyi ya zaunar da ita a 2sitter shima ya zauna, still hannun su na cikin na juna, yace "aure aka min amma bada son raina ba, ke kanki kinsan ke kadai nake so, ki fahimceni" juya masa baya tayi tana share hawaye tace "na fahimta amma ka sani ni bazan zauna da kishiya ba, kaje ka zauna da matarka, Allah ya baku zaman lafiya" cikin kidimewa ya juyo da fuskarta yace "what? Yanzu fateema zaki iya rabuwa dani? Wallahi bana sonta ko kadan kuma nakusa zuwa in bata takardar ta, nima bazan iya zama da villager irinta ba" wasu zafafan hawayene suka sauqo wa fatu yayinda wani baqin ciki ya turnuqe ta, wato itace villagern!!!  daukan hoton tayi ta yayyaga kuci kuci, ta zubar a palourn tace "maza duk halinku daya, jiki da kwalliyan mace kuke bi, baku damu da kamala ba, karka qara taka inda nake" ficewa tayi a gidan ta barshi zaune a gun yana jin radadin maganarta. Shi a iya saninshi mace bata taba hararansa balle ta gaya masa magana. Me take nufi da kalamanta? Tattara pieces na pic din yyi yasa a small dustbin din da yake falon, shima ya fita daga gidan.

Fatu kuma tana fita ta tari keke napep ya kaita gida, tana shigowa palour Allah yaso ba kowa ta haura upstairs zuwa dakin ta, zaman yan bori tayi a tsakiyar room din tacigaba da kukanta. Meyasa mazan ynzu basu damu da addinin mace da kamun kanta ba? Sunfi son wayayya yar boko wacce ta dace ta zauna a gaban mota kuma ta nunawa duniya? Meyasa taimako da tausayi yayi qaranci wanda har ana raba zumunci don son zuciya da kyale kyalen duniya? Tayi alqawari muddin ya saki fatu to bashi ba ita har abada, kallon kanta tayi a mirrow, me ya qaru a jikinta kuma me ya ragu? Gayu da gogewan da tayi yake so ba ba ita ba. "Villager" ta furta ta qara rushewa da kuka, ita tayi setting din draman amma ya dawo mata real life, a tunaninta zai so matarsa fatu ita kuma ta fada masa gaskian wacece ita! But sai hakan bai faru ba, miqewa tayi kaman wanda aka tsikara tace "yanzu inya sakeni ya zanyi? Ni fatu ya zanyi" zuciyar ta taji na mata quna, hakan yasa ta kwanciya akan gado tana aukin zubar da hawaye har bacci yayi gaba da ita.

 

Maman Fateey👯👯

[10:54AM, 7/31/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

35

 

Sultan gidansu ya nufa kai tsaye yayi hanyar garden a can ya zauna. Maganar gaskia yana son fateema amma wani gefe guda kuma yana jin bazai iya sakin fatu ba, don da zai iya da tuntuni ya aikata hakan tun bayan aurensu da 1month, a lokacin ya fara mata aika mata kudi, yaso ya rubuta amma zuciyarsa ta haneshi da aikata hakan, a baki kawai yake fada amma shi kanshi yasan ko yaya zaiyi bazai iya ba. "Shes quit nd innocent" daukan wayarsa yayi ya turawa fateema text....

 

_ban yaudareki ba kuma bana fatan hakan ya taba faruwa, duk da bana sonta 'yar uwata ce kuma marainiya, I dunno what to do, bana jin zan iya sakinta, amma please ki daina batun rabuwa dani, I cnt take it fateema_

 

Tsawon minti goma da turawa ba'a masa reply ba, hakan yasa yace "bata huce ba har yanzu, ya kamata na bata lokaci"

Fatu na tashi daga bacci kusan bayan la'asar tayi wanka da sallah, yanzu kam ta daina jin qunar da zuciyarta yake mata, wayoyinta ta dauko ta fito palour, ba kowa kamar mummy ta fita unguwa farouq kuma yana islamiyya, a kitchen ta tarar da dija na yankan kayan miya suka gaisa dija tace "ya na ganki kamar bakida lafiya? Fatu tace "kaina ke ciwo, ina mummy? Tace "tana gidan hajia sadia, a zubo miki abinci ne?  Fatu tace "a'a kiyi aikinki zan zuba" daukan plate tayi ta zuba tuwon shinkafa ne miyar ugwu yasha kifi da nama sai kamshi yakeyi, spoon ta dauka ta fito daga kitchen din, a dinning ta zauna tafara cin abicinta, wayarta ta dauka sai a sannan taga text din sultan, fuskarta ba yabo ba fallasa ta ajiye, tana gama cin abinci takai kitchen ta dawo falo ta kunna data wayarta, mssgs na sultan ta gani duk na ban hakuri, ta karancesu tsaf ta kashe data ta kunna kallo amma hankalinta baya kai sai tunani, a haka mummy ta shigo tayi sallama bata jita ba, sai da ta taba ta sannan ta juyo a dan tsorice, ganin mummy ne ya sata fara'a tace "sannu da dawowa mummy" Mummy ta kalle ta fuskarta da damuwa, zama tayi tace "fateema lafiyanki kuwa? Idan akwai abunda ke damunki ki fada min, karki boyemin komai I'm ur mum" kanta ta kwantar akan kafadan mummy yayinda hawaye masu dumi suka biyo fuskarta tace "mummy nayi missing din gida ne, tunda nazo banje ba haka kuma banji daga garesu ba" shafa kanta mummy tayi tace "karki damu, in kin kusa komawa skul zakije musu, saboda akwai abunda nake so in aiwatar kafin kije"

 

Maman Fateey👯👯

[12:04PM, 7/31/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

36

 

Yau saturday ya kama ranar da sultan zaije garin modibbo, da kyar da lallami yasa jameel ya shirya ya rakashi, wayarsa ya dauka ya turawa fatu text,

 

_yau zan tafi garin modibbo, pray for me_

 

Sai daya tura kuma yaji haushin kansa, yau kusan kwana uku bata daukan wayarshi bata amsa text dinshi, ko yazo ya aika ta fito bata zuwa, rabon daya ganta tun ranar da lubna ta kopsa masa, amma hala kawai ko abinci zaici sai ya mata text, zuwa unguwa da sauransu, amma bata kula shi. Shiga mota yayi ya zauna yana jiran jameel ya fito daga gidansa. Fitowa jameel yyi tare da lubna sai wani mannewa juna sukeyi suna I miss u, I miss u, haushi ne ya cika sultan ya danna horn da karfi wanda yasa suka dawo cikin hayyacinsu, tsaki jameel yaja yace "mallam zaka kashe min kunnen yaro" ko kulashi baiyiba, yanashiga yaja motar suka fara tafiya. Tittitititi alamar shigowan saqo da sauri sultan yaja birki wanda yasa jameel tsorita shi ya aza ma sun buge wani ne, da sauri Ya dauki wayan ya duba saqone daga fatu

 

_ka gaisheta_

 

 Shine abunda ya gani, wato duk mssgs dinshi tana gani wannan ne kawai taji zata amsa? Jameel wanda har yanzu zuciyarsa bai daina bugu ba yace "amma kai dan iska ne sultan, wannan wani irin ganganci ne zaka tsayar da mota cikin sauri haka? Kuma akan wata kake qoqarin kashe mu duka? Da mamakin shi sultan murmushi yake yi yace "srry dude, na love" jameel bai iya qara cewa komai ba don tsananin mamaki, shi ko ada da yake cewa in soyayya ya kama sultan zaisha wahala to bai taba zaton abun zai kai haka ba. "This is madness" sultan ya kunna motar yace "indeed". A haka suka kama hanyan kumo, jefi jefi sultan na bude saqon yana dubawa, da jameel yaga abun yayi yawa yasa ya karbi driving din, sultan yayi ta gwada calling fatu ko zata dauka amma taqi dauka, daya gaji ya hakura. Fatu kuma yau levels ta kawo mata ziyara, a daki na gansu suna zaune akan gado, fatu tayi wani _silent_ kamar marainiya xahra na bata baki "bai kamata kisa damuwa a ranki, duk da nasan its hardly ace baki damun ba amma gaskia ki sassautawa zuciyanki, addu'a zaki cigaba dayi, ki barwa Allah komai, kinji kam? Fatu da alama bata jin abunda xahra k fadi don wayarta take dannawa a hankali, kwace wayar xahra tayi pics din sultan take kallo, ido xahra ta bita dashi yayinda fatu ta gyara kwanciyarta ta bawa xahra baya, "ehh lallai babyn nan wato ni na zauna ina baki shawara kin maida ni bi ta can ko? Kinata kallon mijinki" tashi xahra tayi ta dauko laptop din fatu da sultan ya saya mata wai na karatu tace "me ma pasaword din? Sarai tasani amma ta tambaya _"SULTAN"_  fatu ta bata amsa, daria xahra tayi tace "soyayya ko wahala" ta cigaba da danne dannen ta har ta samu film din da take so ta fara kallo. Fatu kuma tunani ne fall a ranta na abunda zai faru in sultan ya isa ya tarar fatu ta fita nemansa months back!!!

 

Maman Fateey👯👯

[12:06PM, 8/1/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

37

 

Basu sha wahalan gane gidan ba duk da dan sauyin da aka samu kusan shekara da rabi, yau ma a kofar gida suka samu mal Ameenu yana zaune da wani mutum suna magana. Tun dosowar motar mal Ameenu yake kallonta duk da bashi sultan ya taba zuwa da ita ba amma yana kyautata zaton yau fatu tazo da mijinta. Nesa dasu kadan suka parking yayinda suka fito kowa da dan murmushi a fuskarsa, ganinsu yasa mal Ameenu fadada fara'arsa kaman an mishi bushara, yana leqen bayansu yaga ta inda zaiga *FATUN BIRNI* Kawu muntari da yake gefen mal Aminu yace "baba, ko dai maigidan fatu ne yazo? Gyada masa kai yayi saboda sun iso, sallama sukayi aka amsa musu suka sami guri akan babban tabarman suka zauna, kaka yace "muntari shiga gida ka samo musu ruwa" kawu muntari ya tashi da sauri ya shiga gida. Gaggaisawa sukayi cikin mutunci kaka bakinshi yaqi rufuwa sai hamdala yakeyi yace "ai na aza da ita zaku zo, ashe ku kadai ne" Jameel yace "na'am baba" don bai fahimci maganar ba sultan ma haka. Kaka ya cigaba da cewa "bbu abunda zance maka sultanu sai Allah ya maka albarka, yasa ka gama da duniya lafiya, wato naji dadin wasiqarka, shekara da auranku baka zo ba, nayi tsammanin ko baka son hadin da aka maka ne, har na fara maganan raba auren ganin yanda aka fara surutu a kauyen nan, mutane sunyi gaskia da suka ce 'mai hakuri shi kan dafa dutse har yasha romonsa' nan din ma hakan ya faru, ranar da kayi aika ta hadu da mal usman a hanya ya bata saqon kamar kullum" kallonsu kaka yayi da fara'ar da har ynzu bata bar fuskarsa ba, daga jameel har sultan sun zuba mishi ido, ya cigaba "wasiqan da na gani a ciki yasa na dauka ko ka sauwaqe mata ne, data karanta muka gane" daria kaka yayi amma babu wanda ya tayashi don gabadaya kansu ya daure, sun rasa inda maganarshi ya dosa, fitowan muntari yasa jameel cewa "me ya rubuta" muntari yace "rubutawa sultanun yayi cewa fatu ta bishi gombe zai yiwa mamarsa bazata, ko ba haka kace min ba baba? Kaka ya amshe "ehh" muntari yace "ai naso inje aga gurin da kuke din saboda ziyara, amma fatun tace ita kadai kace taje" tari ne ya sarqe sultan yanayi ba kakkautawa ruwa aka miqa mishi yasha sannan ya tsaya idonshi har yayi jaa, Jameel ne yayi qarfin halin qaqaro murmushi yace "haka fa, abun zai kai wata nawa ma? Daga kanshi yayi kamar mai son tunowa muntari yayi caraf yace "wata takwas ai ko" kiran sallah azahar da aka fara yasa sukayi shiru kowa da abunda yake saqawa a ransa, sai da aka idar mal Ameenu yace bari a kawo muku buta kuyi alwala, shiga gidan kaka yayi da kawu muntari aka barsu su kadai, a sannan ne sultan ya dubi jameel da tsananin damuwa a fuskarsa don a yanzu sun gane komai daya faru yace "ina cikin duhu jameel" girgiza kai jameel yayi yace "ita ta rubuta wasiqa kace taje, tun wata takwas da suka wuce kuma da alama har yau bata dawo ba, sultan, fatu ta bata" shiru sukayi sultan ji yakeyi kamar ya kurma ihu ko zaiji sassauci a zuciyarsa, _FATU TA BATA! IDAN MAL AMEENU YA GANE BATA TARE DASHI YA ZAIYI? IDAN MAHAIFIYARSHI TAJI ABUNDA YA AIKATA HAR HAKAN YA JANYO BACEWAR YAR QANWARTA YA ZAIYI? SHIN FATU TANA RAYE? IDAN TANA RAYE TA INA ZAI FARA NEMANTA? TA INA?_  Tambayoyin da suka cika brain din sultan wanda  babu wanda zai iya amsa mishi, ji yayi zuciyarshi na zafi yana ganin duhu duhu, hakan yayi daidai da fitowan kaka da muntari suka ajiye buta miqewan da sultan zaiyi yaji kanshi yayi nauyi ya zube a qasa.

 

Maman Fateey👯👯

[6:48PM, 8/1/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

38

 

"Innalillahi wa inna ilaihir rajiun" abunda kowannensu yake furtawa kenan sukayo kanshi, jameel ne ya shiga jijjiga shi yana "sultan, sultan ka tashi" yama manta cewa shi doctor ne, ruwan buta yasa aka miqo masa ya yayyafa masa, ajiyar zuciya mai qarfi ya sauqe kafin ya bude idonshi a hankali yace "ina fatu? Ganin zai qara magana yasa jameel saurin cewa "mu daga shi mu kaishi mota, dole sai an kaishi asibiti" mal Ameenu da yake da salallamai a gefe yace "muntari tayashi ku dauke shi, maza maza" hannayensa suka saka a kafadunsu suka kaishi mota kaka na "ashsha Allah ya bashi lafiya" yana girgiza kai. Suna sakashi a mota yana cewa "ina fatu? Ina fatu? Jameel yayi saurin shiga driver sit ya kunna motar, yana tunanin yanda zasu fara nemo fatu, tunawa da yayi cewa fateema ta yaga pic din fatu da suke dashi yasa yayi saurin fitowa daga motar ya samu kaka fuskar shi gwanin tausayi muntari na cewa "baba, sai cewa yakeyi ina fatu fa" alamar akwai matsala kenan, kaka na ganin jameel bai ko saurari muntari ba yace "jikin ne? Ko dai a qira madam nasi (nurse daya da suke dashi a qauyen) ta dubashi? Jameel yace "a'a nima doctor ne, fatu yake son gani, in akwai hotonta a bani" kaka cikin jimami yace "kayya wannan wani irin cuta ce? Fatu bata daukan hoto sai hoton ta daya da aka dauketa tana shekaru uku" da azama jameel yace "a bamu" kaka yayi saurin shiga gida muntari ya mara masa baya, shi kuma jameel ya koma gurin sultan a mota. Yana isa ya samu sultan ya fara dawowa hayyacinsa yace "yarinyar nan tana son kashe ni, tana jawomin matsala a rayuwata ta koyaushe, ina take? Bubbuga bayanshi jameel yakeyi yana cewa "be strong, be strong dude, zamu nemota insha Allah, I'm with u" jameel kaman ya fadawa kaka batan fatu amma yana hango tsananin tashin hankalin da zasu shiga in suka ji labari shiyasa ya shirya qaryan cewa sultan nason ganin hoton ta ne, fitowa kaka yayi muntari na binshi a baya kamar jela, da sauri jameel ya isa gurinsu ya karbi hoton tare da cewa "mungode, amma dole sai mun dangana da asibiti" muntari yace "to wani irin cuta ce wannan da zaisa mutum suma ya tashi da son kallon matarsa? Kaka ne ya harare shi kana ya maida kallonshi kan jameel yace "ai ya kamata ku hanzarta tafiya kafin wata matsala ta kunno" sallama sukayi jameel ya koma mota, ya samu sultan ya dafe kanshi yace "ka rage tunani sultan don kar ka jawowa kanka matsala, zamu nemota duk inda take" motar yaja suka tafi suka bar kaka cikin daurewan kai, meke faruwa ne?

 

Fatu na kwance kamar wacce aka tsikara ta tashi tace "xahra akwai matsala" xahra tasa pause ta juyo tace "a ina? "Yanzu idan suka je suka fadawa kaka bana tare dasu wallahi hankalinshi zai mugun tashi dama gashi da hawan jini, yanzu ya zanyi? Ido xahra ta qura mata tana tuna maganar fatu da take cewa rayuwarta kamar a film, wannan shine asalin film. Kafin xahra ta bude baki fatu ta sauqo daga kan gado ta dauki gyalen dogon rigan da yake jikinta ta yafa kawai tace "tashi muje gidan lubna, kaina ya daure, ban san me zanyi ba, zata fini sanin ya za'ayi" daukan gyalenta xahra ma tayi suka fito a palour suka tarar da mummy sukace zasu je gidan lubna, tace Allah ya kiyaye a gaisheta.

Suna fita daga garin sultan yace "taya zamu nemota bayan bamu san inda ta nufa ba, kuma ko hotonta bamu dashi" Jameel ya miqa mishi pic din da kaka ya bashi ya qurawa hoton ido kaman tana kama mishi da wata daya sani, tunawa da cewa ya taba ganin fatun yasa yabar tunanin, yace "wannan fa tana yarinya ce, ina wanda ka dauke mu? Jameel bai masa magana ba, tunowa da cewa fateema ta yaga yasa yayi zugum yana kallon dajin Allah. Suna shigowa gombe yace "jameel muyi gidanka" haka suka iso kowa da tunanin da yakeyi, ko gama parking jameel baiyi ba sultan ya bude ya fita da sauri jameel ya qarisa parking din ya biyo bayanshi "whats wrong sultan? Ina!! Already ya shige. Ko tsayawa kallon wadanda suke palourn baiyiba ya wuce gurin da dustbin yake ya juye a qasa.

 

Maman Fateey👯👯

[9:28PM, 8/3/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

39

 

Ba fatu kadai ba har lubna da xahra mamakine a fuskarsu, tsintan  pieces na pic din sultan ya fara yana ajiyewa a gefe, jameel ne ya shigo ya tsaya a kanshi yayinda su fatu ma suka matso suna ganin ikon Allah. Sai daya gama tarawa ya kwashe, yazo zai wuce ta kusa da fatu, tsayawa yayi yana kallonta itama ta tsura masa ido, har ta fara tausaya masa ganin a yini daya har ya fara susucewa, kawar da kanta tayi shima ya wuce bai ce mata komai ba, zama yayi a kujera ya jawo centre table ya baza pieces din ya fara jerawa, jameel ne ya zauna kusa dashi ya dafa kafadarshi yace "sultan" bai kalleshi ba yaci gaba da jerawa amma ko kadan basu jeru ba don kuci kuci suke, gumin da yake hadawa ya diga akan wani piece yayi saurin gogewa hakan yasa abunda yayi qoqarin hadawa kusan minti 10 ya wargaje, watsa nakan table din yayi a qasa ya dafe kanshi, ya kwantar da kanshi akan kujera, jameel da yake gefenshi yace "kayi addu'a sultan" addu'o'I ya fara idonshi a rufe yana dafe da kanshi. Jameel ne ya fara basu labarin abunda ya faru tun zuwansu, yana qarisawa sultan ya tashi zai fita, jameel ya tareshi yace "ina zaka je? Ka huta tukun" girgiza kanshi yayi yace "zanje gida ne, ka kai hoton gidan tv a fara cikiyanta don Allah, da gidan radio please" yana gama maganarshi ya fice, jameel yabi bayanshi. Lubna ta juyo da dubanta gurin fatu wacce take danna wayarta alamar bata da matsala tace "fateey ya kamata ki fada mishi kece, kiga fa yanda yake qoqarin zaucewa" tsayawa tayi da danne dannen tace "dadina daya da basu bayyana wa kakana ba" xahra tace "u have to talk to him" tashi tayi ta tsaya tace "a'a ba yanzu ba" murmushi tayi tacigaba "na zauna tsawon shekara daya cikin zullumin inda mijina yake, nayi kuka, nayi addu'a, duk inda nabi mutane magana sukeyi anacewa ga bazar bazar, wato mace mai aure amma ba miji, kaka ya hana ni fita, haka na zama tamkar mujiya, cikin gidan ma ba'a barni ba, goggo asabe cikin gaya min baqaqen maganganu take" juyo da dubanta tayi kan su xahra tacigaba "duk akan waye na sha wannan bakin ciki? Akan sultan, dalilin cewa ni baqauyiya ce, wacce bata waye ba, ban dace dashi ba" lubna tayi ajiyar xuciya tace "bawai na raina halin dakika shiga bane, a'a kinaji yanda DJ ya fadi abunda ya faru, har suma fa yayi" murmushi fatu tayi tace "babu abunda zai sameshi, xahra mu tafi" sallama sukayi wa lubna suka wuce gida, ita lubna har ta fara tausayawa sultan, fatun ma ta tausaya mishi amma tayi alqawarin saiya horu tukun, tana son nuna mushi dan adam ba abun wulakantawa bane, kuma cewa "kare ma yanada rana, balle mutum dan adam mai tunani da hankali"

 

Maman Fateey👯👯

[4:13PM, 8/5/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

40

 

Fitansu suka wuce gidan tv bayar da cikiyan, ba qaramin daru sultan ya tayar musu ba kan sunce bazasu karbi hoton a matsayin wanda zasuyi cikiyar ba, A cewarsu suna buqatan hoton ta na yanzu, yanda jama'a zasu ganeta, da kyar suka karba ganin yana neman daga musu hankali, suka ce zasu saka amma ba dole bane jama'a su gane ba. A gidan radio ma hakan ya faru sun buqaci a fada musu kamanninta da shekarunta, kamannin Jameel ne yayi guessing ya fada shekaru kuma sultan yace "17 noo 18" kallon mamaki ma'aikatan suke binsu dashi, ace yazo a masa cikiya amma bashida  cikekken details.

A hanyansu ta dawowa sultan yayi shiru yana tunanin abunda zai faru gaba, don shi gani yakeyi fatu ta mutu ko kuma an sace ta, gani yakeyi baza a taba ganinta badon wata takwas ba wasa ba, yanzu me zai cewa mammin sa, yanda take muradin ganin qanwarta da zuriyarta, akan son kai irin nashi ya saka mafarkin mahaifiyarshi bazai taba zama gaskia ba. Hawaye naga ya gangaro a fuskar sa, yayi saurin gogewa don kar jameel ya gani, Yace "jameel nayi kuskure kuma nayi nadama, daa na yarda da qaddaran auren yarinyar nan daa haka sam bai faru ba, nayi wa mammi alqawarin nemo mata qanwarta, amma sai gashi ta dalilina da selfish mind dina nayi sanadiyyar bacewar the one nd only blood din aunty na. Ban san a wani hali yarinyar take ciki ba, ko tana raye ko ta fada hannu mara kyau I dunno, jameel Allah zai kamani akan hakkin fatu, tana matsayin matata shekara da wata takwas ban waiwayeta ba" muryan shi ya fara rawa hawayen da yake qoqarin boyewa ne ya silalo, jameel ya kalleshi ya girgiza kai cikin tausayawa, sultan ya cigaba da magana bayan ya share hawayen "jameel da na dauki shawararka tun bayan auren da ban shiga matsala yanzu ba, yarinya ce fa, she's just 17 a lokacin, tana kuka ina fada mata maganganu marasa dadi, kamar qanwata take fa, qanwata ce kuma matata" gyara zamanshi yayi idonshi na hawaye yacigaba "ban san wani hali kakanta da mummy zasu shiga ba in har ba'a samu yarinyar nan ba, ban san da wani ido zan kalle su in musu bayani ba" Zai qara magana jameel ya dafa kafadarshi yace "its ok, ka rage damuwa sultan, za'a sameta da yardar Allah"

[9:17PM, 8/5/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻          

Na Mrs Aslam Haidar

41

 

Sun shigo unguwan jameel yace "mu wuce gidana muci abinci ne? Sultan yace "ka kaini gida kawai, nikam na koshi" gidan su sultan ya nufa, a haraban gidan yayi parking ya fito amma sultan yaqi fitowa, gani yake yana shiga mammi zata karanci abunda ya faru! Jameel ya bude masa kofa ya jawo hannunshi ya fito dashi kamar mara lafiya, a palour gidan ya zaunar dashi ya fara kwalawa amrah kira, amrah da take dakinta ta amsa ta fito ta gaishe shi ta dubi sultan da ya wani sanyi dashi kamar maraya tace "ya sultan bashida lafiya ne? "Ehh, ki kawo mishi abinci" tace "too" ta wuce kitchen, dai dai nan mammi ta fito daga dakinta tana waya, ganin sultan cikin wani yanayi da bata saba ganinshi ciki ba yasa tace da wanda take wayan "zan kiraki anjima" ta kashe, jameel ya gaisheta hankalinta na kan sultan da yake binta da ido kamar yau ya taba kallonta (yayi laifi yana tsoron duka😆) Tace "meya sameka _manga_? Runtse idonshi yayi, ji yakeyi kamar ya fada mata laifin daya aikata na wasa da rayuwar abunda take muradin gani. Jameel ya ari bakinshi yace "kanshi ke ciwo mammi kuma bai ci abinciba, a bashi paracetamol in yaci" amrah ta fito da tray a hannunta ta ajiye a qasa tace "inyi serving ne? Mammi tayi saurin cewa "ehh" jameel ya musu sallama ya tafi gidanshi cike da tausayin halin da abokinshi yake ciki, Amrah ta zuba masa a plate jalof na spaghetti da irish potato yaji kifi, da kyar ya yadda yaci don sai da mammi ta bata rai tukun, magani ta ballo masa ta bashi dolenshi yasha ba don zai yaye mishi matsalan da yake ciki ba. Yana gamawa mammi tace ya tafi dakinshi ya kwanta ko na 30mins ne.

Su fatu na isa gida suka wuce dakinta, tunanin fatu daya yanzu kuma, kar magana ta fito mummy taga laifinta, shiru tayi tana tunano halin da tabar mijin nata ciki, xahra ta buge ta tace "kinyi abu yana damunki, ko a yanzu sultan ya jijjiga, abeg karki sashi kwanciyar asibiti, kinsan ajeebo ne bai saba da damuwa ba" harara fatu ta watsa mata tace "eeyee tunda ni kuma ajeebako ce na saba da damuwa sai in tausaya mishi ba? Levels tace "ba haka bane qawas, lamarin duniyan nan in kowa yace zai rama abunda aka masa fa baza'a zauna lafiya ba, kuma hakuri yana da kyau, ko yanzu ya gane kuskurenshi kuma yayi nadama, shawara nake baki" tana gama fada ta shige toilet. Kogin tunani fatu ta fada  'tana son mijinta sosai, tana son kasancewa tare dashi, amma yini daya yayi kadan a cikin horon laifin daya aikata' ajiyar zuciya ta sauqe ta rafka uban tagumi, alamar an bude kofa yasa tayi saurin sauqe tagumin, xahra na fitow tace "ni zan tafi gida" rakata tayi mal habu ya maida ita, fatu ta dawo gida cikin damuwa, kitchen ta nufa tana taya dija aiki don rage yawan tunani.

 

Maman Fateey👯👯

[10:14PM, 8/7/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

42

 

Sultan a room dinshi ya kasa samun sukuni, ya kai gauro yakai mari, tunaninshi ina fatu zata iya zuwa a nan garin, tuno maganar jameel yayi ranar da aka daura musu aure suna hanyan dawowa.... jameel ya miqa mishi pic yace "ga pic dinka" ko kallonshi baiyi ba yace "don Allah mallam ka barni, duk kai ka jawo min, ka wani saurin amsawa kamar kai za'a aurawa ita, gaskia ni baka min dai dai ba" girgiza kai jameel yayi yace "yarinyar nan tana da nutsuwa ga hankali, baka san alkhairin da ke tattare da auren nan ba, nine kai daukanta zanyi ta zauna a matsayin matata har lokacin da naji na fara sonta, koda ban sota ba zan zauna da ita saboda yar'uwata ce kuma zan iya qara aure nan gaba, ni dai na bata address na gidanku idan baka zo ka dauketa ba zata biyoka" yana tunawa a lokacin haurawa sukayi sosai akan wai jameel yana masa katsalandan a rayuwa "don meyasa zaka bata address dina? Baka taba bata min rai irin haka ba jameel" dawowa daga tunanin yayi yace "may be tazo nan" da sauri ya fita gurin maigadi yana kwala masa kira Iliya ya fito daga bandaki da gudu yace "yallabai gani" yace "wata takwas da suka wuce wata mace tazo nan gidan tana nemana?  Daga kai iliya yayi yace "babu wacce tazo nemanka sai wannan yarinyar sharipa da kace kar in kuskura in barta ta shigo, ita ce take zuwa lokaci lokaci nemanka, wallahi yalla.... sultan ya katse shi yace "ba ita na tambayeka ba, babu wacce tazo kamar yar kauye kauye haka? Iliya yace "a'a yallabai, sai dai yar aiki da hajiyayya ta kawo kwanaki, naji ita ke share maka daki. Juyawa sultan yayi da sauri cikin gida, a palour ya tarar da mammi da amrah na hira, lokacin yamma yayi liss, mammi ta kalleshi tace "sultan ya kaji jikin? Yace "da sauki" don shi har ya fara tunanin ko larai mai gyara masa daki itace fatu, yace "mammi ina larai mai gyara mini daki? Mammi tace "amrah kira min ita" da sauri amrah ta tafi kiranta. Mammi ta dawo da dubanta gurin sultan tace "manga wani abu ta maka? Girgiza kai yayi yace "a'a tambaya zan mata" mammi tace "to" nan amrah ta shigo larai na binta a baya a tsorice Allah yasa ba laifi tayi ba, kallonta yayi, yayinda ita kuma ta durkusa a gabansa jiki na bari tace "gani ranka shi dade" alama ya mata data miqe, da sauri ta miqe amma kanta na kasa, kallonta yayi yana tuno kamannin fatu, fatu fara ce wannan kum baqa, fatu kyakkyawa ce wannan kuma masha Allah😁, fatu yarinya ce wannan kuma da alama ta haihu 7, sai dai rashin jiki da tsayi wanda in baka ganta da kyau ba zaka ce yarinya ce. Tsaki yaja yace "jeki kawai" zama yayi a kujera yayi shiru Mammi da take kallon show din tun daga farko tace "sultan lafita kuwa? Ka kira mata kuma baka ce mata komai ba, me yake damunka ne yau din nan? Kallon amrah yayi yace "kije dakinki zanyi magana da mammi" ba musu ta wuce dakinta. Zamowa yayi ya zauna a kasa kusa da kafafun mammi yace "mammi ki yafe mini, na miki laifi"

 

Maman Fateey👯👯

[7:30PM, 8/8/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

43

 

Kallonshi mammi tayi cikin rashin gane me yake nufi, tace "me ka mini sultan? Ina jinka" qara sunkuyar da kansa yayi ya fara bata labarin tun daga farko har karshe, anan yace "ki gafarce ni mammi wallahi son zuciya ne ya kaini da aikata haka, nasan nine silan bacewarta, zan nemo miki ita a duk inda take mammi" ya qarisa maganan yayinda yake riqe da kafafuwanta, shock mammi ta shiga, Kasa magana tayi don ranta yayi mugun baci, hawaye ne ya gangaro daga idonta, 'wannan wani irin rashin hankali sultan yayi? tashi tayi zata tafi, sultan da yake riqe da kafanta ya dago ya kalleta, hawayen daya gani a fuskarta yasa hankalinshi qara tashi, magiya ya fara yana kuka yana bawa mammi hakuri, kwatar kafanta tayi bata ce dashi komai ba ta shige dakinta, shirun mammi yayi yawa, shi da dukansa tayi ko ta masa fada amma shirunta na nufin abubuwa da yawa har da 'kar in qara kallon fuskar ka' tashi yayi ya fita yana share hawayen da baisan lokacin da suke ambaliyan fitowa ba, in ka ganshi sai kace yayi sati a kwance, duniyar gaba daya yaji ya fita a kansa, idan yau akace an samu fatu to duk soyayyar duniyan nan zai dora a kanta, "where are you fatu" ya furta yayinda ya fice daga gidan zuwa masallaci sallan maghrib. Yana idar da sallah ya shige motarshi ya dinga bin unguwa unguwa ko Allah zaisa yaga fatu, a wata unguwa yayi sallahn isha, ya samu limamin mosque din yace a tayashi da addu'a matar shi ta bata, Limamin ya mishi alqawarin tayashi addu'a, yawo ya cigaba dayi, idan yaga masu neman taimako sai ya taimaka misu, bai dawo gida ba sai kusan 11, abunda bai taba yi ba. Yana shigowa yaga kiran abbanshi ya dauka yayi sallama aka amsa mishi, abba yace "kazo palour na ina son ganinka" cikin girmamawa yace "too abba, gani nan". Da sallama ya shiga ya samu mammi ce da abba zaune, kallon mammi yayi ta dauke kai, daka ganta zaka san tana cikin bacin rai. Gaishe su yayi mammi taqi ta amsa, abba ne ya fara magana "Mahaifiyarka ta sameni da magana wanda banji dadinsa ba ko kadan, hakan da kayi ka nuna cewa kayi girman da mu iyayenka babu ruwanmu da sha'anin rayuwarka, abunda kayi niyya shi zakayi, kusan shekara biyu da aura maka mata amma mu iyayenka bamu da masaniya, baka kyauta ba ko kadan" sultan da kanshi ke qasa tun da abba ya fara magana ya samu bakin cewa "nayi kuskure abba, kasa baki mammi ta yafemin"

[9:09PM, 8/8/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

44

 

Nasiha sosai abba ya mishi kana ya kalli mammi yace "hajia sadia kinsan sha'anin yara da rashin hankali, kiyi hakuri yayi nadama" kasa furta komai tayi, alama abba ya mata da ido yasa tace "naji, wani mataki ka kai na nemo ta? Sultan da yaji sanyi a ranshi yace "na bayar da cikiyanta a gidan Tv da radio, insha Allah za'a sameta" jinjina kai mammi tayi tace "Allah yasa" tambayoyi abba ya mishi ya bashi amsa sannan yace "kaje ka kwanta, zan nemeka gobe akwai abunda za'ayi" da farinciki sultan ya musu sai da safe ya fita. Abba ne ya fara bawa mammi baki sai daya tabbatar ta rage damuwa sannan suka kwanta.

Sultan na shiga dakinshi ya shiga wanka, bayan ya fito ne ya saka kayan bacci daukan wayanshi yayi, ya lalumi aljihun rigan daya cire ya fito da pic din fatu tana 3yrs, inka ganta kaman baby doll, taci kaya masu ado an mata jagira ga jan farce an mata diqo dashi a goshi, tasha kwalli rambadadau, bakinta ne da alama ba'a mishi kwalliya ba don pink ne, zura mata ido yayi yace "sweet matata yar rigima, kina bani wahala" nan take ya tuno da fateema yace "sai na samu fatu zan dawo kanki" daukan pic din yayi a hoto ya postin a facebook, twitter, da duk wani chat da yakeyi yace "duk wanda ya ga mai kama da ita yar 18yrs ya fada masa, akwai kyauta ga duk wanda ya sameta"

 

Fatu tana gama Taya dija aiki ta wuce dakinta, tama rasa me zatayi, gashi ba makaranta balle karatu ya debe mata kewa, chattin ta fara tana karanta novels anan taci karo da sabuwar littafin BEBEELO 'HANNE 💣' daria takeyi tace 'lallae hanne kin cika bomb' kiran sallahn maghrib yasa ta tsaya da chattin ta wuce tayi sallah, farouq ya shigo dakinta yace "anty fateema ki bani laptop dinki inyi game" ya rausayar da kanshi, linke sallaya da hijabin tayi ta ajiye akan bedside drawer ta kamo hannunshi suka zauna akan gado tace "baka ce please ba" kama kunnenshi yayi yace "ok please kinji? Murmushi tayi tace "zan baka amma sai munci abinci tukun" washe baki yayi yace "nagode" taja hancinsa tace "u ar wlcm" hira suka yi har aka kira sallah isha, farouq ya tafi mosque ita kuma ta kabbara nata, bayan ta idar ta sauko palour ta tarar da mummy a palour da alama itama bata jima da fitowa ba, fatu ta mata sannu mummy tace "Yau kuma kin zama matar daki" murmushi tayi tace "na fito dazu kina daki ne" sallama farouq da mahmud sukayi suka shigo, fatu ta fadada fara'ar tace "oyoyo mutan abuja" daria yayi yace "inda wata bata taba zuwa ba" fushin wasa fatu tayi tace "anji, nima watarana zanje" mummy tace "kyale shi, kuje kuci abinci, dadynku ya dawo daga mosque ne? Ta tambayi mahmud, yace "nidai tahowan mu mun barshi da abban amrah a haraban masallacin" "ok" mummy tace ta tashi ta wuce side din daddy. Fatu suka wuce dinnin tayi serving dinsu sai wasa da daria sukeyi ita da mahmud, yana ce mata yar qauye. Bayan sun gama ne ta tattara takai kitchen ta dawo palour suka qara bude babin wani hiran, farouq ya tuna mata alqawarinta tace yaje ya dauko laptop din a daki, bayan ya dauko ta cire masa password din ya fara game suka cigaba da hiransu. Kusan 10 mummy ta shigo tace "farouq kaje ka kwanta" dama ya fara gyangyadi, ya tashi ya tafi dakinsa, su fatu suka mata saida safe ta wuce side din daddy. Sabon hira suka bude anan fatu tace "yau baka ga sultan ba? Yace "na ganshi, ana idar da sallah ya fice a motarsa, kamar ma bashida lafiya" daria fatu tace "yaje garin modibbo ne ya samu bana can shine ya shiga tashin hankali harda suma" zaro ido mahmud yayi yace "yaushe? Murmushi qarfin hali tayi tace "yau" gyara zama yayi yace "kin sanar dashi ne? Girgiza kai tayi alamar a'a. Mahmud yace "karki dau alhakinsa fa madam" tace "bazai kai har can ba" dauko wani zancen sukayi na case din da ya gama abun daria abun haushi yana bata labari, su ne basu tashi ba sai 11, bayan ya fita ta kulle kofa ta haura upstairs zuwa dakinta, wanka tayi tasa kayan bacci ta dauki wayarta ta bude data mssgs suka shigo, updates din sultan ne ya bata daria da tausayi, tace ya kamata in masa jaje, typing ta fara masa.

 

Maman Fateey👯👯

[10:14AM, 8/18/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

45

 

    _Allah ya yasa a ganta cikin sauqi, ya kuma kare na gaba._

 

Abunda ta tura mishi kenan, yana cikin ganin comments din mutane yaga na Fateemah Mahmud da sauri ya karanta, yaji dadin jajen da ta masa, a zuciyarsa yace she loves me.

 

    _Thanks alot baby_

 

Murmushi tayi tace duk randa ka gane nice fatunka akwai drama.

Kashe data tayi ta kwanta amma ta kasa bacci, tunanin mijinta kawai takeyi ko a wane hali yake ciki sai Allah, rungume pillow tayi tana aukin tunanin sultan dinta har bacci barawo ya saceta.

Sultan yaga bata qara masa reply ba a ranshi yace da sauran aiki kenan, ganin dare ya tsala yasa ya shiga toilet ya daura alwala ya fara nafilfili, Allah yasa a ga matarshi fatu.

 

Washe gari haka ya tashi duk jikinshi na mishi ciwo saboda rashin bacci da bai samu ba jiya, hatta idonshi sai da suka kumbura. Misalin 8:12am ya shiga palourn abban nashi, samu yayi mummy na jera abinci akan dinning table duk jikinta a sanyaye, ganin yanayin danta yasa ta tausaya mishi, gaisheta yayi ta amsa ba yabo ba fallasa, tace "sultan kayi bacci kuwa jiya? Shiru yayi tace "magana nake maka" ya dago da kanshi yayi yaqe yace "nayi mammi" bata yarda ba don daga ganinshi bashida kwanciyar hankali. A daidai nan abba ya fito yana daura agogo a hannunsa, mammi ta isa ta tayashi, sultan ya gaishesa, abba yace "kaci abinci kuwa? "A'a, na koshi ne" ya bashi amsa, "kaji mini shiririta, rashin cin abincinka zai warware maka matsala ne, zo nan ka zauna kaci abinci, hajia zuba masa" Zama sukayi duka akan dinning table din mammi ta zuba masa dankali da kwai ne sai ferfesun zabuwa wadda yaji kayan hadi, ga ruwan lipton a gefe, mammi ta tashi zata tafi abba yace "kefa? Tace "ba yanzu zanci ba" dukansu suka bita da ido yayinda ta fice daga falon, sultan kamar yayi kuka, abba ya girgiza kai ya fara cin nasa amma sultan sai jujjuya fork din yakeyi cikin abincin, ganin haka yasa abba yace "idan kaci akwai good news" sultan ya kalli abban nashi, shi kuma ya masa murmushi, cin abincin ya fara don yasan good news a yanzu bai wuce ace an fara tracing inda fatu take ba, yaci abinci sosai.

Suna gama karyawa abba da sultan suka fice daga gidan, driver ne yayi driving dinsu a motar abban nashi, a hanya abba yake fada masa zasu je gidan commissioner ne a watsa masu nemo fatu saqo saqo na gombe a binciko inda take, hatta local govs sai an bincika, dadi ne ya cika sultan, don yana mai fatan Allah ya karbi addu'arshi ya takaita mishi wahalan nemo fatu, gidan suka je aka musu iso nan da nan don abban nashi sananne ne, kuma commssnr abokin shi ne. Bayan sun gama gaishe gaishe abba ya masa bayanin abunda ke tafe dasu, cmmssnr yace "alhaji za'a sa a nemota, kuma ya kamata a fadawa su iyayen yarinyar don watakila ta gurinsu a samu wani haske" abba yace "tashin hankalin da zasu shiga muke tunani, basu da kowa anan garin da zata iya zuwa can" magana suka cigaba dayi ta yanda za'a bullowa al'amarin. Basu tashi ba sai da suka gama tsara yanda za'ayi komai, Sukayi sallama driver ya ajiye abba a office, sultan kuma ya koma gida.

Fatu ta tashi washegari wasai abunta, bayan sun karya ne farouq ya fita wasanshi a cikin gida, suka zauna a palour da mummy suna kallon wani indian series jefi jefi suna hira.

 

Maman Fateey👯👯

[10:21AM, 8/18/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

46

 

 Sultan na dawowa gida ya tarar da mummy a dakinta ta zuba uban tagumi yayi sallama ta amsa, yace "mammi...." daga mishi hannu tayi tace "bana son jin komai daga gareka sultan, idan kana son kaga farinciki na ka kawo min fatu, ban taba tunanin bakada tausayi irin haka ba, yar uwarka ta jini ka barta cikin wahala da uquba don kawai an aura maka ita? Ka tashi ka bar mini daki" tashi yayi ya fita yana share hawaye ashe mammi ba yafe masa tayiba?

Gefen mammi tana tausayin danta amma kowanne second ta tuno bacewar fatu wanda ta dalilin sultan ne sai taji bakin ciki mara misaltuwa, share siririn hawayen daya zubo mata tayi tace "Allah ka bayyana fatu a duk inda take"

Yana fita kai tsaye ya shiga motarshi maigadi ya bude masa gate ya fita, motar jameel ya hango ta nufo shi parking yayi a bakin hanya jameel ya qara gaba kadan shima yayi, tare suka fito jameel ya nufo shi yayinda sultan ya jingina da motarshi, gaisawa sukayi jameel yana lura da shi yace "sultan yaya dai" yace "na fadawa mammi komai" Da sauri jameel ya kalleshi cikin tashin hankali yace "why? Meyasa baka bari har sai mun nemo fatu ba? Baka tunanin mammi zata shiga wani yanayi? Yanzu mebya faru? Sultan ya fada masa yanda akayi jameel ya girgiza kai yace "daa ka nemi shawarata tun farko bazaka fara fada mata ba, yanzu abun ya zame maka biyu, ga neman fatu ga tunanin halinda mammi take ciki" sultan yace "gani nakeyi kowanne daqiqa laifina qaruwa yakeyi, gani nakeyi rashin fada mata da wuri zaisa ta tsaneni, gani nak......." "its ok" jameel ya tareshi yana bubbuga kafadunshi Qoqarin shiga motarshi ya fara jameel yace "ina zaka je? Shiga yayi ya kunna motar yace gidan tv and radio" jameel yace "kace min abba yayi magana da cmmsnr" yace "ehh, bamusan ta ina za'a ganta ba, yafi a bawa ko'ina muhimmanci" jameel yace "ka jirani in ajiye motata a gidanku in fito" kallonshi sultan yayi yace "jameel kar in daura maka wahala" yace "damuwarka tawa ce, what are frnds for? Shigar da motarsa yayi gidansu sultan kana suka tafi. Sunje amma babu alaman nasara haka suka dawo gida jiki a sanyaye nan ma jameel na kwantar masa da hankali, hannayensa ya dora akan steering yace "ka fadawa mammi zan nemo mata fatu, zan zo tare da fatunta, da daina fushi dani" jameel da bai gane nufinshi ba ya fita daga motan yana qoqarin zagayawa ya budewa sultan, kafin ya ankara har sultan yayi reverse ya fice a gidan da gudu. Yayi Saurin shiga motarsa yabi bayanshi amma ko alamarsa bai gani ba, ya nema sa duk inda yake zaton zai samesa amma babu labarinsa, hankalinshi yayi mugun tashi don za'a yi biyu babu yanda ya fita da gudun nan komai kan iya faruwa dashi, naushin steering yayi ya furzar da iska, ji yakeyi kaman shima yayi kukan, da sauri ya lalubo wayarshi ya dialing number sultan amma 'switch off' sauran numbers din ya gwada suma duk a kashe, cikin tashin hankali ya nufi gidansu sultan.

 

Ayi hakuri da rashin jin FATU kwana biu, qanwata aka yiwa aiki a tayamu addu'a Allah ya bata lafiya da duk marasa lafiya Ameen. Masu jaje ta group, ta private har masu kira a waya nagode muku da nuna kulawa, Allah ya saka da Alkhairi👏🏽👏🏽. Luv u all😘😘

 

Maman Fateey👯👯

[8:48PM, 8/19/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

47

 

Da sauri jameel ya shiga gidan kai tsaye ya shiga falo, a zaune ya samu mammi ta qurawa tv ido wanda daga gani hankalinta baya kan kallon. Sallama yayi ta amsa da guntun murmushin ta, ganin yanayin fuskar sa yasa tasha jinin jikinta tace "jameel lafiya? Sai da ya zauna ya gaisheta a gurguje ta amsa tace "ya na ganka haka? Baka jin dadi ne? Girgiza kai yayi yace "mammi sultan ya fita cikin wani yanayi, na kira layukanshi duk a kashe, kin tsananta fushi a gareshi, ina gudun kar ayi biyu babu mammi" tashi tayi tsaye tana "innalillahi wa inna ilaihir rajiun" ta dauki wayarta da yake kan kujera a gefenta ta dialing number abba, sanar dashi tayi ta qarisa maganan tana hawaye Abba bai ce komai ba ya katse wayar, gwada layukan sultan yayi duk a kashe, baiyi wata wata ya dawo gida, a palour ya tarar da jameel zaune ya zuba uban tagumi, mammi kuma sai safa da marwa takeyi tana ta kiran sultan a waya amma baya shiga,

Tana ganinshi tayi saurin zuwa gurinshi gaba daya hankalinta a tashe, tace "ka sameshi? Bai mata magana ba ya maida dubansa gurin jameel daya cire tagumin yana gaishe sa, abba ya amsa shima fuskarsa cike da damuwa yace "jameel me yake faruwa ne? Jameel ya kalli mammi tukun abba yace "fada min komai ba matsala" jameel ya kwashe duk yanda akayi har abunda mammi ta yiwa sultan da safe ya fada masa, "kinga irinta ko? Yanzu kam kinji dadi ai, meyasa ku mata bakwa tunani kafin ku aikata abu?" Abba ya fadawa mammi yayinda takaici ya gama rufesa, ganin haka yasa jameel ya musu sallama ya dauki motarsa ya fice a gidan ya shiga gidansu.

"Sadia na miki magana akan yaron nan, kina ganin halinda yake ciki amma kika qara masa akan hakan! Na samu ya fara walwala, dazu gidan commissioner muka je don a nemo matar tashi, mun gama tsara komai, lokaci daya kin bata komai, sai ki fada min waye za'a fara nema" mummy da ta fara hawaye tun dazu tace "kayi hakuri, wallahi naso danne zuciyata amma laifin da sultan ya mini yayi nauyin da bazan iya boye fushi na ba" abba yace "idan wani abu ya samu sultan....." nan wayarshi ta fara ringin ya dauka.

 

Maman Fateey👯👯

[10:37PM, 8/20/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

48

 

Gaisawa sukayi da wanda yayi masa wayan, mutumin yace "don Allah da ahaji rufa'I nake magana? Abba yace "ehh, shine" gefe daya akace "idan kanada spare key na motar danka kazo nan ebele road its an emergency" abba bai tsaya tambayan meya faruba yace "gamu nan zuwa" don yasan bai wuce ace sultan yayi hatsari kuma motar taqi buduwa ba, ya dubi mammi ta cikinta ya gama kullewa tana kallonshi a tsorice tace "alhaji lafiya? Qin fada mata yayi yace "ana nemana a office ne" bai saurari me zata ce ba yayi fita. Zama tayi a kan kujera gabadaya hawayen ma ta nemesu ta rasa, idan wani abu ya samu tilon danta sultan ya zatayi? Sultan da amrah kadai suka rage mata cikin 'yayanta duk sauran daga tayi miscarriage ko kuma suna jarirai su rasu, gashi Allah ya saka mata son 'yaya, shi yasa take neman zuriyar mahaifiyarta itama tace ga nasu sun tara 'yaya masu yawa. Zufa ne yaketa keto mata ta ko'ina, tana son tashi tabi bayan abba amma ji takeyi kafafunta bazasu dauketa ba, anan ta samu hawaye ya fara zuba, a haka amrah tazo ta sameta tace "mammi, mammi meya sameki? Share hawayen mammi tayi tace "babu komai amrah, kaina ke ciwo" a sanyaye ta tashi ta shige dakinta, amrah tayi zugum tana tunanin me yake faruwa ne a gidan daga jiya zuwa yau, don daga mammi har sultan yanayinsu ya sauya sosai, akwai abunda yake faruwa amma kowa yaqi ya fada mata. (Kai fatu, kinsa mutane da yawa a cikin damuwa) Mammi na shiga daki ta kira layin abba amma bai dauka ba, tayita kiransa shiru, hakuri tayi ta zauna kawai tana addu'a Allah ya dawo mata da danta lafiya. Abba na fita ya wuce dakinsa ya dauko key din, bai ko saurari driver ba yayi driving da kansa zuwa ebele road, kiran layin mutumin yayi ya masa kwatancen inda suke, nan da nan ya isa gurin amma baiga alaman anyi hatsari ba, asalima motar a parkee take a gefen hanya ga mutane sun zagayeta, da sauri abba ya isa gurin zuciyarsa na fada masa ciwo yayiwa sultan yawa ya mutu, duk dauriyansa sai da zuciyarsa ta karye ganin danshi sultan cikin mota kanshi akan steering babu alaman numfashi a tattare dashi bai kula mutanen da suke masa magana ba ya bude motan gaba daya jikinshi a mace, ya jayo sultan, taimaka mishi wani mutum yayi suka maida shi baya yayinda abba ya shiga driver sit ya kalli mutumin daya tayashi yace "kaine ka min waya? Mutumin yace "ehh nine alhaji" abba yace "shiga muje" suka wuce asibiti dama already ya locking motarsa daya taho da ita.

Jameel na shiga gida ya samu ba kowa a falo, ya zauna jagabb a kujera Fatu ce take sauqowa daga steps tana waya, taci makeup ga kayan jikinta sun amshe ta, da qaramin jakanta yayi matching da takalminta tana cewa "ke dallah yanzu ma haka ina qoqarin shiga mota ne" tana sauqowa suka gaisa da jameel a ranshi yace 'bakisan halinda masoyinki yake ciki ba' yace "ina mummy? Tace "ta fita unguwa dazu" Yace "kefa" tayi murmushi tace "wollah zanje birthday party na qawata ne xahra levels" yace "hala bakida labarin am nemi sultan an rasa ko" miqewa yayi zai tafi fatu da ta zama statue ta yi saurin qarisa gurinshi kamar zata shige jikinshi tace "yaa jameel meya samu sultan dina? Ina yake? Tana maganar ne yayinda hawaye ke sintiri a fuskarta kamar famfo, jikinta har rawa yake gaba daya ta fita a hayyacinta kowanne pore na gashin jikinta gumi yake fitarwa "kamin magana yaa jameel" ganin bashida niyyan magana yasa ta fita da gudu, ya kwala mata kira yayi saurin bin bayanta.

 

Maman Fateey👯👯

[1:04PM, 8/21/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

49

 

A haraban gidan ya sameta tana kokawa da kuban gate, (ta manta akwai qaramar kofan fita), yayi saurin qarasawa gurinta yana kiran sunanta "fateema, fateema! Ta juyo tana kallonshi amma bata fasa kokawar ba, yace "ki nitsu, idan har kina son jin inda yake.

 

Abba na isa asibiti aka gangara sultan emergency, likitoci uku ne a kansa suna faman nemo numfashinsa, abba ya zauna akan chair yayi tagumi, bakinsa na motsi a hankali alama addu'a yakeyi, wayarshi ce ta qara ringing bai duba ba don yasan mammi ce, bai san me zaice mata ba. mutumin da abba yazo dashi yace "alhaji ayita addu'a insha Allah babu abunda zai sameshi, zai fito lafiya" abba yace "Ameen, Ameen" mutumin yace "ai muna zaune a shagon bakin hanya muka ganshi yazo da gudu lokaci daya kuma yaja birki ya tsaya, shiru shiru bai fito kusan awa daya, ganin haka yasa na tashi in duba ko lafiya, don na shaida motar, ai nima ta unguwar taku nake amma a pantami, da naje na duba sai na kwankwasa glass din motar, shiru shiru bai dago ba har yan majalisan mu suka taso suma suka zo, anan dai suka tabbatar da cewa ba bacci yake yi ba, Shine na kira masinjanka makwabcina ne, ya turo min numbern ka. Abba yace "nagode kwarai mal dahiru" doctors minti 30 suka dauka akan sultan kafin suka samu daidaituwar numfashin sa, dakin hutu aka kaishi don sunce yana bukatan hutu sosai don jininsa ya hau, zai iya farkawa in da next 48hrs. Abba ya dade tsaye a kansa yana tofa masa addu'a, kana ya fito bayan ya shaidawa family doctor nasu ya kula mishi da danshi sultan sosai, mal dahiru yabi bayanshi yana cewa "alhaji ya mai jikin? Yace "da sauqi Alhamdulillah" a haraban hospital din abba yacewa mal dahiru ya shigo motarsa ya ajiyeshi a shago amma yaqi, yace "alhaji zan hau mashin wallahi, iyalinka na jiranka a gida" abba yace "to shykenan" ya dauko kudi mai dan tsoka yabashi, mal dahiru sai godiya yakeyi har abba ya shiga mota ya fita daga hospital din. Sai da jameel ya tabbatar ta nutsu kafin ya fada mata yanda ake ciki, durkushewa tayi a gurin tana kuka mai tsuma zuciya, "duk ni na jawo, nine na jawo" tashi tayi tana kuka make up din zuwa party ya cabe, ta fita daga gidan, jameel ya dauka akan sabanin da suka samu tsakaninta da sultan ne, jikinta ba kwari ta nufi hanyar fita, jameel ya tsayar da ita yace "bazaki fita a cikin state din nan ba" komawa gida tayi ta zauna tana rabzan kuka, ta rasa me zatayi? Tukunna ma ina sultan dinta??? Tashi tayi ta leqa falo ganin jameel yasa ta tsaya, shi kuma qin tafiya yayi don kar a kuma baro wani aikin, ba'aga fatu ba, ba'a san inda sultan yake ba, to in fateema ma ta fita wayasan inda zata je? Layukan sultan ya qara kira amma shiru, ya kira na abba shi kuma bai dauka ba, (Allah sarki, abba bai ma duba ba don ya dauka mammi ke kiransa) yana son fita nemo abokinshi amma yana tsoron barin fateema ita kadai. Ya kusan 1hr kafin wayarsa ta fara ringin ya dauka.

 

Abba na dawowa ya gida kai tsaye dakin mammi ya nufa don yasan hankalinta a tashe yake tana ganinsa kuwa ta taso yayi saurin zaunar da ita yace "ki kwantar da hankakinki, an samu danki" mammi wacce muryanta ya dashe don kuka tace "ya rasu ko alhaji? Abba yace "yana nan da ranshi sai dai tension da ya masa yawa yasa jininsa ya hau, yanxu yana asibiti zai farka nan da awa 48, tace "Alhamdulillahi, Allah nagode maka, alhaji muje in ganshi" abba yace "a'a kiyi sallah azahar tukun zai muje" ba yanda ta iya tace "to" abba ya fita daga dakin zuwa side dinsa, sai a sannan ya dauko wayarsa ya duba missed calls ciki harda na cmmssnr da jameel, a ranshi yace 'Allah sarki duk inda yake hankalinshi shima a tashe yake, kiran jameel din abba yayi, yace "jameel an samu sultan, yanzu haka yana asibiti" jameel ya miqe tsaye yace "abba a ina aka sameshi, ya aka sameshi? Abba ya fada masa jameel yace "Alhamdulillah, gani nan zuwa nima" fatu da take labe tana jiran jameel ya fita itama ta fita neman mijinta tayi saurin sauqowa qasa har tana tuntube tace "an same shi? Jameel wanda murna ya sakashi murmushi yace "an sameshi, Allah abun godia" itama murmushin tayi idanunta cike taff da hawayen murna ta sharce tace "muje in ganshi" jameel yace "too"

 

Maman Fateey👯👯

[9:05PM, 8/21/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

50

 

Motar jameel suka shiga, ya kunna suka fita daga gidan zuwa gidansu sultan don abba ya fada mishi cewa sai sunyi sallah azahar suma zasu je. A haraban gidan suka sami abba na magana da driver yace "ka hau achaba na bar motana a ebele road gurin *FA'IZ PLAZA*" Abba ya miqa mishi key din driver ya karba ya fita, har qasa fatu ta tsugunna ta gaishe da abba, ita kunyan hada ido dashi takeyi don a dalilinta danshi ya shiga wani hali, shiga cikin gida tayi tabar abba da jameel zasu je masallaci.

Tana shiga falo babu kowa, zama tayi kirjinta na dukan uku uku, tana son ta bayyanawa mammi cewa itace fatu amma tana tsoron abunda zai biyo baya, don yanda mammi take son sultan baza taji dadin abunda fatun ta musu ba, kusan minti biyar tana zaune gashi har an kira sallah, amrah ta fito daga dakinta zata shiga dakin mammi, nan taga fatu zaune a falo da uban tagumi, amrah ta kira sunan ta amma inaa! Hankalinta ya gama tafiya, sai da ta matso sannan fatu ta juyo a tsorice, ganin amrah ne yasa ta kwaqulo murmushi wanda iyakacin shi fatar baki tace "amrah" tace "anty fateema lafiya" tace "lafiya lau" amrah tace "mammi tasan kinzo kuwa? girgiza kai fatu tayi tace "a'a, nima ban jima da shigowa ba" amrah tace "ki shiga dakinta mana" fatu tace "a'a, kaini dakinki inyi sallah" amrah tace "to muje" a dakin amrah tayi sallah tayi addu'a Allah ya tashi kafadun mijinta, tana gamawa ta share hawaye a fuskarta ta koma falo, bata dade da zama ba mammi ta fito tare da amrah kowa da shirin zuwa asibiti, fatu ta sunkuyar da kanta qasa ta tsugunna ta gaishe da mammi, mammi tace "sai kika ji abunda ya faru ko? Kasa cewa komai fatu tayi mammi tacigaba da magana "qaddara baya wuce ranar sa, sai addu'a zamuyi Allah ya tashi kafadunshi" kuka fatu ta fara har da sheksheqa, takaicinta daya, meyasa taqi bayyana kanta tun ranar da sultan yaje ya samu bata nan? Gashi yanzu a dalilin ramuwarta mijinta da take matuqar so yana kan gadon asibiti, muryanta a sarqe tace "ban kyauta ba" mammi tausayin fatu ya gama cikata, tana son yarinyar sosai tana son sultan ya aureta ko da an samu fatu, daga mammi har amrah bbu wanda ya gane abunda ta fada, mammi ta isa gurinta ta dago ta daga tsugunon da tayi, ta kama hannunta suka fito haraban gidan suka shiga mota, jameel yana driving yayinda abba na gefenshi, mammi da fatu na baya amrah a tsakiyarsu. Fatu Hawayen dai bai daina zuba ba, ta juya kanta gurin window tana cewa a ranta 'a yau kowa zai san wacece ni! yau zan dawo fatu! Share hawayen tayi tana mai fatan ganin mijinta ta bayyana masa kanta!!!

 

Maman Fateey👯👯

[10:25PM, 8/22/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

51

 

Suna isowa asibitin suka fito suka shiga ciki har kofar dakin da sultan yake, anan suka tsatstsaya suna lekanshi ta window don ance ba'a son a shiga, fatu ta leqa ta ganshi kwance ga drip an daura mishi, ya wani haske ya rame, kuka ne yazo mata tayi saurin toshe bakinta ta fita da gudu, mammi ta bi bayanta tana kiranta, abba ya girgiza kai ya nufi office din dr, jameel da amrah kuma suka samu guri suka zauna cikin jimamin abunda yake faruwa. A haraban hospital din mammi ta samu fatu akan bench a karkashin wata bishiya tana zaune tana kuka, mammi ta zauna kusa da ita ta jawo ta jikinta tana jijjiga ta, fatu tace "mammi kiyi hakuri na miki laifi, nice na jawo halinda sultan yake ciki" ta qara fashewa da kuka, mammi ta dagata tace "kul! Kar kice haka, bakida laifi ko kadan, nice mai laifi fateema" fatu ta zamo daga kan bench din tayi knelling hannayenta nakan cinyan mammi tace "mammi" mammi ta tace "na'am fateema, ki tashi ki zauna, bana son ganin kina kukan nan, ki tashi" fatu ta girgiza kai tace "mammi kinsan inda fatu 'yar qanwar ki take? Tuno da fatu yasa mammi hawaye ta share tace "a'a fateema, kema kinsan abunda ya faru ko? Muna kan nemanta" Fatu ta kama hannun mammi tace "nice fatu mammi, nice yar qanwar ki rahmatu wacce kike nema mammi, gani gabanki ki mini duk hukuncin daya dace dani" shock mammi ta shiga ta miqe tsaye tana nuna fatu da yatsa, tace "kece fatu? Fatima yar qanwata? Yar mahmud da rahmatu? Fatu dake still a durqushe ta daga kanta alamar ehh hawaye shabe shabe a fuskarta tace "nice mammi, nice wallahi" tsayawa mammi tayi cikin tsananin mamaki tana kallon fatu, wacce sai yanzu take ganin kamanninta dasu sultan da amrah, "ashe ke dama jinina ce, shiyasa nake jinki har cikin raina, nake ganinki tamkar yar dana haifa, Alhamdulillah" mammi ta fada yayinda take hawayen farinciki, lokaci daya kuma ta canja, fuskarta ba alamar annuri tace "meyasa kika kasa sanar dani tun baya??? Dago da kai fatu tayi ganin fuskar mammi yasa ta firgita bakinta na rawa tace "m...mam...mi walla..hi..." mummy ne ta qaraso ita da lubna cikin sauri don tun dazu jameel ya kirasu ya fada musu, ganin yanayin fatu da mammi ya tabbatar musu an bayyana wacece FATU A BIRNI....

 

Maman Fateey👯👯

[11:22AM, 8/23/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

52

 

Mummy na qarisowa ta daga fatu ta dora kanta akan kafadar mummy tana hawaye abun tausayi mummy tace "its ok daughter, its ok, ki daina kukan nan haka kar ya jawo miki matsala" mammi da take kallonsu cikin mamaki kanta ya kulle, yaya akayi fatu tazo gidan hajia kulsum? tace "hajia how comes fatu ta kasance a gidanki? Please ku cireni a duhu, anya itace fatuna? Mummy tace "itace fatunki hajia, kar kiga laifinta na qin sanar dake da tayi, lubna ku shiga ciki keda fateema zanyi magana da hajia sadia" lubna taja hannun fatu suka shiga cikin hospital din, mammi da mummy suka zauna akan bench din mummy tace "fateema bata da laifi ko kadan mammin amrah, in har hakan laifi ne to nice da laifi, hasalima hakan da nayi shi ya kawo kusancin da yake tsakaninta da sultan, wanda adaa babu wanda yake son dan'uwansa" Mammi tace "naso in fahimceki hajia, ni ba don halinda sultan yake ciki bane, a'a Ina matsayin mahaifiyarta tana kusa dani amma ta kasa fada min? Nifa uwace, kuma nasan kin fada mata yanda nake son ganinsu, sultan kuma shi ya jawowa kanshi, banga laifinta ba, ai ya fada min yanda aka yi har aka daura mishi aure da ita" anan mummy ta fada mata yanda akayi ta kadeta da mota ta kawota gidanta har yau da take bata labari, mummy ta qarasa da cewa "ban san sultan yaje neman ta ba, da nazo na warware komai, fateeman ma inaga bata da labarin cewa yaje can garin midibbon" Murmushi mammi tayi ta daga hannu sama tace "Allah na gode maka, Alhamdulillah, Allah ka bawa sultan lafiya ya tashi yaga fatun shi" "Ameen Ameen" mummy amsa itama tana murmushin jindadin yau ta kusan cika burinta, saura haduwan FATU DA SULTAN. Suna zaune a gurin abba yazo zai wuce commssnr yana nemansa ya kallesu yace "hajia zan wuce gidan cmmsnr yana nemana, inaga akan matar sultan ne" da mamakinshi sai yaga dukansu suna murmushi a ransa yace 'mata dai akwai matsala' yasha mur da yake suna wasa da mummy yace "kun tasa ni a gaba kamar qaramin yaro kuna min daria, hala kun shaqi laughing gas ne" ya qarisa maganar da dan murmushin sa. Mummy tace "gashi kaima ka shaqa ai, hajia bari in shiga ciki ki mishi albishir" tana gama fadan haka ta shige cikin hospital din, abba na ganin ta qule yazo ya zauna yana mamakin wani albishir za'a masa, shi dai yasan ba akan sultan bane don yanzu ya baroshi kwance, to kodai an samu matar sultan ne? Noo bazai yiwu ba don basuda link da inda za'a ji labarinta. to menene haka? Kallon mammi yayi yace "bazaki fada min bane sai kinja raina?

[7:16PM, 8/23/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

53

 

Hararanshi mammi tayi cikin wasa tace "bribe me" tsananin sonjin menene yasa yadauki wayarshi ya bata, mammi tace "a'a riqe kayanka, an sami matar sultan, fatu 'yar qanwata rahmatu, tana tare damu kusan shekara amma bamu ganeta ba" abba yace "tana ina kenan" mammi ta bashi labarin komai. Abba cikin mamaki yace "ikon Allah, ranar dana fara ganinta a gida na dauka 'yan uwa ne daga yola, ku dai mata sai a hankali, ai sai ku sanar damu, hakan da kukayi kun nuna bazaku umurci 'yayanku akan abunda kuke so ba, sai dai ku biyo musu ta yanda suke so, munada iko akansu tunda mu muka haifesu, Allah ya kyauta, ni zan tafi gidan commissioner in sanar dashi an samu yarinyar" mammi dai tana shiru har ya dasa aya tace "Ameen, a dawo lafiya" murmushi ya mata yace "ameen, na tayaki murnan ganinta" tace "nagode, sannunka da wahala kaima" bai bata amsa ba yace "sai na dawo" ya tafi gurin ajiye motoci. Mammi ta tashi ta shiga cikin asibitin.

Su fatu na shiga lubna tace "kin fada mata ne? Fatu ta goge hawayen fuskarta tace "na fada mata, yanzu ji nakeyi kamar an dauke min wani nauyi a kaina, saura sultan shima da kaina zan fada masa insha Allah, amma lubna ina tsoron kar mammi taqi yafemin don na sanya danta kwanciya a gadon asibity" lubna ta dafa kafadarta tace "karki damu, mammi ta riga da ta yafe miki na sani, ke dai sultan ne ya rage, shima baza'a samu matsala dashi ba" anan suka iso gurinsu jameel lubna tace "DJ ya labarin matar sultan? Yace "kayya, madugu uban tafiyan ma ya kasa controlling kanshi kin gamshi a kwance, yanzu inaga gurin abba zanje muyi proceeding kafin sultan ya farfado" murmushi lubna tayi tace "u dnt have to" cikin rashin gane inda maganarta ya dosa yace "ban fahimceki ba! Tace "ga fatun nan da kuke nema" ya kalli fatu yayi yaqe yace "lubby u must be joking, ke a wannan halinda muke ciki har kinada lokacin wasa" ya gama maganarshi cikin bata fuska. Amrah da tunda suka fara magana tana binsu da ido cikin rashin fahimtan akan su waye ake magana tace "waye ya bata? Wane sultan? Kallonta sukayi dukansu sukayi shiru, fatu ta isa gurinta tace "ni cousin sis dinki ne, da mammi da mamana mahaifiyarsu daya" Ta cigaba "yayanki yaje nema na aka aura masa ni, to ni yar kauye ce ba ajinsa bane yasa ya tafi ya barni 4 a year bai qara waiwayana ba, ganin haka yasa na fito nemanshi, anan mummyn farouq ta kadeni a bakin tashan nan garin, lokacin da na bata story na tace I should stay with her har randa mai bayyana ta bayyana" fatu ta kalli lubna alamar labarinta yayi daidai yanda za'a fadawa amrah? Lubna ta mata 👍 yayi dai dai, fatu ta maida dubanta ga amrah wacce ta sake baki tana mamakin wannan labari, tace "to meyasa yayana ya kwanta rashin lafiya? Lubna ta karba tace "ya fara sonta, da yaje can garinsu sai ya tarar bata can, shine hankalinshi ya tashi yazo ya fadawa mammi, mammi kuma ranta ya baci, so kinsan yanda sultan baya son bacin ran mammi, dats why he end up here" amrah ta fara tunani tana kada kai, no wonder jiya sultan da yamma yace ta tafi dakinta zasuyi magana da mammi, kuma taga mammi cikin damuwa don ita kanta tasan yanda mammi take son ganin auntyn nasu, ehh lallai biri yayi kama da mutum. Jameel ya miqe ranshi a bace yace "lubna for how long kika san cewa fateema fatu ce? Lubna ta fara inda inda yace "tell me" tace "tun ranarda suka hadu suka fara hira" cikin bacin rai yace "kin kyauta, yanzu idan mutuwa yayi ma babu ruwanki, a dalilin ki tayata ramawa kika qi fada min ina? Weldone, banga laifin fateema ba sai naki don ita sultan ya mata laifi nima shaida ne" yana gama fadan haka yayi ficewarsa, a bakin kofa ya taradda mummy na shigowa yace ina abba? Tace "yana tare da mammi" lubna ta iso gurinsu cikin sauri sau haki takeyi jameel na ganinta yace "mammi bari in dan fita, zan dawo yanzu" ya fice lubna tayiwa mummy yaqe ta bi bayan mijinta, har suka wuce su mammi basu ankara dasu ba, keke napep ya tara a bakin asibitin ya shiga itama ta shiga tana bashi hakuri. Kamar na bisu nace 'kai labarin fatu nake bi ba nasu ba"

Fatu kuma tun fitansu kirjinta yake dukan uku uku, to wannan reaction din jameel ne, yaa na sultan kuma zai kasance a kanta? Zufa ya keto mata tace "kar fa yace bazaiyi accepting dina ba tunda ban tausaya mishi ba" amrah da take gefenta tace "me kika ce anty fateema? Yaqe fatu tayi tace "babu komai amrah, maganar zuci ne" dai dai nan mummy ta qaraso ta fara bawa fatu baki kan ta kwantar da hankalinta, batada matsala da mammi, fatu dai kada mata kai kawai takeyi amma tunaninta nakan irin draman da za'ayi in sultan ya farfado.

 

Maman Fateey👯👯

[8:55PM, 8/25/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

54

 

Suna cikin haka mammi ta shigo itama, fatu sai sunkuyar da kai takeyi bata son hada ido da ita, ganin haka yasa mammi ta isa gurinta ta kamo hannunta suka zauna tace "karki damu kanki, laifinki daya fateema na qin sanar dani wacece ke, mummy ta fada min dalilinki, have no worry dear, uwa bata fushi da danta" rungume fatu mammi tayi tana jin tsantsar sonta cikin ranta, taso ace mahaifiyar fatu tana da rai itama taga wannan rana, hawayen farin ciki ne ya gangarowa mammi ta share ta dago fatu wacce itama fuskarta ya cabe da hawayen, mammi ta ciro hanky a dan qaramin bag din da ta taho dashi tana gogewa fatu fuska, abun ya bawa mummy daria tace "hajia surkuwa ce fa"

Mammi ta dago fuskar fatu tana mata murmushi yayinda fatun ma murmushi takeyi amma idanunta na qasa tace "wannan ba suruka bace, 'yata ce hajia kulsum" mummy ta kada kai tace "hakane hajia sadia"

Amrah tace "nice show👍"

A mosque din hospital din sukayi sallah Daga nan suka dawo suka duba jikin sultan, yana nan kwance kamar yanda suka barshi, abba ya shigo yace "ya kamata ku tafi gida tunda ance zaiyi 48hrs b4 ya farka, zan zauna dashi" mammi bata so ba haka ma fatu, dolensu suka fita. Mummy tayi drivin dinsu a motarta da suka zo ita da lubna a ciki, cikin gidan mammi suka fara sauqa suna maida zance fatu ta kule dakin amrah, basu jima ba mummy tace "hajia zan tafi gida, sai gobe insha Allah zamuje mu duba shi, ina fateema taxo mu tafi" mammi tace "to ba komai Allah ya kaimu, hajia baza ki barmini yar taki bane? Ta fada cikin barkwanci, mummy tace "na bar miki yanzu amma zanzo in dauki diyata" mammi ta kira fatu tace "mummynki tace ki dan zauna a nan, me kike buqata a kawo miki daga gida? Fatu tace "mummy kayan sakawa na" sukayi sallama ta tafi. Anan fatu taji ta wani iri, tafi sabawa da mummy kuma ita kunyan maman sultan din take, komawa tayi dakin amrah ta zuba tagumi tana tunanin mijinta koyaushe zai farka? Sa'I sa'I amrah na mata magana tana bata amsa. Bayan sallah isha farouq yayi sallama ya shigo da dan madaidaicin travelling bag ya kawowa fatu, ta karba yace "mummy tace a gaisheki" ta shafa kanshi tace "ina amsawa" bai jima ba ya koma don dare ne, yana komawa gida ya turnuqe fuska yace "mummy ni a dawo min da anty fateema na, kar ta kwana a gidansu sis amrah" mummy tace "to farouq, gobe zata dawo"

Bayan fitan farouq fatu ta musu saida safe ta shiga daki, mammi na lura da fatu tana cikin damuwa, wanda itama daurewa kawai takeyi don hakan bai taba faruwa da danta sultan ba, mammi ta kalli amrah tace "ki bar mata dakinki, ki kwana a nawa, ni zanje side din abbanku" amrah tace "to" kana mammi ta tafi.

 

Maman Fateey👯👯

[11:01AM, 8/26/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

55

 

Fatu na shiga daki ta bude jakan, phones dinta ne a sama sai kayan sawanta kala biyu da night gown, brush da undies sai dan abunda baza'a rasa ba. Wanka ta shiga ta fito, tana tunawa jiya sultan lafiyanshi kalau amma yau a gadon asibity zai kwana, 'mutum ba'a bakin komai yake ba'

Hakan ta ayyana a ranta, tasa kayanta, bayan ta gama ne amrah ta shigo ta dauki kayan baccinta ta mata saida safe, fatu ta lockin kofar ta zauna a gado ta dauki wayarta ta bude, sai yanzu ta tuno jefar dasu da tayi dazu a falo, daidai nan calling din xahra ya shigo fatu ta dauka a sanyaye tayi sallama xahra tace "fateema kin daga min hankali wallahi, kina lafiya kam? Fatu tace "lafiya" xahra tace "na dauka wani abu ya faru dake, u said yanzu zaki shiga mota, after 15mins inda yaci kin iso sai na jiki shiru, I clld ba'a dauka ba, me ya faru ne? Fatu sai lokacin abun ya dawo mata sabo ta fara hawaye tace "xahra sultan na gadon asibity, zuciyarsa saura kadan ta buga bcos of me" "innalillahi wa inna ilaihir rajiun, garin yaya? Xahra ta tambaya cikin tashin hankali. Fatu ta fada mata yanda akayi, xahra ta mata jaje sukayi sallama akan itama gobe zataje dubashi.

Budo pics din sultan tayi tana kallo a hankali hawaye kuma na wanke mata fuska, wani pic dinshi ne ta tsurawa ido, inda daga gani ba'a nan qasar ya dauka ba, yana sanye ne da suite dark blue tayi matuqar karbanshi, fuskar nan tashi kaman na baralabe don tsaban walwali da kwarjini, murmushi yakeyi wanda har hakan ya sanya idanun shi kyalli da haske, ta cigaba da kallonshi tana shafa fuskar shi ta screen din wayarta, tana ayyana irin farin cikin da zatayi in yau akace sultan dinta ya tashi. A haka bacci barawo ya saceta, karfe 1:30 ta farka dalilin alarm da ta saka ta tashi tayi alwala ta fara sallah tana mai roqon Allah ya bawa mijinta lafiya.

 

Washe gari tun asuba ta gama shirinta ta zauna tana duba agogo lokaci lokaci, qarfe 6 amrah ta shigo ta gaisheta ta dauki uniform dinta, zata fita ne fatu tace "amrah mammi ta fada miki yaushe ne zuwa asibitin? Amrah tace "ehh, wai sai kun karya" fatu tace "ok" Tana nan zaune har amrah ta gama shirin school ta tafi, karfe 7 mammi ta shigo dakin, fatu ta durqusa ta gaisheta mammi ta amsa cikin sakewar fuska, tace "ki fito mu karya sai mu tafi" fatu tace "ina azumi mammi" tace "wani irin azumi keda ko sahur bakiyi ba! Fatu tace "nasha ruwa da asuba" mammi tace "wannan azumin naki fatu baiyi ba, jiya ma haka baki ci abinci da dare ba" shiru fatu tayi kanta na qasa tana wasa da yatsunta, ganin haka yasa mammi tace "to shykenan, bari inna gama zan kiraki, ko zaki fito falo ki zauna? fatu ta kada kai alamar a'a, mammi tasa kai ta fita. Itama mammin kasa cin abincin tayi ta zuba masa ido, tunanin abba takeyi wanda shima a tsatstsaye yayi breakfast ya fita tun da sassafe ya tafi hospital, jiya ma bai dawo ba sai 11 na dare.

Ganin tana bata lokaci yasa tacewa dija tazo ta kwashe gurin, mammi kuma ta saka hijabinta ta kira fatu suka tafi hospital.

[12:54PM, 8/26/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

56

 

Suna isa suka tarar abba na cikin dakin da sultan yake shi da doctor suna magana, mammi suka zauna a chairs din kofar dakin suna jiran su abba. Doc dinne ya fara fita kana abba shima ya fito, fatu ta gaishe shi, ya amsa da sakewar fuska, ya dubi mammi yace "zaku iya shiga ku ganshi, amma ba'a son yawan surutu" mammi tace "ya jikin nashi? Abba yace "to da sauqi dai, likita yace jinin shi ya sauka yanzu, zai iya farkawa any moment from now" Mammi tayi hamdala abba yace "zan leqa office akwai meeting da muke dashi" mammi tace "Allah ya kiyaye" yace "Ameen" ya fita. Shiga dakin sukayi kowannensu jiki a sanyaye, fatu tsayawa tayi a bakin kofa tana kallonshi cikin tausayawa, mammi kuma ta isa gurin shi ta masa addu'a kana ta fita daga dakin, aka bar fatu da sultan su kadai.

A hankali ta isa gurinshi, ta jawo kujera ta zauna daidai fuskar shi, hannunshi ta riqo ta kawo dai dai bakinta tayi kissing dinshi hawayen da ya taru a idonta ya samu damar gangarowa a fuskarta har kan hannun sultan, rungume hannun tayi tana kallon fuskarshi, a hankali ta fara shafa kwantaccen gashin kanshi fuskarta bai daina zubar hawayen ba, magana ta fara a hankali kamar mai rada tace "ka tashi gani nan kusa dakai JANNAH nah, ka tashi ga fatunka da kake nema, ka tashi baby nah, kaji? Wake up" kuka ne ya kwace mata tayi mai isar ta tana kallon sultan wanda har yanzu yana nan kwance bai motsa ba, dora kanta tayi a gefen gadon kusa da kirjinsa, hannunshi na cikin nata ta riqe gamm! Jefi jefi tana daga kai tana kallonshi ko ya farka. A haka su mummy suka zo suka sameta, ta gaishe da mummy tace "fateema ya mai jiki? Fatu tace "da sauqi mummy" tace "Allah ya qara sauqi" bayan fitan mummy ne jameel da lubna suka shigo wanda da alama sun shirya, suma suka mata ya mai jiki suka fita, dangi da abokan arziki sai zuwa dubiya sukeyi amma ganin ana yawan shiga da fice yasa likita yace a daina shiga, mai son ganinshi ya leqa window, kowa ya leqa sai yaga fatu zaune kusa dashi, suna mamakin wacece ita, marasa hakuri sukanyi tambaya sai mammi tace 'yar uwace, ba daman yawan tambaye tambaye haka suke tafiya da dunbin questions a kansu. Dai dai azahar likita ya shigo yace "bai farfado ba? Fatu tace "ehh" ya qarasa shigowa ya duba shi ya

Bude idon sultan ya rufe yace "ya kamata ya farka yanzu" ya dubi fatu yace "ke qanwarshi ce? Fatu tace "ehh" yace "make sure kun kirani idan ya farka, kin gane? Tace "yeah ok" ya fita, Tana nan zaune abba ya shigo ya duba shi yace "ki fito ku tafi, anjima da yamma sai ku dawo" fatu na jin haka tasa kuka harda sheshsheka, abba yace "ki zauna to, shykenan? Ta daga kai ya fice yana murmushi. Daukan su mammi yayi suka koma gida akan sai yamma zasu dawo, aka bar fatu ita kadai. Bayan da idar da sallah ne ta daga hannunta sama tana addu'a, sultan ya fara motsa yatsun shi, a hankali a hankali komai yake dawo mishi kamar a flash yayinda yake qoqarin bude idonshi, haske ya gani yayi saurin rufewa, ya qara budewa ya rufe, a haka har ya saba da hasken, a hankali ya juya kanshi gefen da yake jin motsi, wata ya gani zaune akan sallaya tana addu'a, fuskarta hawaye na bin wasu, ganinta yayi kamar fateema amma lokaci daya yaga kamanninta kamar na wata.....kamar a flash ya tuno kamannin  fatu, da sauri ya runtse idonshi idonshi ya fara recalling........ "Kinyi makaranta? Tace "ehh" yace "a ina kika tsaya? Tace "secondary" yace "shekarunki nawa? Tace "17" yana tunawa dai dai nan ya kalleta 4 d first time, kallon na kan sallayan yayi yaga ta shafa addu'an kanta na qasa tana kuka a hankali, ya tuno fatu wacce ita ma a lokaci kuka take son hadiyewa, yayi saurin kai kallonshi kanta yana tuna fatu tanada wani jijiya a tsakiyar goshinta, wannan din ma hakane tana dashi, kallonta ya cigaba dayi yana ganin fuskar fatu, fuskar fateema a fuskar wacce take kan sallayan nan!! Wacece ita??? Dago hannunshi yayi wanda aka saka mashi drip hakan yasa qarfen da aka dora drip din yayi qara, fatu da take kuka ta dago kanta da sauri, lokaci daya kuma ta miqe kamar wacce aka tsikara, nan da nan fuskarta ta washe da murmushi yayinda idanunta na tsiyayan hawayen farin ciki, ta nufo gurinshi ta kamo hannunshi yace *"FATUUUUUHHH"*

 

Maman Fateey👯👯

[8:28AM, 8/27/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

57

 

"Shhh" tace dashi, "ba inda yake maka ciwo? Ido ya tsura mata, tuno da cewa doctor yace a kirasa yasa ta fita da sauri, shi tsoro ma ta bashi, wacece ita? Shin an samu fatu? To ina su mammi? Tukunna ma waya kawoshi nan?? Qoqarin tashi ya farayi daidai nan aka bude kofa, fatu ne da doctor sai nurse tana riqe da kayan aiki, fatu tazo gefenshi ta tsaya doc ya mishi gwaje gwaje yace "can u talk? Sultan yaqi ya kulashi, ya qara cewa "me kake ji a jikinka? Nan ma shiru yayi, Fatu tace "baby kayi magana kaji? Sai yanzu ya qare mata kallo ya gane muryanta, ya fara qoqarin tashi da sauri ta taimaka mishi ya tashi zaune, kallonta yayi yace "fateema what ar u doing here? Tace "ka amsa tambayar likita tukun" ya maida dubansa kan doctor yace "just headache sai jikina da yake ciwo" doc yayi 'yan rubuce rubuce yace "ki bashi abinci in yaci a bashi magungunan shi, nurse ki basu sai ki fada musu yanda zai sha" tace "ok doctor" ya fita, nurse ta gwadawa fatu yanda zata bashi itama ta fita. Fatu tace ka sauqo kaje kayi brush sai kaci abinci, yace "baki bani amsa ba" tayi murmushi ta cire hijabinta ta ninke, dogon rigan atamfa ne a jikinta wanda daga sama ya kamata, ta qasa kuma ya dan budu, babu make up ko kadan a fuskarta, ta isa gurinshi da murmushinta ta jawo kafafunshi tace "nazo jinyar ka ne, ka sauqo in raka ka bandaki" ba musu ya sauqo yana mamakin meyasa su mammi suka bari fateema na jinyarsa alhali sun san cewa ba muharraman sa bane. Ya shiga bandaki ta tsaya daga kofa yace "ki shigo mana" da sauri ta juya shi kuma yayi murmushi ya rufe kofar, yayi wanka yayi brush ya leqo yace "akwai kaya ne? Tace ehh ta miqo masa t-shirt white da dogon jeans baqi, ya karba ya saka sannan ya fito, jiri jiri yake ji hakan yasa ya nufi gado da sauri ya zauna. Fatu da take nazarinsa tace "jiri kake ji ko? Yace "ehh" tace "rashin qarfin jiki ne gashi kuma akwai yunwa tattare dakai" kada mata kai yayi ta miqe tana zuba mishi abinci, gwaten dankali wanda yaji kayan lambu da kifi, sai kunun gyadan cous cous mai madara ta tsiyaya masa a cup, ta nufo gurinshi, gaba daya shi tunani yakeyi tana isowa yace "kinada waya a hanunki" tace "ehh, akwai" yace "dan bani inyi kira" ta miqa mishi, numbern abba yayi dialing ya dauka yace "Assalamu alaikum abba, sultan ne" abba yana zaune ya miqe  tsaye yace "sultan ka tashi? Baka jin komai ko? Ya jikin naka? Yace "da sauqi Alhamdulillah, an samu fatu abba? "An samu fatu ka kwantar da hankalinka, amm fateema bata fada maka bane? Sultan da mamaki ya kamashi kan a ina abba ya san fateema, kuma me hadinta da fatu? Yace "abba me zata fada min? Nan fatu ta mai alama daya miqa mata wayan, yayi kamar ya hanata amma sai ya miqa mata yaga iya gudun ruwanta, sallama tayi tace "abba yanzu ya farka, yanzu zai ci abinci yasha magani" abba yace "to ki saka yaci abinci kinji, yanzu muna zuwa" tace "to abba, Allah ya kawoku lafiya" sukayi sallama.

Sultan da yake binta da kallo yace "fateema Can you tell me whats going on here?

 

Maman Fateey👯👯

[8:43AM, 8/27/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

58

 

Tashi yayi yana cewa "zan tafi gida...." jiri ne ya debeshi kanshi na juyawa da sauri fatu ta zaunar dashi akan gadon fuskarta dauke da damuwa tace "pls kaci abinci kasha magani, nd I promise zan fada maka duk abunda kake buqata"

Shiru yayi can yace "ok, qarfe nawa yanzu? Ta duba phone dinta tace "2:01pm" yace " Ya kamata inyi sallahn azahar" fatu tayi daria tace "dear salloli da yawa akanka, azahar, asr, maghrib, isha, asuba, azahar" yace "ban gane ba" kallonshi tayi ta debo abinci a spoon ta kawo dai dai bakinshi tace "tun jiya kake kwance baby" bude bakinshi yayi ta saka mishi, a haka yaci abincin sosai tana masa hiran barkwanci, tuni ya manta damuwarsa harda daria, yasha kunun sosai da yake yana son kunu, bayan ya gama cin abuncinne yasha magani ya tashi tsaye,  yaji baya jin ciwon kan, gashi jiri jirin ma babu, kallon fatu yayi wacce take saka magungunan cikin leda, yaji kaman ya jawota jikinshi (ehhh lallai ka qoshi🤔) yana nan tsaye har ta gama ta dauki used plate da cup din ta saka a basket, ta dauki hijabinta ta saka, juyowan da zatayi ta ganshi tsaye, tace "har ka fito? Murmushi yayi yace "ban ma shiga ba" tace "kana jin jirin ne har yanzu? Yace "a'a" dai dai nan abba, mammi da jameel suka shigo, ganin dansu tsaye yana murmushi kamar ba wanda ya tashi daga gadon rashin lafiyaba ya saka su farin ciki, mammi harda dan guntun hawayenta, jameel ya isa gurin sultan ya rungume shi yace "wellcome back dude, fatu ta wahalar mun da kai, amma naga alama she's taking good care of you" sultan yace "ban gane ba" abba yazo ya dafa kafadan shi yace "ya kake jin jikin naka? Yace "da sauqi abba" mammi tace "baka jin komai ko? Kaci abinci? Yace "bana jin komai, naci abinci" abba yace "bari inyi magana da doctor" ya fita daga room din, jameel da mammi suka samu guri suka zauna sultan ya shige bandaki, fatu kuma ta fara kimtsa musu kayansu, sultan ya dade a bandakin yana tunanin maganan abba da sultan ...abba "an samu fatu... fateema bata fada maka bane?  .....jameel "fatu ta wahalar mun da kai, amma naga alama shes taking good care of you" ya dafa kan sink din bandakin maganansu na mishi yawo akai, to Yaushe fatu tazo har tayi jinyar shi? Ganin yana bata lokaci yasa yayi alwala ya fito a ranshi yana cewa tunda dai an sameta shykenan, wani farin ciki ne ya lullube shi

daya tuno da fatun shi yana ayyana irin kyakkyawan qaunar da zai gwada mata. Ganin ba mammi da abba a room din yasa sultan yace "jameel abban bai dawo bane? Jameel da yake danne danne da waya yace "sun tafi gida, zamu tarad dasu a can, an sallameka" sultan ya maida dubanshi kan fatu wacce ta dale kan gadon nashi itama tana danne dannen phone dinta, yace "fateema ina sallaya? Ta shimfida mishi ya fara rama sallolin da ake binshi fatu da jameel na jiranshi ya gama su tafi gida.

 

Maman Fateey👯👯

[11:02AM, 8/30/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

59

 

Yana gama sallolin aka kira asr, jameel yace "mu tafi mosque mubi jam'I" hakan kuwa akayi, sultan a hanyar fitansu yaga fateema sai masa magana takeyi a ranshi yace 'kodai na bata tausayi ne yasa ta ajiye kishinta a gefe? A mota suka barta suka shige mosque din asibitin, a lokacin fatu ta fara tunanin ya zata fara fadawa sultan cewa itace fatu!! Duk irin abubuwan da takeyi daurewa kawai takeyi don zuciyarta har yanzu yana bugawa da sauri idan ta tuno kalan draman da zasu kwashe ita da sultan, ta rafka tagumi, wayarta ya fara qara, xahra ce "sai yanzu zaki kirani? Cewar fatu, xahra tace "tunda safe naso inzo, kakana ne ba lafiya muka kaishi hospital shima, kuna wani ward ne? Fatu tace "ayyah Allah ya bashi lafiya, ai an sallame mu" xahra tace "what? Gani nan fa cikin asibitin! Fatu tace "don Allah? Kizo parkin space 'B' ina gurin a motar ya jameel, bamu tafi ba, sun shiga sallah ne" xahra ta iso a motarta fatu ta fito sukayi huggin juna, xahra tace "ya? Kin fada mishi komai? Fatu tace "not yet, ban samu chance ba" xahra tace "ki fada mishi da kanki don zaifi jin zafi in wani ne ya fada mishi" Fatu tace "hakane, bazan bari wani ya fara fada masa ba" dai dai nan sultan da jameel suka iso fuskar sultan kamar wanda aka aikowa saqon mutuwa, ya hade giran sama da qasa, fuskar sa sai da tayi wani jaa, ya shiga mota next to driver, ganin yanayinsa yasa fatu da xahra suka sha jinin jikinsu, tabbas jameel ya labarta masa, fatu ma tayi sauri ta shiga baya jikinta har rawa yakeyi, xahra da jameel suka gaisa, ta leqo ta window tace wa sultan "ya jiki" yayi yaqe yace "da sauqi, nagode" itama ta nufi motar ta bayan tayi wa fatu kallon tausayi. A hanya babu wanda yayi magana, sautin qira'ar da jameel ya sanya kawai ke tashi a motar, jameel yace "daa baka kulashi ba wallahi, irinsu ne masu tayar da hatsaniya" ya cigaba da cewa "fateema angonki akwai zuciya, an idar da sallah ana fita sultan ya dan bugi wani saurayi bai sani ba, shine saurayin ya hayayyaqo mishi harda barazanan wai zai kulle sultan, to shine gogan naki yaso ya nuna qarfinsa mutane suka shiga tsakanin su" sultan yayi tsaki yace "to fadi ba'a tambayeka ba, parrot, jameel ka koyi surutu wallahi" jameel yayi murmushi ya shafa kanshi yace "zama da madaukin kanwa......" anan suka iso gida, fatu ta sultan suka fito jameel yace "ka huta gajiya, zan zo anjima da dare" ya kalli fatu yace "amarya a kula min da abokina" maigadi ya bude masa gate ya fita. Qaramin basket din hannun fatu wanda suka dawo dashi daga asibiti sultan ya karba yace "kawo in tayaki" ya fara tafiya, tace "ina son magana da kai" ya tsaya yace "mu shiga gida to" tace "noo, anan nake so muyi" ya kalleta a diririce yace "fateema hope ba'a kan matata fatu bane, please ki janye wancan maganan" ta kalle shi da idanunta da suka fara tara hawaye tace "ba shi bane" yace "ina jinki ki fada min" shi ya qagu ya shiga gida ya tarar da fatunshi, ya tambayi jameel ya fada mishi inda aka samu fatunshi da yanda aka sameta amma jameel yaqi sanar dashi, wai fateema ce zata fada mishi, whats so special in fateema ta fada mishi? Anyway tunda ance fatun shi lafiyanta kalau, nd babu abunda ya sameta he can wait fateema ta gama maganarta. Kallonta yayi yace "ina jinki" shiru tayi kanta na qasa, yayinda hawaye ke bin kuncinta tace "NICE FATU"

 

Maman Fateey👯👯

[10:05PM, 8/30/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

60

 

Kallonta yayi yace "fateema please banda joke a wannan time din" Ta dago idanta tace "ba joke bane, gaskia nake fada maka" sultan ya gyara tsayuwarshi yace "ina fatun? Tace "I said nice fatu, nice matarka, na fito nemanka mummy na hadu da mummy" kan sultan ya dau zafi yana kallonta kamar wacce take masa tatsuniya, wani lokacin tana masa dan kama da fatu especially in tana kuka. yace "ban gane ba, ban fahimceki ba, shin rikida kikeyi from fatu to fateema ko me kike so ki fada min? What do you mean? Fatu tace "please muje garden, not here" yace "noo, nan din ma is ok" tace "please" yace "ok muje" a garden suka zauna akan kujerun da suka qawata gurin, ya dafa table din dake tsakaninsu yace "ina sauraronki" Fatu tace "ka min alqawari duk abunda na fada maka baza ka yi fushi ba" sultan daya qagu yaji maganan yace "ba komai, ina jinki" Fatu ta fara bashi labari tun daga zuwanshi garin modibbo har yau, tashi yayi tsaye yana nunata da yatsa jikinshi har rawa yake yi yace "a hakan ne kike sona? Ko kunyar fada bakya yi? Kinada tausayi kuwa? Ya harde hannayensa a qirjinsa yana tsaye a kanta, ranshi a bace, fatu ta miqe tsaye itama ta share hawayen fuskarta ta turo baki tace "ai bani kadai bace mara tausayin, kuma naga abunda kamini na rama" ta murguda baki ita ala dole ta masa masifa. Taci gaba da magana wanda ita a ganinta masifa takeyi, shi dai ya tsaya yana kallonta bacin ran da yake ji zuciyarsa yana raguwa a hankali, Yanda take maganan tana juya idanu ya mishi kyau har baisan lokacin da ya saki murmushi ba, ita kuma kallon gefe tayi ta riqe qugu tana wani girgiza, sauke hannayensa yayi tareda yin nannauyan ajiyar zuciya yace "naji na miki laifi amma bai kamata kimin horo da wannan hanyar ba, kina gani fa yanda na rikice amma ko a jikinki" ta kalleshi taga yana murmushi, a ranta tace 'bari muja ajii' ta qara hade fuska tace "kaima haka kamin, bayan an sanar da kai halinda nake ciki amma hakan bai sa ka tausaya min ba" ta qara murguda baki, ya ciji lips dinsa Yace "wa kike murgudawa  baki? Kallonshi tayi taga ita yake kallo ta kawar da kanta tace "ni ba da kai nakeyi ba" ta qara murguda baki, qoqarin zagayawa gurinta ya fara yi, ita kuma ganin haka yasa ta matsa, Suka fara zagaye table din, shi burinshi ya kamata ko rankwashi ya mata na wahalar dashi da tayi, ita kuma taqi hakan ya faru, ganin yana qoqarin kamata yasa ta kwasa da gudu cikin gida, tsayawa yayi yana kallon yanda take gudun kamar wata small girl, murmushi yayi ya kalli gabas yayi SUJUD SHUKR yayiwa Allah godia da ya bayyana masa fatu ta inda baya tsammani, a hankali ya furta "Allahu Akbar, Alhamdulillah" Ya dauki basket din yayi cikin gida.

 

Maman Fateey👯👯

[2:02PM, 9/2/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

61

 

Fatu sai data saisaita kanta kafin ta shiga falo, mammi ne kadai zaune tana jiran isowarsu, fatu ta mata sannu mammi tace "ina sultan din? Fatu tace "yana shigowa" tana rufe baki ya shigo yayinda ita kuma ta shige room din amrah,  zama yayi kusa da mammi ya riqe hannunta yace "mammina kin yafe min abunda na miki? Ta kalleshi cike da qauna tana murmushi tace "na yafe maka manga na" shima murmushin yayi yace "nagode, duk dana saba alqawari ayau burina ya cika, na samo miki fatu" tace "Alhamdulillah komai yazo da sauqi, yanzu kaje ka huta zamuyi magana anjima da dare" yace "to" mammi ta tashi ta shiga dakinta, sultan na ganin haka yayi sanda ya shiga dakin da fatu take, da alama ta shiga wanka, don ga kayanta data cire, kwafa yayi yace 'Allah ya taimakeki, zamu hadu ne' sosa kai yayi yana murmushi, wani irin farinciki yakeji mara misaltuwa, wai fateema da yake so itace fatun shi da yake nema!! Yayi tunanin ya rama wahalar dashi da tayi amma wata zuciyar ta haneshi da aikata hakan, don a dalilin rama abunda ya mata ya kwanta a asibiti. Ya fita daga room din zuwa part dinshi. Da dare bayan isha anci abinci abba ya tara familyn gaba daya a palour nshi, yace "Alhamdulillah ala kulli halin, komai ya faru ga dan adam muqaddari ne daga Allah, anan nake so naja hankalinku dukan ku cewa kar a bawa kowanne shashe laifi kan abunda ya faru, abunda ya faru ya wuce, kuma ina mai qara jawo hankalinku kan cewa ku kasance masu jin maganan iyayenku, sannan ku daina wulakanta mutum duk inda kuka ganshi, kowanne bawa da baiwar da Allah ya masa, and lastly kuji tsoron Allah, ku kiyaye hakkokin junan ku, duk wani abun da akace hakki ne rataye a wuyanku kuyi iya qoqarin ku wajen sauqe shi don saboda gujewa fushin Allah, ba tone tone ba, kai sultan tun farko daka dauki aurenka a matsayin qaddara ka kuma yi imanin cewa 'matar mutum kabarinsa' da duk wani tashin hankali bai faru ba, zaka iya cewa ai shima qaddara ne, yess qaddara ne amma anbi don zuciya, wanda son zuciya kan kai mutum ga ga halaka, Allah ya kare"  a hankali kowa yace "ameen" jikin kowannensu yayi sanyi da alama nasihar abba na shiga dai dai "sai ke fateema, duk da bakida laifi amma nasan kinyi hakan ne don ki hora shi kan abunda ya miki, shi  hakuri maganin zaman duniya ne, kar ku rama sharri da sharri, ku kasance masu aikata alkhairi ga kowanne mahaluqi, hakan zaisa ku sami babban rabo a gurin Allah, ku kasance masu yafiya wa junanku don gudun nadama nan gaba, Allah ya shige mana gaba a duk al'amuran mu" "ameen" suka qara amsawa. Anan sultan ya kalli fatu wacce kanta na qasa tun shigowanta taqi su hada ido a zuciyarshi yace 'she's now fatu' karaf idanunsu suka hadu, murmushi ya sakar mata yayinda itama ta mayar mishi da murmushin ta sunkuyar da kanta, sosai abba yayi nasiha har amrah an tabo ita kuma akan karatunta, gyaran murya abba yayi yace "sultan yaushe zaka dauki matarka?? Dumm gaban fatu ya buga, don ita duk lissafinta bata taba zaton za'ayi maganar tarewanta nan kusa ba, da sauri ta dago ta kalli sultan shima ita din yake kallo, wannan karon murmushin mugunta ya mata ya kanne mata ido daya yace ".......

 

Maman Fateey👯👯

[2:04PM, 9/2/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

62

 

Yace "abba nan da sati daya" kallonshi fatu tayi kamar zatayi kuka ya qara narka mata murmushi har hakoranshi na bayyana, abba yace "to sultan bakayi gaggawa ba? Mammi ta amshe "ehh gaskia sati daya yayi kadan, ina laifin wata daya? Sultan ya kalli mammi a natse yace "mammi har wata daya? An daure auren fa, kawai ku dauketa ku kaita shine zai dau wata daya? Haba mammi" daria abba yayi yace "kuyi shawara to, amm fateema kefa wanne kike so? Sati daya ko wata daya? Fatu ta kasa magana, ta daga ido ta kalli sultan murtuqe fuska yayi alaman ki zabi nawa, mammi kuma tace "fateema kiyi magana babu mai takura miki" fatu ta nisa tace "abba yanda mammi ta fada yafi" murmushi abba yayi sultan kuma ya bata rai, shi gaskia ba'a masa adalci ba, wata daya ai yayi yawa, mammi ko tausayin shi batayi. Abba yace "sultan sati daya yayi kadan a gama shirye shirye duk da an daura aure kasan mata akwai su da son biki, da sati da wata dayan duk daya ne, hajia sadia ku fada min duk abunda kuke buqata na hidiman da za'ayi, komai da komai" mammi tace "to Alhaji mun gode" sultan dai yana shiru don shi a ganinshi sam ba'a kyauta mishi ba, shi farko ma da cewa zaiyi a bashi matarsa su tafi yanzu tunda yana da gurin zama, amma sai yayi kulaku yace sati daya, kenan sati dayan ma a gurinsu yayi kadan, "wata daya, ina zaman jira?" ya furta a zuciyarsa amma baisan har ya fito fili ba, amrah da take kusa dashi ta tuntsire da daria harda riqe ciki, mammi tace "amrah lafiyanki kuwa? Sultan yana mata ido amma ina bata ma ganshi ba tace "wai cewa yayi 'wata daya, yana zaman jira" duka ya kai mata a baya wanda yasa ta saki kuka mammi tace "kiyi hakuri, kije ki kwanta" tashi tayi tana kukanta ta fita, mammi ta maida dubanta kan sultan wanda yanzu kam kowa yaga yanda ya hade rai tace "to sannunka da cin zali, in kayi wasa sai in qara wata biyu akan dayan, sati daya kamar auren yar tsana za'ayi? Wannan ne karo na farko da zan aurar, kuma 'yaya biyu, haka kawai in sungumi 'yata in baka ba wani biki? Kamar zaiyi magana sai ya fasa ya tashi yace "sai da safenku abba" abba yace "mu kwana lafiya, ka tabbata kasha maganinka kafin ka kwanta" yace "to" yasa kai ya fita. Fatu da tunda aka fara draman nan kanta na qasa ta dago tabi bayanshi da kallo, mammi tace "fateema kema kije ki kwanta, ki huta gajiyanki, Allah ya miki albarka" "ameen" fatu ta amsa ta musu sai da safe ta fita. A hankali take tafiya tana waige waige don bata son haduwa da sultan,

Tazo daidai bakin main falo zata shiga taji ance "fatu" waigowan da zatayi taji an fincikota tayi masauqi a kirjin mutum, tana daga ido ta kalli fuskar sultan wanda yake mata murmushi wanda daga gani murmushin mugunta ne, rufe mata baki yayi da hannunsa ya fara janta zuwa side dinsa.

 

Maman Fateey👯👯

[9:40AM, 9/3/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

63

 

Tirjewa tafara tana qoqarin cire hannunsa daga bakinta amma hakan bai samu ba don wani irin kyakkyawan riqo daya mata, ganin zata bata masa lokaci yasa ya dagata cidok har dakinsa, bai direta a ko'ina ba sai kan kujera, ya juya fatu ta bishi tana magiya yana tattareta yayi locking kofar, key din ya cilla sama ya cafe ya kashe mata ido yace "baby nah, yaya dai? Ji dan rainin hankali ta fada a ranta a fili kuma tace "don Allah ya sultan ka bude mini kofa, don Allah kar kamini komai" tsayawa yayi da karkada key din da yake yi yace "oohh kin dauka wani abu zan miki? Okey wato har kinsan abunda ake yi? Ya qarisa yana daga mata gira, sunkuyar da kai tayi cikin jin kunya ta fara wasa da yatsunta, kallonta yakeyi kamar zai cinyeta, yace "don mugunta ina kika bi shawaran mammi? Shiru tayi yace "answer me" tace "nifa ba haka bane" yace "to mene? Tace "dama ina son zuwa garin modibbo ne" yace "okey, don kina son zuwa garin modibbo shine zai sa ki qi tarewa a gidan mijinki? Shin nace miki baza kije bane ko mene? Shiru tayi yace "da alama yau zaki kwana anan, da nayi niyyan barinki amma shirunki zai sa ki kwana mini" ta dago da kai tace "don Allah...a'a.... to kayi hakuri" matsowa yayi kusa da ita, taja baya, kyakkyawan runguma ya mata sannan ya ajiye nannauyan ajiyan zuciya, batayi qoqarin kwatar kanta ba saboda yanda jijiyoyin jikinta suka mutu lakasss! Sai da suka kusan minti uku a haka sannan ya saketa ya bata key yace "sai da safe" ba musu karba ta bude kofan jiki a sanyaye ta fita ta mayar da kofan ta rufe, wani irin sanyi ne ya bugeta wanda har tsikar jikinta sai da suka tashi, ta kankame jikinta ta fara tafiya, a ranta tace 'anya bazan koma ba? Irin wannan sanyi' murmushi tayi tunowa da cewa ko giyan wake tasha bazata kai kafarta gurinshi ba. A haka ta iso part dinsu ta rufe kofa bayan ta shiga, ta wuce dakin da take kwana.

Sultan kuma da kyar ya saita kanshi ya samu salama, amma tunanin fateema kawai yakeyi, da kyar bacci ya debe shi cike da dreaming dinta.

 

Shirye shirye aka fara tun

washe garin ranar, events 5 mammi ta lissafawa abba wanda za'ayi yace ta rage bidi'an yayi yawa, daga baya aka maida shi 3. Bayan kwana 4 sultan, fateema da mammi suka je garin modibbo, kaka ya rasa inda zaisa kanshi don dadi, koda aka ce masa ga fatu da farko kasa gaskatawa yayi, fatu harda guntun hawayenta ta rungumi kakanta, su goggo asabe suka zubar da makamai don ganin fatu ta musu nisa, dolenta ta dawo ta nan nan dasu, ganin haka yayiwa fatu dadi ta godewa Allah, kawu muntari ma yayi murna inda ya aika aka siyo musu fura da nono mai dadin gaske aka kuma yanka kaji biyu aka musu miya, bayan azahar naga mammi da kaka zaune a cikin zaure, mammi ta kwashe duk abunda ya faru ta sanar dashi tace "daa nace ko baza a sanar daku ba sai abban sultan yace lallai a fada muku kar ranku ya baci kuma kusa shakku a zuciyanku idan magana ta fito waje, nasan 'dana yayi kuskure amma yayi nadama, ina mai baka hakuri a matsayina na mahaifiyarsa" kaka yayi shiru a cikin ranshi baiji dadin abunda ya faru ba, ashe shiyasa ranar da sukazo sultan ya rikice don sanin bata tare dasu? Biri yayi kama da mutum, tun ranar zuciyarsa take raya mishi abubuwa daban daban, in bai manta ba yau sati kenan da faruwan al'amarin. Yace "babu komai hajia, yanzu kam ya zama tarihi" mammi taji dadin yanda bai tsawaita maganan ba ta sako musu hiran bikin fatu da take shirin yi, nan da nan fuskar kaka ta washe yana murmushi yace "diyar ku ce, sai yanda kukayi, fatanmu Allah ya hada kansu ya basu zaman lafiya" sultan da fatu sun tafi gona inda yake ganin yanda ake shuka domin damina ta fara, Basu jima ba suka dawo dalilin kiran da mammi ta musu kan su dawo su tafi gida, tsaraba sosai kaka ya tara musu, goggo asabe ma harda garin kuka, daddawa da man shanu, mammi bata barsu ba sai da ta cikawa kowa aljihunsa ta kuma roqi alfarman cewa idan lokacin biki yayi suzo, kaka yace insha Allah za'a zo. Fatu bata so tafiya ba amma haka suka tafi tana mai kewan su kaka, a wajen fita daga gari ne suka hadu da hafizu dan ladan da alama daga gona yake, fatu tace "ga hafizu" qasa qasa yanda sultan zaiji, yace "waye shi? Tayi murmushi tace "kaka bai baka labarinshi bane? Sai a sannan sultan ya tuno ya murtuqe fuska yace "shine kike kallonshi kina murmushi ko? Tayi tsit, don yanzu tana tankawa qari zai zama kababa. A yanda ta lura dashi yana da kishi sosai Murmushi tayi tace "sorry" daga nan kuma ta dauko musu wani hiran, mammi dai tana baya ko ta kula su, hasalima waya takeyi da wata qawarta yar borno wacce zata hadawa fatu humra, kulacca dasu turaren wuta. Woo mammi🤓. A haka har suka iso gida.

 

Maman Fateey👯👯

[11:56AM, 9/3/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

64

 

Fatu ta koma gidan mummy da zama, mammi ta lura da yanda sultan ya takura mata, hakan ba qaramin dadi yayiwa fatu ba domin in har ta bari suka zauna su kadai to sai yasan yanda zaiyi ya sata kuka da irin abunda yake mata. Shi kuma baiji dadi ba amma ya nuna musu ko a jikinshi, qarshe ma tafiya yayi dubai kan cewa shi zai hado kayan lefe da kayan daki, mummy ta mammi suka rubuta masa duk abunda suke buqata. A ranar da zai tafi ya shigo gidan mummy, a falo ya tarar da mummy tana zaune, ya gaisheta tace "sai tafiya ko? Yace "ehh" tace "fateema tana kitchen, ka shiga kuyi sallama" kamar bazai shiga ba amma yayi missing dinta, a kitchen ya sameta ita da dija suna aiki, dija ta gaishe shi ta fice daga kitchen din, fatu ta gaishe shi tace "ya na ganka haka? Yace "kamar ya? Tace "kamar bakada lafiya" ya shafa sajensa yace "lafiyana kalau, zanyi tafiya ne" zare ido tayi ta matso kusa dashi tace "yaushe? Ina zaka je? Murmushi yayi ganin reaction dinta alaman bata so ba, yace "yau, dubai daga nan in wuce china, sai ana saura kwana biyu biki zan dawo" fatu da idanunta suka fara tara kwalla tace "don na dawo nan shiyasa zakayi nesa dani ko? To zan koma gidan mammi, kaji? "A,a kiyi zamanki, dama kema bakya son ganina, kuma ina takura miki, so kinga inna tafi zaki fi sakewa ayi shagalin biki dake" girgiza kai tayi tace "ni baka takura min ba, don Allah ka zauna, kayi hakuri, bazan iya jure rashin ganinka ba har tsawon kwanakin nan, ban saba da rashinka ba" tausayi ta bashi sosai, amma shima abun tausayawan ne, kuka ta fara ya jawota jikinshi ya rungume ta yana bubbuga bayanta "its ok dear, nima ba'a son raina zan tafi ba, 10 days zanyi kawai in dawo, u happy? Girgiza kai tayi tace "shima yayi yawa" ya dago da kanta ya share mata hawaye yace "kamar yau ne zakiga 10dys din yayi" wayarshi ce ta fara qara ya dauka jameel yace "ina jiranka a waje, kar kayi missin flight naka" yace "ok ganin nan fitowa" jin haka yasa fatu tara wani kwallan ya kalleta yace "in tafi? Tayi shiru, peck ya bata a kumatu yayi ficewarsa don shima daurewa kawai yakeyi, mahmud ya samu a palour, mummy kuma da alama ta shige dakinta, ya tsaya suka gaisa, mahmud ya hango fatu a bakin kitchen tana kuka yace "dukanta kayi ne sultan" sultan ya juyo ya kalleta yace "wai don zanyi tafiya ne, dadi ne ya mata yawa" mahmud ya kwashe da daria yace "dan tsaya don Allah" .....'ashe sabo yana da dadi, amma in za'ai rabo da zafi'..... waqan 'sai wata rana' ya saka musu, sultan yaja tsaki ya fita daga falon, fatu kuma ta fito tayi hanyar dakinta tana matsar kwalla, mahmud sai kwasar daria yakeyi, dai dai nan mummy ta fito tace "me haka mahmud? Ya tsagaita darianshi yace "sultan zaiyi tafiya shine 'yar kauyen nan take ta kuka" mummy ta bata fuska tace "kai kuma qaton banza shine kake mata daria? A haka wai kai yayanta ne? Shiru yayi fatu kuma tasa daria mummy tace "sannu mai kuka da daria" fatu ta haura sama tana murmushi. Sultan ya sauqa lafiya, kai tsaye ya wuce hotel din da yake zama, fatu ya fara kira yace mata ya iso, ta mishi barka da hanya. Yana wanka ya fita zuwa gidan wani abokinshi Ahmad, balarabe ne amma yayi zaman naija, sosai yake jin hausa, matarsa Nihal ta kawo wa sultan abinci ya zauna yaci anan yake bashi labarin aurenshi. Ahmad ya masa murna, sultan yace "ina gayyatarku kaida madam ku tayani sayayya" ahmad yace "karka damu, a shirye muke" daga nan suka dunguma zuwa kasuwan deirah dubai, matar ahmad nihal ita tayita zaban kayan lefe su sultan na tayata, gurin kayan bacci sultan yace "ni zan zabi wannan kam" daria suka mishi ya fara kwasa, a gajiye likis suka dawo gida, shi kuma ya wuce hotel din daya kama.

 

Maman Fateey👯👯

[1:18PM, 9/7/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

65

 

Washe garima haka suka fita, sukayi ta siyayya, sultan na duba list din su mammi, a ranar suka gama hada lefe, akwatuna 12, kowanne shaqe da kaya na gani na fada, Wani set din sarqa, dan kunne, rings da bracelet na gold ya siya mata, wanda fadin tsadarsa ma bata lokaci ne, Shoes nd bags designers, kayan cosmetics gasu nan birjik, undies, dogayen riguna kala kala, kai zan muku video kawai kowa ya gani😜.

Kwanan shi uku a Dubai ya gama siyayyar da zaiyi har da furnitures da kayan kitchen, a rana ta hudu ne ya tura kayan nigeria shi kuma ya wuce china business trip dinshi. Yau saura sati biyu a fara shagalin biki, amarya fatu ta fara shan gyara, takanas qawar mammi yar borno ta aiko matar da zata yiwa fatu dilka da turaren jiki, mummy ta hado "SINADARAI"😉 ingantattu marasa illah. Sultan kuma waya kan waya suke da fatu, don wani irin qaunarta da yake fisgar sa har yakan ji kamar wani zai kwace masa ita. Ita din ma hakan ne, wani zazzafan sonshi take ji a zuciyarta, gashi tayi missing dinshi sosai.

Dangi yan uwa na kusa har sun fara zuwa, mammi ta fadawa dangi an samu fatu, wato dangin mahaifiyarta, murna a gurinsu ba'a cewa komai, kowa yana marmarin yazo yaga fateema nan da mammi take nema. Akwai wata qanwar kakar fatu wacce take kaman uwa a gurin mammi, don itama tasha neman addarta wato maman rahmatu mahaifiyar fatu, ana kiranta inna habiba, tana ganin fatu ta fashe da kuka wai taga yayarta zainabu, kowa ya ganta sai yayi mamaki don kamanni da takeyi da kakarta sosai, duk da basu san rahmatu ba sunyi kewarta a  matsayinta na yar uwarsu, fatu taga dangi, tayi murna ta kuma godewa Allah da ya nuna mata dangin mahaifiyarta masu sonta. Ranar sunday ana saura sati biki, ana yiwa fatu dilka tana wani tutturo baki wai ta gaji da murje murjen nan, salma  cousin din sultan tayi daria tace "murje murje ko? Wannan kadan kika gani" xahra da bizzy (itama cousin din su sultan ne, duk sa'anni suke da fatu) suka fashe da daria, fatu da bata san inda maganan su ya dosa ba tace "ohh nan gaba murjewan zaifi haka? Bizzy tace "sosai ma, kuma wanda za'a miki nan gaba in bakida dauria har kuka zakiyi" suka qara fashewa da daria, fatu tayi shiru tana kallonsu one by one, jikinta yayi matuqar sanyi  tace "baku da kunya" falmata matar da take yiwa fatu dilke wacce bazata wuce 28yrs ba tace "rabu dasu fateema, suma suna hanya ai, ba'a yiwa motar gawa daria" murmushi fatu tayi kawai su salma kuma suka ci gaba da yiwa fatu tsiya falmata na kare ta. Maman dota ne ta shigo dakin tace "wai har yanzu baku gama ba? Kusan azahar, xahra ba kunce zaku je rabon Iv ba? Xahra da take shafe shafe da mirrow a hannunta tace "zamuje, amma sai anjima da yamma" maman dota tace "to shykenan bari a kawo muku abincin ku" tasa kai ta fita, salma tace "haba bizzy ki shafa a hankali mana, zaki sa mu rasa ai, irin wannan makkalawan da kikeyi" bizzy kota kulata ta cigaba da shafawa, salma ta kwace robar dilkan taje bakin kofa ta tsaya, itama tana shafawa, bizzy tace "ai wallahi baki isa ba, ban shafa a wuyana ba fa" zagaye dakin suka fara su xahra na musu daria, da yake dakin babba ne, takanas mammi tasa aka gyara wai wajen gyaran amarya, carpet ne shimfide a dakin sai katifa guda daya da kujeru one one sitter biyu, sai da suka gaji suka zauna suna shafawa tsakani da Allah.

Bayan dilkan ya bushe falmata ta shiga bathroom din dakin don hadawa fatu ruwan wanka wanda shima yasha hadin turarukan wanka masu dadin qamshi, anan fatu tace kallesu tace "nifa banga amfanin shafe shafenkun nan ba, ni kunga mijina nake yiwa, kufa? Harara suka watsa mata, bizzy da aka fi jin muryanta saboda surutu baya mata wahala tace "aikin banza, idan yazo yabon kwalliyan naki mummurje ki zaiyi" suka kwashe da daria da yake sun san bata son kalman "murjewa' Itama daria tayi alamar ko a jikinta tace "wa yaga taliyar hausa ta murji" anan falmata ta fito tace "fateema ki shiga wanka, bari in je in debo garwashin yin turare" ta fita, fatu ta shige bathroom tana kada musu duwawu, salma tace "hhh yarinya zaki gane" bayan ta fito tayi sallah aka mata turaren jiki, Ta saka wani maroon  doguwar riga cotton mai guntun hannu, fatarta ta qara haske, santsi da taushi, jikinta na fitar da wani daddadan qamshi mai sanyi, tayi wani fresh da ita, cream dinta mai hade da kulacca ta shafa a jikinta,  ta murza farar powder ta saka lip balm, da yake ance ta daina kwalliya mai yawa, abinci suka fara ci suna hiransu duk akan yanda bikin zai kasance, suna tsakar ci wayar fatu ta fara ringing ta dauka, sunan sultan ne akan screen din, ta daga ta kashe murya tace "Jannah" gyara zamanshi yayi a kan kujeran da yake yana murmushi yace "Habibteey ya kike" ta rausayar da ido kaman yana gabanta tace "lafiya lau" su salma suka sa ihu har bizzy na kwarewa, yace "su waye haka? Ta kalli su xahra da suke dukan bayan bizzy wacce ta kware suna dura mata ruwa, tace "yara ne suke wasa" hararan da suke watsa mata ne yasa ta juya musu baya taci gaba da wayanta, sultan yace "please kije dakina akan gado zakiga wasu papers a cikin envelope ki bawa mammi" tace "dakin naka a bude ne? Yace "ehh a bude ne" tace "ok" ya kashe wayan ta miqe ta dauki gyalen rigar ta fita zuwa shashen sultan.

 

Maman Fateey👯👯

[10:02PM, 9/7/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

66

 

A hankali ta murda handle din dakin ta shiga da sallamanta duk da tasan babu kowa a ciki, qaramin palourn nashi tsaf tsaf kamar baiyi tafiya ba, ta bude kofar dakin ma tayi sallama tareda kutsa kai ciki, ganin duhu a dakin yasa ta fara lalube gashi bata san inda switch din yake ba, kafarta ne ya bugi gado, ta daga kafar ta riqe tana wayyo Allah na. Tuno da cewa tana da waya hannunta yasa ta kunna light din wayar ta duba qafarta gurin har yayi jaa, ta shafa gurin ta ajiye kafar ta haska dakin, dummm gabanta ya fadi ganin mutum kwance a kan gadon yana kallon ceiling, tare fuskarsa yayi yace 'kina haska min ido" fatu ta kasa motsi don tayi matuqar razana lallai yau tayi gamo da aljani a dakin sultan. Ganin ya tashi yana qoqarin zuwa gurinta ne yasa ta fasa ihu tace "wayyo mammi....na shiga uku" tayi hanyar qofa da gudu har tana jefar da wayarta, nan da nan hasken dakin ya mutu sakamakon mutuwar wayarta da yasha qasa, addu'a takeyi tana kokawa da kofar yayinda kuma tana juyawa tana ganin inda aljanin yake, ji tayi an tuntsire da daria hade da kunna hasken dakin, Balloons pink nd white ta gani ko ina, an qawata dakin dasu, can kuma gefe cake ne madaidaici an rubuta 'fateema is 19' ta dawo da kallonta kan sultan wanda ta tabbatar ba aljani bane tace "jannah" qarisowa yayi gurinta yana murmushi ya kamo hannunta har gurin cake din, kallon mamaki take binshi dashi yayinda tana gani ya dauko lighter ya kunna 3 candles din da suke kan cake din ya juyo gurinta yace "bismillah" a raina nace Karfa ta kashe candle din da ruwa😂, itama murmushine a fuskarta tace "with u dear" Rage tsayi sukayi a tare suka ce one...two....huuuuuhhh suka hure candle din wutan ya mutu, Yana clapping itama tanayi harda guntun tsallenta, a tare suka yanka cake din yana "happy birthday to you, happy birthday to you" ya bata a baki itama ta bashi, sai a sannan suka zauna a bakin gado yace "washhh na gaji" ta juyo tana kallonshi tana cin cake tace "amma guy din nan ka tsorita ni wallahi, tukunna ma yaushe ka dawo? Ba sanarwa haka" Kallonta yakeyi yaga ta qara masa kyau tayi wani bul bul da ita, yace "kinyi kyau" ajiye sauran cake din hannunta tayi murmushi tace "nagode, nd thanks for everything" Murmushin shima yayi yace "u ar welcome dear, now selfie" ai kuwa ta turo baki suka dauka, na biyun kuma tayi murmushi, a haka suka yita daukan pics kala kala, sai da suka tsagaita ya dauko wani qaramin akwatin ring daga aljihunsa yace "ga gift dinki" ya bude wani hadedden zobe ne wanda daga gani na pure azurfa ne, ya saka mata a yatsanta, fatu ta murna yasa ta kasa rufe baki tace "thank u so so so much, Allah ya bar mini kai" daria yayi yace "ke daya? Tace "yesss ofcos" yace "towww" tace "amma kasan na manta cewa yaune birthday na, ya akayi ka tuna ne? Yace "dama ina tune kuma nasa reminder a phone dina, jiya a china na ga remindern, so already na gama abunda nakeyi kawai nayi bookin flight na dawo, tun safe nake gida amma abba ne kawai ya sani" Fatu da take kallonshi tana qare masa kallo don shima yayi dan haske ya mata kyau bata san sanda bakinta ya furta "kayi kyau" ya shafa sajensa yace "godia nake, amma na rame ko? Ta dan hararashi tace "me zai ramar da kai? Yace "rashinki kusa dani" kafin tayi magana ya jawo ta suka fada gado ya kashe light din dakin yace "muyi bacci"

 

Bayan su xahra sun gama cin abinci sukayi wanka, sukayi shirin fita rabon iv, anan suka shiga cikin gida sukayi yiwa mammi sallama tace "da fatan ba da fateema zaku tafi ba? Salma tace "mammi ai ta shigo cikin gida ma" mammi ta kada kai, su kuma suka fita a motar xahra bixxy na driving. Can bayan la'asar sakaliya suka dawo, a bakin gate suka hango dandazon yan biki kowa hankali a tashe wai ba'aga amarya ba!! Mammi tafi kowa rudewa sai kiran numbern fatun akeyi yaqi shiga, ta kira abba shi kuma bai dauka ba da alama yana gurin meeting, dawowansu xahra yasa aka fara tambayansu inda fatu take, anan suka ce rabonsu da ita tun suna cin abinci sultan ya kirata a waya, amma basu san meya fada mata ba ta tashi ta fita a dakin, da sauri mammi ta kira numbern sultan na china, 'is switch off' aka fada mata, ta kara kiran numbern abba shiru, anan ta kira jameel ya dauka yana gaisheta bata saurareshi ba tace "jameel ba'a ga fateema ba, ka kira sultan in kana da numbern hotel din da yake" jameel da mamaki ya kamashi yace "mammi ai sultan yana gida, yau da safe karfe 9 naje na daukoshi a airport" kafin ya karisa maganar mammi ta kashe wayan tayi hanyar part din sultan ranta a bace, ganin haka yasa kowa binta cikin kidimewa kan me yake faruwa????

 

 

Yanzu labari ya fara😜

 

 

Maman Fateey👯👯

[2:07PM, 9/8/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

67

A bakin falon mammi ta tsaya tana knocking, shiru shiru ba'a bude ba yasa ta bude door din ta shiga, a ranta tana ayyana irin bacin ranta da zata nunawa sultan, ganin ba kowa a falon yasa ta tabbatar lalle suna daki, kasa motsi tayi ga jama'a a can a bakin kofa, ga sultan nason sakata kunya, knockin din dakin tayi shiru ba'a bude ba, ta dauki wayarta ta kira sultan din da number nasa na Nigeria.

 

A bacci fatu take jin kamar ana bugun kofa, ta bude idonta tare da zare jikinta daga na sultan wanda baccinsa yakeyi hankali kwance, barin jikinshi da tayi yasa shi farkawa yana mutsike ido, da muryansa ta masu bacci yace "fateey yadai? Fatu data kasa bude kofan don yanda zuciyarta ke bugawa, kuma bata ji an qara knocking ba tace "ana knockin ne" ya tashi a hankali ya bude kofan, wayamm ba kowa, ya leqa falon nan ma ba kowa ya juyo yace "babu kowa fateema" ya qarisa bakin gado ya dauki wayarsa its 4:02pm, yace "lokacin sallah yayi, ki shiga kiyi alwala muyi sallah" tace "a'a nikam zan tafi, wallahi mammi zata neme ni" ya tsaya ya riqe qugu yace "ki shiga kiyi alwala nace" kallonshi tayi ganin ba wasa a fuskarsa yasa ta shiga bathroom din ranta bai so ba, tana fitowa shima ya shiga yayi alwala, kafin ya fito har ta gyara masa shimfidin gadonsa ta kimtsa gurin, sallaya ya dauko musu ta karba ta shimfida, sai a sannan ta tuno bata da hijab, ta kalleshi tace "banida hijab fa" ya bude wardrobe dinshi ya ciro wani pink hijab wanda daga gani ta gane nata ne, zata yi magana yayi kabbara ta saka hijabin ta bishi, bayan sun idar da sallahn sukayi addu'a ta ninke sallayun ta adana, anan ya mata umurnin su fita, daukan cake dinta tayi suka fito, zatayi cikin gida ya jawo hijabinta yace "um um, yau tare dani zaki wuni, muje garden" kallonshi tayi tana murmushi tace "jannah, mammi fa!! Yace "idan kina son mu shirya ki daina kira mini mammi, gutsureki zanyi ne? Ko ni ba mijinki bane? A hankali yayi maganan amma da alama ranshi a bace ne, tace "srry, muje to" qin tafiya yayi, ta jawo hannunshi da kyar ya bita suka tafi. Hira sukeyi cikin kwanciyar hankali har yamma sakaliya. Anan wayarshi ta fara ringing ya dauka yace "Hello mammi" tace "ina fateema? yace "gata nan" tace "ka bude kofan ka bani 'yata" yace "wani kofa? tace "tambaya na kakeyi? Yace "mammi mufa muna garden tun dazu" hamdala tayi zuciyarta yayi fess, ta fito daga dakin tana murmushi ganin haka yasa aka fara tambayan ina fatun?? Tace "suna lambu" su bizzy da salma ne akan gaba harda gudu gudu, suna isa kuwa salma ta hango cake din kan table bata bi ta kansu ba ta qarisa zata dauka sultan ya aza mata rankwashi, "wayyo innata" ta furta a wahale, dai dai nan su mammi suka iso, tana cewa "ka kyauta, kaji? nace ka kyauta" murmushi yayi yace "ina wuni mammi" tace "lafiya, yaushe ka dawo? Yace "dazu ne da safe" tace "shine baka sanar mana ba? Shiru yayi yana kallon bizzy da take qoqarin daukan cake din itama don taga mammi na kusa, ya make hannunta da qarfi, ta cire da sauri tana yarfe hannun don ta bugu, anan ya fara gaisawa da sauran 'yan uwa suna tsokanarsa, sai da kowa ya watse ya rage daga su salma sai mammi, mammi ta cewa fatu "ki shiga gida fateema" ta tashi ta dauki cake dinta su salma suka rufa mata baya (kwadayi😜) Guri ya rage daga mammi sai sultan tace "manga" yace "na'am" tayi shiru can cikin tsigar rarrashi tace "kaga yanzu ka dawo ko? Kuma saura sati a gama biki, to please kar inji wata magana ta taso kaji?" Daria yayi yace "to" da sauri tabar gurin tana cewa "anjima after isha ka sameni a falon abbanku"

 

Maman Fateey👯👯

[10:12PM, 9/19/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

68

 

Tun daga ranar bai qara kiran fatu gurinshi ba, hasalima qaura yayi zuwa sabon gidansu da zasu tare, anyi fenti an saka furnitures da komai an gyara ko'ina das das, gida yayi ready yana jiran amarya. Ranar wednesday aka yiwa fatu lalle jaa da baqi ya amshi fatarta, Anan ta fito amarya sak, ga yanda jikinta yasha dilke tana kyalli, Kitso kanana falmata ta yarfa mata wanda suka zubo bayanta suka qara haska ta, mammi bakinta ya kasa rufuwa don farinciki, qawayen amarya su xahra, bizzy, salma, sai shiga da fita sukeyi. Su kaka sunzo tare da jagorancin kawu muntari, da inna asabe da goggo innani, ba yanda mammi batayi ba kaka ya kwana yace inaa!!! Zasu ga gida daga baya, a ranar suka koma  shida kawu muntari bayan mammi ta cika su da abun biki, aka bar su inna asabe suna santin gida da daular da fatu take ciki.

Ranar thursday akayi KAMU inda amarya da ango suka fito kamar taurari, gashi suna kama, anyi pictures kala kala, abun ya qayatar ba laifi, ranar fariday akayi WALIMA Inda amarya tasha laffaya fara sol mai adon golden, ansha wa'azi sosai kuma anyi rabon kaya irinsu hijabs, paper bags masu hoton amarya da ango, atamfofi,  da sauran kayan da ake rabawa a bikin 'yayan manya. Washe gari saturday aka shirya dinner qarfe takwas na dare no african time, saboda ba'ayi daurin aure ba yasa dinner ya zama big event, abokanan abba, frnds din sultan, abokan kasuwanci duk za'a hallara. Jameel babban abokin ango shi ya shirya komai, babban hall makeke aka kama inda aka qawata shi da ado masu kyau da ban sha'awa, a can step din sama na hall din Royal kujeru biu ne na amarya da ango, a qasa kuma tables ne kowanne da kujeru 4, gurin yasha decoration ba laifi. 8:08 kowa ya hallara amarya da ango kadai ake jira, ko ina ka duba mutane ne kowa yayi shiga ta alfarma, manyan yan kasuwa da qososin gwamnati da sauran jama'a, abba na hango cikin frnds dinsa ana raha hatta daddyn jameel wanda bai cika zaman qasan ba ya hallara. Mammi da mummy ma ba'a barsu a baya ba,  sunyi shiga ta mutunci suna zaune cikin qawayensu ana jiran shigowan amarya da ango, su inna asabe ma sunje. Anan abokin su jameel Naseer ya tashi da mike a hannunsa yadan bubbuga yace "hello" aka ce "hiiii" ya gabatar da shigowan couple, kowa ya qura ido yana jira, a hankali aka saka kida mai sanyin sauti, farouq da wata yarinya ce wacce zasuyi sa'anni suka fara shigowa, yana sanye da coat brown ita kuma gown pink an gyara mata gashinta ya zubo bayanta, farouq na riqe da hannunta sunyi kyau, anan sultan da fatu suka shigo suma hannunsu a hade sai doka murmushi sukeyi, tafi aka fara raff! rafff! raffff! Sanye take cikin riga sa siket na hadedden code lace milk color, sai head da shoe dinta red, veil dinta mai walwali da kyau shima red ta saka a kafadanta daya ya zagayo ta qugunta an riqe shi, sultan kuma jamfa da gare ne milk color sai hularsa zanna brown, takalminsa da agogonsa brown, tafiya suke yi da murmushi a fuskar su, sunyi kyau iya kyau, hasken flashes din camera na masu daukan hoto da kuma phones din mutane ya qarawa gurin haske da walwali, bayansu kuma qawayen amarya sanye da ankon pink gown da head milk, abokan ango suna sanye da brown jamfas, har suka iso gurin zaman su suka zauna suma qawaye da abokai suka zauna a inda aka tanadar musu. Aka bude taro da addu'a, aka fara shagali, jameel ya bada tarihin ango, xahra kuma ta bayar dana amarya, kowa cikin harshen turanci, Mammi, abba da ango suma sun fito sun miqa godiarsu ga baqin da suka halarci wannan taro, sultan da fatu suka yanka cake, ya yanko qarami ya bata a baki ita kuma ta yanko dan babba ta bashi aka saka tafi, An kira amarya da ango su fito yin rawa, abokanan abba suka fita ana musu barin kudi, bayan sun gama qawayen su mammi ma suka fito suka yi nasu liqin, komai ya tafi yanda ake buqata ba hayaniya da cunkusowa, karfe 9:14pm abokan abba suka fice bayan sun cika couple da gifts, su mammi da qawayenta ma suka rufa musu baya, guri ya rage daga abokan ango sai qawayen amarya, sunyi shagalinsu son ransu amma sultan ya hana fatu rawa wai bbu wanda zai gane mishi jikin matarshi na karkaduwa.

An kusan tashi ya jawo hannunta ya rada mata a hankali "daga nan gidanmu zamu tafi ko? Ta harareshi qasa qasa tace "a'a nikam, ka maida ni gurin mammi na" murmushi yayi yace "kina wasa yarinya" qarfe 10:10 suma suka tashi, mahmud sai lilliqewa salma yake yi tana basarwa, da za'a koma gida ma shi ya daukesu dasu bizzy, jameel ya tattari matarsa da qaton cikinta shima.

Sultan ke drivin yayinda fatu ke gefenshi tayi miqa tace "waashhh, na gaji wallahi" kallonta yayi ta gefen ido yace "dats y nace mu tafi gidanmu zaki fi watstsakewa" da sauri ta girgiza kanta tace "um um nikam, gida zan tafi" yanda tayi magana ya bashi daria yace "nayi hakurin 1 month kinga zan iya yin na kwana daya, inace gobe za'a kawoki? Daga gobe shykenan"

 

Maman fateey👯👯

[9:12PM, 9/20/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻          

Na Mrs Aslam Haidar

69

 

Jikinta yayi sanyi tayi shiru, bai qara cewa komai ba har suka iso gida, ta bude kofa ta fita a hankali yana kallonta ta juyi tace "good night" yace "Ahaa" ta rufe motar, jin shiru bai kirata ba har ta kusa shiga gida yasa ta juyo ta tsaya a gurin window dinshi tace "na bata maka rai ne? Ya girgiza kai yace "a'a me kika gani? Tayi shiru kanta na qasa yace "ki shiga gida dare nayi, kinga mune last din shigowa" a sanyaye tayi hanyar gida tana jin jikinta ba dadi, sai data kusan shiga gida yace "heyyy" ta juyo yace "kinyi kyau" murmushine ya subuce a fuskarta tana kallonshi har ya fice daga gidan. Washe gari hka ta tashi jikinta kamar wacce aka yiwa duka, haka dai ta lallaba har bayan isha, tayi wanka aka bata kaya fitted gown na lace green, aka kafa mata dauri tasha make up, jikinta da kayanta sai qamshi yakeyi. Wani abu a gora kamar madara falmata ta miqa mata tace "gashi kisha inji mummy" fatu ta bata fuska tace "nikam abubuwan nan bazasu qare bane? Lubna da take gefenta ta dafa kafadarta tace "kisha fa" fatu ta karba ta kafa kai ta shanye tass ta ajiye goran tace 'Alhamdulillah" daria su salma suka saka. Anan mammi ta shigo da wani babban mayafi white mai adon stones kala kala ta daurawa fatu a kanta tace "muje gurin abbanku" ta riqo hannunta har palourn abba, sukayi sallama suka shigo, mammi ta zauna a kujera fatu kuma ta zauna a qasa gurin kafafuwanta. Fatu ta gaishe da abba, ya amsa yana mai fara'a dai dai nan sultan ya shigo shima sanye yake da green shadda jamfa da hularsa itama green, sai zuba qamshi yakeyi ya samu guri kusa da abba shima ya zauna yana satar kallon fatu wacce ta sunkuyar da kanta qasa sosai har baka kallon fuskarta. Abba ne yayi gyaran murya ya fara musu nasiha dukansu, sosai nasihar sa ya ratsa zuqatansu bayan ya gama sultan ne yayi magana yace "abba mun gode" anan mammi ma ta fara nata, a lokacin fatu ta fara kuka harda shesheka, idon sultan na kanta. Sai da mammi ta gama nata nasihar ta kalli sultan tace "ga amanar fateema, marainiyace gaba da baya, qanwarka ce yar uwa, kuma mata a gareka, don Allah idan tayi laifi a gyara mata ta hanya mai kyau, Allah ya baku zaman lafiya" fatu bata samu damar magana ba don irin kukan daya kwace mata tunowa da iyayenta da tayi, anan ta bawa kowa tausayi, abba yayi addu'a aka shafa. mammi ta dauketa zuwa gurinsu inna asabe, suma nasihan dai suka maimaita aka shigar da fatu mota mummy a gefenta da goggo innani, har aka iso gidanta dake New GRA bata bar kuka ba. Gida ne madaidaici hawa daya, zagaye yake da flowers masu ban sha'awa ciki da waje, ana shigowa zaka iske parkin space wanda a kalla zai dau motoci 5 zuwa 6, sai ta bayan gidan lambu ne shima madaidaici, babban palour ne a qasa mai dauke da set din kujeru da tangamemen tv sai sauran kayan kallo, an qawata falon ba laifi, a palon akwai kitchen sai wasu dakuna biyu, dayan kusa da kitchen daya kuma kusa da toilet in palour, still a palourn akwai wata kofa wacce ba'a bude take ba. Upstairs aka haura da ita, nan ma zaka iske wani qaramin palour ne shima da kayan kallonsa,sai dakuna hudu, A cikin dakunan aka bude daya aka shigar da fatu, har kan qaron royal bed dinta mummy ta zaunar da ita tareda dan daga lullubin kan fatun tace "fateema kukan nan ya isa haka, ki share hawayenki" anan ta ciro hanky daga jakarta ta sharewa fatu fuska ta gyara mata shi, tace "karki qara bata fuskan ki kinji? Fatu ta daga kai tana ajiyar zuciya, lokacin qarfe 8:43pm mummy sukayi haraman tafiya fatu ta riqe gyalenta  tace "mummy zan biku" murmushi mummy tayi tace "kiyi hakuri ki zauna gidan mijinki fateema, ai gasu xahra zasu kwana miki" jin haka yasa fatu murmushi tace "to shykenan mummy" su goggo innani suka mata sallama kan gobe zasu koma kumo, ta musu sallama tace su gaishe mata da kaka" gida ya rage daga amarya sai qawayenta, salma da bizzy na waya da alama da samarinsu ne yayinda lubna da xahra da fatu kuma suke hira, fatu tsakaninta da Allah ta yarda zasu kwana bata san wayo mummy ta mata ba. Goma saura wayar lubna ya fara qara ta dauka ganin sunan mijinta, yace ta sauko su tafi. Bayan ta kashe ne ta kalli su bizzy ta musu ido, nan da nan suka fahimta. Xahra ce ta fara tashi tace "nifa banga gidan nan da kyau ba, bizzy kuzo muje mu gani" aiko nan suka miqe suka fita, lubna da take murmushi ta juyo tace "kinsan nikam bazan kwana ba, bari in tafi DJ yazo" fatu ta marairaice fuska tace "shi yaya jameel dan kwana daya bazai bar mana ke ba? Lubna tayi daria yayinda take yafa gyalenta tace "nima bazan iya ba, sai da safenki amarya" fatu ta tashi zata rakata lubna tace "a'a yi zamanki, ba komai, bari in kira miki su bizzy" Tana fita fatu ta koma ta zauna harda cire mayafi, tana zaune shiru har kusan 15mins kuma bata ji motsin su ba, tsoro ne ya shige ta a take tace badai tafiya sukayi ba. Da sauri ta fito daga dakin, ganin basa palourn sama yasa ta sauko qasa nan ma basa nan, cikinta ne ya fara bada stars tabbas guduwa sukayi, a'a ta haura sama da gudu tana bubbude dakunan tana leqawa, kowanne ta bude basa ciki, room din qarshen ne taga hatta door din daban ne, nan ta murda handle din ta shiga dai dai lokacin da sultan ya fito daga wanka da jallabiya fara sol a jikinshi yana taje gashin kansa, jin an bude kofa yasa ya juyo yana kallonta yana mata murmushi, akan mirrow ya ajiye comb din ya dauki wani remote ya danna saitin kofa, nan take kofar ta rufe, fatu ta juya tana qoqarin budewa da taga bazai budu ba ta juyo fuskarta kamar wacce zatayi kuka tace "inasu xahra? Sultan daya harde hannu yana kallonta sama da qasa yace "jameel ya maida su gida" Ido ta zaro ya gyada mata kai hade da kashe mata ido ya nufo gurinta yana cewa "WELCOME HOME HONEY"

 

Maman fateey👯👯

[2:13PM, 9/21/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

70

 

Tsayawa yayi daff da ita har suna shaqan qamshin jikin juna yace "me zaki yiwa su xahran? Ta dake tace "mummy tace zasu kwana ai" yayi daria yace "wayo ta miki, babu wanda zai kwana miki sai ni kadai" ta turo baki kamar zatayi kuka tace "nifa... nifa..gaskia ka kiramin su xahrah" murmushi yayi ya juya ya dauki remote din ya danna kofar ta bude yace "kije kiyi alwala ki dawo yanzu" tace "nayi salla fa" yace "I know, ko zakiyi anan? Tace "a'a" tare da ficewa daga dakin.

Bata jima ba ta dawo da alama tayi alwala, sai data shigo ta manta bata dauko hijab ba ta juya zata koma, ya tsayar da ita yace "ina zakije? Tace "zan dauko hijab ne" yace "me zakiyi da hijab din? Tace "zan saka muyi sallah mana" yace "sallahn me? Tayi shiru murmushi yayi irin na😎 yace "oohh wato kinsan ana sallah kenan, ashe ba sai nasha wahalan koyar dake komai ba" bata kulashi ba ta qara niyyar juyawa yace "wait" yaje gaban makeken wardrobe dinshi ya bude ya dauko mata wani white hijab ya bata. Mamakine a fuskarta don this is the second time da yake bata hijabi daga wardrobe dinshi kuma duk nata ne. Tace "a ina ka samu? daga kafada yayi yace "nima ganinsu nakeyi a gurina" tace "serious dai" yace "a gurin shanya kaya nake gani sai in dauka" daria tayi tace "to a dalilin me? Me kakeyi dasu? Yace "ohoo, yanzu ba gashi sun miki amfani ba? Lets pray" Ba musu ta bishi yaja su raka'a biyu suka sallame. Ya juyo ya dafa kanta tare da kwararo addu'o'I da musulunci ya tanadar domin samun zaman lafiya da zuria dayyiba. bayan ya gama, ya qara wasu addu'o'in suka shafa. Ya miqe tareda da fita daga dakin, a hankali ta tashi ta linke darduman sallah tareda hijab dinta ta adana su, ta rasa me zatayi gashi gabanta sai dukan uku uku yakeyi, bata qara 2mins ba ya shigo da ledoji a hannunshi, ya ajiye a lallausan carpet din dake tsakiyar dakin ya zauna yace "kizo" ba musu tazo itama ta zauna dan nesa dashi. Murmushi yayi ya kada kai ya ciro kazar dake cikin ledan ya daura ta a kan plate din da ya shigo dashi, fresh milk ya saka a glass cup ya miqa mata, ta girgiza kai yace "what? Tace "na qoshi" bai ajiye hannunsa ba yace "gashi" ta karba, ya qara tsiyaya wani a cup, hankali ya yanko tsokar kazar tare da kaiwa bakinta ta juya fuska, murmushi yayi ya gyara zama yace "kinsan me? Ta juyo tace "a'a" yace "ranar dinner saura kadan in shaqe, cake din da kika bani ya mini qato" daria tayi tace "sorry dear" yace "noo, naqi hakurin" wasa wasa ya rinqa janta da hira har ya miqa mata kazar ta karba ta fara ci tana korawa da fresh milk din, da na hannunta ya qare da kanta ta qara yanko wata tsokar, shima a haka yana ci sai da sukayi nakk! Ya cire hannunshi yace "Alhamdulillah, anaso ana kaiwa kasuwa, gashi ke kadai kin yiwa kazar illah" ta sunkuyar da kanta kasa tana juya empty glass cup din dake hannunta tace "ba wayo ka mini ba, kana ta jaana da surutu" yace "ba wani dama jira kikeyi" ya fada yana murmushi, itama murmushin tayi ta fara tattara gurin ta kai kitchen. Dakinta ta wuce ta cire kayan jikinta ta fada wanka, bata jima ba ta fito ta shafa humran ta mai dadin qamshi saqo saqo na jikinta, ta shafa cream dinta mai kulacca, tana tsaye a bakin wardrobe ta rasa wani night wear zata saka don gaba dayansu basuda M😉. Tana tsaye taji mutum a bayanta ya rungumota a hankali ya daura habarshi a shoulder dinta ya zagayo hannunsa ta kan tummy nata yace "in tayaki zaba?

saboda irin yanda jikinta ya mutu yasa ta kasa koda kwakkwaran numfashi, ya daga ido ya kalleta yaga yanda tayi kasa da kanta dan mitsitsin bakinta a bude tana numfashi, saketa yayi ya shiga duba kayan, ya dauko daya ya manna a jikinta ya dan dubeta, tana nan tsaye kamar statue da dan qaramin towel dinta, ya ajiyeshi ya dauko wani purple dan guntu silky one, gaban rigan anyi ado da pink flowers, hannun rigan irin na bra, ya manna a jikinta yace "wannan zai miki kyau" ta dago ido ta kalli rigan tace "nifa ba irinsu nake sakawa a gida ba" murmushi yayi ya cire rigan daga hanger ya bata yace "banbancin gida da gidan miji kenan, idan kin gama ki sameni a dakina akwai abunda zan nuna miki" ya shafa sajenshi ya fita daga dakin, binshi tayi da ido yana fita ta murguda baki hakan yayi dai dai da juyowanshi yace "ni kika murgudawa baki? Ehhh lallai zaki gane" ya fita. Murmushi tayi ta dauki rigan tana kallo, ganin ba sarki sai Allah yasa ta saka, ba qaramin kyau rigan ya mata ba, ta zamo kamar wata baby doll, kallon kanta tayi a madubi, ta juya ta qara juyawa, qarar wayanta ne yasa ta tsaya da juye-juyen kafin ta dauka ya zama missed call, body spray ta fesa ta saka dogon hijabinta ta kashe light din dakin ta fita tareda rufe kofan.

 

Maman Fateey👯👯

[7:10PM, 9/22/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

71

 

A hankali ta murda handle din kofar sultan ta kutsa kai tareda sallama a bakinta, yana zaune a bakin gado yana danne-danne da laptop dinshi, dago da kai yayi ya amsa mata, tsayawa tayi a bakin kofar tace "kace zaka nuna min abu" yace "yeah, zo ki gani" yayinda ya mai da kanshi kan laptop din yana dannawa. Dan nesa dashi kadan ta tsaya tace "gani" hannunsa ya miqa mata alamar ta taho, kamar bazata je ba amma ta miqa nata hannun, jawota yayi jikinshi tareda cire hijab din jikinta, hakan yayi daidai da mutuwar laptop din, ya rufe ya ajiye a bedside yace "labari zan baki, amma first ki saki jikinki kuma karki tsorita!!!

 

Washe gari misalin 8:45am yaji ana buga kofa, bude idonshi yayi a hankali ya sauqe akan kyakkyawar fuskar matarshi fatu, wacce baccinta takeyi hani'an, murmushine ya subuce a fuskarsa, lokaci daya kuma tausayinta ya mamaye zuciyarsa tuno da irin wahalan da tasha jiya, "she's special" ya furta qasa-qasa yayi kissing goshinta tareda zare jikinshi a hankali daga jikinta. Jallabiyarsa ya zura tareda fita daga dakin zuwa palourn qasa inda ake bugu har yanzu. Salma da bizzy ya gani bayan ya bude qofar kowacce bakinta a washe da food warmers a hannunsu, bizzy tace "sannu ya sultan" salma tace "ina kwana, an tashi lafiya? Bizzy tace "ya gajiya? Kallonsu yakeyi ya zura musu ido kuma bai amsa duk gaisuwan da suke masa ba. Ganin haka yasa suka rage fara'a salma tace "mammi ce tace mu kawo muku breakfast" Tokare qofar yayi yace "da sanyin safiyar nan? Kallon juna sukayi salma ta zaro ido tace "ya sultan yanzu fa karfe 9, ai ko na goye yasan rana ta fito" ya harde hannayensa yace "magana zaki fada min ne? Salma tace "wane ni? Sorry. To bari mu shiga mana" ta fara qoqarin yin step gaba. Ya sauqe hannayensa yace "ba matsala, kawo abincin, mungode" Baki suka sake yayinda ya karbi na hannun bizzy ya ajiye a falon, ya qara karban na hannun salma shima ya ajiye yace "ku huta gajiya" Ruff ya rufe kofar ya barsu tsaye a gurin, mahmud da yake cikin mota don shi ya kawo su ya tuntsire da daria harda riqe ciki, ganin sun juyo yasa ya masge ya fuske. Jiki a sanyaye suka qaraso gurin motar salma kamar ta nitse don kunya don mahmud da take yiwa big time yaga an mata ajii down. Babu wanda yayi magana har suka shiga motar, maigadi ya bude musu gate suka fita bizzy tace "ohhh yanzu karfi da yaji ya hanamu shiga? Daria ne ya subucewa mahmud, yanayi a hankali salma ta harareshi ganin haka yasa bizzy itama tayi daria tace "ba laifinshi bane" anan abun ya zama na tsokana suka dinga darawa har suka iso gida.

 Sultan na komawa daki yaga ba fatu akan gadon, dakinta ya nufa anan ya samu ta shiga bathroom. Komawa dakinshi yayi yana sosa kai shi daya yana murmushi.

 

Ruwan zafi ta qara hadawa ta shiga tayi sitbath duk da cewa jiya sultan ya gasata, tafi 15 mins a ciki sannan tayi wanka da ruwan dumi tayi brush ta fito, ba laifi ta daina jin ciwon da jikinta yake mata sai abunda ba'a rasa ba. Cream dinta ta shafa tayi light make up, riga da siket na wani super wax mai yellow nd blue ta saka, dinkin ya amshe ta kamar a jikinta aka dinka, dauri ta kafa kamar mai shirin zuwa liyafa, bin jikinta tayi da turare ta ko'ina. Tana ajiye kwalban turaren sultan ya shigo shima da alama yayi wanka don ya canja kaya, brown three quarter ne a jikinshi da black t-shirt an rubuta _special you_ a jiki, sai zuba qamshi yake yi sajenshi da gashin kanshi ya kwanta luff luff yana kyalli. Sunkuyar da kanta tayi don irin kallon da yake aiko mata ta mirrow bazata iya juraba. A hankali ya qaraso gurinta ya rungumeta ta baya tace "ina kwana" yace "lafiya lau, kin tashi lafiya? Tace "lafiya" yace "ya jikin kuma? Shiru tayi ya juyo da ita suna fuskantan juna fuskarsa so serious yace "har yanzu kina jin zafi, sorry habebteey. Ok dauko gyalen ki mu tafi hospital" Ta marairaice fuska tare da dago fararen idanunta tace "nifa lafiyata kalau, bari in sauka in mana breakfast"

Ya kama hannunta yana kallon cikin kwayar idonta yace "are sure bakijin komai? Ta daga kai yace "um um fa" tace "Allah naji sauqi" murmushi yayi yace "ok Allah ya qara lafiya, kinyi kyau dear" murmushi tayi tace "thanks" yace "shi kadai kika ji? Baki amsa addu'an da na miki ba" kwace hannunta tayi a hankali ta fara tafiya tace "zan hada mana break fast" binta yayi yana cewa "mammi ta aiko mana" a dinnin ta tarar da food flasks din zata wuce kitchen ta dauko plates da cups ya tsayar da ita yace "ki huta, don naga baki dawo normal ba" ya zaunar da ita kan daya daga cikin chairs din dinning table din shi kuma ya wuce kitchen. Bai jima ba ya fito riqe da plates da cups a hannunsa ya ajiyesu akan table din ya fara servin dinsu, ferfesun kifi ne sai masa da miyan ganye wacce tasha tsokokin nama, kunun gyada ya saka musu a cups din ya turawa fatu gabanta, anan ya kalleta yaga ta zuba masa ido tun shigowansa take kallonsa tana jin wani irin sonshi na fisgarta, dan fulani kyakkyawa wai mijinta ne ita dayanta, gaskia na taki sa'a.... iskan daya hura mata ne yasa ta farka daga kogin tunanin da ta fada, murmushi ne a fuskar sa yace "what are u thinking? Ko na miki kyau ne? Murmushi tayi ta kalli abincin gabanta tace "nagode" A hankali suke cin abincin suna hira jefi-jefi har suka kammala, ya dauki used plates din ya kai kitchen fatu ta bishi da cups din, anan suka wanke hannu, zatayi

 wanke-wanke yace "noo, ki bari akwai masu aiki, zasu zo suyi" zatayi magana ya daura yatsansa a kan lips dinsa yace "shhhh, muje muyi bacci"

 

*AFTER 3yrs*

 

Maman Fateey👯👯

[10:12AM, 9/23/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

72

 

*AFTER 3YRS*

 

Gurin cike yake da mutane, ko'ina ka duba group group ne na family sunzo taya 'yan uwansu murnan gama university. A cikin su na hango familyn su fatu, mammi, mummy, lubna da jameel da 'yarsu yar shekara 2 da rabi, mai sunan mummy ce wato kulsum amma ana kiranta khairy, amrah ce a gefe ta zama budurwa tana bawa al'ameen ruwa a baki, yarone dan shekara da wani abu, yana gama shan ruwan ya wuce gurin mamanshi salma matar mahmud yana cewa "ummii give me cake" dan gaba dasu naga fatu tareda sultan suna zaune abinci take zuba masa a plate yayinda yake qoqarin bude Qaton cooler da sukayi guxurin drinks a ciki, coke ya dauko ya balla marfin ya fara sha, tana gama saka masa ta miqa mishi ya karba ya koma gurin su jameel da mahmud wanda suma abincin ne a gabansu. Anan suke labarin yanda graduation din ya qayatar, fatu ta fito da flying colors wanda hakan ba qaramin dadi kowa yaji ba, mammi harda hawaye. Bayan an gama shagali suka kama hanyar gida. Kai tsaye kowa ya wuce gidansa don irin gajiyar da suka kwaso, tun safe suke cikin GSU sai yanzu bayan la'asar suka koma gida. A falo fatu ta yada zango ta dafe kanta tana tunani. Shigowan sultan yasa tayi saurin sauqe tagumin ta qaqaro murmushi, fuskarsa da damuwa yazo ya zauna kusa da ita yace "what again, nikam bakya tausaya min ne? Ya kike so inyi ne? Tace "babu komai fa, kawai gajiya na debo ga ciwon kai da yake damuna" Hugging dinta yayi tsam a jikinshi yana buga bayanta, a hankali wasu siraran hawaye suka gangaro daga idanunta, da wayo ta gogesu don kar sultan ya gani. Mintuna kadan suka yi upstairs. Dakinta ta shiga shima ya wuce nashi, ta kwabe kayan jikinta ta shiga wanka. Ruwan mai dumi ta hada a bathtub din ta diga turaren wankanta wanda bata rabuwa dashi tun aurenta yau shekara uku. Shiga ciki tayi ta zauna tareda sauke nannauyan ajiyar zuciya. A haka ta fara tunani..... tun bayan aurensu suke dokin samun haihuwa amma har yau Allah bai basu ba, shekara da aurensu mammi ta kira fatu gida take tambayanta "fateema kinyi planning ne? kina school may be kina tsoron wahala, ga karatu ga yaro ko? Don Allah Ki bari ki haihu in yaso ni zan karbi babyn" fatu tace "mammi wallahi babu abunda nayi, har asibity naje a dubani ko inada matsala ne suka ce a'a, mammi ban san ya zanyi ba" ta qarisa maganan tana hawaye. Anan kuma mammin ta shiga lallashinta tana bata baki, tace "ki kwantar da hankali, Allah zai baki a lokacin da ya dace, kinga mahaifiyarki ma sai data shekara 9 kafin ta haifeki a labarin da naji, ni kuma kinga daga nayi miscarriage sai su rasu suna jarirai, mu kuma haka Allah yaso ya ganmu. Muyi tawakkali" fatu ta jinjina kai tana share hawayen fuskarta. Daga ranan mammi bata qara mata magana akai ba sai qoqarin ganin ta kwantar mata da hankali takeyi. Shima sultan ya taba mata kwatankwacin haka still shekaransu biyu da aure lokacin mahmud da salma sunyi aure, salma ta haihu ana gobe suna, sun fita shopping din kayan suna yaga wani feeding bottle dan qarami mai kyau, ya dauka yana juyawa a hannunsa, anan ta dauko wani riga na jarirai tana nuna masa amma hankalinshi nakan feedern, tabashi tayi ya juyo da dan murmushi a fuskarsa yace "wannan ya miki kyau" itama murmushin tayi tace "yayi kyau" yace "zan ajiyewa babyn mu da zamu haifa" daga kanshi yayi kamar mai tunani can yace "yau 2yrs da aurenmu harda wata uku, anya fateema banida matsala kuwa? Ya sauqe Idanunshi a kanta yaga har ta fara kuka, kafin yayi magana ta fita daga gurin, ranshi a dagule yaje ya biya abubuwan da suka siya ya kai mota, a motar ya sameta tana kuka ya ajiye ledojin shopping din a backsit ya zagayo zuwa mazauninsa, yana shiga ya jawota jikinshi yace "na bata miki rai ne? Ta girgiza kai yace "to meyasa kike kuka? Tayi shiru yace "fateema talk to me" share hawayen fuskarta tayi tace "babu komai" yace "don kawai nace ko inada matsala? Last year mammi ta mini magana akan ko munyi planning nace mata a'a, amma ta tambayeki may be kinyi ban sani ba, wanda kuma nasan hakan zaiyi wuya, bayan ta kiraki ne take sanar dani cewa babu abunda kikayi lokaci ne kawai baiyi ba, ta fada min cewa kinje asibity wanda a sanina baki fada min zaki je test ba, amma sanin irin halinda kike ciki yasa kwata kwaata banji raina ya baci ba kuma na nunawa mammi cewa da sanina kikaje" ya dago fuskarta yace "damuwarki daya: mammi tana son jikoki nd ni kadai ne danta kina tunanin ko hakan zaisa in qara aure! Ni mata biyu nake da niyyan yi kuma already na auresu" a firgice ta miqe daga jikinshi lokaci daya kuma tace "aure?? Mata????

 

Maman Fateey👯👯

[10:00PM, 9/24/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

73

 

Ya gyada mata kai yace "dayar fateema mahmud dayar kuma fatu mamuda" ya qarisa yana daria, duka ta kai mishi a kirji kana ta juya mishi baya tana kallon window, share hawayenta takeyi tana murmushi, Allah ne kadai yasan yanda zuciyarta tayi pounding jin cewa sultan dinta yayi aure, ya jayota tana qoqarin kwacewa ita ala dole tayi fushi, matseta yayi sosai ya juyo da fuskarta har suna shaqan numfashin juna yace "u ar d only one I need, kece fateema kece fatu so ke kadai kin isheni" ya dan sassauta riqon daya mata yacigaba "amma saidai bamusan abunda Allah ya tanadar mana gaba, amma in dai nine u ar d one nd only" murmushi ya subuce a fuskarta tace "abunda yasa kaga nayi haka bawai tsantsan kishi ba ne, nooop tunanina cewa kayi aure baka sanar mini ba wanda hakan ya nuna rashin matsayina kenan a gurinka, babu macen da zata ji dadin cewa mijinta

Yayi aure ba tare da saninta ba. Naji dadin maganarka na cewa I am d one nd only kuma daga baya ka fada min gaskia cewa bamusan abunda Allah ya tanadar ba, yana daya daga cikin abunda yasa nake qara sonka fadin gaskiarka, Ban taba addu'an zama ni daya ba don nasan kai *mijin mace hudu* ne littafin eeshmal. Sai dai koyaushe addu'ana Allah ya kawo abokiyar zama tagari" shafa kanta yayi yana murmushi yace "Ameen, in kuma ni mijin mace daya ce Allah ya qara mana zaman lafiya da zuria masu albarka" tace "Ameen Jannah"...... kwankwasa kofan bandakin da akeyi yasa ta dawo daga tunanin da takeyi. Tayi gyaran murya, bude bandakin yayi yace "lemme join u" ta karkada mishi kai alamar a'a, bata fuska yayi yace "please" Tace "ok" wankansu sukayi suka shirya cikin qananan kaya, zama sukayi a palour suna kallo suna hira, wayar sultan ne ya fara ringing ya dauka yace "hello" magana aka fada mishi, ya dan kalli fatu kamar mara gaskia yace "zan kira anjima please, bye" fatu bata ma jishi ba don kallonta take yi. Washe gari da asuba bayan sunyi sallah sunyi karatu dama wannan qa'ida ce har sai rana ta fito, fatu tayi addu'a ta shafa ta miqe ta niyyar kwanciya a gado ya tareta yace "sai ina? Tace "bacci jannah" yace "noop ba yanzu ba, muje in tayaki shirya kaya, tafiya zamuyi" Tace "ok" wankansu sukayi suka shirya cikin qananan kaya, zama sukayi a palour suna kallo suna hira, wayar sultan ne ya fara ringing ya dauka yace "hello" magana aka fada mishi, ya dan kalli fatu kamar mara gaskia yace "zan kira anjima please, bye" fatu bata ma jishi ba don kallonta take yi. Washe gari da asuba bayan sunyi sallah sunyi karatu dama wannan qa'ida ce har sai rana ta fito, fatu tayi addu'a ta shafa ta miqe da niyyar kwanciya a gado ya tareta yace "sai ina? Tace "bacci jannah" yace "noop ba yanzu ba, muje in tayaki shirya kaya, tafiya zamuyi" Ta ware eyes tace "ina? Yace "around da world" aiko da gudu ta dane kanshi tana daria shima tayata yayi. Dama ya mata alqawarin in ta gama skul zasu fita yawon bude ido.

 Saai da suka nitsu tace "thanks jannah, Allah ya saka da alkhairi" yace "Ameen, oyaa dauki abunda kike buqata don qarfe 9 jirginmu zai tashi" a qaramin akwati ta hada abubuwan da take buqata don ya hanata daukan kayan sawa wai zasu sayi new ones, dan sinadaranta, undies da turarukanta sai dan abunda zata buqata, kafin 8 sun gama shirinsu tsaff, suka rufe ko'ina suka fito, doguwar riga ce a jikinta indian design mai purple nd pink, sai baby hijab dinta black, takalmi da jakanta ma black, tayi dan make up tayi kyau abunta kamar sweet 16 kai kace bata yi shekara 22 ba. Shi kuma jeans da riganshi t-shirt ya saka yana riqe da jakan laptop dinshi sai dan qaramin trolley dinshi yana ja, a palourn qasa suka hadu yace "kinyi kyau habeebtey" tace "thanks jannah, kaima kayi kyau kamar wani dan saurayi" daria yayi yace "me banbancina da saurayi? Itama ta dara ta nuna kanta da yatsa tace "gani kuwa, idan aka ganmu tare ansan lallai ka ajiye iyali" Kayansu suka saka a bayan mota tayi driving dinsu zuwa gidan mammi suka mata sallama ta bisu da addu'a, tana jin dadin irin yanda suke zaman lafiya, dadi fall a ranta ta koma gida yayinda drivern abba yayi drivin dinsu zuwa gidan mummy. Itama suka mata sallama farouq yake cewa "da ana hutun school dana biku" fatu tace "next time da kai zamu tafi".

A airport driver ya ajiyesu su kuma sukayi proceeding jirginsu ya daga zuwa abuja, daga nan suka qara shiga wani zuwa Mauritius, daki suka kama a wani 5star hotel, sun zaga cikin gari sun bude ido, kwanansu 5 suka daga zuwa india, shima basu jima ba suka wuce london, paris, china, daga nan suka wuce saudi arabia sukayi umrah, satinsu biyu a qasa mai tsarki sannan suka wuto dubai, anan sukayi masauqi a wani apartment da sultan ya siya, da yake fatu tana zuwa dubai in anyi hutu, kuma harkan business dinsa yafi yawa anan dubai din. Fatu ta cika tayi bul bul abunta ga wani haske data qara. Satinsu biyu sukayo haramar dawowa gida, tsaraba kam sun kwaso shi, da safe jirginsu ya tashi zuwa Abuja Nigeria, daga nan suka hau na gombe, kusan la'asar suka sauqa airport, driver ne yazo ya dauke su ya kaisu gidansu. Kamar koyaushe an gyara musu gida an share ko'ina kamar dama masu gidan suna ciki, bayan sunyi wanka sun shirya suka fito palourn qasa, Amrah suka tarar a xaune da food flasks a gefenta. Ta tashi da dan tsallenta ta rungumesu tana cewa "I miss u guys" sai da suka gaggaisa amrah tace "kai anty fateey wallahi kin qara kyau, ya sultan kaima kayi kyau" fatu tayi murmushi tace "amma cikinmu wa yafi kyau? Na fishi ko? Tafada tana winking din amrah. Daria sultan yayi yace "aiko makaho ya laluma yasan na fiki" buga kofan da aka fara yasa amrah ta miqe tare da budewa, khairy yar jameel ce ta shigo da gudu amrah ta dagata suna daria tace "ina mom dinki? Sallama jameel da lubna sukayi aka amsa musu fatu ta tashi ta tari lubna cikin dokin ganin juna, lubna ta ajiye basket din hannunta sukayi hugging juna, jameel ya zauna kusa da sultan ya bugi kafadanshi yace "ka gansu kamar basa waya koyaushe" daria sultan yayi sukayi hand shake yace "zaka fara ko?

 

Maman Fateey👯👯

[9:09PM, 9/25/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

74

 

Hiran yaushe gamo sukeyi har aka kira sallarn

Maghrib, bayan sunyi sallah suka hadu a dinning table, tuwon shinkafa miyar egusin da amrah ta kawo sukayi serving, snacks da kunun aya lubna ta kawo. Sultan sai kallon fatu yakeyi, in sun hada ido sai yayi murmushi, jameel ne ya bugi kafadarshi a hankali yace "ya? Sultan shima yayi qasa da murya yace "I am confused! To ta yaya zan...." wayar amrah ce data fara ringing ne yasa ya dakata da maganan da yakeyi, har wayan ta katse bata dauka ba, sultan yace "bakiji ana kiranki bane? Ta bata fuska tace "yaya ka bari kawai" bai qara cewa komai ba har suka gama cin abincin ita kuma tasa wayar a silent. 8:19pm su lubna sukayi haraman tafiya, fatu ta kwaso musu tsarabansu ta basu, amrah ma aka bata nata, suna tafiya amrah tace "nima fa zan tafi, bari in kira driver" sultan yayi saurin katseta yace "ki barshi kawai, kizo in kaiki" fatu ta kawo tsaraban su mammi da abba tace a kai musu. Suna isa gida suka sami mammi a falon abba, sultan ya gaishe su, sunyi murnan ganinshi, mammi tace "manga kun dade kam gaskia, har na fara zaton ko kun koma can da zama ne" ya sosa kai yana murmushi yace " a'a mammi" tace "ina fateeman? Tana lafiya? Yace "lafiyanta kalau, tace a gaisheku, gobe itama zata zo" mammi taji dadi tace "to Allah ya kaimu, in banda ita ai da ta huta tukunna" sultan yace "ita ta matsu mu dawo, wai tayi kewan gida" mammi tace "ayya fateema na" bai jima ba ya musu sallama mammi ta fito ta rakashi har gurin motanshi suna hiran tsakanin d'a da uwa, yace "mammi akwai maganan da zamuyi" ya fada wani sunkuyar da kai, tace "wani abune manga? Magana naga yake fada mata tayi shiru tana sauraronsa can tace "amma kunyi bincike ne? Yace "a'a zamuyi dai, amma kar a fadawa abba. Ba yanzu ba" mammi tayi murmushi tace "ai abun farin ciki ne, ya kamata ya sani tun wuri" sultan yace "a'a mammi, to ki bari ni zan fada masa da kaina" daria mammi tayi tace "kai kadai dinka, Allah ya tabbatar da alkhairi" yace "Ameen" shima yana daria, tace "mara kunya, mun gode da tsaraba" ya shige motarsa yana daria. Kafin ya isa gida sai da ya biya ya sayawa fatu chocolates da ice cream sannan ya koma. A dakinta ya tarar da ita ta fito daga wanka tana shafa mai, ya lallaba zai dan tsorita ta sai kuma ya fasa, yayi sallama ta amsa ya shigo tace "ya ka sami su mammin? Yace "lafiyansu sunce ma a gaisheki" tace "ina amsawa, na qagu ai gobe tayi inje inga mammi na" ta qarisa magana tana murmushi. Fita daga dakin yayi yana zolayarta wai goben ma bazata je ba, tana gama shiri cikin kayan baccinta ta mulka humranta ta fito, a falon sama ta hango leda akan kujera ta bude, ice cream ne da chocolates ai da murnanta ta hau sha, kafin sultan ya fito ta cinye tasss, Ya fito shima da kayan baccinsa ya ganta yace "ina nawa" ta ware ido tace "dama baka ci bane? Ya harde hannayensa yace "tukunna ma wayace naki ne? Shiru tayi tana mai murmushi can tace "sorry" yace "zanga wazai siyo miki gobe" ta marairaice fuska ta turo baki tace "bana baka hakuri ba? Yace "its ok, ai bakya laifi, muje mu kwanta" Washe gari fatu ta shirya tun 11 sultan ya sauqeta a gidan mammi shi kuma ya wuce, mammi ba qaramin dadi taji ba ganin fatunta tayi kyau tayi fresh, tana azahar ta wuce gidan mummy itama taji dadin ganinta, ta basu tsarabansu duk na farouq  yafi yawa, anan ta hadu da khadija qanwar jameel tazo da yaranta biyu, khadija ke cewa " Madam ya kamata yanzu kam muga baby" fatu tayi shiru kaman ruwa ya cinyeta, khadija ta qara cewa "kinyi shiru ko har yanzu baku gama amarcin bane? Fatu ta dago kai fuskarta ba yabo ba fallasa tace "kinsan komai sai lokacinsa yayi, kuma mutum bashi yake bawa kansa ba, Allah ne zai kawo a lokacinda ya dace" tana gama fadan haka ta tashi tace "bari in dauko abu a kitchen".

A kitchen khadija ta sameta ta dauki ice cream tana neman qaramin spoon, tace "fateema kiyi hakuri da abunda na miki, I was a victim too, lokacinda nayi aure kafin na haihu sai da nayi 2yrs, irin haka in dangin mijina na qauye sukaje hutu gurinmu sukan fada min irin maganganun nan and bana jin dadinsu, duk abunda baka so a maka kar ka yiwa dan uwanka, kiyi hakuri don Allah" fatu ta dafa kafadarta tana murmushi tace "ni baki bata mini rai ba maman sabeer, don a raina na dauka hakan yana faruwa ga irina, so kinga in nace zan dinga bata rai zan hadu da matsala, haihuwa na Allah ne da kudi ko matsayi basa bawa mutum" Khadija tace "hakane kiyi hakuri" fatu tayi daria tace "c'mon ki daina bani hakuri, nifa ban dauka da wani manufa ba" khadija tayi murmushi tace "nagode" a haka sukayi ta tadi har bayan la'asar sakaliya ta koma gidan mammi. Ana isha sultan yazo suka wuce gida.

 

*Bayan Sati daya*

 

Fatu ne zaune a palourn lubna tana shan kankana yayinda lubna ke kitchen tana aiki take cewa "kayan nan suna ta tafiya fateema, hajia nazifa ta kirani tana son swiss guda 24, dozen biyu kenan" fatu zatayi magana taji muryan jameel a waje yana cewa "kana nufin har yanzu baka fada mata ba? Sultan yake cewa "ka santa da sa abu a rai, kuma ma me zance mata? Dai dai nan suka shigo fatu tayi saurin amsawa lubna maganarta da cewa "idan na koma gida zan aiko miki sai ki tura mata" amma can qasan ranta ta fara tunanin akwai wani abu da yake tafiya, 'something is fishy' kwanan nan ta lura da wani extra care da sultan yake bata haka ma mammi koyaushe saita kirata tana wani lallabata. A ranta tace she has to find out. Zama sukayi suna hira sai bayan isha suka koma gida. Qarfe 9:55pm agogon wayan fatu ya nuna, fitowanta daga wanka kenan tasa kayan baccinta ta feshe jikinta da turare ta nufi palourn qasa inda sultan ke aiki da laptop dinshi lokaci daya kuma yana waya. A gefenshi ta zauna ta canja tasha zuwa zee world, kallonta yakeyi kamar ya cinyeta don wani irin kyau da take qara masa koyaushe, a daddafe ya qarisa abunda yakeyi ya jayota jikinshi yana shinshina wuyanta yace "kin hanani aiki" tayi murmushi tace "dama already ka gaji" ganin abubuwan da yake mata yana yawa yasa ta dan zare jikinta tace "can we talk? Gyara zamansa yayi lazily yace "why now? Meyasa yanzu? Tace "sorry jannah" yace "ina jinki" tace "me yake faruwa ne? Naji dazu kuna magana da ya jameel" ta kalleshi tana son karantan yanayinshi. Fuskarsa ba yabo ba fallasa yace "a ina? Tace "dazu bayan maghrib da kuka shigo gida" murmushi yayi yace "me kika ji? Juya idanunta tayi irin questions din sunyi yawa tace "yana tambayanka dalilin da yasa baka fada min wani abu ba" ta gyara zama ta fuskanceshi sosai tace "mene kake boye min? Yau kam ka fada min, kafin mu tafi mauritius naga kayi waya wanda magananka baiyi tsawo ba kace zaka kira, kamar baka son yin wayar a gabana, ina lura da kai. Ko abokiya zaka kawo min ne? Ta qarisa maganan yayinda wani irin abu ya tokare mata maqoshinta yana qoqarin sata kuka. A hankali sultan yake kallonta da dan murmushi a fuskarsa yace "tunda kinyi smelling ya kamata in sanar dake" ya kamo hannunta duka biyu yana murzasu a hankali yace "fatuhhh....."

 

Maman Fateey👯👯

[10:24PM, 9/26/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

75

 

Yace "fatuhhh" tayi shiru ta qura masa ido kirjinta na bugawa da sauri da sauri, yace "fateema" tace "na'am ina jinka" don ta qagu taji menene don zuciyarta na gab da tarwatsewa. Ya cigaba da murza hannunta yana cewa "ranar da jones nake magana don shi ya mana visa, so bana son kiji a lokacin ne" Tace "uhum" yace "fateey wai u ar pregnant" ya qura mata ido yana kallonta. Ta girgiza kai tace "wai? Kuma... oh god!! Don Allah ka fada min abunda yake faruwa,  nasan ba maganar ba kenan" wani siririn hawaye ya gangaro fuskarta ta share. Yayi ajiyan zuciya yace "wallahi maganan kenan, ranar da muka dawo su lubna ai sunzo, so anan jameel daya ganki yaga alamun masu ciki tare dake, so mun fita sallah yake gaya min, in kin lura muna cin abinci inata kallonki amma banga alamun komai ba" da sauri fatu ta shafa cikinta tana lalumawa kamar mai neman abu, tana cewa "da gaske inada ciki? To tayaya zan gane? ganin hakan bazai nuna mata komai ba ta kwaye rigarta tana dubawa, sultan ya zuba mata ido yayi tagumi, yace "kinga dalilin da yasa naqi fada miki kenan, don kar kizo ki sa rai alhali ba cikin gareki ba ki qara tada hankalinki" Ta dago ido tace "muje chemist mu siyo PT strip" yace "me kenan? Tace "abun gwada ciki ne" tashi muje" Ta miqe ta haura sama da gudu harda harhada steps, tana kulewa sultan ya dafe kanshi yace "ya Allah ka taimakeni, Yanzu in ba ciki bane sai tayi wata daya mood dinta bai dawo dai dai ba" fitowanta yasa ya juya yana kallonta, tasa zani da hijab, ta iso gurinshi tana wani dafe ciki tace "muje to" Ba musu ya dauki key din motarsa da yake kan kujeran suka fita. Da yake dare yayi wasu chemist din har sun rufe,  A.A Aliyu chemist suka samu a bude, ya barta a mota ya shiga, yace "ina son PT strip, abun gwada ciki" mutumin yace "guda nawa? Sultan yace "da guda nawa akeyi? Yace "da guda daya akeyi alhaji" Sultan yace "ok, a bani 5" aka bashi ya ciro kudi ya bayar ya koma mota. Fatu tana can tana jiranshi sai addu'a takeyi a zuciyarta Allah yasa ciki take dashi, sai a sannan ta tuno rabonta da tayi period tun tafiyansu mauritius, kuma cikinta ya dan tashi, amma ta danganta hakan da irin ciye ciye da cin abincin da takeyi kwanan nan, kuma dama tayi dan qiba.

Ya miqa mata ledan suka koma gida, kafin ya fito daga mota har ta shige gida, tayi fitsari a wani dan qaramin roba ta saka strips din duka tana ajiyewa, anan ya shigo bandakin yace "fateema ki nitsu fa" ta matso gurinshi tana kallon agogon hannunshi tace "nan da minti 5 zamu ga result" Zaiyi magana tace "shhh, muyi addu'a jannah, zuciyata tana ta bugawa, kaji" ta daura hannunsa akan kirjinta tace "kaji? Yace "ehh" fatu ta bata fuska tace "kamar kai baka damu ba" yace "ya zanyi? Kin kasa fahimta ta, banso fada miki ba, to yanzu tunda na fada miki dole in biye miki" kallon agogon hannunshi tayi tace "saura 3mins" shiru shiru har 5miins din suka cika. Ta kalleshi tace "ina tsoro, kaje ka duba" yayi ajiyar zuciya ya fara tafiya zuwa gurin ta riqo shi idonta taff da hawaye data kasa tantance na menene tace "zanje" ya matsa mata taje ta dauka bakinta sai addu'a take kwararowa, ta rufe ido ta bude a hankali... "P...popp...POSITIVE" wani irin tsalle ta daka sai akan sultan yace "what? Menene? Gabadaya ya kidime, kukan farincikine ya hanata magana, ya sauketa yaje ya duba, dukansu sun nuna lines biyu red, ya dauki pack din strip din ya karanta, "Alhamdulillah" ya dinga maimaitawa har ya iso gurin fatu wacce take daria ga hawaye shabe shabe a fuskarta yace "its true fateema, kinada ciki, Masha Allah, Alhamdulillah" Gaba dayansu sun kasa controlling farincikin da suka tsinci kansu ciki. (Shekara uku ba wasa ba, d'a kuma da dadi, Allah ka bawa wanda basuda shi Ameen) A bakin gado suka zauna kowa da murmushi a fuskarsa tace "jannah har yanzu na kasa gaskatawa, gani nake kamar mafarki nakeyi" yace "ba mafarki kikeyi ba, yau Allah ya nufe mu da samun abunda muka dade muna addu'an samu" sultan ya kira jameel a cikin daren ya fada mishi, fatu tana hanashi akan ya bari sai gobe amma yaqi don d'oki, har zai kira mammi ma fatu tayita roqonsa sannan ya bari, bude cikin yayi yana ta shafawa can kuma sai ya daura kansa wai zaiji heart beat din babynshi, da kyar ranar sukayi bacci don fatu gani takeyi ma sultan ya fita farincikin samun cikin.

 

Maman Fateey👯👯👯

[10:39PM, 9/26/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

76

 

Washe gari qarfe 10 suna gidan mammi wai daga nan zasu wuce hospital don fara anti natal, a palour suka samu amrah tana breakfast, da murnanta ta gaishesu, sultan yace "ina mammi? Tace "tana dakinta" yace "dear mu shiga" fatu ta noqe kafada tace "a'a nikam ina jin kunya" murmushi yayi ya shiga dakin mammi, bai jima ba suka fito tare da mammi, fuskarta annuri kamar wacce akayiwa bushara, fatu tayi sauri sauqowa daga kan kujera zata gaisheta, dagota mammi tayi ta zaunar da ita a kujeran tace "a'a fateema, ki daina aikin wahala, Allah ya miki albarka 'yan nan yasa ki sauka lafiya" amrah tace "mammi tafiya zatayi? Mammi tace "amrah abun farinciki ne ya samemu, fateema zata kawo mana d'a" amrah tayo gurin fatu da gudu zata rungumeta mammi tace "ke amrah me haka? Zaki bugeta ai, bana son irin haka" sultan da yake gefe yana kallon show din a ranshi yace 'an gamu da mammi yanzu kam' a fili kuma yace "fateema tashi mu tafi asibityn. Mammi tace "A'a ka barta ta huta, zuwa anjima zan kaita da kaina, tukunna ma wani asibity? Wani asibity ne suka fi bada kulawa? Da kyar sultan ya bari mammi ta hakura yakai fatu don yasan fatun bazata sake tare da mammin ba. Private hospital mai kyau ya kaita, doc ya mata tambayoyi ta bashi amsa yace za'a mata scanning. A gurin scanning dinne likitan ya kasa gane 'ya'ya nawa ne a cikinta, don clearly biyu ya gani amma ta gefensu yaga wani kaman babyn, yace "a bisa scanning da mukayi cikinta wata uku ne da sati daya da kwana 3, kuma 'yan biyu ne a cikin nata amma zata fara zuwa anti natal daga jibi thats kowanne wednesday don duba lafiyanta da abunda ke cikinta" sultan da fatu da suka kasa magana don tsananin mamaki don basu tsammaci cewa zasu sami 'yan biyu ba. Suna komawa gida aka fadawa mammi Again murna tayi kamar me, anan ta kira mummy ta sanar mata, ko minti biyar ba'a qara ba mummy ta shigo tana barka barka. Dangi aka kira ana fada musu fatu har abun ya fara bata kunya kamar a kanta aka fara haihuwa.

 

*4months 2weeks later*

 

2:12am na dare, sultan ne zaune ya qurawa fatu wacce ke kan gado ido da goran faro babba cike da madaran shanu a hannunshi yana dan jijjigawa don saboda ya dan huce, a hankali fatu take motsawa, idonta ta bude ta shafo rusheshen cikinta wanda girmanshi har abun kallo ne. Da sauri sultan ya isa gurinta ya taimaka mata ta zauna, ruwa ya fara bata ta kukure bakinta ta zuba a wani container da ya kawo daidai bakinta, straw ya saka a cikin goran kana ya bata tana zuqa a hankali har ta shanye tass,😳 nace kaii!!! Ta dago ido ta kalleshi ya mata murmushi tace "nagode" yace "nine da godia, don yarana suna wahalar min dake, ga ci kamar me" daria tayi tace "lafiya kenan" sai daya tabbatar tayi 30 mins sannan ya gyara mata kwanciya yace "kiyi bacci" shafa gashin kanta ya fara tana lumshe ido ko minti biyu bata qara ba kuwa ta soma bacci. A hankali ya tashi ya koma dayan side din yana tunano irin wahalan da suke sha aka cikin nan, fatansu dai Allah ya sauqeta lafiya....... tun daga ranar da suka fara zuwa anti natal ake mata scanning koyaushe ana cewa 'yan biyu, da cikinta ya cika wata shida aka turasu wani hospital a mata scanning don doc din da yake dubata he's confused yana ganin kamar babies uku ne, thats why ya tura su wani asibitin. A can da aka mata cewa sukayi 'yan uku ne kuma kosassu lafiyansu kalau, wani abun mamaki shine fatu batayi laulayi ba sai na ciye ciye, abinci kam tana ganin damarsa, kuma bata jimawa zata nemi wani. Da mammi taji haka tace to scanning din ya isa, Allah shi yasan komai. Fatu bata wasa da maganin da ake rubuta mata a wurin awo, sam bata skipping, sultan har tausaya mata yakeyi in yaga ta ajiye abinci a gabanta tana ci, watarana haka zata bude mishi tumbin yana ganin yanda babies din suke naushinta har abun mamaki. Da cikin ya cika wata 7 kuwa tashin dare ta fara wai yunwa takeji, haka zai tashi ya hada mata tea tasha amma baza'a jima ba zata qara tashi tace Yunwa, ana haka rannan kaka ya ziyarceta ya kawo mata maganin shawara da ake bawa masu ciki, anan ya kawo musu madaran shanu mai yawa a gallon jarka, a ranar da dare fatu ta tashi tace a bata madaran, sultan ya kawo mata, da yake an saka shi a fridge yayi sanyi tace a dumama mata, dolenshi ya sauka ya duma mata ya juye a gora ya bata, to a ranar bata qara tashi neman abinci ba, daga ranar yake aika mata nonon shanun daga kumo. Marking din lokacin tashinta yayi, kafin ta tashi zaije ya dumama ya dawo ya zauna yana jiranta har ta farka ya bata tasha. Mammi tayi tayi ya dawo da fatu gida amma sai yayita mata kwana-kwana. Yau dai EDD din fatu saura kwana 8, yayi niyyar maida ita gida gobe don kar abu ya tashi baya gida. Dauke wutan da akayi ne yasa ya dawo daga tunanin da yakeyi, da sauri ya dauki handa fan ya fara mata fifita don bata son zafi ko kadan, ba'a yi minti 3 ba maigadi ya kunna generator, anan sultan ya ajiye handfan din ya shige toilet ya dauro alwala, ya gyara mata pillow yayi kissing goshinta kana ya fara nafilfili Allah ya sauqeta lafiya.

 

Maman Fateey👯👯

[7:39PM, 9/29/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

77

 

Washe gari da safe Tana zaune akan gado tana shan Apple shikuma yana hada mata kayanta da zata buqata. Kallonshi takeyi cike da tausayi don ba qaramin qoqari yake yiba, tunda cikinta ya girma ya hanata girki duk da ma sunada mai wanke wanke da shara, Haka kuma koda zai bukaceta ya dinga tambayarta kenan cewa "bazan takuraki ba? A'a "are u in d mood? Da ire irensu, tana mugun respecting dinshi akan hakan. Sultan mutum ne wanda take alfaharin samun shi a matsayin miji, yana tausaya mata kuma bashida saurin fushi. Gashi baya gajiya da mata hidima, takanas ya fita waje ya musu siyayyan haihuwa wanda kwanan shi uku ya dawo wai tunaninta ya hanashi zama. Laluma plate apple dinta takeyi taji wayam, wato har ta shanye apples 8, dai dai nan ya juyo yana kallonta da murmushi a fuskarsa yace "a yanko miki wani ne? Ta girgiza kai tace "a'a, na koshi" yace "to ki tashi in miki wanka mu tafi" tace "to" A hankali ta miqe yayinda shi kuma ya dauko mata towel ya tayata cire kaya yana daura mata towel din. Tace "jannah" ya dago ido yace "maman uku yadai? Murmushi tayi tace "thank u" bai ce komai ba ya jata zuwa bathroom. Don ya saba da irin hakan, koyaushe tana cikin nuna jindadin ta ga yanda yake nuna mata kulawa, hakan shi kuma kan qara masa qwarin guiwa wajen kyautata mata. Wanka sukayi amma fatu na lura da sultan akwai abunda yake damunshi. Bayan sun fito ne take tambayarshi lafiya yace ba komai. Bata fuska tayi tace "ka fada min don Allah" zaunar da ita yayi a bakin gado yace "can u help me? Anan ta gano  bakin zaren, don yau kusan 3wiks rabon daya nemeta wanda tasan duk a dalilin tausaya mata da yakeyi ne, lallai tana da sonkai, tasan yanayinshi ba mai juriya bane amma ta mance dashi tana enjoying sangartata da yakeyi. Murmushi tayi tace "I am sorry jannah, nayi sonkai da yawa...."  bata qarasa magana ba taji an rufe mata baki da lips nasa........

Sai da yaji he's okey ya tashi ya shiga bandaki. Bayan ya fito ya kwaye bargon data lulluba dashi yace "taso kinji, sorry dear" da kyar ta miqe don wani irin ciwo da bayanta ya fara tun dazun. Zai bita bathroom din tace "ba komai zan iya" ganin yanda take cize baki tana riqe da bayanta yace "ko dai nayi hurting dinki ne? Tace "a'a" tare da shigewa bandakin. Da kyar ta samu tayi wanka don irin ciwon da mararta kuma ya fara. Tana fitowa ta samu ya gama shiri har yasa kaya ya ganta wani iri yace "na sani na ji miki ciwo, I am so sorry, ya Allah" ya dafe goshi, tausayinshi taji don haka tadan fuske duk da irin ciwon da takeji tace "kadan ne fa, kuma ya fara tafiya ma" bai saurareta ba don yanda yaga take hada gumi yasan tana jin jiki,  daguwar riga ya zura mata yace "mu tafi hospital" Magiya ta fara mishi wai ita bazata je hospital kar suce haihuwa ne, tana tsoron haihuwa balle ita da aka ce yan uku ne. Kafin ma su isa asibiti abu ya qara jiqa, don yarfe hannu takeyi tana dafe mararta. A gaggauce nurses suka karbeta aka shiga da ita labour room, doctor da take dubata ya kira a waya ya fada mata ya kawo fatu asibity, ko minti biyar bata yi ba ta iso bakin labour room din don dama tana cikin asibitin. Safa da marwa ta samu sultan yakeyi yana kiran sunan Allah sai kace shine mai labourn. Da dan murmushi ta gaisheshi ko amsawa bai yiba yace " ki shiga ki dubata, inaga ba haihuwa bane doctor, coz nine na jawo" da dan mamaki a fuskarta tace "kamar ya? Kamar bazai fada mata amma yaga no need da boye boye shi dai fatanshi a Magance halinda fatu take ciki don haka yace "I...I have.. I have se* with her" doc tace "ba matsala ai hakan, kar ka damu" da hanzarinta ta shiga labour room din yayinda sultan ya cigaba da safa da marwa, anan ya kira mammi ya shaida mata suna asibiti. Minti goma doc ta fito tace "haihuwa ce coz har ta kai 5cm" cikin rashin fahimta yace "me 5cm?  yanzu haihuwa zatayi? Zan iya shiga? Ganin yanda ya rude yasa doc din ta fara kwantar masa da hankali, sai anan ya tuno cewa ai EDD dinta bai cika ba, yace "doc edd dinta next week ne" tace "wasu suna rage kwanaki wasu kuma suna qarawa. So yau Allah yayi zata haihu" Anan mammi ta shigo itama daka ganta zaka san hankalinta a tashe yake.

 

Maman Fateey👯👯

[12:56PM, 10/1/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

78

 

Gaishe da mammi yayi ta amsa tace "ba dai tun jiya abun ya fara mata ba? Yace "a'a yau da safe har mun shirya zan kawota gida" harara mammi ta watsa masa kana ta dubi doc din ta bata wani ruwa bottle din Faro tace "ga wannan ruwan addu'a ne a bata tasha" da sauri sultan ya karba yace "doc zan iya shiga? Tace "ehh zaka iya" mammi da mamaki ya gama rufeta tace "ya zaka shiga gurin haihuwa? Kafin ma ta qarisa sun qule shida doc. A kan gado suka samu fatu tana jijjiga kai tana yarfe hannu, ganin sultan ba qaramin qwarin guiwa tajiba, ya isa gurinta ya kamo hannunta yace "INA TARE DA KE, ki dinga addu'a kinji? So sorry dear" Gyada mishi kai tayi cikin baqar wahalan da take ji, ruwan ya bata, ta girgiza kai yace "na addu'a ne mammi ta kawo miki,  kisha kinji? Jin ance na addu'a ne ta karba tare da bismillah ta shanye. Shiru shiru kusan 20mins.    

Ganin fatu har ta fara nishi nishi doc tace a gwada mata cm nawa take. Daya daga cikin nurse dinne tazo gwada fatu sultan ya tareta yace "what are you doing? Me haka? Da kyar doc ta fahimtar dashi sannan ya yadda. Fatu ko ta kansu bata bi. Nurse din tana gwadawa ta fadawa doc, tace "ina kayan haihuwa? Don mun muku list din abunda muke buqata" sultan yace "yana mota" da sauri yaje ya dauko ya kawo mammi na kallonshi yazo ya qara shigewa. 30mins da haka ta haiho babies dinta hudu duk maza, fatu ta wahala sosai. Murna gurinsu ba'a cewa komai. Su da akace musu uku sai ga hudu. Mammi kam ta rasa inda zata sa kanta don murna, dukansu sai hamdala sukeyi tayi (wani jinkirin ma Alkhairi ne) Awa hudu da haka aka sallamesu bayan an tabbatar da lafiyan maijego da babies. Kafin suna 'yan uwa da abokan arziki sunzo barka. Yara tubarkalla kyawawa dasu tula tula, kama sukeyi da babansu sosai. A ranar suna suka ci sunan Abu-bakr, Aliyu, Usman da Umar. Anyi shagalin suna na gani na fada, mai jego da babies sunyi kyau cikin shiga ta alfarma. Mutanen garin modibbo suma sunzo suna.

 

Maman Fateey👯👯

[11:09AM, 10/2/2016] Mum Fateey: 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

🌻🌻🌻FATU A BIRNI👜👠 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻         

Na Mrs Aslam Haidar

79

 

Su xahra amarya, bizzy mai ciki, (suma sunyi aure) lubna da salma qawayen mai jego sun entertaining baqi sam barka,'YAN MUMBARI tare da MUM FATEEY FANS suma sun halarci wannan bikin suna. Da yamma akayi walima inda Malama Asma'u (maman Al'ameen) ta gabatar da wa'azi kan tarbiyatan da yara bisa yanda addinin musulunci ya tanadar. An ci, ansha anyi guzuri, su Mrs umar, Autar hajia, ummi Aisha, Jabo, da jegal sunfi kowa kwasar abun suna. An raba soveniers kamar ba gobe, taro yayi ansha pictures kala-kala.

 

 *11 years later*

 

Fatu na gani da dan jaririn cikinta wanda bazai wuce 5 months ba, a kan cinyanta plate ne cike da gyada dafaffe tana barewa tana ci. Gefenta kadan sultan ne shima zaune suna kallon wani indian film mai suna "SULTAN" inda SALMAN KHAN ya fito a wrestler. Da alama dukansu hankalinsu ya tafi ga kallon don fatu ko kallon gyadar batayi take barewa tana turawa a baki. Sai ta bare goma tasa a baki, kana ta baro daya ta bawa sultan. Gama film din yayi daidai da Qarewan gyadan fatu ta laluma taji wayam sai bawon gyada kawai. Sultan ya juyo yace "film dinnan ya hadu...." ganin plate ba komai yasa ya waro ido yace "ba dai kin cinye ba? Ta turo baki tace "mun cinye dai" ya lalumi bakinshi da harshen shi yace "kin cinye dai, don nikam banji alaman gyada a bakina ba, matar nan zanyi maganinki, daga yau na siyo abu sai na ci nawa a hanya before na kawo Gida, ko samarin gidan nan baki ragewa ba" daria tayi sosai tace "in kana kiransu samari abun har daria yake bani" tashi yayi ya nufi door inda ake bugawa yace "naga haka kike kiran waleedah (mai sunan mammi, shekaranta 8, mammi ta dauketa tun da amrah tayi aure) fatu tace "waye ne? murmushi yayi yace "inaga sun dawo" a hankali ya bude ya leqa, wasu kyawawan yara yan kimanin 11yrs su hudu na gani bayansu karamar yarinya da bazata wuce 4yrs ba tana matsar  kwalla, sultan yace "kun dauko ta ko? Tare da basu hanya suka wuce, daukan ta yayi ya saba a kafada yace "Ameera munyi missin dinki" ta turo baki Abu-bakr yace "bata jin magana sam, boarding school zamu kaita, da kyar muka banbareta a jikin Al'ameen din aunty salma shima yaje gidan granny" fatu ta tashi tace "wa za'a kai boarding school? Katti daku ba'a kaiku ba sai yar yarinyar nan? To akul dinku naji kun takurata mata, yarinya yar qarama da ita kunbi kun sa mata ido....." karban 'yar tayi taja hannunta suka shige daki tana fadanta. Sultan dai baice komai ba ya samu guri a kan kujeran ya zauna kana ya dubi zaratan samarinsa wanda inka gansu zaka dauka sun kai 13 ko 14, Aliyu wanda duk cikinsu yafi zafi yace "mommah tana sangarta Ameera" Usman yayi murmushi yace "mai sunan mamanta ne ai" zama sukayi dukansu a kan kujera sultan yana binsu da ido cikin tsantsar qauna yace "ba sangartata take yi ba, shekarunta 4 ne, wanda komai a yanzu cikin lallami da wayo za'a nuna mata ba by force ba, kuma haka mommah dinku ta raine ku har  girman ku. And gashi kun tashi a nitse da ilimi both Arabi da boko. Sons I am proud of your mom and i trust yanda take tarbiyantar da yara" Jinjina kai sukayi cikin amincewa anan suka fara maida zance. Gurin driver taje tace ya kaita gidan granny inji momma, shi kuma without bincike ya dauketa ya kaita. Dawowanshi yayi dai dai da dawowan sultan yake tambayrsa inda yaje, driver ya fada mishi, anan sultan ya mishi warning kar a qara daukanta in ba babba yayi magana ba. Shiganshi gida yasamu samarinshi suna taya mamansu hira, ya fada musu suka tafi dauko ta don washegari monday akwai skul. Shine suma suka yi zamansu sai yanzu suka dawo.

 

A hankali fatu ta sauqe ameera akan gadonta wacce take bacci. Ta lullube ta tare da mata addu'a ta kashe wutan dakin kana ta fita. A falon qasa ta tarar da samarin suna kallo, tace "Umar, Usman, Abu-bakr, Aliyu ku tashi kallon haka ya isa, gobe kunada skul, hope kun gama all assignments dinku? Usman yace "yess mommah" Umar yace "dama ni na fara jin bacci" ya miqe tareda kashe socket din. Daya bayan daya suka mata peck suna cewa "gudnight mommah" Suka shige dakinsu dake falon yayinda na Ameera yake sama. Zata juya taji mutum a bayanta yace "good morning mommah, yau tilldawn zamuyi, don sai kin biyani gyada na" Daria sukayi suka haura sama zuwa dakinsu.

 

AND THEY LIVE HAPPILY EVER AFTER.

 

ALHAMDULILLAH

 

GODOYA

Godia ya tabbata ga Allah daya bani ikon gama wannan littafi. Abunda na rubuta dai dai Allah ya bani ladansa kuma ya amfane mu gaba  dayanmu, wanda nayi na kuskure Allah ya yafe.

 

Godia Ga dukkan Groups da suka so fatu.

M Jabo mumbari da Duniyar novels

Mum Fateey Fan's

Mrs Umar hausa novels

Hausa novels (na maman safwan)

Mace Mai Aji

Be his star

Matan Aljanna da

Matar So

Hausa novels (na maman safwan) da duk sauran groups da bansa sunansu ba. I really appreciate ur love nd support.😘😘

 

JINJINA

Jinjina ga sauran 'yan uwana writes. Allah ya saka muku da mafificin alkhairi Allah ya qara basira.

 

Gareku masoyana, nagode da dunbin qaunar da kuka nuna mini tare da FATU A BIRNI. Mum fateey tana sonku sosai nd I Respect u all. Allah ya bar zumunci ya hada kanmu a Aljannatul Firdous. Ameen

 

KUNA RAINA

Salmatun inna, xaynoobiey, sara2 wsg, ummi b, xahrah levels, miss rukeey, stew, wasilatBMI, Ayeesh naner, bizzy, mrs al'ameen, umm marwa, maman zahra, falmata abubakar, ummy naseer jibia, maman dota, maman jawaheer, maman Al'ameen, shatoo, Aysha (ummu abdul) khairie India, Maman Dr, da duk wadanda bansa sunanku ba, kuna raina bil hakki.😘😘

 

Kinfi kowa qaunar FATU, Aunty Zainab (maman hauwa) Allah ya sauqeki lafiya muje cin shinkafa. Rengemm👯👯😅

 

SADAUKARWA

Na sadaukar da wannan littafi ga mahaifiyata Hajia Aishatu Baffa Aliyu

Allah ya qara tsawon rai mai albarka Allah ya bar mana ke Hajiata ya raya miki 'yayanki. Ameen. Luv u mommah.😘😘

 

Maman Fateey👯👯

adsense 2 here
Share:

Burodin ayaba

Barkanmu da ganin wata mai girma tare da fatan kuna cikin koshin lafiya. A yau na kawo muku yadda ake yin burodin ayaba. Za a iya gwada wa a lokacin yin buda baki ko kuma don yi wa bakin da aka gayyato shan ruwa. Kamar yadda muka yi muku alkawari , za mu cigaba da kawo muku nau’ukan girke-girke daban-daban.

Abubuwan da za a bukata:
•Fulawa
• kwai
• Suga
•‘Baking powder’
•Ayaba
•Madara
•Bata
Hadi:
A samu ayaba biyu a kwabasu da cokali mai yatsu, sannan a zuba fulawa a kwano sannan a zuba ‘baking powder’ da suga da madara sannan a kwaba. Bayan haka, a zuba bata kamar cokali biyu sannan a kwaba sosai. Sannan a fasa kwai biyu da wannan kwababben ayabar a cikin fulawar da aka yi masa hadin suga da sauransu. Sai a gauraya don su kwabu. Sannan sai a dauko na’urar gasa burodi a zuba sannan a saka a gidan gasa burodi. Bayan mintuna arba’in da biyar, sai a cire.
Za’a iya cin wannan hadin burodin da shayi bayan an sha ruwa. Kuma za a iya aika wa makwabta domin su dandana sabon salon burodi. A sha ruwa lafiya.


MAJNOON hausa love novels


Matashin saurayine mai kimanin shekaru 30, gashin kansa duk ya kudun dune, Launin fatarsa ya chanza saboda dattin dake jikinsa rigarsa duk ta yage, Farine amma saboda tsabar datti har farin yafara dishewa, fatar jikinsa dukta jeme saboda zafin rana hakama tufafin dake jikinsa, amma hakan bai hana kyan fuskarsa fita ba, kyankywane duk da cikin sigar hauka yake...... Read more

Mutane uku ne a duniya

1. Wasu kamar guba ne gudunsu akeyi. 2. Wasu kamar magani suke, ba a nemansu sai ta baci. 3. Wasu kuma kamar abinci suke, akullum dole a nemesu. Ya kai dan uwa mai daraja, kayi kokari ka zama cikin wadanda akullum ake nemansu saboda amfaninsu. Allah yasa muna cikin wadanda ake nema akoda yaushe, Albarkar Annabi {S.A.W}

Talla a Gidan novels


Litattafan da Muka Kawo Muku

Tunatarwa

ANNABI (SAW) yana cewa:

Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Ya Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani.
Kasa mucika da imani.

Kada ka rama cuta ga wanda ya cuceka!

kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka kai kayi hakuri zaka samu abu biyu sakamakon hakan *na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. *Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

Visitors

Translate

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Contact Form

Name

Email *

Message *